Alkawarin Zuciya Complete Hausa Novel


 💫  ALKAWARIN ZUCIYA  💫


      PROMISE OF THE HEART 💔



          ✍🏻M SHAKUR



1️⃣

~UK~

Tundaga nesa take leke babban building din datake dumfara tana bin uban tulin cars din wajen da kallo kaman akwai abinda take nema kafin daga bisani idanuwanta su sauka kan wata white Bentley car, gashinan kar kar ko alamun a single dust babu ajikin motan, ajiyan zuciya tasauke ahankali murya chan kasa tace “Alhamdulillah he’s still around” sanan tashiga sauri takarasa gaban wajen da ake kira da Cozy, harzata saka hannu tabude kofan tashiga tadanyi jim tsaya kafin ahankali tabi jikin ta da kallo tana sanye dawani white jeans daya kamata tsam dawata yar dark blue top mai shegen kyau wacce da kadan tasauka daga kan cibiyanta, saidan gyalen data yana kanta white shima dayamata kyau sai gashin kanshi dakenan kusan rabi awaje anmata kalaba da attachment kanana dayamata kyau shima, hannunta rikeda wasu books guda biyu dakuma phone nata kirar iPhone 13, sai wata yar karaman jakan datake rataye da ita, ajiyan zuciya takara saukewa kana ganinta kasan she’s nervous sanan ahankali tasa hannu tabude kofan wajen tashiga ciki.



Hadaden eatery ne and bar mai shegen kyau, babu wasu mutane dayawa awajen wayanda suke wajen yawancinsu turawa ne fararen fata maaikatan wajenma fararen fatane hakan yasa zaka gane wajen na bature ne, ahankali take tafiya tanabin wajen gabaki daya da kallo da gefen idanunta, kafin takarasa gaban kanta taja kujeran wajen ta zauna sanan tasauke books dinta agabanta da wayanta, daidai baturen Bar attendant din yakaraso yana kallonta yace “what can I get you miss” dan waigawa tayi kaman tana neman abu awurin tace “Pierre Zēro Rosé please, two shot” ganin duk tana maganan ne batare datama kalleshi ba yasa yace “gotcha” sanan yajuya yakoma yadauko wine din datai order yazuba mata a cups guda biyu sanan yadawo gabanta ya ijiye yace “here we go” dan juyowa tayi da sauri takallai sanan tasauke jakanta da sauri tadauko kudi taba shi tace “keep the change” kafin ma yay magana tasake juyarda kanta tana bin mutanen wajen da kallo one after d other…..



“Kai Zayn look” wani hadadden chocolate guy daga tachan karshen babban falon wajen da aka cikada kujeru ne kowa na zaune yana abinda yake yataba wani kyakkywan thick farin guy dake zaune kan kujera ya lumshe idanu pipe din shisha na bakinshi yana zuka yana fitarda hayakin ta hanci, yana sanye da riga da wando both black na LV, farine shi kal yanada cikan jiki dayake rigan dayasa short sleeve ne hakan yafito da kakkauran murdadden hannunshi, irin guys dinan ne masu manyan gabobi dakuma murdadden jiki, dudda idanunshi a lunshe but idan ka kalleshi bazaka so kadauke idanunka ba dan yanada wani irin kyau kaman mace, lips dinshi sunyi wani kalan masifan ja kodan shishan dayake shane oho, yanada dogon hanci siriri dayazauna akan fuskanshi gwanin ban sha’awa, sai gashin giranshi baki sidik kuma acike yanada tabon salla agoshi sai gashin kanshi baki sidik shima dake kyalli sun nannade kaman na buzu sanan gawani kwantaccen saje a fuskanshi Masha Allah, koda ace shiyay kanshi bazaiyi kanshi da wanan kyau dinba ballema bashi yayba.


Ganin baida niyyan amsashi yasa Mamu ya fizge pipe din shisha dake bakinshi yace “kafara ko ina maka magana kamin banza” ahankali yabude idanunshi dasuka wani lumshe sukai yaushi da idanda zai kalli mace dasu sai lissafinta yarikice sanan yazubasu kan Mamu kaman ance yay magana dan dole yace “what”? Dan murmushi Mamu yayi da hannu yamai alamu yace “look over to the counter ga budurwanka chan, stalker dinka tazo sai kallon ka take wlh, haba Zayn kaiko bazakaji tsoron Allah ka kula yarinyar nan koda sau daya bane tunda dai ta kasa maka magana for morethan 2months yarinyar nan kullum binka take tana stalking naka tana kallonka u know she really really likes u waikai maisa kacika wulakanta mata ne eh? Anyway I don’t blame you ni wlh in mace ne banmaga abin so ajikinka ba mutum dukgaka nan kalan asibiti farin fata kalan cuta, duk baku da karfi” dan murmushi yayi dan yasan Mamu so kawai yake yajashi suyita surutu this afternoon shikuma baida time dinan, hannunshi yamikamai alamun yabashi shishi shi, ijiye pipe din shishan Mamu yayi kan table din gabansu yace “Ya isheka hakanan gashinan duk idanunka sun chanza launi, munada lectures yanzun nan fa I think in the next 5min” dan tsaki yaja yasa hannu yadauki pipe din shisha yacigaba dasha abinshi yana daddanna wayanshi yana hura hayakin ta hancinshi batare dayama daga kai ya kalli inda Mamu yacemai yarinyar nan takeba Mamu nabinshi da kallo yarasa yanda zaiyi yaraba Zayn da shisha, shima bawai bayasha bane no but occasionally yakesha, shiko Zayn zai iya wuni yanashan shisha hakanma yasa baya iyacin abinci sosai, ganin yasake lumshe idanu yasa Mamu yaja tsaki yamike tsaye yace “dalla Malam wuce mutafi” bude idanunshi yayi dasuka dan kankance sukaija sanan ya watsama Mamu harara kafin ahankali ya ijiye pipe din yamike tsaye dogon namiji ne nagaske, budadde sanan kuma cikakke irin mazan nanne da ake kira da burin mata, car key dake kan table din yadauka yana rikeda wayanshi yay gaba abinshi batare daya cema Mamu komi ba yay hanyar kanta.



Tundaga nesa ta hangoshi ya dumfaro gaban kanta, duk taku daya dazaiyi saita jishi har kirjinta yana amsawa, tun kafin ya iso wajen wani kalan kamshin dayakeyi dayake neman sata ta haukace sabida sonshi ya lullube mata hanci ganin ko’ina najikinta yadau kyarma yasa ahankali tasa hannu tadauki cup na drink dinta takai bakinta still tana kallonshi ta gefen idanunta daidai ya iso ya tsaya dab da ita dasauri bartender din yazo yace “u done sir” bai amsashi ba yasa hannunshi a wandonshi yaciro wallet dinshi yabude yana kokarin zaro kudi ko kadan batasan drink din yamakai saman hancinta ba tsabagen yanda take kallonshi kawai numfashin dazata shaka ta shaki wine din wani irin mahaukacin shakewa tayi dabama tasan lokacin data saki cup din akasa ba tana wani kalan mahaukacin tari wine nabin hancinta suna fita idanunta sunyi ja kwalla yacikasu dawani kalan sauri daga Bartender din harshi suka juyo suna kallonta dasauri Bartender din yataho ta saitin gabanta yace “sorry Miss” dudda tarin datake kokarin danne tarin take tana kakalo murmushi dan wanan kwafsin haka har ina baki tabude zatai magana wani tarin yakara sarkaketa wine din na fitowa daga bakinta yana diddiga akan white wandonta duk yay staining sabida Jan wine ne, kaman daga sama taga wani clean white handky agabanta kamshin da ajikin mutum daya tall a duniyan nan takejin kamshi taji yana fitowa daga hanky ahankali tadago kanta sama tanabin Tundaga handkerchief din dakallo harzuwa white hannun dake rikeda shi zuwa kan fuskan Zayn dake kallonta in the eyes, wani sabon bugawa zuciyanta yashiga yi hannunta har rawa yake tasa takarba zatakai kan fuskanta dan sharewa shikuma yajuya ya ijiye kudaden dayariga yaciro daga wallet dinshi yadaura kan kantan yajuya yawuce batare daya kara bata second look ba, ahankali ta janye handky dagakan bakinta tabishi da kallo harsaida yabace ma ganinta sanan tasauke ijiyan zuciya kafin ahankali tasauke kanta tana kallon handky din ko kadan tama manta inda take rungume handky tayi akirjinta tana murmushi sosai.



💫  PROMISE OF THE HEART  💫


      ALKAWARIN ZUCIYA 💔



         ✍🏻M SHAKUR



2️⃣


Murmushi Bartender din yayi inda sabo yasaba yasan yanda yarinyar nan ke crushing on that guy like hell, not just her da many other ladies ma, sabida guy dinan cinikin dasukeyi yanzu a eatery dinan is mind blowing, dazaran ansan yana ciki yammata zasu fara tururuwa suna shigowa from no where so koshima he’s happy for her at least yau yakulata, he hope suyi relationship dudda guy din dumping yammata yake anyhow kaman trash kuma ko ajikinshi dan yasan yanda suke binshi, he just hopes wanan will not be one of his victims, dan yana using babes kaman yanda yake using pen na rubutu idan yagaji da wanan ya yar yadauki sabo.



Tadade awajen ita kadai sai murmushi take tana daddaura handkerchief din akan fuskanta tanajin dadi daga bisani wayanta yashiga kara, dasauri ta kalli wayan ganin Juliana Munari ke kiranta yasa dasauri tadauka tana murmushi sosai tace “Hi Babe ya” daga tachan bangaren wata yarinya tace “ina apartment dinki amman bakinan Ayshu where are you? Ba tundazu muka gama lectures ba” murmushi tayi sosai tace “ina Cozy” dan jim Jully tayi tace “for Godsake Aisha when will u get sense? Eh, look at the way Kabeer ke binki Ayshu yaron nan loves you like a mad man amman kina nan kina stalking wanan heartbreaker da the worst part baimasan kina existing ba” dasauri Aysha tai fari da ido tace “says who, wayace miki baisan ina existing ba? Wlh yasani infect right now ma yanzu haka handkerchief dinshi nake kallo a hannuna it feels warm and smells succulent, OMG it smells just like him wlh, I feel kaman Zayn dina ne anan wajen” shiru Jully tayi saikuma chan tace “Ayshu I am ur friend and I will always tell you the truth, forget that guy he’s nothing but a dream and face the reality face wanda ke sonki ba wanan ba da kowa in our university sunsanshi ba wajen using yammata yay dumping nasu, Ayshu enough of this stalking, sabida yaron nan kin chanza gida kin dawo apartment din dayake, kin biya kudi double of the normal amout sabida acire tenant din dake zaune adakin dakenan directly opposite nashi kinyi parking kin koma compund din, Aysha sabida yanda kike stalking guy dinan kinsan karfe nawa yake tashi, karfe nawa yake fita gym, karfe nawa yake shiga school, sau nake yake da lectures kinsan all his spots, grades dinki kullum low suke karayi sabida soyayyan wanda baisan dakeba ke gabanki kum…” “Jully please enough, allow me to leave my life, ana so by force ne banson KB ki rabudani da maganan shi, kuma zaki gani Zayn will notice me and I will date him” dasauri Jully tace “dating Ayshu bakince min Islam dating babu kyau ba” dan yatsine fuska tayi tace “Jully is because bakisan guy dinan bane saisa, irinsu idan kika basu kanki ne kawai zasu zauna dake, dan gayu ne nafitina kaman ba muslim ba, boko tashigeshi, I want him to be addicted to me kaman yanda yakenan addicted to shisha, I am ready to give him anything, wlh Ina bala’in sonshi, just wait for me, ki dafa mana abinci gani nan zuwa”

tana maganan ta katse waya shiru Jully tayi, at this point zubama Ayshu ido zatayi dan Allah yama Ayshu taurin kai batajin shawara, kuma yaron nan will only break her heart, she will only chop breakfast a hannunshi a nothing will happen yaron da har lecturorin su mata crushing suke akanshi, anyway she just hope for the best.




Wuraren 6 ta shigo gidan, kana ganin gidan kasan na mugun yaran masu kudi ne, elevator ta shiga zuwa floor dinsu sanan tawuce Dakinsu tana kallon nashi dakin datana gani tasan baidawo ba daman baya dawo da wuri kullum sai 11 ko 12 nadare kuma kullu yaumin bata iya bacci saitaga dawowanshi wata rana tai kuka duk randa zai dawo da mace wata tana kuma tai murmushi, the truth is baifiye neman mata ba, wani zubin zaiyi 2month baidawo dakowace mace ba wani zubin kuma saiya dawo da mace zasuyi kusan kwana uku ko hudu tare saikuma shikenan bata kara ganinta dudda batasan dalili ba but kawai haka take gani, kuma baka taba ganinshi da babe din dabataci sunanta babe ba, duk tana tunanin nan tana tafiya ne tana kaiwa gaban Dakinsu tabude kofa tashige ciki tana ihu kitchen tafada tawani irin rungume Jully tana nuna mata handky tace “Jully look” murmushi Jully tayi tana kallon handky sanan tace “Ya akayi yabaki handky shi”  nan tabata labarin from A to Z tana murna, murmushi Jully tayi tace “nidai jeki wanka kizo muci abinci dan Jerry zaizo yadauken” gira daya Aysha tadaga mata tace “Iyye love birds” tai maganan tana wucewa bedroom nata tashiga sanan ahankali ta ijiye handky kan pillow dinta tareda shafawa sanan tawuce ta shiga wanka agurguje tana fitowa tazo sukaci abincin tare sanan Jully ta shirya ta wuce abinta, komawa tayi ta kwanta kan gado tadauki handky tana kallon shi kafin ahankali tace “Zayn! I love you so very much Zayn” rungume handky tayi akirjinta tsamtsam tanaji kaman shita rungume, ahaka bacci ya kwasheta 11 dot na bugawa ta bude idanunta tsam shi kanshi gangar jikinta yasaba da stalking nashi, fitowa falonta tayi tai hanyar window ta ta tsaya dayake wutan dakin akashe ne ta tsaya tana kallon kofarshi tana tsaye awajen kam wajejen 11:30 saigashi ya shigo yana tafiya nan cikeda isa akuma hankali tundaga wajen saida kamshin dayake yadaki hancinta bude kofanshi yayi ya shiga sanan ya maida yarufe kafin ya kashe wutan falon, murya chan kasa tace “good night My love, asuba tagari” sanan ahankali tasauke window blind din tajuya takoma daki ta kwanta saikuma kaman wani abu yafado ranta dasauri ta tashi tadauki handky tafada bayi ta wan ke shi tsaf sanan ta shanya tafito tazo ta kwanta, shida dot tabude idanuwanta agurguje tafada bayi tadauro alwala tafito sallan ma agurguje tayi bama ta tsaya cire hijabin ba tafito ta daga window blind ta tsaya jikin window dan 6:30 dot yake fitowa tafiya gym, tana tsaye saigashi yafito cikin kayan workout gajeren wando da singiletin Riga da safa da canvas, cinyanshi tabi da kallo amunmurde kaman na yan wrestling sanan yaja kofan dayake da pin suke bude kofan yawuce yana jogging yatafi abinshi murmushi tayi ahankali sanan tace “good morning  baby na” sanan tajuya handkerchief din tadauka tai ironing nashi, sanan ta shiga wanka tadade sosai abayin sanan tafito tana ganin 8 saura da sauri tawuce wajen window Wuraren 8 yashigo yana zufa murmushi tayi dasauri tajuya tashiga ciki wani hadaden short gown ta saka daya sauka daga guwiwabta da kadan pink yamata kyau Wanan Karan batasa dankwali ba sai turaren data feffesa sanan tai parking gashin ta in a stylish way sanan ahankali tadauki handky tana kallon kanta agaban madubi ahankali tace “Ya Allah kadaurani akanshi” sanan ta zura slippers dinta tawuce tafita falo ahankali tabude kofa tafito daga flat dinshi sanan kaman wacce abi yafashewa aciki tai hanyar dakin shi kirjinta na daukan uku uku tawuce gaban dakinshi tadade atsaye kafin ahankali ta danna door bell, ankai kusan 5min kaman bazaa budewa farat aka bude kofan gabadaya dasauri tadaga kanta suka hada ido wani irin faduwa gabanta yake tana kallonshi yana daure da bathrobe ajikinshi kirjinshi duka abude gashin kirjinshi akwance ruwa nabi sai karamin towel a hannunshi yana goge kanshi da alamu daga bayi yake, da mamaki yadan kalleta batare datai magana ba, lips dinta har rawa yake sanan ahankali tadaga hannunta dake rikeda handkerchief din murya chan kasa tace “ahhhhhmmm dama, dama, I brought your handkerchief back ne” tai maganan tana wani irin nishi sama sama kaman numfashinta sai dauke, kirjinta nawani irin racing, this is the first time take ganinshi ahaka, ganin still kallonta yake ba yabo ba fallasa kuma bai fasa abinda yake ba wato sharekanshi da karamin towel din dayake rikedashi, yasa taji wani bala’in fargabanshi na cikata jin baice komiba dakyar tadaga hannunta tamai pointing kofan dakinta dake kallon nashi tace “actually that’s my flat, yanzun nan naganka shine nace uhmmm bari nakawo ma” dan yatsine fuska yayi amugun wulakance ya kalli handky datake mikamai tundazu har hannunta na neman sagewa yace “I don’t need it, discard it” yaja kofan zai maida yarufe da sauri tace “uhmmm wait please” chak ya tsaya yana kallon fuskanta da fuskanshi dababu alamun rahama akai face dinshi looking kaman zai maketa, tagefenshi taleka tana kallon indomie da taga yafito dashi zai dafa yacika ruwa a babban pot yazuba albasa aciki ya fasa kwai aciki ruwan na kumfa sosai, dan murmushi tayi cikeda shakkanshi tace “are you trying to cook indomie”? Yana kallonta still a bala’in wulakance yace “uhn” kaman dole akace yay maganan, murya chan kasa cikeda shakkan abinda zatace tace “that’s not how to, lemme cook it for you p…..please” wani kalan wahalallan tsaki yaja ko kunyanta baijiba yace “banso” sanan yay slamming door din on her face batare dayama jira maitake shirin cewaba, kuka taji yazo mata wuya tadaure tahanashi fitowa tadade ahaka awajen sanan ahankali tajuya tawuce takoma dakinta zama tayi tana kallon handkerchief din tama rasa meke mata dadi, tunda take bata taba shakkan wani namiji ba sai wanan menene shi? Jibeta fa tanada kyau babu namiji da bazata iya daukemai hankali ba shi waye, enough of all this, tashi tayi fuu tai kofan tabude tafice sanan direct tai dakinshi ta danna door bell baa wani dauki lokaci ba wanan karan tabude kofan koyana expecting wani ne oho, churus ya tsaya ganin yarinyar dazu, wani irin faduwa gabanta yayi ganinshi dagashi sai dogon wando na Jean da Riga a hannunshi dabai Riga yasaba yanada wani irin broad chest ga cikakken shoulder parts garai, kasa magana tayi saiwani kalan kallon kirjinshi datake lips dinta na rawa tana kallon dark aroelas dinshi, ahankali tace “l…..l….ove……you…..Z….Zayn” Tundaga sama har kasa yake kalleta sanan yace “ke kikama kanki” wanan Karan wani slamming kofan yayi on her face saida yataba goshinta ahankali tajuya kaman an kashe mata yaran ciki tawuce side nata ta zauna dirshan akasa, tana zaune awajen taji fitowanshi yafice, kiri kiri kasa zuwa class din datake dashi tayi sabida yanda komi baya mata dadi.


💫  ALKAWARIN ZUCIYA  💫



     PROMISE OF THE HEART 💔



        ✍🏻M SHAKUR




3️⃣


~Nigeria~

Wata babbar mace ce doguwa chocolate skin tsaye cikin wani lafiyayyen hadadden kitchen ginin zamani, tana sanye dawata doguwan rigan Atampa mai kyan bala’i ga kallabi daure akanta da kana gani kasan daura dankwalin kawai tayi amman hakan baihana kwantaccen black gashinta dake gauraye da farare lekowa ba, tana tsaye agaban wani hadadden babban gas a kitchen tanama wata yar aiki dake juya basmati rice a tukunya dawani wood spoon magana sukaji wata zazzakan murya dake ratsa zuciya na y’a mace ta kwala ma matar uban kira. “Mama nadawo, nakawo miki wasu kawayena ki gansu” wani irin kwashewa da dariya yar aikin dake juya abinci a tukunya tayi takalli Matar da aka kira da Mama datai tsaye kawai tama rasa ta cewa tace “Hajiya wlh tun ina iya kirga yawan kawayen Khairy harna bace a kirgan” kwafa kawai Matar da aka kira da Mama tayi tace “karasa juya abincin sai ki kwashe a warmer Ladid…..” bata idasa maganan ba aka kara rangadamata kira da wanan zakakkiyar muryan kaman ana busa sarewa. “Mamaaaa kina ina zoki gansu” dafa goshinta Matar tayi cikeda takaici tace “Allah nagode maka dakabani wanan yarinya, ina ganin Ummulkhairy ce zata bani hawan jini aduniyan nan” tai maganan tana fitadaga kitchen din ta hanyar bude kofa tafice, tana fitowa dining tai kicibus da yammata kusan su tara a zazzaune kan lafiyayyun kujerun falon suna maganganu suna hira suna kallon lafiyayyen hadaden falon dayaji Cubana furnitures, ganin Matar da kallo daya suka mata suka gane itace mahaifiyar Khairy yasa duk suka zubo daga kan kujerun cikeda girmamawa duk suka gaidata. “Mama ina yini, Mama barka da rana, Mama ina gajiya” lafiyayyen murmushi ta sakin musu tana karasowa tsakiyan falon tana bindi da kallo daidai tace “Masha Allah sassannunku da zuwa yammata yakaratu”? Kafin subata amsa wata kyakkyawan budurwa yarinya chocolate skin color, yar doguwa bachan sosai ba dabazata wuce 20yrs, skin dinta nawani kalan glowing fuskanta babu ko kuraje guda, tanada dan dogon hanci yet kuma dan karami dan diss afuskanta but fitacce, tanada manya manyan pure white eyes, idanunta are very big sunada wani kalan adorable spherical shape that is just damn gorgeous, dan kana kallonta the first thing dazasu fara daukan maka hankali a fuskanta are her big white eyes, ga eyelash dinta dogaye bakake cikakku, hakama gashin giranta, tanada goshi wanda kusan yarabu biyu ne rabi duk gashi ne dayake nan baki sidik sun kwanta daya karama fuskanta wani kalan kyau dan zaka dauka buzuwa ce sai dayan rabin kuma fatarta ne dayataho har gira, tana sanye da dogon rigan atampa itama da dan kwalinta akanta, tawani buga uban ihu da saida falon ya amsa gabadaya. “Mamaaaa” yanda ta kwala mata uban kiran nan yasa  mahaifiyar nata tadago da kanta tareda juyowa ta zuba mata idanuwanta kurii irin na jama’a yaya zanyi da wanan yarinyar ne? Wani irin washe baki Khairy tayi cute saitin white teeth dinta suka bayyana tashiga saukowa daga stairs din dagudu kaman ba ita Mamar kema kallon zaki ganeba kawai tawani irin fada jikin Maman nata tana ihu sosai tana rawa ta kankame Maman kamkam. “Wayyooo Mama wlh nai missing naki, inata nemanki nadauka kin fita ne har hankalina yatashi ashe kina kitchen, Mama tun safe yau banganki ba awa nawa yanzu bansaki a idona ba karfe biyar fa, nai kewanki Maman mu, Mamana, I miss you Mommy Ummulkhaiyr” tai maganan tana kara kankamet Mama cikeda tsananin murna, dudda yanda Mama ke mugun kule da ita saida tai murmushi har cikin ranta duk cikin yaranta babu wanda ke sonta kaman yanda Khairy ke sonta, idan Khairy tadawo gida batanan wani zubin har zazzabi takeyi, Son da Khairy ke mata dabanne, gabaki dayan kawayenta baki suka sake suna kallon Khairy yanda ta kankame mamanta cikeda murna tana rawa kaman wata yar karaman yarinya, murmushi kawai Maman takeyi ganin yanda kawayen ke kallon Khairy sabida wayan nan wasu new set ne basu saba ganin haukanta agidaba yasa Mama tace “ke dalla cikani kije kitchen kitaya Ladidi ku kwaso abinci kiyi serving friends naki kuci” sakin Mama tayi ahankali tana murmushi dake bala’in kara mata kyau tana kallon Mama tace “tom Mama” sanan tawuce kitchen da ihunta ta shiga kitchen din. “Ladi kwas kwas!” Tsabagen yanda Ladidi tafirgita batasan lokacin data saki cokali data rike a hannunta kasa ba, kwashewa da dariya Khairy tayi ganin yanda Ladidi tafirgita, Ladidi ta watsa mata harara tana dafa kirjinta da hannu jin yanda yake  bugawa tace “aniyarki tabiki Khairy bani zaki sawa bugawan zuciya ba wlh” dariya Khairy tayi tadauki spoon tazo kusa da ita tana kallon tukunyar tana murmushi tace “uhmm smells good, let’s have a taste” abincin tadeba takai baki tana lumshe ido, harara Ladidi tabita dashi tana kallon long full lushy eyelash dinta dazakaji kaman ka cire kasama naka sabida kyau, dan murmushi tayi tace “yayi dadi Khairy? Kinga nasa coconut milk dakikace nadinga sawa” bude idanu Khairy tayi ta kalleta sanan ta yatsine fuska tace “yayi dadi ba laifi amman ba kaman nawa ba” batarai Ladidi tayi hakan yasa Khairy tafashe da dariya tace “ki zubamana nida kawayena kizo ku gaisa” hararanta Ladidi tayi tace “Malama ki tsaya ki dauki abincinku ki kaimusu ba inda zani nagaji da gaisawa da kawayenki, nibansan ko kamfani gareki na kawaye ba” turobaki Khairy tayi tace “bakinciki kikemin kinga inada kawaye masu sona ke bakida kawa ko daya” dasauri Ladidi tanuna kanta tace “ni Khairy bakin ciki ana zaune lafiya, kawayenki sunfi dari, ni idan Allah yabani kawaye ko sama da biyu ne bansan yanda zanyi dasu ba” hararanta Khairy tayi tadauki Baban tray da Ladidi tajera musu different abinci akai a different plate guda 5 tafita dasu taje takai musu sanan tadawo ladidi na kallonta tace “yanaga kin dawo” akufule tace “su tara ne plus ni goma, kuma is just 5 plate of food nafita dashi” kasa magana Ladidi tayi kawai tashiga zuba wasu sababbi tass abincin yakare Ladidi tace “yayyinki suka dawo maizasuci” “oho” ta amsata akufule tafice abinta takaimusu abinci suka shiga ci suna hira shaaaa kakeji sun cika falon da hayaniya kadauka biki ake kowani liyafa aka hada, lekosu Ladidi tayi daga kitchen kwafa tayi tace “yo wlh ban kara daura wani girkin barima kiga tafiyata zanyi, masu gida nakema aiki ba kawayenki ba, yarinya kowani kare da doki kawayenki ne, mijinki zai sha fama Khairy” tai maganan tana komawa ciki, hada yan kayanta tayi a handbag dinan sanan tabi takofar kitchen tafice abinta daman inhar tagama aikin yamma indai Hajiya na sama tafiyanta take saidai in tana kasa ne saitaje tamata sallama tawuce.



Sai wuraren 6 sanan kawayen nata suka fito bayan takaisu sama sunma Mama sallama har compound tarakosu inda sukai parking motocin su duk suka shishiga, daya daga cikinsu taleko bayan tama motarta benz key tace “wai Khairy yaushe zaki farajan mota kine eh? Gamu duk mu munaja ke kadaine kullum driver ke kawowa” kaman zatai kuka tace “ba su Mama bane da Baba wai tsoro suke su barni nafara tuki wai nacika rawan kai kumafa na iya wlh Paddy” dariya dukansu sukayi wacce ta kira da Paddy tace “ke da karfin hali zakisa su barki kifara tuki wlh daukan mota kawai zakiyi wataran ki fice, Babe magrib tayi bari muwuce see you tomorrow at school” hannu tadaga musu tace “see yah girls” gateman dinsu yabude musu gate suka fice motoci biyar daidai kuma motocin yayinta na shigowa gida na Baban su biyeda su, washe baki tayi tana tafi ahankali tana kallon motar Baban su dake shigowa last tace “oyoyo Baba” motan na parking tai wajen motan da gudu batare databi na yayyinta da kallo bama.



💫  ALKAWARIN ZUCIYA 💫



      PROMISE OF THE HEART 💔



         ✍🏻M SHAKUR 



4️⃣



Kafin ma Baba yabude kofa tasa hannu tabudemai kofan jikinta har rawa yake tanajin dadi. “Baba oyoyo, Baba sannu da zuwa” wani magidancin mutum ne babba sosai yana sanye da babban riga yanada gemu dayacika da furfura, ga kuma katon ciki irin na manya wayanda suka manyanta dinan, exactly idanunsu iri daya da ita manya saidai nashi daya soma kankancewa sabida tsufa, wani kalan kyayataccen murmushi yasakin mata, cikin kamilallen muryanshi irin na magidantan nan yace “yarinyar Babanta” yay maganan yanajan dan hancinta, murmushi tayi sosai tace “sannu da zuwa Baba” fitowa daga motan yayi yace “to akwasomin kaya akai ciki” gyadamai kai tayi tace “to Baba” yawuce yana kallon yaranshi maza su uku da duk suke tsaye suna jiran fitowanshi, Manaf wanda yake Babba yanada 27yrs, sai Mu’az shima 27yrs twins ne shida Manaf saidai ba identical twins ba ko kadan ma basuyi kamaba idan baa gayamaka yan biyu bane bazama ka yardaba, Manaf na kama da Mama, Mu’az na kama da Baba, sai Maheer dakenan 24yrs, dukansu sun gama makaranta duk a company Baba suke aiki yanzu.


Gaida Mahaifin nasu sukayi cikeda girmamawa kana ganinsu kaga yaran dakeda tarbiya dakuma natsuwa. Cikin so da kauna ya amsasu yana tambayan kowa ya aiki sanan suka wuce masallaci, itakuma kayan Baba su files da wasu yan tarkace tafito dasu daga motan sanan tai cikin gida.


Sama tayi direct zuwa lafiyayyen hadadden falon Baba, ijiye kayan tayi sanan tajuyo tabude kofa ahankali, ganin Mama tsaye abakin kofan kaman ita take jira daman yasa takarasa fitowa tareda maida kofan tana rufewa tana kallon fuskan Mama dake kallonta tana murmushi, harara Mama ta watsa mata tace “ba murmushi nace kimin ba, quietly go to that kitchen kidafa sabon abinci wanda za’aci agidan nan this night tunda wanda aka dafa dake da kawayenki kun cinyeshi tatas” dan turobaki tayi dan wlh tagaji ahankali kaman zata rushe da kuka tace “Mama maisa Ladidi bata dafa wani ba wlh nagaji school fa naje” cikin fushi sosai Mama tace “are you stupid Umma? Inba so kike na makeki ba kiwuce yanzun nan kafin raina yabaci kije ki daura abincin daza’aci this night, I am talking to you kina gayamin Ladidi tadafa, kin zaci sabida ke nadauki Ladidi aiki kokin dauka jakace ita batasan ciwon kanta ba dazata zake tai girkin gida keda kawayenki kuzo kutasa abincin agaba ku cinye tas, yanzu ina gayamiki kije ki daura wani kina neman kawomin gabli da ba’adi, to the kitchen my friend!” Mama tadaka mata tsawa kaman zata kurma ihu tawuce hawaye sun cika idanunta tass tai kasa, harara Mama tabita dashi sanan takada kai kawai tawuce tashiga dakinta.


Kitchen din tashiga tamaida kofan da mugun karfi tarufe kaman zata Balla kofan sanan ta jingina da kofan tana maida numfashi takai kusan 5min sanan tawuce ta kwaso kayayyaki tashiga shirin hada girki.



Saida akai Isha’i sanan Baba da su Manaf suka shigo gida, afalo suka tarda Mama zaune gaidata duk sukayi, Mama ta gaida mijin nata zama duk sukayi, Maheer yace “Mama me aka dafa yunwa nakeji” ahankali Mama tace “Khairy na kitchen tana girki, itada kawayenta suka cinye duka abincin da aka dafa tass shine yanzu dannace taje tadafa wani abincin take kumbure kumbure” dan murmushi Baba yayi yana duba wayanshi ganin yanada miss call, cikeda kufulewa Maheer yace “wlh Mama Allah zan zane yarinyar nan, duk randa takawo kuchakun kawayenta tashiga kitchen tamusu girki da kanta ba abincin muba” cikin fushi shima Mu’az yace “ni I don’t even know wani kalan brain Khairy keda shi, ni tunda nake bantaba ganin wacce takai Khairy yawan kawaye ba, kawayenta sunfi dari biyu, tamaida mana da gida nanne majallisar kawayenta ai gobe Saturday Allah sa takawo mana wata gidan nan wlh daga ita har kawar saina kakkaryasu” Baba daduk ke jinsu yana taba wayanshi wayan ya ijiye yakalli Mama yana murmushi sanan yakalli su Maheer yace “ku kyale yarinyar nan she’s just a small girl, idan making friends makes her happy so be it, abincin gidan banike siyaba taita kawo kawayenta sunaci is no big deal, and you wife” yajuyo yakalli Mama yace “idan abincin gida da kawayenta keciki ki kara yawan abinci since kinsan yarki mai mutane ce, ta yanda zasuzo suci su koshi sanan muma muzo muci okay” tabe baki Mama tayi tace “daman babu wanda ke bata yarinyar nan saikai kacigaba” Mama tai maganan da fushi dan murmushi Manaf da tuntuni baice komiba yayi ganin yanda ran Mama yabaci yace “Mama kudena making issue out of this small thing please bagashi yanzu tana kitchen tana dafa mana wani ba, is just friends ta tara bawai wani bad hali ko dabi’a takeyi wanda yaran yanzu sukeyi ba Mama, please ku kyaleta, she’s still a small girl, inda ace bata gama secondary school dawuri ba da har yanzu bamata shiga university ba ballema tazo hartana final year, ku barta please Mama ahankali zata gyara” murmushi sosai Baba yayi yanajin maganan da Manaf keyi, Manaf nada dabi’unshi sak, ga hakuri ga iya tafiyar da gida gashi da halin manyanta halin Baba, amman Mu’az da Maheer jin kansu suke kaman sa’onnin Ummul Khairy. Baki Mama tabude zatai magana aka bude kofan kitchen din aka fito Khairy ce tadauko wani hadaden warmer, ko kallonsu batayi ba sai uban turo baki take tawuce zatakai warmer dinning Baba yace “zo kawo kulan nan Umma anan falo zamuci” ahankali tajuyo tazo Mu’az da Maheer sai uban ballamata harara suke tana karasowa ta ijiye kulan Baba na kallonta yace “yauwa sannu da aiki Yanmata na” Maheer dake kallonta yace “yi sauri kije ki kawomin plate dina da fork” dasauri ta kalleshi da manya manyan idanunta harara ta watsamai wani irin mikewa tsaye yayi kaman zaiyo kanta dasauri tai baya tareda dan sakin ihu. “Wayyo Ya Manaf kaganshi ko” hararanshi Manaf yayi batare dayay magana ba hakan yasa Maheer yakoma yazauna yana kwafa, Manaf yakalleta yace “go and bring the plate and serve us” gyadamai kai tayi tajuya tana turo baki daga Baba har Mama suka bitada kallo, bata wani dade ba tafito dauke dawani babban tray da plates spoons, bottle water da drinks ke kai sanan takawo tsakiyan falon, sanan tabude kulan wani kamshi ne yadaki hancinsu tadafa wani lafiyayyen taliya da nama, zuzzubama kowa tayi sanan ta tashi, Baba yace “ina zaki zauna kici naki” ahankali tace “nakoshi naci shinkafa dazu, wanka zanje nayi Baba nagaji” “jikiyi yarinyar kirki” wucewa tayi sama sukuma sukahau ci, saida Maheer yajuya ganin hartama shiga dakinta yasa yajuyo yace “at least she’s good in one good aspect, wato girki” murmushi Baba yayi yakalli Mama yace “akwai wacce zata zauna da Wife bata iya girki ba ballema yarta” murmushi kawai Mama tayi batacemai komiba, saida suka gamacin abincin tsaf sanan Maheer ya kwashe komi yakai kitchen kafin su tashi suma iyayensu sallama suka wuce side dinsu.



Tashi Baba yayi yana kallon Mama datai shiru yace “please kidena sa zancen shirmen Khairy aranki, is just like what Manaf said at least friends kawai ta tara bawani mugun hali ba” dan ijiyan zuciya ta sauke sanan ahankali tace “Alhaji still yawan kawaye basu da amfani wlh” ahankali Baba yace “I promise duk randa nai sensing wani bad behavior kokuma wani abu nida kaina zan rabata dasu, please this matter of her friends shouldn’t be an issue again ok” Ahankali Mama tace “ai shikenan  dama kaine ke bata Umma ai” Mama tai maganan tai gaba abinta binta yay abaya yace “wifeyyy common” bata biyemishi ba tabude kofar dakinta ta shige, murmushi yayi kawai aranshi yace “I will handle u later” sanan yay hanyar dakin Khairy, knocking yayi ahankali tareda kiran sunanta. “Umma” jin shiru yasa ahankali yabude kofan dakin, dakine nai kyau dakana gani kasan dakin Yar gata ne anyimai Fenti pink dakuma design na flowers everywhere, tana kwance kan lafiyayyen gadonta mai kyau tana sanye da dogon gown na bacci tana bacci hankali kwance ga dakin uban sanyin AC tachure alamun sanyi takeji, karasowa gaban gadon yayi yace “Umma Umma, mamar ki dake fada ita batasan rashin jin maganan ta kika daukoba” yay maganan yanajan bargon gadon yarufa mata sanan yadau remote don AC yarage AC sosai kafin ahankali yajuya ya kashe wuta sanan yarufe mata kofan yawuce dakin matarshi!!!!



💫 PROMISE OF THE HEART 💫



        ALKAWARIN ZUCIYA 💔



        ✍🏻M SHAKUR



5️⃣



Da asuba kafin Baba yawuce masallaci yashigo yatadata wanda hakan yakeyi kullum.

Da farinciki ta tashi yau sosai kaman ba itane ta kwana da fushi jiyaba, murna take sosai sabida yau zataje bikin kawarta Zainab.


Saida tai salla tai karatu sanan ta gyara dakinta tsaf tafito kasa ta sauka a kitchen ta tarda Mama tsaye zata fara aiki dawani irin gudu taje ta rungume Mama. “Mama good morning” murmushi Mama tasakeyi this is another aspect na halin Umma datakeso ko kadan batada riko, tureta Mama tayi tace “waike karyani kikeso kiyi” dariya tayi tace “Mama dadi nakeji yau bikin Zainab Kawata, Beaty wacce nai ankon ta kin tuna”? Baki Mama ta tabe tace “ina zan tuna wata Besty Bestotin kin sunfi dari, keda kullum cikin bikin kawayenki ake, idan babanki ya shigo kije ki tambayeshi izini baruwana da zuwa bikinki,  bani tukunya nidai kiga” dasauri tadaukoma Mama tukunyar nan suka shiga hada breakfast tanama Mama surutu wuraren 8 suka gama komi suka jera a falo daidai nan su Baba suka shigo gidan duka zama sukai a falo suka shiga kari sai bayan an gama ta kwashe komi takai kitchen sanan tadawo da saurinta tazauna kusa da Baba, fuskanta kadai yagayamai dawani abu hakan yasa yace “Ya akayi Khairiyya?” Murmushi tayi tace “Baba yau bikin Zainab kawata shine nakeso nagayamaka” idanu Baba yazuba mata yace “amman kinsan yau yakamata kije gidan Baffan kiko” gyadamai kai tayi dasauri ahankali tace “Baba gobe zanje gidan tunda yau inada biki please naje Baba”?  shiru yayi sai chan yace “ok kije, but by 4 kidawo gidan nan ban yarda kije kai Amarya ba” murmushi tayi tace “Baba ai daman bazanje ba itada za’akai Kano, kumama ana daura aure wai zaa tafida ita kaga kenan kafin 4 nadawo ma” jinjina kai Baba yayi yace “duk kincikani da surutu, okay to adawo lpy, ki kama kanki banson kula maza okay” dasauri tace “to Baba, bari naje na shirya to” tai maganan tana tashi tai sama, tashi Manaf yayi yace “bari naje na kwanta Mama” binshi Mama tai da kallo yawuce yafita shikuma Maheer da Mu’az Kwallo suka kunna a falon suna kallo abinsu, Baba kuma na duba wasu files dayasa Mama tadaukomai daga dakinshi.




Wanka tasakeyi sanan tashirya cikin wani hadaden ashobe, skyblue, dogon riga aka mata daya kamata daidai ita ya bala’in mata kyau, yabi jikinta sosai, zama tayi gaban madubi tana kallon kanta, dan tsaki tayi takai hannunta tana shafa siman rigan da akabi da net da kana iya hango tudun saman boobs dinta ahankali tace “I hate style like this dake nuna jikina, I will use gyalena narufe Mtsww” tasake jan tsaki sanan ta zauna tai wani lafiyayyen dauri dazaka dauka make up artist ce tayi, kwalli ta zizara sanan tadau wani lipgloss tasaka dayasa lips dinta shining pink din jiki yafito sosai dazaka dauka janbaki pink tasaka, wayanta dake gaban mirror kiran samsung note 22 ta dauka, ganin 10miss calls yasa tace “OMG guys gani nan zuwa kunata kirana” ganin battery ta yay ja yana nuna 10% left yasa takara jan tsaki tace “ohhh namanta bansa chaji ba” arayuwanta babu abinda take kiwuyan sawa irin chajin waya wani zubin sai wayan ya mutu russ ne shine zata dauka ma tasa a chaji, jefa wayan tayi a shinning handbag dinta dake ijiye kan mirror sanan  tajawo wani hill na dolce gabana tasaka sanan tamike tsaye, dan karamin gyalenta tadauka ta warware sanan ta yafashi ta gaba tsaf yarufe mata kirji sanan tadauki turarukanta ta feffesa kafin ta maida komi yanda yake tafito lokacin 12:48PM.



Saukowa tashiga yi daga Mama sai Maheer afalon yana kallon wrestling shima Mu’az yatafi ya kwanta, kamshin dayaji yasa yajuyo ganin Khairy yasa yasaki baki yace “ke kece amaryan Wanan kwalliya haka, Wanan ko ranan aurenki banjin zaki irin wanan kyan ba” hararanshi tayi takalli Mama dake binta da kallo tace “Mama kin ganshi ko” hararan Maheer Mama tayi hakan yasa yay shiru itakuma takaraso wajen Mama tace “Mama zan tafi ina Baba?” Ahankali Mama tace “Ya kwanta, ga kudi ya ijiye miki” tanuna mata bandir na yan 200 dasauri tadauka tana murmushi tace “Allah sarki Babana he’s the best, Mama natafi” tai maganan tana wucewa zatai kofa, Mama tace “ke” dasauri tajuyo takalli Mama dake kallonta, Mama tace “kindaiji abinda Baban ki yace ko, 4 tamiki agida Umma, kuma ki kama kanki, baruwanki da maza ko abokan ango, saura kuma naji kin wuce wani gantalin daban, wlh kika saba any of them bikin dazakije na karshe kenan ban kara barinki fita” dasauri tace “Mama I promise, nida keda bukukuwa I will not jeopardize that Mama, bye, Mama zan kawo miki alkaki” hararanta Mama tayi tace “banso, wuce Direba na jiranki” kofa tabude tafice, Already Adamu Direba harya shiga cikin motan ita kawai yake jira, wata lafiyayyen bakar Benz tabude baya tashiga sanan tace “gidansu Zainab zamu Adamu” “to Hajiya” yay maganan yana tada motan yaja, saida sukahau kan titi sanan taciro wayanta dake nuna 9% yanzu sabida uban kiran dasuke mata, kafin tama danna wayan wani kira yashigo da suna Zainab, daukan kiran tayi tana dariya tace “Amarya kinsha kamshi da turare, kuma wani gida ne gani ahanya” shiru tayi sai chan tace “Okk” sanan tace “Adamu suna gidansu Amal wai” ahankali tace “to” dan babu gidan wata kawarta dabaisani ba, tafiya kai nisa sukayi sanan suka shigo wani hadadden estate daya cika da mutane kana gani kAsan biki ake wani Layi daban ya shiga sanan yay parking agaban wani hadadden gida, murmushi tayi tace “yauwa, Adamu bani key motan narike” dasauri yajuyo ya kalleta, ganin kaman yanaso yaganota yasa tace “zan taimaka musu dashine, ana kwaso one or two things dazamuyi amfani dashi, idan zan dawo zan kiraka saikazo mutafi” tai maganan tana mikamai hAnnu, ahankali yazari key motan yabata karba tayi tace “yauwa katafi to dan sai yamma zan kiraka” tai maganan tana fitowa daga motan shima fitowa yayi sanan tarufe motan ta danna lock tawuce cikin gidan abinta shikuma yawuce yatafi zuwa bakin titi ya tsaye abin hawa yahau.



Tun kafin tashiga gidan takejin tashin kida, murmushi tayi ta shiga gidan an gyara anyi decorating ga yammatan Amarya sai rawa suke suna hangota aka wani hau ihu. “Khairy, Khairy ta iso, ke join us” wani irin murmushi tayi kaman abinda take jira kenan dasauri tai dance floor din, DJ yasakan musu wani mad song rawa sukahau yi suna ihu suna hotuna idan kaga Khairy zaka dauka taje dancing school ne,  suna haka saiga Amarya tafito wani mahaukacin ihu sukasa aiko tashigo itama sukahau rawa kaman mahaukata, Amaryan ta rungume Khairy tana mata magana a kunne, hakan yasa taciro wayanta tana video ganin wayan na nuna mata 1% yasa tai tsaki ta maida bag sanan taciro kudi tana ihu yara sai kallonsu suke taba manna ma amaryan. It was fun she love her friends and she loves wedding har buri takeci irin na shagulgulan da zaayi idan bikinta yatashi.



💫  PROMISE OF THE HEART 💫



     ALKAWARIN ZUCIYA 💔



        ✍🏻M SHAKUR 



6️⃣


Wajajen 3 aka wuce da Amarya Kano, ita kanta Khairy saida tadanyi kuka cus Besty tabata tausayi, bayan an wuce da ita  tama Maman su sallama tawuce dan zuwa chan gidan dasukai party inda motanta yake a pake, ahankali take tafiya ta bala’in gaji sabida rawan dasuka sha, ita kadai kemagana tace “yanzu inda Baba yabarni da hardani za’akai Zainab Kano, gashi akwai more event a Kano” dan murmushi tayi ita kadai tace “Allah kaimu bikina wlh 2 weeks zaayi ana event hmm” dan murmushi tasakeyi tace “nidako saurayi banda shine nake planning biki na” ahankali ita kadai tace “saikace wata mara farin jini, inada samari dayawa but duk mazan Nile ne, basu hadu ba gasu yan rainin wayau saisa i don’t even talk to them” tai maganan tana murguda baki daidai lokacin ta iso wajen motan, ahankali tace “I want to marry hadadden namiji, classic , handsome, miji dat will make mata jealous of my catch” tsayawa chak tayi takalli motan gabanta yadan fadi, saikuma chan tace “don’t be scared Khairy you have to show Baba u can drive sabida yabarki kidinga jan motarki” tana maganan tabude gaban motan tashiga tazauna tana sauke ajiyan zuciya sanan tamaida kofar motan tarufe kafin ahankali tace “Ohhkay let’s see” sitbelt tasaka still gabanta nafaduwa bata taba tuki bafa kawai tasha ganin yanda akeyi sanan Maheer idan tashiga mota dashi yana nuna mata yace “kihaka kihaka this and that” ahankali tace “Bismillahir Rahmanir Raheem” sanan ahankali takunna motar gently gabanta na dum dum tashiga yin reverse kadan kadan kana gani kasan wacce bata iya tuki bane acikin motan nan sanan ahankali taja motan tana tafiya ahankali wani irin murmushi tayi cikeda jin dadi tace “see ba gashi nan na iya ba ina tuki perfectly like a pro” Ahankali takejan motan feeling a bit too sad sabida su Mama basu Bari takai Zainab ba ahaka hartakai gate din estate din tasa kan motarta tafice tana kalle kallen main road din gabanta na faduwa, ganin motoci kowa na zuba gudu na wucewa yasa sabida irin karfin hali irin nata tasa motan ta shige cikin titin sanan tafara gudu Adan hankali, ganin tana gudu kan titi smooth babu wani tangarda yasa tai murmushi tace “wlh na iya” sanan tawani kara uban gudu tana murmushi, ko kadan bata lura dawani keke napep dake bullowa daga wani layi da mahaukacin gudu ba kawai danno kan keken shi yayi batare dayama kalli titin ba rawa jikinta ya dauka dudda da akwai tazara kadan tsakaninta dashi amman sabida yanda jikinta ke rawa tanason takara kara rage gudun datake kawai ta danna sauri before the blink of an eye jikake kwarap!! Motanta yadaki bayan keken da bala’in karfi tacigaba da tura keken gaba jikinta nawani irin rawa tama kasa taka burki. “Innalillahi wa innailaihi raji’un” tafadi arude kaman walkiya sanan ta ci wani mahaukacin burki dayasa dabata saka sit belt ba data buga kanta a siteri, ganin motan ya tsaya chak yasa dawani irin sauri ta murza key ta kashe motan gabaki daya tana wani irin sauke ijiyan zuciya da sauri dasauri tana kallon keken dake manne da gaban motanta zufa nawani irin keto mata daga goshi takasa ko motsi still in shock.



Dawani kalan sauri direban keke napep din yafito yaci Kwalli a idanunshi yana sanye da Yar singileta daya koma brown tsabagen datti da jeans passengers shi maza biyu suma dake baya duk suka fito yana kallon yanda bayan keken shi yay condemn, sauran motoci sukuma sunata wucewa abinsu tunda dai Allah yakawo sauki hatsari ne da babu wanda yaji ciwo to su karata chan anata wucewa ta gefensu.



Saida mai keken yagama duba kekenshi tass yakalli yanda duka kwan fitilan dake bayan keken suka faffashe sun fadi akasa sanan ahankali yadaga kanshi yakalli glass din gaban motan ranshi amugun bace yana kallon Umma dahar lokacin takasa motsi sai numfashi datake maidawa ita kadai tasan yanda cikin jikinta ke rawa, kafinma mai keken yay magana daya daga cikin passenger yace “durun uwanchan amman matar nan yar bala’in rainin wayau ce Auwal, muna tuki abinmu lami lafiya tazo ta dakan mana keke tamana Wanan uban asaran sanan ta zauna hankali kwance a motanta batama fitoba balle ta duba asaran datayi mana ba”……..





Wani hadadden hilux baka dakana ganinta zaka gane da security personnel ne ke gudu akan titin, ganin titin is congested go slow yasa yashiga  rage gudu yana kalle kalle, wani kyakkyawan saurayi ne ke tukin motar yana sanye da kayan yan sanda, daya bala’in haska farin fatan jikinshi, ahankali yake tuki yanabin titin da kallon ganin yanda motoci suka cika hanya tam ga daga chan gefe gefen titi haka  ya hango accident akayi tsakanin keke da wata mota dayaba iya ganin cikin motan cus tinted glass ne, ga masu keken sun fito suna duba keken su uku kana ganin yaran kasan irin rascals dinan ne, dan tsaki yayi ahankali sanan ya gangara gefe yay parking motan shi, murya chan kasa tace “I hate this job Dad!” sanan ya kashe motan yafito yanadan yatsine fuska tareda maida kofan motan nashi yarufe..…..


Cikin wani kalan bakan zuciya mai keken da aka kira da Auwal da idanunshi sukai jajir danshi kadai yasan wuyan dayasha kafin yasami keken nan mezaicema mutanen dasuka bashi haya, cikin fushi ya nuna Umma dake kallonsu kuri ta glass din gaban motan da yatsa, irin warning dinan yama kasa magana tsabagen zuciya, hakan yasa ahankali Umma takai hannunta ta zare sitbelt sanan tabude kofan motan tafito ahankali jikinta na rawa tana kallon gaban motanta itama dayama bare yay kacha kacha saikuma bayan keken dashi ma ya baci wutan duk ya mutu sun faffashe sun fadi, sanan takaraso ta inda suke tsaye nesa dasu zata bude baki tai magana Auwal mai keken ya tare mata numfashi yace “ke dan ubanki dame kike takama agarin nan dazaki min condem din adaidaita sanan ki zauna cikin motarki batare dakinma fito kin duba barnan dakikayi ba balle kibani hakuri..” sosai kirjinta kewani kalan dukan uku uku hakuri tai niyyan tabashi amman yanda yazagi Babanta yasa taji ranta yabaci, cikin fushi tana kallonshi itama right in the eye tace “karka karayin kuskuren zagin ubana again inba hakaba wlh saina wanka maka mari, besides ma kai agidanku ba’a koyamaka kaduba hanya kafin kashigo ciki ba eh”? Cikeda wata kalan bakar zuciya Auwal yana kallonta da idanunshi da ita kanta taga bala’in dake cikinsu yace “ni kike gayama magana?” Dakewa tayi dudda kirjinta kaman zai tsage tace “ai kai kafara, dama ance idan Yaro bai koyi tarbiya agida ba zai koya a titi, dan haka from today karka kara ganin mutum kai kuskuren zaginshi ko iyayenshi” kafin ma Auwal dake dunkule hannu yay magana passenger sukace “ke wai kinada hankali kuwa kin bugemai keke kinmai asara bazaki bada hakuri ba” wani mugun kallo tamusu tace “kune marasa hankali bani ba, kuma hakurin bazan bayarba kuyi yanda zakuyi” tai maganan zata juya jitayi an wani irin fizgo bayan riganta fut tadawo baya hartana turgeda kafa sabida heel din data saka, wani irin bari jikinta yadauka tana kallon Auwal daya fizgota ganin yadaga hannu zai kaimata mari yasa tawani irin kwala ihu tareda kai hannayenta biyun tana kare fuskanta, shiru taji batare dataji saukan Marin ba akan fuskanta, hakan yasa ahankali kaman wacce tai sata ta shiga janye hannunta daga kan fuskanta tana nishi sama sama sanan tabude idanunta da kyau tana kallon gabanta inda su Auwal mai keken suke, wani mutum tagani dogo fari kal sanye da kayan yan sanda yasha gabanta yana rikeda hannun Auwal daya kawomata mari ya murde, dudda bataga fuskan mutumin ba dan yabata baya but she could see yanda bayan shi keda fadi, gawani kalan bakin suma dake kanshi sun kwanta suna kyalli sosai zuwa shi wajen yasa wajen yadauki kamshin dayakeyi. Daga Auwal har passengers din duka tsurewa sukayi suna mutumin, cikin wata kalan kakkausan murya yace “how dare you raised your hand zaka daki mace akan titi, are u mad!” Yadakamai tsawa yana murde 

hannunshi da kyau ihu Auwal yayi jin azaba yace “officer dan Allah kayakuri bazan karaba, wlh bugemin mota tayi opisa” cikin muryan nan nashi nabawasa yace “and u dare to lift your hand up zaka daketa, cause she is a woman, and she is helpless, alone! Inda kanwar kace fa? U deserve to sleep in jail dukan ku the three of you” sosai suka shiga bashi hakuri, tun tana kallonsu tanajin mesuke fadi har taji kanta nawani irin juyawa kaman tanajin jiri, bugawan da kirjinta keyi yay multiplying da kusan dari hakan yasa gently tajuya tana daura hannayenta akan kirjinta tana kokarin ta saita numfashinta dake mata wuyan kamawa tana kokarin tafiya kawai tafiyan taji ya gagareta wani irin zubewa tayi jikin motan, Karan faduwanta da bugewa da motan datayi yasa dawani irin sauri dagashi harsu suka kallo inda take, ganin yanda take nishi tana beating chest nata tana kokarin numfashi at the same time tana kokarin tashi tsaye yasa dawani irin sauri yasaki Auwal yay inda take.






💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



         ✍🏻M SHAKUR



7️⃣


Ganin Officer yasaki Auwal yay wurin yarinya datake abu kaman mai aljanu yasa suka juya da gudu suka shiga cikin keken su suka ja suka bace atitin saurama kadan sukara wani hatsarin Allah ya kiyaye.

Ahankali ya tsugunna agabanta yana kallonta from head to toe, this is the first time yake kallon fuskanta ganin yanda take fitarda  numfashi da kyar yasa yashiga bin jikinta da kallo kota bugene koko tai sustaining any internal injury ne,or something else but babu any sign ajikinta, ahankali yasake maida idanunshi kan fuskarta yana kallon yanda take breathing not knowing exactly what to do, da kyar ta iya bude idanunta tana nishi kaman zata mutu, dishi dishi take gani sosai but she could see mutum akanta yana kaman yana kokarin karantan wani abu, gently taga pink lips dinshi na motsi kaman magana yake mata amman batajin komi, tashi yayi da sauri ganin kaman something is stopping her from breathing maybe tanada blockage a airways dinta, bude gaban motan yayi ya cire jakanta dake wajen ya wurga kujeran mazaunin direba sanan yadawo inda take zaune akasa, ahankali yasa hannunshi yakamo kafadunta sanan gently yadagata yadauketa yakai ta gaban motan yasata aciki yamaida kofan yarufe sanan yazaga ta dayan bangaren direba da sauri daidai ana kiran sallan magrib yabude kofa yana kallon yanda take wani irin dambe da numfashinta da kyar ta iya bude idanunta ta kalli jakanta daya wurga mazaunin direba dayake kokarin daukewa zai zauna ganin haka yasa dasauri yadauki jakan yashigo motan tareda bude jakan cikin zafin nama yashiga ciro abubuwan ciki, kayan shafa, kudi turare wayanta sai daga dan lungun jakan yaga inhaler.




Ganin inhaler yasa dasauri yadauka yana kallon jikinshi sai chan yadaga kanshi yakalleta, ganin yanda take mimmika tana juya idanu yasa yacire Marfin inhaler dasauri yamika mata ahankali yace “You are asmatic” yanda take nishi yasa tama kasa karban abun da hannunta ganin haka yasa yakai bakinta yamakala mata yana kallon fuskanta cike da tausayi cikin muryanshi dabakaman ta dazuba very soft dashi yace “try and breath in, gently” yay maganan yana kallon idanunta dakokadan basa buduwa da kyau dudda hawaye baya gangarowa but dogayen eyelash dinta were completely moist ga gajerun hawaye dasuka tsaya wajajen idanun kana ganinta kasan tana wahala, ganin eyes dinta nakokarin closing rup gashi takasa jan inhaler yasa ahankali yakai hannunshi kan soft cheek dinta ya bubbuga sau biyu yace “ke open your eyes” dan kadan tabude idanunta ta kalleshi dudda bamata ganeshi sosai sama sama taji muryanshi yace “breath in, breathhhh” kaman wani abu yashigeta wani kalan karfi taji yazo mata taja inhaler, jin wani sanyi har kasan kirjinta yasa dasauri tadaga hannunta bamatasan tadaura akan nashi ba tawani irin kama inhaler da hannunshi da kyau tana shaka da sauri sauri. Har cikin brain dinshi yaji wani yirrr jin hannun yarinyar akan nashi, ahankali yake kallonta tana shakan inhaler tana sauke ijiyan zuciya tana dan natsuwa idanunta a lumshe har lokacin kaman tai bacci.

Almost 10min sanan numfashinta ya daidaita tadena motsi jikinta ko’ina yay relax, ahankali yashiga yunkurin janye hannunshi daga nata gently tabude idanunta, dudda garin yay duhu but baihanata ganin fuskanshi ba sabida hasken motocin dake gittawa ta gefensu, ganin dan sanda wanda she is sure wanda yay saving nata from those guys ne yasa dasauri tasaki hannunshi hakan yasa shima ya janye hannun nashi yakoma mazaunin direba yazauna da kyau, ahankali yace “how are u feeling now”? Ahankali tajanye inhaler, kafin murya chan ciki datai sanyi sosai sabida yanda batada karfi ajikinta tace “I am okay” kallonta yasake yi ganin yanda take zufa tundaga goshinta har wuyanta, calmly yace “can you drive back home”? Batare data kalleshi ba ta girgizamai kai tanajin wani abu na tokaremata wuya she try to swallow it takasa sai kawai tadaura hannayenta kan fuskanta tashiga kuka sosai mara sauti jikinta ko ina narawa, cikin kuka sosai tace “I can’t drive” bata tabajin tsoro kaman nayau abinda ma yasa tai having attack kenan, Binta da kallo yayi yanda take kuka  tarufe duka fuskanta da hannun yace “call your family to come and pick you up then” yay maganan yana mikamata wayanda daya cirosu daga jaka dazu, ahankali ta hadiye kukan sanan tasa hannunta ta share fuskan nata tass kafin ahankali tajuyo tasa hannunta takarbi wayan dayake bata, taba wayan tayi ganinshi amace yasa ahankali kaman mai tsoron magana tace “banida chaji tamutu wayan” shiru yayi yana kallonta, yanabin hannunta datake fidgeting da kallo, yadade ahaka  sanan gently yakai hannunshi ya murza key ya kunna motan batare daya kalleta ba yace “where is your house”? Kallon hanya tayi dudda gabanta nafaduwa amman hakanan taji takasa kin fadamai, ahankali tace “Wuse” dan juyowa yayi yazubamata idanunshi dasauri tasauke kanta kasa tana kara kankame inhaler dake hannunta, murya chan kasan makoshi yace “where at wuse” ahankali tace “Ademola adetokunbo way, gidanmu nakan hanya” jan motan yayi da bala’in gudu dayasa taji wani kalan mugun tsoro yashigeta yana sharara uban gudu akan titi kaman babanshi ne mai hanyan, har sukakai wuse din, zuwa layin sanan tanunamai wani dankareren gate din wani gida, karasawa yayi yay horn, lekowa mai gadi yayi ganin wata rubabbiyar mota da duk gabanta tai dameji yasa yafito daga gate din yazo wajen motan ta side din direba daidai police man din na saukar da glass din motan kasa kafin ma yay magana hango Khairy yasa dawani irin sauri cikin farin ciki yace “Khairy!” Dawani irin gudu yakoma cikin gida daganan gate sukaji muryanshi yana ihu yace “Alhaji tadawo ga Ummulkhairy nan” yay maganan yana bude gate din da duka karfinshi tsabagen murna, wani irin mahaukacin lafiyayyen gida ne mai bala’in kyau, ga mutane wanda kallo daya yamusu yasan iyayenta ne duk a tsaitsaye, barinma matan wanda ya kyautata zaton itace mahaifiyar yarinyar ce idanunta sunyi ja, saiga yayyinta daduk yagani rikeda waya a hannunsu da alamu ita suke kira, yanayin yanda yaga damuwa tattare dasu kuma duk motan suke kallo yasa baimayi wajen parking space din dayaga an tanada a compound din gidan ba yayi gabansu inda duk suke tsaye sanan ya kashe motan, duk suna tsaye suna kallonsu kafin ya Manaf shiya fara motsi dasaurinshi yakaraso bangaren mazaunin direban yabude kofan yana kallonta, ahankali yabude motar yafito yana kallon su Baba, cikeda girmamawa yakaraso gaban Baba dake kallonshi kuri batare dayay motsi ba dagashi har Mama cikeda natsuwa yace “Barkanku da dare Alhaji, nadawo da yarku gida ne, she had an accident akan titin Apo itada keke napep, ina cikin mota ganin hold up I had to step out naga what’s happening nan naga hatsari akayi motanta yadaki na keke napep ga masu keken su uku about to beat her because she couldn’t apologize, I step in nahana su, I was about arresting them naji faduwanta akasa breathing somehow, I had to let go off the keke guy and reach out to her, at first nadauka ciwo taji kafi daga baya nagano she’s asmatic bayan naga inhaler ajakanta, bata dade da regaining senses nata ba, ganin she can’t drive, I try to make her call family ta but wayanta akashe I had to ensure her safety dan yarinya ce kuma is not safe for her tadawo gida dakanta, saisa nadawo da ita, here is the car key” tunda yake maganan daga Baba har Mama da yayyinta da ita kanta Khairy da Manaf yafito da ita daga mota kanta nakan kirjinshi tai lamo  kallon police man dinan dako rufamata asiri baiyi ba take, like babu an atom of lie a maganan shi.

Kafin Baba yay magana cikin tsananin bacin rai da damuwa Mama tace “Alhaji kaga abinda Khairy keyi ko, wai Khairy kadai na haifa aduniyan nanne da ita kadai kebani ciwon kai, ga maza yayyinta har uku da sune yama kamata suyi rashin ji amman basuyi sai ya mace ce keyi, yanzu inda wanan bawan Allah this kind hearted officer ya ceceta ba da Allah kadai yasan mezai faru, Allah kadai ne zai sakamai da alkhairi, inda ace bai taimaka mata ba kunsan kalan dukan da masu keken nan zasuma Umma eh, wlh……” dasauri Manaf yace “Mama please we are not alone here” cikin fushi sosai Mama tace “abinda kukeyi kenan dagaku har mahaifinku saisa Khairy duk ta baci haka, zaki gamu dani Khairy” tama Khairy wani mugun kallo taredayin kwafa sanan tawuce ciki fuuuu cikeda bacin rai. 


Dan murmushi Baba yayi sanan yasa hannu yakarbi car key dayake bashi anatse yakai hannunshi yakama na officer cikeda murmushi yace “thank you, nagode nagode, I can’t even thank you enough, Allah yamaka albarka for saving Ummulkhair, nagode officer, Allah yamaka Albarka” gyadamai kai ahankali yayi yace “saida safen ku bari natafi” dasauri Baba yace “bari Mu’az yakaika wajen motanka please is late” dasauri yace “a’a Alhaji, dare yayi, yazauna agida I can manage, saida safen ku” yay maganan yana juyawa zai wuce dasauri Baba yace “youngman, I mean officer” jin Baba yakirashi yasa ya tsaya tareda juyowa yakalli Baba, ahankali Baba yace “baka fadimin sunanka ba” dan jim yayi yana kallon Baba kaman bazaiyi magana ba sai chan yace “sunana ASP Aliyu Hydar Zango” gyadamai kai Baba yayi yace “Allah maka albarka Aliyu Hydar” murmushi kadan yayi tareda juyawa yana tafiya one one kaman Gwarzo yawuce yafita daga gidan.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



        ✍🏻M SHAKUR



8️⃣



Ajiyan zuciya Baba yasauke sanan yajuyo da kanshi yazubama Khairy idanunshi da kallo daya tamai kawai tafashe da mugun kuka, duk duniya babu wanda take tsoro kaman mahaifinta, Baba is the best father amman not just her kowa tsoron fushi Baba yake agidan nan sai Mama dan idan Baba ya burkice ko ita bata iya taroshi, tsugunnawa tayi awajen tana kuka sosai tace “Baba dan Allah kayakuri wlh wlh bazan karaba please I am so sorr…..” baima jira sauran maganan ta ba yawuce ciki shima fuuuu, cikeda tashin hankali takalli yayanta tace “Ya Manaf na shiga uku daga Baba har Mama fushi suke dani” cikin fushi Mu’az yace “da murna kikeso suyi dake sabida bakida hankali do you know how worried they were, saida akasa direba yakoma gidan bikin nan amman baaa ganki ba wai kintafi, Khairy tunda kike arayuwan ki kintaba tuka mota ne dazaki fara yau inda kinje kin kashe kanki ko kinjima kanki ciwo da yaya kikeso muji eh, kawai gakinan ne girma kawai kike amman bakida hankali ko kwara daya stupid girl” yawuce yajuya yay flat dinsu, hararanta Maheer yayi dudda tabashi tausayi yace “babu abinda ta iya sai rashin kunya da tara kawaye, inda police man dinan bai ceceki ba dakin gane shayi ma ruwane, fitsararra kawai” shima yajuya yatafi, ahankali Ya Manaf yasa hannu yadagota yace “stop crying muje kije change this clothes shower kici abinci and sleep” yay maganan yana sakinta yakoma mota ya tattara kayan jakanta yahada mata ya rike sanan yazo yakama hannunta suka shigo falon, Baba kadaine zaune a falon yana rikeda jarida hakan yasa sukai hanyar stairs, cikin kakkausan murya Baba yace “kawomin wayan ki nan” wani irin fashewa da kuka tasakeyi sosai jikinta har rawa yake ta karbi jakanta daga hannun ya Manaf ba musu hannu tasa taciro wayan sanan ahankali tana sheshekan kuka takaraso wajen Baba tabashi wayan, karba yayi ya ijiye gefenshi, sanan yajuyo yakalleta yace “Ummulkhair” muryanta har shakewa tayi tace “Naam Baba” cikin kakkausan murya yace “I ban you from going outside this house for a whole week” zubewa tayi agabanshi tana girgizamai kai tace “Baba please I am sorry dan Allah” cikeda fada yace “nabata ki dayawa, nabaki freedom dayawa kullum your Mum is complaining yau nagani da idanu na, dan haka bazaki saka kafa kifita daga gidan nan ba dagayau har zuwa kwana bakwai, ba school ba islamiyya, sanan ko friend naki guda daya nazo nagani kokuma aka gayamin tazo saina kulleta, i will even tell the gateman koda wasa yabar kawayenki suka shigo cikin gidan nan abakin aikinshi dan haka duk wacce tazo yacemata ma bakinan kowani abun I don’t care” sosai take kuka tana girgizamai kai Baba baitaba mata Wanan kalan punishment dinba tsawa yadaka mata. “tashi daga gabana!” da sauri ta tashi tawuce sama da gudu tana kuka Ya Manaf yabita da kallo yay jim sanan ahankali yadawo falon zama yayi kusada Baba ahankali yace “Baba please kayakuri, punishment dinan yay tsauri dayawa, Khairy batada hankali har yanzu Baba, mudena kallonta kaman wata Babba sabida tana final year a school, Baba she is just 20, yanzu shine lokacin her growth, lokacin datake feeling she’s capable itama takai matsayin ahankali zamu nuna mata this and that, but Baba hanata fita, hanata zuwa school, karbe wayanta, dakuma Hana kawayenta zuwa wajenta I feel is too much Baba, she will be depress” wani mugun kallo Baba yamai yace “Manaf koyamin tarbiyan yara kake?” Cikeda girmamawa yace “a’a Baba” cikin kakkausan murya Baba yace “to tashi daga nan wajen” ahankali yatashi zaiyi sama Baba yace “barin flat din nace kayi katafi naku” ganin ran Baba abace yake sosai yasa baiyi gardama ba ya sauko yazo yajuya yafita daga falon.


Waya Baba yadauka yakira wata number, ko 10min baa daukaba wani doctor magidanci haka yazo, tashi Baba yayi sukai sama, afalon sama Baba yanunama Dr kujera ya zauna sanan yawuce dakin Khairy saida yafara knocking sanan yashiga tana zaune kan gado ta chanza doguwan rigan jikinta tasa wata na Atampa simple tasa hula akanta idanunta sunyi jajir sundan kumbura, tana ganin Baba dasauri ta kwanta, ba Yabo ba fallasa yace “fito adubaki” yay maganan ya tsaya yana kallonta tashi tayi ahankali sanan tasaka slippers juyawa Baba yayi tabishi abaya suka taho falon gaida Dr tayi sanan tazauna, dubata yayi yamata yan tattanbaya tana bashi amsa sanan yabata wasu magani guda biyu kafin yakalli Baba yace “shikenan Alhaji” kallonta Baba yayi yace “wuce kitchen kije kici abinci kisha magani” gyadamai kai tayi sanan yajuya shida Dr suka fice, saida sukakai waje wajen motanshi sanan Baba yace “are you sure Dr she’s okay?” Dan murmushi yayi yace “eh, ai Asmanta yaragu sosai bakaman da ba datake having constant attack, I am telling u abinda ma yatada nayau was mugun tsoratan datayi saisa numfashinta yafara mata wuyan kamawa, wlh she’s very lucky tasami wanda yataimaka mata she would’ve lost….” Dasauri Baba yace “Alhamdulillah she’s fine” gyadamai kai Dr yayi yace “yes, bari idan anything change call me, but for now let her relax and rest system dinta yahuta, magungunan dana bata zaisata bacci sosai” gyadamai kai Baba yayi suka gaisa yashiga motanshi yaja yawuce.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



        ✍🏻M SHAKUR




9️⃣




Wuraren 5 Baba ya shigo da kanshi yatadata don sallan asuba, da kyar ta tashi saida yaga tashiga bayi sanan yajuya yafice, tana idar da salla da kyar ta iya lallabawa takoma gado sai wani baccin.


Wuraren 11:30 ta tashi daga bacci, ita kanta wani dadin jikinta taji taji, ahankali ta tashi zaune tasauke kafanta kasa tana kallon dakin, dakinta very clean and very fine kana ganin dakin kaga dakin wacce akeji da ita, tashi tayi ahankali dagakan gado tai wajen window dakinta bude window tayi haske yawani daki fuskanta lumshe idanu tayi kafin ahankali tabudesu starring into compound dinsu that is very fine  idanunta suka sauka kan motar ta da ake pake agidan, faduwa gabanta yayi ganin yanda gaban motan yay completely baci, maida labulen tayi tarufe window feeling sad sai yanzu ta tuna abinda yafaru sanan tawuce tashiga bayi, wanka tayi tafito daure dawani pink towel, karasawa tayi gaban madubi takalli kanta kodan tayi bacci sosai ne gani tayi tana wani kalan sheki, fatarta nawani kalan glowing and sparkling, yatsine fuska tayi sanan tawuce tadauko kaya a wardrobe tasaka wani pink half gown na cotton, batama tsaya daura dan kwali ba tasaka slippers kawai tafito gabanta na dukan uku uku tsayawa tayi wajen bene taleka falo ganin Mama bata falo yasa ahankali tajuyo tai gaban dakinta, tsayawa tayi sanan tasauke ijiyan zuciya ahankali tasa hannunta tai knocking ahankali, jin baaa amsaba kuma ta tabbatar Mama naciki yasa ahankali tabude kofan dakin tadan leka tana shiga ciki, hada idanu tayi da Mama dake zaune kan couch na dakin tana karanta wani Littafin zikiri dake hannunta, babu ko alamun wasa akan fuskanta tace “fitan min daga daki Ummulkhair” dan rau rau tayida idanunta kaman zatai kuka murya chan kasa kaman na Yar baby amugun shagwabe tace “Mamaaa sorrry please, kinj….” “Get out of this room Khairy” gyadama Mama kai tayi ahankali sanan tajuya tana tafiya kaman wacce ke koyon tafiya tana tunanin abinda zatayi Mama tahakura kaman daga sama Mama kawai taji Khairy taja wani uban nishi tana bubbuga kirjinta tayi baya zata fadi, wani kalan salati Mama tasaki tawani ijiye Littafin kan kujera ta taso dasauri ta tareta da hannayenta tace “Subhanallahi Khairy, Khairy, ina inhaler ki”? wani kalan dadi taji ya lullube ta ganin yanda Mama harta tsorata ta taso, kawai Mama gani tayi yarinya ta kankameta tafashe dawani sangartaccen kuka ajikin Mama tace “Mama please kiyakuri wlh wlh bazan kara abinda nayi jiyaba I promise Mummy, kikai fushi dani ina zansa kaina eh kinaso in mutu ne da ciwo? U are my best friend Mama, u are my happiness kika shareni I will be shattered, Mama dan Allah kinji smile for me haba my world best, best of the best, bestest, the best Mama in the world, Mama dan Allah kiyafemin” tai maganan tana kara kankame Mama kaman wata yar yarinyar da baa dade da yayewa ba, dudda yanda ran Mama yake abace amman saida jikinta yay sanyi sosai, ahankali tadaga hannayenta taciro Khairy daga jikinta ta tsare fuskanta da idanu hardan rama tayi ga hawaye sun cika idanunta, Mama takai hannunta ta share mata idanu sanan takama hannunta tajata zuwa bakin gadonta zaunar da ita tayi sanan tazauna agefenta tana kallonta ahankali tace “Ummulkhair bakiji, ba fushi nake dake ba I am only trying na nuna miki kuskurenki, ke y’a mace ce bazaki dawwama agidan mahaifinki ba dole zakiyi aure kije gidan mijinki, i want to teach you not just life but how to live life Khairy, inaso nakoya miki rayuwa dakuma yanda ake zaman duniya lafiya, ke mace ce Baban ki da yayyinki cannot teach you abinda ni mahaifiyar ki mace zata iya koyamiki, akwai mutuwa, akwai ciwo, akwai kuma tsufa any of the two can happen to me Khairy yaya zaki kare eh? Kin taba tunanin, wanan kawayen yau baki bikin wanan gobe baki bikin wanchan kene aganki achan gidan bikin kina tika rawa ko achan birthday kina tika rawa ko Micheal Jackson yaganki kina rawa saiya baki fili yarinya saikace rainon dujal, what are all this behaviors Khairy? Sabida ana cewa ke yarinya ce kinsan yara nawa wanda ma kin girmesu sukai aure suka hayyayafa eh? Yanzu abin haryakai kija mota dakanki ki shiga titi da daddare Ummulkhairy idan da wani abu yasameki how do you want me to cope? Kasheni kikeso kiyi da damuwa?” Dasauri ta girgizama Mama kai ahankali tace “Mama bazan karaba wlh” Ijiyan zuciya Mama tasauke ahankali sanan tai murmushi tana kallon yanda idanunta sukai zuru zuru long kalaban kanta duksun barbaje sun sauko fuskanta, hannun Mama takai ta gyara mata gashin sanan ta shafa fuskanta tace “ke kadai ne y’a mace da Allah yabani aduniyan nan Ummulkhair, inaso ki natsu, wisen up, anything can happen to me, and I want you to be able to take care of yourself, su Manaf, Mu’az da Maheer, you will be their Mum, kindaiga banda kowa, I told dukanku labarin nan agidan marayu Baban ku yaganni ya auroni ina gidanshi nai karatu, bansan any family naba dazance yau idan bani inada wata danasan zata rikeminku tsakani ga Allah so I want you to take after me kinji, ki natsu and know what you are doing” fashewa da kuka tayi ahankali duk zuciyanta namata nauyi da duhu, bayan hannunta takai ahankali ta share idanunta sanan cikin sheshekan kuka tace “Mama maisa duk idan namiki laifi saikitamin magana kaman zaki mutu eh? Wlh Mama bazan karaba na rantse da Allah kinji, dan Allah kayakuri kuma kawayena zan ragesu, Mama I love you a lot please kidena fushi dani kuma kidena magana haka kinji, Mama you will leave long har yarana zaki goya” murmushi Mama tamata she just wish zata iya daina mata magana hakan, kumatunta taja cikeda so tace “oya stop crying inba hakaba I will snap your face natura a group dinku na nunama friends naki sugan cewa the famous Khairiry dinsu is a crying queen agida” dasauri tasa hannu tashare fuskanta ta washe jerin white teeth nata kananu dakeda bala’in kyau tace “Mama nadena” dan dariya Mama tayi tace “oya je bude drawer nan nawa ki kawo comb da kipiya ayi wanan tsifan” da sauri tasauka dagakan gadon tai wajen drawer dakin Mama tabi bayanta da kallo wani irin girma Khairy keyi da batasan ina zatada girma ba ga shape kaman ita tai kanta, daukowa comb da kifiyan tayi tajuyo Mama tabi damemmen cikinta da kallo tace “wuce kidebo breakfast kidawo” tai maganan tana karban comb din hannun nata, juyawa tayi tafita daga dakin koba komi ta lallashi Mama tahakura saura Baba shikuma da Baffa zata hadashi simple.



Dinning taje, plate tadauka tana bude kula, chips tadeba da sausage batare data taba kwan wajenba sanan takada tea tajera komi a tray tadawo dakin Mama, ganin Mama na rubutu da pen a dairy dinta wanda inda sabo tasaba ganinta tana yan rubuce rubuce aciki yasa tai murmushi ijiye abincin tayi anan kasan carpet sanan ta taso tazo inda Mama take tana kallon abinda take rubutawa da sauri Mama tarufe dairy tadago kanta tana hararanta tace “lpy” turo baki tayi ashagwabe tace “Mama handwriting dinki nake kallo fa, wlh Mama handwriting dinki yafi harna Baba kyau, inama nine nakeda fine handwriting haka, amman rubutuna kaman tafiyan tsutsa” hannu Mama takai ta dakamata duka a kafa tace “kincikani da surutu wuce kije kiyi breakfast kizo namiki tsifan” wucewa tayi tana dan dariya sanan tazauna tanacin abincin tana wasadashi kaman wata yar yarinya Mama kawai ta tasata agaba tana kallo, saida tagama sanan ta kwasa tafita dasu kafin tadawo Mama tahaumata tsifan kan.



💫 ALKAWARIN ZUCIYA💫



        ✍🏻M SHAKUR


🔟

For those asking me how to subscribe Dan shiga group din danake posting all you have to do is pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na.



Dan magana dani directly click on this link

wa.me/+2347012181461



*******

Free page

UK

Karan wayanshi yatadashi daga dan gajeren baccin dayake yi mai dadi sabida shishan dayasha harya bugar dashi, ahankali yasa hannunshi da kyar yajawo wayan sanan yakai gaban fuskanshi yakalli screen din ganin Dad yasa duka baccin idanunshi suka washe da sauri yatashi yana gyara zama ya matsar da shisha pot din gefe sanan yadaura wayan nashi akunne cikeda girmamawa yace “Abba ina yini” daga tachan bangaren cikin muryan dattaku irin muryan daba na yaraba dinan kanaji kasan na Babba ne yace “Zayn naji muryanka wani irin lafiyanka kalau”? Dan yatsine fuska yayi yarasa maisa Abba always gets him, kafin yadan saki murmushi yace “Abba bacci ne daman yadan kwasheni amman nariga natashi, yasu Ammi Abba?” murmushi Abba yayi mai dan sautin ta wayan yace “Ammi dakowa duk suna lpy, Matar kaninka Hafiz tahaihu ansami y’a mace” dan ware idanunshi yayi cikeda mamaki dakuma farinciki sosai yace “Masha Allah, Allah ya raya mana” anatse Abba yace “Ameen ya rabb, when will you be rounding up PHd dinan Son”? Ahankali yace “nan da 2months Abba In sha Allah” “Uhmm” Abba yafadi yana gyara murya yace “Masha Allah Allah yasa kagama lpy Allah ya sanya Albarka acikin sa” ahankali yace “Ameen Abba” dan gyaran murya Abba yayi yace “Zayn tunda kataso bama kai kadai ba duka yaran dana haifa aduniyan nan I always give you all abubuwan dakukeso, I support dreams dinku with all I can, Zayn tunkana yaro dan kankani na lura kai yaro mai kwazo ne sanan gason karatu, I supported you sabida inaso kai leaving dreams dinka, bantaba complain ba dan buri na shine kagama duka karatun dakake, Hafiz yana gama masters dinshi yanuna shi aure yakeso I supported him as well da sauran kanninka mata, burina amatsayina na mahaifi shine naga yarana na cikin farin ciki sanan suna rayuwa yanda sukeso madaman bai sabama koyarwan ma’ikin Allah ba tsira da amincin Allah su tabbata agareshi, dan haka Zayn dazaran watan nin nan biyu dakafadi mini yanzu sun cika, inaso ka tattaro yinaka inaka kadawo nan naijeriya, kafara aikin ka anan sanan kai aure kaima ka natsu kanajina” ahankali yace “eh Abba” yanadan yatsine fuska me a aure please da all this Nigeria’s father values it so much, aure is problem, damuwa ce kawai tacika aure, shifa baijin zai iya rayuwan da he will cater for someone ba, ko babes dinshi whenever he’s honey he feed on them idan yagama ya tashi ke kikasan yanda zaki da kanki, ina zaiwani iya aure dashi zai dinga kulada wata, lallai! “Zayn kanajina” yaji maganan Abba dasauri yace “eh Abba” Abba yacigaba yace “kaine Babban d’ana, tsufa yazo Zayn inaso tun yanzu da raina da lafiyana nahada kan yarana agari guda, yau da wani abu zai sameni kaine babba kaine zaka rikemin gida, dan haka nasanka da natsuwa Zayn dakuma tsoron Allah amman bazan gaji da gayamaka ba kadingajin tsoron Allah aduk inda kake sanan ka kiyayi abokanai marasa kyau, Allah maka albarka, idan na ijiye wayan nan zan aika maka da kudi kaji” dasauri yace “Abba no, inada kudi kamanta ina musu aiki anan ana biyana duk wata” anatse Abba yace “kudin aikinka daban kudin na ni mahaifinka daban as long as bakai aureba baka da iyali naka na kanka nine komi naka Zayn Allah maka albarka” murmushi yayi har cikin ranshi yanason yanda Abban shi ke sonshi, kobakasan komi nagidansu ba dazaran kashigo gidan kagansu duka kasan Abba yafison shi kan duka yaran daya haifa shi kanshi baisan mesa ba, kowan nan zancen haihuwan he’s sure yanaji yakirashi before Ammi kanta takirashi Abba yakirashi sau dubu, Karan alert dayaji yasa yakalli wayanshi, $10,000 dollars yagani, murmushi kawai yayi ya ijiye wayan yatashi yaje yay wanka yasan nan bada dadewa ba shima Hafiz zai kirashi.



Wanka yayi ya shirya cikin wani dan gajeren wando mai bala’in kyau black sai farin riga, feffesa turare yayi sanan yasaka wani black crocs na designers dayama white kafanshi kyau sosai kaman kafan bature, kana ganinshi kaga irin yaran yan gayun nan yan hutu kuma yan iska at the same time sanan yawuce akan table yadauki car key nashi yabude kofa yafito yanadan yatsine fuska ganin rana yafito yau sosai, ciki yadawo yadauki sunglasses dinshi yasaka kafin yafito yaja kofan nashi yarufe sanan yasauka kasa, motanshi yabude yashiga sanan yafice daga gidan yana mahaukacin gudu abinshi waka natashi daga motanshi.



Tana ganin fitanshi zama tayi dirshan anan wajen window jikinta ko’ina narawa kaman zata haukace inda ace zaa gayamata Zayn yamata magani ne da wlh zata yarda sabida wani wutan sonshi datakeji azuciyan ta is another thing, ganin kaman zuciyanta na neman daina aiki yasa ta tashi tadauki wayanta akan dinning tai dialing number Jully, ringing daya Jully tadauka kafin ma Jully tai magana tahau mata magana kaman wacce tazare. “Jully if u ever love me Jully please help me, Jully zan mutu, soyayyan Zayn is about to kill me, I was sent to school amman nakasa komi na school I keep stalking yaron dabaimasan inayi ba, wayyo Allah na wlh zuciyanta kaman ta kumbura sabida son Zayn I just want him, I want him so bad sosai, I want him to hold me, hug me kiss me And tell me he loves me, i am loosing my head my mind and my whole soul, ina tsoron kar watarana ki tashi kiga na mutu because of Zayn, nagayamai yau ina sonshi all he did was slam the door afuskana, Jully help me please” bakaramin tausayi Ayshu tabata ba jitayi kaman tamata kuka, murya chan kasa tace “Ayshu calm down, I am coming don’t do anything just give me 5min u will see me kinji” gyadamata kai Ayshu tayi kaman tana ganinta sanan tacire eayan daga kunenta ta ijiye akasa itama takoma kasa gaban dinning ta zauna idan kaganta zaka dauka ta haukace tana zaune awajen taga wayanta yahau ringing Mommy tagani amman takasa dagawa, wajajen 10min tana zaune awajen saiga Jully tashigo tana sanye da Riga da jeans, da handbag dinta a hannu ganin yanda Ayshu tazauna akasa idanunta sunyi jazur sun chanza launi tsabagen damuwa yasa dasauri tai inda take zama tayi kusada wajen tana kallon fuskanta tace “Ayshu look at you My baby, Ayshu you need help I think we should go see a Doctor” girgiza mata kai tayi cikin wani kalan yanayi tace “Jully I love him, I am madly inlove with…..” “someone that doesn’t even know about your existence Ayshu, yaron nan never loves any woman ke u are an eyewitness yanda kike stalking nashi kina ganin yanda yake chanza babes, kina ganin yanda yake rayuwa, and u still love him kinason ki karake like all his other women” ga mamakinta gyadamata kai Ayshu tayi tace “eh, as long as he will be with me, smile with me, hold me lemme feel his warm soft skin akan nawa and those his succulent lips while he stares into my eyes dawayan nan sexy eyes din nashi dat always look kaman yanajin bacci I want, his eyes use to make my body cringe,Jully I want Zayn” kallonta kawai Jully take dan kawarta is obsess, one a scale na 10, Ayshu is even more than 10 dawanan fitinannen son datakema yaron nan, ajiyan zuciya tasauke tana kallonta tace “Ayshu I want you to define the terms in your own way, sama da kowa kinsan cewa yaron chan is not the love type kinsan cewa bala’in dan iska ne shi, f**k boy and a play boy, Ayshu tell me what do you exactly want from him tunda kinsan shi waye shi” shiru Ayshu tayi tana kallon Jully kafin ahankali tace “I want to sleep with him! I want to know him in and out, I want to have koda one single memory nawa da shi wanda I will always dwell akanshi, I want to share something da Zayn Jully….” Ajiyan zuciya Jully ta sauke tasan menene so amman harga Allah bataso kawarta taso Zayn ba she prefers her Kabir dakenan kaman zai zare akanta amman tace sai Zayn, jakanta tabude sanan taciro wani dan karamin white kwalba dawani blue liquid abu ke ciki tamikama Ayshu, kallonta Ayshu tayi sanan takalli kwalban abin batare data karba ba tace “what is this”? Dan murmushi July tayi tace “this is ur problem solver u have no idea nawa na kashe yanzun nan kafin na iso wajen nan kafin yaran nan su saidamin da abin nan, yanzu dai not that bakince kinsan password din kofanshi ba” dasauri Ayshu ta gyadamata kai, murmushi Jully tayi tace “perfect, u see this serum is for shisha acikin shisha ake zubawa nasanshi kuma he always take shisha, zaki shiga dakinshi get his shisha pot kibude ki kwara serum din aciki” dasauri bakinta har rawa yake tace “mezai faru idan ya kunna shishan ya sha to bayan najuye” hararanta Jully tayi tana murmushi tace “u don’t wanna know” cikeda kosawa tace “please tell me Jully” ahankali Jully tace “this serum dakike gani will turn dat guy to a beast, ke he can even cry for you and beg you kibashi yaci inba hakaba zaiji kaman zai mutu” wani kalan tashi Ayshu tayi da sauri tana karban abin daga hannunshi tace “bayanan Bari naje nasaka” kafinma Jully tamata magana hartai kofa tabude tafice Jully kawai tai shiru bata taba ganin so irin na Ayshu ba tsabagen yanda take monitoring activities nashi har password na kofanshi tasani, she just hope this satisfy whatever crave it is dayake zuciyanta ko tayi concentrating a school tana zaune a inda take saiga Ayshu tadawo da empty bottle din tana dariyan jin dadi sosai tace “done” dariya Jully tayi tace “to mutafi school munada lectures” make kafada Ayshu tayi tace “what if yadawo anjima basai dare ba, kedai kitafi ni yanzu ma Mommy zan kira ta kirani dazu ban amsa ba” tashi Jully tayi tace “natafi” bye friend…..



