Yar Aikin Karuwai Book 2 page 6-10

 


🌼'YAR AIKIN KARUWAI 2🌼

              MATAFIYA



                  6-10




MASU AUDIO WANNAN BOOK NA SIYAR DA SHI,BAN AMINCE A JUYA MIN NOVEL BA IZINI BA.

MASU BUKATAR SAURARAR AUDIO DINSA DA MA WASU ZAFAFAN NOVELS DIN KU NEMI YOUTUBE CHANNEL

S ZARIA TV




Official 


By

AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA

ZAINAB USMAN




PAGE NAKI NE 

NAJIDA ALIYU BICCA





Ina masu bukatar unique kitchen utensils . fabrics adult and children's wears  shoe's and bag's.

Da masu bukatar ahada musu lefe ko masu bukatar iya luggage's din kawai  duk inkazo

R&U EXCLUSIVE KITCHEN AND MORE.

Zaku samu duk abinda kuke bukata ko a awanne state kake zaa kawo


   Masu bukata ga number. 0703 455 9202


https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx







          Cele tana kallo Ayusha ta Gama girke girkenta Basu zauna a dining ba saman carpet ta jera musu abincin suka zauna a kasa tare da tankwashe Kafafunsu,ba tare da saka cokali ba da hannu Ahsan ya fara ci Yana kallon Maheerah wacce ta shagwabe fuska,yayi juyin duniya taci ta ki ci sai lallashinta yake da kyar ta yarda ya fara bata a baki tana ci da kyar,magana yayiwa Cele da hannu tazo Wai itama ta ci,harara Maheerah ta watsa mata ta hau masifa harda kuka akan Kawai yace tazo taci tare da su,Kalar abincin nasu ma Rufaida baza ta iya ci ba da larabci Maheerah tace Masa sai dai taje ta dafa da kanta amma baza ta ci musu abinci ba,Ayusha ya kira tazo tayi Shirin tafiya gida ta gama musu aiki yace ta tafi da Cele, ga Rufaida ta Fadi abinda take so a dafa mata,da zancen kurame ya dinga gwadawa Cele har ta gane wai ta bi Ayusha kitchen suna shiga Ayusha ta dinga masifa da jaraba zata Zama baiwar bakar fata tana zuwa ta hankade Cele,Irin baza ta koyawa Cele girki ba bare tazo ta rabata da aikinta,Cele Ido ta zarowa Ayusha itama da Hausa tace ke jaka nifa na iya girkina ba abinda ban iya ba ki tambaya kiji,Cele ce ni a kaso karewar iya soye soye,ke in kin Isa ki soya awara na gani ko ki soya fanke,yanda kike kyamata Nima Haka nake kyamarki ta karasa tare da dukan kirjin Ayusha,da hannu tasa kirjinta ta hade dana Ayusha ta hankada ta baya saura kadan Ayusha ta Fadi ta dafe jikin bango tana masifa da yarenta itama larabcin ma ta daina,Itama Cele da Hausa tace kina  hauka ne ta daki kirji tace ke burar....kinci me cin....dan.....ashar ce kawai ke tashi,Ayusha taga Cele ta haukace Mata sai tsoro ta Fara ja da baya,Ahsan da Maheerah sunji yare na tashi ga na hausa ga na Yan bangaladesh kamar fada akeyi suka shigo ciki da sauri suka iske Cele taci kwalar Ayusha ta shaketa a bango tana ta fyalla Mata mari,tana kutuntuma ashar tace ai ba a ka'abah nake ba da Zan daga Miki kafa ko Kinga na saka harimi,Dan ubanki Niyyar Umrah ko aikin Hajji Kika ga na dauka ubanki zanci yo ko Umrah ban sauke ba bare na daga miki kafa,Ahsan yazo rabon fada Rufaida ta Masa Elbow a kirji ya ja baya tare da dafe kirjinsa Yana kiran sunan Allah,Ayusha Kuma taga anci uban oga ma Sai ta fara kuka, Maheerah tazo tana bala'i da larabci,Rufaida dai ta haukace ta juyo tana sani ta hankade Maheerah Allah sarki ba karfi sai ga Maheerah a kasa wanwar tana subhanallah, ya Allah,Ahsan har yanzu mulmula kirjinsa yake inda aka Masa Elbow,Ita Kuwa Maheerah daga Dan wannan abin abinka da larabawa sai kuka take tana Ya Allah,Ayusha da kyar ta kwaci kanta ta fice tana kuka itama yau Wai ta daku abin da bana kirki ba amma Wai ta daku har gida tana barka kuka,Cele ganin Ahsan tayi har yau a duke Wai zafi dariya ta dinga yi masa kafadarsa ta dan doka tace shege Ahsan,ya saki ihu, ta kyalkyale da dariya sabo da bai San me tace ba,ta sake cewa Dan duniya Dan duniya,zuwa tayi ta Kama Maheerah ta dagata tana kutuntuma Mata ashar a matsayin Wai hakuri take bata,tana karkade Mata jiki tana cewa sai kinci uwarki, Yar banza Fuska Kamar faten tsaki,baki duk tafarnuwa yan yan ysn.


