Zafin Kai 10

 


_Arewabooks@Mamuhgee_

10


*_MAAB LUXURY HOME🔥💯_*


*_ASSALAMU ALAIKUM JAMA’AR KWARAI JAMA’AR ZAFAFA BIYAR_*


*_KAMAN KO DA YAUSHE DA MUKE KAWO MUKU ABABEN AMFANI GANGARIYA KUMA DAKI BARI MASU AMINCI A KUDADE KALILAN_*


*_YAU MA MUN ZO MUKU DA TALLAN BABBAN SHAGON NAN DA KE KAWO MU KAYAYYAKI NA KASAR GERMANY!! KUNSAN DAI GERMANY SUNE AGABA A FANNIN KAYAYYAKI MASU KYAU DA KARKO_*


*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*



  *_SUN KAWO MUKU DALLADALLAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAWATARWA DANA KITCHEN MASU HASKA DAKUNAN GIRKI… KWASHA KWASHA_*


*_SU DIN KARSHE NE A DUNIYAR KAYAYYAKIN GIDAH DANA KITCHEN NA KECE RAI NI… INA UWAYEN GIDAH, AMARE? ANTOCI, KAWUNNI, YAYYU MAZA, KANNE DA MA IYAYEN MU MAZA?_*


*_KU ZO A DAMA DA KU A WANNAN DAMAR ME DAUKE DA DIMBIN KAYAYYAKI MASU KYAU A KUDI DEDE MISALI WANDA KOWANE ZAI IYA MALLAKA IYA KARFIN SA_*


*_KU ZIYARCI SHAGON DA KE A KANO.. TITIN AHMADU BELLO WAY_*


*_KO KUYI ORDER DA GA SHAFUKAN SADARWA TA INSTAGRAM:@Maabluxuryhome_*

*_FACEBOOK:@maabluxuryhome_*


  *_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH,, INGANCI DA RAHUSA, KYAU A DADE ANA AMFANI DA SU SAI KAYAYYAKIN MAAB LUXURY HOME_*


 *_A NUMBER ONE  STOP SHOP FOR HEAVENLY ORIGINAL HOME DECORS AND KITCHEN UTENSILS_*


*_MAAB LUXURY HOME GOT YOUR HOME AND YOUR KITCHENS COVERED… JUST A VISIT/CALL/DM AWAY_*


  *_08034631010 MAAB LUXURY HOME👈🏽_*




**********

Suna isa dakinsu suka tararda Annensu zaune tana hawaye masu dumi da ciwo sbd duk abinda yake faruwa tsakiyar gidan tana ji amma batada iko ko daman fitowa.

Suna shigowa ta bisu da ita batareda ta motsa ba dan batasan me zatayi ba yanda zuciyarta ke radadi.


Zaunar da Sumayyah Benazir tayi tareda zubewa gefenta itama saida sukai shiru kukan Sumayyah kawai ke tashi tsawon lokaci kowa da damuwar datake yankar zuciyarsu.

Kusan awa daya a hakan kafin Benazir da Anne suka fito sukai Alwala suka dawo daki kafin itama Sumayyah din ta fito cikin azabar tayi alwala ta koma dakin.


Sallah kawai sukai tareda addua suka fito fara aikinsu gadan gadan harda Sumayyah din sbd baa basu damar hutawa daga aikin ba koda ciwo kuwa.


Sai guraren 9 suka gama wanda suka iya suka shirya Hande ta basu abincin karyawan da Ababa ya rage sukaci suka fice zuwa makaranta lokacin kusan Benazir harta rasa lecture dinta na 8 to 10 suna isa ta shiga ta 10 to 12 Sumayyah kuwa kasa shiga lectures tayi sbd wani irin azabababban zazzabi mai qarfin gaske daya rufeta,

Qafarta wani irin radadi da zogin azaba take mata sbd iron din da Ababan ya wurgeta dashi ya kona tafin qafarta sosai ba daman ta nuna azabar datake ciki a haka tayi aiki kafin su fito gashi zuwa lokacin kafar gabaki daya ta cabe daqyar ta iso makarantar ta nunawa Benazir babu wata matsala ne da qafar sbd ta samu ta shiga lectures nata da yanzu bata samun attending yanda ya kamata amma kam tana cikin mawuyacin hali.