Tana zaune all ranan a falo bai dawo gidan ba as usual sai wajajen 1 nadare yashigo gidan, sai addu’a take karya dawo da wata, ganin shi kadai yadawo yasa taji zuciyanta yamata wani dadi daki yawuce yay wanka sanan yafito da boxer as usual tana ganin inuwanshi ta madubi, dauko shisha pot dinshi yayi ya kunna sanan yazauna kan kujera yana tattaba wayanshi kafin taga yamika hannu yadauki pipe din wani tsallen dadi tafara tana yes yes take it, zuka yayi yana tattaba waya sanan yafito da pipe din ya busoda hayakin waje kaman zata haukace sabida dadi rawa tafara sosai.


Comfortably yakeshan shisha shi yana streaming online kafin chan yaga message na Hafiz yaturomai pictures dasauri ya shiga watsapp din yabude hotMunan yana dubawa na baby ne yanadan murmushi he love babies.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫


        ✍🏻 M SHAKUR 



For business advert or promotion chat me up directly on watsapp by clicking on this link:

wa.me/+2347012181461




1️⃣1️⃣

Dan lumshe idanu kadan yayi yabudesu da sauri tareda ijiye wayan tsigan jikinshi nawani kalan tashi  gabanshi na mahaukacin tashi da baida control of, maranshi na murdawa yanajin wani irin bukata dashi kanshi baisan daga ina tazo ba, shishan yashiga sha da sauri da sauri kozaidan bugar dashi yasakashi bacci yanadan tsaki cikeda kulewa yace “shit!” He don’t even know ko shishan karamishi yake oho jiyayi his world is clouding and going sideways, ahankali yasaki pipe din shishan yawani fadi akasa yana cizan lips idanunshi na kankancewa sosai yana sauke ijiyan zuciya kadan kadan, hannunshi yamika yadauko wayanshi daya yar agefenshi da kyar dayan hannunshi kuma yana kaiwa kan boxer cus he’s having mad pains, wayanshi yabude amman bayama gani da kyau ko kadan dazaima iya kiran daya daga cikin yammatan shi, kofanshi yaji anbude anshigo dasauri yajuyo da jajayen idanunshi yakalli wajen, Ayshu ce tashigo tasaka wani red rigan bacci very transparent dababu abinda baya gani ajikinta, tasaki braids dinta kasa tai wani kalan kyau lips dinta na shinning na red janbakin data saka, wani kalan ijiyan zuciya yasauke jijiyan kanshi na fitowa waje tsabagen jaraban dayakeji dakewa yayi yana cizon lips dinshi da kyar ya iya tattaro karfinshi gabaki daya yace “what are you doing here”?  wani kalan murmushi tayi dan yau farin ciki takeji takaraso har inda yake tsugunnawa gaban kujeran itama tayi dab dashi tana kallon fuskanshi da kirjinshi dakenan very very huge ga fadin bala’in gawasu sexy hair dakenan akwance lup lup  kamshin nan nashi da ko daga mafarki aka tadata zata iya cewa shine na shiga hancinta yana penetrating azuciyanta, ahankali takai yatsanta dake rawa tsabagen yanda take shakkan shi amman tadaure tace “I come to sleep here don’t u want my company” yanda take yAwo da yatsanta akirjinshi kafin tai landing akan nipples dinshi tawani murza nipples din yasa yasaki wani kalan kara. “Mmmmmm” murmushi tayi bata taba sanin she can see Zayn like this ba looking so vulnerable yana pleading with his eyes ma har body sabida yanda yakebin kirjinta da kallo da idanunshi dasuka kankance, janye hannunta tayi daga kan nipples dinshi, ganin yanda yake kallonta without action and ita action takeso yasa ta mike tsaye tana wani irin tafiya tana juyamai ass dinta dayake ganin komi ta rigan tadan waigo ta kalleshi tace “come nabaka abinda kakeso, it’s all yours” saida takai daidai hanyar bedroom nashi sanan ta tsaya tajuyo takalleshi ganin har lokacin kallonta yake kaman wani maye she can see yanda eyes nashi suka nuna how badly he wants her, rigan jikinta tawani cire tayar anan gaban kofan bathroom din sanan tawani juyo tana shafa yan matsakaitan boobs dinta tana lashe lips tana kallonshi, wani kalan tashi tsaye yaye ita kanta saida gabanta yafadi ganin yanda boxer jikinshi yatashi kafin tagama tunani jitayi anwani fizgota kaman rago yaaaaa kawai taji ya yaga pant na jikinta kafin yabude kofan bedroom din kawai taji yawani wurgata kan clean royal gadonshi…..




Ahankali take bude idanunta dasuka mata bala’in nauyi, ko’ina najikinta yay wani kalan tsamin gaske, ijiyan zuciya tasauke tanabin gadon datake kai da kallo tana kara lumshe idanu kaman karta tashi takeji, kawai sotake tacigaba da shakan wanan kamshin turaren datakeji nashi komi najiya da daddare nadawo mata she is just sure sumewa tayi, oh my God anya akwai namiji kaman Zayn aduniyan nan kuwa!man that guy is fire in bed. 

Ahankali tana cizan lips dinta ta tashi zaune tana kallon agogo dake gefen side drawer nashi 11:30 nasafe, dakinshi tabi da kallo dakin is so clean very neat, babu datti kodaya, wow! 

Da kyar ta iya sauke kafafunta a kasa sanan tamike tsaye komawa tayi dasauri tazauna dan pains din datakeji ko lokacin datai sex d first time da KB bataji irin wanan ba, tadade ahaka sanan tadaure takara tashi tana kallon bakin kofan bedroom din datagani abude ga riganta na jiya akasa inda tacire tanarshi nan yake karasawa tayi ahankali ta tsugunna tadauka sanan tasaka kafin tadau pant nata daya yaga yake kasa shima tadukunkune tarike a hannu sanan ahankali kanta na kasa tafito falon tana tafiya kadan kadan dan batason ta nunamai ragonta ko wani gazawa nata ko gajiya, yana zaune akan kujera dagashi sai towel a waist nashi yana video call dawata baturiya awaya dan kallo daya tamai ta hango baturiyan a screen nashi, sai kiranshi baby baby take yana murmushi while sipping coffee hankalinshi kwance, gefenshi yan bandur bandur na dollars guda uku ne, kasa jure kin kallonshi tayi tadan juyo tana binshi da kallo kozAice mata wani abu amman kaman baimasan dawata a falon ba magana yake anatse ayangance yana sipping coffee abinshi, daurewa tayi ta wuceshi tai hanyar kofa harta bude kofan zata fice kaman daga sama taji muryanshi yace “you, Hey” danshi harga Allah he don’t even know her name, dan juyawa tayi jin yana kiranta takalleshi ahankali lips nata narawa tace “mu…me?” maida kanshi yayi kan wayan yace “excuse me babe just a sec” sanan yadaga kanshi yakalleta yana nunamata kudaden gefenshi yace “come get this ur pay” wani kalan kallo tamai her pay yadauka ita Yar iskace kaman sauran karuwanshi komene, juyawa tayi dasauri zata fice daga dakin feeling insulted and dan graded. “dont!” Yafadi babu alamun wasa kan fuskanshi, juyowa tayi yakalleshi jitayi zuciyanta na bugawa fast fast hakan yasa tama kasa motsi kawai ta tsaya inda take kaman jira take yabata, kudin yadauka hankalinshi nakan wayan jin yarinyar Namai magana sanan yajuyo yakalleta yajefamata yace “u can throw them away outside but just get them out of my room okay, is ur fee” yana gama maganan yacigaba da video call din dayake abinshi tadade tana kallonshi kaman bashine yake ihu kaman zai haukace akanta jiyaba kafin ahankali ta tsugunna tashiga kwashe kudin ita kanta batasan Mesa take daukan kudin ba all she knows is bataso ta batamai raine sabida wutan sonshi dake cinta arai amman batada abinda zatai da kudin nan cus she lacks nothing. Tashi tayi sanan takara satan kallonshi yanda taji yake dan dariya kadan kadan very classic kaman baisan da wata adakinba sanan ahankali tajuya tafice idanunta sunyi jazur, dakinta tabude tashiga Jully tagani zaune ganinta yasa Jully ta mike tsaye tana binta da kallo tundaga sama har kasa tace “how far Ayshu” wani irin kuka Ayshu tafashe dashi dake kunshe da farinciki bakin ciki dakoma wani kalan emotion tarungume Jully ahankali tace “Jully thank you, u are the best friend in this world” murmushi Jully tayi tace “go and shower stop thanking me, u look terrible” dan dariya tayi tasaketa tana goge fuskanta tawuce tana tafiya ahankali tai daki Jully tabita da kallo ganin yanda yakusan kasheta, girgiza kai kawai tayi ance idan kaga abinda yafi karfinta and bakada abinda zaka iyayi sai ka girgiza kai, kitchen tawuce tanada mata tea lafiyayye da chips sanan tazuba komi tai arranging a tray, tanada paracetamol tasamata akan tray din, tai bedroom dinta, akan gado taganta zaune tasaka wani simple english gown, karasowa Jully tayi ta ijiye tray kan gado tana kallonta tace “are u sure u okay”?  murmushi Ayshu tayi tace “kinga yakusan kasheni ko, what can I say Zayn is a beast” tai maganan tanadan lumshe idanu sanan tabude takalli Jully tace “wlh Jully Kabir is not a man I just wasted kaina akanshi, kinsan ko saida Zayn ya sumar dani” zaro idanu Jully tayi tama kasa magana lumshe idanu Ayshu tayi sanan tawani kwanta akan gado tana tunani tace “Zayn handles me like a beast, kinganshi haka baya surutu bantaba sanin he’s such a talker ba sai last night, he was literally ranting rubbish, feeding on my boobs, knacking me with his big gbola da omg banmasan yaya zan kwatantamiki girmanshi ba sai jiya nagane maisa yammata ke binshi kaman zasuyi hauka dat guy ko Jully wlh God finish work for his body, ga ilimi, ga kyau, ga kudi, ga kira, ga babbar joystick, gashi ya iya aiki da ita, gosh I am crazy for Zayn, Jully I f**king love him” murmushi Jully tamata tace “tashi kici abinci to kisha magani and sleep” tashi tayi ahankali sanan tashiga cin abincin kadan taci takarbi PC tasha bata wani dade ba bacci yay awon gaba da ita na wahala Jully tai tagumi tana kallonta, she just hope this whatever dasukai having will quench heIr thirst na wanan f**k boy din.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



       ✍🏻M SHAKUR



This novel is 1k enjoy ur free pages.


U can subscribe to group danake posting by sending 1k into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment by clicking on this link: wa.me/+2347012181461



1️⃣2️⃣

Free page 

Nigeria

Tuntuni Baba yadawo saida yagamajin maganan datama Khairy tsaf sanan ahankali ya sauke ijiyan zuciya daya nuna tsantsan damuwa sanan yawuce yashiga dakinshi, manyan kayan jikinshi yarage dama sabida Mama yadawo yasan fushi take, koyaya yafita bayan yasan tana fushi to baida kwanciyan hankali, ahankali yazauna kan wata lafiyayyen kujera dake dakin nashi na massage ya mikar da kafafunshi tareda daura hannu dayakan daya yana sauke ajiyan zuciya mai sauti sanan ahankali ya lumshe idanunshi jin kujeran tafara massaging jikinshi sama sama yanajin surutun Khairy datake ma Mama dake mata tsifa, yana zaune awajen yaji Mama tace “taje ta taje kan” sanan yaji karan bude kofa wanda yasan Khairy ce. 

Yadade zaune ahaka sanan yaji karan an bude kofan dakinshi hakan yasa ahankali yabude idanunshi ganin Mama ce tana sanye da doguwan rigan atampa mai kyau ta daura kallabi tai kyau sosai tana kallonshi cikeda so da kauna yasa cikin tausasshen look yasakin mata annurin fuskanshi sanan yamika mata hannunshi alamun ta iso gareshi, murmushi tayi ta maida kofan tarufe sanan takaraso ciki table din tsakiyan dakin tajawo gefen kujeran sanan tazauna kusadashi ahankali tace “ina kwana” hannunta yabi da kallo dayasha jan lallen salatef sanan yasaka hannunshi yakama hannunta nata yarike gam yanajin dumin hannun kafin ahankali yadaura hannun kan kirjinshi sanan yasake sauke ijiyan zuciya yana kallon fuskanta cikin tsantsan muryan so yace “ina sonki Maryam, karki kara fushi dani kinji” murmushi tamai sanan takai dayan hannunta tadaura kan saman nashi tana kallon fuskanshi tace “bazan taba iya fushi dakaiba, sabida irin karfin soyayyan danake maka Baban Manaf” murmushi yamata sanan yazare hannunshi yakama duka hannayenta biyun yakama yakai bakinshi yamusu kiss sanan yamaidosu kirjinshi yanabin fuskanta da kallo ganin damuwa aciki, ahankali yace “menene” dan shiru tayi tana kallonshi tace “inaso kajanye hukunci dakama Khairy kabarta takoma school gobe ta tafi, banson daidai dasau daya Khairy tasan inada wata mu’amala da asibiti kuma kaga gobe zamuje muga Dr” shiru yayi yana kallonta cikin yan sakanni idanunshi taga sun koma sunyija, murmushi tadanyi sanan ahankali tazare hannunta daga nashi sanan takai duka hannayen tana shafa fararen gemunshi cikin wani irin kulawa tace “baka sake cemin komi kan maganan kara Auren dana maka ba?” Hannunshi yasa ya kabar da hannayenta dake kan gemunshi sanan yajuyar da fuskanshi yakalli gefe alamun he’s not interested in maganan, kukan datakeji ta dage ta danne tana kallonshi kafin ahankali takai hannunta takama hannunshi tarike ahankali tace “Baban su Manaf, nidakai we’ve been married for morethan 40yrs today, Alhamdulillah I get to give u beautiful kids ga yan biyun mu nan Manaf da Mu’az, ga Maheer gakuma Khairy mu, kasan dalilin dayasa na roki wanan alfarman agareka I am doing this for yaranmu, barinma Maheer da Khairy wanda sune kanana, i want them to start learning rayuwa da wata daban amatsayin mahaif……” “ya isheni maganan nan Maryam!”Baba yay maganan da tsawa still batare daya juyo ya kalleta ba, yace “naji Khairy will go to school tomorrow, na janye punishment din, but this should be the last time dazakimin maganan kara aure” murmushi tasaki wacce babu komi cikinta sai kunci da daci, ahankali takai hannunta tajuyo da fuskanshi yana kallonta idanunshi sunyi jajir hancinshi tadanja tana murmushi tace “why are you being stubborn eh”? Dan runtse idanunshi yayi cikeda ciwo zuciyanshi namai zafi yanamai radadi sanan gently yabude idanunshi yadaurasu akanta yace “Maryam you are the stubborn one here, kinki accepting treatment, babu yanda banyi dakeba dagani harsu Manaf da Baffan su, akwai wanda baimiki magana ba but kinki, ba kin gwammace ki…..” hannunta tadaura kan bakinshi tana murmushi da duk idan tayi yasan sanyayamai zuciya ahankali tace “yau shekaruna 57 aduniya, na aureka tun inada sha shida, nayi rayuwan aure dakai na shekaru arba’in da daya, and look at me I still look 30 kaman banyi aureba” tai maganan tana dariya tanamai fari da idanu, sanan calmly tace “I am not greedy after enjoying wayan nan shekarun idan Allah yace lokaci yayi sai ince baiyiba? Baban Manaf kasan meke damuna sama da kowa, treatment dinan bata lokaci ne kawai, sanan karasa cinyeka ma yake, I want kullum idan Ummulkhairy tadawo tundaga compound tana kwalamin kiran nan nata tashigo nabata abinci tanaci tanamin surutu, I want to use the little time daya ragemin to be with all my children, inamusu girki, ina tareda su da karfi na ina musu murmushi, banson nazama burden kan yarana yazamto suna kallona da pity, Khairy na final year yanzu inaso tagama school in peace tasami good grade, you know how Umma take tun tana yarinya idan tadawo gidan nan bananan, ba treatment din da a asibiti zan karake da zamaba nadawo kaman agwai, I rather stay here kullum tadawo taganni, kullum yarana maza suka dawo suganni, I want to die here in this house gidan aurena, taredakai dakuma yarana, please kabarni” wasu gajerun hawaye taga sun gangaro daga gefen idanun Baba yana kallonta yanadan sakin huci mai zafi, dasauri takai hannunta ta sharemai sanan ahankali tadaura kanta akan kirjinshi hannayenshi yakai kan bayanta yana shafawa murya chan kasa yace “I hate movies tun ina yaro, amman for the first time in my life Maryam sabida ciwon ki I wish I was a super man kokuma inada wani supernatural powers dana ciremiki Wanan ciwon” dan dariya tayi tanakan kirjinshi tana danne kukan datakeji tace “wayace maka bakada supernatural powers din? Soyayyan ka da kulawanka is what keep me stronger, is what keep me going tun bayan anyi diagnosing dina da wanan ciwon har izuwa yau Baban Manaf, baka taba bacci baka bani magunguna na, kafin kafita aiki dasafe kabani, da rana ko kana office u call, ko katuro any of our boys suzo har gida subani na rana what more can I ask for? U are my Superman, my superhero, my wonderman, mijina rakena” tai maganan hawaye na gangaro mata da sauri ta share da hannunta tana murmushi.



Tana daukan hula tasaka tafito tadawo dakin Mama ganin Mama bata daki yasa tadauki wayan Mama dakekan gado tafito da sauri tai dakinta tana shiga maida kofan tayi tarufe sanan ta shiga bayi, zama tayi a kasan clean bayin nata sanan tashiga contact din Mama number da akai saving da Baffa tai dailing, ringing daya biyu ana uku aka dauka cikin muryan wanda ya manyanta sosai akace “Maryama” dasauri ashagwabe tace “Baffa nine, Khairy ce” cikeda wasa yace “diyar arziki Khairiya kece, yau kuma mekikayi”? Kaman zatai kuka tace “Baffa wai dan nadauki mota shine Baba yace bazan kara fitaba har tsawon sati daya kuma ba school, sanan Baffa ya kwacemin wayata sanan yahana kawayena zuwa, Baffa kasan kai kadai Baba kejin maganan shi, Baffa please ka kirashi kasa ya janye” anatse yace “kimin alkawari bazaki kara daukan mota dakanki ba idan lokaci yayi koninan saina koyamiki da kaina kidinga ja” wata kalan muguwan dariya tayi kaman tana magana da tsaranta tace “kai Baffa kaida kaima tukaka ake chab, saidai Ya Hafiz yakoyamin wlh ni bazakaje ka maidani gurguwa ba” dan dariya Baffan yayi yace “Matar Hafiz ta haihu munsami mace, yanzu kinzama Anty” wani kalan ihu data tsandala da sauri Baffa yace “jama’a zata hudamin dodon kunne” taushe bakinta tayi da sauri tana dan dariya tana kallon wayan ganin Baffa ya katse tace “su Ya Hafiz andawo Dady, finally nazama Anty, Baba please give me my phone back nakirashi Iyye zanje naga Baby” tai maganan tana tashi sanan tafice taje ahankali tabude kofan taleka dakin ganin Mama bata dawo ba ta shige ciki da sauri sanan ta maida wayan tafito takoma nata dakin.





Bayan sallan isha tana zaune gaban madubi tana kallon gashinta yanda yawani kwanta kaman tasa shamfo taji Baba ya kwalamata kira wanda tuntuni take jiran kiran, tashi tayi tadau hulanta tasaka sanan tawuce ahankali take saukowa kowa na falon, gaban baba tazo kaman ta Allah ahankali tace “Baba gani” wayanta yadauka yamika mata sanan yace “ki shirya gobe kije school in Allah yakaimu” kallon fuskan Baba tayi cikeda farin ciki sanan tasa hannunta ta karba tana murmushi sosai tama kasa magana tsabagen murna, hararanta Mama tayi tace “kagamin yarinya bazaki godiya ba ko saini na kwace” dasauri tace “Baba nagode thank u, world best Baba” sanan tajuya takalli Maheer gwalo tamai tareda nunamai wayan zaiyi magana Mama tamai alamu daya shareta Manaf da wayanshi yahau kara ganin Aisha akan screen din yasa Mu’az yace “uhum’uhm” amugun kunyace yatashi yadauki wayan su Baba sukai kaman basusan meke faruwa ba yawuce yafita.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫


     

       ✍🏻 M SHAKUR



1️⃣3️⃣


WARAKA TEMPLE gidan maganin kowacce irin cuta da izinin Allah 

Karin niima da dadi 

Karin dandanonki da duminki

Matsewarki ki dawo yar Sha shida

Gyaran nono 

Sa megida sambatu

Sa kyauta 

Maganin Sanyi 

Da sauran magungunan damuwar da ke addabar mata zaku samu a waraka temple ku tuntubemu a no waya ko Instagram. Don magana dasu directly click on this link


wa.me/+2347042419516






Yau dayake Monday sunada lectures 9:00 wuraren 8:00 tasauko ta sanya wata Dubai gown sky blue dayama skin nata bala’in, sai uban sheki fuskanta yake ka kalleta saika juyo kabata second look, yau flat shoe tasaka baki sanan tadauki black bag shima, tana tafiya tana duba jakanta taga ko tasaka komi dan lecturer su na safen nan shege ne ajinshi you must jot inba hakaba yakadaka waje yace “you are not ready for school” Tundaga stairs take kallon Mama dataga tana zaune dinning takife kanta a table which is not like normal Mama, dasauri takarasa wajen dinning din takai hannunta ta taba bayanta tace “Mama” dasauri Mama ta tashi zaune idanunta sunyi ja irin name mugun zazzabin nan kafinma tai magana Khairy tarigata tace “Mama bakida lafiya ne jikinki zafi” dan zaro idanu tayi takai hannunta tana taba jikinta tace “bawani zafi daga AC kika fito Niko dana gama da kitchen ba dole kiji jikina yay zafiba, zo zauna kiyi break kitafi school” kujeran kusada Mama tazauna ahankali tana kallon fuskanta dan bata yardaba, Mama ta tashi tareda daukan plate tace “kici masa sabida yarikeki” tai maganan tana zubamata sanan ta tura gabanta tace “Oya Oya eat” fara ci tayi tana kallon fuskan Mama data daure iya daurewa, ahankali ta hadiye masan bakinta tace “Mama nakawo miki paracetamol kisha kinga kar zazzabin ya kwantar dake” dan shiru Mama tayi tana kallonta ganin dukta damu yasa ahankali tace “to naji zansha amman dakaina zan dauka Nasha ke yanzu kici abinci kitafi school yi maza ina kallonki” murmushi tayi sosai har ranta tace “yauwa Mama, world best Mama, har hankalina yatashi, wlh Mama ko tari banso naji kinayi balle ciwo sai inji komi bayamin dadi” dan dariya Mama tayi tanaji kaman zatai kuka amman ta daure tace “Malama eat bance kitasani agaba da surutu ba, Ummulkhairy aku” dariya tayi bata kara cewa komibaharta cinye kafinma tai motsi Mama tamikamata ruwa a cup, kallon fuskan Mama tayi sanan tai wani kalan murmushin dadi tace “Mama ya akayi ki kasan ruwa zan dauka” bata kofin Mama tayi tace “sabida ni Maman kine, angayamiki just like that naci wanan sunan world best nabakin ki” wani kalan washe hakori Khairi tayi sanan ta shanye rawan ta tashi tazo kujeran Mama rungumeta tayi tabaya tace “Mama natafi, I love you kinji, Mama karki je ko’ina please, koma zaki fita ki jirani nadawo saina rakaki mutafi tare” murmushi Mama tayi tadaga hannunta tashafa kanta tace “naji, a dawo lpy, banda rashinji, banda kula maza Umma, banda rashin kunya” sakin Mama tayi batare data amsaba tafice daga falon da sauri ganin 8:30, Mama na zaune inda take tana kallonta ta window harta shiga mota mai gadi yabude gate driver yafice da ita.




Ajiyan zuciya tasauke ita kadai tasan metakeji ajikinta, jin tafiyan Baba datun bayan yay breakfast yatafi sama shiryawa dan yau ba aiki zashiba asibiti zaikaita yasa tadaga idanunta takalleshi, hada idanu sukayi dawani kalan sauri ya shiga saukowa daga stairs din yace “wife, ur……Han…..hancinki” yay maganan yana karasowa gabanta ganin jini na gangarowa daga hancinta, dasauri tace “hanci na” takai hannunta ta taba jin abu na gangarowa kafin tadawo da hannun gabanta ganin jini yasa tace “laaa banma saniba” cikeda karfin hali tamike tsaye wani irin mahaukacin jiri yadibeta tai baya dawani irin sauri Baba yatarota tafado jikinshi a sume, daidai lokacin Manaf da Mu’az na shigowa falon cikin shirin zuwa office, ganin Mahaifiyarsu yasa dasauri sukai wajen kafin ma suyi magana Bana yace “Manaf daukomin mayafinta afalo mutafi asibiti, Mu’az get the car” dasauri Mu’az haryana bigewa da centre table yafice waje shikuma Manaf yay sama, har gaban flat din Mu’az yakawo motan sanan yadawo ciki atare dukansu suka dauki Mama sukai mota da ita bata Baba yashiga da ita, Mu’az da Manaf suka shiga gaba sanan suka fita gida.


Wani Babban private hospital sukaje, suna shiga aka karbe Mama sanan akasasu tsayawa awaje, zama Baba yayi da kusan yamafi yaran nashi damuwa, ahankali su Manaf suka zazzauna kusada shi babu iyacema wani kala idanunsu sunyi jajir, suna zaune awajen na kusan 2hrs sanan saiga Dr wanda yake abokin Baba yafito, Baba dagashi harsu Manaf na ganinshi duk suka tashi, kallonsu Dr yayi sanan yace “Alhaji follow me” binshi Baba yayi yay tafiya kusan biyu sanan yajuyo yakalli su Manaf dasukai zuru zuru yace “let’s go” dasauri suka biyoshi abaya har zuwa office na Dr, zama Dr yayi sanan yanunama Baba sit ya zauna sukuma su Manaf duk suka taaitsaya kowa kallon Dr yake with hope koma yayane abasu goodnews, lumshe ido yayi ahankali sanan yabude yace “Alhaji ayanda kuke kallona dagaku har yaranka I wish zan iya gayamuku abinda nasan har cikin ranku shi kukeso kuji, I am sorry I don’t have that sai akasin haka, condition din matarka has become worse da ayanzu riketa a asibiti yama kamata muyi muna bata yan taimakon dazamu i……” kasa jiranshi Baba yayi yakarasa sabida yasan menene zai fadi, cikin wata kalan tsinkakkiyar murya dake cikeda sanyi jiki dakuma lack of hope yace “how long does my wife have?” Kallonshi Dr yayi dan baiji Baba nason yaji Wanan amsan tambayan ba amman ganin kalan kallon dayakemai na ya shirya ji yasa ahankali yace “less than a month” hawaye Manaf yaji yazomai dasauri yajuya yafita daga office din, bayanshi Mu’az yabi da sauri yana goge hawayen dayazubomai, shiru Baba yayi kafin ahankali cikin wata kalan karyayyiyar murya yace “kasan dai kai ba Allah bane ba ko likita dazaka gayamin matata nada less than a month to leave” shi kanshi Dr ya bala’in tausayama Baba cus idanunshi sunyi jajir, cikeda lallashi yace “Alhaji listen to me, niba Allah bane, Allah shine masanin gaibu, kawai ina maka discribing lokutan datake dashine base on science, cells dinta sun soma shutting down daya bayan daya, I am just preparing you ne for the worst, you have to be strong ma yaranka, sabida ayanzu they’re looking up to you, ka dake sanan ka koyamusu sudake, kanunama matarka so da kauna sama da da, karku dinga kuka agabanta koku dinga nunamata damuwa, hakan zai saukaka mata abubuwa da dama, ganinku cikin damuwa da rashin walwala shi zai karamata damuwa da zafin ciwo, dan haka Alhaji I am giving you Wanan chance din cry as much as u want now, after yanzu baka kara kuka ko nuna rashin kwazo sabida yaranka” kaman jira Baba yake ahankali hawaye suka shiga kwararowa daga idanunshi, tissue Dr yadauka yabashi karba yayi dasauri yakai kan idanunshi yana sharewa cikin wata kalan murya dake sosarai yace “I don’t want Maryam to leave me, naso mu tsufa tare sanan mu mutu tare, why are you doing this to me now Eh Maryama diyar albarka” saukan da kanshi las Dr yayi yana sauraron Baba yakai kusan minti 15 ahaka sanan ya share fuskanshi tass da tissue Dr yanunamai bathroom yashiga ya wanko fuskanshi yafito yama Dr sallama yafice zuwa dakin Mama ganin su Manaf tareda ita tana bacci ana mata Karin wani abu kaman yellow madara yasa yafito, zama yayi a kujeran gaban dakin sanan yaciro wayanshi number dayay saving da Amini yay dialing, ringing daya aka daga cikeda barkwanci irin na manya yace “badai kahanamin yarinya zuwa makaranta ba” dan murmushi kadan yayi sanan yace “jikin Maryam yatashi muna asibiti Baffa” anatse  daga dayan bangaren akace “Subhanallahi, turn d car Bala muje asibiti” kawai aka katse wayan.



Yana zaune  awajen ko cikakken 10min ba’a dauka ba, wani Babban mutum da akalla shida Baba zasuyi sa’onni ya shigo cikin asibitin yana gyara Babban riganshi, farine mutumin sol yanada kiba dan yamafi Baba, shida wani dan saurayi dabazai wuce sa’an su Manaf ba dayay kama dashi dukansu fuskokinsu yanuna damuwa sosai, yana karasowa dafa kafadan Baba yayi yace “be strong my friend, Allah yabama Maryama lafiya, Allah yatashi kafadunta, Allah yasa kaffarane” tashi Baba yayi yanadan murmushi sanan yakalli yaron dake gaidashi yace “su Baban Baby girl Hafiz, Allah ya raya” ahankali yace “Ameen Baffa” sanan suka shiga ciki, har lokacin bacci take, da idanu Baffa yama Baba alamu su fito, suna fitowa yace “bazamu fitada ita wajeba ko har yanzu tanakan bakanta”.




I will talk to her idan ta farka, ahankali Baba yace “Allah yasa ta yarda” kara komawa sukayi wajen Dr ko akwai wani solution amman babu, dudda haka Baffa saida yakira some of the best Doctors dayasani a Abuja but is still same thing hakanan suka hakura.


Wajajen 3:00 na rana tafarka, dakin tabi da kallo kafin ahankali tafara yunkurin tashi dasauri Manaf da Mu’az suka dagota, ahankali Mu’az yace “kinajin yunwa Mama mezakici” dakin asibitin tabi da kallo kafin ahankali tasauke ijiyan zuciya tadanyi murmushi ganin duk sun damu tace “ya akayi bakuje aiki ba yau, laaaa is that Hafiz” tai maganan tana kallon Hafiz dake zaune kan kujeran gaban gadon yana kallonta cikeda tausayi, cikeda murna tace “zonan zoka nunamin hoton jikata nagani” dan murmushi yayi yataso yazo, wayanshi yaciro yafito da picture cute baby girl dinshi yabata karba tayi tace “Masha Allah tubarkallah, Allah ya rayamana kaga yarinya kaman Babanta Yan biyu” tai maganan tana nunamusu hoton kafin idanunta ya sauka kan time din wayan ganin karfe uku har da minti goma yasa dasauri tamikamai wayan takalli Mu’az tace “kiramin Dr yasallameni inkoma gida, Khairi takusan dawowa daga school” tana maganan saiga Baba da Baffa da Dr sun shigo tare, Baffa na ganinta yace “ya jiki Maryam” murmushi tayi tace “Alhamdulillah Baffa, ya ji kalle inasu Hajiya Asiya” kafinma taji amsanshi tace “Dr zokai discharging dina natafi gida” ahankali Dr yakaraso wajen yace “Hajiya kibari mu dubaki na kwanaki tukunna saimu sallameki” kallon Baba tayi sanan takalli Dr rai Adan bace tace “sallameni yarana banaso su dawo Bana gida Dan Allah” kallon Baba tayi sanan ahankali tace “daman Wanan ne shirinka idan ka kawomi asibitin arikeni” dasauri Baffa yazo wajen anatse yace “Maryam kalleni nan” ahankali tajanye idanunta dagakan Baba dake kallonta kuri takalli Baffa, anatse Baffa yace “Maryam kiyakuri ki zauna likitocin nan su cigaba da baki gudunmawa, zamanki agida zai karasa ciwon yazama worst ne, dan Allah maryam inhar kinajin magana ta” lumshe idanunta tayi sanan tabudesu ahankali tace “Baffa tun ina yarinya kasanni ban taba cemaka no ba, kome kacemin inayi dan haka yau Baffa dukanku anan zan rokeku alfarma, dagayau dan girman Allah kome zai sameni karku sake dawodani asibiti, Baffa nasan kalan chutan danake dashi, nasan metake nufi, da inzauna anan allurai da maganinsu yakarasa cinyeni gwara in koma dakina, I want to die adakina tareda yarana dakowa, I hate hospital and zaman asibiti shizaifi kasheni dawuri sama da komi, please Baffa dan Allah, idan baka yarda ba naji zan zauna, amman rokonka nake please Baffa” kowa na dakin saida jikinshi yay sanyi har Baffa, ahankali Manaf yakalli Baffa yace “Baffa please grant Mama wish, let’s just take her back home ko Hafiz” gyadamai kai Hafiz yayi da idanunshi sukai jajir, hakama Mu’az, ganin Baffa da Baba sunyi shiru dan su sunfiso tazauna a asibiti tasami lafiya yasa ahankali Dr yace “Alhaji kubarta takoma gida, idan anything come up ku kirani ni zandinga zuwa nadauki Wanan nauyin” ahankali Baffa yakalli Baba dakokadan baisoba, kallon kayakuri takoma gidan, hakan yasa ahankali Baba yace “shikenan” murmushi Mama tayi sosai nan da nan aka zaremata drop din sanan Dr yarubuta mata magunguna suka saya sanan suka dawo gida gabIaki dayansu.




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



        ✍🏻M SHAKUR




1️⃣4️⃣


Free page

Wuraren 8:50Am sukakai school. Adamu na parking wajen parking tafito da saurinta bama ta tsaya mai sai anjima ba tashiga sauri cus 9 dot mutumin nan ke shiga aji gashi baya wasa da attendance, tana cikin tafiya zuwa class saiga wasu yammata su hudu sun taho tunda suka ganta sukahau ihun murnan ganinta Khairy nada wani irin farin jini naban mamaki wajen mata, tareta sukayi. “Khairy how far”? Murmushi tayi dake karamata bala’in kyau tace “lpy lau wlh, yanaga zaku waje daban ba class garemu ba yanzu” yatsine fuska sukayi, daya daga cikinsu tace “wlh dabaki wani wahalar da kanki ba wajen class din Mr Okeme ba ba’a taba ganewa ba, ke saurayinki Ahmad celebrity yazo nemanki fa” hararanta Khairy tayi tace “Malama niba saurayina bane kidena hadani dashi, na wuce class nidai” tai gaba abinta ranta abace, daya daga cikinsu ne ta daga murya tace “idan yakadoki meet us a garden chan mukayi” daga murya itama tayi tace “that’s not gonna happen Ladies” tana tafiya wasu another set na yammata na tareta bamata tsaya sauraransu ba tace “I will see u later ladies inada class now” tahau tafiya gudu gudu sauri sauri, duk inda tabi ana kwalamata kira Khairy Khairy waving mutane kawai take tawuce benen dazai kaita ajinsu tana kaiwa yana shiga tana tsaye yana kallonta yaja kofanshi yarufe, ahankali ta yatsine fuska murya chan ciki tace “this wicked man cannot make heaven” sanan tajuya tana kallon kasa daganan bene yanda student kowa na takanshi sanan ta fuzar da iska ita dai ko itace allazi boko bazata taba tsayuwa jikin window har agama 2hrs class ba, tashi tayi abinta tafara tafiya tawuce tana sauka daga staircase abinta tanadan turo baki ita kadai tana kunkunai.

Sabida yanda ranta yake abace taji bamatason tabi normal hanya friends nata suyita tareta da magana hakan yasa tabi ta parking space dan taje garden daga wajen, ahankali take tafiya ita kadai a parking space din tana cikin tafiya a parking space din taji an kwala mata kira. “Khairy” dan tsayawa tayi jim batare data juyoba jin muryan namiji ne ke kiranta, tunani tafara acikin kanta muryan waye wanan sai chan taja wani kalan annoying tsaki tacigaba da tafiya abinta gani kawai tayi ansha gabanta wasu maza guda biyu sunshamata gaba suna sanye da kananun kaya sun bubbude hannuwa irin suna tareta dinan, wani kalan daure fuska tayi babu ko alamun wasa akai tace “me haka” dan dariya sukayi daya daga cikinsu yace “listen to Ahmed mana Khairy yasan bazaki tsayaba saisa yace mutareki” yay maganan suna nuna mata bayanta, juyawa tayi cikeda masifa wani black skin guy ne da dududu bazai wuce mate nata ba in age maybe 20 ko 22yrs haka yake, yana sanye cikin rugget kayan yan iska dinan, crazy baggy jeans da wata babbar baggy riga yayi dying gemunshi zuwa blond color kana ganinshi kaga irin yan iskan yaran nan gashinan very popular aciki school nasu, wani kalan mugun kallo tamai da manya manyan idanunta tace “kai da boys dinka Ahmad should get out of my way” wani kalan murmushi yamata tareda daura hannunshi akan kirjinshi yana shafawa yace “auuch! I love it when you look at me like that Khairy with those ur big big lulu white eyes, Baby my heart only beat for you” spitting miyau tayi agefenta sanan tajuyo takalleshi tace “you disgust me Ahmad, nagayamaka time without numbers stop wasting ur time on me, you are not my type of guy, idan maza irinkane suka cika duniyan nan I rather die banyi aure ba dana aureka, I don’t like you an taba soyayya dole ne” dan takowa sahu daya yayi zuwa gabanta, tsayawa chak tayi tareda kama waist dinta kirjinta na bugawa fat fat, wani mayen kallo yabita dashi barima kirjinta dayaga yacikamai idanu tunba yauba tunda ya lurada yanda Khairy keda boobs yaji yakara haukacewa akanta, dan hucin zafi Ahmad yayi yana kallonta still sanan yanuna kanshi yana bude kafafunshi da tsabagen effizy sun koma kaman boleg yace “look at me kinsan how many babes anan School namu ke kiyamun laili because of me eh? Look at me Khairy, I have money, I was born in wealth, banda haka I am a hip hop rapper number 1 a arewa, yaro mai zamani, har rap nayi da sunanki natura miki a watsapp u don’t even open my chat balle kiji how much I love you, Khairy tell me mezan miki dazaki soni eh, kinga we are the only ones here, just tell me babu kowa don’t be shy Khairy, baki sona don’t u wish to be mine, don’t u wanna make matan makarantan nan jealous ace Kece tawa, I want you to be my Choima while I become your Davido, lemme make you famous, lemme make u a star gurl, what will I do to make you mine baby na? Don’t u want all of this” all maganganun dayake mata jitake kaman tai amai bala’in kyaman Ahmad take bawai he’s dirty bane, kawai dai yanayinshi yanda yake dressing yana shiga kaman wani su wizkid yayi coloring gemunshi da halinshi na waka ita kawai he’s not her spec, yana mata magana yana wani wawware fingers kaman yana rapping yana kama tsakiyan baggy wandonshi, ko kiranshi amatsayin boyfriend nata ma bataso ta tsani taji anyi, bakin ciki da haushin shi yamasa tama kasamai reply kawai tajuya ta gefenshi zata wuce dan sometimes idan abu is really annoying agareki rasama abinda zakace kake, kawai ji tayi yariko hannunta “don’t go baby wait” wani irin juyowa tayi batai wata wata ba kawai ta daukeshi da mari jikake tass! Wani irin ihu abokanenshi sukayi suna waige waige ko there’s anyone there dayaga Marin datama Ahmad dan zai zama abin kunya ance wata tamari hiphop rapper. “Ke celebrity kika mara” fizge hannunta tayi tana kallon yanda yadaura hannunshi kan kuncinshi yana wani irin kallonta da idanunshi dasukai jajir dan marin ya shigeshi, rawa jikinta yafara da sauri tajuya Ahmad daya bala’in zuciya yace “ku bita” jin haka yasa ta kwasa da bala’in gudu acikin parking space din dababu kowa tana kalle kalle, kaman ance takalli right side dinta, hango wani dogon mutum tayi yabata baya Awani lane na motoci yana tsaye jikin wata suv waya a kunenshi da alamu waya yake, wani irin kwana tayi tana gudu tai lane din dayake batai wata wataba tana kaiwa daidai inda yake batai wata wataba tawani zaga ta gabanshi ta shige kirjinshi at once tana boye fuskanta akirjinshi jikinta ko’ina narawa sosai sabida tsoro yanda maza har biyu komatace uku suka biyota, cikin Yar siririyan muryanta that is trembling sosai tace “please save me…..plss…….I’m sca…….” tana maganan tana nishi da sauri da sauri dayake jinshi harcikin fatan kirjinshi don fuskanta gabaki daya na wajen ne, daidai lokacin daga boys din Ahmad din har Ahmad din dukansu sunzo wajen sun tsaya agabansu suna maida ijiyan zuciya sabida gudun dasukayi, One by one mutumin ke binsu da kallo batare daya furta ko a word ba har lokacin wayan nakan kunneshi bai cireba, faduwa gaban Ahmad yayi ganin fuskan mutumin dake kallonsu, ahankali yajuya sadaf sadaf daso samune ko takalmin shi da kasan wajen karma suyi motsin nuna alamun yana moving sanan ya yafito abokananshi da hannu yace “let’s go guys” dasauri sukace “marinka fa tayi Boss” da saurinshi kaman ana hankadashi yawuce yace “shikenan nidai natafi ku ku tsaya” ganin yanda yake tafiya da saurin bala’i tun bayan yaga fuskan mutumin yasa suma sukasha jinin jikinsu suka juyada sauri suka wuce.


“Eh Gwaggo ina jinki sorry ba shareki nayiba, Abban nake jira nariga nakawo shi…” ahankali tashiga dagoda kanta kaman wata mara gaskiya cikeda kunya jin mutum na wayanshi ta tsokano fada tazo tafada jikin shi, kanta akasa ahankali sadaf sadaf tashiga fitowa tana matsawa baya kafin gently kanta nakasa batare data kalleshi ba tace “thank you” sanan ahankali tajuya tashiga tafiya har lokacin gabanta nafaduwa sosai. “You!” Taji kaman daga sama mutumin yakirata chak ta tsaya batare data juyoba, “turn around” taji muryanshi anatse yet with authority batasan mesaba amman kasa ketare abinda yace tayi tayi hakan yasa gently tajuyo sanan ahankali tadaga fuskanta takalleshi, wani dogon saurayi ne fari sol dashi kaman balarabe yana sanye da jumper na farar shadda bugaggiya kanshi babu hula gashinshi akwance baki sidik sai kyalli yake hannunshi rikeda iPhone 13 yazubamata idanu dababu alamun wasa daidai da digi acikinsu, hakanan jitayi takasa jure kallon mutumin dataga kaman ta sanshi amman ta manta a ina ta sanshi ta sauke kanta kasa, anatse yace “the next time I will see you making trouble I will arrest you!” dasauri tadago kanta ta kalleshi saida yafidi kalman arrest sanan police din ranan yafado mata arai, dauke kai yayi daga kallonta sanan  yabude kofar motan daya tsaya jikinta ya shiga ciki tareda rufe marfin motan da sauri dayadan firgitata sanan ahankali tajuya tacigaba da tafiya ahankali.




Samin kanshi yayi da binta da kallo ta madubin motan, yanda take tafiya ahankali har lokacin bata dawo daidai ba, sanan ahankali yadauke kanshi daga kallonta jin wayanshi na ringing again screen din yakalla ganin Grandma yasa yabude motan yafito yace “this woman will not allow me leave in peace”.


Garden din takarasa tun daga nesa kawayenta dasuka hangota suka kwalamata kira hakan yasa takarasa zuwa inda suke zama tayi sanan tadauki bottle na ruwan dake gaban Farida tabude takai bakinta ta kwalkwale duk kallo suka bita dashi, saida ta shanye goran ruwan tass sanan ta ijiye tana sauke ijiyan zuciya, Farida tace “daga ina kike haka duk kinyi zufa kaman kin fito daga yaki” dan yatsine fuska tayi kaman bazatai magana ba ganin yanda suke kallonta yasa tace “Ahmad na mara shine yabiyoni and someone…..” tadanyi shiru kafin ahankali tace “wani mutumi yataimakeni” atare dukansu all the 5 friends sukace “wani mutumi” shiru tayi sai chan tace “oho nima ban sanshi ba” dukansu dariya sukahau yi dasauri takallesu tace “me” hada baki sukayi sukace bakomi, sharesu tayi kawai cus she doesn’t even feel okay batasan mesa ba, duk suna zaune wata kawarsu tashigo eatery dagudunta tana haki tace “kufito kugani yan sanda sun shigo school dinan anzo ana kwashe su Ahmad da Gang dinsu” dasauri Farida tace “ke haba let’s go video it musashi a internet” dukansu tashi sukayi itama ta tashi tabisu suka fice daga cikin garden din, van suka gani na police gaban wani eatry dake kusada garden din dasuke ciki, dasauri suka karasa gaban eatry din student sun cika wajen suna kallon Van din police, suna tsaye wajen dayay cha da mutane sukaga an fito da Ahmad da akasamai handcuff a hannu an sashi a van din sai abokanen shi na dazsu dasuka biyota guda biyu saikuma wasu guda biyu daban yan sandan sun fito dasu ana sakasu a van din saiga police man dinan shima yafito daga eatry har lokacin yana sanye da kayan dazu farin shadda waya a kunenshi still, hada idanu sukayi batasan mesaba jitayi gabanta yafadi dasauri ta sauke kanta kasa tareda juyawa ahankali tamabar wajen bata kara juyowa ba kawai tai hanyar class nasu, daidai lokacin ana shirin fara wani lecture kujera tasamu atsakiyan ajin ta zauna sanan tabude jakanta taciro note nata da pen aka fara lecture ko kadan takasa concentrating batasan mesa ba she just keep seeing police man face din da what happen today, gabaki daya all through da day har yamma ita kanta tasan yau ba school tazo ba takasa natsuwa tunanin shi da komi yacika mata kai, wuraren 5 na Yamma Adamu direba yazo daukan ta shiga motan tayi ahankali tace “Adamu please kafara kaini Coldstone nasayi ice cream nasha saimu wuce gida” cikeda girmamawa yace “to Miss Khairy” daura kanta tayi akan kujeran tajuyar da kanta tana kallon hanya tareda fuzar da ijiyan zuciya, she just hope tanashan ice cream dinan sanyin shi zaisa brain nata yay sanyi tadena all tunane tunanin datakeyi tun safe.



Agaban wani Babban joint na coldstone Adamu yay parking hakan yasa tabude motan tafito ta shiga ciki, daidai wani Babban Jeep na shigowa wajen parking yayi kusa da Benz da Adamu ke ciki, bude gaban motan yayi yafito ahankali wanan karan yana sanye da kayan yan sanda Rolex din dake daure a hannunshi yakalla shidda saura, sanan yazaga zuwa boot din jeep din yabude keken guragu yaciro ya ijiye ya maida boot din yarufe sanan yadawo bangaren baya yabude motan wata kyakkyawan tsohuwa ce fara sol kaman balarabiya zaune abayan tasaka Riga da zani irin na tsofaffi anmai dinkin Bubu kafafunta da hannayenta sunsha lalli, hannunshi yamikamata batare dayace mata uppan ba hararanshi tayi tana kama hannun nashi tamike tsaye da kyar tana masifa tace “idan kaga dama kai gaba dani dagayau har jibi Ice cream dai saika kaini nasaiwa jikoki na ja’irin yaro kawai” ko kala baice mata ba da taimakonshi ya daurata akan keken sanan yamaida kofan bayan yarufe da karfi tace “kama balla motan baban karfi, ubanka zai sayamin wata Alhamdulilah Allah yamai arziki rufin asiri danasha takaici” cikeda masifa yace “wlh Goggo in baki shiru ba anan zan barki na shiga ciki nasayo” wani kalan murmushi tayi tamaka bakinta tace “yo ai nadauka gaba kake dani to muje nadena” dan murmushi kadan kawai yayi sanan yashiga turata zuwa gaban entrace din dakenan divided into 3, staircase ne gefe da gefe sai tsakiya a bit sloppy floor dazaka haura ka shiga cikin shagon, daidai lokacin security na budewa Khairy kofa tana fitowa rikeda paper bag na ice cream din dakuma handbag dinta rataye a shoulder dinta, saiga wasu yara su biyu maza dabazasu wuce 8yrs ba suna guje guje kowanne rikeda ice cream dinshi dayan kawai ya mamayi brother shi ya fizge ice cream din hakan yasa brother yay ihu yabi dan uwanshi da gudu Khairy dabude mata kofa kenan tasa kafa tafito zata fara sauka daga staircase din kawai yaran suka fito suka mugun bangajeta dayasa ita kanta tasaki wani irin ihu kafanta ya gicce abunku da tiles kawai ta kifo zata fadi da mugun sauri Gwaggo tace “Subhanallahi” dawani irin sauri yasaki wheelchair Gwaggo daidai kanta zai daki dakaIUlin stairs din…




💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫



          ✍🏻 M SHAKUR


Dan magana da M shakur

wa.me/+2347012181461



1️⃣5️⃣



Yasa hannunshi daya awajen kanta ya daki tafin hannunshi bayan hannunshi yadaki stairs din sanan yakai dayan hannunshi yakama waist dinta yajuyo da ita hakan yasa ta mirgino side tafado jikinshi.


Daga yaran, security, iyayensu dasuka biyosu da sauri, Gwoggo dakekan wheelchair duk sandarewa sukai danba karamin faduwa zatayi ba inda Allah bai kiyaye ba, yanda yakeji yanda take nishi a hannunshi yasa ahankali yazare hannunshi daga waist dinta gently yakai hannun kan fuskanta yadago fuskanta yana kallon face dinta yanda ta kankame idanunta gam gam cikeda tsoro pink lips dinta nawani irin shaking dayasa dimples dinta na lotsawa tana nishi sama sama dayake jinshi akan hannunshi, murya chan kasan makoshi while looking into her face yace “are you okay”? Muryan dataji yadaki dodon kunnenta yasa kadan kadan tashiga bude idanunta danta gasgata abinda taji kafin tabude su tass tadaura white fararen idanun nan nata manya manya dasukenan kaman an wanke da madara tadaura su akan fuskanshi, jitayi numfashinta ya makale somewhere in her throat ganin fuskanta dab da nashi yana kallonta as if he’s trying to check something, yatsanshi yakai saitin nose nata jin bata numfashi  kawai takafeshi da manyan white eyes nata yasa dasauri yakalli security man din yanunamai jakanta dake kasa chan yace “give me her bag” dasauri yakawo jakanta yamikamai juye jakan yayi kasa inhaler ta yafado dasauri ya dauka yacire marfin yakai bakinta ahankali yace “breathe in Ummulkhair!” Wani irin bugawa zuciyanta yayi jin yanda yakira sunanta kaman sunanta dayakira ne yay reviving nata batasan lokacin datawani saki numfashinta data rikeshi amakogoronta ba yafito mai kara sanan taja inhaler, zagayesu mutane sukayi barinma parent din yaran da jikinsu yay sanyi ganin Yarinyar da yaranta suka ture is even asmatic, ganin yanda mutane suka cika kansu duk ana kallonta yasa ahankali takai hannunta batare data kalle fuskanshi ba tana kokarin karban inhaler daya rikemata abaki, ganin haka yasa gently yasakin mata ahankali yaran dasuke tsaye sukace “Anty sorry” dan murmushi tayi tana cire inhaler daga bakinta duk dasauri tana kokarin tashi tsaye, tsugunnawa Maman yaran tayi tace “rest a bit please” tai maganan tana maida mata kayan jakanta back aciki tareda daukan mata jakan ice cream dinta da sauri ta mike tsaye tana karban abubuwan ta daga hannun matan tace “I am okay thank u” Gwaggo dake kallonta tace “sannu kinji inane gidanku mukaiki nida jikana” dasauri tace “direbana na nan nagode Ma” sanan tawuce da sauri hartana tuntube tai wajen motansu da Adamu ya kwantar da kujera yanata hira awaya abinshi batare dayamasan meke faruwaba, saida yaga tabude motan ta shiga sanan yakoma wajen Gwaggo yatura keken sukai ciki tace “ohh yara da rashin wayau Hydar, inda badadan kaiba da sunja Yar yarinyar nan tafasa goshi wlh, itama yarinyar uwa batacin abinci yoo nakema wanan maganan haka rainon indomie ce daga ganinta, ace daga yan yara sun bangaje budurwan yarinya haka kawai sai faduwa uwa lagwani, ace yara suci tuwo suki duk irinku ne ai gashinan kaga yara  sun taso basu da karfi ko kadan, kai Allah dai ya wadaran naka subaci, Allah dai yasa kai aure ka haihu, wlh tun yaranka na wata biyu zan fara basu lafiyayyen tuwo da miyan kuka dataji daddawa” hararanta yayi baima cemata komiba ya sassayi ice cream din sanan suka fito tace “minene Wanan abin danaga kanata matsamata abaki” kin kulata yayi yasa ta amota ya maidata gida sanan yafito yatafi aiki.




Har suka shigo anguwan su badaidai takeba yau sau uku kenan tana ganin mutumin nan, saida suka shigo gida tukunna sanan taji wani kalan dadi, parking sukayi sanan tafito dasauri tana kwaso kayayyakin ta tana kwalama Mama kira. “Mamaaaa! Mama nadawo” daga Mama, Baba, Baffa da yayyinta da Hafiz duk suna zaune a falo dan basu dade da dawowa daga asibiti ba babu wanda yama iya wani kwakkwaran motsi, ita tsabagen murna batama lura da Karin mota kan tagidansu ba tai hanyar flat dinsu tana shouting Mama. “Mama nayomiki tsaraba yau nasayo miki ice cream kuma best flavor naki mint ban miki adding any thing ba ayanda kike sonshi plane” tai maganan tana bude kofan falo tana shiga tana kiran Mama. “Maaaam……” kasa karasa kiran Mama tayi ganin mutane a falon ga Mama zaune kusada Baba tana kallonta tana murmushi, hararanta Hafiz yayi yayi yace “inda ace ke kadai keda Mama aduniyan nan Khairy da munsha takaici” cikeda wasa Baffa yace “kagamin d’a kai kanama namiji ka more taka Maman balle ita mace kuma auta, ina tsaraban dakika kawoma Maman bazaki zo kibata ba kin wani tsaya awajen” akunyace takaraso cikin dakin wani irin rungume Mama tayi tana murmushi akunyace ganin duk ana kallonta yasa tadaurama Mama paper bag na ice cream din akan jikinta akunyace ta sauko dagakan jikinta tace “Baffa ina wuni” murmushi yayi yace “diyar Mamanta ya makaranta” ahankali tace “fine” sanan takalli Hafiz tace “Ya Hafiz ina yini ya baby kuma, dan Allah ya Hafiz kasa mata sunana” dasauri yazaro idanu yace “waaaa niii rufamin asiri Khairy sokike y’ata tazama fitinanna irinki” dariya aka hauyi adakin ahankali Khairy tace “Baffa kaga Ya Hafiz ko” kafin Baffa yay magana Baba yace “karya yayi to Khairiya” turo baki tayi kaman zatai kuka Baffa yace “sharesu Yar albarka, sun lashe basusan baiwan dake tattare da sunan ki bane saisa suke magana ahaka” wani kalan murmushi tayi tace “yauwa Baffa” sanan tajuyo takalli Mama tace “Mama kin sha maganin kan yadena miki ciwo muji” takai hannunta tana taba goshin Mama with so much care, gyadamata kai Mama tayi tace “yadena, cikani maza tashi kai ice cream din kisa a fridge kije kiyi wanka kiyi salla idan bakiyi a school ba saiki sauko kici abinshi” gyadama Mama kai tayi sanan ta tashi tana kallon yayyinta dataga sunyi wani iri harzata wuce tace “Ya Manaf kungaji ne haka naga kunyi wani iri, Ya Maheer idanunka sunyi ja kaman kayi kuka” hararanta yayi hakan yasa ta murgudamai baki tawuce abinta sama itama, dayake yana takanshi dayaji ciwon Mama yatashi yau baima biyemata ba.





1️⃣6️⃣


Free page 

😉 enjoy


Kofan dakinta tabude ahankali ta shiga tanabin dakin da kallo yanda ko’ina tsaf tsaf an gyaramata sai kamshi dakin yake, shiga ciki tayi sanan tamaida kofan tarufe kafin awani irin gajiye cikeda sanyin jiki tasaki handbag dinta akasan dakin tafada kan gadon batare data cire takalmin kafanta ba tawani kalan kankame jikinta tanajin wani irin sanyi na shiga jikinta, she don’t even know why amman hakanan fuskan police man dinan take gani a idanunta muryan shi namata yawo a kunne  da kanta gabaki daya yana kiran sunanta Ummulkhair breathe in, runtse idanunta tayi gam gam tana feeling yanda bones nata ke cringing to each other tana ganin fuskanshi namata yawo a idanu kafin idanunta suna hasko lips dinshi wani kalan ihu tayi. “Ahhhh stop!”  dasauri ta tashi zaune tana wurwurga kafafunta cikeda damuwa tace “Stopppp noooo what’s wrong with me”? Wani irin zabura tayi ta tashi tsaye kawai tawuce dasauri tafada bathroom, wanka tayo sanan tafito daure da towel tana tunanin yaushe Mama zatasa amata Kitso dan gashin ya isheta daga tsifemata jiya, wani simple dogon Riga tasaka sanan tasaka hijabi tai salla tana idarwa tafito falo tawuce ganin duk basu tasan sun tafi masallaci sallan magrib, dinning tawuce zama tayi tana bubbude kula rice tazuba kadan sanan tasa nama tafaraci saida tacinye sanan takai plate din kitchen kafin tafito ahankali tai stairs, knocking dakin Mama tayi sanan tabude kofan ganin Mama akan gado ta lullube da bargo yasa tashigo da sauri tace “Mama menene” wani kalan kallo Mama tamata tace “bacci zanyi nagaji” hawa gadon tayi tana kallon fuskan Mama tace “Mama kibari ayi isha’i tukunna nima bacci nakeji” gyadamata kai Mama tayi tana kallon gashinta tace “weekend zakiyi kitso tunda ke kin dawo yarinya daga tsife miki kai kanki yadawo kaman na mahaukaciya” gyadama Mama kai tayi tana hamma, ganin haka yasa Mama tace “Oya tashi kije kiyi sallan to gashinan ana kira saiki kwanta tunda kin gaji, kinmasha ice cream din” girgizakai tayi agajiye tace “gobe zan sha Mama nagaji, gud night world best” night my baby girl, Mama tai maganan tana binta da kallo wucewa tayi tafice daga dakin tana salla ta kallabi tahau gado sai bacci.



Da asuba tana tashi salla tafarayi sanan takoma bacci dan yau batada lectures sai 10 and she wants to sleep sosai cus kanta yay clearing tadena all this banzayen tunanin nan datakeyi. 

Karan wayanta yatadata by 9, da kyar ta iya bude idanunta ta kalli wayan rabon data danna wayanta hartama manta one thing dabai dameta aduniya kenan ba waya, she’s not just a phone person, itadai barta da physical surutu, yawo rawa haaba anan ake samin Khairy, hannunta tamika da kyar tadauko wayan ganin Besty yasa taji duk wani kalan bacci datakeji yafice daga idanunta dasauri tai picking call din tace “Iyye su Besty Amarya ai nadauka kin manta dani yar rainin hankali saisa na shareki banma nemekiba” kuka Besty tasaki awaya dayasa dasauri ta tashi zaune adan tsorace tace “ke menene Besty, what happen? Kinasa inajin tsoro why are u crying?” Cikin wani kalan muryan ban tausayi Besty tace “Khairy wlh nafasa auren mutumin nan kasheni zaiyi tun ranan da aka kawoni abu daya ake har yau nagaji” dan ware idanu Khairy tayi tanajin maganan wani banbaram itadai barta da rashin ji but duk wani harka na maganan banza da Iskanci bata aciki, adan kunyace cikedajin nauyin magannan tace “to ba ance ana sabawa ba” tai dan shiru saikuma ta turo baki tace “idan yaki kihadashi da Maman ku” wani gajeren tsaki Besty taja cikeda masifa kaman tabugama Khairy dundu tace “I don’t even know why I called u you are crazy Khairy, da zancen party ake da yanzu kingama tsara komi, lemme call Amal” tana maganan ta katse wayan, hararan wayan Khairy tayi ta ijiye saikuma chan kaman ta tuna wani abu wayan ta dauka dailing number Besty tayi back ringing daya tadaga, ahankali tace “sorry Besty kinji I seriously don’t know what to tell u or how to advice u” cikin muryan damuwa Besty tace “wai Khairy when will you learn all this stuff eh, u are just hella wired Umma, u are just leaving life kaman bamace ba gashi duk munata aure Khairy keko saurayi bakida shi sai wanan Wizzy dake binki” hararanta Khairy tayi tace “nacemiki kidena hadani da wanan yaron” dan dariya Besty tayi kaman ba itane mai kuka yanzun nan ba tace “naji nadena, yanzu dai kinyi wani saurayin”? Dan shiru tayi kaman mai tunani harta bude baki zatai magana saikuma tai shiru hakan yasa Besty tace “ohhh wowww, Khairy this is something new, tell me who is he? Dan tunda nake dake duk aka miki tambayan saurayi direct kike cema mutum baki dashi wanan dakika kasa magana tell me wayeshi” dan murmushi tayi tayi dan juyi akan gado tana dan lumshe ido saikuma ahankali tace “wlh Besty banda kowa kawaidai wani Police man ne naketa haduwa dashi this days amman ko magana bamayi kawai dai he always saves me from trouble ne I don’t know if that means anything amma dai ba soyayya muke ba ko magana ma bamayi” ahankali akuma natse Besty tace “ohh my Goddd! Khairy kinji yanda harwani natsuwa kikayi kina bani labarin police man dinnan kuwa, My world Khairy you love me! Wlh….” Dan yatsine fuska Khairy tayi dasauri tace “stop it! Mutumin dabanma sanshi ba, yaushe zaki dawo school nidai” dariya Besty tayi sosai tace “tunda u are avoiding maganan ai ba matsala, this weekend zai dawo dani but every weekend zai dinga zuwa” gyadamata kai Khairy tayi tace “sai kinzo bye” tai maganan tana katse wayan da sauri dan tasan Besty bazata taba hakura da topic dinan ba, ijiye wayan tayi ahankali sanan ta mirgina zuwa dayan gefen gadon tana tunani.



Ajiyan zuciya tasauke sanan ta tashi tasauka daga kan gadon zatai bathroom wayanta yashiga kuka cikeda masifa tadawo tace “mekuma kike sake kirana eh” wayan tadauka ganin Glory yasa tai picking wayan takai kunne kafinma tai magana Glory tace “hello fine girl, melanin goddest, pop skin with those sexy milky eyes” dan dariya tayi, Glory is her friend masters ita take a school nasu ta girmeta far far amman tana bala’in son kawance da Khairy, dan murmushi Khairy tayi tace “Hey! Where have u been i haven’t seen u in school this days” dan dariya tayi tace “I travel naje PH chan gida, Khairy u don’t know I am angry with u ba” dasauri Khairy tace “what happen? Why” kaman zatai kuka tace “today is my birthday Khairy” Adan kunyace Khairy tace “ohhh Glory, sorryy happy birthday darling” dasauri Glory tace “come to my party and wish me there, zamuyi a jabi lake mall a cikin jirgin ruwa, dress code is red 4pm sharp” wani kalan juya idanu Khairy tayi tace “ohh okay then bye see u later” ta katse wayan sanan tawuce bayi da gudu wanka tayi agurguje sanan tafito cikin wata doguwan rigan atampa ta shirya tafito tana tunanin yanda zatai planning zuwa party zata dawo gida by 2 wuraren 5 saita tafi tadawo 6.


Tea kawai tasha sanan tawuce school dan tayCi latti sosai.




1️⃣7️⃣



Free page

Ahankali yake tuki ganin ya shigo cikin estate dinsu, saida yakarasa gaban wani dankareren gate sanan ya danna horn, budemai gate da akayi yasa yaja motan zuwa cikin gidan dakeda bala’in kyau kuma babban gaske ga flowers dasuka karama gidan kyau sosai, parking yayi abangaren parking sanan yakashe motan yana kallon cikin gidan dababu kowa sai gardener dinsu daketa yayyanke flowers yana gyara su, yakai kusan 1min cikakke zaune a motan yay shiru sanan ahankali yabude kofar motan yafito yamaida kofan  yarufe sanan yafara tafiya dai dai yawuce zuwa babban flat dakenan shine first flat a gidan, bude kofa yayi ahankali tareda sallama chan ciki sanan yashiga babban falon da babu kowa ciki, falon ya bala’in hadu yaji furnitures, saikuma dan kara dayakeji a kitchen da alamu mai aikice ke wanke wanke, juyawa yayi zai fice kaman daga sama yaji ankirashi. “Aliyu” dan juyoda kanshi yayi ya waigo, wata matace doguwa mai jiki fara kal da ita taci gayu da sarkan gwal a wuyanta wacce bazata wuce 40 ba tana sanye da lace ja da baki ke saukowa daga benen, kallo daya yamata yadauke kai yace “barka da rana Mami” dan murmushi matan tayi sanan takalli agogo bangon falon ganin is just 11 yasa tace “Lafiya kadawo gida ware haka Aliyu”? Batare daya kalletaba ahankali yace “lpy lau Mami” gyadamai kai tayi tana kallonshi still tace “tom shikenan, mezakaci a aiko maka dashi”? Batare daya kalleta ba har lokacin yajuya yace “zanci abinci wajen Gwaggo” yana maganan yajuya yafice tareda rufo kofan binshi da kallo tayi ta jikin window falon har saida yay side din Kaka yabace mata daga gani sanan tasami kujera ta zauna tanadan karkada kafa tunda take bata taba ganin wanda uniform na police kemai kyau kaman Aliyu ba, haryau tarasa maisa Aliyu yawani zama police ba yaron dayay lafiyayyen karatu yakuma gama da good result, kwanciya ahankali tayi tana kwalama Yar aikinta kira dan tazo ta danne mata kafa.



Bangaren Gwaggo shima yanada girma sosai, da sallaman nan nashi chan kasan makoshi yadaga labule ya shiga dakin ko kadan Gwaggo dake zaune tana kada lagwani bataji alamun shigowan mutum ba kawai karan kwas kwas na takalmin dake kafanshi taji akan tile din dakinta afirgice takalleshi tana “Innailaihi wa innailaihi raji’un, waikai Aliyu wani irin murdadden yaro ne eh, bama wanan ba dan ubanka koma ka cire shegen takalmin nan naka dazaka shigomin dashi falo ina salla a ko’ina afalona dan tsarki ne dashi wlh” ko kallonta baiyiba saima hawa kan dogon kujeran ta dayayi yay kwanciya abinshi yanadan lumshe idanu, ijiye komi Gwaggo tayi tamike tana gyara zani tazo kanshi zatahau mai bala’in idanunshi daya lumshe tabi da kallo ganin sundanyi ja yasa tace “kai yaron nan zazzabi kake yine”? Dan bude idanunshi kadan yayi yakalleta dauke kanshi yayi yaki kulata, dasauri ta kalli agogo ganin ko shabiyu batayiba yaron da dazun nan dasafe yafita aiki yasa tace “wlh bakada lafiya Hydar zo meke damunka”? takai hannunta da duk audugan lagwani yake kai zata tabamai fuska dasauri yatashi zaune yace “karki tabani da hannun dattin nan Gwaggo” dan sassauta murya tayi kaman ba ita kemai ihu ba cikeda damuwa tace “meke damunka eh Hydar? Duk wanda yasanka yana ganin Wanan idanun naka yasan bakada lafiya, meke maka ciwo” tashi daga kan kujeran yayi yace “tunda bazaki barni nai bacci ba bari na barmiki dakinki” yay maganan yay hanyar fita tana kwalamai kira kaman badashi takeba, cikeda damuwa tace “ai idan bakaji nawa ba zakaji na ubanka, yaro sai bakin zurfin ciki da shegen share mutane sabida yaga nadamu dashi” duk yanajin ta tana surutunta bai amsata ba flat dinshi yawuce bude kofa yayi yashiga cikin dakin da babu abinda yakeyi sai kamshi ko’ina a gyare kaman babu wanda ke zama adakin, bedroom nashi yawuce yana shiga adaddafe yacire rigan yan sandan ya Yar anan kasan dakin sanan yazauna takalmin kafanshi yacire yazaro wayanshi yadaura saman side drawer sanan ahankali ya kwanta yanadan yatsine fuska bala’in ciwon kai yakeyi daya rasa na menene amman sai uban dauriya, har bacci yasoma daukanshi yaji wayanshi na ringing da kyar yadaga hannunshi yakai wajen wayan dauka yayi batare dayama kalli screen dinba yakai wayan kunne ahankali yace “Hello” daga tachan bangaren muryan wani magidanci ne yace “Aliyu meke damunka?” Dan yatsine fuska yayi yanaji kaman ya rufe Gwaggo da duka akan me zata fadiwa Abba dan gyara muryanshi yayi yace “Abba I am fine” cikin rashin gamsuwa Abba yace “Aliyuuu” dagashi sai Abba sukasan meaning din anytime yakirashi da Aliyuuu hakan yasa gently ya fuzar da dan iska ahankali yace “Abba kaina hurts so bad” anatse Abba yace “is that all”? Ahankali yace “yes Abba” “okay I am coming yanzun nan nadubaka” dasauri yace “no Abba I am fine kazauna please zansha magani” dan jim Abba yayi yace “Aliyu haryau banga wanda yakaika tsanan magani ba” sanin tsaf Abba zaibar hospital yazo yasa yace “Allah Abba zansha I promise” cikeda gamsuwa dan yasan Aliyu baya promise yaki cikawa yace “okay kasha I will call Ogan ka zance mai yabaka the rest of today da gobe kahuta, this work is draining you Aliyu banason shi, anyway that will be another day talk, kasha maganin ka kwanta” ahankali yace “to Abba” Allah kara sauki kaji gyadama Abba kai yayi tareda katse wayan, hannunshi yasa yajawo drawer gefen gadon shi sanan yadauki paracetamol ya ballo guda biyu yana kallon maganin a hannunshi kaman yay amai, yadade yana kallon maganin sanan yasa hannu yadauki goran ruwan dake kan side drawer yabude kurba yayi sanan yajefa maganin da kyar ta hadiye sanan yasa goran abaki saida yasha kusan duka ruwan sanan yaji maganin yatafi ahankali ya ijiye goran kafin yakoma ya kwanta ya lumshe idanunshi bai wani dade ahakaba bacci ya kwasChe shi.






1️⃣8️⃣



Free page 

Wuraren 3 na rana yafarka, ahankali yake bude idanunshi yanabin dakin da kallo jin anrike hannunshi yasa yajuyo da kanshi ahankali wata yar budurwa ce da zatakai 22yrs zaune gefen gadon dake bala’in kama dashi kana ganinta kasan kanwanshi ce takama hannunshi gam tarike tanadan gyangyadi, tana sanye da doguwan rigan atampa, Meena kenan he’s sure Gwaggo ce tagayamata baida lafiya saisa tataho daga dawowanta daga school, dan murmushi yayi sanan ya fizge hannunshi da karfi afirgice tabude idanunta takalleshi tana kara ware idanu tace “Ya Hydar katashi sannu yajiki” hararanta yayi yace “meya kawoki dakina” cikeda damuwa tace “yanzun nan muka dawo daga school muka tarar Gwaggo na kuka wai batada lafiya shine nazo naga kana bacci, cha tayima na sata a keke nakawota wurinka nasan damunka kawai zatayi saisa naki” dan jim yayi yace “jeki cemata tadena kuka I am fine” murmushi tayi sosai tana kallonshi tana kokarin tashi  dagakan gadon tace “Ya Hydar kanason Gwaggo amman kullum fada kukeyi baka nuna mata kana sonta maisa” hanyar bathroom dinshi yawuce yace “kafin nafito kibarmin daki inba hakaba jikinki zai gayamiki” tashi tayi ranta namata dadi ganinshi lafiyanshi kalau tace “Ya Hydar zaka kaimu Jabi lake mall din? Kagama sai Gwaggo takara yarda lafiyanka kalau ko” “go and get ready” yafadi murya chan kasa duk ya gaji yakosa tabar dakin dansai sashi surutu take, shigewa bathroom din yayi abinshi yamaida kofan yarufe, tashi tayi cikedajin dadi tai hanyar fita, sai yanzu tama lurada riganshi akasa dakin tsugunnawa tayi tadauka sanan tamakalamai a hanger tabude wardrobe dinshi tasaka tawuce tafice danta gayamusu su shirya.




Yadade abayin sanan yafito wani simple jallabiya yasaka yay salla sanan yatashi ahankali har yanzu kanshi namai ciwo sosai daurewa kawai yake, shiryawa yayi cikin wani milk yadi mai bala’in taushi danshi baya iyasaka kaya masu karfi, feffesa turare yayi sanan yadauki wayanshi yana dubawa ganin baida miss calls yasa yafito yana tafiya one one, tundaga gaban kofan dakin Gwaggo Meena ke kallonshi ganin yay wani kalan kyau tana murmushi ohh God duk duniyan nan batada wanda takeso kaman Yayanta Hydar, hararanta yayi alamun kallon fa wuce kigayamusu su shirya hakan yasa tawuce tashiga dakin Gwaggo tana kallon Gwaggo dataci gayu itama tana zaune kan tabarman data shimfida akan lafiyayyen carpet din dake falon, girgizakai kawai yayi baitaba ganin rigimammiyan tsohuwa irin Gwaggo ba, gatada carpet amman tsabagen kauyanci saita shimfida tabarma akai, idanko yawone ko jikokin nata wani zubin da gangan sukekin gayamata zasu fita dan tsohuwarnan Allah ya zubamata son zuwa yawo kaman taci kafan kare. 

Wasu yammata guda biyu ne zaune agefenta suma kyawawa dasu Amal dakuma Khadija duk sunci gayu kansu daya, zama yayi abinshi Gwaggo tabishi dakallo bata kulashi ba shima bai kalleta ba yakalli su Amal dake kallonshi suna gaidashi yace “kawomin abinci” tashi Amal tayi dasauri zata fita yace “ina zaki”? Ahankali tace “falon Mami zani nadebo maka” girgiza mata kai yayi yakalli fuskan Gwaggo yace “bani na Gwaggo” daure fuska Gwaggo tayi takalli Amal tace “jeki uwardaka na abincinshi na cikin kula sabida ku na boye kafin ku cinye mai yara saikace mayu barinma wanchan mai idanun kutaren” tanuna Meena tabe baki Meena tayi daga ita har Khadija, Amal tawuce tadauko mai takawo, kafinma Gwaggo tai magana Khadija ta tashi tadauko mai ruwa da drink daga fridge na Gwaggo ta kawomai bude abincin yayi dambu ne lafiyayye yanasan dambu hakan yasa yaci ba laifi Gwaggo tana zaune tana kallonshi ganin yadanji sauki yasa hankalinta ya kwanta sosai saida yagama ci sanan suka kwashe kayan sukai kitchen dashi shikuma yafice suka biyoshi abaya suka fito Gwaggo natafiya ahankali dan kafafun sun dawo a lallaba bata iya tafiya sosai saisa ko’ina za’aje da ita da keken guragun ta tareda ita.



Mami suka gani a tsakar gida kan wani hadadden chair da table agabanta tadaura kafanta kan table din Yar aikinta na gyaramata nails na kafa tana danna wayanta tana tauna cingum tana murmushi, jin sahun tafiya yasa tadago kanta binsu tayida kallo tace “Hydar daga kannenka sai Kakar ku kakeso nibaka sona saisa ba’a taba fita dani ba” tai maganan tana kallon Aliyu dayamayi gaba abinshi kaman badashi akeba, kaman jira Gwaggo take taballamata harara tace “akanme zai soki ke kika haifeshi jimini ikon Allah” dan dariya Mami tayi tai kara da cingum dinta tace “Hajiya Gwaggo maida wukan a dawo lpy” “Mami mun tafi” yaran suka mata sallama, “saikun dawo” Mami ta amsa yaranta tana murmushi tabisu da kallo  tana hararan bayan Gwaggo, saida sukai nisa sanan ahankali tace “Allah yakasheki mayyar tsohuwa kawai na huta, mata takai kusan shekaru dari amman taki mutuwa” tana zaune tana kallonsu yaja mota suka wuce sukabar gidan.




On a normal speed yake tuki yau danji yayi kanshi yasoma ciwo sosai amman yadaure dan baiso Gwaggo tagane ballema tadamu, ahaka harsukakai jabi lake mall din wuraren 5:30. Parking yayi wurin parking sanan suka fiffito, ganin yazauna aciki yasa Gwaggo tace “muje mana” yatsine fuska yayi yafito yabude boot yaciro kekenta yana sata akai yace “zan jiraku anan akwai wayoyin office dazanyi” yay maganan yana bama Meena ATM card dinshi yace “idan kuka kararmin dakudi Abba zansa yabiyani da monthly allowance dinku” dariya sukayi sanan Meena ta tura Gwaggo suka wuce tace “bye Ya Hydar” shiga mota yayi yazauna tareda kwantar da kujeran yana kara karfin Ac sanan ya kwanta kanshi najuyawa ya tsani rashin lafiya saisa baimaso ya kwanta ma wanan, ajiyan zuciya ya sauke ahankali yanaji zuciyanshi natashi cikinshi najuyawa kaman zaiyi amai, jin amai yazomai dawani irin sauri ya yunkuro yabude kofa yafito sai amai, kwaro amai yashigayi anan wajen motanshi sosai idanunshi sukai ja…..



Ahankali ita kadai take tafiya a parking lot din wayanta na kunnenta tana sauraron kwatancen da Glory kemata na inda venue su yake acikin wajen, bakaramin kyau tayiba tana sanye dawani english gown daya kaimata har kasa red yabi jikinta sosai ya bala’in fito da shape nata dudda bawani kamata yayi ba amman sabida kalan yadin yasa yanayin jikinta yafito, fuskanta yay wani kalan kyau yana glowing dudda bata shafa hoda ba dan ita hoda nasata kuraje a fuska saisa tama daina sawa but ta gyara eyebrows dinta sanan tasa kwalli dayawani irin haska fararen idanunta suka fito wallll, sai pink lipstick data kara kan pink lips dinta dayasa lips dinta yay wani kalan crazy baby pink daya kara fito da fuskanta sosai, ta gyara gashinta daya gama hargitsewa tai styling frontal hair din da gel dudda dama gashinta a kwance yake but karawa da gel datayi yasa tai kyau fuskanta yafito sosai takawo wasu simple pearls earring silver tasaka, tayana light peach karamin veil akanta dayadan zame kadan kasa sabida iskan da akeyi uwa za’ai ruwan sama gashi bahadari just that garin is looking damn cozy, tasaka heel dayama kafanta kyau silver dayafito da fine fine sexy toe nails dinta, tana tafiya ahankali tarataya wani karamin handbag na LV a shoulder ta sai goran bottle water na Eva data rike tasha kadan aciki dan she was thirty ahanya ma tasaya yanzun nan dazasuso. 


Kaman daga sama taji kakarin amai na mutum chak ta tsaya at the same time taji kirjinta yawani buga dum! Tsayawa tayi chak sanan ahankali tace “ok I am coming now nagane wurin” katse wayan tayi sanan tajuyo tana kalle kallen inda take ganin bataga kowaba sai shiru dataji yasa tacigaba da tafiya abinta, karajin kakarin amai datayi yasa tasake tsayawa chak ita kanta she don’t even know why take tsayawa amman kaman something is pulling her, komawa baya tashigayi ahankali tana waige waige kafin chan tahango wani Babban mutum dan that doesn’t look like a small boy tsugunne in between wasu manyan jeeps guda biyu yabata baya yana amai, tsigan jikinta taji yawani tashi, tun tana Yar karaman Yarinya ta tsani taga mutum naciwo, part of the reason why kowa is her friend a school kenan inhar Khairy tasan u are sick to far she die there Khairy is damn caring idan mutum naciwo saitamafi mai ciwon damuwa.



Takai almost 20second tsaye tana kallonshi yanda yake amai tsigan jikintai natashi tun yana amai abu na fitowa har kawai amman yake babu abinda kefitowa, ahankali tadaga kafanta zata wuce ta tafi samin kanta tayi dasake juyowa takalli bayanshi sanan takalli bottle water hannunshi kafin ahankali tana tafiya gently tawuce lungun motoci adaidai bayanshi dab dashi ta tsaya tana kallonshi bakinta nadan rawa dan tsoroma takeji mutum na amai tazo meruwanta amman still tadaure ahankali tace “Sir do you want some help nakira maka security”? Batare daya kalleta ba koyajuyo ba ya girgiza mata kai alamun no, jitayi zuciyanta yamata wani nauyi kaman tai kuka tasake dukowa kanshi sosai anatse tace “but u are very very sick, do you want some water, I have water, here gashi” tai maganan da sauri tana budemai goran ruwan tana mikamai ta gaban fuskanshi, goran ruwan yabida kallo, murya chan ciki dabaya fitowa sosai yace “thanks” goran tabida kallo ganin bai karba ba yasa ahankali tace “ka karba ka wanke fuskan ka u will feel better, haka Mama kemin idan banda lafiya nai amai” jiyayi kanshi nawani irin ciwo, azuciye yawani juyo da jajayen idanunshi dake cikeda zazzabi yawani taso kaman zaki zai cinyeta baya tayi atsorace ruwan hannunta yafadi heel din kafanta ya turgude dawani dutse hakan yasa kafanta ya turgude tai baya zata fadi atsorace hannu daya yasa ya chapko hannunta dasauri yana kallon fuskanta da jajayen idanunshi kaman yanda itama a bala’in firgice take kallon fuskanshi kirjinta nabugawa fast fast lips dintaI narawa sosai ganin police man dinaCn ne.





1️⃣9️⃣




Cikinsu duka babu wanda ya iya wani motsi yana rikeda hannunta yana kallon fuskanta kaman yanda take kallon nashi, ganin iska nawani irin kadawa sosai gyalen ta gabaki daya yay baya iska na neman fizgeshi yay sama dashi yasa yay wani irin pulling dinta ta taso saura kiris tafada kirjinshi da kyar ta iya maintaining posture dinta gabanta nafaduwa sosai tasauke idanunta kasa, tundaga yatsunta datake wasa dasu tana yakushin riganta dasu yake kallo har zuwa fuskanta da lips dinta dake rawa sosai zuwa gashinta dakeda bala’in kyau datai parking tai donut da jelan gashin dayay yawa kana gani kasan tanada suma sosai gyalen na wuyanta, ganin yanda ake iska sosai ta sandare awurin not her self yasa murya chan ciki yace “cover ur hair” gyadamai kai tayi ahankali batare data kalleshi ba takai hannunta takamo gyalen daga wuyanta zata yana akanta kwace gyalen iska yayi da karfi saikan fuskan Hydar dasauri tadago kanta, ahankali ya lumshe idanunshi jin wani sassanyar kamshin da gyalenta ke fitarwa da atake yaji ya kwantarmai da tashi da zuciyanshi keyi duk wani amai dayakeji yakoma, gently yakai hannunshi yadaura akan fuskan nashi yadauki gyalen sanan ahankali yamika mata, kallon fuskanshi tayi kafin ahankali takalli hannunshi dake dauke da gyalenta dayake mikamata sanan tasa hannunta ahankali ta karba daidai wani kalan mugun ruwa sama ya sauko da karfinshi dayama firgitata dasauri takalli sama sanan takalleshi kafin tajuya da sauri zata wuce. “Ummulkhair!” Taji yakirata amugun natse dayasa taji gabanta yawani kalan fadi, tsayawa tayi chak ruwan nadukanta sanan gently tajuyo takalleshi gani tayi yabude mata bayan jeep dinsu shima yana tsaye ruwan na dukanshi, batasan mesa ba but kasa mai musu tayi ahankali ta tako tazo har gabanshi sanan tashiga ciki ta zauna, bayan shima taga yashigo dasauri ta matsa chan gefe yamaida kofan motan  yarufe, daganan inda yake yadan mika hannu ya kunna motan sanan ya kunna AC motan yadauki wani bottle water yadawo yazauna yadan bude kofan motan kadan ya kuskure bakinshi kafin ahankali yamaido kofan yarufe sanan ya ijiye goran ruwan akasa ya kwantar da kanshi yana sauke ijiyan zuciya ahankali dukansu suna sauraron yanda ake ruwa da mugun karfi harda kankara ma.



Sunkai almost good 6min a motan babu wanda yacema wani wani abu kanta nakasa tana fidgeting yatsunta, shikuma yana zaune gefenta kanshi naciwo amman kallonta yake kaman an ijiyemai TV, ganin yanda ta takure tanajin sanyi sosai sabida ruwan dayadan daketa kadan sanan ga sanyin AC motan daya kunna yasa ahankali yadan yunkuro hannunshi yamika ya kashe AC sanan yadauki jacket dinshi na kayan yan sanda that is always acikin motan sanan ahankali yawarware shi matsowa yayi kusada ita yana kallon fuskanta bala’in firgitata tayi jin mutum kusada ita sosai dayasa takalleshi dasauri kallonta shima yake ko kyafta idanu bayayi ahankali yadaura mata jacket din kan kafadanta yarufamata shi da kyau yana kallonta kaman yanda take kallonshi tana nishi da sauri da sauri dayakejin hucinshi akan fuskanshi sanan yadan matsa baya zai koma wurin dayake da zama kaman daga sama ahankali murya chan kasa fa inda ace akwai mutum na uku amotan nan bazai tabajin metace ba tace “u are sick” kallon kwayan idanunta yayi kaman baigane metace ba, gyadamai kai tayi idanunta sun cika da kwalla sosai ahankali tace “wlh bakada lafiya, ur body is hot, let’s go to the hospital please” tana karasa maganan hawaye ya gangaro mata daga idanu sharrrr, hawayen yabi da kallo kaman wanda baitaba ganin mace tai kuka ba, murya chan kasa batare daya koma ba he’s still very much close to her ahankali yace “you don’t want me to be sick” gyadamai kai tayi ahankali wasu sababbin hawayen nakara taruwa a idanunta, murya chan chan ciki yana kallon kwayan idanun nata dasukenan farare fat kaman farin gajimare yace “why”? Girgizamai kai tayi saikuma ahankali tace “I don’t know, seeing u sick is making my heart to hurt” dan lunshe idanu kadan yayi sanan yabude su yadaura akan nata, lips dinshi sukai motsi kaman whistling yana kallon yanda take kuka mara sauti yace “stop crying” gyadamai kai tayi ahankali tana kokarin tsayar da hawayen, hannunshi yasa yaciro handky daga aljihunshi yamikama mata yace “here” karba tayi takai kan fuskanta tana goge hawayen saida yaga tagoge tass sanan yakoma gefenta yazauna da kyau yace “mekikazo yi anan?” ahankali tace “today is Glory’s birthday my friend she’s celebrating it anan” dan juyowa yayi yakalleta kaman mai nazarin wani abu yace “how old are you” kallonshi itama tayi kafin tasauke kanta ahankali tace “20” kaman daga sama taji yace “small Gurl” dawani irin sauri takalleshi tabe baki taga yayi batasan mesa ba abin saiya bala’in bata dariya she don’t even know why, dan murmushi kadan tayi sanan tahadiye shi kallonta yayi ganin yanda dimples dinta keta lotsewa alamun murmushi take amman tana hadiyeshi, kaman daga sama taji yasake jefo mata tambayata anatse. “Are you in any relationship”? Dasauri takalleshi, kallonta shima yayi fuskanshi looking he’s serious da tambayan, murya chan kasa yace “kinada any man dakikeso…..or yake sonki”? Yay maganan  muryanshi na breaking cus shi kanshi baisan mesa yakema tambayanta this kind of wired question ba, dauke kanta tayi, sanan ahankali ta girgiza mai kai alamun no, dan murmushi kadan yayi yanajin duk wani ciwon kan dayakeji yana tafiya, jakanta dake in between them yasa hannu yadauka yabude wayanta yaciro Dasauri takalleshi numbershi yasaka sanan yakira kanshi, danne danne taga yanayi awayanta kafin yamaida ya ijiye cikin jakan, ganin ruwa na tsagaitawa yasa tadan kalleshi ahankali tace “zantafi” yana kallonta right in the eye yace “where is ur driver? U should head home” gyadamai kai tayi sanan ahankali tace “yanata chan bangaren” inda take nunamai da hannu yakalla, ahankali yace “ok” bude kofa yayi yafita cikin yayyafin da akeyi yakoma gaba kunna motan yayi yaja motan har gaban motansu yakaita sanan yay parking jacket dinshi tacire ta linkemai ta ijiye ahankali tace “thank you” sanan tabude kofan zata fita kaman daga sama taji yakirata. “Ummulkhair!” Faduwa gabanta yayi batasan mesaba duk idan yakirata sai gabanta yafadi, juyoda kanta tayi takalleshi shima ita yake kallo, ahankali yace “I am a very very jealous Man! Be mine only Khairy! I am in luv with you! Good night!” Dawani irin sauri har hannunta narawa tamaida kofar tarufe sanan tajuya tabude bayan motarsu ta shige kafin yaja motar nashi yawuce.