    Sudai basu San me take cewa ba Suka fice daga kitchen har Ahsan zafi Wai dukan abincin ma fasa ci Suka Yi Suka gudu bedroom Suka datse da key,Rufaida ta Shiga kitchen ta rasa me zata ci Allah yasa taga Oat ta hada da Madara ta sha ta koshi,ga kayan ci da sha Nan iri iri a fridge snacks daban daban,gidan ko Ina a kulle babu yanda za ayi ka iya fita sai da ikon su kofar ma security ne da ita,Dole Rufaida ta zauna iya wayonta ta gwada abin yaki sai hakura tayi ta kwashi biscuits da lemo ta wuce bedroom itama bayan tayi Sallar Isha tayi Shirin bacci cikin sababbin kayan baccinta ta zauna tana cin biscuits dinta da lemo tana kallon film din larabawa duk da ba ji take ba haka take kallo.


     Tana Jin ihun Maheerah da Ahsan suna wasanni iri iri a Palo,kunne ta kasa, ai tashi Cele tayi ta Dan bude kofarta a hankali ta leka kanta palon taga suna ta jaki jaki Yana Mata jaki jaki Suka Gama suna ta kokawa iri iri kamar yara,Cele tace bari mu dauki darasi a nan ake aikata sunna,tana kallo daga Wasa aka Fara romancing sun manta tana gidan,Maheerah ta bude zip ta fito da Nono sutu sutu dake bata haihuwa ras dasu Kuma tana da kiba jajir da su abu manya,Cele baki ta rufe tace naga nononki Maheerah ba abinda zaki fada min kun ganshi a'a'a'a kaiiiiiii can me Zan gani haka nipples sai kace Kan dan Iska,wannan Abu akushi guda Kai Ahsan ka fiye hadama ya maka yawa Ina zaka da shi haka.


  Sake lekowa tayi taga ya lumshe Ido, tace to ai gashi nan Yama rufe Ido baya so ba dadi ai tunda naga hakoranta Zaki ya kashe su duk cin zuma to na shanun ma haka yake can wajen ma magudanar haka take ba komai itama cin zuma ya kamata,a hankali ta rufe kofar ta dawo ta Dan murda handle ai da gudu Maheerah ta Fara kokarin maida rigarta,Rufaida ta fito fit sabo da a San ta gani harda kwalla ihu ta ja da baya tare da dafe kirji tana cewa za a lalatani shike nan an lalatani,Maheerah da Ahsan ko kunya ta maida rigarta ko a jikinsu tana kallo ma suna ta tsotsar bakin juna,Cele ta kalle shi tace dan ubanka Kai kayi Mata kishiya baka San dadin komai ba baki duk cin zuma ya gama da shi me zaka ji,Idon Maheerah ta faka suka hada Ido da Ahsan ta Masa zancen kurame Wai ya samo wata a daura Masa aure da ita tana hada yatsa biyu tana kullawa Wai aure,Kai ya girgiza da sauri wai a'a ya maida hankalinsa ga matarsa suna jira ta tafi taki tafiya ta dawo ta samu kujera ta zauna har da mikowa Maheerah bra dinta tace ungo ni karbi abarki,Takaici ya Kama Maheerah ta rasa wacce irin yarinya ta samo da ace ba cikinsu a jikinta da tuni ta sa an kamata,ko ta Mata wata muguntar ita da gidanta ta hanata sakewa rana Daya ko kwana daya ba ayi ba,haka ta ja mijinta suka shige bedroom abinsu,Lokacin Cele ta tashi ta koma daki ta kwanta duk bata Jin dadin jikinta Sam Jin jikinta take Yi ba yanda ta Saba ba.