A hankali ta daddafa ta kebe kanta cikin mawuyacin hali ta isa inda suka saba kebe kansu ta zauna jikinta na tsananin rawa ko numfashi daqyar take ja,

Dan dago kafar tayi a hankali ta leqa inda konuwar take.

Sanyayyan Numfashi ta sake jikinta na sake daukan rawar zafin zazzafi 

Qafar tini tafara yan ruwa masu maiqo sbd sosai iron din ya shigeta.


Jajir idanuwanta sikayi tana kasa fidda koda hawaye ta samu sassaucin radadin datake ciki cikinta da fili.


Zamewa tayi ta kwanta yashe a gurin azabarta na qaruwa idanuwanta na qanqancewa,

Tsawon lokaci ta dauka ahakan kuma kowace daqiqa tana wucewa ne tareda qaruwar azabarta.


Sama sama take jiyo hayaniya da maganganun mutane masu wucewa,

Tashi takeson yi ko zata iya kai kanta gurin Benazir sbd ciwon yafara fin karfinta yasha ruwa ne caba caba gurin aikinsu na safe hakama duk ta takesa ya cabar da qafar gabaki daya ya zabure da ciwo baji ba gani.


Daqyar idanuwanta dasuke kanne suka budu tana sake kokarin tashi sedai hakan sam yakasa samuwa Na idanuwanta dake rufewa ahankali tana neman somewa sbd tsanani da zafin azaba.


********Bayan Awa bakwai

A hankali ta bude idanuwanta da sukai mata wani irin nauyi sbd baccin wahala da jan azabar dasukai har lokacin basu washe ba.

Akan Benazir dake gefenta idanuwanta suka fara sauka wadda itama nata idanuwan suke jajir sbd tsananin tashin hankali biyu dayake dabaibaiye da ita,

Na ganin yar uwarta a wannan halin dakuma na zaman dasukeyi a tsadaddiyar private asibitin wanda shi kansa sbd gudun asan halin da yake ciki ya sanyashj kawosu wata asibitin ba KAANTE SPECIALIST,

Babban tsoro da mafi tashin hankalinta shine sikai magrib Sumayyah din bata farka ba dan kuwa ko a bayanta ne zata goyata su isa gida kafin magrib din matuqar bata farka ba.


Ganin budewan idanuwan Sumayyah a kanta ya sanyata sake ajiyar zuciya masu karfi a jejjere tareda rintse idanuwanta da sukai jajir Allah ne kawai yasan a tsananin halin data share wainnan awannin tana jiran farfadowar Sumayyah din,


A rayuwarsu bata taba tinanin zasu samu kansu a hali irin wannan ba na zuwa wani gurin neman lafiya kuma a qarqashin kulawan wani namiji wanda ko a tsautsayi Ababa yaji ko ya gano hakan tabbas Allah ne kawai zai ceto su daga mummunan qanin kisar da zaiyi musu.


Daga ita har sumayyah ba da izini ko saninsu Bilal kaante ya dauko sumayyah din ba ya kawo asibiti

Seda ya kawota asibitin bayan ya tsinceta a halin datake ciki a some har saida aka gama yimata komai kafin ma ya koma makarantar ya nema Benazir ya sanar mata suka taho asibitin tare wanda wannan shine karon ta na farko shiga mota.