2️⃣0️⃣

Free page



Wucewa yayi daidai lokacin wayanshi na ringing ganin Meena ce ke kiranshi yasa yamaida kanshi kan tukin inda yasan zai gansu chan yawuce, atsaye ya gansu da alamu shi suke jira, kashe motan yayi yafito yana kallon Gwaggo dake binshi da kallo ganin ya wartsake sosai yace “lpy” hararanshi tayi tace “munafuki nidai sani a mota” sata yayi a mota yana murmushi kasa kasa sanan yamaida kujeran boot su Meena suka saka ledojin abubuwan dasuka siya a boot sanan yarufe kowa yakoma yashiga motan yaja motan zuwa gida yana parking yafito baima tsaya bi takansu ba masallaci yawuce dan yasan zasu tafi da Gwaggo ciki.


Tareda Abba suka shigo gidan daga masallaci magidancin mutum ne yana sanye da suit baki dan daga wajen aiki yake, falo suka wuce, duk su Mami da yaran na falo gaida Abba duk sukayi, ganinshi yasa Mami tace “akawo abincin yanzu Alhaji” girgiza matakai yayi yay hanyar stairs yace “I am coming tukunna muje Aliyu” binshi Hydar yayi har zuwa sama wani babban falo suka shiga wanda kana gani kasan na Baban shine, zama yayi akan kujera Abba yazauna kusada shi yakai hannunshi yabude idanunshi yana haskawa dawani dan tocula dankarami yana dubashi, dan jim yayi sanan yace “you have typhoid Aliyu, I think zan saka on injections tunda bakason magani” yatsine fuska yayi ahankali yace “Abba wlh naji sauki, kainafa kadai ke ciwo kuma yadena” “yimin shiru my friend” Abba yay maganan yana tashi wani babban first aid box yadauko yabude sanan yahada wani allura Aliyu naji yana gani Abba yamai allura, sanan Abba yace “Aliyu this work is draining you, akan me u are a Barrister kawani kama kashiga aikin police with just mukamin ASP eh, why will you choose a police man job Son common talk to me” yay maganan yana kallon Aliyun cikeda damuwa, Aliyu ne kadai danshi namiji, yaranshi duka takwas aduniya, Aliyu ne nafarko he’s 32yrs sai kannenshi mata guda bakwai hudu sunyi aure dukansu baa Nigeria suke aure ba Saura 3 agida suna school, ganin yay shiru yakasa cewa komi yasa ahankali Abba yace “tashi katafi, but make sure kaci abinci kafin ka kwanta kaji” gyadamai kai yayi sanan yatashi yawuce yabude kofa shikuma Abba yashiga cire kaya dan yay wanka duk bayajin dadi.



Yana fitowa da Mami yaci karo anan falon sama tana zagaye, kallo daya yamata yadauke kai yashiga sauka kasa itakuma tawuce tashiga falon Abban da sauri tanabin ko’ina da kallo dan Abba yariga yashiga bayi, ganin allura da first aid box abude yasa tasauke ijiyan zuciya taje gaban wardrobe tana budewa dan samoma Abba kayan dazai sa….

**


Tana komawa gida kayan jikinta tacire tayo wanka sanan tai salla tasauko kasa gabaki dayansu duk suna zaune a falo suna dinner gaida kowa tayi sanan tazo kusada Mama tazauna tana kallon Mama dataga tasaka sweater turtleneck black daya rufe har wuyanta tasaka hulan sanyi shima baki kafanta da bakin safa, kallonta Mama tayi jin ajikinta ana kallonta hannu tasa taja hancin tace “ke abinci zakici ko kallona kikazo yi” dan dariya kadan tayi tace “Mama sanyi kikeji ne AC akashe” gyadamata kai Mama tayi batare data bata amsan tambayan ba tace “mezan zubamiki” kallon abincin tayi sanan takalli madaran da Baba kesha tace “Mama madara zansha banson naci abinci” Madaran da Baba Kesha a cup da zafinshi ma yamika mata da sauri ta karba tana murmushi tace “thank you Baba” hararanta Mama tayi tace “kwadayi Khairy, aikin ki kenan tun kina Yar kankanuwan ki sabida babban ki kullum yanashan dafaffen milk kema kikesha” mikewa tsaye Baba yayi yace “bagashi nan saisa she’s so bright ba ga kwanya, milk is good for children barin ma Wanan na Shanu damuke sha dababu mix, bari naje nai salla” yakalli su Manaf da duk suka tashi suma sukawuce suka tafi masallaci, madaran ta shanye tass sanan ta tashi ta tattara kayayyakin dasukaci abinci takai kitchen sanan tadawo tana kallon Mama dahar lokacin take zaune inda tabarta tace “Mama tashi mutafi sama” ahankali Mama tace “wuce kitafi akwai wani program na wa’azi dazan kalla yanzu za’a fara” sanin Mama da kallon tashoshin wa’azi yasa tawuce stairs abinta tace “Mama gobe zani saloon kitso good night” ahankali Mama tace “Allah yakaimu Khairy” saida taji bude kofanta tashiga daki sanan gently tasa hannunta tadaura kan kujeran dake gefenta tana kokarin tashi tsaye amman takasa idanunta sunyi jazur kana ganinta kasan tana wahala ita kadai tasan metakeji, komawa tayi tazauna ahankali sanan tasauke ijiyan zuciya, hawayen daya zubomata takai hannunta tashare tanajan hancinta jin majina ya tsinke mata kafin tasauko da hannun ta share majinan, sanan ahankali tasauke hannunta kasa tana kallon tafin hannayen nata dasukai jajir kaman wanda yaji ciwo, ajiyan zuciya tasauke majina na gangarowa daga hancinta sanan tadaura hannunta kan hannun rigan tajashi sama tana kallon fatan jikin hannunta dasukai jaaa wasu kalan kuraje dasuka fitomata sunyi dabbare dabbare sunyi chaaaaa wanda is not just hannu ko’ina ajiki suka fesomata har wuya saisa tasaka Riga turtle neck dankar Khairy tagani, hannu takai tashare majinan dataji yana gangaromata yakai mata baki sanan tadaura hannunta kan baki tana kuka mai bala’in tabarai, she don’t even know why she’s crying, tana zaune a inda take aka turo kofan falon aka shigo dago kanta tayi takalli kofan Baba ne yashigo, kallo daya yamata yagane kuka take maida kofan yayi yarufe sanan yakaraso ciki ahankali yazo gabanta tsugunnawa yayi sanan yakai hannunshi yakama nata yakai kan kafadarshi kafin ahankali yadagata tashi tsaye tayi da taimakonshi dan ayanzu sai an dagata an kuma kwantar she can’t really do anything da kanta sabida, har yakaita daki bai iya cemata uppan ba, zaunar da ita yayi akan gado sanan yashiga bayi yadauko baho da buta da kanshi yamata alwala sanan yasamata hijabi kwantar da ita kan gado yayi sanan yace “pray” gyadamai kai tayi da idanunta dasukai jajir sanan tashiga yin sallan isha’i yana zaune gefenta harta idar sanan yacire mata hijabin.

Kashe wutan dakin yayi sanan ya kwanta gefenta yarufa mata bargo kafin yadaura kanta kan kirjinshi yanajin yanda jikinta yay zafi sosai, murya chan kasa tana kara kankameshi tace “nagode Baban su Manaf” gyadamata kai yayi yakasa magana har lokacin, hannunshi takama takai kan kirjinta ta manna sabida yaji yanda zuciyanta ke bugawa ahankali tace “kaji yanda zuciyana ke bugawa ko, tunanin yarana yasa haka, dan Allah ka kara aure banso daidai da sakan daya yarana suyi maraici kaji Baban Manaf” wata kalan huci kai zafi Baba yasaki ahankali yace “Maryam at this junction danake in my life banma da natsuwan dazan iya neman aure, yarana bazasu taba maraici ba, I am here, Baffan su nada mata har biyu they are sounded with mata they can call mom, please tunane tunanin nan will keep on eating u harsai kin daina, please concentrate on your health kinji, gobe zan kira Dr” girgizamai kai tayi tace “please no kabarshi yaje yay saving those that still have chance not me nariga naji ajikina my end is nea…..” Kankameta sosai yayi ajikinshi yana huci mai zafi wasu thick tears na neman fitomai daga idanu ya hadiye su ahankali yana jijjigata ahaka bacci yay awon gaba da ita saida ya tabbatar tai baccin sanan yatashi ahankali gyaramata bargo yayi sanan yawuce yashiga bayi alwala yadauro yazo yahau kan dadduma shafai da wuturi yayi yamata addu’a sanan yakoma gado kusada ita ya kwDanta.




2️⃣1️⃣


Free page

Saida tai sallan isha’i sanan tacire hijabi kayan bacci taciro tasaka tana tunanin abinda yafaru dazu itada Aliyu, dan murmushi tayi sanan ta kashe wutan dakin ta kwanta.

Batasan mesaba tadade kwance rikeda wayanta tana kallon wayan every minute deep down she wish to hear his voice amman kuma bamataso tana tunanin what she wish for din akanshi abin is so so new for her she’s not just use to it, ahaka bacci yay awon gaba da ita wayan nakan kirjinta this is the first ever time in her life da waya ke bacci akan kirjinta.



Wuraren 12 nadare wayan nata yahau ringing afirgice tafarka tana daukan wayan daga kan kirjinta tana danna gefe dan yadena ringing yay silent, sanan takalli screen din da kyau ganin Aliyu Hydar batasan mesaba faduwa gabanta yayi, ahankali takai yatsanta dake dan rawa ta danna wayan na gab da katsewa takai kunnenta, murya chan kasa dake nuna alamun bacci tace “Hello” shiru yayi yana sauraron muryanta da bazaiyi karyaba tunda yake baitabajin macen da muryanta yamai dadi kaman nata ba, dan gyaran murya kadan yayi cikin wata kalan murya dashi kanshi baisan yanada itaba yace “Khairy” ahankali kaman wata Yar karaman baby tace “Uhm yajiki? Kasha magani?” dan murmushi yayi jikinshi namai wani iri jin muryanta like that so naked sabida baccin data fara, sanan har ranshi yaji dadin yanda ta tambayeshi yajiki koyasha magani, ahankali yace “yeah, Abba yamin allura” kaman zatai kuka dan ita harga Allah tanada tausayin mara lafiya tace “auuch that must have hurts, I hate niddles, sorry ko!” murmushi yayi ya gyadamata kai yace “thanks, you are sleepy”? Gyadamai kai tayi tace “Uhm” ahankali yace “alright good night, make sure you plug in your phone sabida yasami chaji, and say your prayer before sleeping okay” gyadamai kai tayi ahankali tanajin wani iri azuciyanta kaman tacemai sucigaba da magana karya tafi tadenajin baccin tace “okay night” tai maganan batare data cire wayan daga kunnenta ba shima bai katse wayanba sunkai kusan 10min ahaka sanan murya chan kasan kasan makoshi yace “I love you Ummulkhair okay” gyadamai kai tayi ahankali tanaji hawaye nazuwan mata dabama tasan na meyeba but ko Allah yasani she just feel damn connected to him and vulnerable around him kaman ba itaba, katse wayan yayi hakan yasa taciro wayan daga kunnenta tarungume wayan hawayen na gangaro mata daga idanu, karan message dataji yasa taciro wayan daga kirjinta dasauri tabude wayan ganin message from Aliyu Hydar, bude messege din tayi da sauri. “Maisa nake sonki Ummulkhair? Well who am I to question faith? All I feel right now is I wanna spend my eternity with you, gud night Khairy”

Takaranta message din kusan sau biyar sanan ta danna reply tai shiru tana kallon blank space din bamatasan mezata rubuta maiba, saikuma chan tashiga typing .

“I feel vulnerable and free around you, my heart beat whenever I hear your voice, duk sanda na rufe idanuna kai kadai nake gani, is that love?“

Yana ganin message din yay mata reply.

“time will tell Khairy na❤️”

Wani kalan murmushi tayi ganin yakirata da Khairy na sanan ta tashi zaune USB takamo dake jone da wall socket ta saka wayan nata kaman yanda yace tayi sanan takoma ta kwanta tadade kafin bacci yay awon gaba da ita.




Da asuba Baba yashigo yatadata saida yaga tashinta dan Khairy nada nauyin bacci sanan yawuce yatafi, bayi tashiga tadauro alawala tazo tai salla, koda tagama karatun Al Qur’ani tayi yau sosai wuraren 6 ta tashi, hijabi tacire yau ita keson yimusu breakfast tunda bazata school ba hakan yasa ta tashi tafice daga dakin tasauka kasa kitchen tashiga tana murmushi tace “idan matarchan tazo yau zataga na hutashe ta” lafiyayyen breakfsat tahada musu dan sinasir tayi da farfesu sai kunun Gyada dasu fried chips, saida tagama tsaf sanan tashiga fito da komi falo ganin Mama zaune afalo kusada Baba yauma sanye da kayan sanyi yasa ta ijiye kulan a tsakiyan falo ta tashi tana kallon Mama dataga tamata haske sosai Mama datake nan baka but tai wani irin haske, kafinma Mama tai magana Baba yace “ke wuce ki kawo mana abinci ga yayyinki nan zuwa” dasauri tajuya tana murmushi tace “Baba naga Mama tai haske ne takara kyau” kitchen tashiga takarasa fito dakomi takawo lokacin su Manaf sun shigo suma zama duk sukayi Baba da kanshi yadebo ma Mama Sinasir yana bata abaki, murmushi tayi tana kallonsu tana taba Ya Manaf, hararanta yayi yace “dalla kauyus” cigaba dacin abinci duk sukayi kowa yay shiru Baba da Mama ne suka fara gamawa sanan yakalli Khairy yace “Maman ki tace zaki saloon ko” gyadama Baba kai tayi tace “eh Baba, gyadamata kai shima yayi yace “yau rabonki da gidan Baffan ki kwana nawa” dan ajiyan zuciya tayi ganin yanda Baba ke kallonta sanan ahankali tace “an dade Baba” jinjina kai yayi yace “kije ki shirya kitafi saloon yanzu ana gamawa kije gidan Baffan ki ki gaidasu sanan kije gaida Matar Hafiz” ahankali tace “to Baba” “tashi kije” tashi tayi tai sama Baba yacigaba dayima Mama hira yau yanaso yakaita asibiti kotaki kotaso dan kwata kwata this days bata iya baccin dare ga kurajen nan kara fesowa suke ajikinta bana wasaba.




Tana shiga dakinta zama tayi kan gado sanan tadauki wayanta dahar lokacin bata cire daga chaji ba tabude message din Aliyu tagani around 5 na asuba.  

“it’s time for subhi, wake up”. Murmushi tayi sosai sanan ta ijiye wayan tawuce bayi wanka tayo tafito direct gaban wardrope dinta taje wani riga da skirt na wani paper lace dinta tafito dashi da akamata dinkin jumper rigan yakai mata har gwuiwa sai skirt shikuma straight skirt daidai jikinta, mustard color ne lace din sai aka ni kayan dawasu bakaken stone, murmushi tayi taje tadaurasu kan gado sanan tazauna gaban mirror tadauki manta tana shafawa tana kallon fuskanta amadubi tana tunanin Aliyu, saida tagama shafawa sanan ta saka kayan dasuka mata bala’in kyau sosai, murmushi tayi black veil tadauka ta feffesa turare sanan tadauki handbag dinta ta jefe wayanta aciki tasa flat slippers yau tafito, afalo taga Baba kan doguwan kujera yana duba jarida Mama kwance tayi filo da kafanshi tana bacci yarufamata bargo, ganin Khairy yasa yadaura hannunshi akan lips dinshi yace “karki tadamin da matata tana bacci” turo baki Khairy tayi ashagwabe tace “Baba yanzu kafisun Mama dani Yar Autan ka” dan dariya tayi yamika mata wasu kudade yace “gashi Adamu na jiranki kije saloon kina gamawa ki wuce gidan Baffa” gyadamai kai tayi ta karbi kudin sanan takalli fuskan Mama dake bacci tace “Baba natafi” adawo lpy.


Saloon suka wuce direct baa wani bata lokaci ba wanke mata kan akayi sanan aka mata kalaba yan manya manya within one hour tagama tafito tashiga mota Adamu yatada motan zuwa gidan Baffa, dan tsaki tayi ahankali kawai dan babu yanda zatayi ne dabataje ba bata wani don zuwa gidan Baffa dudda tana bala’in don Baffa da duka yaran gidan, da Mum amman Ammi kwata kwata jininsu bai hadu ba batasan mesaba, tana cikin yan tunane tunanen ta ta iso gidan, Babban gida ne katoto, gidansu Babba ne but Gidan Baffan su is X2 nasu, mai gadi na ganinsu yahau murmushi yace “oyoyooo Khairy” murmushi itama tayi Adamu na parking tabude tafito dasauri mai gadon yazo wanda yake bayaro ba yace “munyi fushi wlh” dariya tayi tace “Baba Bala wlh school yaboyeni” tai maganan tana ciro kudi a jaka tamikamai 5k cikin kudin da Baba yabata karba yayi yace “nagode Yar albarka, Khairy mutuniyan kirki” murmushi tayi tajuya tana kallon cikin gidan, dankara dankaran flat ne guda uku agidan haka ajere, na farko wanda shizaka fara isa kafin kaje sauran yafi sauran biyun girma saina biyun dana ukun girmansu daya, da sauri saurin ta gudu gudu take tafiya wuce flat na farkon tayi tayi na biyun bude kofa tayi tana ihu. “Mummmmmm Mum” bin falon tayi da kallo daya hadu sai kamshin turaren wuta yakeyi stairs tayi da gudu tai sama daidai wata mata dazata kai 45 kefitowa daga wani daki cikin shiga na alfarma ta harari Khairy tace “ai nayi fushi wlh Khairy” wani murmushi Khairy tayi batayi wata wata ba taje dagudu tafada jikin Mum tana juyida ita cikeda murna tace “Mum I am sorry kinji, wlh school yahanani zuwa, Mum kinyi kyau iyyeee, ina Batool” turata Mum tayi tana nishi tana dafa kujera dan jiri taji tanaji tace “jama’a na shiga uku yarinyar nan zata kassarani” dariya Khairy tayi tajuya tai hanyar wani daki tace “nasan yarinyar nan tana bacci to baki isaba nazo” binta da kallo Mom tayi ganin kullum kara girma Khairy keyi, tana bude dakin taga wata yarinya da atleast zasu iya zuwa mate kokuma yarinyar tabama Khairy 1 zuwa 2yrs haka ta tashi zaune sanye da kayan bacci tana hamma tana hararan Khairy, yarinyar kamansu daya da Mom, wani tsalle Khairy tayi tafada kanta akan gadon yarinyar ta kwasa ihu tace “Mum kinga Khairy ko ni dagani ai wlh fushi nake dake konai chatting naki up baki dubawa kuma baki daukan calls” sakinta Khairy tayi tace “wlh Batool ni taba waya ma wahala yakemin balle responding to calls or chat har gwarama kamin text message ina gani zan reply, but rabona ma dana shiga watsapp harna manta wlh” baki Batool tabude zatai magana Mom ta turo kofan dakin tashigo hakan yasa duk suka kalleta, Khairy takalla tace “kinje kin gaida Ammi Khairy”? Dan zaro idanu Khairy tayi sanan ta girgiza mata kai ahankali, daure fuska Mum tayi babu alamu kan fuskanta tace “Oya tashi kije ki gaidata, fast” tashi tayi kaman ruwan jikinta ya shanye, jakanta ta ijiye kan gadon Batool sanan tawuce tafito Mum tace “duk idan kin shigo gidan nan always ki shiga flat nata ki gaidata kafin kizo nan” gyadamata kai Khairy tayi sanan tawuce ta sauka kasa kafin tabude kofa tafice.



Ajiyan zuciya tasauke tana kallon kofan sanan gently tasa hannu tabude kofan wani lafiyayyen kamshin turare namata sallama ahanci, Babban falo ne sosai dayamafi na Mom girma, zaka dauka dakin wani president ne ko gwamna sunji kujeru da kayan gayu, wata Babbar mace ce mai kiba sosai a falon, kana ganinta you don’t even need to ask twice kaga Hajiya irin cash HajiyUoyin nan.




2️⃣2️⃣



Free page

Fara ce tass kana ganinta kaga bafulatana dan tanada mark na fulani a gefen fuskanta taci gayu na alfarma tana sanye dawani stone gown na exclusive mai pattern, kunenta zinare wuyanta ma haka yatsun hannunwanta guda biyu ne kawai babu zoben zinare ajiki manyan yatsun hannunta sune babu but sauran 4 4 fingers nata duka da zinare tana zaune akan kujera ta hakimce gawani iPad na Apple agabanta tadaura kan wani very very fine stool tana video call dabata iya ganin kowaye a screen din tunda ita daga waje take, hannunta matan rikeda wani white transparent bowl da ita kanta Khairy basuda irinshi agidansu an yanyanka strawberries da kiwi fruits kanana tanaci da fork, kokai waye kaga matan saika shiga taitayinka like duk rawan kanka irin matan nan ne da they don’t even needs to show u su waye kana ganinsu kasan they’re no nonsense powerful woman saisa haryau itadai Khairy bazata iya cewa ta tsani matan bane but kawai bata sonta, hasalima ita tsoronta ma takeji ko haukanta take agidan dazaran Ammi tazo wajen natsuwa take kaman ba itaba kodako da Baffa take magana, kuma agaban kowa ko agaban Baffa ne Ammi zata iya rufe kowa da fada baruwanta saidai in bakayi ba daidai ba.



Kallo daya tama Khairy ta dauke kai, ahankali Khairy tajawo kofan falon ta maida tarufe sanan takaraso cikin falon ta nemi waje ahankali akasa tazauna kanta akasa tana sauraron maganan datakeji na namiji daga iPad din ashagwabe data rasa na waye dan tasan muryan duka yaran gidan nan banda Babban yayansu da akace yana UK.


Ashagwabe yace “Ammi please niki kyaleni I will get the food nafita jibi fa yanda kitchen dina yadawo” hararanshi Ammi tayi tana kallon screen din tace “My friend dauki egg din break it ingani” cikeda gajiya kaman zai fashe da kuka yace “I don’t even know why I called u ki koyamin yanda ake soya egg ma” dan dariya Ammi tayi da saida Khairy dake zaune tadan saci kallonta dan bata taba ganin Ammi ko taji Ammi tai dariya haka ba lallai waye wanan itakuwa.

“Good boy Zayn, tom add a pinch of salt” Zayn! Zayn Zayn! Itako a inama ta tabajin sunan nan Ohhkay kaman shine sunan yayan nasu dake kasan waje ko yayan su Hafiz, tatabaji Baba da Baffa suna maganan. 

Maganan Ammi ne yadawo da ita daga tunanin datake tace “bagashi nan ba kagama soya egg din amman da u are being lazy” dariya yayi sosai yace “Ammi nataba gayamiki u are the world best Mommy? No not just best you are the bestest Mom in this world Ammi na” dan murmushi Khairy tayi dan maganan yasa ta tuna da Mama haka take cema Mama world best, kiss taji yasakin ma Ammi ta wayan yace “love you Ammi bye” murmushi sosai Ammi tayi tace “I love you too Son, speak later, make sure u put on jacket kafin kafita dan u are having cold” “who am I to say no to this fine woman, Ammi this egg taste delicious bye” dasauri Ammi tace “kaci ahankali karka kwar…..” kafin takarasa maganan ya katse wayan murmushi tayi sosai kafin takalli bowl don fruits din hannunta ganin tacinye yasa ta kwalama mai aikinta kira. “Karima” da gudu mai aikin tafito daga kitchen jikinta har yana bari dan inhar Ammi takiraka sau biyu to kora ne, cikeda girmamawa tace “Hajiya gani” bowl din Ammi tamika mata tsugunnawa tayi sanan ta karba tace “akawo miki wani abune Hajiya”? Girgiza mata kai tayi tamata alamu da hannu ta tafi, wucewa tayi tawuce kitchen falon yarage daga Khairy dake zaune akasa ta takure waje daya saikuma Ammi data dauki wayanta Z-flip tana daddannawa kaman batasan da mutum awajen ba.



Ahankali kaman ba Khairy ba tsabagen yanda ta natsu tace “Ammi ina yini” batare da Ammi takalleta ba kota daina abinda takeyi da wayaba tace “yanzu kikaga daman shigowa gaida ni Ummulkhairy” girgiza mata kai dasauri Khairy tayi gabanta nafaduwa da kyar tace “Ammi kiyakuri bansan kin…..” “stand up and get out of this room!” Ammi tadaka mata tsawa dan she finds it insultive ace itace Babba agidan nan ko kare yashigo gidan nan yasan itane Babba an dole ne abata wanan girman balle Wanan Yar karaman yarinyan nan da aka haifa agabanta tashigo gidan nan saita fara zuwa ta gaida kishiyanta sanan zatazo nan, itafa Ammi is like that bata daukan raini kona waye gatada fada, komin girmanka zata iya daga hannu ta kwasama mari.


Tashi tayi jikinta har rawa yake itafa adai rayuwanta yanzu this woman is the only woman datake shakka aduniyan nan, duk iskancin ka baka iya kallon fuskan Ammi kace zaka mata rashin kunya kozaka maida mata da magana wlh bazaka iyaba Allah yariga yabata Wanan haiba da kwarjinin nanne, gabanta nafaduwa sosai idanunta sunyi ja tace “Ammi I am so……” “out!” Ammi tai maganan tana nuna mata kofa dasauri tai kofa zata bude aka turo kofan hakan yasa kofan yabuge mata hannu, baya tayi tana yarfe hannun dasauri idanunta sunyi ja Hafiz ne yana sanye da jeans da riga ganin Khairy yasa yace “Khairy kene agidan” hannunta yabi da kallo yace “ohh no sorry nabuge miki hannu ne” murmushi takakalo tana maida hannun baya tace “Ya Hafiz welcome ina yini” sanan tabi tagefenshi tafice dasauri yabita da kallo kafin ya kalli Ammi dake danna wayanta abinta, maida kofan yayi yarufe yazo kusa da Ammi ya zaune yace “Ammi yaushe Khairy tazo” batare data kalleshi ba tace “maiya hanaka tambayanta kake tambayana” shiru yayi baice komi ba, saida tagama abinda zatayi sanan ta ijiye wayan takalleshi tace “how’s my granddaughter”? Murmushi yayi yace “she’s fine” “tafara shan nonon”? Gyadamata kai yayi yace “tafara Ammi, bata barin mu bacci, koda yaushe shan Nono take bata barin Moon tahuta”  dan dariya Ammi tayi taharareshi tace “idan naga granddaughter na tarame dagakai har matarka will have to answer me I am very very serious Hafiz, anyway anjima idan yan suna sun watse akwai kayan dazaka tafi musu dashi” Gyadamata kai yayi yace “Ammi kinsan irin uban kudi da Ya Zayn yaturomin wai nabama Moon da Little niko sule biyar bai baniba bayan ni namafi mai jegon wahala” dariya Ammi tadanyi saikuma tai shiru kaman mai tunani ahankali tace “I can’t wait to see yaran Zayn shima” dasauri Hafiz yace “Ammi ai nagayamiki Zayn nadawowa kurikeshi kumai aure dan wlh  Ammi Ya Zayn bai shirya yayi aure ba” shiru Ammi tayi batace komi ba, kallon fuskanta Hafiz yayi ganin tai nisa a tunani yace “Ammi kema u believe what I am saying ko” “stop talking about ur brother Hafiz” shiru yayi saikuma chan yatashi yace “ina zuwa Ammi” baijira amsanta ba yawuce yatafi, awaje yaga Khairy gaban tap na wajen flower tana wanke fuskan ta da ruwa, bamata lurada shi ba yana zuwa ya tsaya agefenta yace “after all this years haryau baki gane halin Ammi ba kullum kikazo sai kinyi kuka common my friend, je daki ki dauko gyalenki keda Batool na kaiku gidan suna kowa nachan banda ku” murmushi tayi tajuya da dan gudunta tashiga dakin Mum, basu wani jimaba itada Batool suka fito datai wanka taci gayu motanshi suka shiga sai gidaUnshi.



2️⃣3️⃣



Free page

Gidan Ya Hafiz yacika makil da mutane sabida suna, duka yaran Baffa na wajen, Yaran Baffa takwas, Ammi ta haifi hudu duka maza, Zayn ne babba, sai Hafiz, sai yan biyun da Ammi ta haifa maza da Hassan da Hussain, dukansu manya duk sun gama makaranta suma aure yau ko gobe, dan Ammi da Baffa sunyi aure tun suna yara, haihuwan yan biyun yazo mata da complication da dole aka cire mahaifanta gabaki daya data haifi sama da haka, itakuma Mom yara hudu ta haifan ma Baffa, mata biyu Batool da Zara’u wacce itace auta dan maza biyu kebin Batool kafin Zara’u, Abdulhamid da Abdullahi sai Zara’u, Zara’u ce kadai ke primary school su Abdulhamid yanzu suke SS1 boarding school, Batool itace ke university, dayake ana hutu dukansu suna gidan ga mamakinta harda su Ya Manaf da Maheer, dukansu sun hadu dasu Ya Hassan suna gaggasa raguna, mantawa ma tayi tayi kuka suka shiga shagalin suna ga Matan Ya Hafiz badai kirki ba sunan Moon yabita hakan yasa kowa Anty Moon yake cemata.



Sai Bayan sallan isha’i sanan suka baro gidan itadasu Ya Manaf, tagaji iya gajiya bacci ma tasoma abayan motan tadaura kanta kan kafadan Ya Maheer, bai tadata ba ganin tagaji yacigaba da danna wayanshi abinshi.


Bude musu gate akayi ganin motocin su Baffa yasa daga Ya Manaf har Mu’az din kowa yasha jinin jikinshi, parking sukayi hakan yasa tabude idanunta jin tsayuwan mota ta tashi zaune tana kallon compound dinsu sanan tabude kofa suka fito zata wuce Ya Manaf yace “ke ina zaki”? Dasauri tajuyo takalleshi kafin ma tabashi amsa yace “kibi Maheer kuje flat dinmu su Baffa sunzo magana akeyi” batai musu ba danta gaji tabi Maheer sukai flat dinsu shikuma da Mu’az sukai flat dinsu Mama da saurin su, bude kofa sukayi suka shiga sunabin kowa na falon da kallo, Baffa ne da Baba zaune kan kujera daya, sai Ammi da Mom zaune tareda Ammi akasa da fuskanta ya kukkumbura kaman ba ita suka Bari this morning fuskanta looking normal ba, Mom na rikeda handky tana share idanunta dan takasa rike kuka itakuma Ammi idanunta sunyi ja dan ciwo is something dako enemy naka don’t wish it on him, duk wanda yaga Mama saiya koka mata, kallonsu Mama tayi lurada kaman magana takeso tayi yasa Manaf yakaraso inda take hannunta yakama yarike yace “na tura Maheer da Khairy chan side dinmu Mama” ahankali yace “Mama meke miki ciwo”?  Kafin ma wani afalon ya iya magana aka bude kofa aka shigo Dr ne, rikeda wata karaman Leda a hannu yana zuwa allura yahada yazo wajen hannun Mama yakama yamata alluran a jijiya sanan yakalli Baba da Baffa dake kallonshi yace “can I talk to you sir in private”? Girgiza mai kai Baba yayi yace “likita duk duniya banda family daya wuce Wanan circle din dakake gani anan u can say anything, I think we are ready to hear kome zakace right wife” gyadamai kai Mama tayi kaman ba ita ke wahala ba, huci Dr yayi yakalli Mama yace “alluran nan zai saukar da kumburin fuskan nan da wuyanta, but at this point all I can say is make ur wife as comfortable as possible dan koda ankawota asibiti babu abinda zamu iyayi kuma, daga yanzu kome zaku gani kawai hakuri zakuyi har Allah yayi ikon shi dan komi na hannunshi, just make her comfortable and happy, please kudena kuka agabanta kowani abu dan Allah, that’s all bari nakoma hospital” tashi yayi yafita babu wanda ya iya cemai kala, Manaf yayi yayi yarike kukan nashi but yakalli Mama yaga yanda tadawo but dudda haka she’s still faking smile musu kawai yaji zuciyanshi yay breaking, fuskanshi yakifa akan kujera kusada Mama sai kuka yake da Mu’az dahar lokacin shi yama kasa shigowa cikin falon yana wajajen kofa, ahankali Mama tasa hannu takamoshi wani irin rungumeta yayi sanan tamikama Mu’az hannu alamun yazo zuwa yayi shima kuka wiwi ajikinta babu wanda ke iya magana cikinsu har Maman dan kumburin da fuskanta da wuyanta yayi yasa bata iya magana.



Ranan dukansu suna zaune a falon nan babu wanda ya iya motsi har asuba sanan tai bacci, daki suka Kaita suka keantar da ita sanan Baffa ya kwashi iyalinshi suka tafi gida, suna shiga alwala yadauro kawai yawuce masallaci.



Wuraren karfe 8 nasafe yafito daga masallacin, gida yawuce dayake yana dakin Ammi ne nan yayi bata falo yasan ta kwana hakan yasa yay sama zuwa dakinshi, zama yayi kan wata kujera ta musamman dayake da ita adakin nashi datake nan kaman gado shiru yayi yana tunani, ahankali yamika hannunshi yadauki wayanshi yay dailing number dayay saving da Zayn dayake nan international number, wayan na gab da katsewa yadauka anatse yace “Abba” dan ajiyan zuciya ABBA yasauke anatse shima yace “Zayn nasan is late ko wajenku” gyadamai kai Zayn yayi yana ture shishan dake gabanshi yatashi daga wajen yay bedroom dinshi zama yayi kan study chair nashi jin muryan ABBA somehow couple with the fact Abba baima Saba kiranshi da night ba most time da safe ABBA ke kiranshi ko darana, ahankali yace “Abba what is it are u okay”? Ajiyan zuciya Abba yasauke yace “Zayn Maryam matan Baffan ku batada lafiya, she’s seriously ill, inaso kome kakeyi yanzu kabarshi find any available flight dazaka samu dazai taho naija gobe be it PJ ko normal flight ne kadawo gida” tunda yafara school that’s tun lokacin dayake degree Abba baitaba demanding yadawo gida ba sai this time hakan yasa ahankali yace “okay Abba, but meke damun Mama”? Zayn yay tambayan ahankali dan yanason Mama she’s one humble woman da he admires alot dudda he’s not that close to her shi aduniyan nan ma only Ammin shi ne he’s close too. Ahankali Abba yace “she has blood cancer! Just few days takeda shi left inji Doctors, anyway just come home kayi few days Saika koma tunda baka fara finals dinka ba, good night son” “night Abba” yay maganan ahankali feeling down, yadade ahaka sanan yatashi.



Wuraren 8:00 na safe tabude idanunta ganinta adakin yayyinta saida abin yabata mamaki, murmushi tayi ta tashi zaune sanan ahankali ta sauko daga gadon lallai tagaji ko lace din jikinta bata chanza ba tai bacci, jakanta tadauka tawuce tafita daga dakin tana tafiya ahankali, flat dinsu tashiga babu kowa a falo sama tayi dakinta tashiga alwala tayi tai salla tukunna sanan tacire kayan wata doguwan rigan bacci ta tasaka sanan tafito direct hanyar dakin Mama tayi bude kofan tayi tace “Mama tun jiya nan ganki ba adakin su Ya Manaf na kwana” akan gado taga Mama ta jingina da hango ta sanya sweater tai fayau da ita da hulan sanyi akanta batasan mesa ba but gani tayi Mama tamata wani iri a idanu, karasowa tayi gaban gadon saikuma ta tsugunna takai hannunta tai tagumi tana kallon Mama, hararanta Mama tayi da kyar ta iya dagewa tabude bakinta tace “me haka”? Ahankali tana kallonta still tace “Mama wlh kin chanza, lips dinki are so dry, Mama wai bakida lafiyane kike boyemin kinyi wani iri eh sabida kinsan zan damu, bazan damu bafa Mama ai yanzu na girma saima na kula dake” dan shiru tayi tana kallon Maman dake kallonta tanaso tai magana amman azaban datakeji awuyanta yasa takasa, dasauri Khairy tace “zan damu kadan but zan kulada ke bakid lafiyane Mama” tai maganan idanunta na rau rau dan she’s really believing Mama bata da lafiya,  ganin haka yasa Mama tamikamata hannu sanan tahadiye duk wani azaban datakeji tace “lafiyana kalau kawai gani nayi my little Khairy has grown so sooo big, yarinya na tai girma she can even take care of her Mama come here” dasauri ta tashi hannun Mama takama sai kawai tasaki hannun tafada jikin Mama ta kankameta sosai ahankali tace “Mama wlh ina bala’in sonki, without you bansan ya zan kasance ba, Mama ko idan na kalli wasu yaran ko sai inga they are not lucky sabida bakene Maman su ba, Mama u are the best Mama I the world, u are the coolest Mom, the softest, the sweetest, bakida fada, gashi kina sonmu, we are ur everything Mama, Mama kinsan menene” girgiza mata kai Mamantayi, Khairy tace “all mothers are mothers, but not all mothers are like Mamana, cus Mamana tafi takowa dadi, Mama kinga duk girman dazanyi I will always be ur baby, Yar autan ki, kinga na gama school nafara aiki zan dinga miki komi, Mama nasan kinje makka but zan kaiki makka da kudina da aka biyani albashi wajen aiki” dariya Mama tahauyi sosai dayasa Khairy wani kalan murna, sanan tace “Mama yauma ni zan miki breakfast mezaki ci na dafa miki” ahankali tace “fate nakeso” wani tashi tayi tasauka daga gadon sanan tai juyi tace “then fate it is bari naje” tajuya dasauri tai hanyar kofa hartasa hannu zata bude kofan ahankali Mama tace “Ummulkhair” faduwa taji gabanta yayi hakan yasa ahankali tajuyo takalli Mama tace “naam” dakai Mama tamata alamu tazo dasauri taje gaban gadon, hannu biyu Mama tasa tai cupping face nata tana kallonta kafin ahankali takai goshinta saitin bakinta sanan ahankali ta manna mata kiss a goshin, murya chan kasa tace “I love you Ummulkhairy, Allah yamiki Albarka, Allah ya haskaka rayuwanki, Allah ya tsaremin ke” ahankali tana kallon fuskan Mama tace “Ameen Mama” takasa tashi, ganin kaman she’s trying to read something from Mamas face yasa Mama tace “Oya tashi kije kimin fate na yunwa nikeji Madam kokin fasane tunda kin tasani gaba kaman kin sami talavijin” da sauri ta tashi tana dariya tafice daga dakin.


Bana tagani agaban dakin murmushi tayi tace “good morning Bana natafi yima MaUma fate”.



2️⃣4️⃣



Free page

This book is 1k to join my group pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461



Chat me up directly by clicking on this link

wa.me/+2347012181461


Wuraren 11 tagama faten daya cika gidan da kamshi, fito da kulan falo tayi Mama tagani da Baba zaune afalo saisu Ya Manaf sunama Mama hira, tashi Maheer yayi yatayata suka fito da komi tsakar falo sanan suka zazzauna karban na Mama Baba yayi da kanshi yadinga bama Mama faten bashi kadai ba harsu Manaf sunyi mamakin yanda tasha faten dan tadena cin abinci, tass ta shanye sai dadi Khairy keji saida kowa yagama sanan ta kwashe komi itada Maheer sukakai kitchen tarema sukai wanke wanken tace “lallai yau mutanen mutuncin ka na nan kusa Maheer” hararanta yayi yawuce yafita daga kitchen din itama tabiyoshi tafito, Baba dake kallonsu yace “go and get ready Khairy malamin ki zaizo by 12” sama tawuce agurguje ta shirya tafito falo lokacin ba kowa Baba yakai Mama dakinshi, by 4 malamin yatafi su Manaf suka fita da ita basu dawo gidan ba sai around 10 tana zuwa lafiyan gado tabi.


Gabaki dayan gidan yau basuyi bacci ba sabida yanda jikin Mama yay tsanani, amai tadingayi na jini both tabaki da hanci, jikinta yay zafi sai maganganu take dabama sa ganewa, saida safen nan bacci ya dauketa.


6 ta tashi tana kallon agogo mamaki ma take ya akayi take lattin tashi late this days, wayanta dataga yay haske yamika hannu tadauka 2miss calls tagani na Aliyu saikuma message dayamata bude message din tayi. “I miss you” murmushi tayi ta ijiye wayan sanan ta tashi tawuce bayi wanka tayo tareda alwala Dan yau tanada morning lectures, tana fitowa tasa kaya tai salla sanan tabude kofa tafito su Ya Manaf tagani a falon sama kwakkwance kan kujera suna bacci, mamaki tayi amman ta tabe baki tai hanyar dakin Mama bude kofan tayi zaune taga Baba kan kujeran dakin yabude Al Qur’ani yana karantawa itakuma Mama na kwance kan gado tana bacci yarufa mata bargo, saida yakai ayar sanan ya kalleta tace “Good morning Baba” murmushi yamata yace “morning daughter, Mama is sleeping jiya dukanmu bamuyi bacci dawuri ba munata hira yayyinki na nan falo suna bacci suma” gyadamai kai tayi tace “eh nagansu” Gyadamata kai yayi yace “jeki breakfast yau Monday 8 kikeda lectures i want you to be serious kigama da good grade” gyadama Baba kai tayi sanan tajuya tafita tana kallon fuskan Mama dake bacci peacefully sanan tasauka falo ahankali, kitchen taje tea tadafa musu duka sanan ta soya chips zama tayi dinning zataci amman hakanan taji takasaci jikinta yamata wani irin sanyi kodan ita kadai ke yin breakfast dinne oho, tashi tayi tawuce sama tana kallon su Manaf da still ke bacci ta shiga dakinta dan shiryawa.



Shiryawa tayi tsaf cikin wani black abaya mai bala’in kyau tai rolling gyalen akanta ko kadan batai kwalliya ba but she looks kaman wata Somalian queen, jakanta tadauka sanan tafito, dakin Mama tabude takalli Baba dake karatu har lokacin tace “Baba natafi” saida ya idasa Ayan sanan yadago kudi yaciro yamika mata karba tayi tana murmushi tace “thank u Baba, kacema Mama natafi idan ta tashi bye” murmushi Baba yayi yace “to yarinyar Mama” maida kofan tayi tarufe yasauke ijiyan zuciya Noo yagaji Khairy deserve to know Maman ta is sick, he’s tired of hiding it from her, bari Maryam ta tashi zai gayamata is time sufadi ma Khairy, Khairy is grown up she can handle it.



Fitowa tsakar gida tayi tana tafiya ahankali hakanan jikinta kawai yamata sanyi yasaki tarasa mesa kawai she’s feeling sad and week ma yanzun nan, karasawa wajen motanta tayi Adamu na shiga itama tana shiga baya daidai sunajin horn mai gadinsu na budewa, motar Baffan ne ke shigowa gidan Hafiz ke tuki, sai motar Ammi biyeda su da driver ke parking sai kuma motan Mom, bude kofan motar tayi tafito tana murmushi da saurin ta tai wajen motan Baffa, daidai lokacin Baffa na bude baya yana fitowa yana mata murmushi yace “yan makarantan bokoko” dariya tadanyi tace “Baffa ina kwana, Ya Hafiz Baban Baby ina kwana, Laaaa Ya Hassan da Ya Hussain harda ku akazo yau” kafinma suyi magana Baba yace “wuce tafi school karki latti” yanuna mata motarta da Adamu yatada yana jiranta shiga motan tayi tana waving Mom dake saukowa daga motanta dan har yanzu motan Ammi bama abude ba kuma bamata iya ganin cikin banda driver shima ta glass din gaba taganshi dan motan tinted ne, jan motan Adamu yayi suka tafi nai gadi yamaida gate din gidan yarufe daidai lokacin Baba da Manaf suka fito.



Ahankali aka bude kofar motar Ammi, wani clean white kafane ya sauko dake sanye cikin wani hadadden sandals na Prada black, nails na kumban kafan are so fresh and white, gently yakarasa saukowa daga cikin motan yana yatsine fuska yana gyara bakin sun glasses na idanunshi na kampanin rayban, yana sanye cikin milk color yadi dayay dinkin jumper dashi daya bala’in amsan jikinshi, yanada tsayi dan wajen gabaki dayansu yafisu tsawo babu wanda baya ganin kanshi, yanada cika dakuma fadin kirji, kana ganinshi kaga Ammi kaman tai kaki ta tofar saisa yafi kannenshi kyau dansu Hafiz da Baffa suke kaman, yanada wani irin black very very dark saje dake kyalli kaman na bature, lips dinshi is so pinkish, gashin kanshi a kwance suna shinning, hannunshi ya daura agogo Rolex akai, ita kanta Ammi anytime ta kalleshi she feels proud da Allah yabata Zayn as her son, Zayn is definition na handsome guy, kyakkyawan namiji da babu macen data isa tamai yanga, ganin Baba yataho wajensu yasa ahankali yakai hannunshi yazare eye glasses na idanunshi yadan sunnar da kanshi kasa Baba nazuwa cikeda mamaki yakama hannun Baffa yace “d’ana Zayn nake gani haka” murmushi daga Baffa har Ammi da Mom sukayi, Baffa yace “da asuban nan yashigo gida” anatse Zayn yace “ina kwana Abba”? Hannu Baba yabashi ahankali yasa nashi hannun cikin na Baba, daidai sukaji muryan Maheer yana ihu. “Babaaa” Dawani irin sauri Baba yasaki hannun Zayn yay ciki Baffa da kowama suka bishi sama sukayi, dakin Mama Baba yashiga yatarar da Mu’az yarike Mama dake aman jini sosai tai lakur babu karfi kodaya ajikinta, wajenta Baba yayi yakamata daga hannun Mu’az yadau tissue yana share mata bakin ganin tadena aman, shigowa dakin Mom tayi takalli Baba tace “Alhaji bari mu chanza mata kaya” girgiza kai Mama tayi ahankali tana rike Baba gam batare datai magana ba, kallonta yayi sanan yakalli Mom yace “abarshi tukunna” karasowa gaban gadon Baffa yayi yaja kujera yazauna yana kallon Mama dabata iya bude idanunta da kyau yace “Maryam mutafi asibiti”? Girgizamai kai tayi ahankali, ajiyan zuciya yasauke yay shiru, shigowa ciki Ammi itama tayi tasami gefen gadon tazauna ahankali tana kallon Mama murya chan kasa tace “kina bukatan wani abu Maryam mezaki ci?” Girgizama Ammi kai tayi hakan yasa itama tai shiru, ahankali Baffa yajuya yakalli Zayn daya tsaya chak abakin kofa shima yana kallon Mama sanan Baffa yajuyo da kanshi ya kalli Mama yace “Maryam ga Zayn dakika ce nakira miki yazo” dan yunkurowa kadan tayi da duka karfinta, dasauri Baffa ganin haka yasa yace “Zayn come” karasowa gaban gadon Zayn yayi ahankali sanan gently ya tsugunnawa gaban gadon yana kallon Mama dake kallonshi kallon dakasan baa hayyacinta takeba yace “Mama I am here” hannunta daya tacire daga jikin Baba data rikeshi gam gam jin haka yasa Baba yatayata , kama hannun Zayn tayi hawaye yazubomata daga idanunta sanan kadan tabude bakinta dasauri Zayn da zuciyanshi ta katse yace “Mama I am here mekike so tell me” yakai kunenshi saitin bakinta, magana tashigamai a kunne wanda harta Baba dayake rikeda ita baiji abinda ta Fadima Zayn ba sanan takoma jikin Baba ta kankame shi, Maheer dataga yana kuka sosai mara sauti abakin kofan ta kalla hannu tamikamai ahankali yataso yazo kawai kankameta yayi yahau kuka sosai ahankali yace “Mama dan Allah kiwarke, Mama please karki mutu kibarmu” motsi sosai bakin Mama yafara hakan yasa Baba ya janye Maheer daga jikinta kankame Baba tasake yi takama hannunshi tarike gam gam kaman dats the only thing dake mata dadi sanan cikin wata kalan murya dabata fita da kyau dan hakoranta sun datse tace “Baffa, Ammi, Mom, dukanku yarana ina rokonku gafara ku yafeni idan nataba bata muku, idan Ummulkhair…..” wani kalan nishi tayi tana kuka sosai dabayama fitowa sosai tace “kuce mata nace tayakuri tayafema Maman ta, i hide everything sabida nasan idanda tasan banda lpy bazata dauki abin da kyau ba, Baban Manaf” tai maganan tana kankame Baba tace “ka kulamin da Khairy dan Allah, Baffa nabaku amanan Khairy da duka yarana, Khairy is fragile, and innocent please ku rikemin yarinyata amana ita nafiji araina, zanbar duniyan nan amman Khairy ce araina sabida ita kadaice diyata mace yayyinta maza ne” ajiyan zuciya Mama tasake saukewa sanan ahankali tace “idan narasu Khairy taki kwantar da hankalinta kabata Littafin nan danabaka ka ijiye mata Baban Manaf”  gyadamata kai Baba yayi ahankali hawaye na taruwa a idanunshi Baffa ya bubbugamai kafa alamun karyay kuka, ahankali Mama tace “Baffa kamishi aure dazaran na rasu banson yarana su rasa uwa, Manaf kurike Matar da mahaifinku zai aura kaman ni kada kubata ciwon kai” gyadamata kai Manaf yayi, Ammi kallon Mu’az yayi dake bakin kofa tayi ya tsugunna idanunshi sunyi jajir tace “zo wajen mahaifiyar ka Mu’az” mikewa yayi tsaye da kyar shigowa yayi zuwa wajen gadon kawai yadaura kanshi kan gado yadaura hannunshi kan nata dan that’s what Maheer da Manaf duk sukayi, yanda tazo tana nishi yasa Baffa ya gyadama Baba kai ahankali Baba yasoma karanto mata kalman shahada, saukar da kanshi kasa Zayn yayi, ahankali Mama ta amshi kalman shahadan karfe 12:03 daidai tacika da imani daidai lokacin Khairy ta tashi daga kan kujera sun gama lectures zasu fita jitayi kafafunta sunyi sanyi kawai tai baya zata fadi kaman tai paralyze Rabi dake bayanta ta tareta tace “ke Khairy are u okay” ? rike Rabi tayi tana taba kirjinta tace “gabana fadi yakeyi sosai kafana ba karfi” zaunar da ita Rabi tayi tace “kinyi breakfast kuwa”? Girgiza kai tayi hakan yasa Rabi da sauran kawayenta sukai dariya tace “yunwa ce muje kici abUinci”.




2️⃣5️⃣




Almost good 10min na silent ne yacika dakin, at this point Baba jiyayi kaman shima yamutum ne dan he could feel yanda hannayenta suka sassandare ajikinshi kasa koda motsi yayi hakan yasa Baffa yay taking over, daga Baba tsaye yayi, ahankali Baba yasauke kanshi kasa yana kallonta in disbelief, yadade ahaka sanan yakai hannunshi ya kulle mata idanu kafin yaja bargon yarufeta saikawai yazauna akasa dabas baimasan mema zaiyi ba dan he’s still in shock idan ya kalli su Manaf daduk suke kuka saiyaji zuciyanshi yakara tsinkewa, kafadanshi Baffa yakama ya matsa hakan yasa ya fuzar da iska kafin ahankali yasa hannunshi yakamo su Manaf daya bayan daya duka yarikesu ajikinshi kam kam, juyawa Baffa yayi yakalli Hafiz dashima yay mutuwan zaune hakama su Hassan ahankali yace “Hafiz jeka dauko Khairy daga makaranta” 

Tashi Hafiz yayi ahankali yafice daga dakin tafiya yake but jiyake kaman iska ke kadashi yana tuna all memories dinshi da Mama shikenan daba danta data haifa ba balle kuma yaranta yaya zasuji.


A famfon gaban flower ya tsaya saida ya wanke fuskanshi tass sanan yakarasa wajen mota shiga yayi yatada motan yana kallon yanda mai gadi ke budemai gate he just wish yanada karfin sanar da su, amman ina motarshi yaja yafita daga gidan zuwa school  din su Khairy, har gaban department dinsu yaje accounting yay parking yakai kusan good 20min zaune acikin motan baida courage na facing Khairy, da kyar ya iya gyara mood dinshi sanan yakashe motan yafito yamaida yarufe yana kallon ko’ina kafin ya shiga ciki, Khairy nabashi labarin how popular she is a school so yasan ganinta bazai tabamai wahala ba, wasu yammata guda uku dasuka sauko daga bene yatare yace “hello ladies dan Allah kunga Khairy” daya daga cikinsu ce tace “yanzun nan muka rabu da ita ga ajinsu chan wanchan floor din suna lectures” thanks yace musu sanan yawuce sama zuwa gaban class din excuse yay taking hakan yasa lecturer yafito dan yana ganinshi yasan Wanan baimai kala da dalibin makarantan nan ba, dawowa cikin ajin lecturer yayi yace “Ummulkhair” dasauri Khairy dake zaune ta kwantarda kanta kan table takalli lecturer tace “yes sir” waje yanuna mata yace “ana nemanki” tashi tayi ahankali tana daukan jakanta tafito tana tafiya kadan kadan dan sosai kafafunta basuda karfi ganin Ya Hafiz yasa tabude baki cikeda mamaki takarasa gabanshi da sauri tace “Ya Hafiz mekazo yi a school dinmu”? Hararan ko’ina yayi yay gaba abinshi tana binshi da sauri yace “me zanyi a school dinan naku Baffa yace nakawo ki” dasauri tace “Allah sarki Baffa yana ina tare kukazo kenan” “yana gida” yafadi kai tsaye batare daya juyo ya kalleta ba daidai suna karasa sauka kasa tana binshi abaya tace “Ya Hafiz wani laifin nayi ne wanan da dazu dasafen nan nabar Baffa agida mekuma nayi” juyowa yayi yakalleta daidai yabude mota yay murmushi yace “yarinya laifi dayawa” zare idanu tayi cikeda tsoro tace “hala saisa gabana keta faduwa wlh” tada motan yayi tashigo ganin duktai wani irin yasa yace “common babu abinda kikayi so relax” murmushi tayi dasauri tana sauke ijiyan zuciya but dudda haka she’s not just feeling ok hakan yasa tai shiru kaman ba itaba danda tacikashi da surutu shima shiru yamata baice mata komi ba ahaka har suka shigo layinsu, tundaga nesa take hango tulin mutane ata kofar gidansu maza na alwala hakan yasa ta gyara zama tace “Ya Hafiz maiya faru a anguwan mu”? Hango gate din gidansu abude awangale gakuma mutane yasa taji kawai gabanta nafaduwa ba kakkautawa, shiga cikin gidan sukayi daga baki baki Hafiz yay parking dan compund din yacika da mutane wasu tsaitsaye wasu zazzaune hango mai gadinsu da Adamu direbanta na kuka yasa kawai taji wani karfi yazo mata tawani bude kofan taduro juye juye tafara tana juwa juwa tanabin all mazan da idanunta kan sauka akansu tana kallo, kaman daga nesa taji dodon kunenta yaji wani magana. “Itace diyar Hajiyar data rasu” kafafunta da tun dazu sukai sanyi jitayi karfi yazo mata acikinsu kawai tahau gudu tai flat dinsu dataga kofar abude tashiga uwa an jefota tanabi kowa na falon da kallo matan anguwansu ne makotansu sunci mayafai some da charbi a hannu, stairs tayi dawani kalan mahaukacin gudu kawai neman mutum daya take dan gidansu she wants to know what’s happening idanunta ma sun rufe zuciyanta na bugawa batama ganin gabanta bum! Taji sunci karo da mutum da sauri takoma baya sanan tazaro idanunta tadaga kanta takalli wanda ke gabanta kaman yanda shima yake kallonta, batasan wayeshi ba but she could see kamannin shi da Ammi wani kayatyaccen kamshi nafitowa daga jikinshi, ahankali bakinta ke motsi numfashinta na neman gagaranta yi sabida yanda kirjinta ke bugawa ba kakkautawa ahankali tace “I……ina…….ina….”? Idanunta ne suka sauka kan gawar dataga an shimfide anan falon sama da aka suturta, sai yanzu ma talura da mutanen dake falon saman, Baffa, Baba, Ammi, Mom, Ya Manaf, Ya Mu’az, Maheer, Ya Hassan da Hussain Mama ce kadai batagani, still numfashinta na bala’in katsewa tabi idanun kowada kallo barinma Maheer dake kallonta yana wani irin kuka harda majina da she just think that answers her question, gently tadaga kafanta tana wani kalan kyafkyafta idanuwanta tana dambe da numfashinta dake kokarin daukewa tana kokarin tai taking just a step forward kawai tajita blank tai baya straight, wani irin tareta yayi dawani irin sauri Baffa yataso yana kallon Zayn daya tareta yace “Zayn kwantar da ita akasa she’s asmatic, Manaf get me her inhaler” dakinta Manaf yashiga yafito da sabon inhaler dago kanta Baffa yayi yadaura akan kafanshi yakai inhaler bakinta yana bubbuga kumatunta da kyar ta shaka tai wani irin nishi tadawo Baffa takalla tashi tayi zaune kaman bata hayyacinta tace “Baffa ina Mama na”? Ganin Baffa yay shiru yakasa bata amsa yasa takalli Ya Manaf tace “Ya Manaf ina mama ya akayi banganta ba” saukar da kanshi kasa yayi, ahankali Baffa yace “Ummulkhair” wani irin gyadamaikai tayi jikinta ko’ina na ta rirrike Baffa, all this while Baffa has been mai taurin zuciyan but for the first time yaji Khairy kaman itace zata karyashi, dakewa yayi yace “listen to me Khairy, kinaji” gyadamai kai tayi jikinta har kafafunta bari suke ta rirrike Baffa wani irin zufa na keto mata agoshi, anatse yace “dukanmu anan da mazajen dakika gani a waje ke kawai ake jira domin inaso kima mahaifiyarki addu’a, Ummulkhair inaso kizama yarinya mai Imani da kaddara mai kyau ko mara kyau sanan kisani cewa kullu nafsin za’ikatul maut, i want you to calm down don’t shout and don’t cry kinga kinada Asma karkije kima kanki illa, Ummulkhairy Allah yayiwa…..” Baffa yadanyi shiru ganin yanda tazaro ta kwalalo manyan idanunta waje kaman zasu fado kasa yanda  jikinta ke rawa zaka dauka ajikin injin markade take, daurewa Baffa yayi ahankali yace “Allah yayiwa mahaifiyar ki, Maman ki rasuwa Ummulkhairy”.




2️⃣6️⃣




Wani kalan shuuuuu taji kunenta nayi, itadai tasan taji koke koke, taji maganan Baba, su Ya Mu’az har maganan Ammi tasan taji sama sama kafin chan kuma taga tabude idanunta tana kallon kowa dake kanta, kala batace musu ba rarrafe ta shigayi har zuwa gaban gawan zama tayi dirshan tana kallon farin likafanin hannu tamika zatakai tabude saikuma tai shiru kafin ahankali tasa hannunta taja likafanin kasa fuskan Mama ya bayyana tai wani haske ga alamun murmushi tanayi wani kuri tayi da idanu kaman tahaukace sai kawai idanunta aukahau mata yana kaman Mama murmushi take mata dariya tayi sanan tajuyo ta kalli Maheer dake kuka tace “Ya Maheer dena kuka kaji zoka gani ga Mama nan namin murmushi, Mama bata mutu ba bacci take wlh gashinan zoka gani” babu zuciyan wanda bai tsinkeba adakin ahankali takai bakinta saitin fuskan murya chan kasa tace “Mama Mama, world best tashi kiji, Mama ai bacci kikeyi ko” tasake shiru, ganin ko motsi Mama batayi yasa tai tagumi tana kallonMama tace “zan jira harsai kin tashi kinmin magana” ahankali Baba yataho yazauna kusada ita dasauri tajuyo takalleshi kaman mai karantan wani abu akan fuskanshi, kafadan Khairy yakamo sanan ahankali yace “Ummulkhairy mamanki has been bathling with cancer for so long, blood cancer bataso kisani cus tasan abinda zakiyi kenan idan kikaji she has few days left, u will not take it likely, saisa taboyemiki all this while mamanki has been sick, seriously sick amman taki yarda kisani duk ciwon da mamanki keyi taganki she will pretend she is fine” hawaye masu bala’in dumi ne suka zubo mata dasauri tasa hannu tashare, ahankali Baba yace “karki sakawa Maman ki hakan nan Khairy inhar she’s your world best, kimata addu’a tasan tabar ya tagari aduniyan nan muje mukaita makwancinta, your mum is tired she need rest, go and pray for your mum” ahankali Khairy tasake matsawa kusada Mama she can’t believe Mama ne nan kasa addu’an tayi sai kuka ahankali tace “Mama dan Allah dagaske wai kin rasu?”, zuwa yayyinta sukayi kawai rungumeta ahankali Manaf yace “Mama tarasu Khairy pray for her” Ahankali tace “Mama Allah yajikanki Allah ya gafarta miki, Mama why did u leave me, shikenan bazan kara ganin ki ba, Mama maisa baki bari na rokeki kiyafemin ba, kullum ina cikin batamiki rai inta rashin ji, Mama Tayaya zan cigaba da rayuwa baki aciki Mama Innalillahi wa Innailaihi raji’un” tashi Baba yayi ahankali hakama Baffa dasu Ya Hassan da Hafiz dakuma Zayn zasu dauki Mama dan kaita waje salla, wani Zabura tayi zata tashi dasauri Manaf yariketa, Mom yabama ita tana wani kalan nishi hannu Mom tasa takarbi inhaler ta tace “Khairy Khairy” kaman zata haukace haka takeji da kyar ta iya kallon Mom tace “Mom na shiga uku, Mom Mama tarasu Innalillahi wa innailaihi raji’un, Mom wlh wlh ko….” kawai maganan yakakare takara suma, ruwa Mom tashafa mata a fuska tanamata addu’a, tafarfado ta sume tai having Asma attack haka tadingayi ahaka har akama Mama salla aka tafi da ita, Khairy bamatasan inda kanta yakeba tana jikin Mom, jikinta yay wani mahaukacin zafi dayasa Mom takalli Ammi dake zaune tanajan charbi tace “Hajiya kira Alhaji Dr yazo jikinta yay zafi dayawa, kuma suman nan datakeyi yay yawa” dan jim Ammi tayi sanan tadauki wayanta takira Baffa ta sanar dashi.



Bayan magrib Baba yashigo gidan tareda Baffa gaisawa yayi da matan dake falo dakemai gaisuwa sanan suka taho sama tundaga stairs yake kallon Khairy dake kwance akasa gatanan gatanan ne kawai baa cewa komi, tsugunnawa Baba yayi agabanta ahankali yadagota sharaf ta taso Mom yakalla yace “tayi salla kuwa”? Girgizamai kai Mom tayi, Baba zaiyi magana kawai tasaki wani sabon kuka mai bala’in tabarai dayasa kowa na dakin yazuba mata idanu tana taba zuciyanta kaman ta mutu takeji, kaman tai hauka takeji, kaman tadawo da hannun agogo baya takeji tama Mama duk abinda takeso batare datasa Mama fushi ba, duk su Baba magana suke mata amman harga Allah bata gane komi kunenta ma yadode, duk suna zaune ahaka tai kuka ta sume tadawo Dr yashigo gidan, allura kawai yamata aka samu tai bacci, Baba zai dagata Dr yace “ku kawo bargo kurufa mata, let her sleep anan” Baffa da kanshi yashiga dakinta pink bargonta da filonta yadauko yakawo Baba yakarba yasamata akarkashin kai sanan yarufa mata bargon yana kallonta yana kafin yasa hannunshi yacire rolling gyalen dake kanta ya ijiye gyalen agefe long kalaban ta suka bayyana duk akai shiru.



Hayowa saman sukayi duka yaran Hafiz na rike da jakanta daya dauko daga motanshi Dan dazu amotar tabari dakinta yabude ya shiga ya ijiye sanan yafito yasamu gefe daya yazauna afalon, suma su Hassan da Manaf suka zazzauna, ahankali Zayn ke hayowa stairs din da duk yay wani irin tsayawama waje yayi yin wata waya saisa bai shigo tareda kannen nashi ba,hayowa yayi kallo daya yama Khairy dake bacci akasa da aka lullube da pink bargo yadauke kai sanan yawuce gefen Ammin shi yazauna akasa tareda daura kanshi kan cinyanta hakan yasa tadaura hannunta ahankali tana shafa kanshi, kallon yaran Baffa yayi yace “kutashi kutafi gida mu muna nan” cikinsu duka babu wanda yay motsi, ahankali Ammi dake shafa kan Zayn tace “Son tashi katafi gida kahuta yau ka dawo daga tafiya” girgiza mata kai yayi ahankali yace “I don’t wanna go Ammi” kallon Hafiz Baba yayi yace “wuce katafi gidan ka Hafiz” girgiza kai yayi shima yace “Baba ai basu kadai bane kanwarta damai mata wanka duk suna nan” addu’a Baffa yayi dukansu sanan aka shafa, aka zauna turus duk wanda yaga su Baba da yaranshi saiya tausaya musu abinda kuma yahana yaran Baffa tafiya kenan Dan idan suka tafi gidan zai musu wani iri kai mutuwa batada dadi! Baba da Baffa sauka falon kasa sukayi sukuma yaran duk suna wajen kusan ahaka bacci ya kwashe kowa daga Ammi da Mom da duk suke kan kujera zuwa su Manaf dake bacci rabi rabi falon yarage only Zayn ne baiyi bacci ba dayake tattaba wayanshi maganan da Baffa da Baba keyi akasa yanaji.



Motsin da Khairy tayi cikin bacci yasa yajanye kanshi daga waya yazuba mata idanunshi kusan sai yanzu nema yake mata a very good kallo tunda yazo, hawaye yaga suna gangarowa daga gefen idanunta pink lips dinta na motsi sosai cikin bacci ta kankame pink bargon da aka lullubeta dashi tana maganganu da kana gani kasan mafarki take. “Mama Mama wai kin mutu? Ai baki mutu ba ko, bansan menama su Baffa dasukemin karya ba, Mama zansha madara, in dauka, Mama Mama Maaaaa….” Wani dogon ijiyan zuciya tasauke na kuka kalabanta daya na saukowa kan fuskanta, dauke kai yayi daga kallonta shi dabama danta ba mutuwan yajishi balle yaran data haifa, he can’t even imagine loosing Ammi God no please, Allah ya sassauta musu koma mesukeji a zukatan su.



Wuraren 4 daidai tabude idanunta daga kwance datake tana kallon saman dakin da kallo, the first thing daya fado brain nata is mutuwan Mama, ajiyan zuciya tasauke tana assuring kanta cewa mafarki ne tayi, juyoda kanta tayi tabi kowa na dakin da kallo, Hafiz nakan kujera yatakure yana bacci, Ya Manaf na zaune shima kan kujera yana bacci, Ya Mu’az ma haka Maheer ne kadai akasa yana bacci, sai Zayn da kanshi kekan kafan Ammi yana bacci shima kaman wani auta, Mom dake saitin inda take akan kujera tana bacci itama ta kalla ajiyan zuciya ta sauke zuciyanta na tsinkewa but she’s still in disbelief, bargon jikinta ya yaye ahankali sanan tamike tsaye da kyar cikinta namata wani irin ciwo na yunwa dan jiya all through babu abinda tasa abaka, tadade tsaye tana rikeda cikinta kafin ahankali tafara tafiya jelan kalaban kanta na lilo abayanta tai hanyar dakin Mama, ahankali tasa hannunta tabude kofan kaman a kunnen Zayn danshi baida nauyin bacci hakanan any movement kodan kara daza’ayi yana tashinshi da sauri yajuyo da kanshi yakalli kofan tana tsaye bakin kofa tarike handle na kofan da hannu tana kallon cikin dakin gashinta na lilo.



Ko’ina na dakin takebi da kallo idanunta namata gizo daga taga Mama tafito daga bayi tana mata murmushi saita ganta kan dadduma tana mata murmushi, saita ganta kan kujera tana zaune rikeda littafin zikirin ta saikuma chan taganta kan gado kwance tana mata murmushi, hannayenta duka biyun tadaga takai kan idanunta ta murza idanun da kyau sanan taciresu tasake kallon dakin amman babu kowa ciki dawani irin sauri ta shiga dakin tai bayi budewa tayi dasauri tace “Mama kina ina” ganin babu kowa abayin yasa tadawo dakin tana juye juye kalle kalle bakinta na rawa tace “Mama kina ina”? Gadon tayi ta yaye bargon kan gadon, jini jini datagani a zanin gadon wanda na aman jinin da Mama tadingayi ne yasa taji kafafunta sun kara sanyi kawai tayi kneeling awajen takifa kanta akan gado sai kuka kaman ta kwakulo zuciyanta tayar takeji kukanta sa duk wani wanda zaiji tanayi kuka yake, kowa na falon tunda tafara kiran Mama suka farka amman babu wanda ya iya shigowa yacemata wani abu abar Khairy tai kuka dan ita akama Wanan mutuwan.


Da kyar Manaf ya iya tashi yashigo dakin gaban gadon yazo kusada ita yadaura hannunshi akan bayanta murya chan kasa yace “Khairy stop crying and pray for Mama, kinga tun jiya baki magrib ba balle isha’i, muje dakinki kicire rigan nan shower kiyi salla and pray for Mama, Mama tariga tarasu……” wani kalan ihu tayi da saida gidan gabadaya ya amsa. “Mama bata rasu ba, Mama batada lafiya babu wanda yafadamin, mena muku? Ni yarinya ce dazaa boyemin uwata batada lafiya, nama Mama laifi dayawa bansami dama na roketa gafara ba, nabar Mama agida natafi school nadawo kucemin Mama tarasu, babu wanda yagayamin Mama batada lpy saidai kugayamin tarasu, Mama b…….a…” maganan yasoma gagaranta sabida mugun attack na Asma daya taso daukanta chak Manaf yayi yafito da ita daga dakin yana karban inhaler da Maheer kebashi, Mom tace “please ku kulle dakin nan tadena zuwa ciki” kwantar da ita kan gadonta yayi yasa mata inhaler cus nishi take kaman zata mutu da kyar ta shaka, Mom tashigo dakin takalli Manaf dake kanta tace “tafi Manaf” fita yawuce yayi daga dakin.





2️⃣7️⃣


Free page


Da taimakon Mom tai wanka ta chanza mata kaya zuwa wani simple atampa doguwan Riga sanan tasata tai salla itadai tasan tai salla amman bamatasan metakeyi cikin sallan ba kotana karatu dakyau kobatayi jikinta yay munannan zafi, kwanciya tayi kan dadduman Mom tazo dagata tayi tacire mata hijabi tace “kwanciya akasan ya isa haka nan kar sanyi ya shigeki zoki kwanta akan gado” Mom ta kwantar da ita kan gado ta kwanta lamo kan gado hawaye nabin idanunta suna sauka kan katifan, hannu Mom takai tana sharemata hawayen ahankali tace “Khairy nasan mekikeji aranki yanzu haka amman kisani kome yan uwanki sukayi da mahaifinki sabida mamanki sukai hakan, shi mara lafiya ana so ana cikamai wishes nashi, barinma mara lafiya kaman na mamanki, Mamanki ita ta haifeku duka idan she choose ke kadai zata boyemawa rashin lafiyanta believe me tanada reason nata maybe taga Kece mai weak zuciya u can not take it, and believe me yanzu idan nagayamiki Wanan abin dakike yi yanzu is not what she wants Khairy, be strong dan yanzu Kece maman su yayyinki, kinyi tunani what Baban ki is going through yanzu haka, matarshi dasuka tsufa tare bata kuma dawanne zaiji dake koko da rasuwan da akamai? Khairy ki kwantar da hankalinki kinji, bari na sauka kasa na hadomiki ko shayi ne kisha” Mom tashafa kanta kafin ta tashi daga kan gadon tawuce tafita daga dakin su Manaf zasu shiga tahanasu.



Ranan haka aka wuni Khairy gatanan gatanan ne, takasa cin komi kotaci amai straight, rasuwan Maman ta yabi gari bama asan ya kawayenta sukaji ba before you know it kawayenta suka cika gidan harda Besty duka dakinta aka kawosu kallonsu kawai take kaman ta haukace, babu wanda take amsa gaisuwan shi, duk wanda yazo gaisuwan bazaiyi kuka ba amman dazaran kaga Khairy saikai kuka kawayenta sunyi kuka sunyi kuka harsun gaji, Besty tunda tazo take rungume da Khairy da jikinta kaman wuta tana kuka da kyar ta iya tauna kosai guda da Besty tabata abaki ahaka dare nayi suka tafi.





Hakanan yaji ya bala’in damu cus yakira Khairy yanaganin miss calls din daya sunkai 20 maybe but all ba amsa same with text messages nashi ba reply, he don’t know why but kasa jurewa yayi tashi yayi daga office din nashi yadauki car keys dinshi yafito wajen police station din, motarshi yashiga yajata yafice daga police station din, he don’t even know why he’s driving to layinsu Khairy but yasan zuciyanshi keeps pulling him to go there dudda bawai shiga gidansu zaiyiba, ahaka har yazo layin, kofar gidansu yagani tsaitsaye da maza sanan gashi an bude gate an saka canopy a compound din ga tabarmai maza sun zazzauna, hakanan yaji kirjinshi yabuga dum! Waje yasamo yay parking motarshi yadade zaune sanan ahankali yafito ya tsaya jikin motanshi yana kallon jama’a dake shiga da fita gidan yakasa zuwa, yana tsaye awajen Ya Mu’az yafito tareda wasu friends nashi dasuka zomai gaisuwa, shiga motansu sukayi suka wuce daidai zai juya yakoma ciki idanunshi suka sauka kan Aliyu dake tsaye jikin motanshi yay folding hannunshi yana kallonshi tunani yafara inda yasanshi kafin daga baya kanshi yagayamai police man din ranan nan takowa yayi zuwa inda Aliyu yake tsaye yamikamai hannu dasauri Aliyu yabashi hannu yace “meke faruwane wucewa zanyi naga mutane gate abude shine nai parking, what happen?” Aliyu yasake tambayan Ya Mu’az heart nashi nabugawa, ahankali Ya Mu’az yace “Maman mu ce ta rasu, muje nakaika ciki kaman Baba gaisuwa” Ya Mu’az yay maganan yana gaba binshi abaya Aliyu yayi har zuwa cikin gidan har inda Baba yake kan tabarma tareda Baffa dawasu abokanen arziki Mu’az yakai Hydar, Baba nada gane mutane kallo daya yana Hydar yace “Aliyu” hannu yamikama Baba anatse yace “Baba yahakuri, Allah yajikanta Allah yamata rahama” ahankali Baba yace “Ameen Ameen Allah yayimaka Albarka” sanan yakalli Baffa yace “Wanan ne officer dana gayamaka ranan da Khairy tai shirmen nan yadawo da ita gida” dasauri Baffa yace “Allah sarki, yaro mai hankali angode Malam Aliyu, gashi Ummulkhair ba lafiya da an kirata kamata gaisuwa nasan zataji dadin hakan” gyadama Baffa kai yayi yakasa magana kirjinshi na bugawa dum dum, kafin da kyar ya iya tashi yamika musu hannu yace “bari nakoma wajen aiki” addu’a su Baffa sukamai sosai sanan yajuyo Ya Mu’az biyeda shi har waje zuwa wajen motanshi sanan Ya Mu’az yace “mungode Allah bada lada” murmushi yamai tareda gyadakai har Ya Mu’az yajuya zai wuce yaji yakasa hakura ahankali yace “Ya Ummulkhair take”? Juyowa Ya Mu’az yayi yakalleshi cikeda damuwa yace “not good at all” yay shiru yana kallon Hydar din dayaga ya tsaya yaki tafiya yana kallonshi kaman yana jiran yace wani abu ahankali Ya Mu’az yace “Mama had cancer all this while Khairy bata sani ba cus Mama tahana afadi mata, as it is now kaga yau uku this is the third day da abinci bai shiga bakin Khairy ba, she’s not handling the whole thing very well, she’s not doing okay, kuka suma asma attack duka yahadu mata kaman zatai hauka takeji, kasan she’s very very close to Mama, naji Baffan mu yana cewa yau zasu wuce da ita gidansu Dan gidan nan is not helping her at”. Gyadamai kai Aliyu yayi idanunshi sunyi ja yakasa magana juyawa Ya Mu’az yayi yCawuce ciki.





2️⃣8️⃣



Free page

Shiga motan Aliyu yayi dasauri sanan yatada motan wani irin jan motan yayi da bala’in gudu yayi tafiya mai bala’in tsayi sanan ya gangara gefen hanya ya kashe motan kafin yawani irin daki siterin motan yace “noooooo” he just wish zai iya shiga cikin gidan yaganta, wayanshi yaciro dasauri idanunshi sunyi ja baimasan mezaiyi ba text yashiga turamata.

“Rashin uwa is not something I wish for even my enemy, but muna plan dinmu ne Allah is the master of all planners. Ummulkhair nasan mekikeji, I know abinda zuciyanki kije because I was once there, just know this wherever Mama is she’s resting, tana cikin jannatul Firdaus, I want you to calm down, pray for Mama, cry but just little sabida nasan it hurts alot, babu wanda zai gane how it hurts sai ke, so cry little and pray lot, be strong for me Khairy, and kisani cewa I am here for you koda bana wajen presently but my love and my heart is there with you, I love you to the moon and back Ummulkhair, Allah ya yassaremiki wanan nauyin dakikeji aranki”

Turamata text din yayi yadade ahaka sanan yafuzar da iskan yatada motanshi yawuce.



Bayan sallan magrib Mom da kanta tashigo dakin, Khairy na kwance kan gado tadagota tana kallonta tawani irin rame tace “muje gidan mu, bayan kwana biyu saiki dawo nan bari nakawo miki hijabin ki” bin Mom kawai take da idanu tadauko mata hijabin tazo har gaban gadon tasake dagota danta kara kwanciya tasaka mata hijabin dagota tayi tasauko kasa baya tayi kaman zata fadi dasauri Mom tariketa tana kallon fuskanta idanun idanunta sukai suntum har lokacin jikinta da zafi ahankali tace “kiyakuri Khairy, kiyakuri” fita da ita Mom tayi tana binta luuu kaman wacce tasoma zarewa duk su Baba da kowa na tsakar gida wajajen mota Mom tafito da ita binta da kallo sukayi, dafa Baba Baffa yayi dayaga yana kallonta cikeda tausayi yace “don’t worry she will be fine” karasowa wajen Mom tayi tasata acikin mota bata musu duk yanda akai da ita, kowa shishiga mota yayi Baffa yana su Baba sallama sanan suka tafi da ita.



Suna kaiwa gidan parking suka yi, Zayn yafara saukowa daga motan Ammi side dinshi yawuce dan yagaji he needs rest, Mom kuma tafito da Khairy dahar lokacin take yanda take, Ahankali Baffa dake kallonsu yace “kitafi da ita side dinki tunda akwai Batool” gyadamai kai Mom tayi tawuce da ita itakuma Ammi tadaure fuska tawuce abinta Baffa yabi bayanta yana amsa wayan daya shigo phone nashi.



Kafin suma iso Batool tabude musu kofa tana kallon Khairy dan ita all this while bataje gidan rasuwan ba tana gida tana kulada kannensu, zata fashe da kuka ganin Khairy Mom ta ballamata harara hakan yasa tahadiye kukan taya Mom riketa sukayi sukai sama da ita zuwa dakinsu zaunar da ita kan gado sukayi kwanciya tayi sharaf Batool zatai magana Mom tace “ki barta jekimin tea yanzu zanzo nabata tasha yauma bataci komiba” Gyadamata kai Batool tayi tafito daga dakin tsayawa tayi nan bakin kofa tana kuka ahankali, bude kofa Mom tayi tafito ganinta yasa Mom taidan jim sanan tace “kinsan wahalan da akasha kafin Khairy tadaina kuka? Tana ganinki kina kuka yanzu zata fara” Mom tai maganan tana janta daga wajen kofa sukai stairs, cikeda da bala’in tausayi Batool tace “Mom kaman na Khairy mai surutu ba Mom kaman tazare Innalillahi, duniyan nan babu komi cikinta Mom, look at Khairy damuka sunan Ya Hafiz da ita muna wasa muna rawa, Mom I can’t stand seeing her this way” ahankali Mom tace “then u should support her as ur sister, show her love abinda take bukata kenan yanzu, sanan mudena nuna mata muna tausayinta, kijata ajiki u will help her tadawo daidai” gyadama Mom kai tayi, Mom tace “good yanzu jekiyo mata tea kizo kibata tasha, lemme go and shower” wucewa tayi zuwa kitchen da sauri.


Tea Batool tahado mata tadaura cup din a tray tadawo dakin nasu tana kwance sharaf agadon yanda suka barta, ijiye tea tayi tahayo gadon tadagota ta tashi zaune ahankalli murya chan kasa tace “Khairy zoki sha tea bakici komi ba” tsare Batool tayi da idanu da dazaran kaga yanda take kallon Batool kasan bata hayyacinta don ahankali tace “ina Mama”? Danne kukan datakeji tayi zatai mata magana taji kukan yatokare mata wuya hawaye yazubamata dasauri tashare daidai Mom tashigo hararanta Mom tayi tadauki tea tace “tashi kibani waje” da kyar Mom tasamu ta kurbi tea sau biyu sanan takara kwanciya dagata Mom tayi takaita bayi alwala tamata tasata a dadduma salla tajirata tayi Allah dai ya karba sanan tadagata, wani sabon kayan bacci na Batool Mom ta dauka tasamata bayan tacire mata atampan jikinta spaghetti hand ne dan kaman shimi yake iya guwiwanta ya tsaya mata pink color dan itama Batool nasan komi pink, dawowa tayi kaman wata Yar baby roba akayan looking damn cute, kaita Gado Mom tayi ta kwantar da ita tarufa mata bargo itama kaman abinda takeso kenan rufe idanu tayi dasauri, Mom tazauna abakin gadon tana tofamata addu’a bude kofa akayi Baffa ne yashigo yana sanye da jallabiya ganin Mom namata addu’a yasa ya tsaya yana kallonsu saida tagama sanan yace “tai salla”? “Eh tayi” “what about abinci” Baffa yatambaya anatse, ahankali Mom tace “tasha tea kadan ba laifi, shine na chanza mata kaya nakwantar da ita, karka damu she will be fine nan bada jimawa ba” murmushi Baffa yayi yana kallon Mom ahankali yace “thank you mace tagari” yakalli Batool dake bayanshi tai zuru zuru yace “dama kuka zaki dingayi kika dameni nadawo da ita nan kisami Yar uwa” dasauri ta girgiza kai tace “Bazan karaba Abba” murmushi yayi yashafa kanta yace “jeki kwanta” sanan yakalli Mom yace “jeki kwanta kihuta wife muje narakaki” murmushi tayi ta tashi, itakuma Batool taje gefen Khairy ta kwanta itama tashiga bargon Baffa yakashe musu wuta tareda jawo musu kofa sanan yaraka Mom zuwa dakinta kafin yafito yasauka kasa yakashe wutan falo sanan yaja kofan yawuce side din Ammi.





Wuraren karfe biyun dare tabude idanunta tass jin muryan Mama nakiran sunanta. “Ummulkhairy!” Hakan yasa tabi dakin da kallo ganin Mama tsaye jikin kofa tana sanye da Atampa mai kyau tai lullubi yasa ta yaye bargon data rufa dashi tawani tashi tsaye tai wajen kofan bakinta na motsi, gani tayi Mama tabi ta kofan tafice bude kofan tayi dasauri tafita ko’ina duhu but she could see Mama natafiya akan stairs dan fararen kayane ajikinta, hanyar stairs din tayi itama dasauri ganin Mama tai kofa tafice yasa itama tai kofan, hannu tasa tabude kofan tafice batare data rufe kofan ba, tsakar gidansu kaman rana sabida ko’ina hasken lantarki tashiga sauka daga stairs din gaban kofan tana mika hannu ganin Mama tamata nisa tai hanyar gate murya chan dake cikeda nuna alamun bacci tace “Mama jirani!” 




Zaune yake kan daya daga cikin wasu hadadun kujerun dayake nan barandan flat dinshi, irin hadadun kujerun basket dinan da ake sawa a garden, dagashi sai wani gajeren wando dayakaimai guiwa da farin singlet tass yadaura kafafunshi kan class table din wajen yana shan shishi, tunda yadawo naija saiyau yasamu yakeshan shisha, yama fito waje ne yanasha sabida kar dakinshi yakama kamshin gashi Abba nashigowa dakin dakannenshi duka, jin karan kofa an bude flat din Mom dan daga flat din Mom sainashi at this hour of night yasa yasaki pipe din shishan kasa dasauri yana mika hannu yana sauke shisha pot din daga kan table din at the same time yana kallon kofan yaga wanda zai fito daga dakin.



2️⃣9️⃣





Free page 

Ganin yarinyar nan da Mamanta tarasu dayaga antaho da ita gidansu dazu dazasu dawo dan he can’t even remember her name yasa yadan ware idanu yana binta da kallo yanda take sauka daga kan staircase din gaban flat din Mom, babu takalmi akafanta babu dan kwali akanta kalaban kanta na lilo atsakiyan bayanta, daga ita saidan rigan bacci pink mai hannun taliya daya tsaya a guiwanta, ganin yanda take tafiya one one as if she’s trying to hold something yasa yadanja karamin tsaki yace “God am I a baby sitter now” jin tace Mama kijirani tai hanyar gate yasa yadanja tsaki yatashi dasauri ganin tai hanyar gate, dawani irin sauri yasha gabanta batare dayace kalaba yay folding hannunshi a chest dan ihu yaso yamata but to his biggest suprise gani yayi gabaki daya idanunta are close is she sleeping walking or what? Yatambayi kanshi daidai ta iso gabanshi babu any tazara tsakanin shi da ita tsayawa yayi yana kallonta just to feed his curiosity yaga mezatayi, wani kalan heart melting murmushi tasaki daya bala’in lobar da dimples dinta all the 2 yabayyana set na white teeth dinta, pink lips dinta nawani kalan shinning kafin ahankali takai duka hannayenta biyun tadaura kan hannunshi daya rungume a kirji takama cikin muryanta kaman na baby tace “Mama kinjirani, Mama I miss u, karki kara tafiya ki barni kinji Mama” tai maganan tana warware hannunshi daya rungume a kirji tasaukar da hannun kasa sanan gently takara tako one more step ta shige cikin jikinshi tai wrapping two hands nata around his back tawani kalan kankameshi tana sauke ijiyan zuciya dahar cikin brain dinshi saida yaji ahankali tace “Mama bacci” tunda yake in his life what he just felt now baitaba jinshi ba, sandarewa yayi hannunshi sauke akasan batare daya iya komiba yanajin saukan ijiyan zuciyanta akirjinshi yana kallon tsakiyan kanta da yanda gashinta ke lilo sabida iskan dake kadawa da yanda heart dinta ke biting each beat yana jinshi anashi heart din, yakai kusan 2min ahaka she’s still holding him tight batare data kara magana ba, ahankali yadaga hannayenshi dayaji sunyi sanyi kaman basa functioning kuma yakai saitin hannunta abayanshi zai kwance yanda tadaure hannun abayanshi, kankame hannun tasakeyi saikuma yaji tasaki kuka dabaida kara ko kadan. “Baran sakeki ba Mama, ina sakinki cemin zasuyi kin mutu, Mama nakusan haukacewa da suka fadamin haka ni nasan baki mutu ba, ni ajikinki zanyi bacci anan dakinki zanyi bacci, I will not allow u to leave me ever again and go” yanda hawayenta kebin kirjinshi yasa yaji zuciyanshi ta tsinke shifa baicika tausayin mutane ba but for the first time jiyayi yarinyar nan tabashi tausayi sosai ahankali yakomar da hannunshi batare daya rabata dashi ba, yadan dade ahaka sanan gently yadan duka tareda ita yasa hannayenshi the two yadauketa ajikinshi kankameshi tasake yi gamgan tana kara gyara zaman kanta akirjinshi yana kallon fuskanta saida tagama sanan ahankali kaman yadauki Kwai yafara tafiya har zuwa flat din Mom, shiga ciki yayi daman kofan abude yake yay stairs da ita yana mamakin yanda batada nauyi kaman yadauki paper, dakin Batool dayagani a bude ya tabbatar mai daganan tafito, shiga cikin dakin yayi dudda ko’ina da duhu but he could see sabida hasken window dake nuno compound nasu gently ya tsugunnawa kaman yanda ake kwantar da baby haka ya kwantar da ita kan gadon zai zame hannunshi yaji ta chapke hannunshi da sauri tana sheshekan kuka kaman yanda jarirai kema mamansu takai hannunshi kirjinta ta kankame sosai kaman idan tasaki hannunshi something will happen to her, wani dauuuu yaji a brain dinshi kaman an watsa acid a alkaline environment, dan gabaki daya a boobs nata ta kankame hannun nashi, he could basically feel sign na her sleeping nippy, karya fizge hannun tahau kuka ne this is middle of night a ganshi adakin nan saisa yakeyi ahankali, gently ya tsugunna jikin gado, wani kalan zufa yaji yana ketomai shi kanshi baisan mesa ba this is not the first time yake feeling boobs na mace why is hers different, why so much effect, ahankali yakai dayan hannunshi yadaura akan fuskanta yana shafa kumatunta he don’t even know what to do samin kanshi yayi da hura mata iskan bakinshi a fuskan wani irin ijiyan zuciya ta sauke tasaki hannun nashi kadan bakaman yanda ta kankame hannun a kirjinta da farko ba, ganin haka yasa yacigaba da hura mata iskan yana shafa kumatun nata dayaji yamafi na jariri taushi sanan gently yashiga janye hannunshi kafin yay nasaran janye hannun duka sanan ya dauke hannun kan fuskan nata dawani irin sauri yatashi yafice yaja kofan nasu ahankali sanan yasauka kasa yafice waje abinshi.





Wuraren 6 tafarka daga bacci daga Mom har Baffa daya shigo dubasu da asuba saida sukaji dadi ganin yanda tai bacci sosai yau dan this last few days dudda ana mata allura bata tabakai war haka bata tashi ba 4 ta tashi ko 3 nadare ma.

Kalle kallen data shigayi yasa Mom data shigo dubata tace “Khairy ya akayi me kike nema? Kin tashi” Dasauri zuciyanta na bugawa fast fast tace “Mama ina take?” Shiru Mom tayi tana kallonta hakan yasa tafashe dawani irin kuka tace “wlh ba karya nake ba Mom naga Mama adakin nan takwana tareda ni I was even holding hannunta sabida idan kuka tashi kugani, kuma tace bazata kara tafiya tabarni ba” hannu Mom tasa tadafa cinyanta ahankali tace “Khairy idan aka rasu an rasu kenan mutum baya dawowa, sabida rasuwan Mama na ranki saisa kike mafarke mafarke, Mama tarasu, you had a dream about her, tashi kije ki dauro alwala kiyi salla” tashi tayi ahankali tana goge hawayen dasuke zubomata tai bayi, fitowa tayi daure da alwala tai salla, da kyar tasha kunun da Mom tabata shima kadan sanan Mom tabarta da su Batool da Zara’u daketa musu surutu Khairy na kallonsu kuri kaman tazare itakuma Mom ta sauka kasa.