     Santana mutumin Adamawa ne amma a Sokoto suke da zama,gidansu su goma cif iyayensu Suka Haifa Mata uku maza bakwai Santana Kuma shine na takwas a gidansu sauran kusan duk yayyensa ne mutum biyu ne kannensa,suna da rufin asiri babansu dan kasuwa sannan yayyen Santana mutum uku duk suna da rufin asirinsa su ke kula da iyayensu da sauran marasa karfi duk da cewa Suma ba a wahala suke ba,Santana tunda ya taso yake kwaikwayon Mata ko ya dinga daura zanin babarsa tun suna Masa fada baya ji har ya girma daga nan da kyar ma aka samu ya Gama secondary yace Sana'a zaiyi ya Fara soya doya da kwai,daga nan ya koma wata state din ya koma har waina da miya Yana Yi ta siyarwa,ya koma cikin tasha Yana dafa shinkafa da miya da wake ga waina da miya ga su doya da kwai,tun Yana karairaya Yana canja magana a hankali ya shiga daudu komai mata amma inda Allah ya taimake shi bai taba neman maza yan Uwansa ba shi,Yan da kyankyami Wai sai yace warin maza suke,sosai cikin kawayensa Yan daudu sune suka bashi shawara cewar a kudu an fi samun kudi,sai Suka koma Kwara state,daga nan sai Ibadan,tafi tafi suna Zama sune Tasha Tasha bariki bariki har Suka goge a Iskanci Suka fada sana'ar Mata masu Neman maza suzo su zaba su darje abinsu,Santana bai gama tuba da saduda ba sai da Su Manduwa Suka rasu ya girgiza da mutuwarsu Kuma yaga tasa karara Allah ya tsallakar da shi tun daga lokacin ya saduda ya tuba ga Allah Harkar ma baya son tunawa sai dai iya shegen a baki wannan kuma kafin mutum ya dena to sai a hankali wasu ma ko matan ne har abada basa dena iya shege sabo da Sabo dole ko Yaya sai kaga bariki tayi musu yawa a wani wajen.


  Mudai bikin Santana tunda Namiji ne can gidansu Muka je sokoto a gidan nan bayan murnar biki har da murnar ya shiryu Yan gida suka hada kida na gaske Suka dinga tika rawa yanzu duk da Aurenmu Munyi rawa amma bada yawa ba Kar mazajen mu su gani,Mandula data auri yaro yake juyata kasa shiga tayi tace ba ruwana ya hanani Star tace ke ni da nake matar malami ma gashi na cashe bare ke,Mandula tace in ya fara min fada Ni bana son abinda ransa zai baci,dariya ta kamamu Dan yaro karami, ango Santana da abokansa duk kusan Mata ne sai Yan Uwansa maza sai abokansa da Suka taso suna tare su biyu rak Mata sunzo bikin Santana daga gari gari duk ba na kirki wai sune abokansa can aka je aka dauro auren Jamila Jamcy da Abubakar Santana akan Sadaki dubu dari da Hamsim,Jamcy bata bari ma taga ango ba su Sabreen sune Kawayen amarya, ana gama daurin auren ango ansha babbar riga ai ganin kida da girgiza ya tako ya shigo filin rawar ana ta ihu da dariya domin Santana yafi Mata iya girgiza,ya tiki rawa ya chashe Kamar tsohon dan club ne, aure da yamma likis Suka Kai Amarya lokacin mun koma zamu karbi Amarya a gidan Ango suke iske mu mamaki ya Kama Sabreen ta radawa Jamcy tace kin Shiga uku duk kungiyar su Miracle a bikin gasu nan suna ta iyayi sunzo bamu San a gayyar wa Suka Zo ba,Star ce taga suna kuskus guda tayi tace a matsayinmu na manyan abokan Ango muna yiwa Amarya barka da zuwa,Wise tace duk inda aka je mune dai,nace Rana zafi inuwa kuna,Yar Zabil ta saki guda tace mune a wajen,Barka da zuwa Amarya cewar Mandula Muka shiga dakin,Bayan mutane sun watse sai Sabreen sai Jamcy sai Kuma mu,Su Sabreen sunyi mukus sun San basu Isa ba,Mandula tace amarya yau zata karbi Antaina sai a amsheta hannu bibiyu mune masu siyen baki,wayata na dakko a jakata na Kira Santana,yace Kun taru gani nan, Namiji daya ne ya sauke shi a mota ya juya abinsa yana masa tsiya,mu Kuwa Muka tashi muka fice a motar da na zo da ita nina sauke kowacce a gidanta na wuce gida Nima,Nawwar yayi Shirin bacci tun Yana jirana har bacci yayi gaba da shi,Ina zuwa abinci naci nayi wanka tare da Shirin bacci na kwanta a bayansa tare da hugging nasa.