Rayuwarsu basa fita kaman yanda aka sani,

Sunyi rayuwar karatun primary da na secondary har sukayi suka gama a qafa suke zuwa su dawo a qafa,

Tunda suka gama basa fita koina kullum suna gida a kulle kaman kayan sata,

Yanzu da suke jamia bai taba basu abinda zasu hau mota ba kullum a mashin suke zuwa kuma overload sukeyi shiyasa ko daya nada lecture daya dayan nada fiyeda hakan dole suke jiran juna komai dadewan da dayan zaiyi kuwa sbd Ababa bai taba yarda suna dawowa daban daban sbd kudin abin hawan.


Sumayyah data juyar da idanuwanta da qyar suka sauka kan Bilal Kaante dake tsaye bayan Benazir yana kallonta cike da kulawa da damuwa harma da mamakin halin daya sameta,


Ganinsa yasa hankalin sumayyah dawowa jikinta da sauri ta yunqura ta tashi zaune tana kallon Benazir jikinta na daukan rawa ita kanta Benazir datake cikin halin tashin hankali har lokacin matse take dasu bar asibitin da Bilal din su koma gida da gaggawa.


Saukowa gadon Sumayyah tafara a rikice tana cewa Benazir su tafi gida kada Ababa ya rigasu komawa gidan duk da Hande ko sunr rigasa komawa saita fada masa amma sassauci zai samu idan sun rigasa komawa din.

Benazir da sauri ta miqe tsaye tana kamata ba bata lokaci suka fara kokarin guduwa hankulansu a tashe sbd sam babu wanda yake cikin nutsuwarsa bare wani tinanin da ba nakomawa gida ba yanzu yanzu.


Cikeda mamaki Bilal ya matso ya dakatar dasu yana cewa


"Meye hakan kuke kokarin yi?

Tayaya zata iya taka qafafun nata ta isa gida musamman wannan rawar jikin da kukeyi tana taka qafar zata qarasa tadawa kanta wani matsalan.


Daga Benazir har sumayyahn babu wanda ya iya dagowa ya kallesa sai shiru da sukayi dan dai bazasu iya tsayawar ba hakama bazasu iya qalesa su tafiyarsu ba sbd taimakon da yayiwa Sumayyah din ta saidai itama kila su rasata.


Benazir ce daqyar ta iya bude baki cikin girmamawa sosai kanta a qasa ta basa hakuri tareda masa godiya sosai akan abinda ya musu din.


Kallon Sumayyah datake tsiyayar zufan wahala da azabar tsayuwar datayi akan qafafunta yaji zuciyarsa bazata iya dauka ba dan haka kai tsaye ya kai hannunwan ya maidata zaune kan gadon tareda durqusawa ya kamo qafar ya duba yana jin tsakan jikansa na tashi sbd yanda gurin ya sake cabewa take da yar tsayuwar datayi to bare tace zata taka zuwa gida.


Cikin fada ya kalli Benazir data sake daukan rawar jiki zuciyarta na bugawa kaman zata faso kirjinta ganin yakai hannunsa kan sumayyah wadda itama kusan kanta ya kusa juyewa sbd tsoro da firgicin jin hannun wani namiji a jikinta take tafara kokarin rasa numfashi sbd tino Fuskan Ababa idan ya san hakan.


Benazir din da Bilal sukai kanta suna girgizata 

Sake jij hannunsa jikinta yasata qarasa gigicewa tana neman rasa hankalinta 

Benazir da sauri ta janye hannun Sumayyah din daga hannunsa tana kasa kallonsa ta miqe tana ce masa gida kawai zasu tafi.


Kama sumayyahn tayi wadda ta ringa taka qafafunta cikin azabar datake jin gwara ita da wadda Ababa zaiyi musu idan yarigasu isa gida.


Bilal mamakinsa qaruwa yayi tareda wani irin tausayinsu da soyayyar Sumayyah din mai qarfi na sake mamaye zuciya da jininsa dan kuwa duk takun ta daya har cikin tsakiyan zuciyarsa yake jin radadinta.