Knocking akayi tareda shigowa dakin, Zayn ne yana sanye da kananun kaya yay kyau yana zuba wani uban kamshi, ganinshi yasa Mom tace “Zayn shigo mana zoka zauna” karasowa yayi cikin falon cikeda girmamawa yace “Mom zan tafi” dasauri Mom tace “harzaka koma” ahankali yace “eh something come up dole nakoma dama 1week naso nayi amman bazai yuba” murmushi Mum tayi tace “Allah sarki to Allah kiyaye hanya, Aida nasan yau zaka tafi dana maka su dambun nama wlh yanzu sai yaushe kenan” dan shiru yayi yana tunani sanan yace “let’s just say 2month intotal nagama komi” ahankali Mom tace “Alhamdulilah Alhamdulillah komi yay farko zaiyi karshe Allah bada sa’a Allah ya kiyaye hanya” Ameen yace yana tashi har waje Mom tarakashi Baffa dasu Hafiz suka daukeshi a mota har zuwa airpDort.



3️⃣0️⃣


This book is 1k pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank. Saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461.




LAST FREE PAGE 

Bayan 3 weeks!

Yau 3 weeks kenan chip chip da rasuwan Mama, an dage sosai da addu’a akanta she’s very very much better yanzu, tadena koke koken nan she’s doing everything dakanta saidai she hardly speak, kome aka cemata saidai ta gyadakai tariga ta yarda Mama tarasu and babu abinda zata iyayi dazai dawo da ita, har yau bata iyacin abinci at all, saidai kadan kadan kuma shima liquid, once in a while Besty nazuwa har gidan Baffa dubata dan su Ya Manaf nema suka kawota gidan tasani, sanan Baba yabata number shi yanzu ma haka ance gobe zata koma school danta kira Baba next week zasu fara first semester 400 level exam sauran ta one semester tagama school hakan yasa aketa shiryamata har sababbin dinki Baffa yamata hadadun gaske Mom ma haka, just to cheer her up amman ina bin kowa take da ido dakuma kalman godiya shikenan.




Yau tun safe Mom dakanta ta shigo dakin ganinta zaune kan dadduma yasa tace “laaaa yar nan Oya maza tashi ki shirya yau kinada lectures 8 kika zauna yanzu har 7 yi maza tashi ki shiga bayi” batai musu ba tashi tayi tai bayi wanka tayi tafito, gani tayi Mom tamata arranging kayan dazata saka akan gado, wasu Riga da skirt ne na atampa cikin sababbin da aka dinka mata orange color ne atampa yanada flowers yan kanana brown, sai brown gyale tahada mata jakan makarantan ta da book sai wayanta da tuntuni aka kawomata gidan bata taba tabawa ba shima Mom dukta saka mata, shiryawa tayi tsaf, Mom tashigo dakin dauke da tea da chips tana kallon yanda kayan suka mata kyau dudda tarame sosai takalli kitson kanta tace “satin nan zamu kwance kan nan ayi wani kitso Khairy” takarasa ta ijiye abincin akan carpet sanan tadauki dan kwalin kayan tamata dauri mai kyau kafin tadauki tea tabata, karba tayi da kyar ta iya shan dan kadan sanan ta ijiye, ita kanta Mom batama iya tursasata taci abinci tashi tayi tadauki jakan a hannu da gyalen ahankali tace “natafi” binta Mom tayi tace “dan Allah Khairy kiyi karatu da kyau kinga jarabawa zaku fara next week karki fadi” Baffa suka gani afalo shima wa’azi yamata sanan yakaita har mota saida tashiga sanan yama Adamu alamun yatada motan yatada suka tafi, titi kawai takebi da kallo, jitayi hawaye ya gangaro mata dasauri ta share, she use to kullum saitaga Mama take tafiya school, school sukakai Adamu yay parking ganin taki tashi yasa Adamu yace “tashi kije class Khairy” kukan datake rikewa taji yazo mata fashewa da kuka tayi sosai tasa gyalenta akan fuska tana kuka shiru Adamu yayi takai kusan 20min sanan ta share fuskan nata da gyalen idanunta sunyi jazur tabude kofa tafita tana tafiya kaman iska ya kadata tafadi tarame babu abinda yarage ajikinta sai nono da hips, su kadai ne basu rame ba but wuyanta duk kashi idanunta sun fada ciki sosai, ahankali take tafiya yan makaranta su natareta suna mata gaisuwa gyadamusu kai kawai take tana wucewa dasauri dan bataso taita kuka ta tarama kanta mutane ahaka hartakai aji da lecturer ma aciki, baa hanata shiga ba hakan yasa tashiga taje tasami chan baya karshe chan tazauna ko abu daya bata ganewa ahaka aka gama lectures din lecturer tafita by 10, basuda wani lectures kuma sai 2, zagayeta yan ajin sukayi ana mata gaisuwa gyadamusu kai take tana danne zuciyanta, ganin yanda takeyi yasa class governor dinsu yace “dan Allah kubar Khairy tahuta let’s go guys” fiffita daga ajin suka shiga yi, su Amal sukace “tashi muje cafe Khairy” ahankali tace “kuje ina zuwa” dan jim sukayi suna kallonta babu maison yatakurata hakan yasa duk suka tafi ajin aka watse ita kadai tarage aciki hakan yasa takifa kanta akan desk tahau kuka ita kanta she wants to stop the cry amman bata iyawa tadade ahaka ita kadai a class kaman aljana kanta akife akan table, kaman daga sama taji ance “Ummulkhair!!” Awani irin hankali take dago kanta daga table kafin tadaura jajayen rinannun idanunta kan Aliyu dake tsaye agaban ajin yana sanye da uniform na yan sanda yana kallonta, yarame shima idanunshi sunyi wani kala yana mata kallonda only heart dinshi zai iya sanar da mai kallon ke nufi, jitayi duniyan ya tsayamata chak duk wani bakin ciki emotions, tausayin kanta da sauransu sun taso mata sun tsayamata awuya, jikinta harwani rawa yake ganinshi dan she can’t believe shine, wani irin tashi tsaye tayi tana kallonshi kaman yanda yake kallonta kallon dayana mata zuciyanta nafassaramata dawani irin gudu gyalenta na faduwa akasa tai wajenshi kaman dama shitake jira batai wata wata ba kawai tawani kalan fada jikinshi sai kuka sosai as if she ne dama asalin wanda takeso tama kukan, ahankali ya lumshe idanunshi yana feeling kukan datake in every single bone of his flesh, hannayenshi yadaga gently yay wrapping nasu around her back kafin yakai bakinshi saitin kunenta murya chan kasa yace “I am here for you Pickle, I am here” sake kankameshi tayi sosai cikin kuka tace “Ya Aliyu Mama…..” murya chan kasa dake nuna he’s with her, he’s feeling what she’s feeling yace “I know Pickle” takai almost 3min tana kuka ajikinshi sanan ahankali yacirota daga jikinshi yana kallon yanda take kuka hannunta yakama zuwa first kujeran dake ajin zaunar da ita yayi sanan ya tsugunna agabanta still yana kallonta, jikinta ko’ina rawa yake na kuka, hannunshi yasa a aljihu yaciro clean handkerchief dinshi yakai kan fuskanta yafara share mata hawayen murya chan kasa yace “shiiiiiii” shiru tayi tana kallonshi still, tass yashare mata fuskan harda hancin sanan yamike tsaye yay inda take zaune a ajin da, tsugunnawa yayi yadauki gyalenta daya fadi a tsakar class din sanan yakarasa yadauki handbag dinta sanan yadawo har zuwa inda take a zaune, gyalenta ya yafa mata aka yasauka har kan kirjinta sanan yamika mata hannunshi yace “let’s go” kallon fuskanshi tayi kafin ahankali tasa soft hannunta cikin nashi yariketa gam sanan suka fito daga class din suna tafiya ahankali sai kallonsu ake amman ko ajikinshi har zuwa parking space, gaban motan yabude mata zama tayi tana kallonshi da jajayen idanunta sanan ya maida kofan yarufe kafin yazagayo yazauna wajen mazaunin direba yarufe motan yatada motan yafice daga school din da ita, sunyi tafiya mai nisa sannan taga ya tsaya gaban wani eatry ya shiga batasan meya siyoba yadai bude bayan motan ya ijiye komi sanan yadawo yatada motan, wani waje yakaita ita kanta duk zamanta a Abuja batasan wajen ba, duwatsu ne masu kyau ga kamshin ruwa awajen da alamun akwai water fall ciki, parking yayi sanan yakalleta yace “I am coming” fitowa yayi yabude baya yadauki ledan daya siyo musu dawani babban dadduman dayake dashi mai taushi sanan yashiga wajen baiwani dade ba yadawo, bude inda take yayi yasake saka hannu yadauki jakanta sanan yamika mata hannu ahankali tasaka nata ciki, saukowa tayi yamaida motan yarufe sanan suka shiga wajen, cikin dutse ne kaman cave sanan ga ruwa atsakiyan wajen yana gangarowa daga dutse babu kowa wajen, wajen is so serene and peaceful bakajin karan komi saina tauntaye dana karan ruwan dakuma kamshin ruwan dutse dakakeji.


Zaunar da ita yayi kan dadduman sanan shima yazauna yana facing nata, ledan yabude yaciro take away na biryani rice da rosted lamb sai ruwa mai sanyi daya siya yabude, ahankali yasa spoon din aciki sanan yadebo abincin a spoon yakai bakinta yana kallonta jitayi zuciyanta yawani tsinke wani sabon kuka yazo mata ahankali tashiga reramai kukan, jaaa idanunshi yayi sanan gently ya girgiza mata kai bude baki tayi yasamata abincin taci saiyau tasan ashe tanajin yunwa, kadan tarage abincin all through harta koshi kuka take, yanabata abaki tanaci tanamai kuka sanan yadauki ruwa yabata shima sha tayi sanan ya ijiye.

Ijiye komi gefe yayi sanan ya matso kusada ita ganin taki daina kukan cikin muryan lallashi da murya dake nuna asalin so da tsantsan so yace “I know! and it’s okay I am here for you okay” gyadamai kai tayi tana sauke ijiyan zuciya, hannunshi yakai yakamo hannunta ahankali yadaura hannun nata kan kirjinshi yana kallon idanunta yace “can you feel yanda zuciyana ke bugawa sabida yasan kina cikin damuwa?” Gyadamai kai tayi ahankali murya chan kasa yace “I came to your house tun ranan ban sake samin kwanciyan hankali ba because I know my Pickle is not fine, I lost sleep, I lost peace, bana iya komi sabida ke, kinason zuciyata tabuga because of you ne”? Girgizamai kai tayi ahankali tanajin maganganunshi har a bargon kashinta, murya chan kasa yace “I lost my Mom when I was 25yrs, I know what u are going through Khairy, but if anything yasameki bazan iya rayuwa ba I will die, I love you alot, Ummulkhair I Love You” wani sanyi taji ya ziyarci zuciyanta each magana dayake gayamata zuciyanshi datakejin bugunshi nakara tantance mata cewa gaskiya yake fadi, ahankali yace “when I lost my mum I was depressed but as time goes on nazo ma fahimci this is not abinda mamana keso, she wants me happy, tanaso na cigaba da rayuwana, tanaso nai fulfilling dreams dina and above all she wants me happy and praying for her, Pickle abinda kikeyi yanzu is that abinda Mama kiso”? Girgizamai kai dasauri tayi alamun aa ahankali yace “to mesa kike hakan”? Lips dinta na rawa kuka na neman kufce mata tace “because banajin magana and nasa Mama fushi dayawa, halama saisa taki fadamin she had blood cancer” tafashe da kuka tana kallonshi girgiza mata kai yayi yace “Mama taki gayamiki she’s ill ne because you are her youngest daughter Khairy u can’t handle it, and Mama wants wats best for you, that’s is the reason, trust me pickle you are not stubborn, ke y’a ce dakowani parent will wish to have, I know Mama is so proud of you, ta haifi selfless and fearless yarinya that can stand for her self a ko’ina, karki kara tunanin Mama is angry with u iyaye basa iya fushi da yaransu, and Wanan kukan dakike da rashin cin abinci shizaisa Mama tai fushi dake, cus instead of kinata addu’a kina using time din to cry and not eating zai baki wani sabon ciwo u want to be sick” girgizamai kai tayi dasauri ahankali yakai hannunshi yakama dayan hannunta yace “promise me daga yau kin chanza, u will stop all this, take care of yayyinki and your Dad, do you have any idea yanda sukeji ga rashin Mama gaki” sake girgizamai kai tayi yace “promise me you will change daga yau, u will always pray for Mama, study well and pass exam dazaku fara next week, did u promise” gyadamai kai tayi ahankali tace “Uhm I promise” murmushi yayi he feels kaman yarungumeta yasata ajikinshi and just stay like that forever” ahankali yace “smile for me i finds it healing is my therapy, smile” dan murmushi kadan tayi ita kanta tamanta the last time datai murmushi.



To jama’a anan nakawo karshen free pages zan barku da tambayan nan ALIYU NE KO ZAYN NE???

Dan samin amsoshin nan kucigaba da bina awanan Littafin mai suna ALKAWARIN ZUCIYA!

Dan son cigaba da karanta Wanan littafin zaka iya turo 1k ta 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting.


Dan girman Allah badan niba kubiya ku shiga group ku karanta. Support me🥰


You can chat me up directly by clicking on this link

wa.me/+2347012181461


Thank you

M Shakur🥰



3️⃣1️⃣



WARAKA TEMPLE

wa.me/+2347042419516

Waraka temple gidan maganin kowacce irin cuta da izinin Allah 

Karin niima da dadi 

Karin dandanonki da duminki

Matsewarki ki dawo yar Sha shida

Gyaran nono 

Sa megida sambatu

Sa kyauta 

Maganin Sanyi 

Da sauran magungunan damuwar da ke addabar mata zaku samu a waraka temple ku tuntubemu a no waya ko Instagram.




Murmushi yamata sanan yamika hannunshi yadauki jakanta wayanta yaciro yakunna yace “this phone should always be on” gyadamai kai tayi ahankali tana kallonshi Ya Aliyu is just….bamatasan taya zatai describing nashi ba, he’s just everything datake so, he’s so cool, calm, religious, selfless, caring, loving and above all very handsome. “will you marry me?” Kaman daga sama taji yajefo mata tambayan dan tayi nisa a tunanin shi while looking at him, ware manyan idanunta tayi da sun soma washewa, ijiye wayan nata yayi akan cinyanshi dayagama saita mata dan komi na ciki ya hargitse sanan yadaura mata mayun idanunshi akan nata, ahankali yace “zaki taimaki Aliyu Hydar ki aureshi yazama mijinki?” Batasan mesaba but wani kalan bala’in kunya ne taji ya lullubeta dasauri takai hannayenta duka biyun tarufe fuskanta dashi tana murmushi sosai kaman ba Khairy ba, dan murmushi yayi ganin yanda tambayan shi yabata kunya, matso da fuskanshi saitin fuskanta data rufe da hannayen ta yayi kaman mai whispering yace “I want to go and seeaBaba fa” girgizamai kai tayi tareda makemai kafada batare data bude fuskanta ba hakan yasa yace “what”? Awani irin shagwabe kaman Yar baby one year tace “ni karkaje wajen Baba yanzu” dasauri yana kallon long yatsun hannunta masu bala’in kyau da fararen kumbunanta kal kal yace “sai yaushe” ahankali kaman bataso tafadi maganan tace “sai nagama second semester exam dina nagama school” dan shiru yayi kaman mai calculating dan yamai nisa, dan yatsine fuska yayi yace “to but will you marry Aliyu”? Shiru tayi kaman bazatai bashi amsaba yana kallonta sai chan yaga ta gyadamai kai wani irin murmushi yayi ya dunkule hannu yadaki iska yace “yessssss!” Juyamai baya tayi akunyace tana daukan jakanta ahankali tace “mutafi inada class by 2” dan murmushi yayi ganin kunyanshi takeji dan tace zata aureshi, yace “ok” tashi tayi ahankali tafice daga wajen murmushi yasakeyi ya kwashe dadduman dasauran abubuwa yafito, discarding nasu yayi sanan yazo yasameta tsaye jikin motan tana kallon wasu tsintsaye dake wasa jikin bishiyan wajen, ga gidajensu birjik a wajen da alamu kiwonsu ake awajen, abayanta ya tsaya yana kallon tsuntsayen shima murya chan kasa yace “u like them”? Gyadamai kai tayi da sauri batare data cire idanunta daga kansu ba, wani mutum dakaman shine mai gadin wajen yakira da hannu ko kadan bamata lura ba dan hankalinta nakan tsuntsayen datake kallo, kawai gani tayi mutum yafito dawani basket cage na gidan tsuntsu yazo wajen bishiyan cikin sauki taga yakamo guda biyu yana kokarin sawa ciki,  dasauri tace “Ya Aliyu meyake yi wanchan mutumin”? Ahankali yana tsaye kusada ita yace “I don’t know let’s see” saka tsuntsayen yayi a basket din sanan yataho dasu gabansu da sauri yamikama Aliyu yace “officer gashinan macen da namijin ne kaman yanda kace” hannu yasa ya karba sanan ya ijiye akan motan Khairy tabishi da kallo, hannu yatura a aljihu yaciro wallet kudi dayawa yaciro yamikama guy din godiya yamai sanan yawuce, hakan yasa yamaida wallet din aljihunshi kafin ahankali yadauki cage din yajuyo yana kallon Khairy dake kallonshi yamika mata yace “take” wani cute smile tasaki sanan tasa hannu takarba tana kallonsu tana murmushi sanan tadago kanta takalli Aliyun dake kallonta tace “they are so cute, they’re so tiny and adorable” matsowa kusada ita yayi yana kallonsu shima acikin cage din sanan ahankali yace “mace da namiji ne, this is Aliyu Hydar” yanuna mata namijin, sanan yanuna mata macen da yatsa yace “and that’s the lady, Miss Ummulkhair” wani kalan murmushi tayi she’s so happy bata taba zatan dan tace tanaso zai sayamata ba harma guda biyu, fuskanta yakalla yanda take murmushi tana kallonsu, ahankali yace “are you happy Pickle”? Juyoda fuskanta tayi takalleshi, gyadamai kai tayi ahankali tace “I am very happy” “mutafi to”? Gyadamai kai tayi da sauri tace “a ina zan ijiye idan zan shiga class”? kofar motan yabude mata shiga tayi dan shiru yayi kaman mai tunani sanan yace “I will keep them for you harki gama class, how does that sound” “perfect” tafadi tana girgiza case din dake jikinta dan suyi attempting flying wani dadi taji tace “yayyyy they’re flying, Ya Aliyu kalli” kallonsu yayi yana mamakin yanda abin kesata murna, maida kofan yayi yarufe yanajin wani kalan sanyi aranshi, duk wani damuwa da kunci dayakeji yatafi ganin yanda take murmushi looking happy.



Shigowa motan yayi yatada yaja motan kusan every minute and second saiya juyo ya kalleta yanda take wasa da tsuntsayen sosai, yana bala’in son Khairy shi kanshi baisan adadin son dayake mata ba, ahaka har sukakai school dinta around 15min after 1 na rana, parking yayi hakan yasa takalleshi daidai shima ya kalleta, dan sunnar dakanta tayi akunyace yace “2 zaku shiga class ko?” Gyadamai kai tayi, what time zaki gama lectures yau, ahankali tace “5” dan ajiyan zuciya yasauke yace “yanzu jeki salla a mosque kafin ku shiga class, I will come back later nakawo miki birds dinki kitafi dasu gida, what do u want me to get for u when coming back?” Girgizamai kai tayi tace “babu komi” jakanta tadauka sanan tadan saci kallonshi ganin kallonta yake kaman yauya fara ganinta yasa tajuya da sauri tareda bude kofan tafita tafara tafiya dan murmushi yayi yakafeta da ido yana kirga step dinta waiting for something, kaman taji kiran da zuciyanshi kemata juyowa tayi dudda motan is tinted but samin kanta tayi damai waving hannu dan tasan yana kallonta sanan tajuya da sauri tawuce feeling so happy da shi can not even deny, bata taba sanin she can feel this happy ba bayan rasuwan Mama gashi she’s feeling it.”



Kaman yanda yace tayi hakan tayi masallacin su tawuce tai salla abinta sanan tazauna ganin 2 batai ba, jin tunanin Mama yazomata rai yasa tadaga hannu sama tamata addu’a sosai ta shafa sanan tafito ganin 2 saura, class dinsu tawuce su kansu Amal mamaki sukayi ganin tazo kujeran dasuke tazauna harma tana karban note dinsu tana dubawa kafin lecturer yashigo wani kalan dadi duk sukaji, shigowa lecturer yayi yafara musu lectures and Alhamdulillah tana gane komi. Wuraren 3 suna zaune a ajin taji wayanta na vibrating hannu tasa ajakanta taciro ganin message ne daga Aliyu Hydar yasa dasauri tabude.

“Are u moody or teary? Concentrate on lectures okay, by the way this birds dinan naki are naughty, sai kuka sukemin sun tsaneni obviously sunsan I am not their owner”

Bakaramin dariya tayiba dataga text dinshi reply nashi tayi.

“I am happy thanks to Ya Aliyu Hydar, tell my birds not to cry, Mommy takusa gama lectures bye”

Saida tai sending message din sanan tafarabin messages din dayake turamata tun bayan rasuwan Mama tana karantawa one after the other tana murmushi, Amal dake kusada ita ta mintsileta tace “Khairy wai waye Wanan new boyfriend din naki” tai maganan tana leken abinda take dawaya dasauri tarufe wayan tamaida jaka tareda murguda mata baki ta maida hankalinta kan lectures din da akeyi.



3️⃣2️⃣





Five daidai suka gama lectures, fitowa tayi suka jero tareda su Amal, kafin su wuce itakuma tai parking space data hango Aliyu tsaye jikin motanshi wanan karan ba kayan yan sanda ne ajikinshi ba, Jean da shirt yasaka, wani black jean dawata dark blue shirt dasukamai bala’in kyau suka haska shi, hannun rigan yakama murdadden muscles nashi sosai, rigan ma kaman yamai kadan sabida yanda yakama kirjinshi fum fum ya kara bayyano da cikan kirjinshi, sajenshi ya kwanta yay lub lub hakama gashin fulanin kanshi sai kyalli yake, lips dinshi yayi so sooo pink kaman ya shafa man baki pink waya nakan kunneshi yana magana, gani tayi kaman ma kayan yan sandan nan ragemai kyau sukeyi yanda jean da rigan nan suka karbeshi zaka dauka wani American celebrity ne ko wani hip hop rapper hakanan, gashi da tsayi, ko kadan bai lurada itaba jidayayi ajikinshi ana kallonshi yasa yajuyo da kanshi, da sauri tadauke kanta kaman bashi take kallo ba, dan murmushi yayi sanan yacigaba da wayan dayake harta karaso inda yake, zare wayan yayi daga kunenshi yana kallonta, dan lunshe idanu tayi sabida wani irin classic kamshi dayakeyi ahankali tabude su, murya chan kasa tace “ina yini” dan murmushi yayi jin yanda tagaidashi bai amsa ba yabude gaban motan yaciro tsuntsayenta dakuma wani paper bag da popsicles ke ciki duka yasamata a hannu, kallon paper bag din tayi ganin sunanshi yasa takalleshi ahankali tace “thank u” murmushi yamata yamaida kofan motan yarufe sanan yace “direban ki yazo?” Gyadamai kai tayi hakan yasa ya karbe cage din yace “muje nakai miki” jerawa sukayi gabaki daya duka tsawonta a shoulder shi ta tsaya, har wajen motan yakaita gaidashi Adamu yayi ya amsa sanan yabude bayan motan ya ijiye case din sanan yakalleta yanda take tsaye gefenshi yace “get in” shiga tayi ahankali tazauna sanan yamaida kofan yarufe yamata waving hannunshi, murmushi tayi itama tai waving nashi back sanan Adamu yaja motan suka wuce, komawa motanshi yayi tashiga ciki yazauna kafin yaja motan shima hankalinshi ya na bala’in kwantawa.




Gidan Baffa suka wuce, parking Adamu yayi tafito rikeda case nata na tsuntsayen dakuma jakan popsicles dinta tai side din Mom, da sallama tashiga ganin Mom azaune tana koyama Zara’u homework yasa tai wajensu tace “Mom nayi tsuntsu” wani ihu Zara’u tayi tana murna tace “Ya Khairy kibani daya” makemata kafada Khairy tayi tace “zandai aramiki amman bani baki” ihu tayi cikeda murna Khairy tai murmushi wani kalan dadi Mom taji ganinta haka dayasa tama manta ta tambayeta waya bata, cikeda farinciki tace “Ya school din?” Ahankali tace “lpy lau Mom” Popsicles din taciro tabama Zara’u daya tace “ina Batool Zara’u” tana bacci, mikama Mom daya tayi, Mom tace “waaa rabani da kayan zakin nan naku Khairy” dariya tayi takai sauran fridge tarike daya tanasha dayan kuma na Batool tai sama Mom tabita da kallo cikeda mamaki dakuma farin ciki at the same time.


Duka ta dakama Batool dake bacci dasauri tabude ido tana turo baki ganin Khairy ne yasa tama manta dakomi ta rungume ta turata Khairy tayi tace “dalla gashi” dagudu ta karba suka shiga sha tare Batool namata hira, saida ta shanye sanan ta tashi tashiga bayi wanka tayi tafito daure da alwalan magrib salla tayi sanan itada Batool suka tafi dakin Mom.

Adakin Mom Baffa yazo yagansu dukansu sun taru suna koyama Zara’u homework, wani kalan dadi da Baffa yaji zaka dauka kyauta akamai fitowa Mom tayi tasameshi a falon sama wani kalan rungume Mom yayi ahankali yace “thank you for taking Khairy like your own wife” dan hararan Baffa tayi kafin ahankali tace “d’a nakowa ne, karka kara godemin Khairy y’ata ce, Ya Alhaji ya yarda yabika neman Auren kuwa”? Gyadamata kai yayi ahankali yace “amman da kyar, yanzu dai anyi magana nan da sati daya za’a daura auren, for now zan rike Khairy anan duk randa taji tanason zuwa gidan su she can go amman dai tana nan koya kika gani” gyadamai kai tayi tace “hakan yafi, kaga at least nan ga Batool ga Zara’u  suna sata surutu, kaga takoma chan ita kadai ba kanne sai Yayyi kuma fita aiki suke abinsu” Gyadamata kai Baffa yayi cikeda gamsuwa da maganan ta yace “bari naje na kwanta nagaji” ahankali tace “mu kwana lpy” kashema ta idanu yayi yace “ashirya min da kyau gobe ina nan” dan dariya tayi tawuce ciki batare daya tankashi ba tunda yan tsokanan nashi ne suka tashi”.




Har wuraren 11 nadare takasa bacci tuni Batool tai bacci amman ita sai juye juye take tarike wayanta gam a hannunta babu abinda kemata dadi muryanshi kawai takeso taji ko zuciyanta zai mata dadi, tana haka wuraren 11:30 wayanta yahau vibrating, har wani dan gajeren ijiyan zuciya tasauke sanan tadauki wayan takai kunnenta dawata kalan murya da ita kanta batasan tanadashi ba tace “Ya Aliyu ina yini” wani dan kalan murmushi yayi da saida taji sautin murmushin tawaya dataji yasa hankalinta yawani kwanta, ahankali yace “how you?” Murya chan ciki ashagwabe tace “fine” dan shiru yayi sai chan yace “I am sorry nan kirada wuri ba, ina tareda Abba ne, most time around 11 yake barina, sorry for keeping waiting” gyadamai kai tayi ahankali tana turo baki. “Kinci abinci”? “Eh” ta amsashi kadan, “me kikaci” ahankali tace “tuwon shinkafa Mom tayi da miyan taushe” dan murmushi yayi yace “iyye kinci sosai” girgizamai kai tayi tace “oh’oh banci ba” murya chan kasa yace “why Pickle” ahankali tace “miyan was peprish, banson yaji yanasa cikina yay ciwo” cikeda kulawa yace “ohh no sorry about that mekika zo kikaci yanzu” dan murmushi tayi da saida yaji sautin murmushin tace “popsicles dina nakarasa shanye wa” dan zaro idanu yayi yace “duka kika shanye” dasauri ta girgizakai tace “naba Batool da Zara’u, nabawa Mom itama taki karba wai batacin zaki” ahankali yace “who is Batool and Zara’u” anatse tace “yaran Mom ne, Batool ne babba shes 22, itama tana 400level a baze sai Zara’u tana primary one, sai Ammi itakuma ta haifi su Ya Zayn shine Babba, sai Ya Hafiz, sai twin Ya Hassan da Hussain” ahankali yace “Uhm Masha Allah” dan shiru yayi hakan yasa ahankali tace “kaci abinci”? Dan shiru yayi saikuma yay murmushi dan ya bala’in jin dadin tambayan yace “yes, I just had tea yanzun nan tareda Abba, dazu da yamma naci tuwo awajen Gwaggo” wani dan murmushi tayi tace “Gwaggo, u have a grandmom”? Yanda tai tambayan he could feel excitement a voice nata that just tell him batada grandma nata are late.

Ahankali yace “Gwaggo is my grandma ta haifi yara goma amman Abba kadai ya rayu, she’s Fulani daga adamawa, she’s very old though sai masifa da kaima Abba gulma….” Dan dariya kadan dayaji tayi yasa yaji wani dadi hakan yasa tacigaba, yace “she’s very old bata iya tafiya dakanta yakai 10steps haka saida wheelchair nata, but dudda haka garin kaima Abba gulma ranan taje tafadi yanzu ko 5 step bata iyayi dakanta” wanan karan dariya tayi sosai bata taba sani Aliyu ya iya nada labari hakaba. Ahankali yace “why are you laughing I am being serious Gwaggo can gossip” wani irin rushewa da dariya tayi ashagwabe tace “stoppp Ya Aliyu u are so mean” dan murmushi yayi yace “are u supporting that old woman now”? Girgizamai kai tayi tana taushe bakinta, murya chan kasa yace “do you wanna meat her some day”? Gyadamai kai tayi ahankali tace “yes” anatse yace “ok u will meet her some day, zakiga abinda nake fadi, I have sisters also but duk ba anan naija suke aure ba, so they hardly visit sai salla salla, then my little sister Meenah, she’s your age mate kinaso kiganta?” Gyadamai kai tayi tace “eh” ahankali yace “you will I promise, do u have any lectures tomorrow”? Girgizakai tayi tace “a’a gobe Mom tace zanje saloon nai kitso” dan murmushi yayi yace “ayi mai kyau, idan kin tashi da asauba after observing subhi makesure to read Qur’an and ur books afterwards okay” murya chan kasa tace “okay” agogo ya kalla ganin 1 nadare yasa yace “u need to sleep okay” gyadamai kai tayi ahankali tace “saida safe” murya chan kasa dan daso samune suyita magana yace “Allah bamu alkhairi, I love you Ummulkhair!” Dip taji ya katse wayan, wayan tabi da kallo kafin tarungume wayan kam kam ahaka bacci yay awon gaba da ita.




3️⃣3️⃣


This book is 1k pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank

Chat me up directly by clicking on this link 

wa.me/+2347012181461



Yau bayan sun tashi sunyi salla  tama Mama addu’a sosai hana Batool dake kokarin komawa bacci tayi taja hannunta suka shiga kitchen, lafiyayen Moi moi tayi dayaji kifi da kawai sanan tai kosai dakuma kunun gyada koda Baffa yashigo gidan yaganta a kitchen suna girki itada Batool baisan lokacin daya ciro waya yamata video batare datasani ba ya aikama Baba sanan yazauna kusada Mama a falon suna hira sanan suka fito dakomi Baffa saida yazauna yaci kosan da kunun dudda abincin shi is ready, suna zazzaune saiga su Manaf sunzo dubata as usual once in a while zokaga dadi bajewa akayi akai lafiyayyen breakfast afalon Mom saida aka gama tass sanan sukai clearing tazo itada Batool zasuje sama suyi bacci ganin Baffa namagana dasu Ya Manaf, kiranta Baffa yayi hakan yasa tadawo, zama tayi akasa dan gyaran murya Baffa yayi yace “Khairy kafin mahaifiyanki tarasu tanata fama da Baban ki ya kara aure sabida ku amman fir yaki” yadanyi shiru sanan yace “dazata rasu agaban kowa yayyinki nan duk suna wajen ta barmini wasiyya kan na aurar da Baban ki karna barshi baida mata” dan ijiyan zuciya yasauke yace “dalilin dayasa nakira su Manaf kenan su biyo tanan kafin su tafi aiki, inaso nagaya muku nasamoma mahaifiyar ku mata” yasake shiru yana kallonsu sanan yace “bayan long bincike akanta, yar limamin masallacin Utako ne, ba yarinya bace ta taba aure da yara biyu, amman mijinta yarasu, yaran na hannun Maman mijin, tayi karatu a FCE tana koyarwa Awani primary school dashi take taimakon kanta haka, tanada natsuwa ga kirki gakuma ilimin addini, na nemama Baba aurenta inaso nan da sati daya ayi Auren hope kun yarda Ummulkhairy” Baffa yakirata ahankali, murmushi tayi ahankali tace “Allah sanya alheri” cikeda jin dadi Baffa yace “Ameen tashi to kitafi” tashi tayi tawuce shikuma Baffa yacigaba da magana dasu Manaf.




Zasu koma bacci Mom tashigo tace su shirya suje saloon, shiryawa sukayi driver ya kaisu saloon tsife kan akayi aka wanke ana gyaran kafansu, kitso akamata mai kyau shiku daya fito da fuskanta, aka mata pedicure da manicure sanan suka biya kudi suka dawo gida, ganin yanda taketa duba wayanta yasa Batool tace “wa kike jira ne awayan nan” hararanta tayi batace komiba saikuma chan tace “Besty” hararanta Batool tayi tace “wlh karya kike” hararanta itama Khairy tayi tace “serious bata dawo school ba yakamata kuma tashigo Wanan dazamu fara exam next week” “laulayin ciki hala take” dasauri Khairy takalleta tace “ciki” Gyadamata kai Batool tayi tace “haka kawata Zara tana aure yanda kikasan da cikin tai tuntube abakin kofa sai ciki” dan murmushi tayi saikuma ta kalli flat cikinta tana picturing kanta da ciki, sosai Batool kemata surutu har suka kawo gida, duba kitson da akamusu Mom tayi kitson yay kyau sosai barinma na Khairy dan tanada wani irin gashi mai bala’in kyau, ga tsayi ga ciki gakuma santsi.

*****



Yau asabar tun ranan daya siyamata tsuntsu basu kara haduwa ba sabida yanason tai karatu saidai waya da night, baicika kiranta during day time ba sabida aiki, most time text yake mata just to check up on her, ko Allah yasan tanama Aliyu wani kalan so ne dan he’s super good to her, he’s caring ya iyasa taji all damuwanta are gone, bata taba sanin she can’t put mutuwan Mama behind her ba amman Aliyu helped her to, he’s just like her strength, yau sosai take murna sabida zata ganshi, yace he’s taking her out yatura mata sunan french restaurant din dazasu hadu.



Shiryawa tayi cikin wani dogon riga, silk ne milk color yadin is so lush rigan yazauna ajikinta dazaka dauka wata black American model ne, zama tayi tadaura wani black cotton dan kwali tai wani plain simple dauri tasaki jelan gyalen agefen shoulder nata, tadanja dan kwalin baya daya bayyana gaban kitson kanta dayay kyau, kwantaccen gashin gaban goshinta tadau karamin brush tai styling nasu da a bit gel daya bada wasu wavy corners subhanallah bakaramin kyau tayi ba, kallon fuskanta tayi a madubi ganin wuyanta empty yasa tadauki wani simple two step necklace dinta dakeda pendant na diamond tasaka awuyanta wuyanta yafara wani kyalli, sanan tadauki kananun dan kunnensu tasaka, mikewa tsaye tayi tanabin kanta da kallo ganin yanda kayan yabi jikinta yanda boobs dinta suka wanisa gaban rigan yay kyau yasa taji wani kalan kunya, wardrobe dinta tayi tadauko wani simple dark army green a bit transparent veil normally dark green goes with milk a whole lot yafashi tayi tagaban hakan yarufe kirjinta but still kana hango kyallin diamond necklace dinta ta gyalen, komawa tayi tazauna kan kujera sanan tadauki brush ta taje full black giranta sanan tadau man baki dake shining ta shafa kan lips dinta dayawani haskaka pink lips din, ganin idanunta sunyi bala’in haske dayawa yasa yadauki kwallin Batool ta zizara Omg, dan murmushi tayi dan ita kanta tama kanta kyau kaman taje studio tai hoto, tashi tayi ahankali yau batajin saka hill hakan yasa tasaka slippers na Hermes shima dark army green daya hadu yau complementing dressing nata gabaki daya, she look very simple but yet super super elegant, wani cute little handbag tadauka na Charles and Keith beige color dayasa tai kaman zata gasan kyau sanan tadauki turarukanta tafesa tanadan tunani mezata gayama Mom tabude kofa tafito, afalo tasami Mom zaune Batool batanan taje gidan kawarta amso note sabida fitanta da Aliyu yasa bata rakataba, ganinta yasa Mom tace “wanan gayu haka sai ina Khairiry”? Dan murmushi tayi ahankali tace “Mom zani wajen Besty dubata batada lpy” ahankali Mom tace “ayyah, laulayi Batool tagayamin dama, ki gaidamin da ita Allah sarki yarinya, haka tadinga sintirin zuwa dubaki, ki gaishemin da ita please” gyadama Mom kai tayi tawuce tafita Adamu na ganinta yatada mota shiga bayi tayi tazauna tagayamai inda zasu suka wuce.




Wani hadadden eatry sukaje, saida Adamu yay parking sanan taciro wayanta daga jaka kafin tai dialing number shi taga kiranshi ya shigo hakan yasa tadauka takai kunenta, murya chan kasa taji yace “come out of the car” sanan ya katse wayan, ahankali tafito daga motan tama Adamu bye yatada motan yawuce sanan tajuyo tana waige waige dan bata ganshi ba. “You look breathtakingly beautiful Miss” taji muryanshi ta gefenta, dawani irin sauri tajuyo da kanta ta kalleshi yana sanye dawani yadi mai laushi fari tass, yana wani irin kamshi mai dadi yasanya black glasses a idanunshi yana kallonta hannunshi rikeda flowers masu kyau combination na white and red yamika mata ahankali yace “flowers for Miss Khairy” fuskanshi takara kallo wani irin murmushi tasaki daya bayyana white teeth nata tasa hannu takarbi flowers din sanan ahankali takaisu saitin hancinta tai breathing in wani irin kamshi taji sunayi mai sanyaya rai kafin ta fuzar tasake dago kanta takalleshi cikin wani classic voice tace “I love flowers thank you Ya Aliyu, they’re beautiful” glasses na idanunshi yacire  murmushi yamata yace “shall we” gyadamai kai tayi sanan suka wuce ciki tana rikeda flowers dinta kaman wasu english couples, akwai mutane amman badayawa ba table din daya musu reserving yakaita wajen sanan yajamata kujera zama tayi ahankali tace “thank you” sanan ta ijiye flowers nata agabanta tana kallonsu tana shafasu da hannunta, zama yayi kujeran dake facing nata yana kallonta baisan maisa ba but yau kyan datamai daban ne kodan yakwana biyu bai ganta ba, abincin daya musu placing order aka shiga kawomusu abinma mamaki yabata dan abincin sunyi yawa, this is a brunch date wow! Murya chan kasa yace “do you like it” gyadamai kai tayi ahankali tace “thank u” murmushi yasakeyi yace “zakici kosaina baki abaki” makemai kafada tayi akunyace sanan tadauki cutlery tashiga cin lasgana dashi yafi shiga idanunta tsayawa yayi yana kallonta Khairy nada wani irin natsuwa da inba kana tareda ita ba bazaka taba cewa tanadashi ba, she does everything a natse calmly batada rawan jikin nan, kaman taji ajikinta ana kallonta hakan yasa tadago kanta hada idanu sukai dashi akunyace ta sauke kanta tanajan gyalenta zata rufe fuskanta dasauri yace “nooo Pickle sorry bazan kara kallonki ba look nazama makaho” kallonshi tadanyi ganin yanda yay da idanu abin yabata dariya dan dariya tayi shima yayi sanan yafara ciCn nashi .



3️⃣4️⃣




Saida sukaci suka koshi sanan suka ture ga uban abinshi sun rage akwai wayanda bama sutaba ba ahankali yace “shall we?” Gyadamai kai tayi yatashi hakan yasa itama ta tashi suka fito maiikatan eatry namai godiya suka wuce motanshi yabude mata shiga tayi sanan yamaida kofan yarufe yadawo yazauna yatada motan suka bar wajen bini bini yake satan kallonshi ganin sunzo wonderland yasa tawani ware idanunta aljihun motanshi yasa hannu yaciro mata 2 ticket dinsu yamika mata Wanan Karan takasa boye excitement dinta tace “wowwwwww Ya Aliyu I am so sosoooooo happy thank uuu” u welcome baby yay maganan yana shiga ciki parking yayi a inda ake parking sanan yafito itama fitowa tayi she’s so happy datama kasa boyewa zagayowa yayi ta inda take yace “are u happy” gyadamai kai tayi tana dan tsalle tace “yes thank uuu” murmushi yamata yace “let’s go” ciki sukayi yariga yay recharging card nasu yace “me and u competition yau zamuyi kin yarda”? Gyadamai kai tayi tace “and I will win cus I am a born winner” murmushi yayi yace “let’s see then” da bumper cars suka fara suka shiga, both of them were literally screaming suna bubbuge juna da motan shi kanshi Aliyu baitaba sanin he could do this childish play ba sai yau, bugeshi tayi motanshi yakoma baya tahau ihu ta waigo tanamai gwalo kwafa yayi sanan yatashi yafita itama fitowa tayi tana tsalle sosai kaman Yar yarinya tace “I won yayy” hararanta yayi yay gaba dasauri tabishi sukaje next game dayakeso suyi shooting target, indai target ne babu wanda yakaishi but da gangan yabarta shima taci wayyo Ummulkhairy kaman zata zuba ruwa akasa tasha dan dadi, ice cream yasaya mata takarba tanasha saida yajiraa ta shanye sanan suka shiga wajen 3D zasu buga car race, nan ma ita taci, yanda takemai dariya ko shi kanshi baisan ta iya dariya hakaba she was really feeling herself, ta iya game sosai sabida su Maheer dan sunayi a gida, all games na wajen nan saida tayi har teddy bear saida taci katuwa tadauki abinta tana dariya, hararanta yayi yay gaba dasauri tabishi tace “Ya Aliyu wait, fushi kake sorry but I told you I am a winner” juyowa yayi yace “nine looser ko” hannu tadaura akan bakinta tana hadiye dariyan dake zuwa mata tace “uhm’uhm” hararanta yayi yace “let’s go waje kiga wanda zamuyi I promise u will be the one to loose” dasauri with confidence tace “eh muje” tabishi dasauri gaban rollercosta taga sunje koda tana yarinya bata yarda tai abin nan ba sabida tsoro hakan yasa ta ware idanu, magana taga Aliyu yayi da mutanen sanan yazo inda take tsaye yace “harkin fara tsoro ne” turamai baki tayi tace “never” dan bakinta data turamai yakalla saikuma ahankali yace “mutafi to aga who will lost, and yarinya kikamin kuka ko” dasauri tace “ni Bana kuka saikace wata baby” dariyanshi yahadiye dan he already saw d fears a eyes nata, yace “let’s go” tana bite dashi suka shiga wajen, ganin tsoro a fuskanta yasa bai bari ta shiga wajen one person ba, two sitter slot suka shiga na mutane biyu, zama yayi sanan itama tashigo tazauna kusadashi ahankali sakamusu abinda zai rike mutum yahanasu faduwa yayi sukadai akan makeken roller coaster dinan sanan Aliyu yakalleta yace “kin shirya” gyadamai kai tayi gabanta na faduwa tim tim, juyowa Aliyu yayi yakallesu yace “we ready” ajiyan zuciya tasauke hakan yasa yay dan dariya yaciro wayanshi yana bude camera yace “I need evidence” turo baki tayi tana hararanshi sanan aka kunna abun, rawa hannunta yafara tun kafin su fara moving, kawai jitayi sunyi sararin samaniyan Allah wani kalan ihuuu tayi. “Wayyoooo Ya Aliyu banyi banyi nafasa, huuuuu wlh nafasa kayakuri” tai maganan tana kankame idanunta jin kaman hanjin cikinta zai fito shiko dariya kaman zai mutu yana musu video, jin suncigaba da sama abin nawani chillarasu kaman zai kaisu lahira yasa kawai tawani kankameshi tana boye fuskanta akan kirjinshi. “Innalillahi, Ya Aliyu zanyi fitsari, wlh u won, Dan Allah kayakuri kace subari wayyooo Allah na na shiga uku, Ya Aliyu zan mutuuuu” alamu yamusu da hannu dasu kashe jin yanda heart nata ke beating, amman har suka dawo kasa bata saniba ta kankameshi gam gam tana cewa zatai fitasari, yadade yana zaune ahaka feeling her ajikinshi kafin ahankali yace “sokike kimin fitsarin ajiki cus we are down already” dago kanta tayi daga jikinshi ahankali kaman matsoraciya kallon idanunshi take dake cikeda dariya sanan takalli ko’ina ganin suna kasa, dan hararanta yayi yace “matsoraciya kawai harda kuka” dan turo baki tayi sanan akunyace tasake takoma gefenta, ciremusu abin rike mutum din yayi sanan yabude sit din yafita dagangan yashiga duba jikinshi yace “hope bakimin fitsarin ajikina ba” rufe fuskanta tayi da hannu tace “ni banyi ba” sanan ta sauko tagefenshi tabi da gudu tai restroom dan tagani wajen dasuke zuwa, shikuma yawuce dan sayomusu snacks yana kallon video daya musu awayanshi. 



Popcorn yasai musu, unsweetened yasaima kanshi dan baicin sugar shi ko kadan itakuma yasaimata mai milk sanan yazauna yana jiranta.


Fitsari tayi sanan tafito tanadan murmushi ita kunya ma takeji, tana cikin tafiya taji an kwalamata kira Ummulkhairy dasauri tajuyo, ganin class governor dinsu yasa tadan tsaya tana murmushi shima yakaraso wajenta da sauri yana rikeda cotton candy guda biyu a hannunshi da alama bashi kadai bane, ganinta yasa yace “wow kema kinzo shakatawa” murmushi tayi tace “eh Governor ya aiki ya shirin exam” ahankali yace “Alhamdulilah” yana kallonta ganin yanda tai kyau yadade yanason Khairy amman yakasa gayamata dan yake yayi yace “u look good Khairy” murmushi tayi tace “thank you bari naje” tajuya zata wuce dasauri yabiyota gabanta yasha sanan yamika mata one cotton candy dake hannunshi yace “atleast take this” girgizamai kai tayi tace “no thank you Governor” dasauri yace “I insist Allah saikin amsa, nawane dana little sister na dama, nakoma nakara sayowa, idan baki amsa ba zanta binki ne wlh” badan taso ba bataso taga kaman wulakanci tamai wanan ma daya rantse saita amsa yasa gently tamika hannu takarbi wanda yake bata sanan tace “thank u” tawuce da sauri binta dawani irin mayen kallo yayi sanan yace “see you on Monday Khairy” ko tankashi batayiba dasauri take tafiya kanta akasa dan tabata lokaci tabar Ya Aliyu chan, jitayi ajikinta ana kallonta, ahankali tadaga kanta, Aliyu tagani tsaye rikeda pop corn guda biyu a hannu, fuskanshi kadai tagani ya tabbatar mata da yaganta tareda class governor dinsu, jitayi kawai jikinta yahau rawa sakin cotton candy don tayi akasa sanan ta taho da sauri kafin takaraso gabanshi gani tayi cikeda bacinrai yawani irin jefar da pop corns din akasa yajuya fuuu kaman zaki yawuce dasauri tabishi tana kiranshi. “Ya Aliyu Ya Aliyu” amman ko waigowa baiyiba har wajen dayay parking mota kafin ta isa wajen dan one step dinshi shine like 3 or 4 step nata harya shiga mota wani irin jan motanshi yayi Saura kiris yabuge wasu yarama ita kanta saida tai ihu Allah yakiyaye bai bugesu ba yafita daga wajen da balCa’in gudu.




3️⃣5️⃣




Jiyayi kafafunta sun mata sanyi wani dan dakali tasamu tazauna bata taba sanin cewa Aliyu nada fushi dakuma zuciya hakaba sai yau, sabida yaganta dawani saiya tafi yabarta anan, jiyayi duk wani iri zuciyanta badadi kaman ba ita bane tagama dariya yanzun nan ba, ahankali tabude jakanta taciro wayanta kiranshi tayi amman har kiran ya katse bai daukaba, hakan yasa takira Adamu tafadamai inda take, baa dauki cikakken 20min ba saiga Adamu yazo mota tashiga suka wuce gida.


Amota ma sake trying nashi tayi amman bai dauka ba, kaiwa gida sukayi hakan yasa tamaida wayan jaka ta fito tashiga ciki, Mom tagani afalo tareda Batool Mom tace “yamai jikin” murmushi tayi tace “yaji sauki Mom tace na gaidaku” “muna amsawa, jeki chanza kaya kiyi wanka ana ma kiran salla saiki salla ki sauko kici abinci” gyadama Mom kai tayi tawuce, daki tashiga wanka tayo tafito salla tayi sanan tazauna shiru jin Mom nakiranta yasa tafice taje abinci taci tadawo daki wasa wasa har 12 bai kirata ba kasa hakura tayi she called him twice bai dagaba kuma bai kirata ba da kyar bacci ya kwasheta ranan hakan yasa washe gari duktai wani kala data tashi takasa tabuka komi koyasan da hakan ne message dinshi taga ya shigo wayanta. “Go and study for exam naki u have paper tommorow” 

Dudda message din baiyi  acknowledge na calls nata but tadanji nauyi yasauka daga mind dinta, kasa hakura tayi tamai reply.

“Ya Aliyu I am sorry, please kayakuri” jin shiru baimata reply ba yasa tasake turamai wani sakon.

“I know him, class governor namu ne saisa nama amsa maganan shi, but I will not do it again I promise”


Almost 5min but bataga reply ba, sosai taji ta bala’in damu sake turamai wani sakon tayi.

“Ya Aliyu I am sorry”

 Tana turawa yamata reply.

“I said kije kiyi karatu” gyadamai kai tayi kawai ta ijiye wayan book dinta tadauka ta tashi taje tazauna kan dadduma dudda karatun rabi tunanin shine but hakanan ta tursasa kanta tayi.


Yau rabonta dajin muryan Aliyu sati daya chur kenan dan gashi nan wata asabar din ta zagayo, exam ma adaddafe take tabashi hakuri harta gaji yaki hakura dudda kullum saiya mata text yasata tayi karatu but other than that shiru kakeji, har dan ramewa tayi dayake ansan exam take babu wanda yabama abin attention, yau tunda gari yawaye Mom tasata ta shirya taje tagaida matan Baba da tuni akai biki harta tare, bataso taje amman bazata iya cewa no ba hakan yasa ta shirya dan yau at the same time zaa raba gadon Mama abinda yasama bataso taje kenan.



Parking direba yayi acikin gidansu gani tayi gidansu ya chanza an sake penti, Baba tagani akujera a tsakar gidan da alamu shan iska yake yasa farin jallabiya ga flask don shayi agabanshi dawasu papers yarame sosai ganinta yawani fadada murmushin fuskanta yabude mata hannu dawani irin gudu tazo batai wata wata ba tawani rungume shi she miss baba so much, sun dade ahaka sanan tasakeshi yazauna kan kujeran dake kusada shi tace “Baba ina yini” murmushi yamata yana tana kumatunta yace “Khairy na ya jarabawa next week zaki gama ko” gyadamai kai tayi yace “yaushe zaki dawo gida” gidan tabi da kallo sanan ahankali tace “bayan jarabawa Baba” Gyadamata kai yayi sanan yadauki papers dake gabanshi yabata yace “ga gadon Maman ki nan dakika samu na filaye biyu dakuma gidan kifinta guda daya, sai kayayyakin ta, duk wani abu na Maman ki daidai da cokali an raba, duk suna store, su Manaf duk sunkai nasu gidan marayu sunyi sadaka dasu naki kome kikace ayi dasu haka zaayi” ahankali tace “Baba akai gidan marayu, kayanta na sawa zan cire wanda nakeso sauran sai akai” Gyadamata mata kai yayi sanan ahankali yakama hannunta yace “I am here for you Khairy okay, hope bakida any damuwa” dan murmushi tayi tace “Baba I am fine Allah kuwan, ina su Ya Manaf” “sun tafi office” gyadamai kai tayi ahankali tace “ina new Mom”? Yadade yana kallonta sabida yanda tafadi sunan kafin ahankali yace “tana ciki” tashi tayi tace “bari naje nagaidata” tawuce ciki Baba yabita da kallo, ahankali tabude kofar falonsu wani sanyi yamata sallama tadade tsaye kafin ta shiga cikin falon daidai da foot mat nabakin kofa an chanza har tv bango an chanza komi tatas kaman ba gidansu ba kaman ba falon Mama ba, abin was so strange, mutuwa mutuwa wlh karshe ne! yanzu shikenan this falo is not for Mama again na wata ne, Anya zata iya cigaba da zama agidan nan kuwa Anya bazata koma da zama gidan Baffa gabaki dayaba Dan what she is feeling right now jitayi kaman ta kurma ihu hatta labule duka bana Mama bane jin kuka yazo mata sosai dawani irin sauri tajuya zata fita taji ankirata. “Ummulkhairy” chak ta tsaya, sanan takai hannuwanta ta goge hawayen dasuka zubomata daga idanunta tass kafin ahankali tajuyo, sabuwar matan Baba tagani batada wani makusa Babba ce itama amman daga gani Mama ta girmeta sosai, doguwa da ita kana ganinta kaga natsassiyar mace, murmushin dole Khairy ta kakalo ahankali tace “ina yini uhnnn” tama rasa sunan dazata kirata dashi murmushi matan tayi daidai takaraso gabanta hannunta tasa ahankali takama hannun Khairy tace “sunana Mariya, maisa kika tsaya anan bakin kofa keda falonku shigo mu gaisa” taja Khairy cikin falon danne kukanta Khairy tayi sosai sanan ta zauna akan kujeran da Mariya ta zaunar da ita sanan tace “ina zuwa” dasaurinta ta wuce kitchen tafito da drinks a tray takawoma Khairy ta ijiye sanan tasake zama kusada Khairy data kasa kallonta dan wani iri takeji, ahankali takai hannunta tadaura kan cinyan Khairy cikeda tausayawa tace “ina tunamiki da mahaifiyanki ko” dauke kai Khairy tayi da sauri tana kokarin danne hawayen dake gab da zubowa tace “uhn uhn” ahankali Mariya tace “Khairy I am so sorry about your mother’s death, Allah ubangiji ya haskaka makwancinta, Allah yasaka mata da gidan aljanna” ahankali Khairy tace “Ameen” murya chan kasa tace “Khairy mijina na farko nima yarasu so I understand pains dinki sabida yarana suma sunma mahaifinsu kuka, at first da akazo nemama babanki aurena nariga nai alkawari bazan kara aure ba but danaji matarshi tarasu tabar yara abinda yasa na aure mahaifinki kenan sabida inaso nazama uwa ga yaranshi dan ni bansami chance dinan nama yarana hakaba” dasauri Khairy takalleta tana share hawayen daya zubomata, Gyadamata kai tayi tace “bayan rasuwanshi iyayenshi suka karbe yaran, kafin naga yarana yanzu sai Hutu Hutu akawosu sumin kwana biyu, tuntuni naso nazo dakaina ma har gidan Baffan naku ko Baban ki ko yayyinki sukawoni nadawo dake gidan mahaifinki, Khairy just know this, nasan ba lallai ki daukeni ko ki kalleni a matsayin mahaifiyanki yanzu ba saidai a matsayin kishiyaneuwa, I want to assure u ke y’ata ce Khairy, u can come to me for everything and anything, zan rikeki da yayyinki amana kaman yaran da na haifa, bazan taba cutar daku ba kinji” Gyadamata kai Khairy tayi sanan ahankali tace “thank u” hannu Mariya tasa tashare mata hawayen sanan tace tashi muje sama binta Khairy yayi Baba dake kofa yaji komi baitaba jin sonta aranshiba sai yau, tunda akai auren basuma taba kwana daki daya ba dan gani yake kaman yacuci Mama amman yau yakudiri aniya komi zai chanza zai saki ranshi da ita.



Khairy bata bar gidan ba sai bayan sallan magrib shima saida matan Baba tasa tamata alkawari dazaran tagama jarabawa zata daCwo gida.




3️⃣6️⃣




 Yauma hartai bacci Aliyu bai kirata ba ita at this junction tama fara tsoro haka Aliyu keda fushi, abinma haduwa yayi yataru yamata yawa hakan yasa ta tashi da zazzabi jikinta zafi gashi hancinta yatoshe mura, wuraren 7:30 tafito kasa, ganinta wani iri yasa Mom tace “meke damunki idanunki sundan kumbura da hancinki” ahankali tace “mura ne” jin yanda take magana da hanci yasa Mom tace “Ayyah sannu zoki breakfast bari nakowa miki maganin mura” kunu tadeba tafara sha bata wani dade ba Mom tasauko rikeda maganin mura karba tayi tasha sanan takarasa shanye kunun ta tashi tama Mom sallama ta tafi.


Tun kafin sukarasa wajen parking space din ta hango Aliyu tsaye yay wani irin bala’in kyau yakara haske kaman wani balarabe, yana sanye da uniform din yan sanda jingine da motanshi yay folding hannunshi a kirji yana kallon motansu tunda ta doso, idanunshi sun fada ciki kadan kana ganinshi kasan shima yawahala yan kwanakin nan kaman yanda itama ta wahala.



Jitayi wani abu yazomata wuya amman ta danne, parking Adamu yayi hakan yasa tafito daga motan ahankali kallonshi tayi kaman yanda yake kallonta, hawayen dataji yazo mata yasa takauda kanta gefe dasauri taredakai bayan hannunta tashare sanan ahankali tadaga kafanta tafara tafiya wuceshi tayi ahankali kaman bata ganshi ba dawani irin sauri yasha gabanta hakan yasa chak ta tsaya batare data dagokai ta kalleshi ba dan dazaran ta kalleshi zata iya kuka kuma bataso tayi, ahankali tace “excuse me please I have exam by 9” dan ijiyan zuciya yasauke tareda lumshe idanunshi jin muryanta sanan ahankali yabude su yadaura akanta, murya chan kasa yace “Ummulkhair!” Wani abune yataso mata tundaga cikinta harzuwa wuyanta dataji inbata amayar dashiba zata iya mutuwa dago idanunta dasukai jaa tayi sun cikada kwala tace “don’t call my name again Ya Aliyu, nadauka ai kadena daukan wayana, kadaina kirana, kadaina texting dina? Why are you here then? Mekazo nema wajena”? Kallonta yake idanunshi sundanyi ja, jiyayi zuciyanshi na tafarfasa, ko kadan baiso yanunama Khairy fushin shi that’s the reason why he avoided her yamaki wayada ita, wani irin zuciya yakawomai wuya ciki wani irin harsh tone that’s not loud yace “kinmin laifi and kina fushi dani? Why would you talk to anyman har kina karban abinshi why?!” Yamata wani kalan ihu da saida tadan firgita tadan koma baya tana kalle kalle tagodema Allah dababu kowa awajen, zuciyanshi yanuna mata yace “kinsan what you did to me? To my heart haaa? Why will you talk to anyman why?? Akanme zaki tsaya kinama wani namiji magana bayan kinsan I love you! My heart beats for you! You are my life! U are my happiness! You are my everything Khairy haaa” yanda idanunshi taga sunyi jajir saida abin yabata tsoro kaman zai daketa, jijiyoyin kanshi sun fito, bayan hannunta tasa tagoge hawayen daya zubomata kafin ahankali tace “Ya Hydar akanme zakai tunanin wani abu bayan nacemaka class governor dinmu ne, is it my fault we bumped into each other that day? Ya Aliyu akanme zakai tunanin wani nakeso bayan nariga nama zuciyata alkawari cewa ita taka ce, zuciyata, gangan jikina, ruhina duka nakane Ya Aliyu Wanan shine ALKAWARIN ZUCIYA na, akan me zakai tunanin bana sonka uhmm”? Hawayen daya zubomata ta share, kawai tawuce fuuuu hannu yamika zai kirata amman yakasa cikin wani irin fushi yadaki motanshi da kafa shikanshi baisan mesa yake da mugun kishi nan ba.



Adaddafe tai exam din ranan, inda ace batai karatu ba dababu abinda zata iya rubutawa sabida yanda babu abinda kemata dadin nan, bata taba sanin haka akeji idan akai fada da masoyi ba sai yau, she miss Aliyu badly, she just miss him.

Tana gama paper tafito bata tsaya jiran su Besty da Amal ba sabida yanda batajin dadin komi ga jikinta yakara zafi, fitowa tayi yanda takeji batajin zama ta iya jiran Adamu yazo daukanta ba hakan yasa tafara tafiya tai hanyar gate, wani irin shan gabanta da mota Aliyu yayi tana ganin motan tajuya zata chanza hanya da sauri yafito baima tsaya mata magana ba hannunta yaja ganin mutane yasa tabishi dan ayanda yake zai iya cewa daukanta zaiyi gaban mutane idan bata bishi ba, bude mata yayi tashiga batare data kalleshi ba sanan yamaida kofan yarufe yazagaya yashiga mazaunin direba yaja motan, batare data kalleshi ba tace “kana fita daga gate kasauke ni natare cab natafi gida” kallonta yayi da jajayen idanunshi cikin husky voice dinshi yace “idan naki fa” hannunta tadaura akan fuska tafashe da kuka sosai cikin kuka tace “I said I am sorry, I don’t have anything to do with class governor munhadu ne by accident, he said yazo wajen da sister shine, and he insisted saina karbi candy hannunshi, I don’t wanna be rude koyaga namai wulakanci saisa na amsa, nabaka hakuri kaki hakura what do you want from me, what do you want from me?” Wani irin fizgota taji anyi da bala’in karfi, dawani irin sauri tabude idanunta jikinta na rawa, tuki Aliyu yake da hannu daya akan titi amman ya fizgota da karfi tana jikin kafadanshi yakai hannunshi ta waist nata yariketa gam ajikinshi takasa kwace kanta yana kallon hanya, dasauri takalli hanyan jikinta narawa tace “Ya Aliyu dan Allah zamuyi accident kayi parking” gangarawa gefen hanya yayi yawani kalan taka burki kaman motan zai kife kankameshi tayi tareda runtse ido gam gam jikinta narawa still, habanta dataji ankama yasa tabude idanunta ahankali, hada idanu sukai da Aliyu da idanunshi sukai ja faduwa taji gabanta nayi, cikin wani irin murya yace “you ask wat do I want from you” gyadamai kai tayi tana wani irin shakkan shi, wani kallon fuskanta yake ahankali yace “I want you Ummulkhair! I want you so bad saisa my heart can not stand yaga kinama any namiji magana, zuciyana yakusan bugawa ranan I had an accident” dan zaro idanu tayi cikeda mamaki, lumshe idanu yayi sanan ahankali yakai fuskanshi dab da nata yana kallonta dawani irin sauri ta lumshe idanunta gabanta nafaduwa dasauri dasauri yadade yana kallon fuskanta ahaka kafin ahankali yadaura goshinshi kan nata yanajin saukan numfashinta akan fuskanshi, cikin wani whispering voice dake nuna so yace “I am sorry for hurting you, I couldn’t help it, Ummulkhair ina sonki da yawa and Aliyu is a very very jealous man bayin kaina bane, can you put up with me? I can’t help it bazan iya magance kishina akanki ba, zaki iya rayuwa dani eh Ummulkhair?” Jitayi zuciyan ta gabaki daya yasaki gyadamai kai tayi ahankali tace “but don’t ever hurt me the way you did by not answering and responding to my calls, Ya Aliyu I….Love yhuu” this is the first time tafadimai kalman daya dade yakeso yaji daga bakinta, ahankali yace “you are the PROMISE OF MY HEART Khairy” ahankali tace “Ya Aliyu nima kaine ALKAWARIN ZUCIYA ta” ahankali yamata peck a forehead sanan yakai hannunshi yashare mata fuska tass sanan gently yasake ta yamaidata kujeran datake kafin ahankali yatada motan zuwa pharmacy, magunguna yasayo mata da ruwa da kanshi yabata sai kallonta yake sanan yadawo motan yatada har anguwan su Baffa yakawota nesa da gida yay parking sanan yakalleta, kallonshi tayi sanan ahankali tabude motan tasauka tawuce saida yaga shi ganta gida sanan yatada motan yabar anguwCan.





3️⃣7️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Wuraren 10 yau taga kiranshi wayan na gabda katsewa tadauka ahankali tace “Ya Aliyu” ahankali shima yace “Ya muran? Jikinki yadena zafi” gyadamai kai tayi tace “eh yadena naji sauki” dan ijiyan zuciya yasauke kafin ahankali yace “I am sorry for hurting you Pickle, will you forgive me” gyadamai kai tayi tace “bakomi yawuce” dan ijiyan zuciya yakara saukewa ahankali yace “kinada paper ranan Monday” gyadamai kai tayi tace “yes but in the morning” ahankali yace “good, I want to invite you to my promotion stuff zakizo” wani irin murmushi tayi tace “za’ayi promoting naka awajen aiki”? Dan yatsine fuska yayi yace “kind of and I want you to be there for me, ina stage ina ganinki ina murmushi” dan murmushi tayi sosai tace “to baranzo ba” Dasauri kaman dan yaro yace “pleaseeee Khairirin Baba” dan dariya tayi ganin yanda yake tsokanta ahankali tace “okay shikenan zanzo but kaizaka daukamin jakana” dasauri yace “zanma goyaki like my baby idan kinas..…..” katse wayan yayi dasauri jin alamun mutum tsaye adakinshi, dago kanshi yayi ganin Abba tsaye yana sanye da jallabiya ya rungume hannunshi yana murmushi yasa yaji wani kalan kunya, daman abinda yasa baije wajen Abba ba sabida yay wasu manyan baki ne, patient dinshi saisa baije ba.


Ahankali Aliyu yatashi zaune daga gadon kasa kallon Abba yayi dan murmushin da Abba keyi kadai ya tabbatarmai da yaji all maganan dayake da Ummulkhair, akunyace yace “Abba bakin sun tafi” dan murmushi Abba yayi yamaida kofan yarufe sanan yashigo dakin har zuwa inda Aliyu yake zaunen sanan yazauna agefenshi, ahankali yace “Aliyu so kanada yarinyar dakakeso haka baka sanar dani ba” kunya yasakeji ganin yakasa magana yasa cikeda kulawa Abba yace “what’s her name”? Ahankali murya chan kasa Aliyu yace “Ummulkhair” dan murmushi Abba yayi yadade yanaso yaga Aliyu yayi aure amman ko budurwa Aliyu baidashi, daurewa yayi yay hiding farin cikin shi karya nunamai yace “yaushe zamuje mu nemamaka aurenta”? Dan murmushi yayi dashi kanshi Abba saida yaga murmushi hakan yakara tabbatarmai da yanda Aliyu ke sonta sanan yace “inaso dama takarasa gama school ne Abba” ahankali Abba yace “nan da kaman yaushe kenan” ”sauran mata just one semester, Accounting takeyi” gyadamai kai Abba yayi saikuma yatashi tsaye yana kallonshi ganin yanda har yanzu yakasa hada idanu dashi, cikeda tsokana yace “bari natafi nabarku kucigaba da soyayyan ku, anyway greet my daughter in law for me” dan dariya yayi Abba yawuce yafita ranshi fess. Kiran Khairy yakarayi sai after 1 sanan sukai sallama.




Yau Monday wuraren 12 tadawo gida dan 11 tagama paper ta na yau, tanacin abinci tai bacci dan 4 zata wajen ceremony na karin girman Aliyu.



4 ta tashi agurguje tashiga bayi wanka tayo tana fitowa tai salla sanan tashiga shiryawa cikin wani embroidery exclusive atampa, gold and red, an mata dinkin doguwan riga A-shape dayay mata kyau, dan kwalinshi ta daura dayay kyau akanta sanan tadauki wani simple red veil tasa kafin tadauki wani warwaron zinare ta tasaka da dankunnen zinare mai kyau sanan takalli kanta a madubi kwalli tadauka tasaka ma manyan idanunta kafin tashafa man baki, wani takalmi mai tudu tasaka red, sanan tadauki gold jaka tahada sake kallon kanta tayi amadubi tai wani irin kyau kaman amarya, dan murmushi tayi sanan tafito tana kallon agogo 4:40, sallama tama Mom da sunan zata gidansu sanan tawuce Adamu yadauketa she wants to get a gift for him is his promotion and banda hakama bata taba bashi anything ba, hakan yasa tacema Adamu yakaita wani Men’s boutique.


Shigatayi ciki tana kalle kalle kayan maza ne awajen babu abinda babu gaban wani Jaguar special edition watch tana kallo, yanda take kallonshi yasa mai shagon yadauko yabata murmushi tayi tace “how much is it”? 359k, gyadamai kai tayi sanan tazabi wani bakin sunglasses dayamata kyau shima designers product na police shikuma 156k sanan taciro ATM card dinta tabiya, indai kudi ne tanada shi, every month tun suna yara Baba nabasu monthly allowance, yayyinta nabata kudi just like that, Mama ma nabata kudi, Baffa shima every month saiya bata kudin break dan haka yake kiran kudin, banda random kudin datake samu every now and then bata kashe kudi tanada komi, wrapping everything aka mata sanan tasa aka rubutamata congratulations a paper tag aka makala jikin cute bag din sanan tafito tashiga mota suka tafi wuraren 5:15 sukakai wajen, tana rikeda abin tashiga wajen bayan tanuna IV dinta daya turamata awaya, wajen yacika makil baya tasamu tazauna tana kallon stage lokacin ana decorating Aliyu ana karamai stars a uniform nashi murmushi tayi tahau tafi, yayi wani irin kyau kaman bashiba, bata wani dade da zama ba aka gama abin Dj yasa waka, gani tayi Aliyu ya sauko daga stage din yafara tafiya dudda ana tareshi ana gaisawa dashi but idanunshi nakanta chass, ita bama tasan yaganta ba sai yanzu dataga yana kallonta dauke kai tayi daga kallonshi ganin yanda mutane ke kallon inda yake kallo tahau wasa da yatsunta chan kuma taciro wayan ta daga jaka tana daddannawa. “U look beautiful Pickle Anya zan iya jira kigama school kuwa”? Taji muryanshi akanta, dan turobaki kadan tayi sanan takalleshi ganin yanda yake kallonta yasa akunyace tadau bag dinshi tamikamai murya chan kasa tace “congratulations” wani irin kallon cute bag din yayi sanan yay murmushi yasa hannu yakarba yace “Pickle got me gift, I promise dazaran nakoma gida shi zan fara budewa thank yo….” Bai karasa maganan ba jin wayanshi na ringing zaro wayan daga aljihu yayi yakalli screen din sanan yamaida kafin yakalleta yace “come muje lemme introduce u to some people” makemai kafada tayi ahankali tace “ni kunya nakeji kabari natafi” dan hararanta yayi yace “kokizo muje Kona daukeki wlh” dasauri ta tashi daga kan kujeran tana turomai baki, murmushi yayi  yace “muje gimbiyar Aliyu” jerawa sukayi atare yana kallonta ganin yanda take bin wajen da kallo tayi kyau ba kadan ba kaman amarya, wajen dasu Gwaggo ke zaune yakaita, Gwaggo da Mami sai Meena da Khadija da Amal ke zaune Abba ne kadai bashi awajen shima bai dade da tafiya ba sabida emergency da aka kirashi for a hospital, ita binshi kawai take har gabansu Gwaggo dabatasan suwaye ba, dukansu kallonsu suke sanan yadan juyo yakalleta ahankali yace “meet my family Pickle” Innalillahi! Tafadi dasauri jitayi zata nitse akasa dawani irin sauri tajuya zata gudu dan bama tasan mema zatayi ba, hannunta ya chapke yanadan dariya cikeda wani irin mugun sonta yace “come back here” wani rin boyewa abayanshi tayi tana jan gyalenta trying to cover her face, sanan Aliyun yakalle su Gwaggo kafin ma yay magana Meena tace “Ya Hydar Anty Khairy ce”?Gyadamata kai yayi sanan yakalli Gwaggo hararanta yayi yace “ga Ummulkhairy nakawo miki kiganta” wani irin washe baki Gwaggo tayi itakuma Meena tashi tayi tazo har bayan Aliyu tawani irin rungume Khairy tace “Anty Khairy oyoyooo please kibari inga fuskanki dan Allah” kafinma Khairy tai magana tashi Gwaggo tayi ta dakama Meena duka abaya tace “ke dalla tashi kibama mutane waje da rawan kai zakija yarinya tafadi bakiga kunya takeji ba, angayamiki irinku ce ita fitsararru muna kallonku kuna kallonmu kuri, Khairiya ta yaki kinji” Gwaggo tai maganan tana kamo hannun Khairy, sakin hannunta Aliyu yayi yana binta da kallo ahankali Khairy tabita still tana rikeda hannun Aliyu dake murmushi dudda shi yasaketa, sosai Mami tabi tundaga hannun nata data rike Aliyu dashi da kallo harzuwa fuskan Aliyu dazata iya cewa bata taba sanin yanama murmushi hakaba sai yau, wani irin kallon yarinyar yakema yarinyar kaman zai hadiyeta, zama Gwaggo tayi akan kujera  Khairy kuma tadan tsugunna agabanta sanan ahankali taja gyalen Khairy baya sunnar da kai Khairy tayi kasa murya chan kasa tace “ina yini Gwaggo” wani irin washe baki Gwaggo tayi tace “Allah nagode maka Aliyu wayyo Allah na, yarinya ga ladabi ga biyayya gakuma kunya kagama biyana Hydar, Allah ya tabbatar da Alkhairi, inane gidanku gobe zanzo na nemama jikana aurenki” dagota Aliyu yayi dasauri yana hararan Gwaggo yace “ni bazakije neman mini aure ba hakanan kisa ahanani” Mami yadan kalla sanan yadauke kai yace “ga Mami Pickle” ahankali batare data dagakai takalli Mami ba tace “ina yini Mami” kan Mami nakan waya batare data kalleta ba tace “lpy sannu” Khadija da Amal ne duk suka gaidata suna murmushi sanan yakalli Gwaggo yace “bari narakata sai indawo mutafi” dasauri Gwaggo takara tashi tana warware kullin zaninta tace “bari nabata kudin mota” dariya Aliyu yayi yace “direbanta na waje Gwaggo” “kai wlh makirin yaro ne Aliyu bakin ciki kake zan bata kudi kai bani baka, katon banza kawai andaiji kunya” dariya Khairy tayi kanta akasa, sanan Gwaggo takawo dubu daya tasamata a hannu tace “gashi asaiwa kanne tsaraba ki gaidamin da mamanki kinji” Gyadamata kai Khairy tayi tace “nagode Gwaggo” Aliyu ya harareta irin hararan makwaduwa dinan yace “muje” Meena tace “bye Anty Khairy” bye tamata sanan suka wuce Mami tabi Khairy da kallo tundaga kasa har sama daya tabbatar mata da Yar masu kudi ce, ga zinare a hannunta da kunne atampan jikinta kadai is worth 260k gashi kuma taji Aliyu nacewa direban ta na jiranta awaje, a ina Aliyu yasamo Yar masu kudi haka, iska tadan fuzar ahankali takara kallonsu yanda Aliyu ke kappa kappa da ita kaman Yar Kwai, jitayi zuciyanta namata zafi, “kinga Zainabu kiramin mijinki awayanki bani da kati atawa in gayamai danshi yasami mata ohhh ashedai zanga Auren Aliyu kafin na mutu iyye, kai Allah nagode maka Allah, kiramin imaza” akufule tace “nima banda katin” dasauri Meena tazo wajen tace “Gwaggo inada shi bari nakira” wai Gwaggo kaman zata zare, sabida murDna.





DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA





Dakin Ammin shi yawuce, tana zaune as usual cikin shiga na alfarma kaman matan shugaban kasan Nigeria waya a kunnenta tana waya, kan stool na gabanta kuma fruits ne yankakku da spoon aciki da alamu sha take sai wayan ya tsayar da ita, zama yayi kusada ita sanan yadauki bowl na fruit din nata yafara sha abinshi wayanshi yaciro yana dubawa miss calls yagani like 9 daga number daya shiru yayi yanaji ranshi na baci baisan ya akayi Faisal yabama that Aisha girl number shi ba, bayan yabar Abuja lokacin da Mama tarasu daya koma baima sauka agidan ba hotel yakoma da zama dan he’s tired of yanda yarinyar keep stalking him school gida kaman zata haukace akanshi, he just had sex with once which he paid which infact ma bashi yama nemeta ba, Wanan halin datakeyi yasa kwata kwata bayama neman yaran naija, all babes dinshi achan turawa ne cus sunsan menene sex for fun not sex for attachment, dan tsaki yaja ganin tasake kiranshi ya ijiye wayan Ammi datagama call tace “kai lafiya kana neman fasa wayanka” ahankali yace “Ammi damuna wata mayyan yarinya take ne wlh” dan murmushi Ammi tayi tace “kai haka kakema yammata wulakanci ahaka zaka sami matan kayi aure, danni wlh tasaka zanyi agaba Kwanan nan zakai aure dan bazan barka hakama yaro kanada 36 kana neman 37 ace ba mata ina, akwai ma wata yarinyar kawata danakeso kaje kadubo bakaga yarinyar ba kaman baturiya” ijiye bowl na fruits din yayi yace “Ammi please don’t start niba yaro bane dazaki dinga nemomin mata ba I will get married but lemme take my time baaa rushing ayi aure, I still young bawai tsufa nayiba” tunda yake maganan Ammi ke kallonshi tace “wai kai Son na lura bamaka son Auren nan gabaki daya” murmushi yayi ya kwanta akan kujeran yana daura kanshi kan cinyanta ashagwabe yace “Ammi kaina kaikayi sosamin” hannu tasa cikin soft gashin nashi tana sosamai scalp tace “daga ina kake dan na aika dakinka bakanan” ahankali yana lumshe idanu yace “dakin Mom” tsayarda susan tayi tace “akanme zakaje gaida matan nan ita yaran datake zama dasu bata taba turosu sun shigo sun gaidani ba barinma Wanan mai idanun mujiyan Khairy” shiru yayi yana jinta baice komiba yace “ita tanaso yarana sudinga girmamata ita batasa nata sunyi hakaba” murya chan kasa yace “common Ammi nowww, yaran gidan nan waye baya tsoronki masifanki yasa babu wanda keso yashigo side dinki ya gaidake” ture kanshi tayi dagakan cinyanta tace “ni uwarka kake kira masifaffiya eh” maida kanshi yayi kan cinyanta yace “Ammi ok bazan kara zuwa ba cigaba damin bacci nakeji wlh” yanda takeson Zayn yasa shi kadaine bata iyawa masifa da wanine yau daya shiga uku, cigaba da sosamai kan tayi baidauki cikakken 4min ba yay bacci ahaka, ta tasashi gaba tana kallo ahaka Baffa yashigo side din yana kallonsu murmushi yayi yace “kin sangarta yaron nan dayawa wife” murmushi tayi tace “wai nan lallabashi nake yaje yadubo yar kawata idan tamai mu musu aure koya kagani dan wlh Alhaji na lura Zayn bayason yau aure at all” tunda tafara maganan Baffa yay gim yana kallonta, ganin yanda yayi yasa Ammi tace “tunanin me kake bakace komi ba” dan murmushi yayi yawuce sama sanan yace “idan bayaso karki takuramai” binshi da kallo tayi dan reply din Baffa seems strange, dan tabe baki tayi tace “zaimaje kuma zai sota atoh”.





Wuraren 4 tana zaune adakinta tana waya da Aliyu da this is the third time yake kiranta tun bayan text datamishi dazu kan ta yanke duk yadamu harda cemata zai dawo tahanashi karya dawo dudda haka yaki yarda, turo kofa Batool tayi tawani fado gadon tace “Malama Ya Zayn yace kifito kuje” ahankali tace “kije kicemai nafasa zuwa” hararanta Batool tayi tace “wacece Yar aikenki ni kinga tafiyata wajen Mom bye” Aliyu dakejin maganan su yace “waye Zayn? Ina zaku”? Dan yatsine fuska tayi tace “gidan mu zani wajen Baba, Ya Zayn kamanta Babban yayanmu dandan Baffan mune” dan ijiyan zuciya taji yasauke kafin ahankali yace “go and tell him u are not going, gobe Adamu yakaiki” gyadamai kai tayi tace “tom bari naje” katse wayan tayi ta ijiye kan gado sanan taja wani gyalen Batool data jefar kan gado tadaura akanta dababu dan kwali tazura silipas tawuce tafita”.




Yana zaune cikin mota yakafa black sun glasses a idanunshi kaman wani makaho yana kallon kofar flat din Mom, sai uban kamshi yake yasaka wani gizna mai ruwan toka ajikinshi kaman wani ango, bude kofan flat din Mom da akayi yasa ya gyara zama yana kallon flat din da kyau, fitowa tayi babu komi a hannunta sanye dawani pink bathroom slippers da kumbunan kafanta sukai Zara zara sukai kyau aciki, har lokacin tana sanye da gown din dake jikinta dazu, hannunta dataji ciwo saiwani kaffa kaffa take dashi kaman Yar yarinya daga ganinta kasan bata sabajin ciwo ba and she hates getting injured, fuskanta looks so innocent and so beautiful tana wani irin glowing idanunta subyi fari kal kaman tana wankesu da hypo, pink lips dinta ko daganan zaune amota da bakin glass dinan a idanunshi yana iya ganinsu, gani yayi ta tsaya takalli waya nan tsuntsayen dayagani anan barandan Mom acikin cage dinsu masu kyau dankoshi dazu dazai shigo saida ta tsaya ya kalli tsuntsayen dan sunyi kyau, murmushi tayi sosai da he could see all side dimples nata na lotsawa jerin gajejjerun white baby teeth nata sun fito tana kallonsu sanan ta tashi tajuyo tana saukowa daga staircase din, ahankali yakai hannunshi yadaura kan kirjinshi dayaji every step datai taking yana jinshi a heart dinshi, tunda yake shi he never baitaba jin haka on anygirl ba, shi baima taba tsayawa yakalli any girl kaman yanda yakalli Khairy yauba, he don’t know mesa kawai he just like how innocent she is, dan iska always know dan uwanshi idan yaganshi but anytime yakalli Khairy he sees yarinya that doesn’t know anything, yayi nisa acikin tunanin yaji tai knocking glass din motarshi wani irin daure fuska yayi batare daya saukarda glass din kasa ba yay unlocking car din hakan yasa tabude kofar motan kallo daya tamai sanan tadan sunnar da kai ahankali tace “Ya Zayn baranj…..” “you don’t talk to me daga waje get in kafin nabata miki rai” jitayi ranta yabaci ahankali tashigo motan tazauna zata fara magana yace “rufemin kofan mota” rufe kofan motan tayi ahankali kafin tai magana yatada motan yaja ana budemai kofa dasauri tace “Ya Zayn bazani ba shine abinda nazo nafadama” batare daya kalleta ba yace “idan munkai kidawo” dan jim tayi ranta nabaci, batare daya kalleta ba yace “sit belt Miss” jan sit belt din tayi tasaka sanan ahankali tamaida kanta tana kallon hanya.




Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




Sakin hannunta yayi dawani irin sauri tajuya gabanta nafaduwa dum dum Batool sai hadiye dariyanta take ganin yanda duk Khairy ta birkice sanan suka wuce suka shiga flat dinsu, suna shiga Batool tafada kan kujera tana dariya tana kallon Khairy datai kuriii jikinta har lokacin bai dawo daidai ba, kallonsu Mom data fito daga kitchen tayi tace “ya akayi” cikeda dariya Batool tace “Mom Khairy taje takankame Ya Zayn tadauka nine saura kiris yamaketa bakiga yanda dukta rude” hararan Batool Mom tayi tace “wlh daya makemin mu danama mai godiya, yara daga tashinku kunbi gida kuna guje guje ko kayan bacci baku cireba ku wuce kuje kuyi wanka kuchanza kaya kafin na sassaba muku” Khairy tafara gaba kafin Batool tabita abaya, hartahau stairs sanan tajuyo takalli Mom tace “Mom yaushe Ya Zayn yadawo”? Batare da Mom takalleta ba tace “around 2 nadare ya shigo gidan nan kuna bacci lokacin” wani irin tsalle Batool tayi tace “yanzun nan bai wanka zanje nasame shi Mom yabani kudin ankon Na’ima” “kinfi kusa” Mom tai maganan tana shiga kitchen abinta itakuma Batool tajuya tai dakinsu, shiga tayi ganin babu Khairy afalon yasa tafada kan gado tana jiranta tafito daga wankan.


Fitowa Khairy tayi daure da towel dinta pink akirji ko kallon Batool din batayiba tawuce wajen wardrobe dinsu, tashi Batool tayi zaune tana kallonta tace “towai fushi kikedani danna tadaki daga bacci sorry to” juyowa tayi ta balla mata harara tace “ni gidanmu zan ma koma Wanan da wanchan Yayan naku yafaramin gorin gida daga ganina bazan dauka ba” dasauri Batool ta tashi dan idan akwai abinda ta tsana shine taji Khairy tace zata tafi gidansu, dasauri ta tsaya kusada Khairy dake shafa mai ahankali tace “ke dalla don’t mind Ya Zayn, wlh Ya Zayn nada bala’in kirki barshi dai da iyaji da kanshi amman yanada kirki kinga duk wulakanci Ammi baya biyemata wlh, Bakiga yana shigowa nan ya gaida Mom ba dudda Ammi bataso shi baruwan shi kuma yana sonmu, yana bani kudi koban tambayeshi ba hakama Zara’u, har dakinshi tana zuwa taitamai surutu wlh baida wulakanci, dan Allah karki kara cewa zaki tafi” kwafa tayi tajuya mata baya tanasa bra sanan tajuyo binta da kallo Batool tayi tace “ke Khairy ai wanan Bra yamiki kadan, kinada nono wlh Khairy kaman muyi musanye” dan tsaki tayi tadau riganta tana sawa, Batool cikeda tsokana tace “iyye su Ya Aliyu zai more” dawani irin sauri tajuyo zata dakamata duka ihu Batool tayi tawuce dagudu tafada bayi, dan murmushi tayi tana kallon kanta a madubi saikuma akunyace tamake kafada tace “ni bazan ma taba bari yaganni bama rigaba balle ma yaganni” karasa shiryawa tayi abinta cikin wani plain dogon rigan atampa ja batare data daura dan kwali ba tafito zuwa saukowa tayi kasa Mom ce kadai tanashan tea a dinning dayaji kayan kamshi ganinta yasa tace “ko kefa jibi yanda kikai kyau” dan murmushi tayi Mom tace “oya zoki zauna kiyi breakfast” karasowa wajen tayi tace “Mom ni indomie zandafa” baki Mom ta tabe tace “Allah dai yay wadaran naka yabaci, nidai kinga tafiyata bari naje natado Baban ku daga bacci, yadan kwanta shima yazo yay kari” kitchen tawuce itakuma Mom tai sama abinta.



Wani karamin tukunya tadauko sanan tashiga store dinsu tadauko indomie daya da kwai guda daya tafito sanan ta tara ruwa tukunna gas don tadaura  sanan tawanke kwan a tap tazo tasaka a ruwan pot din tarufe pot din sanan takoma store, albasa tadauka awajen, wani black wukan datagani ijiye tunkwal shikadai a store din tadauko tace “hala Mom ta manta da wukan nan a store ne baga wajen wukake duk suna nan ba” takalli cabinet din wukansu wucewa gaban tap tayi tadauraye wukan sanan tasa wukan ta yanke kan albasan sanan tabare albasan tass, kafin tasa wukan taraba albasan biyu ta ijiye rabi akasa sanan tadauki rabi daya tasa wukan tafara yankawa cirrrr wukan yawani irin yanketa a tafin hannu lafiyayyen yanka dayasa batasan lokacin data saki wani azababben ihu ba daga wukan har albasan nafadi akasa daidai lokacin Zayn na shigowa falon yana sanye da 3quater dawata faran riga, jin ihu acikin din Mom yasa yay kitchen din dasauri ganin Khairy tana yarfe hannunta da jini ke tsayaya ya diddiga ko’ina a kitchen din tana ihu tana kuka ga wuka da albasa akasan kitchen din yasa yay kitchen din da sauri hannunshi yasa ya karbe hannun nata data yanke dasauri yay tap da ita kunna tap din yayi ya tare hannun kasan ruwa wani kalan fashewa da kuka tayi zata kwace hannun amma yaki yana wanke jinin daidai lokacin daga Mom har Baffa dasukaji ihunta sun shigo kitchen din dasauri wukanda Mom tagani akasa yasa tai salati. “Innalillahi waya fito da wukan daga store” cire hannunta Zayn yayi daga tap but still jini zuba yake ganin haka yasa Baffa yace “kawo first aid kit dinan Wife” fita Mom tayi daga kitchen din, ahankali Zayn dake rikeda hannun yakalli fuskanta yanda take kuka da yanda har gumi yafeso agoshinta dan ita anytime she’s stress or in pain tuni zakaga gumi yaketo mata a goshi, yanda gumi yasa gashin gaban goshinta ya kwanta ga hawaye na gangarowa daga idanunta datake gogewa da bayan dayan normal hannunta idanunta duka suna kan hannun da jini kefitowa dagakai yasa yaji beat din heart dinshi na raguwa, ahankali kaman wanda wani abu ke controlling yakai hannun saitin bakinshi kafin ahankali yadaura bakinshi kan hannun wajen yankan yanashan jinin yana kallon fuskanta, wani irin sanyi taji bakinshi yayi akan yankan kaman yadaura ice akai shiru yadena mata zafin dayake dawani irin sauri takalleshi tana ware manyan idanunta duk wani hawaye datakeyi ya tsaya chak Baffa dake bayansu tsaye ya tsaya chak yana kallonsu daidai nan kuma Mom tashigo dagudu tace “gashinan Zayn” firgigit! Kaman wanda  yadawo hayyacin shi, bakinshi yazare dagakan ciwon, sanan yana rikeda hannun nata yakarbi spirit din da Mom kebashi yazuba mata akan hannun wani kalan ihu tayi dasauri yashiga hura mata hannun da iskan bakinshi hakan yasa tai shiru, auduga yakarba daga hannun Mom yadaura kan hannun sanan yasa plasta akai kafin ahankali yakalli Baffa yace “Abba akaita tayi tatanus injection” Dawani irin sauri Khairy tace “Baffa no dan Allah dan Allah Baffa kar Amin allura” dan dariya Baffa tayi yace “Khairy Khairy, ai Khairy tun tana yarinya batasan allura wuce kije ki zauna wai mema tazo yi a kitchen din” Mom tace “wai indomie zataci ga abincin normal mutane amman Khairy indomie zataci wuce tafi nadafa miki, wukan nan sabida yanda nasan kaifinshi yasa naboyeshi a store ko ya akayi tafito dashi oho” Mom tai maganan tana daukan wukan itakuma ahankali tawuce tafita hannun namata zafi, Baffa yakalli Zayn dayadan saci kallonta yace “let’s go Son, yaushe kashigo” dan murmushi yayi yace “yanzun nan nazo gaida Mom ne shine naji yarinyar chan na ihu kaman bera”




Juyowa dasauri Khairy tayi jin ita yake kwatantawa da bera, mugun kallo Baffa yamai yace “karka kara kwatantamin y’a da bera” zama tayi a dinning ahankali Baffa da Zayn suka wuce falo suka zauna akan kujera.