 Har nayi nisa a baccina Kawai sai zuciyata ta Fara tashi da sauri na tashi cikin daren na shiga toilet sai amai amai Kawai nake shekawa,Nawwar ne ya farka ya shugo toilet din da sauri yace ko dai wani abin Kika ci a gidan biki Kuma, ya rikeni na gama amai na sannan na kuskure bakina nayi flowshing Muka fito Yana min Sannu cike da kulawa, ko saman bed ban kai ba na koma toilet na fara sheka sabon Amai yace ko asibiti zamu je ne? Idona cike da kwalla nace a'a,sai da na gama har wanka ya sake min ya canja min kaya,yace me Zaki iya ci yanzu Kinga cikinki ba komai nace Data Kawai nake nema ko goba idan ba su ba bana son komai,yace a Ina Zan samo wani Data yanzu,nace kyaleni to na kwana haka na koma saman bed na kwanta,yace ni yanzu Ina Zan samu goba a Daren nan,to ga Apple kici Mana,bana sonta ni ga abinda nake so nan kawai,Kaya ya saka ya fita wajen me gadi yace Dan Allah Ina Zan samu goba ko Data yanzu,Ido me gadi ya zaro yace Sha biyu fa ta wuce Oga akwai dai Wanda na sani Yana siyar da goba sai dai muje gidansa,Nawwar ya shiga mota tare da me gadi Suka je har gidan mutumin Suka kwankwasa Masa kofa ya fito,Suka ce goba suke so idan akwai yace Amma wannan me nema me ciki ce kunyi sa'a a kwai ya shiga ya fito da ita kwali guda manya lafiyayyu Nawwar ya siya min ta dubu uku Suka dawo,Ina Jin ya shigo na mike yaje ya wanko min su duk ya zubo a bowl yace gashi aci lafiya ya tube kayansa ya kwanta sai bacci ni Kuwa sai gobata nake ci sai da na koshi sannan na kwanta bacci.