Suna fitowa harabar asibitin bai tsaya komaiba ya qaraso gurinsu ya kama sumayyah din ya isa da ita motarsa ya bude ya sakata a seat din gaba ya rufe ya kalli Benazir datai mutuwar tsaye kai tsaye ya nuna mata bayan motar fuska a daure yace ta shiga.


Daga inda take tsaye bata motsa ba sbd wannan wani abun ne da bazai taba yiyuwa ba gashi kai sumayyah cikin motarsa ya gama firgita duk wata qarfin zuciya datake dashi.

Ganin bata motsaba itama ya dawo inda take ya kamota ya bude bayan motar ya sakata sbd shi rayuwarsu da sukayi a turai yasa bai tsaya tinanin komaiba ya kama sumayyah dan daukanta a matsayin matarsa insha Allah,

Ita kuma Benazir ya janyota ne sbd yariga ya sakata matsayin daya da Aleeyah kanwarsa.


Yana shiga motar bai tsaya sauraran tsananin tashin hankalin dasuke cikiba ya tada motar ya fice daga asibitin.


Tinda ya tinkari hanyar gidansu kowaccensu ta rasa motsi sbd sunsan yau Alkiyamarsu ta tsaya.


Wani babban chemist ya tsaya ya siya magani masu yawa da aka rubuto ya qaraso har hanyar dajin gidansu yayi parkin daga nesa dayake duhun magrib ya fara suka fito ya miqa musu ledan maganin A tare suka girgiza kai suna cewa bazasu iya tafiya dashi gidan ba.


Sumayyah ya zubawa kyawawan idanuwansa yana kwatanta radadin datake ciki sai kawai ya bude motar ya fito yana cewa" muje na kai maganin da kaina"


Suna jin hakan sumayyah ta fashe da wani irin wahalallan kuka ita kanta Benazir hawaye tafara batareda ta sani ba take suka zube qasa suna rokonsa kaman bayin da zaa cirewa kai.


Kallansu yayi ransa na suya sbd zuwa lokacin baya kaunar ganinsu a irin hakan.


Kallon Benazir daya fahimci itace qanwa amma itace ke fadan yanda sumayyah din zatayi yace


"Idan har bakwason naje da kaina gidan to sai kunyi alqawarin yarda da kullum zan kaiku asibiti aduba ciwon ana dressing harta warke idan ba haka ba zata iya rasa qafarta gabaki daya.

Idan kun yarda shikenan idan ba hakan ba a ynxu zan biku har gidan nayi bayanin yanayin ciwon nata.


Babu wani tinani ko nazari Benazir ta gyada masa kai ta amince sbd yabar gurin kada mummunan kaddara tasa wani ya gansu kokuma muguwar kaddara tasa ya bisu gidan.


"Kin tabbatar?" Yafada yana kallon Benazir din wadda tini suka fara tafiya hankali tashe ta sake gyado masa kai suna jefa qafafunsu cikin sauri hankali tashe.


Wani irin sanyayyan Numfashi ya sauke tareda komawa cikin mota ya zauna yana kallonsu ta mirror har saida suka shige kwanar gidansu.


Tayaya 'yaya mata daya kamata su zama zinariyar kowane Ahali ace suna cikin irin wannan tsoron mai muni?

Meyesa iyayensu ke musu tsanani haka wanda ya ciresu daga lafiyayyun mutane sbd tamkar Mujiya suke acikin mutane.

Tada motarsa yayi yabar gurin yana sake jinsu acikin ransa fiyema da baya dan kuwa a yanzu bayajin zai iya janyewa daga kaunarsa ga Sumayyah.

#MAMUH#

#DD KAANTE 

#KAANTEs

#BENAZIR

#BILAL KAANTE 

#ABABA

#HOT LOVE

#BILLONAIRES

#CONTRACT#MARRIAGE#LIFE#ROMANCE


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR 'KASHI

Safiyya Huguma


-FURAR DANKO

Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at

09033181070

09032345899


Zafafa🫶🔥🔥

No comments

Powered by Blogger.