Baffa yace “yanzu tunda kagama komi yaushe zaka fara company and start managing everything, I want to retire nima nahuta” anatse yace “Abba bari nadan huta” atsanake Baffa yace “I am giving you just 2 weeks to rest Zayn am I clear” gyadama Baffa kai yayi cikeda girmamawa, saikuma chan yamike tsaye ahankali yace “bari naje wajen Ammi” gyadamai kai Baffa yayi yace “okay yaushe zakaje gaida Baffan naka” dan ware idanu Khairy tayi jin ana maganan gidansu, ahankali Zayn yace “anjima da yamma” ganin yanda Khairy ke kallonsu yasa yace “zakije” dasauri ta gyadamai kai tana murmushi kallon Zayn Baffa yayi yace “to kaje da Khairy idan zaka tafi” dasauri daga Zayn din har Khairy suka kalli juna dan bata taba tunanin Baffa saice Zayn yaje da ita ba ita tazaci kawai zaice taje idan ta shirya Adamu yatafi da ita, wani kalan mugun kallo Zayn yamata sanan yawuce yafita daga dakin.




4️⃣1️⃣





Babu abinda ke tashi amotan sai cool music da AC dataji yamata yawa sanyi ma takeji, kiran wayanshi da aka farayi yasa wakan ya tsaya dan yay connecting wayan da motan ne, harya gama ringing bai daukaba saiga another call shima bai daukaba sai ga third call din again, ganin idan bai daukaba this girl bazata barshi ba yasa yamika hannu yadanna wayan ta jikin motan sanan yakoma yazauna dakyau yana tuki abinshi.

“Hi Zayn” Ayshu tafadi ahankali, shiru yamata bai amsaba, ahankali tace “Faisal told me kagama komi kakoma naija, nima this week zan gama komi nadawo gida, nima a Abuja gidan mu yake” shiru yakarayi baice komiba, ahankali tace “Zayn please I know ina damunka but all i am asking for is kadinga daukan wayana, I love you beyond words” dan zaro idanu Khairy tayi tana tabe baki lallai ne!




Ahankali Ayshu tace “take care Zayn I love you so very much” akufule yace “thanks” sanan yamika hannunshi yakatse wayan yacigaba dajin wakanshi tabe baki Khairy tayi aranta tace “dan wulakanci kawai” 

Wuraren 5:20 sukakai gidansu horn yayi mai gadi yabude musu yaja motan ciki yay parking wani dadi taji ya lullubeta ganin Baba zaune kan kujera a tsakar gida jarida yake karantawa but hangosu yasa yarufe jarida yana murmushi, dan satan kallonta Zayn yayi ganin yanda take murmushi tana kallon Baba yasa yay unlocking motan dawani irin sauri tabude kofan tafito sanan tatafi dagudu tana murmushi batai wata wata ba tawani fada jikin Baba ware idanu Zayn yayi saikuma yadan tabe baki yabude motan yafito ahankali yana cire glasses dinshi sanan yataho ganinshi yasa Baba yace “ke cikani katuwa dake ko kunyan yayanki bakiji” juyowa tayi takalli Zayn murgudamai baki tayi tareda juyamai idanu karaf akan idanunshi sanan tawuce ciki abinta shikuma Baba yashiga gaisawa da Zayn.





Baba bai bari sun tafi ba sai bayan sallan isha’i sabida su Manaf sun dawo suma duk aka taru a falo anata hira, rakosu duk sukayi Matan Baba nama Khairy tsiyan tasaba alkawari tana bata hakuri sanan tabude mata motan tashiga, Baba sai murmushi yake bude musu gate akayi sanan suka fice Khairy nama yan uwanta bye bye.



Kaman ba itane tagama surutu agidansu ba kaman aku shiru tayi tai lamo akan kujera tana kallon hanya, agaban wani babban waje dataga an rubuta Variety Pot Zayn yay parking, kallonta yayi daidai itama ta kalleshi dan batasan mesukazo yi ananba, ganin sun hada idanu yasa dasauri tadauke kanta, ahankali yace “stay in the car I am coming” maida motan yayi yarufe yashiga cikin wajen bayan yabar motan a kunne dan yabar mata AC akunne, wajen tabi da kallo bata iya ganin komi naciki tadaiga maza daban daban na shiga ciki harma da mata, tabe baki tayi ta gyara zamanta abinta babu abinda kemata dadi data fito da wayanta da yanzu takira Aliyu tamasan ya kikkirata yanzu Mtsww.




Tana zaune shiru almost 30min tacika tai fam sabida yanda ranta yabaci bacci ma harya soma kwasheta sama sama taji anyi knocking kofan motan tareda bude motan gabaki daya dan Zayn bai rufe motan ba dama sabida AC daya barimata a kunne, bude idanunta tayi takalli mazaunin direban dan tama zaci shine yadawo, ganin wani saurayi yashigo ciki kaman an wurgoshi yana sanye da Riga da wando irin rugget dinan yadaura handkerchief a goshi yazauna gakuma wani ta kofan inda take tsaye yana kallonta  hannunshi daya rikeda sigari yana busamata a fuska, saikuma taji an bubbude kofofin bayan motan guda biyun wasu maza biyu suma sun shigo sun zazzauna suna rufe kofan back yasa taji kirjinta yabuga da mugun karfi, wanda yazauna mazaunin direban ne yakalleta yace “Madam rufin asirinki shine ki sauka daga motan nan batare dakince ko uppan ba” dudda gabanta nafadi dan tagane barayi ne saida tadaure tace “akanme zan sauka daga motan gidanmu saidai ku ku sauka” hannu wanda yake gaban kofan motan kusada ita yasa zai jawota dasauri tawani irin kwala ihu tareda saka hannunta ta tureshi yay baya tangal tangal zai fadi dan ya kwale sosai, sanan tajuyo na bangaren direban bakinta takai kan shoulder shi tawani irin gantsaramai cizo dayasa ya kwala ihu yana tureta su amman ko gezau mazan bayan suka shiga kaimata duka suna kokarin finciketa ganin tana neman cire ma Oga fata amman taki sakin fatanshi da hakoranta.





Yana zaune yanashan shisha shikadai akujeranshi yanadan lumkunshe idanu dan sosai yasoma bugarda shi kawai jiyayi heart dinshi yabuga at the same time yaji kaman Khairy ta kwalamai kira, tashi yayi dasauri yana kallon agogon shi this is almost 30 minutes daya barta a car shi wlh yama manta da ita, mikewa tsaye yayi dasaurin shi yawuce yafita.



Fincike bakinta nabayan sukayi da kyar daga jikinshi saigata kwaaaa daga namanshi har yadin riganshi abakinta kaman vampire ta tofarmai a fuska sanan suka wani irin jefata kasa kara tayi saida tabugu sosai dan motarshi jeep ce tanada tsayi daidai Zayn nakarasowa wajen dawani irin gudu dayan dake waje yazo zai shiga motan kafin yay one step Zayn ya damkoshi hakan yasa Khairy tamike tsaye da kyar tana ihun security barayi, ganin haka yasa sauran sukaja motan da gudu suka tafi suka bar dayan da Zayn kecin ubanshi ganin karfinshi baikai na Zayn ba ga Khairy na ihun security jama’a barayi gang dinshi sun tafi aka kama shi kuma ya shiga uku yasa yaciro wata yar wukanshi daga bayan wandonshi kaman ance Khairy ta kalloshi dawani irin sauri tazo wajen ko tunani batayi ba wani irin kwalama Zayn kira tayi. “Ya Zayn wuk” juyowa yayi zai kalleta dawani irin gudu ta taho ta tureshi yafadi akasa dan ita azatonta idan ta tureshi barawon zai hakura tunda babu wanda zai chakamawan tana wani murmushi ita adole hero tana kallon fuskan Zayn din gani tayi Zayn yataso dagudu amman ina yachaka mata wukan aciki daidai security da jama’a na zuwa wurin yaron yatafi dagudu security suka bishi itakuma tazaro idanunta atsaye tana kallon Ya Zayn jin wani sharp pain har brain nata jikinta nawani irin bari, ahankali takai hannunta saman cikinta dataji kaman ruwa nabulbulowa nabin jikinta ta shafa sanan tadago hannunta takalla taga jini wani irin baya tayi zata fadi dasauri Zayn yatareta shikanshi jikinshi rawa yakeyi zuciyanshi nawani irin tsinkewa, mutane dasuka taru akansu sukace. “Any Dr anan idan babu akaita asibiti”.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Itadai shuuu kawai taji bamatajin maganganun mutane, sama kawai take kallo tana kallon watan dayay haske sosai ga stars ko’ina, hannun Zayn tarike gam daya bala’in rude ahankali tace “Ya Z…yn ni…..” ganin bata iya magana da kyau the more tana magana the more jini na bulbulowa ga wukan acikinta an hanashi yacire yasa yace “stop talking Ummulkhair” wani irin rawa jikinshi yakeyi maganganun da Mama tafadimai akunne kafin tarasu nadawo mai fresh akai. “Ka kulamin da Ummulkhairy Zayn, nabaka amananta, dan Allah, Khairy bata wani jin maganan yayyinta, Khairy nada fitina, tanada rashin ji, tanada fada, ka kulamin da ita, kasa idanu a al’amuranta, protect her for me, protect my little girl…..” maganan Khairy yadawo dashi daga duniyan tunanin dayaje jin takara kankame hannunshi tace “Ya Zayn zan mutu naje wajen Mama ne nima? Zan ganta ko, ga Mama nan ma tazo wlh” daidai nan aka taya Zayn dagata aka shigarda ita mota manager wajen yace “kai Yayanta ne” gyadamai kai Zayn yayi yama kasa magana, ganin yanda baya hayyacin shi yasa yace”



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



 “bani wayanka nakira iyayenku” aljihun gaban riganshi yanunamai daukan wayan yayi shikuma Zayn ya kankame hannunta gam tunda yake baitaba jin what he is feeling now ba, kaman zaiyi kuka yakeji , yanaji kaman wukan yadawo cikinshi, sumbatu kawai take dayake daga wajen zuwa inda Baffa yace su kaita da nisa shidai Zayn kawai yagansu Awani private asibiti ga Drs kusan biyar agaban asibitin da nurses da gado ga Baffa da Baba da Yayyinta da yanzun nan sukabar gidan duka awajen, gasu Ammi da Batool duka ana jiransu, wajen motan sukayi Drs din suka shiga, wani torchlight suka haska suka kalli yankan da wukan kafin su dakansu suka dauketa suka sata agado Ahankali, amugun rude Baba da hankalinshi ya bala’in tashi yakama hannunta yana kiran sunanta. “Ummulkhairy gani nan inatare dake kinji” batare data bude idanunta ba tace “Baba karka damu….. wajen Mama zani” Baya Baba yayi zai fadi dasauri Baffa yatare shi sanan daya daga cikin Dr din yajuyo yakalli daga Baba har all the family dasukai zuru zuru yace “don’t worry yanzu X-ray zamu fara Muga inda wukan yay puncturing kafin muyi operation mucire she will be fine” hannun Dr Baba yarike idanunshi sunyi jajir yace





Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


“Dr save my Daughter, ban dade da rasa mahaifiyanta ba, dan Allah save my daughter dan Allah” gyadamai kai Dr yayi sanan yakalli Baffa dasu Manaf alamun su tafi da Baba sanan suka kamashi suka zauna, wajen Zayn da sai yanzu yasauko daga motan tayi tana kallonshi arude ganin jini a hannuwanshi da jikin kayanshi tace “are you okay Zayn dina”? Gyadamata kai kawai yayi kamo hannunshi tayi suka shiga asibitin duk suka zauna Baffa nabin Zayn din da kallo yanzu Khairys health first he don’t have time to go into details.




Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️

Batool dake zaune kusada Mom idanunta sunyi jajir ganin wayan Khairy data maida vibration da tun dazu bayan fitanta Aliyu ke kira yanzu ma da magriban nan sai kira yake yasa ahankali ta tashi dasauri Mom tace “ina zaki” ahankali tace “bayi” bayin datagani a reception tawuce sanan tashiga tamaida kofan tarufe tasaka sakata tsugunnawa tayi ahankali tana kallon wayan da Aliyu ke kira still kafin ahankali tai picking takai kunnenta.

“Pickle kinaso kibani heart attack ne, I’ve been feeling restless tun dazu, where have you been” ahankali Batool da muryanta kerawa sosai tace “Ya Aliyu” shiru yayi jin muryan daba na Khairy ba sanan gently yace “is this Batool”? Gyadamai kai tayi tace “y…es” jiyayi heart beat dinshi na bugawa ba kakkautawa jin yanda Batool ke kuka, adake yace “what happen to Ummulkhair”? Anatse dudda voice nata na breaking sabida kuka tace “dazu Baffa yace tabi Ya Zayn suje gidan su, tace bazata ba Bari taje tafadama Ya Zayn daganan I don’t know what happen suka tafi, shine dazun nan duk muna zaune muna dinner afalo wani mutumi yakira Abba yace wai manager wani guri ne that barayi sunyi attacking yaranshi an chakama Khairy wuka aciki…….” Wani irin fashewa da mugun kuka tayi, Aliyu jiyayi zuciyanshi na nema yafito tabaki lips dinshi nawani irin rawa yace “wher……i……my….Khairy….nw” cikin kuka tace “Baffa yafada musu clinic dinmu sun taho da ita yanzu, she’s still alive Dr sunce za’afara yin X-ray aga ina wukan yahuda kafin a shiga da ita operation, mutumin daya kira Abba yace ankama daya daga cikin barayin an ankaishi police station, Ya Aliyu Khairy tacemin you are police please those people should pay for what they did to Khairy, kaga Babanta yanzu kaman zai haukace Maman ta bata dade da rasuwa ba yanzu gashi itama ana nema akasheta, Ya Aliyu I don’t want anything to happen to Khairy” ahankali Aliyu yace “Ummulkhair will be fine” katse wayan yayi sanan ta tashi wanke fuskanta tayi tass kafin ahankali tabude kofa tafito.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️

Almost one hour duk suna zaune a reception din kowa yay tsur, sukaji kukan motan police dayasa dukansu suka kallo wajen, wani kalan wawan parking Aliyu yayi sanan ahankali yasauko daga motan yana cikin full dressing na police uniform dayawani irin fito da kyanshi dakuma haibanshi waje, second police car din dake tareda nashi yay parking wasu police guda hudu suka fito wani irin sarama Aliyu sukayi, ahankali daga Baffa har Baba suka tashi ganin polisawa, gaba Aliyu yayi sauran polisawan biyedashi suka shiga reception din ahankali Baba yamikama Aliyu hannu dan yana ganinshi yagansshi yace “Aliyu waya chakama y’ata wuka meta musu eh?” Anatse Aliyu da idanunshi sukai ja yana rikeda hannun Baba yace “at this moment Baba all information din damuke dashi shine barayi ne su, but we have reasons to believe cewa sun dade suna monitoring activities shiga da fita na gidajenku duka biyun, abinda yakawo mu nan kenan munaso muyi bincike mai kyau sanan mu muku tambayoyi daya bayan daya wanda zai taimaka mana wajen kamo sauran mutanen, sanan yataimaka mana wajen sanin ko kuma rayuwanku nacikin hadari ko baya ciki” gyadamai kai daga Baffa har Baba sukayi, ahankali yace “Baba karka damu koma waye will pay for abinda yama Khairy and Ummulkhair will be fine” ahankali Baba yace “nagode Aliyu, nagode” gyadamai kai Aliyu yayi yace “zan sa boys dina sumuku tambayoyi, ina wanda yake tareda ita abin yafaru”? Aliyu yay tambayan dudda yana shigowa wajen kallo daya yama Zayn dake tareda Ammi yadaura kanshi akan shoulder Ammi yay lamo yaganeshi sabida yanda jini yabata riganshi, nunashi Baffa yayi yace “Zayn zo ayi magana dakai” kallon Aliyu Zayn yayi batare daya tashi ba ahankali Ammi tace “go and give him your statement” ahankali Zayn yatashi yataho gaban wajen inda Aliyu yake tsaye yana kallonshi, tsayawa Zayn yayi agaban shi yakalleshi ido na ganin idanu, cikin wani kalan murya more of angry and arrogRant voice Aliyu yace “who are you!”?.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️





Wani kalan kallo Zayn yamai from head to toe kafin ya yatsine fuska yace “Zayn, her brother” wani kalan wuta Aliyu yaji yana cinshi azuciya anatse yace “wani irin brother ne kai dakana tareda kanwarka mace, a fragile human, da akai creating nata from one of your ribs as a man that’s to show you how weak women are zaka bari wani yay attacking nata harma achaka mata wuka all I see is kai bakai sustaining even a pinch of injury ba” wani kalan kallo Zayn kema Aliyu kaman yanda Aliyu kemai idanunsu duka yay jajir more of wuta yahadu da wuta! Cikin wani irin dark voice dan Zayn daurewa yake dan kowa na wajen yace “what are you trying to pin point anan? Are you saying ina tsaye ina kallo aka chakamata wuka banyi komiba Policeman”? Zayn yakira sunanshi rudely, dan murmushi Aliyu yayi more of murmushin wuta wlh da ace babu su Baffa anan baiga abinda zai hanashi throwing punch at this arrogant stupid guy ba dayakasa protecting Khairy har wani abu yasameta sanan yakalli Zayn yace “care to explain”? Baki Zayn yabude zaiyi magana saiga Dr da bala’in gudu dayasa not just su Baba shi kanshi Aliyu mantawa yayi yana magana da Zayn suka kallo Dr, dawani irin sauri Dr yace “who among you is O Negative?” Atare daga Zayn har Aliyu sukace I, dayasa duka reception din har ma’aikatan suka kallesu yanda sukai magana atare kaman dama jira suke ayi tambayan, da Aliyu da Zayn din kallon juna sukayi suma sanan suka kalli Dr, arude yace “come with me nai testing naku, we have run out of O negative blood, and bazata iya jira har blood bank sukawo jini ba cus tai loosing so much blood, direct transmission ma za’ayi” wani lab Dr yakaisu atake aka deba jinin su akai running test cikin 3 minute sanan matan tabama Dr result din yakalla sanan yakalli Aliyu yace



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



“come with me” sanan yakalli Zayn yace “u are running temperature, I will call in a Dr yazo yadubaka bakada lafiya probably jikinka yay zafi sabida accident dinan ne” Zayn jiyayi ranshi yabaci tashi yayi fuuu yawuce yafita su Baba dasuka ganshi sukace ya akayi Zayn, ahankali yace “I am running temperature, suntafi da police man din theater shi zai bayar” ahankali Baffa yadubi Baba yace “yaron nan mutumin kirki ne wlh” gyadamai kai Baba yayi har lokacin hankalinshi yaki kwanciya sai yaji yarshi tafita daga danger.



Saida aka sashi yacire kayanshi tass sanan aka bashi wani hospital gown yasaka yawanke hannuwanshi kaman yanda Surgeons keyi sanan yasa hula da hulan kafa aka shiga dashi theatre, wani irin kallon wukan cikin Khairy yakeyi da aka haska da wutan theatre cus that’s d only thing yake gani baya iya ganin fuskanta, wani lafiyayyen gado aka nunamai ya kwanta sai a lokacin ya iya hango fuskanta anyi intubating nata tana baccin alluran anesthesia, ga hawaye a gefen idanunta sun bushe, lumshe idanu yayi yanajin ana huda hannunshi suna kome zasuyi ana transfusing jinin jikinshi zuwa jikinta sanan aka cigaba da surgery ana monitoring blood level nashi incase idan yay dropping ayi disconnecting sanan ana operation nata.


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Ahankali yana kallon fuskanta murya chan kasa yace “stay with me Ummulkhair, kika tafi kika barni I will not forgive you, bazan iya rayuwa babu keba, please karki tafi, Aliyu loves you morethan yanda yake son kanshi, please fight for me, fight for the sake of our love kinji” yay maganan yana share wani gajeren hawayen daya gangaromai ta gefen ido.



Yana kwance awurin yana kallon fuskanta dan baiso ya kalli abubuwan da doctors din keyi acikinta yaji suna fadin is out yaji suna clapping hakan yasa yadan dago kanshi yakallesu ganin sun ciro wukan ne yasa yasauke ijiyan zuciya ahankali, Dr yatambayi anesthesiologist din dake monitoring vitals nata. “How far?” Yace “vitals stable, heart rate back to sinus rhythm, all good” cikeda jin dadi Surgeon din yace “alright let’s stitch her up” ajiyan zuciya Aliyu yasauke sanan yakalleta yace “thank you Pickle” saida aka gama operation din tass sanan Dr yajuyo yakalli Aliyu yana ciremai abubuwan dasuka saka a hannunshi yace “weldone young man, angama operation din she’s out of danger, but u need to rest, yanzu nurses zasu fito daku zaa baka wani magani dakuma maltina dazaisa kasami karfi, i advice you karkai wani aikin karfi daga yanzu har safiya just rest okay” gyadama Dr kai Aliyu yayi sanan ahankali yarike hannun yace “thank you Dr for saving Khairy” murmushi Dr yayi sanan yajuya yafita, Nurse din dazata Iftar da Khairy takaita ICU tazo zata gungura gadon ahankali Aliyu da baida wani karfi sosai ya yunkuro zai tashi dasauri tazo wajenshi tace “please kakwanta katashi zaka fadi” murya chan kasa yace “please give me one minute to see her” yanuna Khairy dake bacci, idanunshi kadai takalla taga son Khairy a idanunshi, ahankali tace “okay” sanan takama hannunshi da taimakonta Aliyu ya iya mikewa tsaye sanan yarike gadon da Khairy ke kai ganin haka yasa tasakeshi tawuce tafice daga OR din ta tsaya agaban kofan ahankali.




Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Kallon fuskanta Aliyu yayi yana kallon yanda aka cire intubation din da aka mata tabaki aka sakalamata small small oxygen stream yan kananu ta hanci to help her breath on her own, ahankali yakai hannunshi yadaura kan fuskanta he’s just so short of word all he knows is he’s so grateful to Allah dayasa operation din yazama successful, ahankali yadaura kanshi kan goshinta batare daya daura mata any nauyi ba murya chan kasa yana kallon fuskanta yace “thank you for fighting Pickle, I will not rest sainai brought justice to those that did this to you” shiru yayi sanan murya chan kasa that sounds so weak yace “ba lallai nasamu naganki yanda raina keso ba because of your family but just know that Aliyu loves you alot Pickle” yay maganan gently kafin yakalli pink lips dinta dayaga sun bushe sosai, ahankali jikinshi harwani rawa yake batare daya raba fuskanshi danata ba yawani irin lumshe idanu sanan gently yay placing bakinshi kan nata, yadade ahaka without doing anything he knows this is wrong dan bai riga ya aureta but wani irin sonta dake pulling nashi yasa yashiga kissing mouth dinta calmly and so very very cool yana sauke ijiyan zuciya ahaEnkali wani kalan sanyi na ratsa shi.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Tunda yake in his life he has never ever kissed anygirl sai yau, almost 30sec yadauka yana kissing dinta kafin ahankali yasaki lips dinta da automatically sukai looking so moist yatashi tsaye yana kallonta daidai lokacin nurse din ta turo kofan dakin ta shigo, maidashi gado tayi sanan yana kallon ta tafitar da ita daga dakin, bata wani jimaba tadawo tafitar da Aliyu zuwa wani lafiyayyen daki da uniform dinshi keciki sanan takawo mai wani magani karba yayi yasha sanan yasha malt din data bashi da some vegitable salad daya kasaci dan bai son abincin asibiti, fita tayi hakan yasa yatashi yana tafiya ahankali yawuce yadauki kayanshi yashiga bathroom yasa sanan yafito daidai zai bude kofa yafita Dr yashigo tareda Baba ganinshi yasa Dr yace “ina zaka haka this is 4 nadare kabari safiya tayi please kazauna kahuta” dan murmushi yayi ahankali yace “I am fine” dan baida karfin magana sosai, anatse Baba yakama hannunshi yace “muje kazauna Aliyu dan Allah” ahankali Aliyu yabishi zama yayi kan gadon yadan sauke kanshi kasa dan bala’in kunya Baba yakeji, ahankali Baba yace “this is the second time you are saving y’ata Aliyu, without you Aliyu da hala Ummulkhair bata rayuba dan dukan munan babu mai jinin da ake nema dan haka from the depth part of my heart Aliyu ubangiji Allah yamaka albarka kaji, Allah ya azurtaka da farinciki duniya wa lahira, ankai Khairy dakin hutu likita yace nan da awa biyu ko uku alluran zai saketa tahuta she’s out of danger komi lafiya lau nagode Aliyu” gyadamai kai Aliyu yayi ahankali yakasa kallonshi, karasowa har gaban gadon Manaf yayi sanan gently yamikama Aliyu hannu ahankali yace “Aliyu can u be my friend nima” dasauri Mu’az yazo ahankali yace “wlh narigaka” dan dariya Baba yayi yace “mehaka kubar Aliyu yahuta dan Allah” dan murmushi kadan Aliyu yayi sanan yamika musu hannu suka gaisa kaman yagaya musu yanason kanwarsu bala’in so ma amman yakasa sundanyi some minutes tareda shi sanan suka fice daga dakin dan komawa gaban dakin da Khairy take dan baaa bari kowa ya shiga ba.



Shiryawa Baba yayi tsaf sanan yashigo dakin yana kallonta yace “Ummulkhairy” kallon Baba tayi dasauri tamikamai hannu kaman jira take tafashe da kuka sosai dasauri Baba yayi kanta hannunshi yakai yashare fuskanta yace “common stop crying Khairy na is a strong girl, babu kyau kuka idan akai operation kar dinkin ya kwance, dena kuka kinji” gyadamai kai tayi ashagwabe sanan murya chan kasa tace “Baba I thought zan mutu naje wajen Mama ne” girgiza mata kai Baba yayi yace “kowa idan lokacin shi yayi will go, you are alive Alhamdulillah nagode ma Allah, ya isa kinji I am here now” shiru tayi tana kallon fuskan Baba dan ji tayi kaman taji muryan Ya Aliyu yace mata I am here now, kanta Baba yashiga shafawa da hannu daya dayan hannunshi kuma yana rikeda nata.




Ijiyan zuciya Baffa dake kallonsu yayi sanan yajuya yakalli su Mom da Ammi batare daya kalli Zayn ba yace “kutashi mutafi, anjima dasafe saimu dawo mukawo abinci, Manaf kai Maman ku gida da Maheer, Mu’az saiya zauna da Baban ku anan” Matan Baba batai musu ba tashi duk suka zo zasu wuce juyowa Baffa yayi ganin Zayn azaune yasa yace “tashi mutafi” ahankali yatashi batare dayay musu ba duk suka wuce sanan suka shishiga mota suka wuce.



Suna kawai gida kallon Zayn Baffa yayi sanan yace “with me” faduwa gabanshi yayi rabon dayaga Baffa yay fushi haka harya manta maybe tun yana yaro cus Baffa is a very simple father gashi da raha da son yara, atsakiyan falon Ammi Baffa ya tsaya yajuyo yana kallon Zayn dake shigowa dakin zuciyanshi na tafarfasa, shigowa Ammi tayi waje tasamu tazauna ganin yanda Baffa tun a asibitin talura dayanda take takenshi yana wani share Zayn saikace shine yachakama Yar gwal din wuka. 

Ahankali Zayn yakaraso cikin falon ya zauna ahankali akasa yakasa dago kanshi, juyowa Baffa yayi yakalleshi yahade hannunshi tabaya cikin kakkausan murya yakira sunanshi. “Zayn!” Dagokai ahankali Zayn yayi yakalli Baffa ahankali yace “naam Abba” babu wani alamun wasa akan idanun Effa yace “mekajeyi a Variety Pot”?



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Faduwa gabanshi yayi ahankali yafara kokarin saukar da kanshi kasa dan ko kadan bazai iya ya kalli kwayan idon Abban yamai karyaba, cikin kakkausan murya Baffa yace “look at me Zayn bance ka saukarmin da kanka kasa ba” ahankali yakalli Baffa, cikin fushi Baffa yace “Zayn shaye shaye kakeyi”? Dawani irin sauri Ammi takalli Baffa jin kalman shaye shaye tace “wai Alhaji sabida Yar gwal dinku da aka chakama wuka dan tana tareda d’ana shine haryakai afara tuhuman d’ana da shaye sha…..” dagamata hannu da Baffa yayi afusace yasa takasa karasa maganan cikin kakkausan murya yace “kimin shiru Rabia’atu, I am not ready for sakarcin ki this morning” sanan yamaida kanshi kan Zayn yace “daya daga cikin offisoshin dayamin yan tambayoyi yasanar dani agaban Variety Pot kai parking motanka kashiga ciki Khairy kabarta amota anan waje, wajen babu abinda ake saidawa sai kayan shaye shaye da kayan maye daban daban Innalillahi wa innailaihi raji’un Zayn yaushe kafara shaye shaye tarbiyan danamaka kenan shaye shaye!” Baffa yay maganan yana kallon fuskanshi dan fuskan Zayn bayatabamai karya, kallonshi kadai  yakara tabbatarmai da yes shaye shaye yaje yayi, Baffa jiyayi ranshi na tafarfasa yace “Zayn tayaya zaka dauko mace, Yar yarinya ka ajeta gaban wajen da ake shaye shaye da kasan criminals nanne majalissan su, kashiga ciki kaje shaye shayen ka kabarta inba sakarci da rashin hankali irin naka ba” Baffa yadanyi shiru yana kallonshi kafin cikin ihu da saida gidan ya amsa yace “inda yarinyar nan tamutu tayaya kakeso na kalli mahaifinta dabai dade da rasa matarshi ba iyye? Tayaya!” Baffa yay ihu da saida Ammi tadaura hannunta aka, Baffa yace “kasan menene tsakanina da Baffan ka mahaifin Khairy kuwa?? Bamuda dangantaka ta jini amman duk duniyan nan ko yan uwana basukai Baffan ka matsayi, kima da daraja awuri naba, azuciyata ba daduka duniyan nan Zayn, duk duniyan nan banida kaman Baban Khairy, bakuma zan taba samin kaman Baban Khairy ba, kabani kunya Zayn kabani kunya, kayi karatun addini kasani cewa shaye shaye is haram, duk wani abu aduniyan nan dakesa maye haramun ne annabi yahana sha, bari Khairy ta warke zaka sha mamaki” Baffa yay stairs dasauri Zayn yatashi zai bashi hakuri amman ina harya wuce hakan yasa yadawo yazauna yadaura hannunshi akai, saida Ammi taji rufe kofan Baffa sanan takalli Zayn da duk yabi yadamu ahankali tace “karka damu kasan mahaifinka bazai taba iya fushi dakaiba relax I will talk to him, kaga abinda yasa banson yarinyar nan ba banmason hadinka da ita, nasan cewa zaka dauketa kaje gidansu da ita dana sani ai da bazan taba bari kadauketa ba, akan me zata wani jazawa d’ana bakin jini, har ana kiran d’ana da dan shaye shaye, Zayn dina dako hayaki bayaso, mtswww aikin banza wlh ko ganinka nasakeyi a inda take saina cimaka mutunci Zayn nagaya maka baka ba ita dagayau” saida Ammi tagama surfafamai bala’i sanan ta tashi tai sama yadade zaune awajen sanan ahankali yatashi yafita daga dakin zuwa nashi dakin.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Baki Ammi tabude zata kara magana Baffa yadaga mata hannu cikin fushi, anatse yace “kinsan maisa duka wanan ihun dakike yi danki tozartani bazai taba bani kunya ba”? Dan murmushi yayi yace “sabida agaban dan uwana da yarana kike ko zaginane zaki iyayi” Baffa yasake murmushi yace “auren nan ba marigayiya kadai tai tunanin shi ba har mu nan, duk duniyan nan babu wanda zai rike Khairy amana kaman dan uwanta kuma Yayanta Zayn! Bata fita daga family ba zamu riketa amana dan dan uwanta take aure, banda kwanciyan hankali daya wuce nasan d’ana ke auren Khairy da mahaifiyarta tabani amana, nasanki karki manta na zauna dake tsawon shekaru danmu na farko shekarun shi 36 so babu wanda zai iya bada labarin halinki kaman ni, nariga nasan bakison mahaifiyar Khairy hakan zaisa bazaki tabaso auren shi da yarta ba abu nafarko dayasa naji bazan taba fadamiki ba kenan sai ranan da zan hada yaran nan nafada musu kisani kema, dan haka kome zakiyi kiyi Zayn mijin Ummulkhair ne nan da wata daya za’ayi walima ta tare agidanshi, kutashi kutafi” cikin yaran babu wanda ya iya cewa uppan duk mikewa tsaye sukayi banda Khairy data kasa mikewa tsaye tana kallon Baba idanunta sunyi jazur Baba shima yana kallonta, hannunta Batool takamo zata dagata tace “tashi muje Khairy” ahankali Baba yace “barta Batool” tashi yayi ahankali sanan yadauki wata yar jakan dake kusada shi yabude wani littafi yaciro tana kallon littafin ta tunashi Dairy Mama ne, karasowa gabanta Baba yayi ahankali sanan ya tsugunna agabanta yana kallonta, ahankali cikeda so dakuma tsantsar kaunar yarshi yace “Khairy kingan mu nan we are not bad parents idanma abinda kike tunani kenan, all abinda kikeji azuciyanki yanzu nasani, kina tunani tayaya aka miki aure tun kina karama baa taba sanar dake ba, auren ma da Yayan ki Zayn, wanda baki taba kallo da fuskan so ba, wanda bakisan koshi yana sonki ba” dan murmushi yayi yace “kituna babu aure mai albarka kaman wanda iyayenka suka zaba sanan suka maka banda haka kiyi tunanin auren nan mahaifiyarki dakikafi komi so aduniyan nan tahada ita tama miki shi Ummulkhair, and lastly mahaifiyarki tace nabaki Wanan abin ki karanta idan rana irin tayau tazo gashi” Baba yasamata book din a hannu, wani irin kankame book din tayi gam gam sanan Batool tadagata bin Batool kawai take suka wuce mota suka shiga suka zauna itama ahankali Anty Mariya tashigo taxauna tana kallona Khairy da idanunta suka bushe babu hawaye ko digi bazama ka iya tantance metake going through ba, chan saiga Baba yafito tareda Baffa motansu yazo yashiga yaja suka tafi sanan Baffa yawuce yakoma ciki biyoshi Ammi tayi tafara surfafa bala’i amman tak bai cemata ba



4️⃣6️⃣





Kallo daya Anty Mariya tamai taganeshi cikeda girmamawa tace “bismillah Aliyu shigo” hannunshi yasa ahankali yazare glasses na idanunshi sanan yakalli Anty Mariya ahankali yamika mata ledan hannunshi yace “sauri nake daman na shigo na duba mara lafiya ne bari naje” yajuya zai tafi dawani irin sauri Khairy data yunkuro daga gadon tana yatsine fuska sabida zafin datakeji inda aka mata dinki tace “Ya Aliyu!” Chak ya tsaya batare daya juyoba kirjinshi na tafarfasa dan ana bude kofan idanunshi suka sauka kan Zayn da yanda yaga yana kallon Khairy, juyowa yayi ahankali yazubamata mayun idanunshi hawayen dayaga sun taru a idanunta da yanda yaga tana yatsine fuska sabida tasowan datayi yasa yadago kafa ahankali yashigo dakin batare dayakai wajen gadon ba yay folding hannunshi akirji yana kallon kwayan idanunta da ita kadai zata iya fassara maganganun dake cikinsu asanyaye yace “lay ur back” gyadamai kai tayi kaman Yar baby shi, sanan takoma ahankali ta kwanta back, murya chan kasa yace “Ya jiki”? Ahankali kaman ba itane kemagana da dan kyau ba dazun nan tawani narke kaman wacce ke shirin fashewa da kuka yace “fine” kasa daurewa yayi zuciyanshi namai zafi da ciwo sosai, ahankali yace “meke miki ciwo”? Daga Anty Mariya har Zayn kallonta sukayi, gently takai hannunta tanunamai gefen cikinta, boyayen ijiyan zuciya yasauke sanan yajuya yace “lemme call Dr for you” yawuce zai fita, saida yakai daidai kofa tasake kiranshi amugun hankali. “Ya Aliyu” chak ya tsaya still, kafin chan batare dayajuyo ba yace “I will get the Dr for you, sai anjima Anty” dasauri Anty Mariya tace “sai anjima Aliyu an gode” kallon Khairy yayi nakusan 1min dayaga takife kanta a filo sanan yatashi shima yakalli Anty Mariya yace “bari naje anjima zan dawo” murmushi tayi tace “tom Zayn angode” sanan yawuce yafita, Anty Mariya da takaranci komi that just happen in this room tasauke ijiyan zuciya ahankali tana kallon Khairy datai kaman tana bacci taji anbude kofa Dr yashigo.




Aliyu na gab da tada motanshi yaji anyi knocking glass din motar, juyowa ahankali yakalli wajen ganin Zayn ne tsaye yasa ahankali ya danna botur yasaukar da glass din motar yana kallon Zayn din da idanunshi dasuka dan chanza launi, folding hannu Zayn yayi akirji dan idan baiyi hakaba ayanda kirjinshi yaji yana tafarfasa da mugun kishi zai iya dambe da wanan dan sandan, cikin wani yanayi na rashin mutunci yace “what’s between kai da kanwata”?Wani kallo Aliyu yamai ido da ido kaman yazaro bindigarshi ya bindige Zayn yakeji, akufule yace “go and ask ur sister” wani irin kallo Zayn yamai ganin kome yake takama dashi shima haka Aliyu yake takama dashi yasa awulakance yace “stay away from this hospital and stay away from my sister, I don’t want you handling case din barayin nan zanzo nasa abama wani dan sandan, duk randa nakara ganinka anyway near my sister law zai rabamu” wani matsiyacin kallo Aliyu yamai kafin yadau bakin glasses dinshi yasa a idanunshi yakalli Zayn din awulakance yace “I am the law! So do your worse” yana maganan yadaga glass din motanshi sama  yawani ja motar da mahaukacin gudu yafita dashi daga asibitin yanaji kaman zai mutu da bakin kishi.





Kwana uku Khairy takara a hospital aka sallameta gidansu tace zata Anty Mariya kaman an mata kyauta, fir Batool tace itama gidan Baba zata koma babu wanda yahanata suka koma wajen nan tabama Khairy labarin all abinda yafaru har jinin da Aliyu yabata sanan tace taji Baffa yace ankama duka barayin sun saida motan Zayn din amman an samo motan itama, sanan Zayn suka dinga bi tun ranan farko daya fara zuwa Variety suka ganshi suke binshi dan sunga big boy ne.




Wuraren 11 nadare tai dialing number Aliyu harya katse bai daukaba saigashi yakirata dawani irin sauri tadauka ahankali yace “Pickle” murya chan kasa tace “Ya Aliyu ina yini” ijiyan zuciya yasauke yace “ancemin an sallameki yau ko hope u are good” shiru tadanyi kafin ahankali tace “Ya akayi kasan an sallameni” murya chan kasa yace “I come everyday to check on you dudda bana shigowa dakin” wani kalan murmushi tayi tanason Aliyu over ko Allah ma yasani, murya chan kasa taji yakira sunanta. “Ummulkhair!” Dan faduwa gabanta yayi dan wani irin faduwa gabanta yaje most time idan yakira sunanta haka, murya chan kasa tace “na’am” dan shiru yayi nakusan good 1min, sanan ahankali yace “is there anything between you and dan uwanki Zayn da I don’t know about” dan zaro idanu tayi dan bama tagane kan tambayan ba hakan yasa takasa ma magana, ahankali yasake maimaita tambayan. “Akwai soyayya tsakanin ke da Zayn ne?” Wani irin zaro idanu tayi adan rude tace “ni? Nooo a’a wlh, why will you ask me such question”? Dan shiru yayi sai chan taji yasauke ijiyan zuciya yace “abar maganan tunda kince no I believe you” tsoro taji yadan shigeta ahankali tace “Ya Aliyu are u fine” ijiyan zuciya yadan sauke sanan da kyar yace “I am now!” Yasake yin shiru saikuma chan yace “remember I told you I am a very very jealous person, banda yan uwanki danasan kun fito ciki daya su Manaf I can’t stand inga any man on this earth yana baki any affection look, Khairyyyy I love you don’t you get that, I am crazy and obsess dake” dan murmushi tayi sai yanzu tama gane maganan dayake yadauka ita da Ya Zayn soyayya suke saisa duk yay wani iri Ya Aliyu nada mugun kishi kam, dan murmushi tayi tace “Ya Aliyu kai kadai nakeso aduk duniyan nan, nima I am obsess with you, saisa nama zuciyana alkawari kai nata ne, THE PROMISE OF MY HEART is you” murmushi yadanyi kafin ahankali yace “Khairy inaso naturo iyayena suga Baba” dasauri tace “Ya Aliyu dan Allah kabari nakarasa school kagafa baifi 2month yaragemin ba nama fara project ta online nake turama professor na yana dubawa, kaga I want to enjoy my wedding ayi event kala kala nai rawa kasan na iya rawa” dan murmushi yayi yace “so I heard” dariya tayi tace “dagaske fa” hira tadinga mai kaman ba ita aka sallamo daga asibiti ba harsaida yasaki zuciyanshi sosai sanan wuraren 1 yasata tai bacci badan taso ba.


Kusan kullum sai Zayn yazo gidansu batasan mesa ba kofan tambayan da Ya Aliyu yamata ne hakanan saita fara gujemai, dazaran yazo tagaidashi zata wuce dakinta zatajishi dasu Manaf suna hira afalo Baba ma yadawo duk suhade sai dare yake barin gidan amman ita bata taba saukowa, kullum tana zuwa school tadage da project dinta Maheer natayata yi yanzu ma haka tana chapter 4.


Yau duka duka saura 14 days sufara final exam dinta tadage da karatu sosai, at the same time Baba da Baffa da abokanen su sukaje nemawa Manaf Auren Aisha, Mu’az kuma Auren Maimuna sanan washe gari sunday Baba yasa dukansu su shirya dan gidan Baffa zZasu yau zasuyi family meeting.🥰



4️⃣7️⃣




Ahankali take shiryawa dan ita ko kadan bataso taje gidan Baffan dan bamataso su hadu da Zayn dataga Kwanan nan wani mugun kallo yake mata kaman zai hadiyeta, Batool da harta gama shiryawa tace “wai bazakiyi sauri ba kinata abu ahankali kaman bakida kayan ciki” hararanta tayi tace “dalla chan” bude kofa Anty Mariya data shirya tayi takalli Khairy tace “har yanzu baki gama ba” gyalen abayan data saka tadauka baki tace “na shirya Anty” sanan tadauki jakanta Batool ta tashi suka fito zuwa compund ganin Ya Manaf da Mu’az yasa tai wani murmushi cikeda tsokana tace “angwaye wai kwana nawa aka saka ne” hararanta Baba daya fito yayi yace “ban fadamusu ba sai munje gidan Baffan su zasuji” dariya tayi tace “wlh Baba duk sun kosa” hararanta Manaf yayi yashiga motan shi yace “karki sake kizo motana Batool taho kinji” dasauri Batool tai wajen, Baba yace “manta dasu muje motana kinji” gwalo tamusu suka wuce tashiga motan Baba, Anty Mariya na gaba ita kadai abaya sanan suka wuce batasan mesa ba hakanan taji gabanta nafaduwa dum dum dum, daura hannunta tayi kan kirjinta tana addu’a azuciyanta tana kallon hanya ahaka har sukakai gidan Baffa, Babban falon Baffa sukaje, tunda tashigo taga Zayn na kallonta kaman zai hadiyeta dawani irin sauri tadauke kanta tagaida Ammi data amsata ciki ciki sanan tawuce wajen Mom tazauna kusada kafanta Batool ma tazauna awajen tana gaida Ya Hafiz dake zaune kusada matanshi yana rikeda Babyn su dake bacci, gasu Hassan a zaune kowa a zaune, Baffa na zaune kusada Baba




Ahankali tadago kanta hada idanu sukayi da Zayn dataga yasakin mata wani cool smile dasauri tadauke kanta takalli Baffa dake gyaran murya.

Anatse Baffa yabude taron nasu da addu’a sanan yace “jiya munje gidan iyayen yarinyar da Manaf dakuma Mu’az sukeso su aura, Alhamdulillah komi ya daidaita bamu sanar daku komi gabe da abin bane sabida akwai abinda mukeso musanar daku wanda dukanku nan babu wanda yasan maganan dagani sai Baffan ku nan” yanuna Baba saikuma “marigayiya mahaifiyan ku Manaf” yanuna su Manaf, tsit dakin yayi, gyaran murya Baba yasakeyi yace “an sakawa Manaf da Mu’az ranan aure kimanin sati hudu wato wata daya kenan” murmushi duk akayi Hafiz najan bayan rigan Manaf dake murmushi cikeda tsokana yana kabarda hannunshi sanan anatse Baffa yace “yara nata aure amman asalin Babban yayan gidan nan shiru” dariya Hafiz yayi Ammi ta ballamai harara, anatse Baffa yace “gawata labari” sanan ahankali yafara magana yace “shekaru ashirin dasuka wuce abaya, lokacin Zayn yashiga JSS 1, Hafiz na primary school, su Hassan na Hussaini sune yara alokaci dudda suma primary suke, Maryama wato mahaifiyan Ummulkhairy ta haifi Ummulkhair” Baffa yadanyi shiru, ajiyan zuciya yasauke yace “bayan an haifi Khairy Maryam was very very sick, after series na test and investigations alokacin ne aka fara gano cewa mahaifiyar ki nada blood cancer!” Shiru kakejin dakin kaman ruwa ya hadiye kowa, ganin Baffa yakasa magana yasa ahankali Baba yace “Maman ki was very very scared Khairy son da Mama kemiki tun ranan dakika fado duniya ne, bansan mesa ba kodan agidan marayu ta taso tana matsayin ya mace batasan kowa nata ba tai wahalan rayuwa, kodan sabida taga kema mace ce batason kiyi wahalan rayuwan datayi gashi ance tanada cancer bazatai wani rayuwa mai tsawo ba dan lokacin bama agama sanin kan treatment na blood cancer ba yasa ranan cikin dare ina bacci akan kujera naji Mamanki ta tabani tana kiran sunana” Baba yadanyi shiru ahankali yace “bude idanu nayi naganta zaune kan gadon asibitin rikeda ke a hannu” Baba yakarayin shiru yadan fuzar da iska nai dumi, Ahankali yace “Maman ki was very very sick jikinta yay bala’in zafi tacemin tana ganin one of this days zata mutu dan haka nakira Baffa nacemai idan zai taho yazo mata dasu Manaf dake gidanshi wajen Ammi nacemata to ganin hankalinta atashe yake sanan takara kallonki” Baba yay shiru yace “tana kallon fuskanki tacemin batason Ummulkhairy tasha wahala, sanan duk duniyan nan banda ni babu wanda ta yarda dashi kaman Baffan ki tasan ko Bana duniya sai inda karfinshi yakare akan yarana sabida haka tanason ta aurar dake tun yanzu datake da ranta a inda ko yanzu  yanzu tafadi tamutu zata tafi batada damuwa” Baba yakara yin shiru kowa na kallonshi, handkerchief yaciro daga aljihu yakai kan idanunshi dan ko kadan bai son yay kuka agaban yaran shi, kafadan shi Baffa ya matse sosai yakalli yaran yace “Baban ki yadauka awanan daren Maman ki zata rasu, bayan tamai maganan nan tasashi yakirani awaya, kunga acikin kuryan darenan haka nashiga mota nazo asibitin nan, cikin tsananin zazzabi tana rike dake a hannunta tace tanaso tabani amanarki sanan tana neman alfarma wajena…..” wani irin faduwa gaban Khairy dake kallon Baffa chass takeyi dabama tasan na miyeba, ahankali Baffa yace “Maman ki tace tanaso nahada Ummulkhair da Zayn babban dana wanda Mamanki takeso sosai sun shaku da mamanki sama da su Hafiz ma, tace tanaso nahada ku aure” Zayn da tunda aka fara maganan kanshi ke kasa sai alokacin yadago kanshi yakalle Babanshi dake Magana, Baffa yace “jikin Maman ki yay zafi yay tsanani duk mun zaci zata rasune, Gyadamata kai nayi na nuna amincewa na, tace mukaita masallaci adaura auren, I remember Baban ki yafita waje yadauko keken guragu muka daurata akai muka gungura keken har zuwa masallacin dake asibitin nan dayake nan kaman ba dare ba jama’a duk suna zazzaune some a kwance iri masu jinyan nanne, da sauransu limamun muka kira mukamai bayanin komi ya matukar tausayama Maman ki sanan aka gungurota aka shiga da ita masallaci tana rike dake a hannu limam yadauki microphone aka tada duka mutanen dake bacci” tsinkewa gaban Khairy yahauyi yana dawowa daidai hakama Batool, Ammi, Zayn dakuma Anty Mariya, kowa na kallon Baffa, murya chan kasa Baffa yace “all I had was 20k ajikina haka na bayar kudin sadaki dani da mahaifinki limamin masallacin mahaifiyar ki jama’an dake wajen suka shaida daurin aure tsakanin Ummulkhair Ahmad Muhammad da Zayn Abdullahi Gabas akan sadaki naira dubu ashirin!” 

Khairy jitayi numfashinta zai dauke kunenta yay dummm kaman ta sume ne kaman tafice hayyacinta ne oho ita kanta bazata iya tantance wani yanayi take ciki ba, daga Baba har Baffa murmushi sukayi suka kalli juna, Baffa yace “inda ace Baffan nan naku nada yara mata dayawa zansa yarana maza duka su aurensu sabida inaso muhada zuru’a wanan amincin dake tsakanin mu na abota takoma na jini, saisa bayan mun daura auren muka yanke shawarana sai yaranmu sunyi girma sun mallaki hankalin junansu zamu sanar daku, yanzu ma bikin su Manaf ne sabida munaso muhada bikin su da kuma taron bikin su Zayn ayi atare saisu tare nan da wata daya lokacin Ummulkhairy itama tagama jarabawa tagama makaranta ko aminina” gyadamai kai Baba yayi yana wani irin murmushi, Ammi dajitayi komi na duniya ya tsaya mata chak takalli mijin nata, cikin wani irin masifa tace “Alhaji na dauki cikin Zayn na wata tara, na tsugunna na haifo dana dakaina batare da wata ko wani yatayani ba ninasan ciwon kan d’ana nasan wahalan danasha na tarbiyantan dazai ka kama shekaru kusan ashirin kenan kama d’ana aure baka sanar dani ba wlh wlh wlh kayi kadan!” Ammi tama Baffa magana babu ko shakkan shi guda akan idanunshi dayasa kowa yakalleta shima Zayn yakalleta uppan Baffa baice mata ba hakama Baba duk kallonta suke da Mom da Anty Mariya dasauran yaran.


Hannun kujera Ammi tadaka cikeda bala’in dakin na amsa masifanta jikinta na girgiza tacigaba da magana. “Idan zuri’a kukeso kuhada abotanku yadawo tajini inace nan nan nan ga Batool nan diyar kace maisa baka hadata da Manaf ko Mu’az ba koma Maheer sai akan d’ana Zayn dina, kasan plan din danake dashi , buri danaci akan yaron nan nawa dazaka hadashi da yar gwal dinku? Kasan wace yarinya nakeso Zayn ya aura kasan matsayin Baban ta anan Nigeria kuwa kaga kyan Aisha? Wlh bazaka maidani karaman mutum a idanun kawata ba” takalli Zayn cikeda ihu tace “Zayn kalli fuskan mahaifinka kacemai bakason auren nan yanda sukayi suka hada auren subi haka su warware” shiru Zayn yayi kanshi nakasa shi bazai iyama cewa farin ciki yake ba ko bakin ciki all he knows is yaji dadin wanan labarin dayajita bagatatan haka kaman daga sama.


Baki Ammi tabude zata kara magana Baffa yadaga mata hannu cikin fushi, anatse yace “kinsan maisa duka wanan ihun dakike yi danki tozartani bazai taba bani kunya ba”? Dan murmushi yayi yace “sabida agaban dan uwana da yarana kike ko zaginane zaki iyayi” Baffa yasake murmushi yace “auren nan ba marigayiya kadai tai tunanin shi ba har mu nan, duk duniyan nan babu wanda zai rike Khairy amana kaman dan uwanta kuma Yayanta Zayn! Bata fita daga family ba zamu riketa amana dan dan uwanta take aure, banda kwanciyan hankali daya wuce nasan d’ana ke auren Khairy da mahaifiyarta tabani amana, nasanki karki manta na zauna dake tsawon shekaru danmu na farko shekarun shi 36 so babu wanda zai iya bada labarin halinki kaman ni, nariga nasan bakison mahaifiyar Khairy hakan zaisa bazaki tabaso auren shi da yarta ba abu nafarko dayasa naji bazan taba fadamiki ba kenan sai ranan da zan hada yaran nan nafada musu kisani kema, dan haka kome zakiyi kiyi Zayn mijin Ummulkhair ne nan da wata daya za’ayi walima ta tare agidanshi, kutashi kutafi” cikin yaran babu wanda ya iya cewa uppan duk mikewa tsaye sukayi banda Khairy data kasa mikewa tsaye tana kallon Baba idanunta sunyi jazur Baba shima yana kallonta, hannunta Batool takamo zata dagata tace “tashi muje Khairy” ahankali Baba yace “barta Batool” tashi yayi ahankali sanan yadauki wata yar jakan dake kusada shi yabude wani littafi yaciro tana kallon littafin ta tunashi Dairy Mama ne, karasowa gabanta Baba yayi ahankali sanan ya tsugunna agabanta yana kallonta, ahankali cikeda so dakuma tsantsar kaunar yarshi yace “Khairy kingan mu nan we are not bad parents idanma abinda kike tunani kenan, all abinda kikeji azuciyanki yanzu nasani, kina tunani tayaya aka miki aure tun kina karama baa taba sanar dake ba, auren ma da Yayan ki Zayn, wanda baki taba kallo da fuskan so ba, wanda bakisan koshi yana sonki ba” dan murmushi yayi yace “kituna babu aure mai albarka kaman wanda iyayenka suka zaba sanan suka maka banda haka kiyi tunanin auren nan mahaifiyarki dakikafi komi so aduniyan nan tahada ita tama miki shi Ummulkhair, and lastly mahaifiyarki tace nabaki Wanan abin ki karanta idan rana irin tayau tazo gashi” Baba yasamata book din a hannu, wani irin kankame book din tayi gam gam sanan Batool tadagata bin Batool kawai take suka wuce mota suka shiga suka zauna itama ahankali Anty Mariya tashigo taxauna tana kallona Khairy da idanunta suka bushe babu hawaye ko digi bazama ka iya tantance metake going through ba, chan saiga Baba yafito tareda Baffa motansu yazo yashiga yaja suka tafi sanan Baffa yawuce yakoma ciki biyoshi Ammi tayi tafara surfafa bala’i amman tak bai cemaHta ba.🥰



4️⃣8️⃣





Koda sukakai gida kasama fitowa daga motan Khairy tayi duk Baba na kallonta da taimakon Anty Mariya da Batool suka fito da ita sanan suka shiga ciki Anty Mariya tace “tafi da ita dakinku Batool” wucewa da ita sama Batool tayi sanan tajuyo takalli Baba zatai magana Baba yadaga mata hannu anatse yace “Zayn shine best husband da Ummulkhairy will ever wish for, please karkimin wata magana aikin gama yariga yagama beside auren nan mahaifiyanta tamata shi” shiru Anty Mariya tayi tana kallon Baba saikuma ahankali tace “ok” sanan tajuya tawuce sama abinta.


Suna shiga daki Batool tazaunar da ita abakin gado sanan tamaida kofansu tarufe tasa key sanan tazo gaban gadon da gudu tazauna akasa kanta tadaura kan kafan Khairy tace “Khairy why are you not crying Innalillahi wa innailaihi raji’un, yanzu Khairy kefa matan aure ce, matan Ya Zayn, Khairy what about Aliyu? Ya Aliyu yaya zakiyi dashi? Khairy I am so sad for you not because Ya Zayn is a bad person but because of soyayyan da kukeyi da yanda kike sonshi da yanda Ya Aliyu yake sonki, Khairy how are you going to tell him eh? How”? Sai alokacin wasu kalan hot hawaye suka zubomata, jikinta harwani tsuma yake tana kuka mara sauti itama Batool kasa hanata kukan tayi saima rungumeta datayi suna kuka sosai, sun dade ahaka ganin asma ta na neman tashi yasada sauri tasaki Khairy tawuce tadauko mata inhaler ta dake kan drawer takawo mata tace “shaka and stop crying” ahankali ta shaka but takasa daina kukan, wani kalan bakin ciki da damuwa ne taji ya lullube mata zuciya littafin Mama ma sai kallonshi take takasa karantawa, da kyar da daddare ta iya shan tea tana zaune kallon wayanta kawai take idanunta sunyi jazur sun kumbura, wuraren 10 Batool tai bacci ta barta, tana zaune awajen tana kallon wayan shadaya nayi wayanta yahau ringing wani irin lumshe idanu tayi batare data kalli screen dinba hawaye taji sun zubomata sharrrr ajiki, tunda tasan Ya Aliyu kullum doki take yakirata yaune rana na farko dataji tana tsoron tadauki wayanshi ma dan gani take dazaran yaji muryanta zan gane and tayaya zata iya fadamai Wanan bakin labarin da tasan halinshi yanda yakeda mugun kishi idan wani abu yasameshi this night fa, kozata fadamai labarin nan she needs to think it through sanan tasami hanyan dazata iya fadamai batare datai breaking heart nashi ba dan batason wani abu yasameshi.

Wani kiran nashine yashigo ahankali tadauki wayan, maida wayan silent tayi gabaki daya sanan tasauka daga kan gadon ahankali tadauki littafin Mama, gaban wardrope taje tazauna ahankali akasa tana rikeda book din tana kallo tsoron ma karantawa take hawaye ta share dasauri sanan tabude book din ahankali tafara ni tana karantawa.


Tunda aka haifeta Mama tafara rubuta mata book dinan, taushe bakinta tayi jin wani mugun kukan dayake zuwan mata, sanan tacigaba da karanta littafin page after page, Mama na bata labarin komi wahalan datasha rayuwa kafin tahadu da mahaifinta, da ranan da ciwonta zai tashi da ranan da ciwonta zai lapa haka takebin littafin nan word by word tana taushe bakinta hartakai pages na karshen dataga yanayin rubutun mama ma ya chanza.

“Ummulkhair bansan maisa ba but anytime nake rike da littafin nan dakuma alkalamin nan babu abinda bana iya fayyace miki, yanzun nan kika fita kika tafi makaranta, lokacina yakusa ni kaina inaji ajikina saisa nace bari namiki Wanan one final rubutun. Ummulkhairy inaso kisani cewa duk cikin yaran dana haifo duniya babu wanda nakeso kaman ke! Nasan ance babu kyau uwa tafadima yaranta tafison Wanan kan Wanan nafadamiki hakane sabida inaso ki natsu aduk lokacin da Littafin nan zai sameki. Khairy ni mahaifiyanki nine na zabamiki miji Zayn sanan umarnina ne agareki kiyi zaman aure dashi!” Wani irin sakin book din Khairy tai akasa kawai tashi tayi dagudu tafada bayi ta kunna ma kanta shower tana wani irin kuka tamai sosa zuciya ahankali tace “Mama whyyyyyyyy? Mama Ummulkhairy ki Ya Aliyu takeso, Mama whyyy” wani irin kukan datayi batajin koda Mama tarasu tayi irin kukan nan ba, takai kusan awa daya abayin karkashin ruwa kuka take sanan da kyar ta lallashi kanta tafito bayan ta tube kayan tadauki towel tadaura akirji tabude kofa Littafin taci karo dashi ahankali ta tsugunna tasa hannu tadauka sanan tabude tacigaba da karantawa.

“Nasan bama kiwani san Zayn da kyau ba amman tun kina yarinya Zayn na bala’in sonki kuma yanaji dake, Zayn nada tausayi, yanada Imani sanan yanada kirki ni mahaifiyar ki na yarda da Zayn, karki tunani babu soyayya a tsakaninku so yakanzo daga baya, Khairy kaman yanda nafadi miki abaya na zaba miki Zayn ne sabida inaso hankalina ya kwanta aduk inda nasami kaina nan gaba dan haka y’ata don’t reject Zayn! Accept him and accept the marriage do that for me Ummulkhairy, do it for world best Mom dinki! Karki tadama Baban ki hankali ko yayyinki trust me nasan Baban ki will be going through alot kinsan kuma farin cikin ki shine farin cikin mahaifinki da yayyinki karki basu damuwa kinji Khairy na” Awani irin hankali ta gyadama Mama kai wasu sansanyar hawaye nabin idanunta suna saukowa kasa sanan tasake kallon book din.

“Allah yamiki albarka, inhar kayi abu for the sake of iyayenka dan ka farantamusu rai Allah zai albarkace ki, sanan zai baki kome kikeso cikin sauki, Khairy don’t stress your heart kiyi tunanin anything kibi umarnina dana mahaifinki bazaki taba tabewa ba Allah yamiki albarka daga mahaifiyanki Maryama”




Ahankali ta maida littafin tarufe sanan ahankali ta tashi tamike tsaye jinta take kaman iska zai kadata tafadi wardrobe tabude tadaga karkashin kayanta ta tura littafin sanan tajawo wani dogon Riga tasaka na bacci kafin tazo gado ahankali ta zauna tana kallon wayanta, ahankali tasaka hannu tadauka sanan ta danna 5miss calls tagani na Aliyu saikuma messenge, message din ta danna ahankali.

“Pickle are you sleeping? Maisa kikai bacci dawuri haka? Wait are you fine are you okay? Wani abu namiki ciwo ne??? Umm I am worried”

Hawayen daya gangaronata ta share ahankali sanan gently tashiga scrolling tundaga farkon message din dasuka farama juna harzuwa na yau tana karantawa wani irin jefar da wayan tayi kan gado takifa kanta kan gadon tana kuka, idan ta tuna Aliyu ta tuna yanda yake sonta da yanda yake mugun kishinta saitaji she can’t hurt him, bazata iyaba bazata iyaba! Ganin tana nema ta shige yasa tashaki inhaler ta sanan ta tashi tashiga bayi tadauro alwala wato idan kaga bala’i rasa bacci kake hijabi tasaka kawai tahau kan dadduma tana kuka tana fadima Allah komi itadai tasan tanata salla wajajen asuba barawon bacci yasaceta anan kaHn dadduman.🥰




4️⃣9️⃣





Bayan sunyi sallan asuba tareda Baffa da Zayn suka fito daga masallaci, tun bayan hatsarin nan haryau Baffa fushi yake da Zayn bayama amsa gaisuwan shi sai sa’i sa’i suna shigowa gida hannun Baffa Zayn yakama ahankali yace “Abba listen to me please” chak Baffa ya tsaya sanan ahankali yakalli Zayn din yay shiru, hannu Zayn yakai yakama kunnenshi ahankali yace “Abba nasan namaka laifi amman dan Allah ka yafemin and listen to me” wuceshi Baffa yayi zuwa kujerun dake garden na tsakar gidan masu kyau yazauna sanan yanunama Zayn daya daga cikin kujerun alamun yazo yazauna, ahankali yataho wajen yazauna yana kallon Abba, anatse Abba yace “Zayn shaye shayen ka bani kama laifi ba ubangijin daya hallito mu kamawa” murya chan kasa yace “Abba I know! Tun bayan abin yafaru I couldn’t live up to myself, Abba anytime naji inaso nayi I remember cewa abin yasa kanwata dat I care for wacce mahaifiyanta tabani amanan ta tace na kula da ita takusan mutuwa kan shan shishana, Abba ba lallai ka yarda ba wlh tun ranan ban kara marmarin shan shisha ba I even hated myself for shan shishan, Abba I am sorry” shiru Abba yayi yana kallonshi dan ya yarda da maganan shi dari bisa dari dan idanun Zayn basatabamai karya, ahankali Zayn yasa hannunshi yakama hannun Abba murya chan kasa yace “Abba I love Ummulkhairy tun kafin namasan da zancen auren and I want to promise you abu daya” yadanyi shiru sanan yace “Abba nasan bakada yanda zakayi ne daka tana auren mu tunda kagano ina shan shisha, Abba listen to me I have amended my ways wlh, and Abba namaka alkawari zan rike Khairy amana, bazan bari any harm to fall upon her ba, and I promise you Abba I will forever cherish and care for her batare dana bari Ammi ko anybody yatakurata ba and I will talk to Ammi zata yarda all those drama zata daina kaji Abba” hannunshi ahankali Baffa yakai kan bakinshi ya sumbace shi ahankali yace “Allah maka albarka Zayn” murya chan kasa yace “Ameen” tashi katafi, tashi ahankali Zayn yayi yawuce Baffa na kallonshi jiyayi duk wani nauyi da zuciyanshi yamai ya saukar tunda har Zayn din dakanshi yazo yay accepting mistakes nashi and promise to work on kanshi Abba jiyayi hankalinshi ya kwanta yanzu Ammi kadai tarage yasan ko itama she will come around.






All through ranan akan gado tayishi takasa fita school, takasa daukan wayan Aliyu takasa cin abinci gatanan ne kawai, wuraren magrib Anty Mariya tashigo dakin tana kallon Khairy dake kan gado maida kofan tayi tarufe sanan takaraso tazauna agefen gadon tana kallon idanun Ummulkhairy dasuka kumbura har lokacin hannunta takai tadagota tazauna sanan ahankali tace “maisa baki fadima Baban ki Aliyu kikeso ba” shiru Khairy tayi tana kallonta dan batasan ya akayi tasan aliyu takeso ba, ahankali Anty Mariya tace “nasan kinason Aliyu shima yana sonki tun a asibiti na karanci all of that, maisa baki fadiwa mahaifinki ba eh Ummulkhairy?” Ahankali tace “Anty kona fadamai is too late bazasu iya komi akaiba” shiru Anty Mariya tayi tana kallon Khairy she just wish tanada wani karfi dazata iya magance this whole case but her hands are tight, ahankali tace “Yaya zakiyi da Aliyu”? Wani irin ajiyan zuciya tasauke dasauri takai hannunta tashare hawayen daya zubomata sanan taja hancinta danji tayi majina zai gangaromata tace “zan gayamai gaskiya” ajiyan zuciya Anty Mariya tayi tace “to ki gaggauta fadamishi dan kinsan bai kamata kina magana da namijin daba naki ba ko” gyadama Anty Mariya kai tayi, ahankali Anty Mariya tashafa kumatunta tace “karki damu duk wanda yabi iyayenshi bayaci baya kinji” gyadama Anty Mariya kai tayi, Anty Mariya ta tashi tace “yanzu zan Aiko Batool da abinci yakawo miki kici” sanan tawuce tafice daga dakin, abinci Batool takawo mata kadan taci sanan tai sallan isha’i ta kwanta yau by 9 ma Aliyu yashiga kiranta, kallon wayan Batool tayi sanan ta tashi ahankali tafita daga dakin danta basu waje suyi magana, kasa daukan wayan Khairy tayi a third call dinne tadauka takai kunne.

Cikeda damuwa Aliyu yace “I am sick worried, Pickle what’s happening? Tun jiya I’ve been calling you baki dauka sokike ciwon zuciya yakamani” girgizamai kai tayi da sauri muryanta na rawa tace “n…..o” shiru Aliyu yayi hakan yasa dasauri ta taushe bakinta tana kokarin hana kanta kukan datakeji, yakai kusan 1min yay shiru kawai, kaman daga sama yace “waya saki kuka”? At this point zare hannun kawai tayi daga bakinta tafashe dawani irin kuka Aliyu knows her so well, if she’s happy yasani, if she’s sad yasani, if she cried yanajin muryanta yasani, shiru yayi yana sauraron kukan ta kaman yashiga wayan yazo inda take yakeji, almost good 2min yabarta tai kuka yanda takeso sanan ahankali cikeda iya lallashi yace “I always tell you I am here for you, why will you be crying haaa? Oya yishiru kinji” gyadamai kai tayi tana kokarin Hana kanta kukan, murya chan kasa ahankali yace “maiya sameki why are you crying”? Jitayi wani kukan yazomata tasake saki, cikeda damuwa sosai Aliyu yace “Pickle wai kasheni kikeso kiyi? U want my life eh? Kinsan yanda kukan ki ketabamin zuciya kuwa? Did you have any idea wlh idan kikaji ance I slump and die kece” rage sautin kukan tayi ahankali dan tasan ko karya daya baiyiba, cikeda lallashi yace “tell me menene, nazo gidanku naganki” dasauri ta girgizamai kai dan tasan wlh zai iya tace “a’a” ahankali yace “to what’s the matter”? Batasan yaya ma akayiba jitayi tace “cikina ke ciwo” tasake taushe bakinta jin takasa fadamai gaskiya for the first time yau tama Aliyu karya, shiru yadanyi sanan ahankali yace “sorry, is it MP? All this menstrual cramps shi?” Gyadamai kai tayi ahankali tace “eh” murya chan kasa yace “sorry, sannu, stop crying, kinsha magani kona siyo nakawo miki” ahankali tace “nasha” murya chan kasa yace “then it will stop soon, hey you this MP cramps I command you to leave my Pickle alone or I arrest you, nayi arresting nashi”? gyadamai kai tayi tana dan murmushi tace “eh” murmushi yayi jin tadanmai murmushi yace “okay MP u are under arrest for disturbing the peace and harmony na Miss Khairy, for taking away her smile and bringing her kukan banza back” dan dariya tayi, hakan yasa yace “yes koba kukan banza bane kikemin ba, idan kika ganni saiki kara wani narkewa kina kuka just to worry my heart Khairy angayamiki  ban sani bane” at this point wlh tama manta itane mai kuka dariya tafara sosai, ganin haka yasa yace “haka ranan nazo asibiti u were very fine fa hira ma kike, kina ganina kika kokkobe fuska ashagwabe zaki faramin kuka sabida kawai ki rudani this girl keko don’t worry eventually zan saki kukan mai dalili” dariya tayi dan ita bamata gane last maganan ba, ahankali yace “kinci abinci”? Gyadamai kai tayi tace “but small baran iyaci dayawa ba” murya chan kasa yace “tom anjima idan yalafa sai ki karaci ko” tom, murya chan kasa yace “if it persist tell Batool tasa towel a warm water tamiki massaging abdomen it will stop” gyadamai kai tayi ahankali tace “tom” ahankali yace “gobe zaki school” girgizamai kai tayi tace “no sainaji sauki” Gyadamata kai yayi yace “okay, bari na barki kihuta idan pain din yadawo call me but don’t cry for me again” murmushi tayi tace “saina maka bye” dan dariya yayi ahankali yace “I love you Ummukhairi” katse wayan yayi dip, ahankali tajanye wayan daga kunnenta takasa koda kwakkwaraZn motsi.🥰



4️⃣9️⃣





Bayan sunyi sallan asuba tareda Baffa da Zayn suka fito daga masallaci, tun bayan hatsarin nan haryau Baffa fushi yake da Zayn bayama amsa gaisuwan shi sai sa’i sa’i suna shigowa gida hannun Baffa Zayn yakama ahankali yace “Abba listen to me please” chak Baffa ya tsaya sanan ahankali yakalli Zayn din yay shiru, hannu Zayn yakai yakama kunnenshi ahankali yace “Abba nasan namaka laifi amman dan Allah ka yafemin and listen to me” wuceshi Baffa yayi zuwa kujerun dake garden na tsakar gidan masu kyau yazauna sanan yanunama Zayn daya daga cikin kujerun alamun yazo yazauna, ahankali yataho wajen yazauna yana kallon Abba, anatse Abba yace “Zayn shaye shayen ka bani kama laifi ba ubangijin daya hallito mu kamawa” murya chan kasa yace “Abba I know! Tun bayan abin yafaru I couldn’t live up to myself, Abba anytime naji inaso nayi I remember cewa abin yasa kanwata dat I care for wacce mahaifiyanta tabani amanan ta tace na kula da ita takusan mutuwa kan shan shishana, Abba ba lallai ka yarda ba wlh tun ranan ban kara marmarin shan shisha ba I even hated myself for shan shishan, Abba I am sorry” shiru Abba yayi yana kallonshi dan ya yarda da maganan shi dari bisa dari dan idanun Zayn basatabamai karya, ahankali Zayn yasa hannunshi yakama hannun Abba murya chan kasa yace “Abba I love Ummulkhairy tun kafin namasan da zancen auren and I want to promise you abu daya” yadanyi shiru sanan yace “Abba nasan bakada yanda zakayi ne daka tana auren mu tunda kagano ina shan shisha, Abba listen to me I have amended my ways wlh, and Abba namaka alkawari zan rike Khairy amana, bazan bari any harm to fall upon her ba, and I promise you Abba I will forever cherish and care for her batare dana bari Ammi ko anybody yatakurata ba and I will talk to Ammi zata yarda all those drama zata daina kaji Abba” hannunshi ahankali Baffa yakai kan bakinshi ya sumbace shi ahankali yace “Allah maka albarka Zayn” murya chan kasa yace “Ameen” tashi katafi, tashi ahankali Zayn yayi yawuce Baffa na kallonshi jiyayi duk wani nauyi da zuciyanshi yamai ya saukar tunda har Zayn din dakanshi yazo yay accepting mistakes nashi and promise to work on kanshi Abba jiyayi hankalinshi ya kwanta yanzu Ammi kadai tarage yasan ko itama she will come around.






All through ranan akan gado tayishi takasa fita school, takasa daukan wayan Aliyu takasa cin abinci gatanan ne kawai, wuraren magrib Anty Mariya tashigo dakin tana kallon Khairy dake kan gado maida kofan tayi tarufe sanan takaraso tazauna agefen gadon tana kallon idanun Ummulkhairy dasuka kumbura har lokacin hannunta takai tadagota tazauna sanan ahankali tace “maisa baki fadima Baban ki Aliyu kikeso ba” shiru Khairy tayi tana kallonta dan batasan ya akayi tasan aliyu takeso ba, ahankali Anty Mariya tace “nasan kinason Aliyu shima yana sonki tun a asibiti na karanci all of that, maisa baki fadiwa mahaifinki ba eh Ummulkhairy?” Ahankali tace “Anty kona fadamai is too late bazasu iya komi akaiba” shiru Anty Mariya tayi tana kallon Khairy she just wish tanada wani karfi dazata iya magance this whole case but her hands are tight, ahankali tace “Yaya zakiyi da Aliyu”? Wani irin ajiyan zuciya tasauke dasauri takai hannunta tashare hawayen daya zubomata sanan taja hancinta danji tayi majina zai gangaromata tace “zan gayamai gaskiya” ajiyan zuciya Anty Mariya tayi tace “to ki gaggauta fadamishi dan kinsan bai kamata kina magana da namijin daba naki ba ko” gyadama Anty Mariya kai tayi, ahankali Anty Mariya tashafa kumatunta tace “karki damu duk wanda yabi iyayenshi bayaci baya kinji” gyadama Anty Mariya kai tayi, Anty Mariya ta tashi tace “yanzu zan Aiko Batool da abinci yakawo miki kici” sanan tawuce tafice daga dakin, abinci Batool takawo mata kadan taci sanan tai sallan isha’i ta kwanta yau by 9 ma Aliyu yashiga kiranta, kallon wayan Batool tayi sanan ta tashi ahankali tafita daga dakin danta basu waje suyi magana, kasa daukan wayan Khairy tayi a third call dinne tadauka takai kunne.

Cikeda damuwa Aliyu yace “I am sick worried, Pickle what’s happening? Tun jiya I’ve been calling you baki dauka sokike ciwon zuciya yakamani” girgizamai kai tayi da sauri muryanta na rawa tace “n…..o” shiru Aliyu yayi hakan yasa dasauri ta taushe bakinta tana kokarin hana kanta kukan datakeji, yakai kusan 1min yay shiru kawai, kaman daga sama yace “waya saki kuka”? At this point zare hannun kawai tayi daga bakinta tafashe dawani irin kuka Aliyu knows her so well, if she’s happy yasani, if she’s sad yasani, if she cried yanajin muryanta yasani, shiru yayi yana sauraron kukan ta kaman yashiga wayan yazo inda take yakeji, almost good 2min yabarta tai kuka yanda takeso sanan ahankali cikeda iya lallashi yace “I always tell you I am here for you, why will you be crying haaa? Oya yishiru kinji” gyadamai kai tayi tana kokarin Hana kanta kukan, murya chan kasa ahankali yace “maiya sameki why are you crying”? Jitayi wani kukan yazomata tasake saki, cikeda damuwa sosai Aliyu yace “Pickle wai kasheni kikeso kiyi? U want my life eh? Kinsan yanda kukan ki ketabamin zuciya kuwa? Did you have any idea wlh idan kikaji ance I slump and die kece” rage sautin kukan tayi ahankali dan tasan ko karya daya baiyiba, cikeda lallashi yace “tell me menene, nazo gidanku naganki” dasauri ta girgizamai kai dan tasan wlh zai iya tace “a’a” ahankali yace “to what’s the matter”? Batasan yaya ma akayiba jitayi tace “cikina ke ciwo” tasake taushe bakinta jin takasa fadamai gaskiya for the first time yau tama Aliyu karya, shiru yadanyi sanan ahankali yace “sorry, is it MP? All this menstrual cramps shi?” Gyadamai kai tayi ahankali tace “eh” murya chan kasa yace “sorry, sannu, stop crying, kinsha magani kona siyo nakawo miki” ahankali tace “nasha” murya chan kasa yace “then it will stop soon, hey you this MP cramps I command you to leave my Pickle alone or I arrest you, nayi arresting nashi”? gyadamai kai tayi tana dan murmushi tace “eh” murmushi yayi jin tadanmai murmushi yace “okay MP u are under arrest for disturbing the peace and harmony na Miss Khairy, for taking away her smile and bringing her kukan banza back” dan dariya tayi, hakan yasa yace “yes koba kukan banza bane kikemin ba, idan kika ganni saiki kara wani narkewa kina kuka just to worry my heart Khairy angayamiki  ban sani bane” at this point wlh tama manta itane mai kuka dariya tafara sosai, ganin haka yasa yace “haka ranan nazo asibiti u were very fine fa hira ma kike, kina ganina kika kokkobe fuska ashagwabe zaki faramin kuka sabida kawai ki rudani this girl keko don’t worry eventually zan saki kukan mai dalili” dariya tayi dan ita bamata gane last maganan ba, ahankali yace “kinci abinci”? Gyadamai kai tayi tace “but small baran iyaci dayawa ba” murya chan kasa yace “tom anjima idan yalafa sai ki karaci ko” tom, murya chan kasa yace “if it persist tell Batool tasa towel a warm water tamiki massaging abdomen it will stop” gyadamai kai tayi ahankali tace “tom” ahankali yace “gobe zaki school” girgizamai kai tayi tace “no sainaji sauki” Gyadamata kai yayi yace “okay, bari na barki kihuta idan pain din yadawo call me but don’t cry for me again” murmushi tayi tace “saina maka bye” dan dariya yayi ahankali yace “I love you Ummukhairi” katse wayan yayi dip, ahankali tajanye wayan daga kunnenta takasa koda kwakkwaraZn motsi.🥰



5️⃣0️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Ranan ma bacci barawo yasace ta da kyar ta tashi dasafe tai salla, tana zaune da safe ita kadai akasa taji an bude kofanta hakan yasa takalli kofan Baba ne, shigowa dakin yayi hakan yasa ahankali tace “Baba ina kwana” zama yayi akasa kusada ita shima ahankali yana kallonta yace “yauma bazaki school ba” gyadamai kai tayi ahankali tace “bama komi sai ranan exam zanje” shiru yayi yana kallonta hakan yasa ta saukarda kanta kasa, ahankali yakai hannunshi yatallabo fuskanta yana kallon kwayan idanunta yace “have you been crying Ummulkhairy”? Dan murmushi takakalo sanan ta girgiza mai kai, baki Baba yabude zaiyi magana dasauri ta girgiza mai kai tana hadiye miyau sanan tasa hannunta ta goge hawayen daya zubomata da sauri sanan takalli Baba murya chan kasa tace “Baba nariga na karanta Littafin Mama na karanta komi naciki” shiru tadanyi sanan tasauke ijiyan zuciya ahankali, murya chan kasa tace “Baba babu abinda bazan iyama mahaifiyata aduniyan nan ba she’s my number one dan haka karkaji komi” tasakeyin shiru tana saukar da ijiyan zuciya ahankali tace “I accept Ya Zayn amatsayin mijina wanda kuka auramin Baba” tai maganan tana danne hawayen ta, wani irin farin ciki dataga ya lullube fuskan Baba yasa tasakinmai murmushi ahankali, rungume ta yayi yana mata addu’a sanan yacirota yace “kome kikeso nasaya miki Ummulkhair kifadamin ko yaushe I will buy it for you, I know Maman ki is very very happy dake, Allah miki albarka, bari naje nafadima Anty ki dan ta shirya tafiya Dubai yomiki shopping zaki bita kutafi tare” girgixamai kai tayi tace “zanyi karatu for final exam Baba” “ohhh hakane nama manta tsabagen farin ciki bari naje” Baba yay maganan yana fita daga dakin cikeda farinciki datama dade bata ganshi da irinshi ba tun Mama nada rai, hannu tasa tashare fuskanta ahankali tace “Ya Aliyu I am sorry” ko kadan batasan tayaya zata fadima Ya Aliyu ba ita batamajin zata iya fadamai ba bama tasan tayaya zatai avoiding nashi ba tana zaune tana tunanin Batool tashigo dakin ganin idanunta sunyi jajir yasa Batool tamaida kofan tarufe tazo inda take zaune akasa tazauna tace “Khairy zakije kisawa kanki wani ciwo ne wai, kin fadama Ya Aliyu”? Girgizamata kai tayi cikin muryan kuka tace “Batool I don’t know Tayaya zan fadamai, I can’t hurt Ya Aliyu, I can’t hurt him, I don’t even want to imagine what he will go through Idan yaji wanan zancen, banson wani abu yasameshi” ta karashe maganan tana goge kwalla duk Batool na kallonta tace “to tayaya zakiyi avoiding nashi yanzu I am sure sabida shine kika kasa zuwa school, Khairy you need to think of something” hawaye tadan share sanan takalli Batool tace “na chanza SIM card”? Dasauri Batool tace “ko kin chanza SIM card ai yasan gidan nan, saidai” tai shiru dasauri Khairy ta kalleta tace “saidai me”? Ahankali Batool tace “call him up kifadamai zakuyi tafiya kauyen su Mama garin kuma babu service gobe zaku tafi ba lallai idan yakira yasameki ba saiki kashe wayanki kawai, karki kara zuwa school din saikun fara exam baduk idan kina exam baya zuwa school wajen kiba” gyadamata kai Khairy tayi tace “to kingani dazaran an gama exam din karki kara fita kawai nasan idan aka kaiki gidan Zayn zai chanza miki layin waya shikenan, idan bai ganki ba daga baya yaji kinyi aure zai hakura” shiru Khairy tayi tana kallon Batool Wanan shine simplest thing datasan zata iya dan she can never ever hurt Ya Aliyu, hannu Batool tasa akan fuskanta ta sharemata hawayen tace “kirashi yanzu” ahankali tadauki wayanta tai dialing number Aliyu, saida wayan ya katse sanan yakirata back, ahankali yace “good morning Miss Khairy yaya jikin I was about calling you Boss dina yarikeni a office annoying man kawai, cikin yadena ciwo”? Gyadamai kai tayi ahankali tace “eh” sanan tai shiru dukan cinyanta Batool tayi hakan yasa dasauri tace “Ya Aliyu zamuyi tafiya yau” dan shiru yadanyi kafin ahankali yace “ina zakuje”? “Kauyen su Mama zamu” ahankali yace “ina ne kauyen”? Dan shiru tayi tana kallon Batool data Balla mata harara dan tana jin maganan Aliyun daga inda take, ahankali tace “uhmmm namanta sunan kauyen, nataba zuwa sau daya da ita secondary school” ahankali yace “ok yaushe zaku dawo”? Murya chan kasa tace “sai Baba yafada I don’t know” hararanta Batool tayi hakan yasa tace “Ya Aliyu kauyen babu network” danjim yayi kafin ahankali yace “Tayaya zan dingajin muryan ki to” hawaye taji yazo mata ahankali tace “nima bansani ba” jin yanda muryanta yayi zatamai kuka yasa yace “to shine zakiyi kuka? Ki tambayi Baba sunan kauyen saiki fadamin kafin kutafi duk randa naji nagaji da rashin jin muryanki I will just enter road and come cus I can’t survive this life banganki ba kuma banji muryanki ba, so don’t cry okay” ita kanta jikin Batool wani sanyi taji yayi ko itane she can’t hurt a guy kaman Aliyu haka with pure heart gashinan so cool and calm. Ahankali Khairy tace “okay” murmushi yadan mata yace “mai kukan banza, lemme get back to office kafin boss dina yay firing nawa in the middle of minute nadauki excuse nafito, bye I love you Miss Khairy” ya katse wayan da alamu sauri yake ajiye wayan zatayi taga kiranshi yashigo ahankali tadauka gudu taji yanayi yace “I forgot to tell you Allah kiyaye hanya, kidauki mosquito cream, insecticide and mosquitoe net kauye akwai sauro I don’t want them biting you, and go with indomie da some cereal incase bazaki iyacin abincin kauye ba, and again go with some bottle water karkisha ruwan rafi kinji, take care of yourself for me kinji Ummulkhair” gyadamaikai tayi ahankali tace “naji Ya Aliyu thank you” dan murmushi taji yayi sai chan taji ya tsaya dagudun yace “shitt! Pickle my heart kinda feel sad, I guess I am missing you already, zanyi missing Khairy na very very so so sooo much” murmushi tayi tace “me too” sanan tace “Ya Aliyu ka koma meeting bye bye” takatse wayan dasauri sanan tafada jikin Batool tace “Batool na shiga uku ina cikin tsaka mai wuya yaya zanyi da ALKAWARIN ZUCIYA NA?” Bubbuga bayanta Batool tayi tace “kaddaranki kenan kiyakuri Khairy” da kyar ta lallashi Khairy, sanan tadauki wayan Khairy tacire SIM card dinta tawuce bayi amasai ta Kefa SIM card din tai flushing dan that’s the only thing dazata iyama Khairy dan yasan yanda so yake lokacin dazata kunna wayan nan takira Aliyu bazata sani ba and she needs to let him go dan tanada mijinta, dawowa dakin tayi kawai ta rungume Khairy suna kuka sosai.




Wasa wasa 2weeks kenan bataji muryan Aliyu ba, gidansu sai gyare gyare ake na bikin da za’ayi nata dana yayyinta, Anty Mariya was just like a mother to Khairy dan mai gyara ta dauko daga Sudan aka bata daki daya tana gyara Khairy in and out, Khairy tarame tun tana kuka da hawaye yanzu tasoma mara hawaye kawai gatanan ne, yau zasu fara exam duka duka 1 week zasuyi sugama, shiryawa tayi cikin hijabi har kasa da nikabi duk wani abu datasan Aliyu zai iya ganinta yaganeta dashi ta chanza sanan tafito tama Anty Mariya sallama, amotan da Baba yasiyawa Anty Mariya da direbanta tadauka suka tafi bayan ta sanar da mai gadi idan wani namiji yazo nemanta ace batanan, har gaban department dinsu tasa direban Anty Mariya yayi parking sanan tawuce tashiga exam hall wanda yake zasuyi 2hrs aciki tana gama paper ta bama tajira kawayenta ba tafito tana tafiya ahankali kamshin Aliyu taji kaman daga sama amman tadaure taki dago kanta saima sauri data kara zuwa motan, baya taje zama amman saitaje gaba tabude ta zauna suka wuce saida suka sanyi nisa sanan tajuyo Aliyu ta hango tsaye yana sanye da kananun kaya yana kallon exam hall din tasan ya tsaya ne yana jira afara fitowa kozai ganta jitayi kuka yazo mata nikabin takama afuskanta tana kuka sosai.


Wasa wasa yau Friday yau tagama last paper ta yauma still saida taga Aliyu a school dinsu yarame sosai yay duhu yau kukan datayi yafi na kullum dan tasan yaune last day dazata ganshi dagayau bazata kara fita ba ahaka suka tafi.