     Santana Ango ansha manyan Kaya shadda sea blue ya shigo harda wani nutsuwa,da kyar Sabreen ta gane shine tace no wonder naga su matar Papa na a bikin Nan ashe nan ma Kun sake kutso mana rayuwa amma nayi mamakin shiriyarka ka daina daudun ai Jamcy bata San Sanda ta watsar da mayafin amarci ba tace dama Dandaudu ne? Santana yace ki godewa Allah sai da na shiryu na aureki da Abaya ne ma haka Ina dauduna Zaki aureni yanzu kuwa rayuwa ta canja,Sabreen dariya a ranta ta tashi tace Amarya sai da safe,tana fita Jamcy tace sai ka sakeni nafi karfinka nafi karfin Zama da kai Santana yace iyyeee bari na cire hular na fito Miki a macena sak ashe yau za a yita wlh alo tsiya alo danja yau a cikin gidan,galala Jamcy tayi tana kallon ikon Allah komawa tayi ta zauna tayi lakwas,kice tak ki gani wlh yau sai na sa Antaina na goge ki tas na Miki wankan tsarki ni Zaki yiwa diban albarka yaja Tsaki Yana masifa dan ma an samu na shiryu shine ake min Iskanci ana min gani gani matar da asiri na rufa Mata bata da mashinshini anyi kwantai a gida,Nan Iyayenki murna suke kin samu masoyi Abubakar Santana na dakkoki sabo da rufawa Oven dinki asiri Zaki Zo Kina wani magana da wata muryarki a shake Kamar ta tsuntsu Kinga ga kaza nan ci abarki ni in zaki iya,Jamcy ta kalli katuwar ledar ta kalle shi,yace karki cuci kanki yarinya ki Danni kaza ki Sha Madara ki daina wani iyayi Kamar Yan 16yrs 30-32 yrs kuke sa'annin Nawwar ne ku guzumaye kawai,Ni dai tunda na maka Shuru ka kyaleni Kuma haka ehe cewar Jamcy,Santana yace ato ni a Nan baza ki min kwaya ba,kayan mayen ku da kike Sha ba abinda ban sani ba ke kin taba Shan Kuskura? idan kinsha kuskure to a ciki wacce Kika taba Sha Hajiya Salma ko Farida ko Hajara duk sunayensu ne,wannan kayan mayen da ya lissafa duk Jamcy ta sansu amma bata Shan ko Daya ciki,yace karamar Yar kwaya Allah yasa na kamaki kina Sha Kinga yanda Zan baki tarbiyya da Antaina ita kadai ta isheki ya shige toilet harda murguda duwawu, yayi wanka ya fito,harda gadara Yana Jan aji,Jamcy yunwa take ji kazarta ta ci ta bari taki tashi bata da Niyyar yin komai,Santana yace har nayi Shirin bacci kina me kije kiyi wanka,tashi tayi Jamcy taga wannan ya fita tsiya tana shiga Santana Yana cewa a wanke ko Ina da kyau lungu da sako a cude a dirje Kar a manta da hammata itama,Jamcy sai data Yi dariya tayi wanka ta fito,Santana harda kallonta daure da towel yace see fine girl ya mike zaune yace sa hijab muyi Sallah, ta saka har kasa ya jasu Sallah yayi Addua ta tashi ta karasa shirinta tana Fushi tana cika tana batsewa haka ta saka rigar baccinta peach tayi kyau,hand bag dinta ta dakko da Niyyar ta Sha kayan maye yanda zata fada saman bed nan take ta sume ko shi Santana bai Isa ya kusance ta ba abinda Suka shirya da Sabreen kenan,tana duba jaka wayam babu kayan maye,ta sake dubawa tace a'a tana faman dubawa Santana yace gasu na kwashe kayan mayen naki ni fa yarinya ba Kalar barikin da ban sani ba kin gansu ta gansu a gabansa,da sauri ta fada saman bed din tana cewa ka bani kayana Santana ya toshe Mata baki da nasa,nan take jikinta ya Fara saki Santana anyi Ashawo ansha daukansa Yana sarrafa Mata yasan duk Kan wata mace da wuri ya samo Kan Jamcy cewa take ma yayi sauri ya shigeta yace uhm an San maza tun a waje an baki dai dai ke Maganar Allah ta tabbata danbanza na Yar banza ne,sai gashi Jamcy an bige da sarrafa Santana bata da control ko kadan, Santana yasha dadi ga Boobs mashaallah,Bai Sha wahala ba ya shigeta sabo da tana sex dama a waje amma duk da Haka ta Sha gyara a matse take tsam ba irin Sabreen ba, Santana an ragargaji dadi itama Jamcy har ta fishi zaucewa sabo da duk kule kulenta bata ci Karo da irin Santana ba me iya harka,washe gari da safe sai gashi ta Riga Santana tashi sai kallo take Kare Masa tana tuna daren jiya,toilet ta shiga tayi Brush da Alwala ta fito duk tsiyarta ita tana Sallah akan lokaci,tashin Santana tayi ya mike tace anyi kira,shima brush yayi da alwala ya fita masallaci sai da Rana ta Dan kyallo sannan ya dawo gida,Jamcy an kiyayi Santana sai gashi harda cewa Yaya Ina kwana,Santana irin me gidan nan yace kin tashi lafiya ana wani Maganar maza irin a dake, kwanciya Suka sake Yi suna ta bacci tana rungume a jikin Mijinta,sai 11am Suka ji ana knocking,Santana ya fita ya bude driver ya Mika Masa basket yace gashi inji Wise,yace kace na gode oh su Wise anji jiki kace Ina godiya Yan banzan Yara suna kaunata.


  Jamcy ce ta fito yace Matar baban kawarki wato babarku Wise ce ta kawo Abinci,Jamcy tace hmm wannan marar kunyar,ke ki kiyayi kanki Kar na sake ji da ki zagi su Wise gwara ki zagi babban yayana Wanda muke uwa Daya uba Daya Idrisa ato, Jamcy tayi mukus ganin ya hade rai, Suka ci lafiyayyen Karin safen su,da Rana zata yi girki yace a'a za a kawo,ai Kuwa 1:20,pm sai ga abinci Seraline ta aiko,da dare Yar Zabil ta kawo,Star ta Aiko da Farfe su,Jamcy tace ban taba ganin masu kaunar juna da hadin Kai irinku ba,inama mutane idan Zama ya hadasu haka akeyi ko ace makwabci ma haka ake da hadin kai,Santana yace ke dai bari Allah ya hada jininmu ya jawo Jamcy saman cinyarsa suna soyewa.


    Mami Mahmood ya kwarzabeta duk ta rame sabo da Sex ko yaushe ba daga kafa a Rana sai yayi sau biyar ga dadewa yake bai kawo ba irin jarababben hariji ne na gaske,Mami sati biyu tace ya saketa baza ta iya ba yafi karfinta,shi Kuma yace gaskiya bazai iya ba ta hadu Yana Jin dadin sex da ita,Mami gajiya tayi tana ta daga Masa kafa amma Sam baida hankali Kawai sai ta gaji ta dakko wuka dama tsorata shi tayi ta nufo shi,ba karamin tsorata yayi ba,Mami ta cilla Masa biro da takarda tace sake ni,a tsorace ya rubuta Mata saki daya,sannan yace na warware igiyar aure na Daya ya furta da turanci dama sabo da kasuwa Yana Dan Jin hausa harda gwarancin hausarsa ya furta sakin,Mami ta dauki takarda abinta ta hado kayanta kaf ta fice daga Nan sai gida Nigeria,Nawwar tayiwa waya tace kazo airport ka daukeni na dawo,mamaki ya kamashi yace Mami wai da gaske ke da Kika Yi aure kwana nan har muna shirin zuwar Miki hutu,bana son surutu idan zaka Zo ka daukeni kazo.

   Baffa kuwa hankalinsa yayi Matukar tashi Jin labarin Mami tayi aure a Madina Kuma balarabe,Bai sani ba sai da Mami ta kwashe sati biyu a gidan miji bai San lokacin ma har an sake ta ba,da sassafe ya Kira Nawwar ya tambaya Nawwar ya tabbatar Masa da haka.


    Wajen Iyamami ya shiga yana zuwa Idonsa jajir sanye cikin shadda sky ya zauna bayan ya gaishe ta yace Wai kinji Mamin Nawwar tayi aure a Madina? Iyamami tace Kai dai dan nan bari haka naji labari kayi hakuri idan rabonka ce zata dawo ka kalli yanda ka rame akan Salamatu haba Sulaiman duk ka lalace bana Jin dadin ganinka a haka, ko tsohuwar matarka ce tunda bata da wani laifi ka dawo da ita,Baffa yace har abada bazan dawo da ita ba ni auren ma na gama shi har abada bazan sake ba na daina bazan sake aure ba,ai duk ke Kika jawo min gashi nan taje ta auri wani,balarabe me kudi shike nan Sirrina ya gani,wallahi duk Wanda yayi silar rabani da matata bazan yafe Masa ba ko waye idon Baffa ya kawo kwalla ya tashi ya fice.