Parking sukayi a compund dinsu da ake fentin tsakar gidan, ahankali ta sauko nikabin kanta tacire sanan tawuce flat dinsu, ahankali tabude kofa tashiga Zayn tagani zaune afalon su taci gayu yay wani irin bala’in kyau tana magana da Anty Mariya ganinta yasa yadago kai ya kalleta dawani irin sauri ta sauke kanta kasa ahankali tace “ina yini” sanan tawuce dasauri tai stairs. “Ummulkhairy” yakira sunanta ahankali chak ta tsaya batare data juyoba, tashi Anty Mariya tayi tace “bari kaga naje na dudduba aikin da akeyi Zayn” tai maganan tawuce ta gefen Khairy tai sama abinta, ahankali Zayn yace “Khairy” juyowa tayi ahankali kanta nakasa sanan ahankali ta taho yana binta dawani irin kallo ganin yanda takara kyau fatarta harwani sheki take, zama tayi akan kujera kanta akasa, dan murmushi Zayn yayi sanan yadauki wani Leda da flowers red keciki dake gefenshi sanan yataso yazo har gabanta tsugunnawa yayi agabanta sanan ahankali yadaura hannunshi kan nata wani irin rawa jikinta yafara dasauri takalleshi wani cute smile yasakin mata sanan ahankali yakama hannun nata yana kallon fuskanta yasamata flowers don aciki yace “congratulations u are now a graduate wife” wani sarawa taji kanta yayi dawani irin sauri ta lumshe idanunta sanan tabudesu ahankali takalli flowers din Aliyu kawai taji yafado aranta, sharrrr hawaye yazubo daga idanunta dasauri Zayn yace “why are you crying” hannunshi yakai kan fuskanta zai sharemata dasauri ta kauda fuskanta tace “kaina keciwo I want to sleep thank you” sanan tabi ta gefenshi ta tashi dasauri zata wuce karaf taji yakamo hannunta, dawani irin sauri tajuyo takalleshi tashi yayi ahankali yana kallonta sanan yazo ta gabanta Ya tsaya yay folding hannunshi akirji ahankali yace “I love you Ummulkhair! And I wanna spend the rest of my life with you! I accept you as my wife cus ina bala’in sonki! Allah yajikan Mama data bani ke, and I will forever be greatful to her data zabeni a matsayin soulmate na yarta, Ummulkhairy Zayn love you alot” wani irin fizge hannunta tayi dawani irin gudu tai stairs zuwa dakinta maida kofa tayi tarufe tasa kwado sanan tawani cillar da flowers nashi gefe jikinta na kyarma sabida kalamanshi Aliyu kawai suka dinga tunamata fadawa gado tayi tana kuka ahaka bacci yay awon gaba da ita.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



5️⃣1️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Yau tun safe yama kasa tashi yakai kanshi bayi yay alwala yay salla sabida mugun zazzabin dayake, Abba dabaiganshi a masallaci ba daman jiya Gwaggo tacemai baida lpy amman da Aliyun yazo wajen ya tambayeshi yacemai lafiyanshi kalau yasa yana shigowa gidan daga masallaci straight side din Aliyun yayi ahankali yabude kofan dakinshi yashiga dakin tsaf babu kowa a falo bwdroom nashi yayi yana budewa kakarin aman Aliyu yaji abayi, Aliyu tun yana yaro ciwon shi always comes da amai dawani irin sauri yashiga bayin ganinshi a duke yasa Dad yace “Subhanallahi Aliyu” ruwa yatare Awani bowl yakawo mai da kyar ta kuskure bakinshi sanan Dad ya wankemai fuska sanan yadaukeshi yafito dashi yanajin yanda jikinshi yay zafi, bargo yasa ya lullube shi sanan yajuya zai fita dawani irin sauri Aliyu yakama hannun Dad ahankali yace “Dady” dasauri Dad yazo gaban gadon zama yayi yace “Aliyu menene” ahankali yace “Dad last 3weeks dasuka wuce Ummulkhair called me cewa zasu village, and a village nasu basuda network, Dad I’ve been going to school masu all through last week sabida zasuyi final exam amman batazo ba, Dad I am so worried did something happen to Khairy?” Shiru Dad yayi yana kallon Aliyu duk cikin yaranshi babu wanda yadauko zuciya da hali irin nashi kaman Aliyu, Aliyu bai iyason abu ba, bai kuma iya kin abuba, Aliyu loves da zuciya daya, and he loves completely without rage space, Aliyu is very cool, baida hayaniya da rigima amman akwai zuciya na masifa. Ahankali Dad yace “sabida bakaga Khairy bane yasa kake neman kashe kanka Aliyu? When was the last time kaci abinci” murya araunane yace “I can’t remember Dad” shiru Baban shi yayi yana kallonshi sanan anatse yace “yanzun nan zan taho maka da magani da abinci write down address na gidan su Ummulkhairy for me zanje gidansu, I will go and check her up for you daganan zan nema maka aurenta wajen mahaifinta kafin kaje ka kashe kanka sabida soyayya” Dad yay maganan cikeda tausayinshi dakuma jin haushin shi duka atare sanan ya tashi yafice, yana fita daga dakin sukaci karo da Gwaggo datasa Meena ta turata akeke ganin danta yasa tace “haba nakasa bacci lafiya tun tsakar dare Nike damun ja’irar nan takawoni naduba takadirin yaron nan dan jikina yabani baida lafiya amman taki wai nabarta tai bacci yanzu ma saida nahada mata da kuka tafito dani, wlh Abdul bakai dacen yara ba ko kadan, shikuma ina yake yana cikin ne”? Ganin yanda Maman shi tadamu dan shi kanshi baisan iyakacin irin son da tsohuwar nan kema Aliyu ba yace “muje Gwaggo baida lpy amman yanzu zan bashi magani yayi bacci” kirji Gwaggo tafara tace “hala yanata amai dan cutan Aliyu kenan duk ciwo yay ta uban amai na shiga uku, meke damu shi eh gayamin” shiru Dad yayi ganin yanda tadamu ihu tamai tace “nace kagayamin Abdul” kallon Meena yayi yace “wuce kitafi” wucewa ahankali tayi ta tafi tsugunnawa Dad yayi yace “Gwaggo sabida yarinyar nan dayakeso yake rashin lafiya wai tunda tai tafiya zuwa kauye bai kara samunta awaya ba ko ganinta” fashewa da kuka Gwaggo tayi tace “to laifin wa inba nakaba, tuntuni nike damunka muje mu newama yaron nan Ummulkhairy amman kaki wai abari tagama makaranta yanzu idan wani aka bamawa fa iyye, kaini daki na shirya yau kafata kafanka gidan su Khairiya zamu billahillazi kuwa” kaita dakinta yayi sanan yawuce yahado magani yabawa Aliyu da shayi dakanshi sanan yamai allura kafin mene bacci yakamashi fitowa yayi yakoma nashi dakin shiryawa yayi cikin manyan kaya yana fitowa tsakar gida yaga Gwaggo itama ta shirya cikin lafiyayen atampan ta jajir dashi da aka mata dinkin bubu kan kekenta tai kyau sosai fesfes da ita duk wanda yaganta yaga Yar fulani. Girgizakai kawai Dad yayi cikeda takaici yawuce dakin Aliyu Yar takardan daya rubutamai address yakalla to ai yasan gidan nan gidan Alhaji Muhammad shine Dr Mama data rasu, yasan sunada yarinya mace though baitaba ganinta ba cus yasan basu fadama yarinya Maman nada cancer though baisan sunanta ba, ajiyan zuciya yasauke sanan yafito Gwaggo yasa abayan mota yasa keken ta abaya sanan yashiga gaba yaja motan har zuwa gidan Baba.

Dayake gateman yaganesu budemusu gate yayi sanan yawuce ciki dasauri bin gidan da kallo Dad yayi ganin kaman ma shagalin biki akeyi ko minti daya ba’ayiba Baba dakanshi yafito hakan yasa Dad yasauko daga mota yana bashi hannu yace “Dr barka da zuwa” murmushi Dad yayi yace “mun same ku lpy ina zuwa tareda Gwaggo nake” yay maganan yana ciro keke sanan yazaga yafito da Gwaggo yadaura ta akai ganin tsohuwa yasa har kasa Baba ya tsugunna yace “ina kwana Gwaggo” washe baki yayi yace “lpy dan albarka ya aiki” dasauri Baba yace “Alhamdulillah kushigo yau gidan cike yake dayake ana shirye shiryen biki ne” dasauri Gwaggo tace “bikin wa” murmushi Baba yayi yana bude musu kofan flat dinshi dan a shiga da Gwaggo yace “na yarana” shiga da ita akayi, falon Baffa ne zaune sai Mom dan Ammi bata biyosu ba dan haryau bata shiri da Baffa, sai Anty Mariya afalon, shima Baffa na ganin Dad yace “aaa Doctor kaine” murmushi duk akayi aka shishiga gaisawa Anty Mariya taje takawo musu lemo sanan aka zazzauna akai shiru Gwaggo takalli Baba tace “kaine mahaifin Ummulkhairy” dasauri Baba yace “eh nine” Gwaggo zatai magana Dad ahankali yace “Gwaggo” shiru tayi sanan anatse Dad yakalli su Baba dake kallonshi yace “duk kun sani anan, sunana Abdullahi Abdulwahab Yola, ni likita ne, Gwaggo itace mahaifiyata, matata daya yanzu haka, tafarkon tarasu, yarana bakwai namiji daya sauran duk mata yanzu saura mata uku agida sauran sunyi aure, Yarona na farko sunanshi Aliyu Police ne shi dudda lawyer ne dan abinda yakaranta a school kenan he’s a barrister but he choose aikin police sabida mahaifiyanshi data rasu abinda taso yazama kenan, ASP Aliyu Hydar though Kwanan nan akama karamai girma” dasauri Baba yace “Allahu Akbar ai mu dukanmu nan munsan Aliyu, yanzu dama Aliyu danka ne kaga yanda duniya yake ko amini” Baffa yagayadamai kai sanan yashiga bama Gwaggo da Dad labarin abubuwan da Aliyu yana yarsu Gwaggo sai washe baki take kaman gonna auduga.

Anatse Dad yace “to Alhamdulilah akwai abinda yakawo mu gidan nan naku yau dasafen nan nida mahaifiyata” Dad yadanyi shiru sanan yace “d’ana Aliyu kwanankin baya yazo yasameni yasanar dani yanason Ummulkhairy amman ita tafiso sai tagama makaranta sanan yanemi aurenta…….” Nan yabama su Baba labarin komi har zuwa tafiyan kauyen datace sunyi da yanda Aliyu yadamu baigantaba har zuwa abinda ma yasa sukazo yau shine rashin lafiyan dayakeyi dakin shiru kakeji kaman ruwa yacinye kowa.

Anatse Baba da mamaki ta cinyeshi yakalli Anty Mariya yace “dalilin dayasa Khairy ke zuwa exam da nikabi da hijabi har kasa kenan”? Ahankali Anty Mariya tace “bansani ba gaskiya” shiru Baba yayi sanan ahankali yakalli Dad da Gwaggo ahankali “yashiga basu labarin rayuwansu daga farko har zuwa ranan da Khairy tasani har zuwa yau wanda bikinsu jibi ne ranan asabar yau alhamis…. Baba yakarashe da “Inaga Khairy takasa fadamai gaskiya ne saisa tamai karyan mun tafi kauye” fashewa da kuka sosai Gwaggo tayi afalon dasauri aka shiga bata hakuri, sauka tayi daga kan kekenta ahankali kowa na kallonta dukawa datashiga kokarin yi yasa kowa yamike tsaye ganin tsohuwa tukup tukup zata duka musu dawani irin sauri Baba yatashi yariketa yace “Gwaggo dan Allah karki duka mana” cikin kuka sosai tace “kuwa Allah kubama jikana Auren yarku, wlh sabida marigayiya batasan Aliyu na bane wlh Aliyu zai kulamata da Khairy, zai rikemata Khairy amana, dan Allah kuji tausayin Aliyu na kar wani abu yataimakeshi, Baban Zayyanu Dan darajan iyayenka kubama jikana yarku” jikin kowa yay sanyi babu wanda ya iya cewa wani abu, Dad da jikinshi yamutu da kyar yatashi Gwaggo dake kuka sosai ajikin Baba yakama yanadan murmushi yace “Gwaggo zoki zauna kiga” dakyar ya zaunar da ita sanan yakalli su Baba dakowa jikinshi yay sanyi zaiyi magana Baba yakama hannunshi yace “da ace babu zancen Zayn babu abinda zai hanani baku y’ata naga Aliyu nakuma yaba da tarbiya hankali da natsuwa irin na Aliyu, Aliyu yaro ne nagari nai kare yancin kowa, kuyakuri Dr, kuyakuri” dasauri Dr yace “dan Allah kudena cemin nayahakuri mutum baya wuce rabonshi inda Khairy ta Aliyu ce zai sameta cikin sauki, Allah ubangiji ya Sanya alheri, Allah kuma yabasu zaman lpy, bari nakai Gwaggo gida sai anjiman ku” har wajen suka rakosu Gwaggo na kuka sosai yasata amota jikin koCwa yay sanyi.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




5️⃣2️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Harsukakai gida kuka Gwaggo takeyi hakan yasa Dad yakai Gwaggo side dinta yace “dan Allah Gwaggo kidena kuka kar Aliyu yagane idan yaji sauki saimu fadamai gaskiya dan Allah Gwaggo” bakin zani takama ta warware ta fyace majina tace “Abdul nafi kowa sanin yanda Aliyu keson yarinyar nan tunda harkaga yadauki yarinyar nan dungurungum yakawomin, Allah kai zurfin cikin nan aiko kasan yana sonta tayaya zamu gayamai jibi ne bikin yarinyar nan eh”? Ahankali Baba yace “Gwaggo Aliyu zai hakura daga baya yaji sauki dakaina zan mishi bayanin komi kinji kema kiyakuri bari naje nadubo shi” gyadamai kai Gwaggo tayi tace “tom jeka” fita yayi daga dakin Meena dake uwardakan Gwaggo dataji komi komawa gadon Gwaggo tayi da gudu takwanta kaman kai bacci tana hadiye kukan datakeji Gwaggo tashigo dakin ganinta tana bacci yasa tace “Alhamdulilah nasan inda munafukan nan taji zata iya zuwa tafadimai” tai maganan tana daukan kwaryan maganinta tana dafa bango tafito falo tazauna kurban maganin tayi sanan tabuga tagumi ahankali saikuma tafashe da kuka wiwi.



Ahankali Dad yashiga side din, ganin Aliyun na bacci yasa yadan sauke ijiyan zuciya sanan yajuya zai fita daga dakin kaman daga sama yaji Aliyu yakira sunanshi. “Dad”juyowa Dad yayi ahankali wearing a smile a face nashi sanan yakarasa gaban gadon yace “kai Aliyu ashema nasan mahaifinta nine Dr Maman Ummulkhair kafin tarasu” ganin yanda Dad kemai murmushi yasa ahankali yaji wani karfi yazomai da karfinshi ya yunkura yatashi zaune yana jingina da gado, murmushi Dad yayi yace “ance jibi zata dawo daga kauyen wai rasuwa aka musu saisa suka tsaya, Babanta da Yayyinta kadai ne agida ita da Amaryan Baban nachan kauye, kana damun kanka ne for nothing, danaji haka shine nace okay bayan sun dawo kaima lokacin kaji sauki garau basai muje dakai a nemo aurenta ba, so get on ur feet yarona” dan murmushi yama Dad ahankali yace “thank you Dad” murmushi Dad yamai ya shafa fuskanshi yace “bari naje nadan kwanta tunda yau bazanje aiki ba” gyadama Dad kai yayi ahankali yawuce yafita wani dan karfine yaji yazomai ahankali yatashi yana dafa bango dan har yanzu kanshi na sassarawa yashiga bayi alwala yayi sanan yafito dadduma ya shimfida yayi salla sanan yakoma kan gadon yasake kwanciya yana lumshe idanu.

Wuraren 1 aka bude kofan dakinshi lokacin yanakan dadduma ya idar da salla, Meena ce tashigo dauke da tray da mug na coffee kekai dakuma sandwich agefe karasowa gabanshi tayi akan dadduman ijiye tray din tayi sanan tazauna ahankali tace “Ya Aliyu namaka coffee” muryanta dayaji yasa yakalleta dasauri ganin yanda idanunta sukai jaa yasa ahankali yace “what happen?” Girgizamai kai tayi dasauri sanan tace “bakomi sha coffee please kaci abinci kaga kai kadai gareni” tai maganan hawaye na zubomata gyara zama yayi yana kallonta dan murmushi yayi da kyar sabida yanda kanshi keciwo yace “are u like this sabida banda lafiya”? Girgizamai kai tayi dasauri tana kokarin danne kukanta amman takasa tafashe da kuka sosai dayasa yarike hannuwanta yace “menene Amina?” Kallonshi tayi cikin kuka da bakinciki tace “Ya Aliyu Ummulkhairy ta yaudareka jibi ne bikinta” wani irin daran kaman karan kararrawa yaji zuciyanshi nayi dasauri yakalleta dan baigane inda ta dosa ba, ahankali tace “dazu naji maganganun su Dad da Gwaggo dake kuka sosai afalo bayan sun dawo daga gidan su Khairy, babu inda Ummulkhairy taje tana gidansu bikinta za’ayi ranan Saturday dinan jibi dawani Yayanta Zayyanu inji Gwaggo dan tun dazu sambatu takeyi tana kiran sunanshi, Ya Aliyu I am very very sad for u kaman in kashe kaina nakeji sabida nasan yanda kakeson Khairy, su Dad basuso su fadama wai saika warke amman Bikin Ummulkhairy ranan satur……..” “stop it!” Aliyu yadaka mata wani mummunan tsawa dasaida takoma baya dasauri, runtse idanunshi yayi batare daya budesuba yace “leave this room Meena” dawani kalan sauri Meena ta tashi tafice tana goge hawayen datakeyi, Aliyu yakai kusan minti ashirin zaune inda yake he’s trying yafadama kanshi maganan da Meena tagayamai karyane na Baban shine gaske, kunnenshi keeps hearing bikin Khairy jibi ne Ya Aliyu, wani irin mikewa tsaye yayi kaman zaki car keys dinshi dake kan gado da wayanshi yadauka yawani fice kanshi nasarawa amman bayamaji tsabagen fitinannen kishinn dayakeji azuciyanshi, motanshi yashiga gateman nabudemai yaja motan feee yawuce, gudun dayake akan hanya zaka dauka yazare ne cikin ikon Allah yakawo har kofan gidansu Khairy awani irin hankali yay parking yana kallon kofar gidan dayaga anyi pentin shi gate din gidan a bude ana shiga dasu kanopi da kujeru cikin compound din ana jerawa hannunshi ahankali yadaga yadaura kan kirjinshi dayaji yanamai zafi sosai kaman an zuba garwashi akai, wani irin rawa da bari jikinshi yafara yana kalle kalle baimasan maiyakeyi ba, wani irin bude kofan motan yayi marfin kaman zai balle sanan yasauko daga motan, duk wanda zaiga Aliyu zaisan baya cikin hayyacin shi, shiga gidan yayi yana kalle kalle ko’ina, dayake mai gadi baya wurin yana wajen masu saka kanopi yana tayasu aiki yasa Aliyu yawuce ciki yana kallon banner dasuke kokarin makalawa abango an rubuta #KhaZy saikuma a tsakiya ansa Ummulkhairy weds Zayn! Jiyayi gabaki daya kwakwalwan shi yafara boiling babbabaaa, bayamaji da kyau chak  bakumaya gani da kyau ya tsaya kaman wanda yasami tabin kwakwalwa yawani irin kwalamata kira babu ko shakka ko tsoro atattare dashi. “Ummulkhairrrrrrr!” Wani irin amsawa gidan yayi da su kansu masu aikin saida kowa ya tsaya chak suka juyo suna kallonshi.


Ummulkhairy na zaune dasu Batool da Anty Mariya da Besty afalon sama ana mata lalle akafa daya dan yanzu aka fara, cikin besty yafito tai kyau sosai kaman daga sama taji muryan Aliyu harcikin kashin zuciyanta taji yanda yakirata dawani irin sauri ta zabura tamike tsaye zumbur tana kalle kalle tama manta lalle ake mata hakan yasa daga mai lallen harsu Besty sukace “ke lpy”.

“Ummulkhairrrrrrrree!” Aliyu yasake kiranta akaro nabiyu da gidan ya mugun amsa danko su Anty Mariya saida sukaji dan kaman yay using microphone it was so audible, dawani irin gudu Ummulkhairy tajuya tai stairs su Anty Mariya da Batool suka biyota dasauri, wani irin bude kofan falo tayi tafito ido da Aliyu tayi da Aliyu dake tsaye tsakar gidansu idanunshi sunyi jajir kaman jini wallahi, fuskan Aliyu dakenan fari kal yau fuskanshi yay ja shima, wani irin zufa naketomai akowani bangare na fuskanshi.

 Fuskanshi kadai tagani taji zuciyanta ya tsinke she saw his pain and agony Wanan kuma shine abinda yasa she avoided him takasa fadimai, ahankali tadaga kafa zata tafi wajenshi Besty tarike hannunta, muryanta nadan rawa tace “Besty, Anty Mariya dan Allah kubari naganshi nagayamai gaskiya please, kar wanda yabiyoni lemme talk to Ya Aliyu” karbe hannunta tayi sanan ahankali tashiga sauka daga stairs din tana wani irin kallonshi kaman yanda yake kallonta suma ma’aikatan kowa yacigaba da aikinshi ganin anma San mutumin sunsan juna tunda ga amaryan tafito taganshi, yanda taga Aliyu kaman zaki yasa takasa karasawa gabanshi, dan nesadashi ta tsaya ayanda taganshi kaman zai Chaka mata wuka yake murya chan chan kasa dake mugun rawa tace “Y……Ya Aliy……” bata karasa maganan ba jin wani fizgo hannunta dayayi kaman zaki kawai yashiga janta dawani irin sauri kaman jirgin sama su Mom Anty Mariya dasu maigadi damasu aiki suka biyosu amman ina! Kafin suma fito waje Aliyu yajefata amota yaja motan da arnen gudu ma’aikatan nabin motan dagudu, arude Anty Mariya datafito har waje ba hijabi ba mayafi takalli su Batool da Besty arude tace “kubani wayaZna nakira Baban ku Aliyu yasace Khairy Innalillahi wa innailaihi raji’un”.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



5️⃣3️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Dawani irin gudu Batool tayi cikin gida hankalinta abala’in tashe tadauko both wayanta dana Anty Mariya tana zuwa Anty Mariya data  bala’in rude hankalinta atashe tabama wuyanta dasauri tashiga kokarin kiran Baba, itama Batool a bala’in rude ko’ina najikinta na kyarma tashiga kiran Mom dinta amman wayan Mom baya shiga hankali tashe tama rasa yanda zatayi ta danna ma Ammi kira, Ammi na zaune a falonta tana surfafa ma Zayn bala’i kan auren nan yay shiru kawai yanajinta danshi yafi kowa murnan Wanan news din, kawai kallonta yake yay shiru danshi kanshi bala’in uwarshi yafi karfinshi, ganin wayanta na ringing yasa cikeda masifa tadauki wayan takara akunne tace “ubanme kike kirana ko Gulman kine yatashi” arude cikin kuka sosai Batool tace “Ammi ina Mom Ya Aliyu yazo yasace Khairy yatafi da ita” wani irin kallon wayan Ammi tayi da taciro daga kunne takalla danta tabbatar Batool ne hakan yasa ta maida wayan kunnenta tace “waye kuma Aliyu?” Cikin kuka tace “Ammi saurayin Khairy ne baisan an musu aure da Ya Zayn ba shine yazo yanzu yasaceta please kifadama Abba da Mom mun shiga uku” takatse wayan wani irin ajiye wayan Ammi tayi sanan tashiga tafi da hannu tana kallon Zayn dake kallonta tace “kagani ba kai aka rainama wayau, yarinya itama basonka takeba kai kananan kanamin Yar murya kana bani hakuri nabar batun nan gashinan takira saurayinta Aliyu yazo har gida yadauketa sun gudu shashasha kawai rago” wani irin kallon Ammi Zayn yayi dan baima gane metake nufi da maganan ba Aliyu kawai yasan yagane amaganan ahankali yace “Ammi what are you saying”? cikin bala’in fushi tamai dakuwa tace “kaci ubanka da what are you saying, Zayn wai anya nina haifeka kuwa? Ubanka yakama yahada maka auren da bakasan dashi ba gashinan har gida saurayinta Aliyu yazo yadauketa sun gudu inji Batool” wani irin mikewa tsaye Aliyu yayi yana kallon Ammi dakemai wani mugun kallo tace “idan nabari kazauna da Ummulkhairy amatsayin mata shegiya uwata tahaifeni Zay……” kafin takarasa kiranshi Zayn yawani irin juya dagudu yafita daga  dakin Ammi takwalamai kira amman ina bamayaji sabida yanda zuciyanshi ke tafarfasa kaman zai sume, cikin ikon Allah yakai gidan daidai daga Baba, Baffa su Ya Manaf duk suna kaiwa gidan kana ganin kowa kasan hankalinshi atashe yake atare duk suka shiga falo ita Anty Mariya tana zaune tana kuka daga ita har Batool, Besty damai lalle ne ma sukai zuru zuru kowa cikeda damuwa.





Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️

Ahankali Baba yace “maiya faru”? Kasa amsashi duk sukayi Besty ce tace “Baba dukanmu muna zaune a falon sama, mai lallen nanma bamata dade da zuwa ba an fara mata lalle kenan akafa daya mukaji muryan Aliyun yawani irin kwalamata kira arude Khairy tashiga sauka muka biyota, Baba yana tsakar gida tsaye wlh kaga idanunshi zaka rantse jini ne aciki, bakaramin tsoronshi naji ba Khairy zata tafi nakama hannunta, tace mana dan Allah mubarta taje tamai bayanin komi, shine tawuce tana zuwa gabanshi kafinma tayi magana yaja hannunta…… “ wani irin runtse idanu Zayn yayi yay baya kaman zai fadi dasauri Manaf yatare shi yace “Zayn” dan bude idanu kadan yayi yakalli Manaf sanan ya fuzar da iska, Besty tace “dukan mu nan har masu aikin kanopi saida muka bishi amman babu wanda ya iya cimmishi yasata amota yatafi” tarushe da kuka dakin yay shiru, awani irin zuciye Zayn yaciro wayanshi zuciyanshi na tafarfasa yace “I will inform the police” yashiga kokarin dialing wata number, jiyayi an karbe wayan daga hannunshi hakan yasa yadago kanshi dasauri yaga Baba ne, katse kiran Baba yayi sanan yabubbuga kafadanshi anatse yace “I know you are hurt Zayn amman nobody is involving police in this case, nasan Aliyu Zayn na yarda da tarbiyan Aliyu dudda ba d’ana bane Aliyu bazai taba, I mean it Aliyu bazai taba cutar da Ummulkhairy ba, rabuwa da masoyi nada ciwo kota wani kala kona mutuwa ne kona aurene, I know fushi yake, kuma zuciya ce tadebeshi har yazo nan yatafi da Ummulkhairy, zai dawo da ita kayakuri babu abinda zai sami Ummulkhairy, lokacin dabai Santa baba yataimaketa yadawo da ita gida lami lafiya balle yanzu, dukanku kuyakuri” yakalli su Mom yace “kudena kuka lemme call his father”.


Dad na zaune kan dadduma dan yamakara yanzu Mami tazo tadatashi sallame sallan shi kenan yaga wayanshi na ringing, mika hannu yayi ahankali tadauki wayan Ammi dake hadamai shayi a mug tajuyo tadan kalleshi ganin Baba ne abin bakaramin mamaki yabashi ba ahankali yace “tomekuma yafaru lpy suke kirana ko wani abun ne?” Dad yama kanshi tambayoyin kafin ahankali yay picking call din yakai kunne, zumbur din da Mami taga yayi yasa tasaki tea datake hadamai tazo wajen tace “menene Alhaji lpy” hannu yadaga mata alamun tayi shiru yana sauraron maganan da Baba ke gayamai kafin ahankali yace “Innalillahi wa innailaihi raji’un, Innalillahi wa innailaihi raji’un” yama kasa fadin wani magana sama da haka kafin ahankali yace “Alhaji dan girman Allah kuyakuri, I am so ashame of myself, banmasan fitan Aliyu ba, da Izinin Allah duk inda Aliyu yashiga saina nemoshi zakaji daga gareni, assha wanan labari baimin dadi ba” zare wayan yayi ahankali daga kunnenshi Mami data damu sosai tace “wai Meya faru ne”? Cikeda damuwa yace “yarinyar da Aliyu keso Ummulkhairy daya nuna muku amma yarinyar aure tun tana karama ita kanta bata sani ba yau damukaje nemama Aliyu aurenta…….” Gabaki daya abinda ke faruwa Dad ya sanar da Mami cikeda tashin hankali tace “ina Aliyu yakai Yar mutane yanzu, ohhh Allah kayayema Aliyu Wanan zuciya tashi jama’a, ina yakai yarinyar mutane” fita daga dakin Dad yayi dasauri zuwa dakin Gwaggo cikin fushi yakalli Gwaggo dahar lokacin kuka take idanunta sun kumbura yace “Gwaggo ke kika fadama Aliyu yarinyar nan anmata aure” wani kalan zaro idanu Gwaggo tayi tace “nikuma nida tun dazu nike nan wajen kuka nike inagayawa Allah kome zakama magana haka, yanaganka haka menene wai”? Gwaggo tai maganan ganin damuwa karara a idanun dan nata, cikeda damuwa yashiga bama Gwaggo labarin abinda Aliyu yayi firgita tayi tamike tsaye tace “mun shiga uku jama’a wani irin bala’i Aliyu ke neman jefamu ciki, yo a ina yasan da maganan nan”? “Ninagaya mishi Gwaggo” kaman daga sama sukaji muryan Meena data fito daga uwardaka ta tsaya idanubta sunyi jazur, ahankali takaraso gabansu murya chan kasa tace “Dad I am sorry nina fadamai, Ya Aliyu is suffering abanza, gwara yasani and get over her yaden……” wani mugun mari da Dad ya kwasa mata ita kanta Gwaggo daba ita akamawa ba saida ta kwasa uban ihu, cikin balain fushi tace “kai Abdul kashe min jika zakayi ne” ta riko Meena data fashe da mugun kuka, cikeda zuciya Dad yace “angayamiki I don’t know abinda nakeyi ne danai deciding to hid the truth from Aliyu eh Aminatu? Nine ubanku I know halayyanku daya bayan daya, nasan waye Aliyu, nasan kalan zuciyan d’ana idan yanzu yaje yay abinda zaiyita nadama daganan har karshen rayuwanshi fa? How do u want me to handle this case? He kidnapped this girl kinsan idan suka kaima hukuma kara yayanki da kikeso kike gani abin arziki kikamai by telling him will spend the rest of his life agidan yari kinsan dahaka, hauka kikeyi ne Aminatu” yasake daga hannu zai daketa Dasauri Gwaggo tashiga gabanshi tafashe da kuka tace “dokanni Abdul ai abinda nake fadi kenan halinka sak Aliyu yadauko ko abu guda bai rage ba” takalli Mami dake tsaye awajen kofa tace “kawomin ruwa” takama Dad da jikinshi kerawa tsabagen bacin rai yana kallon Meena dake kuka sosai ta durkusa tazaunar dashi daidai Mami takawo ruwan karba Gwaggo tayi tace “yi bisimillah kasha Abdul yanzu ba lokacin fushi bane, sha dan Allah yi bisimillah” ahankali yay bismillah sanan yakafa bakinshi yasha, dan dama dama yaji, janye ruwan Gwaggo tayi daga bakinshi tace “yanzu ina kakega Aliiyu zai kai diyar mutane”? Ahankali yace “bansani ba Gwaggo but zansa all properties nashi da gidajen shi adubamin su daya bayan daya hopefully he will be in one” ahankali Gwaggo tace “to tashi kaje kayi abinda yakamata kadaina fushi Allah zai daidaita mana komi ka gwara kiranshi?” Gyadama Gwaggo kai yayi yana mikewa tsaye still dialing number Aliyu yace “all his lines are not going, duka layikanshi Gwaggo basa zuwa bari naje” yay maganan yana fita Mami tabishi da sauri zama dirshan Gwaggo tayi akasa tace “Ya Allah kashigo Wanan lamarin oh ni Tani, wani irin bala’i Aliyu ke neman jefamu, yaro yaje yasace Yar mWutane Amarya na shiga uku na lalace”.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



5️⃣4️⃣




Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Juyawa Zayn da zuciyanshi ke tafarfasa yayi stool dake gefenshi yay wani irin ball dashi dayaki kofa dayasa kowa ya kalleshi cikeda damuwa Manaf yadafashi yace “calm down Zayn” cikin tsananin bacin rai dababu wanda yanashan Zayn nada irinshi yace “don’t tell me to calm down Manaf! Wayeshi? Meyake takama dashi? What gives him d right yashigo har gidan nan yadaukan mun mata eh, wlh wlh saina kashesh…..” dasauri Baffa yatashi dakuwa yamai rai abace yace “kaci gidanku Zayn, lafiyan ka kalau dazaka faracin alwashin kisa? Awanan rayuwan anything u are doing try not to be selfish, bawai ina justify abinda Aliyu yayi bane is totally wrong but we all are humans, all of us have flaws, put yourself in his shoes for once and just imagine kanka idan kaine yaya zakayi? How will u handle new din wacce kakeso kuma kuke soyayya jibi ne aurenta how???? Kowa have his own way of handling emotions Zayn, now is not time for fada or hauka is two choice komubi komi ahankali musamu yadawo da Ummulkhairy kokuma mukabi ta karfi kota hayaniya muga akasin haka so just calm down kabarmu mu manya muyi handling abin” fuuuuu Zayn yawuce yafita, goshi Baba yadafa yana salati ahankali, dafashi Baffa yayi yace “don’t worry Allah zai magance mana Wanan matsalan” ahankali Manaf yace “Baffa ko za’a daga bikin mune” girgizamai kai yayi yace “a’a Manaf babu abinda za’a chanza kucigaba da shirye shiryen biki, Aliyu yarone mai hankali da natsuwa Khairy zata dawo gida kunji, nasan duk inda yake mahaifinshi zai nemoshi kutashi kuje” fita su Manaf sukai daga dakin zuwa flat dinsu da Zayn yayi.

******



Wani irin gudu da Aliyu keyida mota yasa tama fashe da kuka tana jijjiga marfin kofan motan kozai bude amman akulle tafita ganin yana neman kashesu, tunda take bata tabajin tana tsoron Aliyu ba sai yau sabida yanda taga yanayinshi, wani daji taga suna shiga arude takalleshi tace “Ya Aliyu ina zaka kaini dan Allah kamaidani gida, dan Allah kayakuri” kaman baimasan tana magana ba gani tayi sun bullo gaban wani container mai kyau, parking motan yayi motan na dukan jikin wata bishiya dayasa ta runtse idanunta jikinta narawa yawani irin bude mota yafito yazagayo ta inda take yabude kofan komawa baya tayida sauri tana kallonshi tana girgizamai kai tana kuka. “Ya Aliyu ina ka kawoni dan Allah kamaidani gida, bazan bikaba” wani irin fizgota yayi daga motan tashiga kokarin kwace kanta tana ihu chak yadauketa yana zuwa gaban container yasa password agaban kofan sanan yabude kofan yashiga lafiyayen daki ne ga kujeru harda tv akwai aciki da AC aciki, wani irin jefar da ita yayi akan kujera dawani irin sauri ta tashi dagakan kujeran tana kallonshi tana komawa baya kaman yanda yake kallonta yana kulle kofan yana dannamai password, saida yagama sanan yadago da kanshi yana kallonta dawasu irin idanu da sukai kaman jini tsabagen jan dasukayi, ko’ina najikin Khairy rawa yake kirjinta nabugawa fas fas tana kallonshi tana komawa baya, ahankali yadaga kafa yataho yana biyota yana kallonta tana komawa baya, jin bayanta abango yasa dasauri tajuya takalli wajan ashema takai karshen dakin, dawani irin sauri tajuyo zata gudu taganshi tsaye gabanta dab da ita dan tanajin saukan numfashin shi akan fuskanta, faduwa gabanta yasakeyi tazo tagefenshi zata wuce yatareta ta hanyar saka hannunshi daya abango sanan dayan hannun nashi yawani irin dakan bangon dasaida ya lotse azuciye yace “why did you lie to me!” Yamata wani irin ihu dasaida tajishi har cikin brain dinta, tunda take bata tabajin tarude takuma tsorata irin wanda takeji yauba kasa kallonshi tayi dan jitake idan takalli idanuwanshi zata iya fitsari ajiki, sake mata ihu yayi yasake dukan bangon. “Maisa kikamin karya Ummulkhair” wani irin fashewa tayi da kuka dake tsuma rai har lokacin takasa kallonshi tace “Ya Aliyu I don’t want to hurt you, nima bansan anmin Auren ba tun ina yarinya akamin, Ya Aliyu I know you nasan kishinka, banson inyi hurting naka, dan Allah kayakuri kabarni natafi kaga gida xa’a damu jibi bikina” Wayyoo Allah na Aliyu jiyayi kaman ta watsamai gishiri aciwo wani irin fizgo gaban riganta yayi gabaki daya tafada jikinshi yawani irin matseta yana kallonta da idanunshi kaman na wanda yay shaye shaye yace “nikike gayama jibi bikinki Ummulkhair”? Girgizamai kai tayi  tana wani irin kuka mai sosarai ahankali tace “Ya Aliyu ina sonka this thing is hurting me sama da yanda yake hurting naka, Ya Aliyu kayakuri ka manta dani Allah zai baka wata wacce tafini” wani irin wurgata yayi bayanta yabugu da bango yanuna zuciyan shi kaman wanda yazare yace “what about PROMISE OF OUR HEART? Ina ALKAWARIN ZUCIYAN mu yaje? Who told you I want any woman in this world samada ke? I gave you my heart gabaki daya batare danarage space ko kadan aciki ba, maisa baki fadamusu bakison Auren ba?Maisa baki fada musu kinada wanda kikeso ba? Maisa bakice araba Auren ba? Maisa kika yaudareni kikaci amanata kikamin karya eh? Why did you toil with my feelings”? Ahankali Ummulkhairy ta tsugunna danji tayi kafafunta can not hold her any longer, kafafunta sunyi sanyi kaman yanda jikinta dakowani gaba dake ciki yay sanyi, murya chan kasa that sounds very very weak tace “Mama tahada auren Ya Aliyu, is my mother’s dying wish, bazan iya rabuwa da Ya Zayn ba! Ya Aliyu I’ve already accepted this marriage! I am ready nai rayuwa da Ya Zayn sabida mahaifiya…….” Kasa karasa maganan tayi sabida hawayen datagani sun sauko daga idanun Aliyu duka biyun masu bala’in dumi yana wani irin kallonta, kallon dake kunce da maganganu dayawa, da kunci dayawa, da bakin ciki dayawa. Jitayi zuciyanta yawani irin tsinke takasa karasa maganan datake, wani kalan kunci takeji aranta seeing Ya Aliyunta cry, Aliyu is hurt because of her jitayi babu abinda kemata dadi azuciya, murya chan kasa dake rawa sosai tace “Ya Aliyu I am so sorry, I am sorryyyyyy babu abinda zan iyayi dazai gyara komi, yanda nadauki abin amatsayin kaddara kaima ka daukeshi ahaka, alokacin da mumini zaiyi accepting whichever kaddara da yazo way dinshi saikaga for that imani dayayi Allah yasakamai da wani kyakkyawan abu dabai taba tunanin zai samu ba, Ya Aliyu kayakuri dan Allah”  yadade ahaka yana share hawayen dasuka kasa daina zubomai yakai hannunshi yana sharewa sanan ahankali yajuyo da fuskanshi yakalleta da jajayen idanunshi saikuma yajuya yay wajen wani kujera dayake ijiye daban adakin, daga foam na kujeran yayi saiga wata Yar karaman bindiga daukan bindigan yayi yajuyo yana budeta ganin bindigan is fully loaded yasa yataho inda take a tsugunne tana share hawaye, hannu yasa yadagata tsaye dasauri takalleshi ganin bindiga a hannunshi yasa tawani irin zaro idanu jikinta ya shiga kyarma tace “Ya Aliyu mekakeyi” hannunta yachapke cikin zafin zuciya yasaita hannun nata kan bindigan tana kokarin fizge hannun nata amman yasaita kan bindigar da karfi dayaji yakama hannunta gam kan bindigan sanan yakai gun din daidai saitin heart nashi yakalleta kaman yanda tawani zaro idanu tana kallonshi birkicewan datayi yafi na dazu tace “Ya Aliyu mehaka? What are you doing Innalillahi” damke hannunta yayi da kyau ta yanda bazata iya zare hannunta ba ahankali yana kallon hawaye na zaro idanunshi yace “Pickle kince kinyi accepting Zayn amatsayin mijin ki ko sabida wish din Mama ne, kinyi accepting Auren zaki zauna dashi” yadanyi shiru sabida hawayen dasuka sake zubomai kafin yay wani irin huci yace “instead of kalaman nan naki sudinga kasheni slowly I have a better idea miki, just shoot me lemme die in peace, shoot me!” Yay wani mahaukacin ihu yana gyara yatsanta akan trigger dayasa ahaukace dan duka ta daburce tafashe dawani irin kuka tana girgizamai kai tama kasa magana, ihu yamata yace “kill me Ummulkhair, ki kasheni saiki huta kiyi rayuwan Auren ki in peace I will never be a problem for you in this life, wlh the only way dazaki iya rayuwa da Zayn shine kawai ki kasheni I am giving u the best option now, kill me and enjoy marriage dinki matan Zayn, shoot me Ummulkhair!” At this point numfashinta ma neman daukewa yake kawai girgizamai kai tayi hawaye kaman kogi takasa ma magana kawai girgixamai kai takeyi, gyara hannunta yayi jin yana kokarin pulling trigger da yatsanta and the only way she can save Aliyu from kashe kanshi yadawo hayyacin shi is just one way. 




Cikin wani kalan karfi karfi ta tureshi da dayan hannunshi sanan ta fizge hannunta dagakan bindigan taredayin wani irin sound ihu da sunanshi kai tsaye. “Aliyu!!!!” Gabaki dayan dakin saida yadauki yanda takira sunanshi yana echo adakin dayasa ya tsaya chak da jajayen idanunshi yakalleta, jitayi duk wani tsoronshi ya tsaya tadake dan she needs to help him and set him right tariga tai aure, tai aure, itada Aliyu can never work so she just have to help him yay getting over her, or even hate her. Cikin wani kalan kakkausan murya dako ita batasan tanada shi ba takalleshi right in the eye kaman yanda yake kallonta tace “why are u selfish maisa kacika son kanka dayawa Aliyu?” Tai maganan bitterly, tace “kataba gayamin sabida Maman ka dudda u were a barrister kaje kazama police from a scratch ma you fulfill wish na mahaifiyarka then who are you to try to meddle in the business of fulfilling my own mother’s  wish bayan kai u are doing the same thing who do you think you are Aliyu!” Tai maganan tana kallonshi, kafin Awani irin zuciye tanunashi da yatsanta tace “uwa batafi uwa ba Aliyu! Soyayya is nothing compare to abinda mahaifiyata keso, zan zabi Ya Zayn so dubu akanka dan yafimin kai sau dubu cus shine zabin iyayena! Aurena dashi zai fimin albarka kan Auren ka dan u are nobody Aliyu pace a policeman, Ya Zayn is an Auditor, Business Auditor sorry I mean International Business Auditor unlike kai da u are nothing but a Divisional Police officer!” Aliyu jiyayi yayi baya zai fadi tsabagen yanda yaji karfin jikinshi yakare dasauri yakama bayan kujera yajuyo yana wani irin kallon Ummulkhairy dat was pointing finger at him tana kallonshi tsap jiyayi idanunshi na juyawa, cikin wata irin murya dabata fita sosai yace “Ummulkhair!” Yana kokarin yakara gasgata abinda take fadi, gyadamai kai tayi tana danne kukan datakeji ganin how she’s hurting him adake tace “yes Aliyu after zama danayi nayi all those analysis tsakanin kaida Ya Zayn, waye kai who know you, sainaji gwara Zayn, Zayn is better than you in each and every way na rayuwa! Zayn yafika komi! Gata, aji, kudi, ilimi duka yafika, Zayn is a PHd holder kaiko wani kwali kakeda? Saisa na yanke shawara namayi flushing SIM card dina sabida banson mutum irinka nakira na, listen attentively da wanan maganan dazanyi Aliyu, ni UMMULKHAIR MUHAMMAD I love mijina! I so sooo much love my husband, Ya Zay………” kawai gani tayi idanun Aliyu sun juya sama kafafunshi dake kasa sun daga sama yay wani irin suma ta saman kujera kanshi yay kan kujera zuwa kasa yaWwani irin mummunan faduwa daFyasa tai wani gagarumin ihu. “Ya Aliyuuuuu”.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




5️⃣5️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Dawani irin gudu tai kanshi tana kuka sosai, hannunta takai tadaura akan fuskanshi tana bubbugawa ahankali tace “Ya Aliyu dan Allah katashi, Innalillahi mena maka haka, Ya Allah kaduba zuciyata I don’t want wani abu yasami Ya Aliyu” jin baya numfashi yaki farkawa yasa tamike tsaye tashiga kalle kalle adakin kozata ga ruwa amman ko alamun ruwa batagani ba wajen kofa tayi ta murda ina yaki budewa saitasa password kuma batasan mene ba, dawowa tayi hankalinta ya bala’in tashi tazo jijigashi tashigayi tana kuka. “Ya Aliyu katashi dan Allah katashi kaji Ya Aliyu” mikewa tsaye tayi tama rude tana juye juye tarasa maizatayi hannu tasa tazare dan kwalin kanta ta warware dasauri sanan tashigamai fifita dashi da sauri da sauri tanamai addu’a.



Almost 5min tadauka tanamai fifita sanan ahankali taga idanunshi na motsi hakan yasa ta tsayar da fifitan datakemai tana kallon fuskanshi daga tsaye datake akanshi gently yabude jajayen idanunshi yadaurasu akanta all kalaman data gama fadamai suna dawowa kanshi zuciyanshi da kirjinshi namai wani irin ciwo kaman ana kona garwashi acikin kirjinshi wasu zafafan hawaye ne suka fito daga idanunshi suka gangara gefen idanunshi yana kallonta motsi datagani yayi da bakinshi dan yanda kirjin kemai zafi baijin zai iya wani ihu ba dawani irin sauri tai kneeling kusada shi takai kunnenta saitin bakinshi tana sauraron meyake fadi, cikin wata kalan raunanniyan murya yace “I hate you Ummulkhair! Na tsaneki with every bone and flesh na jikina, I regret the day I ever told you ina sanki! Nayi daman saninki arayuwana, I regret knowing you and even spending time with you, Ummulkhair Muhammad I Aliyu Hydar Abdullahi Abdulwahab hate you with every drop of blood na jikina!” wasu kalan hawaye taji sunzo mata amman tadaure ahankali tadago da kanta tajuyo takalleshi gani tayi yadauke kanshi yakalli gefe yana cijan lips dinshi kana ganinshi kasan wani abu kemai ciwo, ahankali yace “the door password is Pickle open and go back home” jitayi jikinta kaman yay kankara takasa ma wani kyakkwaran motsi daga inda take takai hannunta kan bakinta ta taushe sabida kukan datakeji tana kallonshi ganin yanda Aliyu ya tsaneta duk wani soyayya dayake mata ya rikida yakoma kiyayya bamayason yakalli fuskanta kaman ba Aliyun taba. “Leave from here!” Yadaka mata wani irin tsawa yana kama kirjinshi da karfi yana wani irin nishi, ahankali ta tashi jikinta narawa sosai tana kuka mara sauti taje gaban kofan danna keyboard din tayi tasaka pickle tana sakawa kofan yabude fita tayi sanan tajawo kofan tarufe ta tsugunna agaban kofan tana wani irin kuka mai bala’in tsuma rai, kaman tai hauka takeji, ita kanta batasan tanason Aliyu hakaba saida ya furta mata he hates her jitayi her whole world is crippling before her eyes, ahankali tadaga hannayenta sama hawaye na zuba daga idanunta. “Ya Allah na, Ya ubangijin al’arshi ubangijin sammai da kassai, Ya Allah kai kadai na yarda dashi, Ya Allah kaga zuciyana all I am doing is bin umarnin iyayena, Ya Aliyu is suffering” tai maganan tana wani irin fashewa da kuka kafin ahankali tace “Ya Allah yau ina gabanka I am even confuse on what to ask you and what to pray for all I know is addu’a kawai nake amman bansan na miyeba, Ya Allah kaduba lamarina and solve this problem for me domin ko babu abinda yafi karfinka kaine Azza Wajal” tafashe da kuka takasa tashi ta tafi dudda yabata chance din dan bazata iya tafiya tabarshi ba.




Da kyar Aliyu ya iya ciro wayanshi daga aljihun gaban riganshi ya kunna, ko kadan baya gani da kyar shidai baisan ya akayi yama kira number Dad ba kawai daura wayan yayi a kunnenshi ringing daya Dad yadauka arude cikeda tashin hankali Dad yace “Aliyu where are you? Aliyu don’t do anything stupid dazakazo kayi nadama nan gaba, dan Allah kafadamin inda kake”? Murya chan kasa Aliyu yace “security post Dad come and get me” wayan yafadi daga kunnenshi Dad na hello hello amman shiru wani irin gudu Dad yakara amotan babban abokinshi Dr Sani yace “yagaya maka inda yake”  gyadamai kai Dad yayi yana tukin cikin minti 10 suka iso wajen, ganin mota yasa Khairy ta tashi tsaye dasauri tana share idanunta dasukai jajir, bude kofa Dad yayi da Dr Sani suka fito yana binta da kallo saukarda kanta kasa yayi yakarasa gabanta anatse yace “Ummulkhairy kiyakuri I apologize on my son’s behalf” kasama cema Dad kala tayi sabida kukan dake zuwan mata Dad da Dr sani suka shiga dakin bayan Dad yasa password din tana tsaye wajen, ko 5min basuyi ba taga sun fito da Aliyu kaman wanda yamutu dawani irin sauri tazo wajensu tana kuka tace “maiya sameshi” sashi amota Dr Sani sukayi suka rufe sanan yabama Dr Sani car key yace “go to hospital with him bari namaida Ummulkhairy gida zan biyoka abaya” gyadamai kai Dr Sani yayi sanan Dad yakalli Ummulkhairy yace “let’s go” wajen motan Aliyu sukayi suka shiga Dad yatada wayan, wani irin kuka tahauyi cikin kuka tace “Abba I am sorry, dan Allah kuyafemin, dan Allah kuyafemin” dan murmushi Dad yayi yana tuki yace “kidena kuka Ummulkhair, non of this is your fault, Aliyu will be okay, muje namaida ke gida hankalin iyayenki ya kwanta stop crying now” umarnin Dad tabi ta share fuskanta, ana kiran sallan magrib sukakai gidan, kowa na tsakar gida dan Dad yariga yakirasu yace musu gashinan zuwa da a Khairy, parking yayi sanan yafito Khairy itama ahankali tafito kowa na binta da kallo barinma Zayn da idanunshi sunyi jazur yana kallonta tundaga kasa har sama, dawani irin gudu tai wajen Baba fadawa jikinshi tayi cikin wani irin murya tace “Baba Ya Aliyu zai mutu, he’s very sick Baba, an wuce dashi asibiti, Baba idan Ya Aliyu yamutu because of me yaya zanyi da rayuwana” alamu Baba yamata datai shiru sanan yakalli Anty Mariya hakan yasa tazo ta karbeta tawuce da ita ciki.




Hannu Dad yahada duka biyun yana kallonsu Baba yace “dan Allah ku yafema d’ana abinda yamuku yayi bala’in kuskure” hannunshi Baffa yakama yana girgizamai kai cikeda kulawa yace “Ya jikin Aliyun”? Dan murmushi yayi yace “he will be fine asibitin zan tafi yanzu saida safen ku” gaggaisawa yayi dasu Baba sanan yawuce motanshi kowa yabishi da kallo haryabar gidan sanan Baba yasauke ijiyan zuciya yace “Alhamdulilah muje muyi salla” wucewa sukayi dukansu Zayn na juyowa yana kallon gidan, suna idar da salla yafito daga masallacin batare daya jira kowaba yataho gidan.



Direct sama yawuce sanan ahankali yay knocking tareda bude kofan yana sallama kasa kasa hada idanu da Anty Mariya dake zaune bakin gado tana juya mata tea data hada mata, ganinshi yasa ta mike tsaye tace “Zayn kaine tana bayi wanka take” Gyadamata kai yayi batare dayace mata komiba, ahankali itama Anty Mariya ta ijiye tea sanan tazo tabi tagefenshi tawuce tafita daga dakin tareda rufomusu kofa.



Yana tsaye yana kallon kofar bathroom din tabude kofa tafito ahankali chak ta tsaya ganin Zayn tsaye yakafeta da idanu, ahankali tamika hannunta tadauki hijabinta dake kan gado zata zura karaf taji an rike hijabin dayasa tadago kanta takalleshi dasauri hada idanu sukayi idanunshi sunyi jaaaa, fizge hijabin yayi ya yar akasa yana wani irin kallonta yace “ina yakaiki and meyamiki”? Wani irin kallonshi take batare datace komiba, cikin fushi yace “what did that police man did to you Ummulkhairy”? Kaman bazatai magana ba saikuma ahankali tace “babu komi” huci yashiga yi yana kallonta, cikeda bacin rai yace “just so you know duk randa policeman dinan yakara zuwa kusada matata I swear by Allah saina kasheshi” yay maganan yajuya fuuu fita daga dakin yayi yasa hannu yawani buga kofan yafice dakin su Manaf yayi dan baimaso yabar gidan gani yake kaman Aliyu zai kara zuwa yadauketa yatafi hakan yasa agidan ya kJwana.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



5️⃣6️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Washegari jummaa yaune kamu, gabaki daya tadawo wata kalan tausayi babu wani abu na duniya dake mata dadi she just wish akwai wani abu dazata iyayi ace all this things mafarki ne, Mama bata mutu ba ta barinmata wani littafi ba or anything of such, takasa daina tunanin Aliyu, duk idan tai tunani yanachan baida lpy suffering saitaji zuciyanta na shattering, saiyau yanzu ta yarda soyayya yafi komi dadi sanan yafi komi daci, condition da situation kesa kadandana kowani part, inda tasan cewa ahaka soyayyanta da Aliyu zai karake da batama hadu dashi arayuwanta ba dayafi mata alkhairi, tanaji tana gani wuraren 4 aka shiga shiryata ana mata makeup za’ayi kamu mai makeup dake mata tayi ta tsaya kusan sau hudu sabida sai anacikin yi kawai tashiga kuka, saida Anty Mariya tazo sanan ta lallasheta tai shiru aka gama mata aka shiryata cikin wata atampa na kampala pink sabida is her colour kuma anaso ayi kamun da abinda takeso aka fita da ita tsakar gida mata na gudu kawayebta sun cika gidan dan Batool da Besty duk sun gayyace su wani irin kuka na zuci kawai take, ana haka akai announcing zuwan ango da abokanenshi saiga Zayn dayaci wani irin gayu Subhanallahi kaman balarabe yayi kyau da Mamu da Faisal zaka dauka turawa ne nan kawayen Khairy aka shiga rawan jiki, da dollars yabiya kudin siyan fuskanta sanan aka budemai fuskanta tsugunnawa yayi agabanta yana kallonta tamai kyau iya kyau kasa dagakai tayi ta kalleshi kanta nakasa, hawaye taji sun zubomata sharrrr ahankali yakai hannunshi kan fuskanta murya chan kasa yace “don’t cry Mrs Zayn” wani kalan guda aka dauka awajen ana shewa jin sunan daya kirata dashi, dan murmushi Zayn din yayi dan baisan anjishiba sanan yajuya suka fice daga gidan yana murmushi Mamu yace “wowww Zayn kagama iskancin ka ka auro natsassiyar kamilan yarinya haka” murmushi yadanyi yace “itace first ever girl dana taba so dakaina” ahankali Mamu yakama kafadanshi zaiyi magana Zayn yace “please don’t ruin my mood da maganan that Ayshu I was never and will never be interested in that girl, is not like am a bad person banma taba bata fuskan tasoni ba” ahankali Mamu yace “but you f*cked her” yatsine fuska yayi yace “I never wanted to, dudda haka i paid her ai ko so bata bina any bashi nima haka let her go her way I go my way” shiru Mamu yayi dan yana bala’in tausayin Ayshu dake neman kashe kanta kanshi, ahankali Mamu yace “kaini gidanku to naje na dauko suitcase dina tunda kace kai anan kake” yatsine fuska Faisal yayi yace “nidai bai hotel i need sleep” baima jirasu ba yawuce yashiga dayar motarsu yawuce abinshi, yatsine fuska  Zayn yayi yace “kasan dai I’ve been running away from that old woman ko, sokake taganni ta tasani gaba da bala’in masifan ta” dasauri Mamu yace “wlh bazama tasan kazo ba gidanku cikeda jama’a, let’s go please wajenka nazo agarin nan babu abinda zaisa naita bin direba yana kaini ko’ina zani” hararanshi Zayn yayi yace “kana dan Abuja amman tsabagen rayuwa outside babu inda kasani agarin ku” shiga motan sukayi yaja motan har zuwa gidansu parking sukayi Zayn na mota bai saukoba dan baimaso aganshi Mamu ne kadai yasauko yawuce side dinsu shikuma yajingina kanshi jikin kujeran motan yana tunanin fuskan Khairy murya chan kasa idanunshi a lumshe yace I love her, knocking glass din motan da akayi yasa yabude idanunshi ahankali ganin Yar aikin Ammi yasa gabanshi yafadi, ahankali tace “Ammi tace kazo tana falon ta” Gyadamata kai yayi tawuce tafice, dan gajeren tsaki yaja sanan ahankali yatashi bude kofan yayi yafice daga motan zuwa flat din Ammi.

******




Yau tunda gari yawaye kuka Ummulkhairy keyi sabida tasan dagayau shikenan itada Aliyu, har kasan ranta jitake inama ace Mama batabar wanan wasiyyan Auren Zayn din nan ba, da kyar su Batool da kawayenta suka shiryata sukasa tai shiru aka mata kwalliya babu wanda zai kalli Khairy dabazai kara kallo ba sabida yanda tai kyau fatarta taji gyara kaman me, ta tsumu iya tsumuwa shi kanshi Baba daya ganta rungumeta kawai yayi sabida all the thing was so damn emotional he can’t believe his little Ummulkhairy is going to gidan mijinta yau.

Karfe 2 daidai na rana za’a daurama both Manaf da Mu’az aure awani Babban masallaci dakenan cikin gari, tunkafin 2 tayi mutane suka cika makil ana jiran 2 yayi adaura Auren dan daga Baba har Baffa sunada mutane gakuma tawagan yaransu, daga Baba har Baffa dukansu kaya iri daya suka saka duk suna tsaye waje suna amsan bakinsu ana gaggaisawa, parking mota ahankali Mamu yayi dayasha wanka yay wani kala sanan yafito, Baffa dake gaisawa da jama’a kaman ance ya waigo ganin Mamu natahowa shi kadai babu Zayn yasa yay murmushi yacigaba da gaisawa da mutanenshi daidai Mamu yakaraso gabansu, Baba yace “ahh Mamu kunzo ina Zayn din”? Baba yay maganan yana duba motar da Zayn yay parking, juyowa Baffa yayi yakalli Mamu da akama tambaya yay shiru yakasa amsawa kai tsaye Baffa yace “ina Zayn”? Ahankali yasa hannunshi a aljihu sanan yaciro wani envelope fari yamikama Baffa yace “Zayn yace nakawo maka Dad” kallon envelope din Baffa yayi sanan yasaki yar murmushi yasa hannu ya karba sanan yabare envelope din yazaro doguwan paper dayake ciki yana karanta abinda ke ciki Baba na kallonshi saida yagama karanta takardan tass sanan yakalli Mamu yace “wuce kaje Mamu nagode” ahankali Mamu yawuce yatafi dasauri Baba yace “menene a wasikar” mikama Baba wasikar yayi sanan yasa hannu yaciro wayarshi daga aljihu yay dialing number Ammi kai tsaye yace “na sake ki saki daya!” Ihu Ammi tahauyi kawai ya katse wayan yajuyo yakalli Baba dake kallonshi ranshi a bala’in bace yace “mehaka bansanka da irin wanan fushin gaggauta yanke hukuncin b….” Hannu Baffa yadagamai sai kawai yakama hannun Baba yajashi zuwa chan nesada masallacin anatse yace “ka yarda dani amini na”? Gyadamai kai Baba yayi, Baffa yace “ka yarda da hukunci na”? Ahankali Baba yace “sama da kowa aduniyan nan” anatse Baffa yace “inhar hakan ne kuma na isa nacemaka kayi abu aduniyan nan kayi inada wanan kiman a idanunka kiramin mahaifin Aliyu yazo wajen nan yanzun nan” wani kalan kallo dayakemai yasa Baffa yace “amini na, akwai wani abu damu karan kanmu amatsayin mu na iyaye bamu da iko akai, nasan mahaifiyar Ummulkhairy taso Zayn da Khairy amman karka manta da abu daya koda take raye mahaifiyar Zayn bata taba sonta ba hasalima basa shiri, Wanan sakin datasa Zayn yama Khairy Allah yasa hakanne mafi alkhairi bazan maka karyaba naji dadin hakan tun yanzu kafin aje ko’ina yasaketa ba sai bayan aureba bayan yagama wulakantata ba yasako mana ita ba, ni nan da kai mun yarda da tarbiyan Aliyu dakuma natsuwanshi, sakin da Zayn yamata was not his fault trust me Allah shine jagoran abin nan dan haka karmuyi gardama komujada hukuncin Allah, kira mahaifin Aliyu atare dasu Manaf yau za’a daurama Khairy da Aliyu aure” ijiyan zuciya Baba yasauke ko Allah ma yasani batun yauba har cikin ranshi yanason Aliyu inda ace babu aure akan Khairy dazai bashi, kiran Dad yayi yacemai dan Allah kome yakeyi yabari yazo it’s urgent, Dad bai musaba dayake clinic dinshi inda Aliyu yake kwance baida wani nisa da masallaci duka duka cikin 5min saiga Dad yazo yana sanye da manyan kaya.


Dad hawayen farinciki ne kawai baiyiba da aka fadamai komi atake yanke aka tafi masallaci aka daura Auren Manaf da Aisha, Mu’az da Maimuna, sai kawai sukaji Liman na gyara speaking kawai ji sukayi an daura Auren UMMULKHAIR DA ALIYU akan sadaki dubu dari uku wanda sune all the kudi dake aljiJhun Dad.




ARE YOU GUYS HAPPY💃

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




5️⃣7️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




Ana gama daurin Auren duksu Manaf sukazo zasuma Baba magana hannu yadaga musu alamun later sanan shida Dad suka gaisa kafin su rungume juna ahankali Dad yace “thank you” cikeda farin ciki Baba yace “thank you nima, anjima ku aiko adauki amaryan ku and In sha Allah zuwa dare idan mutane suka ragu zamuzo mu gaida Aliyu” sakinshi Baba yayi suka rungume juna cikin aminci da Baffa sunama juna godiya sanan yajuya yatafi, sai alokacin su Manaf sukazo wajen su Baba kafinma suyi magana Baba yabawa Manaf takardan hakan yasa yakarba dasauri yashiga budewa.

“Abba, Baffa ina neman gafarar ku, ku yafeni banda haka inaso na shaidamuku da gaskiya ta wanda Allah yaga zuciyana yasan hakan ne, Abba inason Ummulkhairy da duka rayuwana, inaso zama da Ummulkhairy amatsayin matata har zuwa karshen rayuwana, Abba……” sai maganan ya yanke kafin yaje next paragraph.

“Nasaki Ummulkhairy saki daya, biyu, uku, Abba Ummulkhairy deserve happiness and some light arayuwanta, ayanda Ammi hates her Kona aureta I doubt I can give her that, kuyafeni Zayn!” Linke takardan Manaf yayi ahankali yabama Abba sanan yawuce abinshi Mu’az biyedashi bawai ya tsani Zayn bane kodaya shi dama bayason auren da Zayn sabida tun mama nada rai ba shiri suke da Ammi ba, Ammi har Baffa ma tana nema tafi karfinshi ballema so bayason kanwarshi taje taita wahalanta, banda haka Aliyu is a great guy infact he’s even happy, Zayn din yaje chan yakarata da wacce Ammi keso ya aura atleast sister shi yanzu tasami Aliyu datakeso shima yake sonta so Alhamdulilah dagashi har Mu’az da Maheer babu wanda abin yama ciwo.


**

Waiwaiye Baya Kadan!

Falon Zayn yashiga ahankali yana kallon ko’ina yanda yake nan tsaf tsaf an gyara, wata Yar aikin Ammi yagani tana saukowa daga sama cikeda girmamawa tace “Hajiya tace kasameta adakinta na sama” danjim yayi sanan yawuce sama ahankali yana hawa benen, bude kofan dakin Ammi yayi da sallama chan kasa yashiga Ammi na zaune kan gado as usual taci gayun nan kaman wata matan shugaban kasa tabi Zayn din da mugun kallo yanda yay wani kyau shi adole ango sanan tace “kazaci bansan abinda nakeyi bane dani kake wasan buya Zayn” ahankali yamaida kofan yarufe sanan yazo gabanta ashagwabe zaikai hannu yatabata cikeda lallashi tawani irin dakamai tsawa tace “don’t touch me Zayn, don’t you dare” tsayawa yayi chak yana kallon, hawaye yaga sun zubo daga idanunta cikeda kunci tace “bantaba nadaman haihuwa ba sai akanka Zayn” wani irin zaro idanu yayi cikeda damuwa yace “Ammi why are you talking like this mena miki ne dan Allah” nuna kanta tayi sanan ta bubbuga kirjinta tace “Zayn ni mahaifiyar ka kake tambaya mekayimini iyye?? Ni, Zayn nikake nunama banda daraja da amfani a rayuwanka eh? Okay listen bari kaji abinda yasa nakiraka” sauka daga gadon tayi tamike tsaye jaraba fall idanunta sanan takai hannunta takama nononta guda tana kallonshi tace “inhar nacika uwarka Zayn wacce ta tsugunna tahaife sanan tabaka wanan nonon kasha, ta raineka sanan ta tarbiyantan dakai harzuwa kawowa wanan lokacin, inhar nakai matsayin uwa agareka Zayn to ayau ni mahaifiyarka nake baka uBmarni kasaki Ummulkhairy ka auri Aisha yarinyar kawata dana zaba maka”….

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️





5️⃣8️⃣





Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




Wani irin kallon mahaifiyar shi yake yana mamakin wanan wani irin tsana ne me Ummulkhairy da mahaifiyarta sukama Ammi datakisu haka, cikin fushi sosai Ammi tace “nikake kallo kamaida Yar iska ko bari kaga” filon kan gadonta tadaga tadauko wani sharp wuka tace “ai ita Ummulkhairy wish din dead mahaifiyarta ake cikawa akanta nima bari na kashe kaina maybe alokacin ne zakabi umarnina” kawai Ammi tadaga wukan da gaske zata chakama kanta dawani irin sauri Zayn yazo hannunta da wukan kekai yakama chak yana kallonta saiga hawaye sun zubo daga idanunshi sharrrrr murya chan kasa yace “Ammi basai kin dauki rayuwanki bane zan miki biyayya ba” ijiyan zuciya yasauke kana ganinshi kasan abin namai ciwo sosai hawaye yasake gangarowa daga idanunshi yana kallonta still. Ahankali yace “Ni Zayn nasaki Ummulkhairy” da dayan hannunta dabai rikeba Ammi tanunamai uku, wasu uban hawaye ne sukai gushing daga cikin idanunshi zuciyanshi namai ciwo ahankali yace “saki uku” sanan yakarbe wukan hannun Ammi ahankali kafin yajuya zai fice cikeda zafi tace “ina zaka sami paper ka rubuta kabama Mahaifinka nasan zaice nina saka amman na shiryamai kome zaimin yayi, dolenshi dai yaje ya nema maka Aisha ka aura” bude kofanta yayi yafice yana goge idanunshi yay side dinshi jiyayi yama tsani komi da komai bazaima iya kara 1 good minute anan Nigeria ba, flat dinshi yawuce koda yashiga Mamu na bathroom hakan yasa yadauki paper da buro yashiga rubutu yana share hawaye kafin ya linke yasa a envelope yadaura kan gadon sanan yadauki wani bag pack yadauki su international passport dinshi da other necessary abubuwa dayake bukata kafinma Mamu yafito yawuce kawai yafita yashiga mota straight to airport.

Wanan kenan!!!




Wuraren 4 Baba da Baffa suka dawo gidan bikin dudda akwai mutane cikeda gidan sama sukayi zuwa dakin Baba sanan suka tura Batool taje ta taho da Ummulkhairy.

Ummulkhairy na zaune adakinta abin duniya yamata yawa babu abinda kemata dadi aduniya, tai wani irin zuru zuru Batool yashigo dakin tace “tashi muje su Baba nakiranki zaa fara miki fadan Amarya” kallon Batool tayi tama kasa tashi ita kanta bazata iya explaining yanda takeji yau dinan ba kaman tamutu kawai takeji, kamata Batool tayi tana gyara mata lullubi sanan suka wuce zuwa falon Baba da ita suka bude kofa suka shiga, daga Anty Mariya sai Mom da Baba da Baffa zaune suka shigo zama sukai akasa Baba na kallonta yanda tai kyau sanan yay gyaran murya yace “Ummulkhairy nazo miki dawani sabon labari dudda nasan ba lallai bane kiso kijishi ba” Baba yadanyi shiru kafin ahankali yace “dazu muna wajen daurin Auren yayyinki babban amincin Zayn yakawo mana wata wasika daga Zayn” Baba yasakeyi shiru, ahankali Baffa yace “Ummulkhairy d’ana Zayn ya aiko da wasika dake dauke da saki, yace yasakeki saki uku!” Dawani irin sauri daga su Mom har Batool da ita kanta Khairy ke kallon Baffa, dan ijiyan zuciya Baffa yasauke anatse yace “I don’t want to go into details Ummulkhairy, nasan Auren Zayn burin mahaifiyar kine, amman wanann da tunkafin akai ko’ina Allah ya wargaza al’amarin inaga akwai wata aya da Allah ke kokarin nunamana Ummulkhairy dan haka kiyakuri” wani irin gyamboo taji zuciyanta namata tun dazu zuciyanta namata ba dadi amman na yanzu is like times 1000, Aliyu kawai take tunanowa da wulakanci datamai, ta wulakanta wanda ke sonta kaman zai haukace, tacimai mutunci, tamai gori da Zayn, tayi insulting pride na Ya Aliyu gashi yanzu wanda yasa tamai haka yasaketa tunkafin akai ko’ina kaico! Wani kalan kuskure tayi arayuwanta ne haka Ummulkhairy! Baffa ya katse mata tunani ta hanyar kiranta hakan yasa ta kalli Baffa, anatse Baffa yace “Ummulkhairy mun daura miki aure da Aliyu ga sadakin ki nan!” Wani irin zaro idanu tayi tanajin maganan kaman amafarki taga Baba yatashi ya ijiye mata wasu bandir na kudi akan cinyanta, ahankali Baffa yace “saidai mijin naki Aliyu baida lafiya sosai har yanzu yana gadon asibiti mahaifinshi yace ayanzu haka baimasan wanda ke kanshi ba, anjima dukanmu nan bayan sallan magrib zamubar kome mukeyi muje mu duboshi, kekuma nan bada jimawa ba dan mahaifinshi yariga yakiramu za’azo daukanki gidansu za’akaiki for now, idan yazo yaji sauki In Allah ya yarda sai ayi duk bikin dazasuyi akaiki gidanki ki tare kinsan yanzu babu wani shirye shiryen da akayi bikin yazo mutu bakatatan” Baffa yay shiru sanan Baba yace “Ummulkhairy inaso idan kinje gidan mijinki kiyi koyi da halin mahaifiyarki, nasan Aliyu baida mahaifiya tarasu, amman yanada Kaka da Matan Baba da kanne, nasanki da girmama mutane inaso kibisu sau da kafa karnaje complain akanki sai yabo, ki kasance mai tsoron Allah da biyayya ma mijinki dan yanzu aljannar ki na karkashin mijinki ne……..” Baba yashiga mata fada mai ratsa jiki dayasa tafara kuka, har cikin ranta dataji ance an aura mata Aliyu jitayi kaman an cire mata wani babban kaya azuciya amman kuma aliyu ya tsaneta, but ba matsala idan shine battling dinta agidan mijinta she is ready zatai fighting for her love back she will win Ya Aliyu back and taroki gafaranshi lokaci yayi yanzu dazata zama dat sensible and matured girl da Mama koda yaushe kEhso tazama.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




5️⃣9️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️





Daga Baffa, Anty Mariya, Baba da Mom babu wanda bai mata fada da wa’azi cikinsu ba, wajajen 6 Baba yace “wife kutafi da ita ta shirya motocin daukanta na hanya” gyadamai kai Anty Mariya tayi sanan suka dagata ahankali tana kuka sosai daki aka kaita wanka akasa tayi sanan aka bata ruwan turare tayi dashi sanan tafito shiryata sukayi cikin wani milk hadadden lafaya mai bala’in kyau, 6:40 hadaddun motoci sunyi layi gaban gidansu kowane mota dan sanda ne da full uniform keja dan duka boys sun Aliyu Dad yakira.

Tsaf aka shiryata bakaramin kyau tayiba aka lullubeta sanan aka fito da ita takasa daina kuka she can’t believe shikenan dagayau tabar gidan iyayenta rungume Baba tayi gam gam ana guda ana ayiriri sun dade ahaka shima Baba idanunshi sunyi ja sosai sanan yadagota yace “ya isa haka kukan kar kanki yayi ciwo” ahankali yakama hannunta yasaukar da ita kasa ana binsu suka fita tsakar gida har zuwa kofar gida da kanshi yabude kofar motan kafin ahankali yace “go in peace Ummulkhairy, ubangiji Allah yama aurenki albarka, ina rokon Allah to bless your new home yakuma haskaka rayuwan aurenki, go my daughter” yay maganan yana sata cikin motan ta zauna ahankali tana kuka, shiga motocin su Mom sukayi da kawayenta da Batool sanan aka tafi da ita.




Tsakanin gidansu Aliyu da nasu nada nisa sosai, dan sai wajajen 8 nadare sukakai, wowww Batool dake gaban motan tafadi ganin Babban gidansu Aliyu, an bude gate wato kudi nada kyau dudda su kansu basusan da bikin ba but they were able to pull something an zuba kujeru hadadun agidan ga DJ an kawo, yan uwa sun cika gidan ko’ina hayaniya ga girke girke abinci kala kala na yawo a tsakar gidan, kafin sufito daga mota Gwaggo da Mami dasukaci gayu na gani afada sukazo taransu idan kaga Gwaggo zaka dauka an mata bushara da Aljanna ne, fito da Khairy akayi daga mota kawai Gwaggo tafashe da kuka Dan she can’t believe Ummulkhairy ce aka kawomata amatsayin Matar Aliyu danta, taruwa akai kan Gwaggo dake kuka cikin kuka tace “ni kubani y’ata na rungume” murmushi su Mom sukayi sanan suka kawo mata Ummulkhairy dakenan alullube tawani irin rungumeta tana mata ruwan saman addu’a a godiya aka sanan tasaketa tace “kushigo” shigowa sukayi babban falon Mami aka fara kaita aka zaunar da ita atsakiyan dakin ana waka ana rawa Mami na murmushi ana cemata saita saya baki zata ganta, kudi Mami takawo da box na warwarayen zinare tadaura kan jikin Khairy ana ihu ana guda sanan aka bude mata fuskan Khairy kallon fuskan Khairy da idanunta ke kasa tayi sanan tamata addu’a kafin a dauketa akaita dakin Gwaggo, Gwaggo da dan kafafunta dababu lafiya rawa tahauyi Haba zokaga dariya sanan takawo turaman zani guda ashirin tabama Khairy da bandir na yan dubu dai dai guda uku, da zoben azurfa da warwaron azurfa da sarkan azurfa masu kyau sosai aka dinga guda, tashi Mom da Anty Mariya sukayi sukai sallama da su Baffa najiransu suzo aje aduba Aliyu,  da Kyar Khairy tasakesu suka tafi sai kuka take sanan Kaka takaita dakinta dan fir tace “ita awajenta Khairy zata zaune har zuwa aliyu yaji sauki tanada dakuma daban daban dayawa a side nata, wani hadadden daki aka kai Khairy gadon ciki ma sabone fill dan dazu da rana Dad yasa wani furniture company suka kawo aka chanza komi na dakin aka fitarda nada zaunar da ita akai akan gado itada Batool da Amal kawarta sauran mutane duk suka tafi.




Wuraren 10 su Baba sukakai asibitin Dad, Dad dakanshi yazo yadauke su akasa yace “barkanku da zuwa” gaisawa sukayi suna sama Baba yace “yajikin nashi” ijiyan zuciya Dad yasauke yace “Alhamdulillah muje” sukai sama har zuwa wajen wani daki, bude kofan Dad yayi ahankali yashiga su Baba biyedashi Aliyu na kwance kan wani hadadden gado da kayan asibiti idanunshi akulle he’s attach to wani machine, salati su Baba sukayi, Baffa yace “what’s the plan yanzu” dan ijiyan zuciya Dad yasauke yace “wanan machine din shine taimakama heart dinshi to beat, beating na heart nashi is very slow, so yanzu dai gobe zamu fitardashi zuwa Oman akwai wani heart Dr achan he’s my very close friend tare mukai karatu a Ukraine yace nakawoshi Aliyu will be fine” dukansu ajiyan zuciya suka sauke Baba yace “In sha Allah zaiji sauki, please if u need anything we are here for you yanzu munzama family” murmushi Dad yamusu cikedajin dadin maganan su yace “Allah yabar zumunci nagode sosai” motsi da Aliyu yayi yasa dukansu suka kalleshi dasauri Baban yay wajen gado yana kama hannunshi yace “Aliyu, Hydar I am here can you hear me”? Wani irin bude idanunshi Aliyu yayi kadan da kana gani kasan baya cikin hayyacinshi sanan murya chan kasa yace “Um….mulk….hair” kafin yakara lumshe idanu kaman bashi ne yay motsi ba, sakinshi Dad yayi yadanyi murmushi yajuyo yakalli su Baba da jikinsu yay sanyi sosai yace “tun shekaran jiya haka yake saidai yadan bude idanu kadan yakira sunan Ummulkhairy yakoma” dan murmushi Dad yasakeyi sanan yakalli Aliyun yace “one thing I am sure of shine d’ana na bala’in son Ummulkhairy so thank you Alhaji dakuka auramai Ummulkhairy bazan taba mantawa da wanan kyautatawan dakukamin da d’ana ba” yay maganan yana juyowa yakalli su Baba daduk sukejin badadi suna addu’a Allah yabashi lpy, sun dade a asibitin sai wajajen 12 na dare sanan suka tafi, Baba da Baffa sun dade suna magana sanan kowa yawuce gidanshi.



Saida sukakai gida sanan Mom takalli Baffa kafin tafita daga cikin motan ahankali tace “one thing danasani cewa inaso gamedakai shine rashin yanke hukunci acikin fushi, nasan ba hurumina bane nan amman inaso na roki alfarma biyu daga wajenka” tai dan shiru tace “nafarko shine inaso kamaida Ammi and inaso kai kokari and look at her situation and understand her, batasan da Auren nan ba itace mahaifiyar Zayn, taci buri kan danta is understandable idan taki yarda da Auren nan kowa da kalan zuciyanshi, kuma yanda Zayn bai auri yarinyar nan ba barabonshi bace wlh inda rabonshi ne daba Ammi ba ko duk aduniyan nan ne basu isa suraba Auren nan ba, sai alfarma tabiyu shine ko’ina Zayn yaje ka kirashi danka ne, nasan yanachan cikeda damuwa yasa kazama karamin mutum da sauransu kanunamai bahaka bane yadawo gida, Auren Ummulkhairy ko rashin aurenta won’t change kai mahaifinshi ne yazo idan yanason wacce Ammi keso ya aura wato Aisha kaje ka nemamai Auren idan bayaso yakawo kowa yakeso ya aura, rayuwa batada tabbas kowa datashi kaddaran just look at Aliyu yanzu yanachan kwance rai hannun Allah yay giving up but Allah yaga zuciyanshi cikin sauki yabashi Ummulkhairy, komi yafaru nada dalili sometimes abinda mu iyaye kesoma yaranmu is not the best or Khair for them, I know u are hurt amman kayakuri and forget everything let this family continue to be in peace kaji”? Gyadamata kai Baffa yayi ahankali bude kofa tayi zata fita dasauri yakamo hannunta hakan yasa tajuyo takalleshi, ahankali yace “I am so lucky to marry a wife like you, Allah yamiki albarka” murmushi tayi tace “Ameen” sanan tawuce ta tafi shikuma yadan dade zaune a motan sanan yaciro wayanshi yakira number Zayn ringing yake yana gab da tsinkewa yadauka.


Ahankali Zayn yace “Abba kayafemin I am so sorry” murya chan kasa Baffa yace “shiiiiiii Zayn i understand you Allah yasa hakanne mafi alkhairi, kana ina”? Murya chan kasa tace “ina wani hotel ban sami flight ba yau saida safe” anatse Baffa yace “dare yayi yanzu dan haka forget about tafiyan nan gobe dasafe kadawo gida kajini, I am not angry with you one bit hakama Baffan ka shima he’s not, so kadawo gida kadauki komi amatsayin kaddara inda Ummulkhairy matarka ce da Ammi n ka bata isa taraba Auren nan ba, so it’s okay, kadawo gida inaso kafito dawata yarinyar ka aura idan wacce mahaifiyarka keso ne to idan ma ba ita bane duk daya kaji” gyadamai kai yayi ahankali yace “thank you Abba” murya chan kasa Abba yace “don’t cry again good night son” ya katse wayan.




6️⃣0️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Jirgin karfe 6 nasafe Dad da abokinshi sukabi aka wuce da Aliyu Oman.

****


Dukansu adakin sun makara sabida yanda akai bacci late jiyada daddare, Ummulkhairy tafara bude idanunta wuraren 8 nasafe, saman dakin tabida kallo komi nadawo mata sabo she can’t believe ita Amarya ce and tana gidan iyayen mijinta Aliyu anan ta kwana, tashi zaune tayi ahankali tana kallon Batool da Amal dake shargan bacci sanan ahankali tamike tsaye tawuce bayi, shiga tayi ta maida kofan tarufe sanan tabude tap wanke fuskanta tayi takalli madubi tai wani irin fresh fatarta tayi da sulbi sulbi yakeyi tsabagen dirzan gyaran jikin da aka mata tarame babu abinda yarage ajikinta banda boobs da hips, ijiyan zuciya tasauke ahankali sanan tadauki brush sabo dake dakin tadauro alwala tafito daga bayin ganin Batool zaune yasa tashimfida dadduman dake dakin tadauki hijabi tasaka tai salla.


Koda ta idar zama tayi tai shiru tana tunani, Aliyu kawai zuciyanta keso yagani tabashi hakuri, tsayawa akanta Batool data fito daga bayi tayi tace “tashi kije kiyi wanka ki shirya” gyadama Batool kai tayi sanan tamike tsaye ahankali tana kallon Amal dake bacci still sanin bata salla yasa tawuce bayi batare data tadata ba.



Wanka tayi tafito daure da towel set na akwatin da Baba yamata Batool tashigo da daya shigo daga cikinsui sanan ta ciro mata wani lafiyayyen lace ja, shiryawa tayi da taimakon Batool duk wanda yaganta saiya kara kallonta, mayafi Batool takawo mata tayafa mata aka sanan ta feffesa mata turare tace “fita kije ki gaida Gwaggo tana falo” Gyadamata kai Ummulkhairy tayi sanan tabude kofa ahankali tafice tanabin corridor dake kamshin turaren wuta sanan tadaga labule tafito falon, Gwaggo na zaune afalon kan daya daga cikin jerin kujerun dake falo 3sitter  tana burga wani lafiyayyen fura a kwarya, Meena na zaune kusada ita itama tasaka atampanta mai kyau sosai, ganin Khairy yasa tawani irin ijiye wani empty kwaryan dake hannunta wanda tarike tana jiran Gwaggo tagama ta tsammata tadauke kai, kaman ance Gwaggo ta waigo sabida kamshin turaren da jikin Khairy keyi ganin Khairy gaban corridor kanta akasa kana ganinta kasan kunya takeji yasa tawani washe baki tana kallonta tace “jama’a kuzo ku kalli Matar jikana Ali Gadanga kusar yaki” dan gajeren tsaki Meena taja mara kara tana kara dauke kai kaman taga kashi, ahankali Khairy takaraso gabanta sanan ta tsugunna har kasa akunyace tace “Gwaggo ina kwana” dungure kan Meena Gwaggo tayi tsabagen dadi tace “dan gidanku kalli yanda ake gaida manya ba irinku ba da kullum kedamuna da kud moni daga tsaye kuna shanyemin jini masu bakin hali, tashi tashi kinji diyata Allah ya lullubeki da albarka, zauna kenake dama ma fura zo zauna nan kusadani ke Meena matsa mata” gyara zama Gwaggo  tana kara matsa mata girgiza matakai Khairy tayi akunyace tana kokarin zama akasa dasauri Gwaggo tace “kul karki zauna akasa, sokike sanyi ya shigeki kina amarya, zauna nan kan kujera kusadani kiga, matsa mata Meena” tai maganan tana tunkude Meena wani mugun kallo Meena tama Gwaggo kaman ta maketa sanan ta tashi fuuuu tafice daga dakin Gwaggo tabita da harara tace “kinga bakin hali yan gidan nan ko dukansu haka suka gaji Wanan bakin halin daga wajen ubansu, zauna kiga” zama ahankali Khairy tayi kan kujeran Gwaggo itama ta gyara zama da kyau sanan takarasa kada furan tamika mata tace “ungo sha kena dama mawa” ahankali tasa hannayenta biyu takarba tana murmushi sanan takai bakinta takurba furan kadan dadi sosai tadade bataci abinci hakaba tass tashanye furan Gwaggo nawani irin murmushi sanan takarbi kwaryan tace “kawo nan kiga banson kiyi komi, ko sauro banson ya cijeki zan taya Aliyu kula dake harsu dawo daga kasan waje” kallon Gwaggo Khairy tayi dan batagane metake nufiba hakan yasa Gwaggo tace “yauda sassafe aka tafi dashi kasan waje sabida zuciyanshi ba lafiya Baban shi yakaishi wajen wani abokinshi likitan zuciya kidinga ma mijinki addu’a kinji In sha Allah zaiji sauki” gyadama Gwaggo kai tayi ahankali tana kokarin rike hawayenta dan duk itane dalilin Wanan rashin lafiyan nashi.


Yan aikin Mami ne suka shigo da manya manyan kulolin abinci zasu ijiye a falo tace “tafin musu dashi chan dakin Amarya” wucewa cikin sukai sa abincin, ahankali Gwaggo tace “tashi kije kiyi Kari ki kwanta ki huta anjima kawayena zasuzo su ganinki kinji” gyadama Gwaggo kai tayi sanan ahankali tace “nagode Gwaggo” wani irin washe baki Gwaggo tayi tace “ohh Allah yabani mai mini godiya, gantalallun yaran gidan nan kome zan musu babu godi bare nagode, yimaza jekiyi Kari ki kwanta kihuta Khairiya Allah yamiki albarka” wucewa ciki tayi tana dan murmushi.



Da rana kawayen Gwaggo tsofaffi su kusan goma sukazo gidan damai kidan kwarya, wasu tsofaffin wakoki suka dingayi suna sa Khairy rawa sai dariya ake kafin daga baya su bata gift nasu, buhun gishiri, goruba, aya dasauransu sai dariya ake sanan suka tafi wajajen 6.



Bayan sallan isha’i mota yazo zai tafi da Batool da Amal Khairy tai kuka kaman me hakanan tana gani suka tafi babu yanda ta iya aka barta ita kadai agidansu Aliyu danma Gwaggo na sonta kaman tahadiyeta da abin duniyan sun mata yawa.

*****


Shigowa yayi falon Ammin nashi ahankali yana sanye da  jumper na faran shadda yayi kyau saidai yadan rame da ita kanta Ammin tagani but she knows he will be fine, tashi Baffa yayi babu yabo ba fallasa yakalli Ammi dabasa wani good times yanzu sosai saidai yamaida ita yace “muje ko” gyadamai kai tayi tana murmushi sosai ta mike juyawa Zayn shima yayi sanan suka fito Mmotan Baffa suka shiga Zayn najan motan Ammi na nuna hanya harsukakai gidan Aminiyanta dasuke kira da Hajiya Kwangila.



Babban gidane sosai ga ma’aikata ta ko’ina suna parking a compound din wata mata wacce kibanta kenan kaman na Ammi bakinta hakoran makka guda hudu na gold sama biyu hakiran kasa biyu tafito cikin shiga na alfarma tareda mai gidanta wanda yakenan business mogul Chanchangii kenan, karasowa sukayi matan tawani rungume Ammi tace “barka da zuwa aminiyata, ina yini Alhaji” tai magana tana gaida Baffa dake gaisawa da mai gidan cikin mutunci sanan takalli Zayn da kanshi ke kasa ahankali yace “ina yini” cikeda fara’a tace “surukina Zayn Oya dan Allah kushigo kun tsaya anan” tai maganan tana kama hannun Ammi sukai ciki shikuma Zayn yagaida Baban daya rungume shi cikin ao sanan akai cikin gida, wani lafiyayyen falo suka shiga aka zazzauna yan aiki suka shiga kawo kayan kwalama shaaaaa kafin sugama suwuce.