    Nawwar Kuwa tare muka je Airport din Ina gaban mota Muka hango Mami ta rame tayi zuru zuru duk ta wani firgice,Nawwar Yana Fitowa a mota ya dinga sheka dariya a gaban Mami yace me na fada miki,Zan mareka wallahi Nawwar ta furta,Hannu ya Mika Yana faman dariya yace muga takardar sakin? Saki uku ne ko Daya,Ina gefe suna birge ni a Raina nace inama nima Ina da iyaye,mota Suka Shiga Muka tafi gida Ina yiwa Mami Sannu da zuwa Muna hira har Muka je gida,Mami a part din da su Star suka zauna Nan ta zauna gaba daya ta dawo gidan a Nan take idda babu Wanda yasan ma tana gidan sai iya yaranta ko su sulatana Basu San auren ya mutu ba Kawai ance tazo ganin gida ne sai Murna suke kusan kullum sai sun zo gidan har Auta,yau munje part din Mami Bayan Sallar Isha muna hira har Nawwar bakina ya cika da yawu sabo da turaren da Mami ta saka a palon sam bana sonsa duk Kuwa da irin dadin kamshinsa, toilet naje na zubar da yawun na dawo Muna hira minti daya yawu ya Kuma cika na tashi,Mami tuni ta lakanci hakan Kawai sharewa tayi,Nawwar ya kalleni bayan ya fito yace karki sa Mana tashin zuciya irin wannan yawu haka Mami bata da lafiya wurin kwana nawa amma taki yarda aje asibiti,haba dai a'a Rabia kuje asibiti ai gwara a San mene ke damunki Mami ta furta da sauri Nawwar yace bazai wuce ciki bane ai ta Sha Miya ma ta dade Bata samu ba,Kaga Ni bacci nake ji ku tashi ku tafi Mami ta koro mu,muna Fitowa Mami tace lallai Rabi tayi lafiya da dane da yanzu tana fitsara iri iri,Muna Fitowa na harari Nawwar nace ko Ina sai kace ciki ne dani Kai baza ayi sirri da Kai ba ko,shi Kam murna yake sosai Yana farin ciki Ina da ciki tun kafin muje asibiti.


     Muna komawa cikin main palo ya daukeni Muka haura sama a saman bed ya direni ya fara murza ni,kicin kicin nayi bana so a rabeni yanzu tunda na fara laulayi, ya kalleni yace wai wannan wanne irin ciki ne yanzu da kyar kike yarda dani da kuwa sai abinda nake so,jiya haka Kika hana kememe,bakya tausayina ne, hakura nayi na yarda haka na bada hadin Kai sosai Kar ya  shiga wani hali,washe gari Kuwa asibiti ya kaini aka min duk wasu test lafiya kalau nake Kawai Ina da ciki har 4mnths, Nawwar sai Murna yake fama,a ranar Kuma Malam Abulkhair ya dawo da koyamana karatu kullum a gidana kowaccenmu tana zuwa har Santana.


     Iyashege bamu fasa ba musamman star,yau ma muna zaune Malam Yana zuba karatu Star sai magana take Masa da Ido Yana kallo shima da idon yake bata amsa,Wise tace Malam Wai ciwon Ido kake ne? Yace me Kika gani ya basar tace naga sai ka dinga ta mintsina ido,Shuru yayi Mata yaci gaba da karatu, Yana karatu Star ta dauki biro tana rubutu yazo har gabanta Hannu yasa a littafin yace da kyau sarkin kokari da Allah ku tafa Mata,Muka kalli juna sannan muka tafa Mata ba dalili,tunda ya aureta kullum sai yasa an tafawa Star sau uku idan anzo karatu,nace mu wato bamu da galibu bamu da gata kullum Star ce me kokari,Star har gwalo take mana.

   Ana karatu tayi rubutu a takarda ta dagawa Malam wai Honey ya jiya da dare? Malam Abhulkhair harda sakin Murmushi Yana Kare Fuska da littafi muka ji yace great Masha Allah bamu San me ta rubuta Masa ba,Seraline ce tayi tambaya tace Malam mijina kullum mukan harari juna amma bada fada ba ta sigar soyayya hakan da kyau ba raini? Malam Abhulkhair ya jinjina kai a ransa yace yaran nan baza su shiryu ba Ina ganin Iftila'i nikam,a fili yace Alhmdllh Kinga Kamar Me Sunan Tauraro gaskiya tana da kaifin basira yabon gwani ya Zama dole ba Wai dan Muna da alaka ba ita gaskiya idan tazo dole a fadeta amma ban taba gani the most intelligent girl irin me sunan Tauraro ba,Dole mu jinjinawa Iyayenta da Allah ya basu ikon haihuwarta anyi farar haihuwa,kafin a sameta sai da akayi Addua da alama,dukkanmu Muka bude baki bazai karatun kirki ba sai yabon Star da iyayenta kullum,Yar Zabil tace Malam mufa ba taruwa mukayi ba don a bamu karatu akan Star ba ayi Mana karatu mu tafi,yace  bakwa son gaskiya kasar nan ta lalace har kullum mu munfi so a zagi dan uwanmu shine dai dai idan gaskiya tazo dole a fade ta, nutsuwarta ce ta sa,Star tayi mana gwalo, Malam yaci gaba da karatu babin Tajweed