Cikeda natsuwa Baffa yay gyaran murya yace “Alhaji to ga d’ana nan Zayn, da izininka inaso idan ka aminta dashi kabashi permission na neman yarka, idan sunga juna sun aminta da juna sai mufara maganan aure ko” wani kallon juna da Ammi da Hajiya sukayi sanan suka kama hannun juna suna murmushi, Alhaji yace “Alhamdulillah Alhamdulillah, naji dadin hakan kuma ina fata Allah yatabbatar mana da alkhairi kira Aisha wife” tashi Hajiya tayi tai sama sanan Alhaji yace “sunan Y’ata Aisha, a UK tai karatu tayi Mass com, Aisha nada kirki dakuma hankali da girmama na gaba da ita” ahankali Baffa yace “Masha Allah” 

Wani hadadden daki Hajiya tashiga ganin wata yarinya zauna gaban madubi tasaka hadaddun kaya tajuya ma kofan baya yasa tace “wai dan gidanku Aysha bazaki sauri ba maisa bakijin magana ne namiki alkawari zakiso Zayn” hawayen idanunta tashare ahankali tace “Momy ni Zayn din danakeso daban dan Allah ki karamin 1month na nemeshi yana nan Abuja kinji” fizgota Mom tayi tadagata ciked masifa tace “wlh zan kwada miki mari nizaki maida karaman mutum ga yaro chan da iyayenshi afalo da babbanko kinki fitowa dau gyalenki jor” ahankali tadauki gyale zata yafa karba Mamanta tayi tayafa mata tana murmushi tace “kinga yanda kikai kyau kuwa wuce muje” yakama hannunta saukowa falon sukayi, tunda suka fara saukowa Zayn ke kallonta idanunshi kur akanta jiyayi zuciyanshi na bugawa fat fat fat ahaka har suka karasa saukowa kasa kanta nakasa tace “ina yini Abba, Mom ina wuni” daga Baffa har Ammi murmushi sukayi ganin yarinya mai natsuwa gata kyakkyawa gatanan fara kaman Zayn din, murmushi Ammi tayi sosai tace “Zayn tashi kuje garden ku zanta mu muna nan muna namu na manya” dasauri Hajiya tace “kai shi Garden Aisha” tashi tayi ahankali kanta akasa hakama Zayn shiya fara gaba suka fita tana biyedashi kanshi akasa har zuwa garden suna shiga garden yawani irin fizgota da mugun karfi baki tabude zatai ihu yadaura hannunshi kan bakinta yana mannata da bango yana wani irin huci ware idanu tayi gabanta na mugun faduwa ganin Zayn Zayn data dade tana nema, hannunshi yazare daga bakinta yanunata da yatsa yace “how dare you Ayshu” wani irin murmushi tayi tanaji kaman zuciyanta zai fito sabida murna tace “Zayn” da yatsa yanuna ta yace “listen to me kome zaki fadama iyayenki kifada musu baki sona karki sake kibari ahada Auren nan dan bazaki taba jin dadin aure na, i can’t marry a girl datasan namiji awaje” wasu hawaye masu zafine suka zubomata murya chan kasa tace “Bantaba son wani namiji kaman ka ba Zayn” yana kallonta in the eyes yace “amman kuma kika bama wani chan virginity naki” jitayi zuciyanta yamata zafi, ahankali tace “I regretted everything, I had sex once u were the second sex danayi in my life dan Allah that shouldn’t be a barrier to aurenka Ya Zayn idan bansameka amatsayin miji ba I can die” dauke kai Zayn yayi yawuce kawai yaje yazauna rayuwan shi babu abinda kemai dadi but he just feel Allah ne ke kamashi, he has been a bad boy, yaci mata daban daban turawa yasha shisha gashinan yanzu the only woman daya taba samu bai sameta ba, look at yarinyar da Allah yahadashi da ita his life is ruin.



6️⃣1️⃣

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️






Yau one month kenan da bikinta, Baba, Anty Mariya dasu Ya Manaf babu wanda baya kiranta yaji yaya take hakan namata dadi. 

Ko kadan babu wani wanda yake kuntata mata agidan kawai dai she feels agidan Gwaggo kadai ke sonta da Dad sauran harda Mami duk basa sonta barinma Meena, ko Meena natare da Gwaggo dazaran tazo wajen zata tashi fuuu tafice, hakama su Amal da Khadija, Mami kam ko kallo bata isheta ba gashi batada hanyan waya da Ya Aliyu taga yayake, tana zaune da Gwaggo dabata barin ko tsinke ta taba kullum cikamata ciki da abinci da magani, bata wani iyacin abinci ko Gwaggo ta lurada hakan fura indomie sune tafici indomie shine kadai aikin da Gwaggo tabari tanayi shima sabida taga tana sone.



Yau ma kaman kullum tana zaune adakinta taji Gwaggo ta kwala mata kira, da sauri ta sauka daga kan gadonta tana sanye dawani simple dogon Riga na atampa kai kyau, dan kwali tadauka tadaura sanan ahankali tafito daga dakin nata tabude kofa tazo falon ganin Dad yasa wani irin kunya yakamata da sauri tajuya takoma daki Gwaggo tai dariya tace “kaganta nan Abdul haka yarinyar nan keda kunya wlh naji dadi da Aliyu yasami yarinya mai natsuwa haka, mayafi takoma tadauko fa” dan murmushi Dad yayi danshi kanshi ta burgeshi, bata wani jimaba tafito da Babban mayafi sanan tazo har gaban Dad ta tsugunna zata gaidashi dasauri yace “Ummulkhairy zauna zauna” ahankali tazauna sanan kanta na kasa tace “Abba ina kwana andawo lpy” ahankali yana kallonta yace “lpy lau Ummulkhairy yaya kike hope babu wani matsala ko” gyadamai kai tayi ahankali zuciyanta namata wani kalan dadi buri ta kawai taga Aliyu, kaman Dad yashiga mind dinta anatse yace “Aliyu yaji sauki garau Alhamdulillah, amman mun baroshi chan ya tsaya yin wasu abubuwa nan bada jimawa ba shima zai dawo” gyadama Dad kai tayi ahankali tanajin hawaye na zuwan mata amman tadaure tahana kanta yi, dan murmushi Dad yayi yace “Bayan aurenku nai tafiya batare dana baki gift dinki ba Ummulkhairy, ungo” Dad yay maganan yana mikamata key mota, ahankali tadago kanta takalli Dad dake mikamata key ahankali tasa hannunta takarba kafin tamai godiya Dad yace “mota nasiyamiki as my gift, nasan baki iya tuki ba nai hiring direba dazai koya miki tuki cikin 3 weeks yatafi kidinga jan motanki da kanki kullum zai dinga zuwa yana daukanki 3hrs daily kinji” wani irin murmushi tayi har ranta taji dadi tace “Abba nagode Allah yakara budi” sanan ta taho wajen Gwaggo anatse tace “Gwaggo Abba yabani mota” wani irin murmushi Gwaggo tayi tace “Iyye akashe lafiya muje Muga motan” tashi tayi tana kama Gwaggo suka fice Dad yabita da kallo now he sees why danshi ke sonta Ummulkhairy is extremely calm ga natsuwa hankali ga kunya wani mad Benz Dad yabata sabo fil ko Leda baa cireba, fitowa Mami tayi kallo daya tama motan takoma daki abinta, Gwaggo tace “Oya shiga kitafi kifara koya kai ka ko yamata mota ahankali kajini ko” Gyadamata kai direban yayi sanan suka tafi, shi kanshi Direban saida yay mamakin yanda tai catching up kome yake ko yamata fast.



Kullum direban ke zuwa before one week Ummulkhairy ta kware saidai yan abubuwan dabaza arasa ba bayan 2weeks direban yafadama Dad ta iya, Dad dakanshi ya shiga motan nata tajasu har zuwa inda zaai mata license, nan da nan aka mata komi sai murmushi take, sanan Dad yakaita shopping just to make her happy dan harga Allah yanason Yariyan kuma kome yaranshi keso yanaso dudda Aliyu na claiming baya sonta kawai jinshi yake u can’t fight love bari yadawo, duk wani abu datakeso saida Dad yasaya mata saida yamma sanan ta tukosu suka dawo gida parking tayi a compound din batare da Dad yafita daga motan ba yace “Ummulkhairy” kallon Dad tayi ahankali tace “naam” ahankali Dad yace “I know kin damu this is almost 2month dabikin ku bakiga Aliyu ba, Aliyu is fine he’s just going through a lot now, but I assure you yakusan dawowa, all I want from shine ki kwantae da hankalinki idan wani abu nadamunki always come to me, always come to me, sanan duk randa kikeji zuwa wani gu saloon or wani abu ko bananan kifadama Gwaggo ko Mami kafin kitafi, ki kula da kanki kinji, everything will be fine, Allah yamiki albarka” ahankali tace “Ameen Abba nagode” tashi kije zan sa’a kawo miki kayanki ciki” gyadama ABBA kai tayi sanan tawuce ta tafi.



6️⃣2️⃣




Bayan 3 month!

Sosai Ummulkhairy tai kyau kyau da wayansu barinma some kawayenta cewa suke tanada ciki nan ko basusan haryau batama saka angon nata a idanu ba, tayi kyau sosai fatarta tai fresh yana wani walkiya, jikinta ne har yanzu bai dawo ba sabida rashin iyacin abinci, yanda Gwaggo da Dad ke sonta abin har mamaki yake bata ita badadan tamasan yanda Baba ke sonta ba dazata iya cewa Dad yamafi Baba sonta itadasu Mami dasu Meena haryau suna nan yanda suke. Wuraren 10 tashiga bayi danyin wanka bayan tagama gyara dakinta dana Gwaggo dudda Gwaggo tahanata amman ina taki tasaka turaren wuta, wanka tayi tafito tana kallon wani kofin tsumi da zafinshi akan madubinta tasan aikin Gwaggo ne tun kafin bikinta har zuwa yau babu ranan da baa bata magani dauka tayi tasha tana tabe fuska sanan ta shafa mai tadauko wani pencil gown na atampa light blue da ash tasaka yama jikinta dam yafito da kyanta fitowa falo tayi Gwaggo tace “wuce kiyi kari kafin kitafi saloon din amiki kitso, Baban ku yama ijiye miki kudin saloon din kafin yafice asibiti yanakan gadona jekiyi kari tukunna masa ce da farfesu” gyadama Gwaggo kai tayi sanan tawuce ahankali tadebo masa biyu kachal tazuba farfesun tadawo kusada Gwaggo tazauna tagumi Gwaggo tayi tace “ohh ni bantaba ganin makiyar abinci irin Khairiya ba” dan murmushi tayi tafara ci biyun ma sabida Gwaggo tasata agabane tacinye tass sanan ta tashi takai kwanon cikin wankewa tayi takife sanan takoma daki, wani karamin gyale ash tadauka da karamin hand bag da wayanta da car key dinta tafito, Gwaggo tabita da kallo tace “yarinyar kirki kinga yanda kikai kyau kuwa” murmushi tayi Gwaggo tace “saima kinyi kitso da lalle zakiga yanda zakiyi kyau yau jedauko kudin akan gadona” wucewa dakin Gwaggo tayi tadauki kudin datagani kan gado yan 1k bamatasan iya yawansu ba tafito rikedasu zatabama Gwaggo Gwaggo tace “inyi me dasu wuce kitafi sabida agama dawuri” gyadama Gwaggo kai tayi tace “Gwaggo natafi insiyomiki goro idan zan dawo”? Dasauri Gwaggo ta Gyadamata kai tace “eh adawo lpy ayi tuki ahankali” gyadama Gwaggo kai tayi sanan tawuce tafita daga dakin, wajen motarta tahango Meena tsaye taci gayu kaman fita zatayi hango Khairy nazuwa yasa tajuya baya ta tashi daga jikin motarta karasawa wajen Ummulkhairy tayi harzata shiga motanta saikuma taji no bazata iyaba she needs to talk to this girl today, dawowa tayi sanan tasha gabanta tana kallon fuskanta ahankali tace “Meena ina zaki I can drop u naga direban ku bayanan, let’s go with my car” dauke kai Meena tayi tace “I don’t need anything na wacce tayaudari Yayana taso takashe shi, I hope idan yadawo yarabu dake cus u don’t deserve Ya Hydar wlh” ji Ummulkhairy tayi jikinta yay sanyi all this while dama tasha zargin fushin da Meena keyi da ita kenan gashinan yau ta tabbatar, kasa motsi tayi ganin haka yasa Meena kawai taja tsaki tawuce side din Gwaggo, Khairy takusan 3min ahaka sanan tawuce tabude motarta tashiga sanan tadata aka budemata gate tafice, wani babban saloon taje aka wanke mata kai akai drying kalaba tasa aka mata yan kanana sanan tasa amata red lalle dan batason baki nan aka shiga mata wani lafiyayyen jan lalle atafin hannu da yatsu dakuma kafanta, bayan angama around 3 tasa aka mata facials da lip therapy, wani irin kyau fuskanta yakarayi lips dinta yay jajir wuraren 5 tagama komi tabiya kudi sanan tafito, tsayawa tayi agaban building din tasaima Gwaggo goro sanan tadawo tashiga motanta ta tada motan taja tana kallon hannayenta yanda sukai kyau kaman wata Amarya tana kallon fuskanta ta madubi kaman ba itaba fuskanta yay kyau lips dinta kaman na new born baby tsabagen pink din dasukayi, ahankali take driving abinta looking so adorable harta shigo anguwansu, tsayawa gaban gate tayi tai horn daidai wayanta na ringing kallon wayan tayi ganin Batool ne yasa da sauri tadauki wayan da hannu daya tasa akunne daidai ana bude mata gate batare dayama kalli cikin gidan ba taja motan tana waya. 






“Mara mutunci wai bazaki zo wajena ba” parking tayi awajen parking sanan takashe motan tabude tafito ahankali waya na kunenta still tana sauraron labarin da Batool kebata awaya, sanan tasa hannu tadauko jakanta da ledan goron Gwaggo kafin tadauki gyalenta dake kan sit tarike a hannu shima sanan tamaida kofan tarufe tafara tafiya tana murmushi tace “are you serious Batool, yanzu yaushe zasuzo asa ranan I am so happy for you Batool” tai maganan tana kokarin saka hannunta tabude kofan dakin Gwaggo daidai anrigata bude dakin,  Amal da Khadija suka fito dagudu dan Gwaggo ce tabiyosu sata sukai mata ko kadan basusan da ita ba suna bude kofan suna fitowa aguje suna bugeta wani irin ihu tayi daga jakanta wayanta dake kunnenta da car keys din hannunta zubewa sukai akasa itama tai wani irin baya zata fadi dan gabaki dayama tasadakar faduwa zatayi chak taji an tarota bayanta yafada kirjin mutum hannunshi gabaki daya kan flat cikinta ta kankame idanunta gam sabida yanda ta bala’in tsorata ahankali ta furta “Ya Aliyu” danshi kawai yafado mata arai yanda he always hold her idan zata fadi, tsayawa chak Amal da Khadijan sukayi jikinsu narawa suna kallon Gwaggo datafito arude tace “Innalillahi badai ihun Khairy naji ba zubarmin da diya kukayi” murya dakuma kamshin turaren da bazata taba manta kalanshi ba da jikin datasaba jinshi ba yasa ahankali tashiga bude idanunta tadaurasu kan Gwaggo dake gabanta tana kallonta, dasauri Gwaggo tace “sannu Khairiya da Aliyu bai tareki ba dakinyi mummunan faduwa barayin banza kawai ku kwashemata kayayyakinta” ahankali tagyara tsayuwanta jikinta narawa gabanta nafaduwa sotake tajuya takalli Aliyun amman takasa tsoron yin hakan ma take tanajin beating heart dinshi abayanta, gently taji yana zare hannunshi dagakan cikinta kafin yacire gabaki daya, gently taji yaraba jikinshi da nata yajuya dasauri, dasauri Gwaggo tace “bazuwa kayi kasha furan ba dakace nadama maka” kaman daga sama Ummulkhairy taji maganan Aliyu.

“Nafasa sha adakin ki, kiba yaran nan sukawomin” Dawani irin sauri Ummulkhairy tajuya tadan saci kallonshi bayanshi kadai ta iya tagani dudda bataga fuskanshi ba gani tayi yakara wani irin haske gashin kanshi yakara yawa kaman tunda yaje baiyi aski ba gashin yay baki sun nannade looking so coily, hannunta dataji an kama yasa dasauri tajuyo Gwaggo ce tana rikeda kayayyakin ta dasuka fadi akasa tace “wuce muje kukuma barayi duk wacce tashigomin daki wlh saina chanza mata kamanni” dariya su Amal sukayi suka wuce flat din Mami abinsu.


Suna shiga daki Gwaggo tace “dazu kina tafiya Saloon mijinki na dawowa nai nai da shegun yaran nan sukiramin wayanki nace ki dawo sukaki, zoki kaimai furanshi flat dinshi kidawo” kallon Gwaggo tayi dasauri hakanan taji gabanta nafaduwa kwaryan furan Gwaggo tabata data rufe ahankali takarba tana kallon Gwaggo, Gwaggo tace “wuce ki kaimai tunda yadawo baici komi ba yanzu ma da kyar nasamu yace zai sha furan, tafi kafin yay fushi” Gyadamata kai tasake yi sanan ahankali tajuya jikinta rawa yake sosai tafice daga dakin tai flat din Ya Aliyun kirjinta na bugawa more the more she’s getting closer to flat din, tsayawa tayi agaban kofan takasa motsi ahankali tadaga hannunta knocking kofar tayi shiru babu wanda ya amsa babu wanda yabude mata takai kusan 3min ahaka sanan kaman wacce tazo sata tasa hannunta tabude kofan ahankali tana kallon falon ganin bataga kowa ciki ba yasa ahankali tashiga cikin falon dakenan sanyin Ac mix da kamshin turarenshi, ahankali takai kwaryan furan kan centre table na dakin tsugunnawa tayi ta ijiye sanan tamike tsaye dasauri tajuya zatai kofa tafice kaman daga sama taji muryan Ya Aliyu yakirata. “You!” Chak ta tsaya batare daya juyoba gabanta nafaduwa sosai, cikin wata kalan murya da she will define it more of hatred voice yace “zokidau abinda kika ijiye and take it out” gyadamai kai tayi ahankali sanan tajuyo batare datama iya dagakai takalleshi balle tamasan daga ina yakamata maganan ba sanan tazo ahankali ta taugunna tadauki furan sanan tamike tsaye. “Next time idan tanason naci kome tamin tabama wani yakawomin not you” wani irin sanyi jikinta yayi dasauri tadaga idanunta dasuka wani cikeda hawaye ganinshi tayi yana tafiya akan stairs zai koma sama bakinta harwani rawa rawa yake tace “Ya…..Ali….yu” chak ya tsaya batare daya juyo yakalleta ba, ahankali takai dayan hannunta dat is very tashare hawayen dasuka zubomata sanan gently tace “Ya Aliyu I am sorry, dan Allah kayafemin”




6️⃣3️⃣





Wucewa sama taga yayi abinshi batare daya juyo yakalleta ba, tadade tsaye awajen sanan ahankali tajuya tafice daga dakin rikeda kwaryan furan jitayi babu abinda kemata dadi, dakin Gwaggo tashiga ganinta da kwaryan furan yasa Gwaggo tace “ya shanye”? Girgixama Gwaggo kai tayi tace “yace bazai sha ba” cikeda masifa Gwaggo tace “shiya sani ijiye kije kihuta abinki kinji” ijiyewa tayi sanan tawuce dakinta tana shiga tafada kan gado kwanciya tayi dasauri tafashe da kuka sosai murya chan kasa tace “he hates me, he hates me” tama rasa mezatayi wayanta da Gwaggo ta ijiye mata akan gado ta dauka sanan tai dialing number Batool tana kira tadauka tace “maiya sameki dazu naji kinyi ihu haka faduwa kikayi” kasa magana tayi kawai tafashe da kuka cikin kuka sosai tace “Batool Ya Aliyu yadawo ya tsaneni sosai, Batool I don’t even know what to do dan Allah help me, kinji” yanda taji tana kuka yasa Batool tace “batun yauba bayan kin bani labari what u told him nagayamiki kinyi kuskure Khairy that’s not how to make him rabu dake, but that one now is bygone, yariga yafaru Khairy rana daya so baya komawa yazama ki, bansan Aliyun kiba kene kika sanshi, kinsha bani labarin fushin shi da Kishin shi, Aliyu na sonki har gobe har jibi so ma mai karfi kuwa, you should just be diplomatic about it, kinunamai kin waye u are a graduate, cikin sauki kija ra’ayinshi make him come for you batare dayasan he’s even coming for you ba, you know his weak point, karki bada mata please, zan turamiki number M shakur kibiya kudi ki shiga group din matan aurenta kiga yanda ake karkato da hankalin muji mai taurin kai stop crying kinji kiyi wanka pray kije ki nemi abinda zakici” gyadama Batool kai tayi ahankali murya chan kasa tace “thank you” katse wayan Batool tayi hakan yasa ta ijiye wayan share hawayenta tayi tass sanan tasauka daga kan gadon, ahankali tawuce bayi bayan tacire kaya tana kallon kalaban da akamata dasukai bala’in kyau kaman anmata kafin attachment nan ko gashinta ne, hannunta tanunama madubi ta kalla shima yayi kyau sosai sanan tawuce tai wanka tadauro alwala tafito daure da towel akirji tabude wardrobe wani rigan bacci pink tasaka daya saukan mata zuwa guiwanta, rigan bacci yazo dawani open cap dinshi hakan yasa ta ijiye cap don kan gado tahau kan dadduma tai sallan magrib, tana idarwa wayanta tadauka takira Ya Maheer sunata hira sai wajen isha’i sanan sukai sallama ta tashi tai sallan isha’i, jin cikinta na kuka dan saida yanzu ta tuna tun wainan safe bata sakecin wani abu ba yasa ta tashi hulan kayan baccin tadauka tasaka ipen cap ne hakan yasa duka gashinta yazubo gadon bayanta, tai kaman wata Cinderella, silipas dinta na gida tazura akafa sanan tabude kofa tafito ko kadan batasan Aliyu na falon ba saida tafito falon, da kallonshi kadan tayi tadauke kanta dasauri sai yanzu nema taga fuskanshi woww! Wlh kaga Ya Aliyu zaka dauka balarabe ne gashin gemunshi da sajenshi sundan kara yawa kadan daya haskaka fuskanshi, yana kwance kan dogon kujera waya a kunnenshi yana magana ahankali, kallo daya tamai tadauke kai dasauri Gwaggo dake binta da kallo tace “indomie ko Khairiya”? dan murmushi tayi akunyace dayar karaman muryanta tace “Gwaggo Kwai zan soya” tai maganan zata shiga ciki dan kunya takeji Ya Aliyu yaganta ahaka daga ita sai Yar rigan baccin da pant da tasaka aciki ko bra bata sakaba, ganin zata komaciki yasa Gwaggo tace “ina kuma zaki yoo ba kitchen zakiba tundake bakicin abincin da normal mutane keci” ahankali tace “Gwaggo hijabi zan dauko” baki Gwaggo tasaki tace “yau kuma nikike sama hijabin koko mijin naki Hydar, wuce kitchen kije kinemi abinci kisama cikin ki kafin ciwon yunwa yakamaki” gyadama Gwaggo kai tayi sanan ahankali tafito tawuce feeling so uncomfortable tana tafiya kafafunta na harhardewa, daga inda yake kwance dudda waya yake but all abubuwan da Gwaggo kefadi yanaji, kasa hana kanshi yayi yakalleta dan satan kallonta yayi sanan yamaida kanshi kan wayan dan bayason yana kallonta motsamai da soyayyanta yake aranshi, juyowa Gwaggo tayi tana kallonshi cikeda korafi tace “ni babanka yamazo yay maganan bikinku akaita chan gidanka, yarinya batacin abinci salon wani abu yasameta ace nine bana bata abinci Iyye ni wlh banajin dadin wanan lamarin ko kadan, tun safe fa waina biyu kawai taci bata karacin wani abu ba” kofan da aka bude yasa tajuyo ganin Meena ne yasa ta watsa mata harara tace “munafuka dayake yayanki yadawo dole na ganki a bangarena to fita” dariya Meena tayi tashigo wata kyakkyawan budurwa dake kama da Mami biyeda ita tace “Hajo tazo hutu gidanmu shine fa nakawota ta gaidaki, Mami tahanamu dafa indomie a kitchen dinta shine mukazo mudafa anan” tai maganan Meena na zama kusada Ya Aliyu da gama wayanshi kenan yana kallon Meena, Hajo datadan saci kallon Aliyu tashigo tana gaida Gwaggo da Ya Aliyu dabai amsata bama sai tambayan Meena su Amal dayake tacemai sunyi bacci sanan ta tashi takalli Meena tace “zomuje mudafa” wucewa kitchen din sukayi Gwaggo na ihu karsu bata mata kitchen ganin Khairy a kitchen tana soya kokarin soya egg guda daya tahada tea a mug tana juyawa da cokali yasa Meena tajuya cikedajin haushi tace “zomuje” dasauri Hajo takalli Khairy da itama kallonsu taje batare data kulasu ba tace “akan mene muda kitchen din gidanmu zamu tafi” dan tana ganin Khairy tagane matan Ya Aliyu ce dantaga video bikin da akayi a gidan nan, wucewa Meena tayi tafice tace “to nidai ina falo kika dafa saiki kawo mana muci” tai tafiyanta itakuma Hajo tashigo kitchen din tana daukan tukunya daya dan tara ruwa tana habaici, “adai gama yawo da kaya babu breziya bazamu so mutum ba, dazu inaji rokonshi ake yama zauna da ita yanaki aikin banza” tafashe dawani makirin dariya, dudda maganan ya sosama Ummulkhairy rai batace komiba besides bamatasan waye yarinyar ba, juya kwanta tayi sanan tawuce tadauko plate tazo ta kwashe itakuma Hajo tadaura ruwa agas din tanabin Ummulkhairy kallo da gefen ido ganin yanda yarinyar keda shape dakuma diri ga kirji kaman zasu fasa riga atsaye fam dasu hada komi Ummulkhairy tayi a tray tazo zata wuce da gangan Hajo tazo dabaya dabaya kaman mai neman abu ta bangaje Ummulkhairy da saura kadan tafadi tai maza ta dafa fridge dinsu amman gabaki dayan tray da kwan ta dakuma shayinta saida yazube akasa da tray abin suka hadu sukai wani bala’in kara dayasa Gwaggo tai ihu daga falo tace “meya faru wayamin bari a kitchen!” Takalli Aliyu tace “dubomin kitchen dina dan Allah” 



Wani irin dago kai Khairy tayi zuciyanta na tafarfasa sabida bacin rai ta kalli Hajo, wani irin makirin murmushi Hajo tasakin mata tace “oops my bad” ji Ummulkhairy tayi tazo wuya dawani sauri ta yunkuro zata dauramata mari akunci. “Ummulkhair!” Taji muryan Aliyu daga bakin kitchen din yakirata, juyowa tayi takalleshi da idanunta dasukai ja sosai, kafinma yay magana ganinshi yasa Hajo tai kwabkwab da fuska kaman zatai kuka tace “Ya Aliyu sabida nazo na kunna gas kusada ita taketa zagina shine garin bangajeni tazubar da abinda datafa shine kuma zata maran, what is wrong with her” Dawani irin sauri Ummulkhairy tajuya tai kanta tace “nikikema karya”? Takai hannunta zata chakumeta cikin fushi Aliyu yashigo kitchen din Khairy ya kalla yadaka mata tsawa yace “ke wace irin mara tarbiya ce, why do you look for trouble? Get out of this kitchen, out!” Dawani irin sauri takalleshi jin yanda yadaka mata tsawa, daure fuska tamau yayi yana kallonta, jitayi kuka na zuwan mata amman ta daure wlh ba zatayi ba agaban yarinyar nan ba kuma wlh idan bataci uban uarinyar nan agidan nan ba ba sunanta Ummulkhairy ba, ahankali tajuya zata fice, fashewa da kuka Hajo tayi tace “Ya Aliyu batacemin sorry ba” batare daya kalleta ba yace “come back here and say sorry” chak Ummulkhairy ta tsaya bura’uba tsanan haryakai haka juyowa tayi da kanta ta kalleshi ido na cikin ido batare data kalli Hajjo ba, ahankali tace “sorry” sanan tajuya dasauri tafice Gwaggo dake zaune ganin Khairy tafito dagudu yasa tace “menene me aka miki?” tama kasa amsa Gwaggo dakinta tayi da gudu tamaida kofa tarufe tafada gado tana kuka.


Ahankali yasauke ijiyan zuciya yabi tea ta da kwan data soya da duk suka bare a kitchen din da kallo, yasan cewa he hates her bayamason yanasa idanunshi akanta dan the more he’s looking at her the more yana tuna abinda tamai amman jiyayi bazai iya yabari ta kwana batare dataci abinci ba.




“Ya Aliyu nadafa indomie dakai”? Kaman daga sama muryan Hajo yadaki kunenshi juyowa yayi yazuba mata mugayen eye dinshi dayasa taji zuciyanta yabada ras! Cikin kakkausan murya strictly yace “this should be the first and last time dazaki shiga harkan matata, off this gas get a mop and clean this mess kibar flat din nan” gyadamai kai tayi ahankali sanan yawuce yafita daga kitchen din yafito falo daidai Gwaggo nafitowa daga ciki tace “mekuka ma Khairiya take kuka”? Dauke kai yayi yana kwanciya yace “bansani ba” daidai Hajo nafitowa daga kitchen din bayan tagama abubuwan dayasata tayi ganin babu Meena ma afalon yasa tasan tawuce side din Mami, cikeda masifa Gwaggo tace “dan ubanki kika kara dawomin daki saina maidake  gurguwa fita” fita tawuce tayi Gwaggo ta ballama Aliyu harara tace “kaima wuce kafita bacci zanyi” akufule yace “saiki zo kifitar dani” tsaki Gwaggo tamai ta tashi tashiga ciki tace “kaiyita zama karube anan mai bakin hali” tawuce dakinta tashige ta kwanta kan gadonta ranta abace akanbar shikadai afalon.




6️⃣4️⃣






Shi baimasan mesa yama damu dabataci abinci ba taje ta kwanta, dan gajeren tsaki yaja sanan yatashi tsaye yawuce corridor yashiga yana kallon dakin Gwaggo da wuta kenan kunne, hannu yasa yadan daga labule ganin Gwaggo yayi kan gadon kauyenta dan haka suke kiran gadonta babu yanda basuyi da itaba Dad ya chanza mata gadon nan ba amman taki tamakalema gadon kaman mayya tana kwance share share tana bacci tabude baki tana minshari nada kara sosai hararanta Aliyu yayi yasaki labulen ahankali yace “fitinanniyan tsohuwa” sanan yakalli kofan dakin da Khairy keci dakenan akulle dan jim yayi yana kallon dakin kaman wanda aka ingiza yawuce gaban dakin ya tsaya yay shiru yana kallon kofan kafin ahankali kaman barawo yasa hannu yabude kofan ahankali wani kalan cool kamshinta ne mai bala’in dadi yadaki hancinshi dasaida yasa yasauke ijiyan zuciya ya lumshe idanu tareda budewa sanan ahankali yasa kafan damanshi sanan yashiga dakin dakenan da duhu yasa hannunshi ahankali yakunna wutan dakin yanabin ko’ina na dakin da kallo dayake nan tsaf tsaf very clean a tidy kafin ahankali yasauke idanunshi kanta, tundaga kan kafafunta yake kallonta sai yanzu yakema kallon kafan da kyau da jan lallen yamai kyau kaman yaje yashafa, dogayen kafafunta very fresh yabida kallo harzuwa kan cinyanta kafin idanunshi yasauka kan cikinta dayay flat pas kaman bata tabacin abinci ba gently yasauke idanunshi kan boobs dinta he knows yanason Ummulkhairy but baitaba tsayawa yamata kallon kurilla ba sai yau sabida yau yasan halas yake kallo, baitaba sanin she’s this booby ba sai yau wani kalan ijiyan zuciya yasauke bashiri sanan yakalli fuskanta she’s sleeping peacefully da dan ragowan hawaye a idanunta kitson kalaban datayi duk sun zubo gaban fuskanta kaman yadauketa yagudu yakeji tafin hannunta yakalla dayaga lalle sunma hannunta kyau wayanta dake side drawer dayay vibrating yay wajen yana tafiya without making sound screen din wayan yakalla messege yagani daga Batool.

“Kinsamu kinyi apologyzing din” hannunshi yasa yadauki wayan ahankali sanan yabude yana karanta all messages datakema Batool din tun bayan aure, daga tace takasa daina tunaninshi batasan halin dayake ciki ba no body is saying anything to her saikuma messege datama Batool nacewa Gwaggo da Dad kadai kesonta, Meena hate her waita yaudari Yayanta, Mami kuma doesn’t even look at her zare idanunshi yayi daga wayan yakalli fuskanta sonta har tsakiyan bargon kashinshi yakeji but at the same time yakasa dainajin haushi ta da tsananta on abubuwan data fadimai kan Zayn is just like abu biyu na dambe azuciyanshi SO da TSANA, saida yagama bincika wayan nata tass sanan ya ijiye yakalleta.


“Ke!” Yadaka mata tsawa daga inda yake tsaye akanta ko kadan batamayi motsi ba, dan gajeren tsaki yaja sanan yakai hannunshi ya bubbuga filonta tareda kiran sunanta da karfi. “Ummulkhair” wani irin firgita tayi tawani taso saura kadan ta tumbulo daga gadon yatareta da hannunshi dawani irin sauri takalleshi idanunta sundanyi ja na nuna alamun bacci acikinsu, hannunshi yadan kalla yanda ta rirrikeshi kaman zata shige jikinshi ganin tafarka daga baccin tass yasa yadaure fuska yace “cikani” ahankali tazare hannayen ta da jikinta daga nashi tana komawa baya sanan taja bargo tana kokarin rufe jikinta zuwa kirjinta, dauke kai yayi batare daya kalleta ba yace “go and find something a eat, nobody sleeps with hunger agidan nan stand up” wani abu taji yazo mata wuya hakan yasa takalleshi ganin ko kallonta bayayi yama dauke fuska ne yasa ahankali tasaki bargon ta tashi daga kan gadon wardrobe tabude tadauko wani doguwan rigan boubou sanan tashiga bathroom dagudu jin tabude kofan bathroom yasa yajuyo yakalli kofan bathroom din, bude kofan tayi ahankali tafito kampala boubou yamata wani kyau ajiki tama manta babu Dan kwali akanta ta gefenshi tabi tabude kofan dakin tafice yajuya tail yana kallonta kaman baitaba ganinta ba yadade tsaye awajen sanan yawuce yafita daga dakin yadawo falo a dinning yaganta zaune tazuba wani dan karamin rice tasa spoon tana kallo batare datama tababa. 



Dan jim yayi sanan yataho batare dayace mata komi ba yabude flask na rice don dayake nan da zafinshi yadebo yakara mata akai abincin takalla sai kawai tashiga raira kuka ahankali, wucewa da sauri yayi yawuce falo yay kwanciyanshi akan kujera tadade tana rera kukan sanan tagoge fuskanta tadauki spoon tashiga cin abincin tana turo baki baisan ya akayi ba samin kanshi yayi da ciro wayanshi daga aljihu ya danna video yana mata tanacin abinci tana turo baki tana goge hawaye da bayan hannu kamna irin kananun yaran nan da aka tursasa suci abinci yana wajen yana mata video har saida ta cinye sanan tazuba ruwa a cup tasha batare daya kalleshi ba ta tashi daga dinning din fuuuu tai ciki samin kanshi yayi da dan murmushi sanan ya tashi daga kan kujeran yay wajen dinning din yana kallon plate din da cokalin dake plate din data bari awajen samin kanshi yayi da bude warmer yadebo rice shima yazuba plate din sanan yadauki spoon dinta yadebi rice din yakai bakinshi yayi dan murmushi daidai wayanshi na vibrating kafin ma yakalla yasan dad ne hakan yasa yatashi yadauki plate na abincin yafita daga daga flat din Gwaggo yanaci zuwa flat din su Mami Dad ne kadai zaune a falo glass a idanunshi yana wasu yan ruCbuce rubuce.





6️⃣5️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




Ganin Aliyu yasa ya ijiye komi yature yana kallon plate na abincin hannunshi yace “sai yanzu kake dinner Aliyu” gyadamai kai yayi yana zama kusada Baban nashi ahankali, yace “Dad ina yini” Dad na kallonshi yace “how are you”? Abincin ya ijiye ahankali sanan yace “am fine Dad” shiru Baban yayi yana kallonshi sanan anatse yace “Aliyu kadawo don’t you think yakamata kamin magana” dan shiru yayi yasan mai Dad kefadi kafin ahankali ya yatsine fuska murya chan kasa yace “Dad I told you I don’t like her again” shiru Baban yayi yana kallonshi kana ganin yanda yake magana kasan karya yakema kanshi abinma saida yasa Dad yadan murmusa yace “duk fushin nan dakakeyi naka na banza ne, ranan dakadan bude idanunka dana sanar da kai na aura maka Ummulkhairy daga ranan kafara jin sauki, koda kaga nadawo na barka dakacemin ba yanzu zaka dawo ba I just leave you ne dan nasan you need time to clear your head dan haka Aliyu bikinku nan da 3weeks” dan zaro idanu yayi yana kallon Dad, mugun kallo Dad ya watsamai yace “and kafito da kudi ka kawo aje ahado mata akwatin aurenta kaji sauki ko biyar dina bazan kara kashemaka ba dan kaji” dan murmushi yayi yaka plate din abinci yafara ci yasan kawai tsokananshi Dad yake, Dad dake kallonshi shima yana murmushi yace “inaso kuma gobe ka kaita chan gidan Baffan su gobe zasuyi sha’ani nasama Yayanta Zayn rana da wacce zai aura Aisha” ko kallon Dad baiyiba saima cin abincin shi dayacigaba dayi Dad yace “kanajina” gyadama Dad kai yayi kafin ahankali yace “yes Dad” Dad yace “kaje duk wani gyare gyare daza’ayi agidanka kasa ayi, zan kira Baban ta gobe nacemai mun tsayar da ranan bikinku da tarewanku nan da 3 weeks, tashi kaje” ahankali yadauki plate din yatashi haryakai kofa Dad yakirashi. “Gadanga” juyowa ahankali yayi yakalli Dad, dan murmushi Dad yayi yace “I can’t wait to see my grandkids” Dawani irin sauri yabude kofa yafice Dad yahau dariya sosai kaman wasu abokanai yadade yana dariya kafin yamaida glasses dinshi yacigaba da aikin dayakeyi.




Side din Gwaggo yawuce yana mamaki yanda harwani dadin zuwa side din Gwaggo yakeji yanzu shida da kyar da yake zuwa bude kofa yayi ya shiga akan kujeran falon ya ijiye plate din sanan yau corridor yana yatsine fuska jin mazuran Gwaggo ahankali yakarasa gaban kofan dakin Khairy bude kofa yayi ahankali hada idanu yayi da Khairy data fito daga bathroom ganinshi yasa ta tsaya chak tama kasa magana, binta yayi da kallo daga sama har kasa yanda take wasa da yatsunta sanan yaja wani gajeren tsakin jin takaicin mema yake pulling dinta towards him, juyawa dasauri yayi zai fita dasauri tace “Ya Aliyu wait!” Dan juyowa yayi yakalleta kaman yanda take kallonshi lips dinta nawani irin rawa tana kokarin magana, ganin takasa fadin anything yasa dasauri yafice hakan yasa da sauri tadauki hijabin salla ta dake kan dadduma tasaka tana binshi kafin takai falo harya bude kofa yafita da sauri tabishi tana kiran sunanshi ahankali ganin darene.


“Ya Aliyu, Ya Aliyu wait please” flat dinshi ya shige yamaida kofa yarufe daidai takai gaban flat din, muryanta narawa tai knocking kofan tana kiranshi ahankali dan so take tabashi hakuri she is tired of yanda yakejin haushinta. “Ya Aliyu open the door please and listen to me, Ya Aliyu” tai maganan hawaye na saukowa daga idanunta tana knocking still, wani irin bude kofan akayi da saida taji gabanta yafadi kawai hannunshi tagani yawani irin fizgota cikin dakin dayake nan dimdin wutan ko’ina na falon akashe sai bala’in kamshi da sanyin AC da dakin keyi, yanda ya fizgota fitsari ne kawai bata saki ba, maida kofan yayi yarufe da karfin tsiya dayay kara sanan yawani kalan saka hannu cikin hijabinta yawani yaye shi daga jikinta ya cillar sanan yabugata da kofan yawani irin manya jikinshi a nata ya matseta sosai cikeda mugunta yanajin duk wani nishi da faduwa da gabanta keyi cikin wani irin murya kaman na zaki da baida karfi sosai yace “why can’t you let me be Ummulkhairy what do you want from a Divisional police officer irina haaaa tell me” rawa jikinta yakeso yayi amman sabida yanda ya matseta tama kasa sai internal organs dinta ne kerawa, ko tarin kirki kasawa tayi danji yake kaman idan tayi zai iya kasheta tamutu tai gum sai hawaye dake zuba afuskanta uncontrollably. “Stop crying!” Yadaka mata tsawan dayasa taji kukan ya tsaya chak yace “mekike nema awajena? Kin kasa bacci kina bina cikin tsakiyan Daren nan kowa na bacci kinamin kuka kin kusa kasheni Allah bai baki iko ba kinzo ki karasa cika burinki ne tell me” girgizamai kai tayi ahankali bakinta narawa still takasa magana ihu yamata datajishi har tsakiyan brain dinta yace “talk Ummulkhair!” Wani irin gagaruman ijiyan zuciya tasauke kafin ahankali ko’ina na cikin jikinta na shaking batare datai kukan dayahanata ba tace “Ya Aliyu nasan I’ve hurt you with my words, nai nadaman hakan, I wish I have power na maida hannun agogo baya na gyara maganganun dana maka ranan danayi, I know babu abinda zan iya gayamaka dazai kankare all da nafadi maka ranan, all I want to say now is Ya Aliyu I am sorry, the truth is I’ve never seen a selfless, generous, kindhearted, sweet and cool man like you in my Life, Ya Aliyu inasonka with all my heart, I loveeee you Ya Aliyu, I love you alot” lumshe idanu yayi sanan yabudesu ahankali yana kallon fuskanta kaman yanda take kallon nashi cikin duhun, hannunta yakai hannunshi yakamo gently sanan yadaura akan kirjinshi daidai saitin heart dinshi, murya chan chan chann kasa kaman mai whispering yace “and I hate you Ummulkhairy” dawani irin sauri ta girgizamai kai some new hawaye na bulbulo mata daga idanu amugun hankali yace “my heart hates you for what you did to her, na tsaneki Ummulkhairy sosai” yay maganan yana sakin hannunta yajuya fuuu zaitafi chak yaji takamo hannunshi dawani irin sauri yajuyo yace “what do you want from me???” Saikuma yadanyi shiru kafin chan yace “ohhh I remember ance ni mijinki ne fa yanzu ko, hakkin ki kikeso ne nabaki, Shap na manta this is 3 month kina bukatan hakkinki ko muje sama nabaki” yawani irin ja hannunta tirjewa tayi tana girgizamai kai tace “no Ya Aliyu” dasauri yace “baki isa ba muje” kawai yadauketa kaman yar yarinyar yay sama da ita, ita bama tasan tayaya yake gani cikin duhun nan ba taji bude kofanshi zuwa wani daki dayamafi falo sanyi kawai taji yajefata kan gado dayasa tai ihu ta diro kasa tana tattaba bango tana kuka ahankali tana kiran Gwaggo. “Gwaggoooo, Ya Aliyu dan Allah kabarni natafi” jitayi an wani irin fizgota bata ankaraba kawai jinta tayi jikin Ya Aliyu babu kaya ajikinshi, fatar jikinshi wani irin laushi ga dumi dataji Ya ratsa fatarta gabaki daya zuwa tsakiyan kwanyarta dayasa tasaki wani irin ihu.



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️







“Wayy………” bata karasa maganan ba taji saukan bakinshi cikin nata tareda sauke ijiyan zuciya dawani irin sauri kaman yadade dama yana jiran hakan, wani irin tafiya yashiga yi da ita still bakinshi na cikin nata sanan yawani irin bugata da bango ya bala’in matseta kafin ahankali yashiga kissing lips dinta yana wani irin lumshe ido brain dinshi nawani irin juyawa, lips dinta are so succulent gawasu irin taushi kaman yana tsosan soft softest ganda, wani irin sanyi gabobin jikinta suka mata kaman an sakasu a ices yanda Ya Aliyu yawani bala’in matseta abango yana kissing dinta yasa taji duk wani kuka datakeyi ya tsaya dakanshi chak, wani strange new abu takeji azuciyanta dan tanajin yanda heart din Aliyu ke beating fast fast all she could feel daga heart dinshi shine how crazy and inluv he’s with her, lips dinshi dabakinshi gabaki daya dadi kaman wani tuwon madara da akai garnishing with a little bit of strawberry jam, bata taba sanin baki nada dadi haka ba saina Aliyu, tura harshen shi dayayi cikin bakinta yasa taji jikinta ya idasa sagewa taiwani yauuuu kaman yakuwa zata zube, ijiyan zuciya yake saukewa sosai yana kissing nata gently yakai two hannayenshi saman kanta hulan dake kan yawani fizge ya yar sanan yasaka hannunshi yana barbaza kalaban dake kanta suna sauka agadon bayanta, yana wani irin kissing nata passionately kaman zai ciremata baki, ko yaji ajikinshi cewa tana gab data fadi ne jitayi kawai yadauketa chak batare daya raba bakinshi da nataba hannayenshi taji duka biyun yakai kan bombom dinta yawani irin matsesu da karfi yayi wani nishi kaman wanda yazare jin yanda hannunshi suka nitse cikin bombom din sabida taushin dasukeda shi kaman dough din donut. “Mmmmm” gaban madubin shi yakaita still yana kissing dinta zafi zafi yacire hannu daya daga kan bombom din yan tarkacen shi nakan madubin yasa hannu yawani irin watsar dasu kasa sanan yadaurata gaban madubin yana daga kasa yana kissing nata sosai kaman wanda zai shide, sakin bakin nata yayi ahankali yana kallonta kaman yanda itama take kallonshi bakinta har wani yaji yaji yake mata lips dinta jitayi kaman sun kumbura tsabagen yanda yashasu, hannunshi yamika batare daya cire idanunshi daga kanta ba yakunna bedside lamp ganin haske dudda bana asalin wutan dakin ba yasa taji wani irin kunya dasauri tajuyar da kanta gefe takai duka hannayenta tarufe fuskan nata dan bazata iya kallonshi ba bayan this uban kiss dinan dayamata gashi kuma bataga kaya ajikinshi ba banda boxer, binta yayi dawasu irin mayun idanu batare dayace mata kala ba, tundaga kan cinyanta dasuke awawware dan yana tsakiyan kafafunta ne he could see lace red pant din datasaka da duk ga alamun jikewanan atare da pants din, wani irin kara tashi tsigan jikinshi yayi kaman yasaka hannu ya tsinka pant din yakeji and have his water dan baiso a single abu should go to waste ajikin yarinyar nan, da kyar ya iya zare idanunshi daga wajen sanan yadaurasu kan boobs dinta dayaga nipples din sun fito sharp bur bur dasu tajikin rigan baccin ta abinka da cotton shirt, wani irin rawa jikinshi yafara baitaba sani Ummulkhairy nada nono hakaba and now dayagani all he could say is Alhamdulilah, yanason mace da nono cus he always dream sune zasu zama comfort zone dinshi bayan aure, koyay fada da matanshi, ko yana cikin kunci ko fushi dazaran yazo he will just suck them and sleep shikenan.



Ahankali hannunshi duka biyun har wani bari suke yakai ta saman rigan nipples din dasukai shooting out looking pointed kawai yakama su da yatsunshi gam kaman yakama kan balanbalan, wani irin zare idanu Ummulkhairy tayi jin hannun Ya Aliyu akan nonon ta kafin tawani irin cire hannunta dagakan fuskanta tajuyo da kanta da sauri hada idanu sukayi tunda take bata taba ganin Ya Aliyu da irin idanunnan ba kaman na yan iska dinan sun kankance sosai ba sai yau, yana kallonta still yawani irin matse kan dayasa tawani irin cije baki sabida zafin dataji cikin wani irin murya dabaya fita sosai yace “does it hurt”? Gyadamai kai tayi batare data sake bari sun hada idanu ba ta gyadamai kai, finger tips dinshi yadaura akan nipples din yafara liliyawa yana kallon fuskanta wani Un authorize ajiyan zuciya tasauke tana kokarin twisting kanta ta kwace boobs nata dan no man or woman has ever touch her breast banda ita idan tazo wanka, yau dataji hannun Ya Aliyu akan nipples dinta wani irin effect yake bata na bala’in dadi dayasa taji tanaso ta harde kafafunta kotaji saukin abinda takeji, kafafunta yabi da kallo yanda takeso ta hardesu sabida yanda yake wasa da nipples dinta kadai har yanzu baima kama boobs din duka ba fa, murmushin mugunta yayi yasan bata tabajin something like this ba saisa bamatasan inda zatasa kanta ba, ahankali yawani irin kare ware kafafun nata yana komawa side din left kafafun sanan gently yakai hannunshi yawani irin jaaa rigan baccin nata kasa big boobs nata all the two sukai flashing right before his eyes. “Wayyoo Allah na!” Aliyu yafadi cikin wani irin murya na mugun sha’awa kasa motsi Ummulkhairy tayi takuma kasa magana sai idanunta data kankame gam gam sabida bala’in kunyan datakeji jikinta yasaki sosai tanajin Ya Aliyu najamata rigan bacci kasa takasa cewa komi, wani irin lashe baki Aliyu yashiga yi yana kallon big boobs dinta dakenan a tsaye warrr kan sun fito wull areola nata yawani irin tattare yana nuna how horny she is, ahankali yadaura kanshi kan shoulder nata gently yakai bakinshi in a very slow mo, wani irin sanyi da dumi Ummulkhairy taji saman nonon ta sai chan kuma taji wani irin zafi da dadi at the same time sabida yanda yawani fizgi nipples dinta kaman mahaukaci yashiga sha dayasa batasan lokacin daya kira sunanshi ba. “Y……a Ali…..” 


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



6️⃣6️⃣




“Wayy………” bata karasa maganan ba taji saukan bakinshi cikin nata tareda sauke ijiyan zuciya dawani irin sauri kaman yadade dama yana jiran hakan, wani irin tafiya yashiga yi da ita still bakinshi na cikin nata sanan yawani irin bugata da bango ya bala’in matseta kafin ahankali yashiga kissing lips dinta yana wani irin lumshe ido brain dinshi nawani irin juyawa, lips dinta are so succulent gawasu irin taushi kaman yana tsosan soft softest ganda, wani irin sanyi gabobin jikinta suka mata kaman an sakasu a ices yanda Ya Aliyu yawani bala’in matseta abango yana kissing dinta yasa taji duk wani kuka datakeyi ya tsaya dakanshi chak, wani strange new abu takeji azuciyanta dan tanajin yanda heart din Aliyu ke beating fast fast all she could feel daga heart dinshi shine how crazy and inluv he’s with her, lips dinshi dabakinshi gabaki daya dadi kaman wani tuwon madara da akai garnishing with a little bit of strawberry jam, bata taba sanin baki nada dadi haka ba saina Aliyu, tura harshen shi dayayi cikin bakinta yasa taji jikinta ya idasa sagewa taiwani yauuuu kaman yakuwa zata zube, ijiyan zuciya yake saukewa sosai yana kissing nata gently yakai two hannayenshi saman kanta hulan dake kan yawani fizge ya yar sanan yasaka hannunshi yana barbaza kalaban dake kanta suna sauka agadon bayanta, yana wani irin kissing nata passionately kaman zai ciremata baki, ko yaji ajikinshi cewa tana gab data fadi ne jitayi kawai yadauketa chak batare daya raba bakinshi da nataba hannayenshi taji duka biyun yakai kan bombom dinta yawani irin matsesu da karfi yayi wani nishi kaman wanda yazare jin yanda hannunshi suka nitse cikin bombom din sabida taushin dasukeda shi kaman dough din donut. “Mmmmm” gaban madubin shi yakaita still yana kissing dinta zafi zafi yacire hannu daya daga kan bombom din yan tarkacen shi nakan madubin yasa hannu yawani irin watsar dasu kasa sanan yadaurata gaban madubin yana daga kasa yana kissing nata sosai kaman wanda zai shide, sakin bakin nata yayi ahankali yana kallonta kaman yanda itama take kallonshi bakinta har wani yaji yaji yake mata lips dinta jitayi kaman sun kumbura tsabagen yanda yashasu, hannunshi yamika batare daya cire idanunshi daga kanta ba yakunna bedside lamp ganin haske dudda bana asalin wutan dakin ba yasa taji wani irin kunya dasauri tajuyar da kanta gefe takai duka hannayenta tarufe fuskan nata dan bazata iya kallonshi ba bayan this uban kiss dinan dayamata gashi kuma bataga kaya ajikinshi ba banda boxer, binta yayi dawasu irin mayun idanu batare dayace mata kala ba, tundaga kan cinyanta dasuke awawware dan yana tsakiyan kafafunta ne he could see lace red pant din datasaka da duk ga alamun jikewanan atare da pants din, wani irin kara tashi tsigan jikinshi yayi kaman yasaka hannu ya tsinka pant din yakeji and have his water dan baiso a single abu should go to waste ajikin yarinyar nan, da kyar ya iya zare idanunshi daga wajen sanan yadaurasu kan boobs dinta dayaga nipples din sun fito sharp bur bur dasu tajikin rigan baccin ta abinka da cotton shirt, wani irin rawa jikinshi yafara baitaba sani Ummulkhairy nada nono hakaba and now dayagani all he could say is Alhamdulilah, yanason mace da nono cus he always dream sune zasu zama comfort zone dinshi bayan aure, koyay fada da matanshi, ko yana cikin kunci ko fushi dazaran yazo he will just suck them and sleep shikenan.



Ahankali hannunshi duka biyun har wani bari suke yakai ta saman rigan nipples din dasukai shooting out looking pointed kawai yakama su da yatsunshi gam kaman yakama kan balanbalan, wani irin zare idanu Ummulkhairy tayi jin hannun Ya Aliyu akan nonon ta kafin tawani irin cire hannunta dagakan fuskanta tajuyo da kanta da sauri hada idanu sukayi tunda take bata taba ganin Ya Aliyu da irin idanunnan ba kaman na yan iska dinan sun kankance sosai ba sai yau, yana kallonta still yawani irin matse kan dayasa tawani irin cije baki sabida zafin dataji cikin wani irin murya dabaya fita sosai yace “does it hurt”? Gyadamai kai tayi batare data sake bari sun hada idanu ba ta gyadamai kai, finger tips dinshi yadaura akan nipples din yafara liliyawa yana kallon fuskanta wani Un authorize ajiyan zuciya tasauke tana kokarin twisting kanta ta kwace boobs nata dan no man or woman has ever touch her breast banda ita idan tazo wanka, yau dataji hannun Ya Aliyu akan nipples dinta wani irin effect yake bata na bala’in dadi dayasa taji tanaso ta harde kafafunta kotaji saukin abinda takeji, kafafunta yabi da kallo yanda takeso ta hardesu sabida yanda yake wasa da nipples dinta kadai har yanzu baima kama boobs din duka ba fa, murmushin mugunta yayi yasan bata tabajin something like this ba saisa bamatasan inda zatasa kanta ba, ahankali yawani irin kare ware kafafun nata yana komawa side din left kafafun sanan gently yakai hannunshi yawani irin jaaa rigan baccin nata kasa big boobs nata all the two sukai flashing right before his eyes. “Wayyoo Allah na!” Aliyu yafadi cikin wani irin murya na mugun sha’awa kasa motsi Ummulkhairy tayi takuma kasa magana sai idanunta data kankame gam gam sabida bala’in kunyan datakeji jikinta yasaki sosai tanajin Ya Aliyu najamata rigan bacci kasa takasa cewa komi, wani irin lashe baki Aliyu yashiga yi yana kallon big boobs dinta dakenan a tsaye warrr kan sun fito wull areola nata yawani irin tattare yana nuna how horny she is, ahankali yadaura kanshi kan shoulder nata gently yakai bakinshi in a very slow mo, wani irin sanyi da dumi Ummulkhairy taji saman nonon ta sai chan kuma taji wani irin zafi da dadi at the same time sabida yanda yawani fizgi nipples dinta kaman mahaukaci yashiga sha dayasa batasan lokacin daya kira sunanshi ba. “Y……a Ali…..” kasa karasawa tayi jin hannunshi daya saman kan pant nata daya bala’in jike yana wani irin shafa vijay nata ta saman pant din up and down yana yagwalgwala wajen batare daya saka hannunshi ta karkashin pant din dan yataba skin to skin ba, dayan hannunshi kuma nakan dayan boobs nata yana murzashi son ranshi.





Komi na brain din Khairy daina aiki yayi, tama rasa inda zata saka kanta sai kara bude kafafunta take giving Ya Aliyu more access yana jagwalgwala mata Vijay ta saman pant tana gushing out water kaman an bude pampo, kaman tai ihu takeji tana kara turamai kirjinta da kyau wanda haka daman yakeso yanasha kaman zai ciremata su, he’s just happy cewa Ummulkhairy ba Yar iska bace dan inda ace she’s one da tuni angama da ita dan yalura tanada karfin sha’awa which is another prayer dayasha yima Allah yabashi, dan tuna yana SS1 Allah ya jarabeshi da mugun sha’awa abun kadan hankalinshi yatashi yadage da azumi dan baiso ya lalace, he will not lie dan Iskanci baitaba Iskanci arayuwanshi ba but babu wani iskanci movies dabai kalla ba da kyar yazo ma yadena, yanzu da yay aure sunan matanshi sorry all abunda yakalla saiyay mata su.



Nishi Ummulkhairy tafara kaman zata mutu tawani irin kankame kanshi jikinta narawa sosai tace “Ya….Al…..” tama kasa magana, ganin kaman kawowa takeso tayi this little thing dayamata that means bamata da kwari yasa yawani irin fizge jikinshi daga nata batare daya bari takawo ba dan yay alkawari he will punish her and makes her yearn for him harkuka saiyasa tamai, juyarda kanta tayi da sauri har lokacin jikinta nawani irin rawa hakanan tanaji kaman takamoshi yacigaba sabida yanda takeji sanan Awani irin kunyace taja riganta tamaida boobs dinta ciki tana nishi kasa kasa yana kallonta gently yace “fita daga dakin nan” dan juyoda idanunta dasukai ja suka kankance sosai tayi tadan kalleshi sanan dasauri tamaida kanta gefe. “I said out kosainayi throwing naki out, nabaki hakkin ki dakika zo nema ko now out” wani iri taji zuciyanta yamata da kyar ta iya saukowa daga gaban madubin kunya kaman zata nitse akasa riganta duk yajike harta gaban kaman tai fitsari ajiki tama kasa magana sai wasada yatsunta data shigayi, danne zuciyanshi yayi dan ji yake kaman yakamota yadanneta adakin nan fuck her blue black har safiya bazai barta tai bacci ba amman no he will suppress kanshi just to make her extremely regret abinda tamai.


“Out Ummulkhairy bana baki abinda yakawoki ba kobai isheki bane” hawayen dayazubo nata ta share dawani irin sauri sanan ta tsugunna tadauki dan kwalinta dasauri tai hanyar kofa hartasa hannu zata bude tafita yace “one last thing” tsayawa tayi chak sanan yataho harzuwa inda take ya tsaya bayanta sanan ahankali yace “I might be a local divisional police officer, wanda baida gata, kyau aji da all those you’ve mentioned, But!” Yay dan shiru dan anything yatuna maganan zuciyanshi namai zafi ahankali yace “But! I am the only man that can make you this wet kaman kinyi fitsari ajiki! I am the only man dazai iya juyarda kanki ya juyarda tunanin ki, I am the only man that can make you cry and beg me nakara miki kinsan maisa cus Aliyu Hydar is sweet in every aspect of life!” Hawaye taji yagangaro mata daga idanunta, shima idanunshi ja sukayi sosai sanan ahankali yace “and I forgot to tell u something Ummulkhairy u are a liar! Dan bakitaba son wani and bazaki taba son wani aduniyan nan sama da Aliyu ba!” Dawani irin gudu tafice daga dakin tai kasa tana kuka ahankali tana share idanunta tana bude kofan falo tafice zuwa flat din Gwaggo saida yaga tamaida kofan Gwaggo tarufe sanan yabar window falon yawuce fridge yadauko kankara zama yayi yana daura kankara akan joystick dinZshi kozai samu tasaki ta kwanta…..



6️⃣7️⃣





Fadawa kan gadonta tayi tana kuka tadade ahaka sanan tashare fuskanta tass, bazata gaji da fadin tai nadaman maganganun data fadima Ya Aliyu ba wanan comparison din datayi tsakanin shi da Ya Zayn shiyafi cin mata zuciya ko ita takasa mantawa balle shi Aliyun datamawa Tayaya zata goge Wanan tabon aranshi? Ita kanta batasan iyakan Son datakema Ya Aliyu ba, tanason Ya Aliyu sama da tunaninta, tanason Ya Aliyu sama da komi na rayuwanta cus bata taba ganin mutum mai kirki ba dashima ya iya sonta ba irinshi saisa maganan dayafadi dazu yataba ranta na cewa he’s sweet, bata taba ganin a Sweet generous, calm and cool guy irin Ya Aliyu ba, saina ka zauna dashi zaka gane how cool and sweet he is halinshi daban ne, yasanta sama da kowa aduniyan nan tai kuka yasani, kome ke damunta yasani, tasan har yanzu Ya Aliyu na sonta kawai yakasa manta abubuwan datafadi nai ne yakasa bacci saida ya tabbatar taci abinci still yadawo dan yadubata yaga kotai bacci.



Ahankali takai hannunta ta share hawayen kan fuskanta tass, murya chan kasa tace “inhar akwai an atom of sona aranka Ya Aliyu I will make you crazy about me kaman yanda kake da, I will en leash that demon of love and jealousy dake cikinka, Ya Aliyu inhar nine Ummulkhairy dakake mutuwan so da har ciwon zuciya yakama ka kanni I will bring you back to the mud potopoto, this is now a game between me and you let’s see idan bazan iya mantar dakai ba, I love you and I will fight and win you back, Mama naso nazama yarinya that can address life ayanda yazo mata and zan nunama Mama Ummulkhairy is now a grown married woman that can manage her life dakanta” tai maganan ahankali tana taba boobs nata dake mata zafi sosai maranta shima yanadan juyamata dayasa tajuya takife cikinta agado tana lumshe idanu but komi da Ya Aliyu yamata nadawo mata akai kaman yazo yakarayi, juye juye tashiga yi akan gado dan bakinshi takeji akan boobs nata, hannunshi takeji akan vijay dinta kaman zata haukace ita kanta tama kasa tantance meke damunta Zabura tayi ta tashi tashiga bayi kayan jikinta tacire tai wanka sanan tafito tadanji dama dama chanza kaya tayi sanan tazo ta kwanta.



Har asubahi takasa bacci tai wanka kusan so uku tana chanza pant dan dazaran ta tuna abinda yamata saitaji tajike kuma ta tsani taji tajike, wanka tasakeyi tazo tai sallan asuba sanan takoma gado sabida wani mugun bacci dataji a idanunta tana kwanciya yay awon gaba da ita.




Wuraren 12 Gwaggo tashigo dakin nata, wuta ta kunna sanan tazo gaban gadon ta bubbuga kafafuwanta. “Khairiya baccin lafiya kike haka tun dazu nakeso nazo natadaki amman Aliyu yahanani yanzu danaga bazan iyaba gwara nazo natadaki nagani ko lafiya, tashi tashi kiyi wanka ki shirya zakuje gidanku yanata jiranki” tashi tayi ta zauna ahankali tana gyadama Gwaggo kai, sanan ahankali tace “ina kwana Gwaggo” Gyadamata kai Gwaggo tayi tace “lpy lau Khairiya tashi to kije kiyi wanka tun bakwai Aliyu ke falo yana jiranki” gyadama Gwaggo kai tayi sanan tawuce bayi ahankali, tadade abayin wanka tayo sanan tafito daure da towel shiryawa taci cikin wani haddaden lace mai ruwan toka dayawani amshi jikinta dogon riga aka mata amman fitted dayabi jikinta dam yafito mata da hips dinta dakuma boobs nata sosai, ji kawai tayi tanaso yau tai kwalliya sabida Ya Aliyu, dan murmushi tayi tazauna tasaka kwalli ta gyara giranta da brush, tadauki wani red janbaki tasaka dayawani haska fuskanta tai kyau na wuce misali, ijiye dan kwalin lace din tayi akan gado tadauki ribbon only da gyalen dazata saka shima kai ruwan toka sanan ta feffesa hadaddun turarukanta tasaka silipas tafito gashinta na lilo abayanta tai wani irin kyau, tana daga labulen corridor suna hada ido da Ya Aliyu dake zaune akan kujeran dake facing corridor waya nakan kunnenshi yana magana, ganinta yasa yakasa cigaba da maganan sai kallonta dayakeyi, daukekai tayi daga kallonshi tafito ahankali Gwaggo na murmushi tace “Iyye ni bakimin kwalli yan nan Ummulkhairy sabida zaki gidanku ne shine kikaci gayu haka kinga yanda kikai kyau kuwa kaman Yar misira” dan murmushi tayi daya lobarda dimples dinta duka biyu sanan tazo ta daidai kujeran da Aliyu ke zaune yana wayan dabaya magana yana kallonta still Awani irin hankali tadaura gyalenta da ribbon dinshi akan cinyanshi tana shafa cinyanshi da hannunta kaman batasan ta tabashi ba innocently tace “Ya Aliyu rikemin plsssss” tai maganan amugun shagwabe sakin wayan dake kunnenshi yayi yafadi dasauri tajuya kaman bataga lokacin da wayan yafadi ba tana wani irin tafiya da ita kanta batasan yanayinsh ba sabida tasan kallonta yake taja kujera a dinning din tazauna ahankali, dawani irin sauri yadauki wayan yamaida a kunenshi yanadan gyara murya sabida yanda tsigan jikinshi yatashi yace “yes yes ina jinka” murmushi Khairy tayi kasa kasa tadebi Irish kadan tafara ci, bata wani jimaba tagamashi tadauki plate din takai kitchen sanan tadawo falon ganin Gwaggo bataciki sai Aliyu dake daddanna wayanshi har lokacin gyalenta da ribbon dinta nakan jikinshi yasa tazo gabanshi dasauri tsugunnawa tayi tadaura kanta kan kafafunshi tace “Ya Aliyu kamamin kitson nan da ribbon plssssss” wani irin ijiyan zuciya taji yasauke baima iya cewa komiba ganin tana neman tadamai da hankali yadauki ribbon din yakama mata gashin sanan tawani irin juyoda ita tana kallon fuskanshi yanda yake kallonta yasa tadauke kai dasauri Dan yana tunamata da jiya, jin Gwaggo zata fito yasa ta kwace kanta dasauri tana daukan gyalenta Gwaggo tace “yauwa harkin gama to tashi Aliyu kuje” tashi yayi yadan kalleta sanan yadauke kai yace “jekisa Hijab ko babban mayafi” yana maganan yabude kofa yafice baki Gwaggo tasaki tace “yo wai wanan wani irin fitinannen jikane Allah yabani ina laifin gyalen nan yarinya tai kyau haka, je dauko babban mayafi Khairiya zanyi maganin shi, saifa kin dage da addu’a dan Allah yabaki fitinannen miji mai shegen bakin hali” wucewa Khairy tayi ciki babban mayafi tadauko ranta abace sanan tayafa tama Gwaggo sallama tafice, Mami tagani a tsakar gida da yaran suna zazzaune ana musu gyaran kunba, ahankali takarasa wajen tace “Mami good morning” kallonta Mami tayi sanan tazubar tace “morning” Amal da Khadija suka gaidata amsawa tayi itakuma Hajo ko kallonta batayiba itama haka tai wucewanta dan Meena bata wajen, Aliyu na zaune a mota yana kallon komi ta glass, ahankali takarasa tabude gaban motan tashiga tana tuna yanda yake budemata gaban mota zama tayi sanan tajawo kofa tarufe zata zauna da kyau kawai taji tajawota saida tafirgita habanta yarike yana wani irin mayen kallon lips dinta yace “where do you think u are going with this abakinki”? Kafinma tai magana yadaura bakinshi kan nata yashiga kissing nata kaman dama abinda yake jira yayi kenan yana kallon kwayan idanunta kasa jure kallonshi tayi dasauri ta runtse idanunta, Wanan iskanci ne kawai Dan kusan 15min good one yadauka yana kissing nata sanan yasaki bakin nata ahankali ya shanye janbakin tass sai uban pink da lips dinta yayi idanunshi sunyi jajir yasaketa ahankali takoma kan kujera tazauna tana maida ijiyan zuciya sanan yatada motan sukabar gidan, Mami kaman haushi zZai kasheta……..



6️⃣8️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Tunda akai bikinta sai yau zataje gidansu she’s so excited but ga mamakinta saitagan su agaban wani babban police headquarter sai gaida Aliyu ake yaja mota suka shiga ciki, awani special place yay parking sanan yakashe motan ya sauko yazagayo ta inda take yabude kofan yana kallonta kaman yanda take kallonshi adan tsorace tace “Ya Aliyu uhnnn ba, ba gida zamu ba” wani mugun kallo yamata yace “bazaki ba” sanan yace “come down” ahankali ta sauko batare daya matsa bayaba tana gab dashi yabita da kallo hannunshi yakai ya kara gyaramata babban gyalen data yafa sanan yawani jata jikinshi yamaida kofan yarufe sanan ya danna lock a key hannunshi sanan yakama hannunta batare dayace mata komiba sukai ciki, suna shiga tafi taga an fara all yan sandan wajen saiga cake babba an kawo da aka rubutu happy married life, hannunta yakama atare suka yanka cake din yanadan murmushi sanan yadauko yajuyo yakalleta yabata akahau tafi, mataye police na wajen sukace kema kibashi ahankali takai hannunta tadauki cake din sanan tajuyo takalleshi kaman yanda yake kallonta takai bakinshi, akahau tafi Ogansu wanda shi Aliyu kebi a matsayi yamai kyauta na 1M sai ihu ake itadai murmushi take ahankali tanadan bobboye fuskanta sunkai kusan 30min ana dan shagalin kafin agama yana rikeda hannunta sukai sama, wani hadadden office yabude mata ganin hotonshi babba da uniform yasa tagane office dinshi ne yahadu office din, shiga tayi shima yashigo sanan yamaida kofan yarufe wucewa tayi ahankali zuwa dogon couch din dake cikin office din shikuma yawuce yazauna kan kujeran gaban desk dinshi yana bude wasu files yana dubawa, dan juyowa tayi tadan saci kallonshi wani irin bala’in kyau yamata, wanan gashin daya tara mai yawa, da yanda sajenshi yakara cika yay yawa yasa yawani irin kyau ga fatanshi sai kara haske yake da ace all yaranta zasuyi kama da Ya Aliyu data more, murmushi tayi tasauke idanunta kan bakinshi yanda lips dinshi shima yakara zama pink tsabida tsabagen uban kiss din dayamata jiya, tuna yanda bakinshi yadinga shamata nono jiya yasa taji kaman ma tajike, kaman daga sama yace “how many time kika chanza pant jiya before you finally get to sleep”? Wani irin zaro idanu tayi takalleshi jin maganan dayamata still yana abinda yakeyi bai kalleta ba Awani irin kunyace tadauke kanta dasauri tashiga wasa da yatsunta, murya chan kasa yana yan rubuce rubuce yace “you know if you want again I can help you” Dawani irin sauri tajuyo takalleshi daidai shima yadago kanshi yakalleta suka hada idanu, dawani irin sauri tadauke kanta dan bazata iya juran ganin idanun yan iskan nan nashi ba, jitayi yaja kujeran dayakekai baya yatashi yana tahowa inda take every step daya dauka tanajinshi har heart dinta tasa hannunta takara kankame jikin riganta dashi.




Ahankali yawani irin zauna kusada ita kamshin turaren dayake nawani irin shiga hancinta yabi gefen fuskanta da kallo yana kallon lips dinta dake rawa sosai, ahankali yakai hannunshi cikin gyalenta sanan gently yadaura kanshi kan shoulder dinta murya chan kasa yace “tell me to stop idan bakiso” yay maganan yana wani huramata iskan bakinshi a fuska dayasa tashiga lumlumshe idanunta da kyau sanan gently yadaura hannunshi saman riganta daidai saitin boobs dinta yakama nonon yawani kalan matse dayasa ta lumshe idanu dasauri tsigan jikinta natashi tama kasa murya dayan hannunshi yakai yana warware gyalenta kaman mai whispering yace “you like it”? Kasa magana tayi ita batasan mesa bama muryanshi kashemata ma jiki yakeyi, zare gyalen jikinta gabaki daya yayi ya ijiye akan kujeran yana kallon clean bayanta ga gashi kwance ta kasan wuyanta sun kwanta lub lub wasu sun kanannade he can’t believe Khairy halas dinshice yanzu, gently yakai hancinshi saitin bayan nata kafin ahankali yamanna mata wani irin peck akeya mai kara. “Muahh!” Jitayi tsigan jikinta yatashi gabaki dasaida yasa tai wani irin stretching wuyanta yakai hannunshi kan zip din bayan riganta yaja zip din gently yana sakinma bayan kiss har zuwa waist dinta yama kiss, kankame riganta tayi da karfi sabida yanda takeji kaman zatai fitsari sanan yadago da kanshi yakalleta yanda ta kulle idanunta gam ta rirrike riganta da hannu ta wajajen cinya dan murmushi yayi kaman zai cinyeta sanan ahankali yakai hannayenshi yakama nata dake kan cinyarshi yadaga dawani irin sauri tabude idanunta, hada idanu sukayi dayasa takara kulle idanunta dasauri, sake sakin murmushi yayi sanan ahankali ya kwantar da kanshi kan saman cinyoyinta kaman wani dan yaro dayasa tasake bude idanunta dasauri takalle, hannayenta dayarike yasaki sanan yakai hannunshi gaban wuyan riganta dawani irin sauri ta lumshe idanu tana girgizamai kai kunya kaman zata nitse awajen, jan rigan nata yayi kasa hakan ya bayyana cute pumpy boobs dinta dake cikin wani white formless lace bra, rawa jikinshi yafara yana kallonsu dayaga nipples dinta harsun shooting out, dawani irin sauri yakai hannunshi yasaka cikin bra din yanajin yanda jikinta yahau bari sanan yaciro boob din nata guda daya kaman yana rige rige dawani Dawani mahaukacin ya fizgi nonon cikin bakinshi yanasha dasauri dasauri kaman wani jariri datun safe baiga uwarshiba…..

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




6️⃣9️⃣




Ummulkhairy jitayi kaman jijiyoyin jikinta na neman tsinkewa sabida yanda Aliyu keyi, jin yana neman ciremata nono yasa dawani irin sauri takai hannunta zata karbe batare data kalleshi ba chak taji yakama hannun nata yakara rirriketa yanayin abinda yakeyi, knocking office dinshi da akayi yasa tashiga turashi amman ko gezau baiyiba ganin yana neman tonamata asiri yasa tace “Ya Aliyu dan Allah stop please kaga ana knocking” bude idanunshi yayi ahankali yakalleta ganin yanda taki kallonshi harta fara zufa agoshi yasa ahankali yasaki nonon yana kallon shi yanda haryay ja kadan kan, hannunshi yakai yataba nipple din murya chan kasa yace “sorry Buddy” sanan awani irin hankali yadago kanshi da sauri tamaida boobs din bra tana kokarin jan zip din riganta taji hannunshi awajen hakan yasa tacire hannunta ahankali zip din yajamata sanan yadauki gyalenta ya yafa mata yana feeling wani irin new energy yasauka dagakan kujeran yanadan gyara kanshi eyya kofa ahankali yasa hannu yabude kofan, wani yaronshi ne yakawomai some files da ake bukatan signature nashi karba yayi sanan yaron yawuce yatafi yamaida kofan yarufe yakoma kan kujera yazauna yacigaba da aiki dan ji yayi yanajin wani sabon energy.



Suna zaune akai knocking dan dagokai yayi yakalli kofan sanan yadan ture kujera baya yatashi zuwa kofan yabude wata Yar budurwa ce da police uniform amman ita tasaka karamin breziya hijab tadaura hulan yan sanda asaman hijab din wani kalan murmushi tamai tace “Yaya Hydar yanzun nan nashigo akace you are married all this while I thought u were on sick leave wlh ashe aure kayi” dan murmushi kadan Aliyu yayi yakoma kan kujeranshi yace “come on in Safiya” shigowa tayi tazo inda Khairy take zaune data dagakai tana kallonta batare datace mata komi, murmushi sosai matan tayi batare data dena kallon Khairy ba tace “Masha Allah, you have a very beautiful wife, no wonder aka kimu ace wanan queen din gareka, ya sunanki Amarya” wani kallo Khairy tamata dan all abinda tagani a idanun matan is bala’in son Aliyu, jitayi kishi yacikata ahankali tace “you can call me Mrs Aliyu” Aliyu dake rubuce rubuce yanajin su wata Yar murmushi ne ya kubucemai, dan murmushin yake matan tayi sanan tawuce zuwa inda Aliyu yake tana kallonshi tace “Oga Aliyu kaga yanda ka kara kyau kuwa duk amarcin ne Masha Allah, Allah baku zaman lafiya” ahankali Aliyu yadago kanshi bayan ya ijiye pen din dayake rubutun dashi yakalleta sanan yace “thanks Safiya, you can go back to work now” gyadamai kai tayi ahankali sanan tawuce tafice daga office din Khairy tabita da harara Aliyu na kallonta ta kasan ido, knocking aka karayi dayasa tasake ware idanu Aliyu yace “come in” wani dan sanda ne da ledoji na takeaway na abinci daga KFC Khairy Aliyu yanunamai hakan yasa yawuce wajenta yakai mata cikeda girmamawa yawuce yafita, tashi aliyu yayi yana kallon agogon hannunshi yace “bari naje mosque” dan kallonshi kadan Khairy tayi dan kunyan hada idanu dashi take sanan tadauke kai ahankali kaman bataso tai maganan tace “yaushe zamu wuce gidan” dan kallonta yayi yay jim sanan yace “bazaki ba” dawani irin sauri takalleshi mugun kallo yamata sanan yace “make sure you remove your pant kisashi ajaka daga yanzu always carry spare one tunda ocean flow gareki, pray before I come back” yay maganan yana bude kofa yafice abinci yamaida kofan yarufe tana jinshi yana kulleta a office din ta tabe baki, tashi tayi wani kofa datagani acikin office din tabude tashiga karamin dakine mai kyau ga gado da alamu kullum ake gyarawa wani kofa datagani acikinshi tawuce tabude ganin bathroom best yasa tashiga yanda yace tayi haka tayi pant din tacire wankeshi ma tayi ta rataya akan wani hanger datagani abayin zai iya bushewa kafin su tafi sanan tadauro alwala tafito dadduma tadauka tadauki wayanta tabude compass tagane gabas sanan tai salla tana idarwa tafito abinci ta tadauka takoma ciki zama tayi taci kasan sosai dan tanaso sanan ta ture komi bayan tasha ruwa tai dialing number Batool ganin bata daukaba yasa tasan suna cikin hayaniya tana zaune kan gadon shiru ganin baizoba yasa ahankali ta kwanta ko 2min bMatayiba bacci yay awon gaba da ita.



7️⃣0️⃣




Sai bayan yay la’asar ma yadawo office din maida kofan yayi yarufe yana kallon ledan abincin dayake wajen sanan ahankali yawuce yabude kofan dakin ahankali ganinta yayi kwance kan gado tana bacci peacefully looking so sexy, fuskanta ya tsare da idanunshi kafin ahankali yace “why do I love you this much Ummulkhair?” Dan lumshe idanu yayi yabude yasake daurasu akanta yana kallonta soyake yay fushi da ita he try his best yayi but yakasa Allah ma yasan yakasa, he can’t stand seeing her sad, seeing her moody kotana kuka, he’s greatful to Allah daya auramai ita dan inda ace bai sameta ya aura ba Allah kadai yasan mezai sameshi, he can’t live without Ummulkhairy, bazai iyaba, every beat na zuciyanshi natunamai da itane, anya zai iya jiran Wanan sati ukun da Baba yadauka na bikinsu akaita gidanshi kuwa?? Allah ma yasan bazai iyaba, yana bukatan matarshi yana son ya sadu da ita yatabbatar ma da kanshi yariga ya zamad da Ummulkhairy nashi, a bala’in bukace yake da he don’t think zai iya hakura, he loves this girl kaman a fool, ajiyan zuciya yasauke ahankali sanan yashigo dakin yamaida kofa yarufe, hannunshi yasa yakashe wutan dakin ko kadan baiso yakaita gidansu shi kanshi kishin shi tsoro yake bashi baimaso suma hadu dawani Zayn ballema yaga matarshi suna nan office har magrib yariga yafadama boy dinshi duk wanda yazo nemanshi yacemai bayanan.


Rigan jikinshi da wandon yacire yarataya abango yarage dagashi sai boxer, ahankali ya kwanta kan gadon yana kallonta yanda take shakan baccinta hankali kwance yariga yasan tanada nauyin bacci, hannunshi yakai bayanta yaja zip din riganta zuwa kasa sanan awani irin hankali kaman yar jaririya yashiga ciremata rigan, tass yacire mata rigan batare datai motsi ba yatashi yarataya rigan inda nashi yake sanan yadawo yana binta da kallo barinma soft big bombom dinta da hips dinta dababu komi akansu, sanan yadawo da idanunshi ta gaban jiyayi he’s going Gaga dawani irin sauri yakai hannunshi yakama joystick dinshi dakemai ciwo sosai yaciroshi daga cikin boxer, awani irin hankali yashiga kwantowa ajikinta hannunshi na tabayanta yana unhooking bra dinta sanan yakama hannunta daya yazare hannun kafin yakama dayan yazare hannunta sanan ahankali yacire bra yawullar yawani kwanta samanta gently, hannunshi nakan left boob nata yawani danna erected joystick nashi amaranta sosai yana nishi sama sama yakai bakinshi saitin nata ahankali yace “Pickle” cikin bacci tace “uhmmmmm” gently yadaura bakinshi kan nata ita jitayi tana mafarki dasauri tashiga kissing nashi son ranta hakan yasa yawani zare yashiga kissing nata yana sauke tagwayen ijiyan zuciya akan fuskanta yakama hannunwanta yakai saman bombom dinshi matsewa Ummulkhairy tayi tana moaning in sleep yana gurje mata boobs son ranshi tasakin mai jikinta da kyau kaman zasu cirewa juna baki da kiss jikinshi nawani irin bala’in rawa yana bubbude mata kaffafu da kyau yanaji idan bai sadu da itaba kaman zai mutu, sanan yakai joystick dinshi wajen yanda yakeji kaman zai shide ahakan yadage yabuga joystick dinshi kan baby hole dinta waras Ummulkhairy taware idanunta, idanunta ne suka sauka kan Aliyu dake samanta yawani irin kankameta sosai idanunshi arufe yana wani irin mahaukacin kissing nata tana shafamai abinda tasan bombom ne yana wani irin nishi akanta kaman zai sume yana squeezing both boobs nata da hannuwanshi kaman zai tsinkamata su, dudda akwai duhu adakin rass take ganinshi takuma gane ba mafarki takeba tun dazu datake ganinshi cikin mafarki, bata ankara ba taji yawani irin kara bugamata joystick a hole dataji kaman kusa aka bugamata dawani irin mugun gudu tafizge bakinta jin azaba tana kokarin tashi tana sheshekan kuka murya chan kasan makoshi tace “Ya Aliyu what are you doing to me” wani irin kankameta yayi batare daya bari ta kufcemai ba jikinshi har bari yake yace “sex Pickle” wani irin faduwa gabanta yayi take ta tuna kukan da Besty tadinga mata, dawani irin sauri tashiga tureshi tafashe da kuka tace “Ya Aliyu dan girman Allah karkamin dazafi sosai wlh, Ya Aliyu please” girgizamata kai yayi yana rike gam da ita yama kasa magana sai tsuke baki dayake yakara kaimata 3hit dayasa ta kwala ihu dawani irin sauri yakai hannunshi yadaura akan bakinta gabaki daya yazare yace “Pickle please kibarni nayi I am your husband is my right dan Allah stop crying for me kinsan kukan ki nada muna” ture hannunshi tayi daga bakinta tana bala’in kuka tarirrike shi tace “Ya Aliyu dagaske ka tsaneni ne” girgixamata kai yayi dasauri yace “No pickle nan tsanake ba, I never did, I love you morethan my life” cikin kuka tace “inhar you love me morethan my life please Ya Aliyu karkayi sex dani dazafi I can’t take it, please Ya Aliyu” kankameta yayi sosai da muryanshi dabata fita sosai yace “to zakisa nakawo”? Dawani sauri ta gyadamai kai dudda bamata gane what exactly yake nufiba but all she knows is inhar bazai mata sex ba she’s willing tayimai kome yakeso, ahankali taji yasaketa, yakoma gefe ya kwanta yana dagota yace “come here” dasauri tazo tana kallonshi, murya chan kasa yana wani irin nishi yace “suck me make me cum ko I sex you” yay maganan yanakai fuskanta wajen joystick dinshi, wani dum kirjinta yayi sai yanzu tagane meyake cewa, kallon gabanshi gaban kato yasa taji kaman tai wani taboo dasauri tarufe idanunta bata taba ganin gaban babban mutum ba, na Aliyu dogo kaman wani maciji ga kauri kaman ice sai wani mimmikewa abin yake kaman mutum, murya chan kasa Aliyu yace “suck me Pickle plssss” jikinta harwani rawa yake takai kanta samanshi duk cikin tsoro dayay sex gwara tamai wanan dan bude idanunta kadan tayi tasake kallon abin, wani kalan mikewa taga abin nayi kaman ita yake nema awani irin hankali tabude bakinta dawani kalan sauri Aliyu yatura kanta yashige bakinta couldn’t take everything, wani kalan ihu Aliyu yayi. “Aahhhhhh, uhmmmm, urggghhhh” bamatasan what she’s doing ba kawai bakinta ne akai Aliyu na bubbuga mata shi a throat, the thing feels hella wired, but jin yanda Aliyu ke sumbatu yana gurnani yasa taji tsigan jikinta nawani irin tashi ta matse kafafunta.




Koya lurada hakan ne jitayi yadagota yadaurata akan jikinshi yasaka hannunshi yawani jawo waist dinta yazaunar da ita akan fuskanshi batare daya mata komiba ahankali yace “continue sucking me” maida bakinta tayi kan joystick din shikuma ahankali yaciro tongue dinshi yashiga lasheta wani kalan zabura tayi zata kwace kanta jin bakin Ya Aliyu agabanta amman yarike ta gam yazaunarda ita da kyau ne ta yanda babu yanda zatayi ta kwace kanta, yanda yashiga ya mutsa gabanta da harshe da hanci da dan gemunshi yasa taji kaman zata mutu rasa yanda zatai da kanta yasa takife kanta kan joystick dinshi tashiga sha kaman that’s her only support Aliyu na wargazata yana tsotso ruwa shima yana feso precum, wani kalan rawa da jikinta yafara yasa yasan she’s about to cum wani kalan iska yahurata kaman ice shaaaa tasaki yamaida bakinshi jikinta nayi kaman zata mutu sai chan yaji tasaki gabadaya, murmushi yayi yawani dagota ya kwanto da ita gefenshi bakinta yay kissing yana kallon yanda ta kulle idanunta sabida kunya yace “lazy girl, 1minute wife kawai” boye fuskanta take kokarin yi akanshi yace “get ready to make me cum inba hakaba I am going back to the only thing danasan can make me cum” zuwa ta saman fuskanta yayi yana kallon yanda ta lumshe idanu ahankali yace “haaaa” bude bakinta tayi ahankali kawai jitayi yawani kalan dannamata bataso tai karya but jitayi kaman yama wuce makogoronta wani kalan fucking mouth dinta yashigayi tana kakari kaman zatai amai ganin haka yadagata zaune yacigaba yarike kanta gan jiyake kaman zai haukace idan bai kawoba, Khairy idanunta sukai jajir Aliyu yakai one hour fucking mouth dinta yakasa kawowa, ganin she’s extremely exhausted yasa kawai ya kyaleta ya kwanta yana jawo ta yace “come here” bakinshi yawani kafa kan boobs dinta yakama hannunta yakai kan joystick din dayaki kwanciya tsabagen bala’i yana murzawa tanajin saukan hawayenshi nabin kirjinta yana wani irin nishi kaman zai mutu, jitayi jikinta yay taushi yawani irin bata tausayi Aliyu ya wahala akanta dayawa, ahankali takai hannunta tagogemai hawayen tadaura fuskanshi kan nata dayake kan kirjinta tama rasa mezatamai besides ita yanzu matan aure ce she needs to learn yanda zatai satisfaying mijinta ahankali takai harshenta cikin kunenshi sanan hannunta daya rike yana sata matsa gabanshi ta kabar dashi ahankali tashiga damke joystick don tana wani murje kan while sucking his ear da kyau, wani kalan nishi taji yayi yawanijaaaa nipple dinta abakinshi kaman zai katsa dayasa tai ihu. “Wayyooo Ya Aliyu” ko kadan baimasan metakeyi ba jan nipples dinta yake da kyau yana wani irin komawa baya yanajan dayan da hannunshi yana bankaremata sosai yana hawaye, azaban datakeji kaman zata mutu kuka tahauyi mara sauti tacigaba da gurjemai kan joystick don dakyau tana lasan middle na kunnenshi yanda yaja nonon nata wanan karan yana wani bankarrwa saida tafashe da kuka sosai wani kalan amai ruwa mai kauri taji yana fitowa daga kan joystick din Aliyu nawani irin nishi yana fizgan boobs nata kaman yana dambe sai yanzu tana gane ashe kawowan yake matse kan joystick din tayi da kyau tana jinshi yakarasa kawowa tass yanabin hannunta yanabin joystick din sanan yasauke wani irin ijiyan zuciya yacigaba dashan boobs dinta ahankali yana wasa da dayan ahankali sai chan taji hannunshi yasaki yafadi akan cinyanta alamun yay bacci while bakinshi nakan boobs nata daya, ahankali tazare bakinta dagakan kunnenshi sanan takalleshi ahankali, bacci yake but still bakinshi nakan boobs nata yana tsotsa kadan kadan, shiru kawai tayi tana kallonshi sonshi na ratsa ko’ina ajikinta tasan Ya Aliyu nasonta fushin shi kawai yayi yauya tabbatar da hakkan, in sha Allah tayi alkawari she will give her husband all her love, tanason Ya Aliyu sosai, bata taba ganin cool calm guy irin Aliyu ba, Aliyu is a special man, sabida batason sex look at wahalan dayayi shida he could easily forced her amman yahakura, binshi da kallo tayi yanda yakeda dogayen gashin idanu, ahankali tai kokarin kwace boobs din zata koma baya dan azaban zafi yake mata kaman yajimata ciwo ma biyota yayi batare dayasaki ba yana nishi dasauri tadaura hannunta saman kanshi ahankali tace “shhiiiiii sleep I will not take it from you” lamo yasakeyi yanasha kaman yajita, hannunta takai kan sajenshi tashafa murya chan kasa tace “today u are my little baby Ya Aliyu” dan murmushi tayi kafin ahankali tana kallonshi still tace “Mama I love Ya Aliyu sosai bazan iya rayuwa dawani ba, Mama please bless our marriage kinji Aliyu Khairyn ki keso” murmushi tasakeyi kafin ahankali tashafa sajenshi tace “Ya Aliyu I love you with every drop of blood, tissues, and muscles na jikina, and I am ready to take this journey with you, I pray Allah yabani ikon faranta maka”.



Har aka fara kiran sallan magrib suna wajen Aliyu bacci yake kana ganin baccin kasan yamai dadi bacci ne daya DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFE MATA BA WLH. dade bai sami irinshi ba, tadada shi amman ina yakasa tashi idan Mamman ta tadashi karajan nono bakinshi yake yakamo dayan da hannu yarike gam kaman zaa kwace mai ita abinma mamaki yabata to kodai baa shayardashi bane dayana karami ba, sai wajajen isha’i yatashi lokacin itama tasoma bacci, dakin duhu dumdun.




7️⃣1️⃣






Sakin boobs dinta yayi ahankali yana dan murmushi he’s feeling so very happy and satisfy tashi yayi ahankali yawuce bathroom wanka yayi agurguje sanan yafito ya shirya dan baiso yana missing jam’i karasowa gaban gadon yayi yadagata sama chak hakan yasa tabude idanu, hannunta yakama zuwa bayi yana bin jikinta da kallo da kyau saikuma yacire idanunshi dasauri tunawa da yayi alwala yace “go and perform gusl kifito kiyi salla nadawo zamu tafi” yajuya dasauri yafice, ahankali tai tafiya jin zafi zafi dudda ba wani abu yamata ba sanan tai wanka tafito tana tsane kanta da towel kafin tadauki kayanta ta saka da pant dinta daya bushe tai salla tana idarwa gyara gadon tayi tadauki tissue datagani adakin ta goge gadon inda suka bata ta yayyafa ruwa sanan takara gogewa tai flushing komi abayin sanan tafito tadawo cikin office din tana zama yana shigowa karasowa ciki yayi yana kallonta da yanda taki kallonshi ahankali yazauna gefenta bakinshi yakai saitin kunnenta yace “thanks Mrs Aliyu” faduwa gabanta taji yayi hakanan, hannunta yakama ahankali yahadashi da nashi sanan yadan fuzar da iska ahankali yace “and I am sorry for telling you that I hated you, Ummulkhair bazan taba iya tsanankiba kece rayuwa dakuma zuciyan Aliyu gabaki daya” ahankali tadago idanunta takalleshi danso take ta gasgata abinda kunnuwanta suka fadi mata, gyadamata kai yayi ahankali yace “I tried to hate you but duka was out of jealousy sabida karyan dakika min and all those stuff dakikace kan wanan” yadanyi shiru yana cijan lips dinshi dan baima so yakira sunan Zayn tsabagen masifan kishi irin nashi, dan iska ya fuzar kadan sanan yasake kallonta yace “because of that dan uwan naki” yasakeyin shiru, kafin yasauke ijiyan zuciya mai karfi ahankali yana kallonta kaman yanda take kallonshi yace “Ummulkhair I’ve never lied to you tunda muka hadu, I told you I am a jealous man ni kaina inda akwai magani na rage kishi da fushi dana saya nabama kaina, I am an obsessive and possessive man kan abinda nakeso I can’t help it, tunda nake arayuwana bantaba son wata ba sai ke all this years, I am 30yrs old going to 31 bantaba son wata ba tsawon all this years saike, you are my life partner, are you ready to accept Aliyun ki the way he is let’s date again Pickle?” Yay maganan yana kallonta waiting for an answer, shiru tayi tana kallonshi hakan yasa yadan lumshe idanu sanan yabudesu ahankali murya chan kasa yace “I know I can be annoying, hard, tough, stubborn sometimes but kinsan 1thing I am sure of shine inasonki sosai Ummulkhairy and I know ke kadai zaki iya chanzani uhm, so will u date me again let’s rekindle our love Babyna Matata Ummulkhairy Mama?” Wani kalan murmushi tayi sai kawai yaga ta matso tafada jikinshi ta rungumeshi sosai tana kuka dan she couldn’t hold her happiness and regret ahankali tace “Ya Aliyu kayafemin all those maganganu dana gayamaka erase them please a heart dinka and kamanta dasu, i said all of that sabida nasa kahakura danine but my approach was wrong, Ya Aliyu I am so sorry for hurting you kaji” dagokanta yayi gently yasa hannunshi ya share mata fuska tass yace “na yafemiki that is past tense kinji” gyadamai kai tayi yamike tsaye yana dagata yabata key na jeep nashi yace “muje drive us zuwa gidanku yau kin kararmin da karfi na” murmushi tayi ta karbe key, suka fito tare sai kallonsu ake amman ko ajikinshi yana rikeda hannunta suka fice bude mata gaban motan yayi tashiga ta zauna sanan yakoma dayan side din yazauna yana kallonta takunna motan tajasu sai murmushi yake feeling so proud of her, awani super market suka tsaya sukai shopping tarkace na kaiwa gida sanan suka wuce gidansu, suna shiga gidan parking tayi tana murmushi sosai tayi kewan gidansu.



Saukowa tayi shima Aliyu yasauko sanan yakama hannunta suka wuce ciki daidai zasu bude kofan falo aka rigasu budewa Zayn ne da Ya Manaf suka fito atare, ido da ido sukayi da Aliyu Zayn yawani irin dauke kai batare daya basu second look ba yawuce, shikuma Manaf yay murmushi yabama Aliyu hannu suka gaisa cikin mutuci Khairy tarikemai hannu tana mai shagwaba kan baikawo nata Aisha ba yabisu suka koma falon, Baba na falo zaune da Anty Mariya da Baffa suna ganin su Aliyu aka shiga gaisawa while mai gadi na shigo da abubuwan dasuka kawo.



Sunyi hira agidan kaman nothing has ever happened sai wuraren 11 Baba yashiga kwalama Khairy da Anty Mariya tajata sukaje sama tana hadamata wasu hadaddun kayan mata kan suzo sutafi dare yayi.

Saida Anty Mariya tagama hadamata sanan tazaunar da ita abakin gado anatse tace “Khairy nasan niba mahaifiyar ki bace amman yanzu nine ke matsayin mahaifiya a rayuwanki, kinriga kinyi aure yanzu iya zama da miji da dabarun ki na mata sune zasu zaunar dake, kinga maza all of them are thesame, Ummulkhairy biyayya shine abu na farko dazaisa ki siye mijinki completely, kinga Aliyu mijinki yarone mai natsuwa ma gaske, ga kunya gashinan very very calm kinga maza irinsu dinan dako abokanai basuda shi matayensu sune komi nasu, dole zaki daura damnaran zama dashi, kinga shiru shirun nan masu sanyi sanyi sunfi kowani namiji jaraba da yawan bukata, Khairy dole zaki daure ki biyamai kinaganin Aliyu ke kadaice mace dakuma namijin rayuwanshi, u are his mom his everything kika iya tafiya dashi za’adauka kin magance shi ne sabida yanda kome kikace shizaiyi, ki rike sirrin mijinki komene ne bayaso ki kiyayi abin, kinga maza masu suna Aliyu akwai zuciya barin ma wanan nakin dani naga zuciyanshi da idanuna ranan da yazo ya saceki” dan murmushi kadan Khairy tayi tunawa da ranan, Anty Mariya tace “kidage da shan magungunan nan naki kinji karkiyi wasu dasu, sanan karkice kesaikun tare menene menene yakiraki shimfidan shi ki amsa kinajina”  Gyadamata kai tayi jin Baba yasake kwalamata kira yasa Anty Mariya ta tashi tace “muje kinga Babban ki chan yana kiranki” tai maganan tana bude kofan suka fice, falo suka sauka babu kowa a falon hakan yasa sukai waje, dukansu na tsakar gida harda Zayn dataga Baba namai magana tareda Aliyun dabata san na meye ba, ganinta yasa Baba yajuyo ya kalleta yace “tahonan ku tafi Khairy dare yayi” gyadama Baba kai tayi takaraso tanaso ta gaida Ya Zayn but sanin halin mijinta yasa ko inda yake bata kalla ba agaban kowa Aliyu yakama hannunta sanan yakalli su Baba da Baffa yace “goodnight Baba saida safen ku” saida safe duk suka musu sanan Baffa yace “muje kaga Zayn, saida safe Amini” suma suka wuce motansu Zayn yaRshiga mazaunin direba yajasu suka fice daga gidan.




7️⃣2️⃣





Suna kaiwa gida bude musu gate akayi suka shiga ciki parking yayi wajen parking sanan yakashe motan batare daya budeba yakalleta kaman yanda tajuyo takalleshi yace “leki ijiye kayayyakin nan kima Gwaggo sallama kizo wajena ki kwana” makemai kafada tayi ahankali tace “ni kunya nakeji” dan murmushi yayi yace “ashe ko ni zan biyoki let’s go” murmushi tayi suka bude mota suka fito, tai hanyar flat din Gwaggo dagudu Aliyu ya tsaya yasaki baki yana kallonta saikuma yadan saki murmushi kafin yamaida kofan motan yarufe yawuce side din Mami, sallama yayi yashiga falon, daga Dad sai Mami ne afalon tana zaune kusada Dad shikuma Dad yana some paper work ganinshi yasa yature kome yakeyi ya kalli Aliyun, dan murmushi Aliyu yayi yace “Dad ina yini, Mami ina yini” yagaidata batare dayama kalletaba murmushi tayi ta amsa tace “ai mun zaci dagachan ka gudu da amaryan kane wanan dahar shadaya baku dawoba” Dad da tunda yashigo yake kallonshi babu wanda yakaishi understanding Aliyu a duniya yace “Yaya akayi Gadanga?” Kallon Dad Aliyu yayi yanaso yamai maganan yana jin nauyi kuma yama kasa Dad Ya tsareshi da idanu yace “talk what is it”? Ahankali yadan saukan da kanshi kasa murya chan kasa yace “Dad bazamu iya maida tarewan this week ba dole sai in 3weeks time” dan murmushi Dad yayi na manya ba Aliyun dayake cewa ya tsaneta bane wanan ba hmmm lallai yaran zamani tunda harshi dakanshi yay magana haka gwara ya maida tarewan this week kafin ayi abin kunya agidan nan, maida kanshi yayi kan rubuce rubucen dayake yace “okay Allah yakaimu wanan satin zaku tare zan waya da Babanta tashi kaje” dasauri yatashi yanajin wani dadi da kunya at the same time haryakai kofa zai bude Dad yace “one more thing Aliyu” dasauri yajuyo kanshi akasa, ahankali Dad yace “you are not allowed ka shiga side din Gwaggo dagayau, dagayau karka kara ganin Ummulkhairy sai ankaimaka ita gidanka, inhar kabi kan dokan nan dana shimfida maka to baza’a tare wanan satin ba kanajina” gyadamai kai Aliyu yayi ahankali dudda baiso hakan ba amman he’s willing yay hakan yau Saura kwana hudu asabar din, wucewa tayi yafita dasauri Mami tace “yaza’ayi ka yarda Alhaji bayan kasan ba’a gama shirye shirye ba” anatse Dad yace “akwati ne kawai baki gama hadawa ba kuma kece kebata lokaci, gobe duk wani kaya da ake bukata na akwatin nan ni dakaina zansa akawo, wata na hudu kenan ake da bikin nan basu tare ba, tunda shi harya cire kunya yace yanaso atare abarshi yatare Aliyu ba yaro bane ina fata kin fahimta” gyadamai kai Mami tayi ahankali tadade tanama kanwarta Hajo kwadayin Aliyu sabida yanda mijinta keson Aliyu, babu wanda yasan assets nashi dakomi nashi passwords pins nakomi nashi sai Aliyu, ga Aliyun banda company da gidaje da mahaifinshi yabashi shi kanshi Aliyun nada businesses da dama dake yielding mai bala’in money, wani kalan bakinciki taji aranta dayasa ta tashi kawai tama wuce sama.




Suna kaiwa gida bude musu gate akayi suka shiga ciki parking yayi wajen parking sanan yakashe motan batare daya budeba yakalleta kaman yanda tajuyo takalleshi yace “leki ijiye kayayyakin nan kima Gwaggo sallama kizo wajena ki kwana” makemai kafada tayi ahankali tace “ni kunya nakeji” dan murmushi yayi yace “ashe ko ni zan biyoki let’s go” murmushi tayi suka bude mota suka fito, tai hanyar flat din Gwaggo dagudu Aliyu ya tsaya yasaki baki yana kallonta saikuma yadan saki murmushi kafin yamaida kofan motan yarufe yawuce side din Mami, sallama yayi yashiga falon, daga Dad sai Mami ne afalon tana zaune kusada Dad shikuma Dad yana some paper work ganinshi yasa yature kome yakeyi ya kalli Aliyun, dan murmushi Aliyu yayi yace “Dad ina yini, Mami ina yini” yagaidata batare dayama kalletaba murmushi tayi ta amsa tace “ai mun zaci dagachan ka gudu da amaryan kane wanan dahar shadaya baku dawoba” Dad da tunda yashigo yake kallonshi babu wanda yakaishi understanding Aliyu a duniya yace “Yaya akayi Gadanga?” Kallon Dad Aliyu yayi yanaso yamai maganan yana jin nauyi kuma yama kasa Dad Ya tsareshi da idanu yace “talk what is it”? Ahankali yadan saukan da kanshi kasa murya chan kasa yace “Dad bazamu iya maida tarewan this week ba dole sai in 3weeks time” dan murmushi Dad yayi na manya ba Aliyun dayake cewa ya tsaneta bane wanan ba hmmm lallai yaran zamani tunda harshi dakanshi yay magana haka gwara ya maida tarewan this week kafin ayi abin kunya agidan nan, maida kanshi yayi kan rubuce rubucen dayake yace “okay Allah yakaimu wanan satin zaku tare zan waya da Babanta tashi kaje” dasauri yatashi yanajin wani dadi da kunya at the same time haryakai kofa zai bude Dad yace “one more thing Aliyu” dasauri yajuyo kanshi akasa, ahankali Dad yace “you are not allowed ka shiga side din Gwaggo dagayau, dagayau karka kara ganin Ummulkhairy sai ankaimaka ita gidanka, inhar kabi kan dokan nan dana shimfida maka to baza’a tare wanan satin ba kanajina” gyadamai kai Aliyu yayi ahankali dudda baiso hakan ba amman he’s willing yay hakan yau Saura kwana hudu asabar din, wucewa tayi yafita dasauri Mami tace “yaza’ayi ka yarda Alhaji bayan kasan ba’a gama shirye shirye ba” anatse Dad yace “akwati ne kawai baki gama hadawa ba kuma kece kebata lokaci, gobe duk wani kaya da ake bukata na akwatin nan ni dakaina zansa akawo, wata na hudu kenan ake da bikin nan basu tare ba, tunda shi harya cire kunya yace yanaso atare abarshi yatare Aliyu ba yaro bane ina fata kin fahimta” gyadamai kai Mami tayi ahankali tadade tanama kanwarta Hajo kwadayin Aliyu sabida yanda mijinta keson Aliyu, babu wanda yasan assets nashi dakomi nashi passwords pins nakomi nashi sai Aliyu, ga Aliyun banda company da gidaje da mahaifinshi yabashi shi kanshi Aliyun nada businesses da dama dake yielding mai bala’in money, wani kalan bakinciki taji aranta dayasa ta tashi kawai tama wuce sama.





Saida sukakai gida zai bude kofa yafice Baffa yarike hannunshi hakan yasa dasauri yakalli Baffa, murmushi Baffa yamai yace “sit Zayn” komawa ahankali Zayn yayi yazauna yana murmushi, ahankali Baffa yace “abokinka Mamu yabani labarin Aisha da kai achan kasan wajen dakukai karatu Zayn” Baffa yakirashi ahankali yace “Naam Abba” ahankali Baffa yace “kagadai bani na zabamaka Aisha bako amman duk wanda yayi abu domin iyayenshi baya tabewa, hakki nane nai guiding naku and put all my children a right tract, naga amincin dayake tsakanin mahaifiyarka da mahaifiyar Aisha, duka duka bikinku saura sati daya Zayn, inhar kai imani da kaddara sanan kama iyayenka biyayya trust me reward dinka is with Allah, Son ka manta da Ummulkhairy Khairy aranka, Allah yariga yakaddara cewa ita Matan Aliyu ne, yaron nan abin tausayi ne shima Zayn baida mahaifiya kaman Khairy gakuma mugun ciwon zuciya, kakosan yanzu haka akwai yan abubuwa na likitanci dake supporting heart dinshi acikin zuciyanshi” kallon Baffa Zayn yayi shiru, gyadamai kai Baffa yayi yace “yes Zayn, nasan ka nasan koda bakasan Aliyu ba ayanda yake neman mutuwa kan Khairy zaka iya barinmai kai musulmi ne kuma zaka iya soma dan uwanka abinda kake soma kanka, Zayn I love you kaine d’ana nafari I don’t want you to waste your life, Zayn kaso Aisha for me, for ni mahaifinka, for mahaifiyarka, for sake na ita Aishan dake sonka Allah will reward you for that kaji yaro na” ahankali ya gyadama Baffa kai yanajin duk wani nauyi da zuciyanshi yamai natafiya, hannu Baffa yakai yakama kuncinshi sanan ahankali ya matso ya manna mai peck akumatu da goshi ahankali yace “Allah yamaka albarka Zayn” ahankali yace “Ameen Abba” murya chan kasa Baffa yace “start planning your wedding kome kakeso tell me kaji” gyadamai kai yayi ahankali sanan Baffa yawuce yafita daga motan zuwa flat dinshi.



Ijiyan zuciya Zayn yasauke he hates Aisha sosai but for the first time yau kalaman Abba yasa yaji he’s ready to give her a second chance, kowa arayuwan nan deserves second chance, idan yana cewa yar iskace ita shima ai hakan ne, Yar iska da dan iska kowa deserves a chance inhar yayi tuba na gaskiya, tunda aka samusu rana kusan kullum Aisha kuka take tana rokonshi ya yafemata, kullum test messages ta rantse takara rantsewa cewa sex din dasukai da Kb sau dayane kuma shima was a mistake ranan sunyi drunk yasa tasha shisha, sex din datayi kuma dashi was all out of love tadauka ayanayinshi that’s the only thing dazaisa ya sota he’s really to let go off everything yama iyayenshi anything, babu amfanin d’a dabazai iya sacrificing happiness nashi for iyayenshi ba, he was a bad boy before but sanadin Khairy kasheta da aka kusayi yasa ya shiru idanunshi suka bude yaga gaskiya, ya tsani shisha, kwadayin mace wanan da kyar yakema bacci saisa kullum yake azumi yana istigifari bazai kara zinaba shida mace sai halaliyanshi, ijiyan zuciya ya fuzar sanan ahankali yasa hannunshi yaciro wayanshi daga aljihu number Aisha yaciro ahankali yashiga yimata text.

“Aysha I’ve accepted you, but I need to ask for your forgiveness, nasaki kuka, bakin ciki, i judged you call you all sort of names bayan ni I am even far far worst than u are, ance iskanci awajen namiji ado ne but is all a lie, wutan jahannama guda ce for mace da namiji, kiyafeni let’s ask Allah for forgiveness, build a new life and forget our past, this is to new beginning, I can’t wait to make you mine Ayshatu” 

Turamata text din yayi tareda sakin murmushi dan yasan she will be delighted taga messege dinan sanan ahankali yabude mota yafito yana kulle motan yawuce ciki.




“Iskanci bin mata, shaye shaye bashine farin ciki da wayewan rayuwa ba, shidama ance sabon Allah nada dadi, Allah nada so many ways na kama mutane, I hope all of us mun gyara kanmu ta hanyar daina sabon Allah damukeyi azahirance dakuma aboye, Allah ya shiryemu gabaki daya, Allah ya yafemana kura kurRanmu Ameen”.



7️⃣3️⃣




Gagarumin biki ake shiryawa agidaje uku, gidansu Aliyu gidansu Baffa da gidan su Aysha.


Baba yama Khairy lafiyayyen kayan daki da aka kai babban gidan Aliyu an jeramata komi, akwatinan da Aliyu dakuma Dad da Gwaggo sukama Khairy kusan 40 dan set daban daban designers, fir daga Dad har Gwaggo sun hanashi ganin Khairy da akema lafiyayyen gyara sai yanzu Khairy takeji aure take tasa Batool tamata inviting all her friends ranan Friday da Saturday ne za’ayi biki asabar da night akaita gyara akema Amarya na ban mamaki.



Ranan Friday wajen kamu aka bari Aliyu yaganta bayan yabiya kudi dayaga Khairy saida yadan kusan zarewa akahau nai dariya Dan rudewa yayi su Meena sai dariya suke dan tunda Aliyu yakirata yanunamai shiya yafema Khairy komi yawuce between them kuma yanaso tabata hakuri sudawo kaman sisters taje tabama Khairy hakuri da ita da Batool sune manyan kawayen amarya akai shagali har dare ko kadan ba’a bari Aliyu yakebe da Khairy ba Aiko yacika yay fam yace zata ganene sai dariya take.



Yau babban ranane wajen both Aliyu da Khairy wato babu abinda yakai soyayya dadi sunma kosa dare yayi tabar gidan nan ta tafi gidanta wajen Aliyun ta dan tayi kewan shi sosai kwana nawa bata ganshi ba.



Karfe 8 nadare aka tafi da Ummulkhairy gidan mijinta gidan Aliyu Hydar.

Karfe 8 nadare aka kai Ayshu gidan mijinta Zayn.



VIP kunason amarcin this two angwaye konasu KhairRy kadai???




7️⃣4️⃣





Dagaske Aliyu one single friend bayida shi saidai yaran aiki, hakan yasa Dad yadaukeshi amota sai uban kunya yakeji har zuwa Babban gidanshi, cikin gidan Dad yashiga gidan yahadu bana wasaba kaman wani gidan gwamna, kallonshi Dad yayi yace “Oya get down and go kasayi baki kasan yanda zakayi da kawayen amarya sutafi nidai saida safe” awani irin kunyace yace “Daddd plssss” hararanshi Dad yayi yana murmushi yace “don’t Dady me, Allah baku zaman lpy gud night son” ahankali yabude motan yasauka yabude baya ya kwashi manya manyan ledojin dasuke nan aciki sanan yamaida kofan yarufe Dad yaja mota abinshi yawuce yay tafiyan shi.




Okay Gidan yabida kallo sanan ahankali yafara tafiya zuwa gaban flat din ahankali yabude kofan ya shiga gidan wani haddaden kamshi yake banawasa ba, furnitures na ciki zaka dauka villa kaje, ganin babu kowa a falo yasan suna sama yasa yawuce wani hadadden daki dakenan kasa yabude kofan yashiga dakin shima yahadu yasha furnitures ga kanshi da dakin keyi ijiye komi yayi awajen sanan ya kwanta kan gado wayanshi yaciro yay dialing number ta amman harya gama ringing bata dauka ba hakan yasa yamata text.


“Suwaye tareda ke”? 

Ko 1min text din baidauka ba tamai reply.

“Gwaggo, da Meena, da Batool da Amal, Ya Aliyu wai kwana zasuyi please kazo na ganka yau kwana nawa I didn’t see you” 

Wani kalan murmushi yayi yana tunanin yanda zaiyi dawanan jarababbiyan kakan nashi, tashi kawai yayi yawuce sama Gwaggo yagani zaune falon sama dawani katon ghana masgo guda daya tana lissafin wani daki zata dauka adakunan dake saman tana ganin Aliyu tace “yauwa Gadanga zo bani dakina da kanka kagani naje najera wayan nan kayan a sip, gobe direba zai karasa kwasomin kayayyakina na jera adakin nawa” wani kallo Aliyu yamata daidai Meena tafito daga dakin da Khairy keciki ganin Ya Aliyu da Gwaggo yasa ta gimtse dariyan datakeji tazo wajen da sauri tace “Ya Aliyu Gwaggo tahada kayanta tass wai gidanka zata dawo dazama bazata iya rabuwa dakai ko Khairy ba” wani kallo Aliyu yama Gwaggo da itama kallonshi yake yace “wlh bazaki zaunamin agida ba ki koma chan gidan danki kicigaba da zama” nuna kanta Gwaggo tayi tace “ni zakama rashin mutunci” hararanta yayi yace “eh” cikeda masifa ta tafa hannu tace “yo idan ka isa Aliyu zoka korani daga gidan nan” wuceta yayi yay dakin dayasan Khairy keciki yabude dakin, Khairy na zaune kan gado an rufemata kai da lafaya ga Batool da Amal duk akan gado suna mata hira, ganin Aliyu yasa duk suka gaidashi, dan murmushi yayi yasa hannu a aljihu yaciro bandir na yan dubu guda biyar ya ijiyemusu akan gado yace “ka kudin siyan baki ina zuwa bari na ari Mrs Aliyu” yay maganan yana kama hannunta dayasha lafiyayyen lalle, ahankali tabiyoshi ta sauka kanta alullube yawuce suka fito daga dakin ganin yafito da Khairy yasa Gwaggo ta mike tsaye tace “ina zaka kaita kasayi kudin bakin bakin ne” ganin acike Gwaggo take dashi yasa ahankali yace “magana zamuyi da ita afalo Gwaggo, kuma ai nasaya ko Meena” dasauri Meena ta gyadama Gwaggo kai tace “ga kudin chan adakin” dasauri Gwaggo tace “muje ingani” tai hanyar dakin, dawani irin sauri Aliyu yaja hannunta suka sauka kasa zuwa dakin maida kofan yayi yarufe yasaka key yakai hannunshi ahankali Ya yaye gyalenta murya chan kasa yace “Assalamu Alaykum” wani irin murmushi Ummulkhairy tayi tai wani tsalle ta rungumeshi, wani irin fito da ita daga jikinshi yayi kawai Ya dauketa sama yana murmushi sosai yace “I miss this girl, me kikamin ne”? Sauketa yayi dawani irin sauri tazauna kan jikinshi tana kallon fuskanshi yanda yamata kyau ahankali tadaura hannunta kan kirjinta dayan hannunta kan kirjinshi tace “wani sirri ne da only this 2 zasu iya ganewa” hannunta yakama ahankali yamma hannun kiss yana kallonta kaman baitaba ganinta ba yanda takara kyau fatarta na taushi tana kamshi turare bana wasaba, jin Gwaggo na kwalamai kira yasa yace “bazata taba sani we are here ba, let’s go and perform ablution” gyadamai kai tayi suka wuce bayi alwala sukayo sanan suka fito dakin akwai dadduma kowani daki na gidan an ijiye dadduma hakan yasa suka shimfida sukai salla bayan sun idar yamusu addu’a yaHkama kanta yay addu’a sosai sanan ya warware mata gyalen.




7️⃣5️⃣





Murya chan kasa yace “have you eaten”? Girgizamai kai tayi alamun no hakan yasa yajawo ledojin daya kawo yabude musu bankararrun kajin da yogurt yace “muci” gyadamai kai tayi sanan tabudemai baki, murmushi yayi yace “1 minute wife kawai” wani kalan kunya taji tasauke kanta ya yago kaza yakai bakinta tafaraci sosai taci shima sosai yaci sanan yatashi dagata itama yayi yawani fizgota jikinta yana wani irin kallonta kunya taji yakamata dasauri ta sunnar da kanta kasa tai bayi dasauri shima yabiyota hannunta ta wanke sanan tadauki daya daga cikin savon brush dake bathroom din ta wanke bakinta shima haka tarigashi gamawa hakan yasa tajuya zata fita da hannu daya yariketa hakan yasa ta tsaya tana kallonshi yanda yay kyau farin shaddan dake jikinshi bakaramin kyau yamai ba, Ya Aliyu nada kyau da ace zata haifi all yaranta suyi kama dashi data more gashi fari fat unlike ita datake nan black beauty. “Kinsan cewa I am yours now” Aliyu yay maganan flashing water on her face ganin yanda take kallonshi, wani irin murmushi tayi ta lumshe idanu tabudesu ta daura akanshi, bude kofan bathroom din yayi sanan yadauketa kaman wata Yar yarinya yace “maisa kike kallona” yay maganan yana kashe wutan dakin yana dauke da ita yay gado da ita wani irin jefata kan gadon yayi sanan yahau kanta batare daya sakin mata nauyi ba yakai fuskanshi daidai saitin nata murya chan kasa yace “maisa kike kallona” kaman wata Yar baby da murya kar karama akuma shagwabe tace “Ya Aliyu you are so cute, inaso yarana suyi kama dakai” wani irin kankameta yayi cikin kalan muryan yan iska yace “bari naciki namiki ciki zakiga zaki haifi masu kama dani Pickle” murya chan kasa tace “Ya Aliyu I love you” shiru yayi dan kalman har ranshi yajita, ahankali yama lips nata peck, murya chan kasa yace “and I love you Ummulkhairy, I love you” gyadamai kai tayi tana kai duka hannunta saman kanshi ta cusa hannayenta cikin soft gashin kanshi tanajin wani irin shauki nashi ita kadai tasan yanda takeson Aliyu, ahankali tace “Ya Aliyu” murya chan kasa yace “yes Pickle” murya chan ciki tace “Ya Aliyu I love you” shiru yayi yana kallonta he could feel yanda the words came from heart dinta, Awani irin hankali yasaukar da lips dinshi daidai saitin lips dinta suka hade, da edge na voice nashi yace “I love you Ummulkhair” murya chan ciki data katse sosai tace “Ya Aliyu I love you! Kaman in cinyeka nakeji” dan murmushi yayi ahankali batare daya janye lips nashi daga kan nata ba yace “Ummulkhair I love you da sonake na cinyeki yanzu, should I baby”? Gyadamai kai tayi ahankali hakan yasa yashiga kissing nata ahankali tana maidamai da martani ko’ina na jikinta nawani irin yin shauki, dagota yayi batare daya raba bakinsu ba yadaurata akanshi yana kissing nata dazafi zafi yakai hannunshi bayanta yawani ja zip din riganta kasa sanan yadagota zaune still kissing her rigan yacire mata ya yar baimasan a ina ya yar ba, gyalen lafayan ya yaye shima ya yar, sanan yasaki bakinta tana kan jikinshi still yana rikeda ita yacire rigan shaddan jikinshi ya yar da singlet sanan yamaida bakinshi kan nata yawani irin fizgo yashiga kissing nata, yakai hannunshi kan zariyan wandonshi yacire yaja daga Wandon har boxer kasa ya cire ya yarda, ahankali yawani irin daukanta yasata akan jikinshi yakai hannunshi tabayanta yay unhooking bra dinta bata hanashi ba yakama hannayen ta yazare ya yar sanan yaraba bakinshi danata yana kallon fuskanta cikin duhun kaman yanda take kallonshi itama cikin duhu kirjinta nafaduwa dum dum, gently yawani kwantar da ita ahankali kan gadon sanan yakai hannunshi kan maranta, ahankali yadaura hannunshi kan pant nata yashigajan pant don kasa ahankali tana wani irin nishi sanan yakarasa cirewa yayar.


Feet nata yabi da kallo kafin ahankali yadukar da kanshi yabude bakinshi gently yatura babban yatsanshi cikin bakinshi wani yirrrrr taji dayasa ahankali tasaki wani irin malalacin kara washhhhh tana juyarda kanta, yanda yakeshan yatsun kafanta yasa taji kaman zatai fitsari sabida yanda abin kemata waiwayi da dadi dake juyamata brain, ahankali yacire bakinshi daga yatsun kafan nata daya gama jagwalgwalawa sanan yafara kissing ko’ina akafanta yataho sama har zuwa kan cinyanta, wani irin nishi tafara dataji yazo wajen, kafafunta dake kwance akan gadon taji yakama yadagasu sama yawani kalan waresu da duka hannunshi sunyi side side, yanda take nishi fast fast yanaji daga kafanta ahankali taji yanakai kanshi wajen wani kalan zabura jikinta yafara dasauri yace “shiiiiiiii” kafin yawani yi blowing dripping Vijay nata da hot and cold breezing na bakinshi wani kalan datse hakoranta tayi  kaman maranta zai fashe haka takeji, ahankali yakai tip na tongue nashi yana flicking all the chubby and chunky meat na wajen more water na dripping out Khairy nawani irin motsi kaman tahade kafafunta amman ina yariga ya bude mata kafafu tatas kaman zai yagata, ganin yanda take motsi jikinta na rawa yasa yadan janye kanshi back yadena komi awajen kawai yana kallon Vijay din in the dark yana jira tai calming down, jin shiru bai mata komiba yasa jikinta yafara relaxing tana sauke ijiyan zuciya almost good 3 min, saida Aliyu yalura ta natsu to the core kaman wani irin kura agujen bala’in kaman damisa yawani kai kanshi dammm kakeji yawani buga bakinshi awajen yanashanta kaman mahaukacin dabaisan Vijay yakesha ba. Ihu Khairy tayi danji tayi Aliyu kaman yana neman yahaukatata ne, kankame zanin gado tayi tana wani irin bucking up tana juyi da kanta trying ta fisge gabanta daga bakinshi amman takasa sabida yanda yariketa kaman na zuba abinci mai dadi awajen haka yakeci da sha awajen.

“Ahhhhh Ya……Ali stopp,….Ya Aliyu wlh fitsari, Innalillahi wayyo Allah na dadi Ya Aliyu zan mutu wlh….. uhmmm” ko kadan tama manta metakeyi surutu kawai take Aliyu kuma sakin nishi da gurnani yake kawai awajen yana zukan wajen, vibrating dayaji jikinta yafara kaman an jonamata electric shock yasa yaciro kanshi ahankali yana karanto addu’a aranshi bamatasan yafito ba sabida yanda jikinta kerawa, shima rawa jikin Aliyun yafara hakan yasa yakama boobs nata abakinshi dawani irin sauri yana bude kafanshi dan idan bai sadu da ita yau dinan ba zai iya mutu he don’t care da mutane agidan su suka sani, ahankali yashiga turawa kaman an tsuguleta taware idanunta tass tafara tureshi cikin wata kalan murya dabata fita sosai tace “Ya Aliyu wat are you doing?” Da kyar yasaki boobs nata dudda bayaso but dole yay hakan yakai bakinshi saitin nata ahankali yace “zan sadu dake Ummulkhair, I want you this night” kafin tai magana yahada bakinshi da nata yawani kalan matseta gam wato namiji namiji ne, fara yaki da gabanta yashigayi yanaji tana kuka abakinshi tana kokarin kwace kanta shi kanshi yasan real mugunta yamata dan mugun matseta yayi ko motsi bata iyayi yashiga ramming wajen kaman mahaukaci, da Khairy taji azaba iya azaba kaman kasheta yakeso yayi wani mugun karfi ne yazo mata tashiga dambe da kokawa dashi ta fizge bakinta tafado kasan gadon, kafin ta tashi yabiyota zatai ihu yadaura hannunshi kan bakinta Ya matseta anan kasa Ya shiga kwakumanta tass tasume, dudda yaji tasume bai bartaba sai lokacin yama shigayi da kyau da kyar yasamu yashigeta wani kalan rawa jikinshi yafara baitabajin what he is feeling ayanzu kaman kaman zaiyi hauka yashigaji, daburcewa yayi yashiga banging nata very very well shi kanshi baisan cewa he’s this wild ba, baitaba sex ba yau da yasamu yakasa controlling kanshi dudda yasan this is her first time dan dadin dayakeji kaman zai har duniya, wuraren 3 yakawo sanan batare daya ciroma ya kankameta ahaka yamika hannunshi da kyar yajawo bargo daga kan gadon ya lullubesu dashi ahaka bacci yay awon gaba dasHhi da ita.



7️⃣6️⃣





Wuraren 7 nasafe maganan Gwaggo yatadashi daga bacci yaji tana ina Aliyu yakai Khairiya jama’a, wai wani kalan fitinannen yarone Aliyu jama’a, da kyar yabude idanunshi dudda dakin da duhu but da Kwai dan haske haske na gari yawaye, kallon kansu yayi yanda suka dukunkune juna kan carpet din kasan dakin sun lulluba da bargo ahankali yajaye jikinshi daga nata sanan ya lullubeta da kyau yawuce bayi yana tunanin all that happen yesterday baitaba sanin sex feels this good ba, kaman zai mutu jiyan nan da dadi infact he can’t wait for the second time dazaiyi, murmushi yayi yay wankan shi tsaf sanan yafito baida kaya adakin hakan yasa yadauki nashi kayan da duk ya watsar jiya akasa yasaka yay sallan asubahi sanan yay facing gabas yay salla saida ya idar sanan yasake cire kayan yabar only boxer yazo wajen datake a kwance, hannunshi yasa ya yaye bargon datake lullube dashi yanabin fuskanta da kallo yanda ya kumbura ta wahala sanan ahankali yadauketa chak, yasanta da nauyin bacci dama barinma yau dabai barta tai na dare ba hakan yasa yabude kofan bayi yashiga da ita jinta cikin ruwan zafi yasa tawani zabura zata tashi tsaye jin azaba da sauri yariketa yana tsugunnawa yace “sorry Pickle” tureshi tayi tafashe dawani irin kuka na azaba, yana kallonta tana kukan bai cemata komiba har saida ruwan yahuce yazo zai taimaka mata makemai kafada tayi cikeda fitinannen shagwaba tace “leave me alone” tsabagen yasan baida gaskiya ahankali yace “ok” cikin fushi tace “go away I want to shower” Gyadamata kai yayi yace “yes Pickle” sanan yawuce ahankali yafice tareda rufomata kofan yafito ya jingina da jikin kofan tareda fuzar da iska, ahankali yace “yanzu yaya zan lallasheta”? Yana tsaye awajen yanajin saukan ruwa abayin harya daina ji hakan ya tabbatarmai datagama wankan, bude kofan bathroom din yayi yaganta tsaye ta daura towel a kirji dakuma daya akanta tana ganinshi ta daukekai zuwa gabanta yayi kaman matsoraci yace “should I carry u Pickle”? Dan kallonshi tayi sanan tadauke kai batare data kulashi ba gently ya matso kusada ita ahankali ya dauketa kaman yadauki kwai sanan yafito da ita yakawota ya zaunar da ita bakin gado yashiga bude wardrobe nadakin dan waigowa tayi tasaci kallonshi yanda yake komi dasauri dasauri zakasan yadamu sosai kuma wlh zaisani, hijabi yagani da abaya a wardrobe din hakan yasa yadauko yadawo da sauri ya ijiye gefenta sanan yakama towel din kanta ya warware yana goge kanta sanan ya ijiye bayan gashin ya tsane ya shiryata tsaf ya shiryata sanan yadagata fashewa da kuka tayi dasauri cikeda tausayinta yace “sorry Pickle plssss” yakai hannunshi yana kama kunenshi, turomai baki tayi tahau kan dadduma sanan ta tada salla zama yayi bakin gadon ahankali sanan yadauki wayanshi yay dialing number Dad, Dad na dauka kafinma Dad yay magana yace “Dad please get Gwaggo and everyone in this house out please Daddd” sanan yakatse wayan cikeda kunya, yadawo kusada Khairy yanajira ta idar da salla, tana idarwa yadauketa yamaidata kan gado sanan ya lullubeta ganin jikinta yay zafi yadauki kayanshi yasaka sanan yakalleta yace “ina zuwa” ficewa yayi daga dakin tana jinshi yana kulle dakin daga waje yawuce tsakar gida yashiga motanshi yafice abinshi.



Wani babban pharmacy yaje yasan mai pharmacy wanda yake Dr fadamai komi yayi yahadamai magani biya yayi sanan yafito yashigo mota yadawo gidan yatatrar Dad yaturo an tafi dasu Gwaggo dasu Batool, murmushi yayi yawuce kitchen yana kallon manya manyan kulolin dake dinning na abincin da aka kawomusu, tea yahado mata sanan yafito yadauki plate yazuba mata pepper soup yasaka spoon yay arranging komi a tray yay hanyar dakin datake yakasa mata abinda yafaru jiya da kalan dadin dayaji kaman yasakeyi yanzu.


Dakin ya shiga ya tarar bacci yasake daukanta ijiye komi yayi yakarasa gaban gadon yadagota yanajin yanda jikinta yay zafi wanan karan kasa gardama tayi sai kuka datahau yi tea yajawo yana bata abaki tana sha tasha sosai sanan yabata magani tasha pepper soup din kasaci tayi hakanan yahakura ya barta zata kwanta yahanata hakan yasa suna zaune kanta nakan kirjinshi bacci yay awon gaba da ita.




Bayan 3 days!

Ko Allah yasan Aliyu hakuri kawai yake yanaso yabarta ta warke da kyau, but ko kadan yakasa manta that experience, koyaya yake zaune shi kadai koya kalleta abinda yake tunawa kenan, baitabajin abinda yakai saduwa da mace dadi ba, wani kalan daraja da kima na musamman Khairy takara aranshi yanda take natsassiyar yarinya, wani irin so yakemata ita kanta Khairy har mamakin shi take ba’a cewa so yay yawa amman son Aliyu kam yamata yawa.

Hakanan ganin yafita zuwa sallan isha’i a mosque kawai taji sotake ta sauko tasaka turare agidan dan jinyan datake yasa bata taba saukowa kasa ba tunda Aliyu yadawo da ita sama daga dakin dayamata aika aika. Tana sanye dawani sexy gown da bayanshi gabaki daya kenan abude, batasaka bra ba dan boobs nata ciwo suke mata sabida wahalan dasukasha hannun Aliyu ranan saisa harsu tahanashi tabawa tun ranan rabonshi dasu, sosai red gown din yamata kyau kanta babu dankwali akai sai gashinta data gyara tai parking nashi atsakiyan kanta kaganta zaka dauka wata American actress ce, tana cikin kunna turaren taji anbude kofa, dawani irin sauri ta juyo tareda mikeHwa tsaye ganin Ya Aliyu ne.



7️⃣7️⃣







Hada idanu sukayi hakanan taji gabanta yafadi sabida wani irin kallo dayamata, ganin yanda yakamata red handed yasa takoma ta tsugunna ahankali, wani kalan murmushi yayi yamaida kofan falon yarufe sanan yataho cikin falon yanabin bayanta da kallo daidai tagama saka turaren tamike tsaye jin bataji maganan shi ba tasa tadan juyo zata saci kallonta wani irin fizgota taji anyi dasaida tafirgita fadawa jikinshi tayi ya tareta kirjinta da nashi na haduwa yabi fuskanta dawani irin kallo batare dayace mata kalaba, ahankali tadago yan kananun idanunta tadan kalleshi hada idanu sukayi dasauri ta sunnar da kanta kasa, dan murmushi yayi yana kallon gashinta data gyara yace “wai har yanzu baki daina fushi dani bane amaryan Aliyu” turomai baki tayi wani irin ijiyan zuciya yasauke ahankali yace “I am crazy about you Ummulkhair Oh My God” yay maganan yana kama joystick dinshi dake tashi da hannu sabida dan turomai bakin datayi ashagwabe, dan kallon abinda tarike tayi wani irin kunya taji batasan lokacin da tajuya dasauri zata gudu ba tana murmushi yawani kamota yace “come here” makemai kafada tayi tana tahowa ashagwabe tace “Ya Aliyu dazafi please karka sakemin” murya chan kasa kaman wani maraya yace “kin warke fa Ummulkhairy, please just once karna sume miki” yay maganan yanakai bakinshi saitin gefen wuyanta ya manna mata kiss ahankali. “Muah” wani irin tashi tsigan jikinta yayi batasan lokacin data lumshe idanu dasauri ba murya chan kasa dabaida karfi sosai tace “stop” ahankali shima cikin wata malalaciyar murya yace “I want you Ummulkhairy, did you know bantaba sanin mace ba sai akanki, I’ve never ever felt the way I did, Pickle kinfi komi dazan musantamiki dadi, Baby idan ban having that your tiny hole naki ba yau I can die don’t you want me”? Yay tambayan cikin wata kalan murya dake sanya mace shiga yanayi na sha’awa yana manna mata wani irin kiss acikin kunne dayasa tashige jikinshi dasauri tana kankameshi takasa magana.



Hannunshi daya yakai ahankali yadaura kan ass dinta tasaman riga yadaura bakinshi kan shoulder nata yana kissing all over yace “remember how I use to make you shiver kaman nasaki acikin snow don’t you wanna feel that dadi? Yau Kwanan ki 4 bantaba kiba don’t you miss my touch Pickle”? Yay magana nan yana spanking ass nata dayasa alalace tace “auuchhh” dago hannunshi sama yayi yadaura bayan riganta yaja zip din kasa ahankali sanan yaciro fuskanta daga kirjinshi yakalleta idanunta lumshe huramata iska yayi akan idanun dayasa tabudesu Dasauri tadaurasu akanshi staring directly a pink lips nashi dayake turomata, dan murmushi tayi akunyace zata daukekai dasauri yace “common kiss me kaman yanda kikai ranan first night namu” wani irin daura hannayen ta kan fuskanta tayi akunyace hannun yaaa nashi hannuwan yasauke sanan yay grabbing lips nata ahankali yashiga kissing yana unhooking bra nata yakai yacire ya yar sanan yawani irin juyar da ita yasa bayanta akirjinshi yakawo duka hannayebta biyu ta bayanta yakai kan joystick dinshi yakai bakinshi kan kunnenta yace “just grab this” sanan ahankali yakai hannunshi yadaura kan boobs nata yashiga murjesu yanajan nipples din sama kaman zai ciresu tana wani kara bankarewa sabida dadi dakuma zafi datakeji ahankali tana grabbing joystick din da kyau.



Almost 4min yayi yana dirzan boobs nata da hannayenshi saida taji kaman nema yake ya tsinkemata su ta fizge kanta da sauri zata gudu yataba wani abu jikin 3sitter couch nasu kawai ta warware takoma gado yajefata kai yashiga cire kayan jikinshi tana kallonshi tana wani irin nishi sama sama dake cikeda tsoro da fargaba, all Wanan tabe taben she is enjoying it asalin abin ne da zafi shine kuma bataso yayi fadowa kanta dayayi yasa tazabura zata tashi kamata yayi yace “come here wlh bazaki gudu ba” yakai bakinshi kan boobs nata yanasha dasauri dasauri yana bude mata kafa tanajin haka tafara kokarin dambe ta kwace kanta danneta yayi da kyau da karfi da yaji yashige da kyar, fashewa da kuka tayi dudda taji zafin bakai na ranan ba but still dazafi, tanaji tanagani rasa kan Aliyu tayi hauka yashigayi akanta gurnanin shi kaman zai fasa falon dasuke ciki, juyata yake ta every angle wayace sex is sweet romance is sweet but sex is painful inji Ummulkhairy dataji Aliyu na neman kasheta.




Wuraren 3 na asuba da kyar yabarta shima sabida uban kukan datakemai ne dan yau bata sume ba, sai kuka datakeyi da kyar ya barta, daukanta yayi idanunshi sunyi jajir yay sama da ita zuwa bayi, wanka yafara mata sanan yafito da ita ya kwantae da ita akan gado shima yakoma yayi sanan yadawo ya shirya zuwa masallaci dan anfara kira yafice dan yasan idan yakoma zai makara yanajin wani kaRlan dadi dabai tabajin irinshi ba aduniya.





7️⃣8️⃣





*****

Yau kwana sha shidda kenan da bikinsu that’s 2weeks da yan kwanaki kenan, duka duka sau biyu Ummulkhairy tabari Aliyu yay sex da ita, Aliyu nada bala’in hakuri, ko kadan bai son kukan ta, tunda tagane hakan koyaya yay making attempt natabata kawai saita saki kuka tadinga cemai ita zafi takeji hakan yasa yadage iya dagewa yahakura bayama zama kusada ita dan inhar he’s close to her he can’t help it but touch her, saidai yayta binta da idanu kaman zai cinyeta abin bakaramin dadi yana Ummulkhairy ba.




Yauma kaman kullum yana shigowa daga gidan daga sallan asuba yaga kiran Manaf hakan yasa yadauka da sauri, dan murmushi yayi yace “saikun zo” sanan ya katse wayan yashiga ciki, a dinning yaga Ummulkhairy tana kokarin jera musu abinci a dinning tana sanye dawani dogon Riga na lace pink dayamata bala’in kyau, ance duk inda Amarya take kyau ne da ita, binta yayi da kallo kaman zai cinyeta jin ana kallonta yasa tajuyo ko kadan bataji shigowanshi ba ganinshi yasa ahankali tace “good morning Ya Aliyu” binta yayi da kallo ahankali yace “morning wife, why did you cook”? Murya chan kasa tace “hakanan nagaji da zama ban fara girki ba, zokaci” dan jim yayi batare dayazo wajen ba dan baiso yaje he’s so horny wlh, ahankali tace “please Husby” dan kallonta yayi jin sunan dayakirata dashi, kashemai idanu daya tayi tace “come” ahankali yataho yana tafiya dai dai tana binshi da kallo kaman taje ta rungumeshi yazo wajen kujera tajamai tun kafin yakaraso hakan yasa yazauna ahankali yanabin kulolin dayagani kan dinning din da kallo yace “tun karfe nawa kika fara girkin nan”? Ahankali tace “ina idarda sallan asuba, lemme serve you” tai maganan tana bubbude kulolin dasauri, tundaga kan yatsanta yakebi da kallo da gashin dakenan afatar hannunta akwance tsabagen hutu, zuwa yanda dogon rigan yabi jikin dam zuwa kirjinta dayake hangosu daga inda yake zaune sabida yanda tai bending tana debamai abinci, rawa kafafunshi suka fara gabanshi nawani irin tashi zuciyanshi na tafarfasa all at the same time mikewa tsaye yayi kaman an tsikareshi dasauri takalleshi tajuya tacigaba da zubamai abincin datakeyi tace “mekakeso”? Ganin yanda ya tashi, ahankali taji saukan hannunshi kan nata dawani irin sauri tajuyo da fuskanta ta kalleshi.




Gani tayi idanunshi sunyi jaaaa sosai, ahankali yakarbe spoon da plate datake zuba abincin akai ya ijiye ya maida hannunshi kasanta batare dayay attempting cire mata rigaba cikin wata irin murya dake nuna fushi yace “ba breakfast nake bukata ba, what I want is hakki na awajen matata, I am tired of looking at you kullum ina hadiye miyau saikace wani gauro” kiiii! Ummulkhairy taji yawani barka mata pant dayasa taji jikinta narawa gabanta nafaduwa wani irin tsoron Aliyu take idan taga yay fushi barinma idan idanuwanshi sukaija dinnan, jallabiyanshi yadaga sama yana rikeda ita gam yawanija boxershi kasa dasauri tarufe idanunta ganin yanda joystick dinshi harwani nishi yake tsabagen yanda yamike, jin ya dagamata dogon Riga sama yasa jikinta yakara zabura yana bari sama da da, jin yawani tura joystick dinshi da duka karfinshi batare dayama bita ahankali ba kaman rana na biyun nan dasukai akan kujera ba yasa takai hannunta tana rirrikemai baya cikeda bala’in tsoro, wani irin mugun shiga Aliyu yamata dasaida yasa ta kwala ihu da babu abinda zai hana maigadinsu ji dan she’s extremely tight koyaya Aliyu yay making attempt na shiga azaban datakeji yawuce misali, kankameshi tayi tace “Ya Aliyu dan Allah kabari” wani kalan nishi yature abinci da kulolin dake kan table din yawani dagata batare daya rabasu ba yadaurata kan dinning din da gangan yazare kanshi waje sanan mercilessly yawani koma ciki da mugun gudu yanaji kaman zai haukace yace “zaki kara”? Wani irin girgizamai kai tayi tanaji kaman zata mutu tace “uhnn’uhn” sake fizge joystick din yayi yafito waje da karfi sanan kaman zai barkata yakoma ciki da makirin gudu yana ihu dazakasan na dadi ne. “Zaki kara”? Kankameshi tayi tana kokarin dura kasa taji abinda yafi karfinta tace “wlh a’a dan Allah kayakuri” wani murmushi yayi yawani fizgoshi waje sanan yakoma baya yana cire jallabiyan danta dameshi yana kallon yanda take kuka ahankali takasa hade kafanta gadan tiny hole din harja yayi yaji wuya kuma yau yay alkawari saiya bata wuya, dole tadawo jaruma Wanan rakin banzan tadena, yarda jallabiyan yayi da wandon duka anan kasa sanan yakaraso inda take kan dinning yasa hannu yajawota batare daya dauketa ba sanan yajata zuwa tsakiyan falo tana tafiya da kyar tana bubbude kafa suna kaiwa tsakiyan falon ya bude kujeran yajefata kai zata tashi zaune yafado kanta yace “who told you I am done with you, all ranakun nan zan rama su yau” baki tabude zatai magana dasauri yace “yimin shiru” hadiye kukan tayi kafafunta yakama yadagasu zuwa saitin goshinta sanan yahau kanta yatura joystick dinshi cikin yafara knacking her brains out ihuuuu Ummulkhairy tafara dan wani kalan makirin dadi dazafi takeji kaman zai fasata kaman zai shiga cikin cikinta, ita tadauka tana sume ne Aliyu baitaba mata abinda yamata yauba he delt with her sai wajajen 10 yabarta shima dan yasan zasuyi bakine da 24hrs yamata batare daya dagata ba yasauka dagakan kujeran yanajin wani sabon energy da farin ciki nothing beats sex in life yace “your brothers are coming jeki shirya” yay maganan yawuce dinning kayanshi ya dauka yawuce sama yana kallonta ta gefen idanu yanda take sauke ijiyan zuciya tai lagwab kaman lagwani.





Takai kusan 20min takasa motsi sanan ahankali ta tashi zaune da kyar kafin tamike tsaye ahankali tajuyo tana kalllon yanda suka bata kujeran, turobaki tayi ahankali murya chan kasa tace “Ya Aliyu Yamin mugunta kuma zan rama” store tawuce tadauko sabon tissue da ruwa awani bowl tazo ta gyara kujeran tsaf sanan tamaida komi yanda yakamata kafin ahankali tawuce sama tana tafiya ahankali, dakinta tashige tai wanka lafiyayye da ruwan zafi sanan tafito shiryawa tayi cikin wani nude abaya mai kyau bata daura dan kwali ba tabar gashinta ahaka sabida yakarasa bushewa sanan tasauko kasa tunkafin takai dinning taganshi zaune yasa wasu simple kaya na zaman gida farin riga da 3quater na polisawa yanacin sandwish datayi ga cup na shayi agabanshi, daukekai tayi tawuceshi tadauki plate tabude warmer da chips keciki tadeba da egg tadauki cup tazuba shayi duk yana kallonta sanan tahada a tray tadauka zata wuce tashi yayi sanan yasa hannunshi ahankali yakarbi tray ya ijiye kan table yawani jawota jikinshi yace “mekike shareni fushi kike dani dan nai breakfast dake anjima fa zanyi lunch sanan inyi dinner in the night” fashewa da kukan shagwaba tayi tana makemai kafada dasauri yay dan dariya yace “Okk sorry wasa nake, zauna kici abinci kusada ni to” yay maganan yanajan kujeran kusada ita, ahankali tazauna shima yazauna yadauki fork yadebi Irish din yakai bakinta, ahankali takecin abincin harta cinye sanan suka tashi tare suka wuce kitchen wanke plate din yashigayi itakuma tahau dauramusu kayan abinci bai iya komi kan harkan kitchen ba ko plate din saida takara wankewa, banda bare bari da dauko abu da mikamata babu abinda yakeyi saikuma chan ya rungumeta yay kissing nata yadauketa everything, ita mamaki takema why does Aliyu loves her this much kaman basune sukai fada dazun nan ba love lives here.


Wuraren 1 tagama komi suka jera a dinning yawuce mosque itakuma tawuce sama dantai wanka tai salla.

Tana cikin shiryawa taji ana bude gate wani murmushi tayi jikinta har rawa yake takarasa shiryawa cikin wani Riga da skirt na atampa red daya amsheta takafa dauri.



VIPs we are almost roundRing up




7️⃣9️⃣






Kallon kanta tayi amadubi tayi kyau bana wasa ba Amarya sak, jan baki tadauka red tasaka daya karama fuskanta kyau kaman yaune ranan bikinta sanan ta feffesa turare taijiye sanan tajuyo tafito tana murmushi jin hayaniyan su afalo, ahankali tashiga saukowa daga stairs tana tafiya ahankali falonta cike makil dasu, dan Baffa ya tattara su gabaki daya yace suje su dubo kanwarsu Ya Hafiz, Su Ya Hassan, Ya Manaf, Mu’az Maheer, da matayensu dakuma Batool dake kallonta tana murmushi cikeda don Khairy ganin yanda takara kyau, tana saukowa hannunta tasa ta ture kan Batool tareda turo baki irin kallonfa, sanan tawuce wajen Anty Asiya matan Ya Hafiz datafi saninsu wani irin fadawa jikinta tayi tanajan gyalenta tana rufe fuskanta tace “Anty ni kunya nakeji wlh gasu matan Bros” fizge gyalenta Anty Asiya tayi tace “dalla tashi ki gaisa dasu ga Aysha matan yayan ku Zayn” ahankali Ummulkhairy takalleta kaman yanda Aysha itama ke kallon Ummulkhairy da aka kusa bikinta da mijinta yarinyar kan akwai kyau ga diri, gatanan so adorable she don’t even know how to explain it, hannu Khairy tamata waving tace “sannu da zuwa ina yini, ina Ya Zayn” dan murmushi Ayshu tayi tace “gashinan” inda Ayshu tamata pointing takalla Ya Zayn na zaune kan one sitter yana danna waya kaman bashi adakin, dauke kanta tayi dasauri ganin Aliyu zaune kusada kujeran dayake kai yana kallonta, ahankali tace “Ya Zayn sannu da zuwa ina yini” anatse batare daya kalleta ba yace “how are you Ummulkhairy”? Ahankali tace “fine, sanan takalli sauran matan su Ya Manaf ta gaidasu” kafin ta tashi taje wajensu Ya Manaf babu kunya kaman Yar yarinya ashagwabe tafada jikin Ya Manaf tana kankameshi tana tattaka Mu’az da Maheer tana murmushi, cikeda masifa Maheer yace “Ya Manaf kaga tana takani ko” dariya akai afalon, gwalo tamai tace “Ya kufadamai yanzu na girmeshi nai aure ko” yunkurowa yayi kaman zai daketa tai ihu tana kankame Ya Manaf, duka dakin akahau dariya banda Zayn dake abinda yakawo yake dawaya ko kadan baiso yazo ba tursasashi Baffa yayi, shida Aliyu basa fada ko yima juna wani kallo and at the same time shida Aliyu are not friends and don’t think they can ever be.

Aliyu na zaune inda yake yana kallonta yanda take wasa da yayyinta he could see love and care tareda dukkansu, she’s so happy, dan murmushi yayi yasauke ijiyan zuciya baiso yadameta gashi ko ruwa basu bama bakinsu ba hakan yasa yatashi yawuce yay hanyar dinning, tureta Manaf yayi batare dakowa yaji maganan suba yace “is this how u make mijinki work for you agaban guest naki Ummulkhairy”? Yay maganan yana kallon hanyar kitchen dayaga Aliyu yashiga ciki, girgixamai kai tayi dasauri sanan ahankali ta tashi tawuce kitchen itama, tana shiga daidai yagama saka bottle water a wani fine tray, murmushi tayi tai wajenshi dasauri ahankali tace “sorry Ya Aliyu” dan juyowa yayi yakalleta kaman mai nazarin abu, maida marfin fridge din yayi yarufe sanan ahankali yadaura tray din kan saman fridge din kafin yakai hannunshi kan waist dinta yawani jawota dab dashi yana kallon fuskanta, faduwa gabanta yashigayi tana kallonshi da idanunta dasukai zuruu, hannunshi yakai yakama habanta yana kallon lips dinta yace “wayace kisa Jan baki wasu maza nagani” rawa lips dinta yafara zatai magana yahada bakinshi da nata yashiga kissing nata saida ya shanye janbakin tass sanan yasaketa ahankali muryanshi haryadan shake yace “jeki dauko babban mayafi” gyadamai kai tayi batare datai musu ba tawuce tafita daga kitchen din tai sama mayafi tadauko tayafa sanan ta sauko a kitchen din tasameshi yakama zuba drinks da ruwa a 2 different manyan trays, tare suka dauko suka fito falon dashi suka kawo suka ijiye, sanan suka koma dinning kulolin abincin datayi suka kawo nan falon da plates sanan aka zazzauna aka faracin abinci ana hira akasa tana zaune kusada Ya Aliyu da dakanshi ya zubamata abinci, he’s so caring and possessive of her dakowa dake falon yalura da hakan.


Saida suka gamacin abincin tahada all the plates zata daukan Aliyu yace “is too heavy Pickle, go with the cans” yay maganan yana kwasan plates din falon yay tsit, itakuma tadauki gorunan abubuwan shan tadaura a tray tawuce dasu kitchen, tare itadashi sukai clearing wajen Manaf sai murmushi yake dan yasan ko’ina Mama take this is what she wanted for Khairy namiji dazai sota yakuma kula da ita tasami hakan awurin Aliyu, fita mazan sukayi zuwa mosque yin asir hakan yasa ta kwashe matan sukai sama zuwa dakinta dansuyi alwala, Anty Asiya yakama hannunta zuwa wani daki daban tashiga da ita tareda kulle kofa hakan yasa tace “zauna Ummulkhairy” zama Khairy tayi ahankali tana kallonta, Anty Asiya tace “how are you” murmushi tayi tace “fine” murmushi itama tayi tace “Ummulkhairy I am happy for you Allah yabaki miji mai sonki, lura dake dakuma kulada ke haka kigodema Allah” dan murmushi tayi akunyace, Anty Asiya dake kallonta tace “Ummulkhairy mijinki nada jarababben kishi and he’s so possessive of you kinga yanda yake kallonki dakina wasa da Maheer kuwa” ahankali tace “haka yake Anty Asiya” anatse Anty Asiya tace “kidena bari yana correcting naki on certain things, koyaya kukai baki kidena fitowa haka babu mayafi kinji, please Khairy take care of your marriage life kinji” Gyadamata kai tayi ahankali jin kukan little dake wajen Batool yasa tace “ohh Noo tafara, Khairy pls tafasamin ruwa kadan nahada mata madara, bantaho da ruwan zafi ba” dasauri Khairy ta tashi tace “tom” itama Anty Asiya ta tashi tafito tashiga dakin Khairy da Batool da baby keciki, itakuma Khairy tawuce kasa zuwa kitchen babu kowa afalon dudda an idar da  salla a masallaci basu shigo ba.



Tana shiga kitchen maida kofa tayi tarufe sanan tayaye katon mayafin nan ta ijiye kan stool tawuce gaban  gas ta kunna tasaka ruwa mai kyau  1 cup tana tsaye awajen saida yatafasa sanan takashe gas din tadauko wani cup mai kyau tajuye ruwan sanan tadauko tray tadaura ruwan akai ta ijiye tadauki katon mayafin tayafa tana tura baki dan mayafin haushi suke bata sun cika girma kaman na iyaye tsofaffi sanan tadauki tray tabude kofan kitchen tafito, hada idanu tayi da Ya Zayn dake zaune shikadai afalon yanashan juice acikin wani glass cup kallo daya yamata yadauke kai hakan yasa ahankali tafara tafiya gefen gyalenta najan kasa tawuce staircase tafara hawa da sauri sauri jin kukan Little na karuwa taka gyalenta tayi da slippers na kafanta hakan yasa santsin gyalen dana tiles na staircase din suka wani jata tai baya zata fadi ruwan hannunta na shaking zai kwaro mata aka ihu tasaki. “Wayy……” chak taji anwani irin fizgota an kabar da ruwan zafin hannunta batasan lokacin daya kankame koma waye yafizgota ba daidai anshigo falon jin ihunta su Batool suma sun fiffito daga dakinta asaRma.


8️⃣0️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Ahankali take bude idanunta jin ana tureta hada idanu tayi da Zayn daya fizgota, wani irin ijiyan zuciya tasauke tana fita daga jikinshi ahankali tanabi tray da kofi da ruwan zafin dake tiriri anan kasan tiles din idanunta ne suka sauka kan hannun rigan Ya Zayn dataga yajike that means ruwan zafin yasauka kan hannunshi daidai yajuya zai wuce karaf tarike hannunshi batare data kalli fuskanshi ba tace “Ya Zayn ka kone” tai maganan tana kokarin jan hannun rigan sama ta kalli fatan wajen cikeda damuwa kaman zatai kuka, dawani irin sauri ya fizge hannunshi daga nata yawuce yace “I am fine” binshi tayi dasauri tace “Ya Zayn ka kon…..” shiru tayi sabida hada idanu datayi da Ya Aliyu dake tsaye gaban dakin tareda yayyinta da duk suka shigo tare, car key Zayn yadauka dasauri yazo gaban dakin batare daya kalli kowa ba yace “let’s go” sanan yafice, dan murmushi Manaf yayi yakalli su Batool dake stairs yace “kumutafi yamma tayi” sanan yakalli Aliyu dake kallonshi idanunshi harsun dan chanza launi yace “bari muje bro zamuyi magana awaya” gyadamai kai Aliyu yayi sukai musabaha sanan suka fito dukansu atare har zuwa waje inda Zayn yake tsaye ahankali Aliyu yace “how’s your hand?” Gyadamai kai Zayn yayi yace “is nothing serious thanks” daidai lokacin matan suka fito tareda Ummulkhairy dake yake sanan duk akai sallama suka shiga mota gateman yabude musu gate suka wuce gateman yamaida gate yarufe, ahankali Ummulkhairy gabanta har faduwa yake tajuyo ahankali takalli Aliyu da idanunshi suka chanza launi zatai magana yawuce fuuuu kaman zaki yay ciki, faduwa gabanta yashigayi sosai, ko Allah yasan cewa wanan fushi da zuciyan Ya Aliyun tsoronshi da fargabanshi take yanzu ita yaya zatayi dashi.



Ahankali tawuce ciki itama, gaban stairs din tayi ta tsugunna ahankali tadauki tray da cup din sanan tawuce kitchen ta ijiye sanan tadauko rag tadawo ta idasa goge wajen sanan tawuce ta ijiye komi a kitchen din sanan tafito zama tayi afalon faduwa gabanta yake banawasa ba, tashi tayi tsabagen tama rasa mezatayi burner ta kunna tazuba turare akai sanan takara dawowa tazauna ahabkali kan kujera tai shiru tana tunani, tsoron ta tunkareshi takeji yanda yake cikin fushin nan and at the Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️

same time mijinta ne yanzu bataso bai kamata tabarshi yana fushi ba, banda haka tasan halinshi tsaf ta aureshi so is high time takoyi facing problem nata bawai tsoronsu ba menene tasandai duk haukan fushin dayakeyi Aliyu will never raise hand on her.

Ahankali ta tashi daga kan kujeran sanan tawuce sama, gaban dakinshi taje ta tsaya kirjinta na bugawa dum dum dum, da kyar tadaga hannunta dake rawa tai knocking kofan lips dinta na rawa sosai ahankali tace “Y……Ya…Ali…..yu” jin shiru bai amsata ba yasa ahankali tabude kofan dakin, babu kowa acikin dakin hakan yasa dasauri tashiga cikin dakin ganin kofan bayinshi abude yasa takalli bayin ganinshi tayi gaban wash hand basin yabude tap din wajen yatara kanshi ruwa na zuba cikin gashinshi yanabin fuskanshi da wuyanshi kana ganinshi kasan matsiyacin kishi kecinshi kaman zai mutu, ahankali tacire babban mayafin tadaura akan gadonshi sanan gently kaman kai kofan tafiya tai hanyar bayin ahankali tashiga ciki, gaban wash hand basin dinta tsaya sanan ahankali tana kallonshi takai hannunta takashe tap din sanan ahankali tace “Ya Aliyu” wani irin dago kanshi yayi yazubamata jajayen idanunshi da ruwan kanshi ke gangarowa suna sauka kan fuskanshi, wani irin ijiyan zuciya mai karfi tasauke tana kallonshi lips dinta yashiga rawa tana kallonshi kaman yanda yake kallonta tace “Ya Aliyu kayaku……” “how dare you touch a Man in my house!” yay maganan azuciye yana wani irin dukan kan tap din da  karfi dayasa kan yawani irin lankwashe take yanke hannunshi yahau fitar da jini yajima kanshi ciwo, dawani irin sauri Khairy tazare hannunta takai hannunta da sauri takama hannunshi tana kallon yanda jini kezuba tace “Innalillahi wa innailaihi raji’un! Ya Aliyu blood” hannunta takai jikinta narawa sosai ta fizge dan kwalin kanta takai zata dauremai hannun da jini kefitowa sosai yawani irin fizge hannunshi saida tai baya kaman zata fadi tadafa bango dasauri yafito daga bayin azuciye hannunshi na diddiga da jini yazauna akan gado yadaura hannayenshi biyu asaman kan fuskanshi yana wani irin huci jinin jikinshi na tafarfasa yakasa daina ganin yanda Ummulkhairy tafado jikinshi yanda ta kankameshi dakuma yanda tawani kamo hannunshi tana kokarin duba hannun kaman zai haukace yakeji bama yajin yanda hannunshi ke azaban zafi.



Daga bayin Khairy tajuyo tana kallonshi hannunta tadaura kan bakinta tana taushe kukan dayake zuwan mata tana kallon Ya Aliyu cikeda so dakuma tausayi, duk wanda yace kishi is not real baiga Aliyun ta bane, Aliyu is suffering shi kanshi baisan yaya zaiyi da kanshi ba, Innalillahi what did she just do, ya akayi ta manta waye mijinta har taje tana rirrike Ya Zayn, look at Ya Aliyu yanzu jini yanda yajima kanshi ciwo, jibi yanda yakeyi kaman sai zare, ahankali tafito daga bayin zuwa inda yake, ahankali ta tsugunna agaban gadon tana kallon hannunshi da jinin kafita har gefen fuskanshi yakebi cikeda damuwa tace “Ya Aliyu dan Allah dan Allah kabari lemme treat you, your hand is bleeding, kaji” takai hannunta ahankali zata kama hannunshi wani irin hankadeta saida bayanta yabugu da drawer taidan malalacin kara sanan ta taso da kyar tadawo tace “kome zakayi kayi but bazan taba ganin ciwo ajikinka nabarshi ba” tasake kama hannunshi zata goge da dankwalinta, wani irin dagata yayi yamike tsaye yabugata da bango tawani irin matseta jijiyoyin gaban kanshi suna bullowa yace “do you still love that man haaa, answer me, do you have feelings for Zayn!” Yadaka mata wani kalan tsawa da saida ta taushe kunnentRa dan dodon kunnenta saida ya amsa.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




8️⃣1️⃣

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️






Fizgota yayi daga bangon ta hanyar kama gaban riganta idanunshi sunyi bala’in jajir yana kallonta sun cikada hawaye yace “how dare you touch him eh?? Wayace kitaba wani namiji bayan ni, are you sick upstairs Ummulkhairy, do you still wish dashi kika aura bani ba eh? Are you still in love with him” yanda yashaketa zaka dauka kasheta zaiyi, Ya Aliyu nabata tausayi he’s not okay, zuciyanshi akwai device aciki dake taimakonshi and just look at the stress dayake saka kanshi ciki now, hawaye yazo mata dasauri tashare dan she needs to be strong no more baby stuff, hannunta tadaura kan nashi daya shake gaban riganta dashi tana kallonshi itama da idanunta dasukai ja ahankali da muryanta dabaya fita sosai tace “Ya Aliyu dan Allah calm down kaji! Kaga ur heart is extremely beating fast, Ya Aliyu kainake so kuma kai kadai bazan taba son wani ba sama dakai, Ya Aliyu kaga wanan gyalen nataka na turgude zan fadi nadaukoma Anty Asiya hot water zaama little milk, wlh I thought kaine karikeni danasan bakai bane da na gwammace ruwan zafin yakonani, hannunshi kuma I was trying to see koyakone ne I wasn’t thinking straight, I am so sorry Ya Aliyu na, no emotions attach banason Ya Zayn, he’s my brother he will always be that kai kadai nakeso believe me” wani kalan ihu yayi yasaketa yana dukan bedside lamp da hannunshi yace “u are lying!” Tarrrrr karan fashewan bedside lamp kakeji daya daka yafashe, kankame kanta Khairy tayi danji takeyi kaman zai rufe ta da duka. “Stop lying to me” Aliyu yasake ihu yana buga wani cute table da desktop dinshi kekai daga table din da desktop din duka suka  zube kara kawai kakeji, sanan yajuyo yakalleta idanunshi kaman jini yazuba acikinsu sabida yanda sukai jajir yanuna kanshi ahaukace yace “Ummulkhair ke mata tace ni kadai! I own you ni kadai, jikina kadai ne aduniya ya halattan miki, idan kika kara kallon wani kokika kara taba wani I will kill har lahira kina jina!” Yadaka mata tsawa da sauri ta gyadamai kai tana hadiye kukan datakeji tana kallon yanda dayan hannunshi shima kejini yaji ciwo sabida dukan bedside lamp dayayi wani irin fizgota yayi yajijjigata yace “kinajina!” Gyadamai kai tayi jikinta har kyarma yake, kyaaaaaarrrr kawai taji ya barka rigan jikinta da duka fushi da zuciyan dayake yi kaman akan rigan yake huce haushin rigan yay kasa, wani irin hannu yasa ya barka gaban bra dinta, datse idanuwanta tayi dasauri wasu irin hawaye masu bala’in zafi suna sauko mata akan kunci, tanaji pant dinta ma ya yaga kawai karan yagewan kaya kakeji adakin kaman ana yankasu da almakashi sanan taji karan barka nashima, kafin taji yawani irin juyarda ita yahadata da bango sanan yataho yahada kirjinshi da bayanta, yanda taji kirjinshi nabugawa abayanta saida taji mugun kuka yazo mata, wani irin mugun shiga yamata dayasa tasaki kuka ahankali.

Ajiyan zuciya yasauke zuciyanshi na tafarfasa yana kara matseta abango yana ramming nata madly yace “you are mine! I own you Ummulkhair! You are no one else’s! Ke gonata ce babu wanda ya isa yaketamin, you are mine kinajina!” Yay maganan yana wani jawota daga bango zuwa tsakiyan dakin yadukar da ita tana share hawaye yashiga mata wani mad doggy dayasa taji kaman zai fito da duka hanjin cikinta ne, duk dauriyan dataso tayi takasa kuka tashigayi dan Aliyu was literally punishing her, har aka kira magrib yana abu daya yadauketa yajefata kan gado hawa kanta yayi yakwanta samanta yana kama nonon ta abaki yana bude kafafunta yana shiganta da kyau sanan yafara surutai. “I love you Ummulkhairy hakanan inaji kaman sonki zai zama ajalina I can’t control yanda nakeji, bayin kaina bane, I can’t even explain abinda nakeji idan image danagani dazu na flashing a eyes dina, ohhh my Gooddddd, ahhhhhhhhh, urrrrrrghhhhh” yawani riketa kaman zai ballata yaja nipple dinta abakinshi kaman zai cire sanan yakawo, gam ganin yariketa batare daya rabasu ba gently tanajin saukan hawayenshi akan kirjinta suna gangarawa har cikinta dayaji taji jikinta yay sanyi, yadade ahaka sanan yazare joystick dinshi yasauke jikinta yakoma side nata yana saka dayan boobs din cikin bakinshi yana sauke wani irin ijiyan zuciya na kuka saikuma taji yadaura hannunshi kanta ya rirriketa jikinshi na saki bugun zuciyanshi nadawowa normal normal sanan ahankali taji yasauke ijiyan zuciya bacci yay awon gaba dashi ahaka.Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Takai kusan 10min ahaka sanan gently tabude idanunta tadaurashi akansu, har lokacin jijiyan kanshi bai gama komawa ba, hannunshi dake kan jikinta tabi da kallo yanda yaji ciwo jitayi zuciyanta became so weak, ahankali tazare boobs nata daga bakinshi sanan ta tashi zaune ahankali, sauka tayi daga gadon tana bin dakin da kallo sanan da kyar tamike tsaye tana share hawayen dayasake zubomata tawuce bayi tana tafiya da kyar da kyar in baiji mata ciwo ba ayanda takejin zafin nan, towel dinshi taja tadaura sanan tabude drawer bayin tadauko first aid box tafito still tana tafiya ahankali tazo gaban gadon, bargo taja ta lullube shi sanan tazauna ahankali takama hannunshi taciro audiga tashiga sharemai hawaye na gangaro mata sanan tasaka bandeji akai, tama dayan hannun ma haka sanan ahankali takalli fuskanshi tadade tana kallonshi sanan ta tashi bayi takoma ta ijiye kit din sanan tafito tawuce dakinta bayi tashige direct ta tsugunna tana kunnama kanta shower tahau kuka sosai mugun son da Aliyu kemata karyaje yahalaka kanshi! How is she going to face this only problem datake dashi agidan miji? Mata da mazajensu keda kishi da zuciya irin na Aliyu yaya suka zauna dasu? Aliyu yajima kanshi ciwo sabida she just try to check on Ya Zayn, look at abinda yamata just because of that.


Da kyar ta iya tagasa kanta sanan tai wankan tsarki tafito tasaka wani simple gown da hijabi tai magrib da isha’i anan kan dadduma bacci yay awon gaba da ita.




Tayaya ake zama da miji mai zuciya, fushi da bakin kishi irin na Aliyu Mumies????



VIPs nagama this book ko mu 


budada rayuwan Auren nan? Let’s see how Ummulkhairy will fight for her marRriage???



Muyi part 2???


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️





8️⃣2️⃣



Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️



Ahankali take bude idanuwanta jin zafi datakeji ajikinta, Aliyu tagani ya kankameta akan gadonta yana bacci dagashi sai singlet fari kal da gajeren wando ya lullube su da bargo, agogon bangon dakin ta kalla ganin karfe bakwai gently tazare jikinta daga nashi zata wuce bayi tajuyo takara kallonshi komawa gaban gadon tayi sanan ahankali taja bargo ta lullube shi sanan tajuya tawuce bayi, brush tayi tadauro alwala tazo tai salla tana idarwa takoma bayi tai wanka bataso ta tadashi hakan yasa tabude wardrobe tadebi kayan dazata saka sanan tafito afalo ta sanya jean da Riga na english wears ta gyara gashinta ta taje tai parking atsakiyan yana lilo tasaka dan kunne sanan tafeffesa turarukanta ta kwashi komi takoma dakin ta maida ta ijiye sanan tafito, kitchen tawuce tafara kokarin hada musu breakfast Wanan dataji jikinshi na zafi tasan zazzabi ne yakamashi tsabagen masifan fitinan dayayi jiya, smoothies ta hadamai na fruits tasaka a fridge sanan tashiga hada lafiyayyen girki, sinasir tayi da farfesu tana aikin ne komi daya faru jiya yana dawomata abin Ya bala’in damunta batasan wanda zata fadamawa ba batason koda wasa yan gidansu susan abinda yafaru, bamataso susan bakin mahaukacin kishin Ya Aliyu but at the same time bama tasan yanda zatayi ba all she knows is tanason mijinta so sosai ma bana wasa ba.

“Pickle!” Taji ankirata da karfi dayasa firgigit tafarka daga dogon tunanin data tafi daidai Aliyu ya matsar da ita daga gaban fas da sinasir wanda yake shine last one din datake toyawa yakone sosai.


Sauke pan din yayi daga wuta dasauri ya ijiye a sink sanan yajuyo yazo gabanta dasauri yakama hannunta yana dubawa kota kone cikeda damuwa yace “are you okay”? Kallon kwayan idanunshi tayi kafin ahankali ta karbe hannunta daga nashi tace “I am, thanks, ina kwana” tai maganan tana wucewa wajen warmer datake zuba sinasir din tasa marfin tarufe tadauka dasauri yazo gabanta hannunshi yasa ahankali ya karbe kulan yace “lemme help u” batacemai komiba tawuce wajen fridge tabude tadauki smoothie dinshi duk yana binta da kallo tawuceshi tafice daga kitchen din, ijiye smoothie tayi kan dinning batare daya kalleshi ba tanuna smoothie da hannu ahankali tace “I made smoothie for you it will help with temperature dakake running, nama sinasir da pepper soup, have your breakfast after kagama kaje hospital” yanda take maganan wani irin sanyi yaji jikinshi yayi banawasa ba, juyawa tayi dasauri zata wuce chak taji anrike mata hannu hakan yasa ta tsaya batare daya wuceba ta lumshe idanunta jin hawaye na zuwan mata, ahankali yasauke kulan sunasir din da hannu daya sanan yataho inda take tsaye jikinshi yay mugun sanyi ahankali yahada kirjinshi da bayanta Awani irin hankali ya rungumeta yana daura kanshi akan wuyanta sanan yadaura hannayenshi akan cikinta, lumshe idanu tasakeyi ahankali jin yanda jikinshi yay zafi kafin ahankali tabudesu, cikin wata Yar murya kaman nadan yaro ahankali yace “are you angry with me”? Shiru tayi batare datacemai komiba, murya chan kasa yace “ki hukunta ni Pickle but my heart can not take this silent treatment please” shiru tasakeyi batacemai kala ba.



Cikin wata kalan raunanniyan murya yace “I am sorry Baby, I am sorry about everything bazan karaba, please forgive me kinji Ummulkhair, forgive Aliyun ki” wani irin juyowa tayi takalleshi ido cikin idanu sanan takama hannayenshi duka biyun da bandeji kekai tanunamai su tace “did you say I should forgive you bayan kajima kanka ciwo haaaa”? Dan lunshe idanu yayi yabude su yadaura kan idanunta da all he sees is irin fushin datakeyi dashi, cikin fushi sosai tanuna kanta tace “Ya Aliyu is mee, mee Ummulkhairy ka, what made you think zan taba so wani sama da kai eh? Why will you think of that” sake lumshe idanu yayi sanan yabude su ahankali, cikin fushi sosai tace “I am human aren’t I? And I am bound to make mistakes and to feel pity, koba komi Ya Zayn is my brother idan naganshi injured I should attend to me, Ya Aliyu why will you be thinking so negative eh, why? Kanaso ka kashe kanka ne kana jima kanka ciwo u were bleeding so bad inda jinin ka yakare fa, kazaci I can leave without you ne?” Hawayen daya zubomata tashare dasauri sanan tasake kallonshi cikin idanu sosai tace “no I will not forgive u, just eat ur breakfast and leave for hospital” tai maganan tawuce fuuuuu sama yadade tsaye awajen yana binta da kallo yadade tsaye awajen sanan yadawo dinning ahankali wani babban tray yadauka ya ijiye sanan yazuba musu iya abincin dayasan zasu iya cinyewa yahada komi kan tray din sanan yadauka yawuce sama yana tafiya ahankali sabida kanshi kaman zai faZdi.

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




8️⃣3️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️




Kofan dakinta yabude ahankali tana zaune kan gado tana linke wasu kaya ganinshi yasa tadauke kai tamike tsaye ta kwashe kayan daya gama linkewa sanan tawuce wardrobe tabude tana saka kayan ciki ahankali ya ijiye tray akan side drawer sanan yataho inda take gaban wardrobe gently yakai guiwowinshi duka biyun kasa, maida kofan wardrobe din tayi tarufe tajuyo chak ta tsaya ganinshi kneeling agabanta ahankali yakai hannayenshi duka biyun yahada yana kallonta murya chan kasa yace “I am sorry Ummulkhair, I am so sorry baby” wani irin kallonshi take sai kawai tajuya zata fice daga dakin ya chapke hannunta, cikin fushi kaman abinda take jira kenan tace “sakenmini hannu Ya Aliyu, and stop kneeling kana cemin sorry, ur sorry won’t change anything, kanka zakacema sorry tunda kaine mai matsalan not me, Ya Aliyu!” Tai maganan tana juyowa ta kalleshi right in the eye sanan asanyaye tace “Ya Aliyu we just got married but look at problem damuke facing, I don’t know why but sainakeji kaman wanan fushin da mugun kishin naka zaisa auren mu bazaikai ko’i…………” wani irin mikewa tsaye yayi yakai hannunshi yadaura kan bakinta jikinshi nawani irin bari yana girgiza mata kai idanunshi nacika da kwalla sosai, all she could see a udanunshi was fear na abinda zata fadi, hawaye ne masu dumi taga sun gangaromai ahankali cikeda bala’in tsoro yace “what happened yesterday will never happen again I promise, Ummulkhairy I can’t live without you, dan Allah karki tsaneni koki barni kinji, dan Allah, please baby help me kinji” yanda yay maganan saida taji har cikin ranta yabata tausayi, hawaye ne suka gangaromata dasauri tajuyar da kanta zata goge da dayan hannunta dabai rikeba gently taji yarike hannunta hakan yasa takalleshi, ahankali yatako zuwa gabanta sanan yasauke hannayenta biyun kasa kafin ahankali yakai duka hannayenshi yakama habanta yana kallon fuskanta dawani irin shaukin so kafin ahankali yasa tongue dinshi yashiga lashe hawayen dake zubomata sanan ahankali yadaura goshin shi kan nata hancinshi na gogan nata murya chan kasa yace “I am sorry Pickle, I will never hurt you again, I will never, namiki alkawari kinji” gyadamai kai tayi ahankali sanan gently yadaura bakinshi kan lips dinta ahankali yabude bakinta yashiga kissing nata tana maidamai martani sanan yawani irin daukanta yayi gado da ita, abincin daya kawomusu a tray yadauka ya ijiye akasa sanan sukahau gadon yana ciremata wani kalan sweet makeup sex sukai having kaman basuba yabata hakuri yafi sau dari wajajen 11 yabarta wani kalan lafiyayyen bacci tayi ajikinshi.


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️


Ahankali yay kissing forehead nata yana gyara gashinta daya hargitsa, yanason Khairy tana sonshi but yarasa maisa masifaffen kishin shi ke neman ruguzasu, baisan mesa ba he couldn’t help it dayaganta da Zayn, Allah ya yayemai wanan kishin da zafin zuciya, murmushi yayi yasake manna mata kiss yanaji duk wani zazzabi dayakeji na tafiya.



Bayan 3 months.




Kofan dakinta yabude ahankali tana zaune kan gado tana linke wasu kaya ganinshi yasa tadauke kai tamike tsaye ta kwashe kayan daya gama linkewa sanan tawuce wardrobe tabude tana saka kayan ciki ahankali ya ijiye tray akan side drawer sanan yataho inda take gaban wardrobe gently yakai guiwowinshi duka biyun kasa, maida kofan wardrobe din tayi tarufe tajuyo chak ta tsaya ganinshi kneeling agabanta ahankali yakai hannayenshi duka biyun yahada yana kallonta murya chan kasa yace “I am sorry Ummulkhair, I am so sorry baby” wani irin kallonshi take sai kawai tajuya zata fice daga dakin ya chapke hannunta, cikin fushi kaman abinda take jira kenan tace “sakenmini hannu Ya Aliyu, and stop kneeling kana cemin sorry, ur sorry won’t change anything, kanka zakacema sorry tunda kaine mai matsalan not me, Ya Aliyu!” Tai maganan tana juyowa ta kalleshi right in the eye sanan asanyaye tace “Ya Aliyu we just got married but look at problem damuke facing, I don’t know why but sainakeji kaman wanan fushin da mugun kishin naka zaisa auren mu bazaikai ko’i…………” wani irin mikewa tsaye yayi yakai hannunshi yadaura kan bakinta jikinshi nawani irin bari yana girgiza mata kai idanunshi nacika da kwalla sosai, all she could see a udanunshi was fear na abinda zata fadi, hawaye ne masu dumi taga sun gangaromai ahankali cikeda bala’in tsoro yace “what happened yesterday will never happen again I promise, Ummulkhairy I can’t live without you, dan Allah karki tsaneni koki barni kinji, dan Allah, please baby help me kinji” yanda yay maganan saida taji har cikin ranta yabata tausayi, hawaye ne suka gangaromata dasauri tajuyar da kanta zata goge da dayan hannunta dabai rikeba gently taji yarike hannunta hakan yasa takalleshi, ahankali yatako zuwa gabanta sanan yasauke hannayenta biyun kasa kafin ahankali yakai duka hannayenshi yakama habanta yana kallon fuskanta dawani irin shaukin so kafin ahankali yasa tongue dinshi yashiga lashe hawayen dake zubomata sanan ahankali yadaura goshin shi kan nata hancinshi na gogan nata murya chan kasa yace “I am sorry Pickle, I will never hurt you again, I will never, namiki alkawari kinji” gyadamai kai tayi ahankali sanan gently yadaura bakinshi kan lips dinta ahankali yabude bakinta yashiga kissing nata tana maidamai martani sanan yawani irin daukanta yayi gado da ita, abincin daya kawomusu a tray yadauka ya ijiye akasa sanan sukahau gadon yana ciremata wani kalan sweet makeup sex sukai having kaman basuba yabata hakuri yafi sau dari wajajen 11 yabarta wani kalan lafiyayyen bacci tayi ajikinshi.




Ahankali yay kissing forehead nata yana gyara gashinta daya hargitsa, yanason Khairy tana sonshi but yarasa maisa masifaffen kishin shi ke neman ruguzasu, baisan mesa ba he couldn’t help it dayaganta da Zayn, Allah ya yayemai wanan kishin da zafin zuciya, murmushi yayi yasake manna mata kiss yanaji duk wani zazzabi dayakeji na tafiya.



Bayan 3 months.

Sosai take wani irin mugun laulayi, itada Aliyu batamasan wayafi wani laulayin ba, ko ciwon kai yaga tanayi kaman zai ihu yakeji, ita abinma mamaki yake bata yanda Aliyu ke sonta yana binta kaman jeka zaka dauka magani tamai, Aliyu extremely loves her, kishine matsalan shi saisa itama tadage da addu’a takuma kiyaye bata iyawa da wanan manyan mayafin hakan yasa  tasashi ya dinka mata manyan hijabi sutake sawa duk inda zata and she’s extremely happy, babu abinda yakai Auren soyaya she’s happy with aurenta da Aliyu, tanason mijinta shima yana sonta, suna building rayuwa na gaskiya dakuma girmamawa suna rainon dan cikinsu tare, once in a while yana kaita gidansu taje tawuni yadawo yadauketa dan yahanata tuki tunda tai ciki, kowa na family su yasan yanda Aliyu kesonta hakan kuma nama kowa dadi.



9month daidai tahaifi danta namiji mai kama da Baban shi a clinic dinsu Dad, daga Dad har Aliyun dawowa sukai kaman yara sabida murna, kafin kace me asibitin yashiga da Yan uwa harda su Zayn da matanshi Ayshu da itama kedauke da karamin ciki, mantawa da duk wani kishi Aliyu yayi yakawomai Baby, Zayn yama baby addu’a.

3days tayi a asibiti aka sallameta suka wuce gida bayan 7days yaro yaci suna Hilal.

Rayuwa kenan, ance inhar akwai soyayya koyaya wanda kikeso yake zaki iya zama dashi, Aliyu baida matsala kodaya sai zafin kishi da fushi and Ummulkhairy learn to live dashi like that, and they cherish each other har karshen rayuwa.


END!!!!



This novel is one novel dana raba kan fans dina akai, wasu nayin Aliyu wasu nayin Zayn!!!!

I promise you next novel dina will be epic, team Zayn I will make it up to you all.



Kuskuren danayi cikin Wanan novel din Allah ya yafemin.


M shakur loves you and thanks for supporting me❤️



Love concur everythingZ❤️

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461 

To chat me up on watsapp 


This novel is 1k

Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461

Thank u❤️

No comments

Powered by Blogger.