       Washe gari da safe Ahsan ranar hutunsa ce baya zuwa aiki ita Kuwa gogar Maheerah ita kadai yau ta Sha fresh milk da snacks ta wuce wurin aiki Ahsan bacci yake sosai abinsa,Ayusha tazo da nikaf da doguwar riga,Cele Kuwa tana tashi wanka tayi tunda tayi sallar asuba ta shirya cikin riga da skert dinta sababbi cikin kayan da Suka siya mata,ta daura wani dankwali irin na larabawa ta fito,kitchen ya shiga Ayusha tunda ta kalleta sau daya bata sake ba sabo da tsoronta , gas ta kunna gefe Daya ta dauki kwai har guda uku ta soya yaji hadin Albasa harda Maggi ta gani wasu Kalar ba irin namu ba,bayan ta soya ta soya dankalin turawanta me yawa ta hada tea me kauri, sai ta Koma Palo tare da kunna kallo abinta ga abincinta ta zauna kenan a kasa Ahsan ya fito ya Sha wanka sanye cikin Jallabiya fara tana uban sheki sai kamshi yake,Murmushi yayi ya kalle ta dai,bata iya gaisuwar su ba tace Salamu Alayk,ya amsa mata Kuwa Yana Murmushi ya kalli abincin da take ci, shayinta cikin katon cup din da ya siya mata dan ita duk rashin ci irin na Cele tafi karfin irin cup irin na su Ahsan.


    Kallon cup din yake da irin shayin dake ciki yana kunshe dariyarsa a cikinsa,wani sabon bread data dakko a kitchen din me kyau ga laushi haba har lumshe Ido take tana korawa tana ci Kamar Wasa yaga ta cinye komai ta shanye komai,ya zaro Ido Yana kallonta ya gani ko zata iya tashi sai yaga ta mike tsaf ta kwashe kwanikan ta Kai kitchen ta wanke komai ta adana ta dawo kitchen dauke da ruwan roba tana sha,a ransa yace har space ne na ruwa a cikinta duk abincin da ta cinye, sai satar kallon cikinta yake shi jaririnsa yake ji Kar a kashe shi da abinci,gashi yana son taba cikin amma ba damar hakan,ita Rufaida bata San ma tana da cikinsu ba a jikinta Kawai dai bata Jin dadin jikinta ta rasa dalili.


    Da Hannu ya yafito Cele wai taje,zuwa tayi ta tako gabansa tana tafiyar Yan sarauniyar kyau ta rike kugu tana harde kafafu Kamar dai yanda masu gasar sauniyar kyau suke Yi tana zuwa gabansa ta tsaya tare da tsuke dan bakinta,Murmushi ya saki ba shiri kujera ya nuna Mata ta zauna nesa da shi kadan gaba daya kamshinsa ya tafi da imaninsa ji take idan bata shaka ba Kamar zata suma ta baza hanci harda Mika wuya tayi dogon wuya,mamaki yake a ransa yanda take clean haka,a haka aka kawo Masa abinci yaci sannan agogon hannunsa ya kalla me tsada ya tashi ya fice abinsa,yau shi yayi driving kansa,ita dai Cele tashi tayi ta shiga kitchen ta iske Ayusha tace da Hausa ke Wai me ake nufi dani ne a gidan nan? na rasa dalilin kawo ni gidan nan an sato ni maimakon Naga ana gallaza min azaba iri iri amma anyi Shuru sai zaman lafiya nake yi,ga me gidan sai kirki yake min wai me ake nufi Dani ne,Hannu tasa ta daki sink tace me ake nufi ne wai an rabani da Kaka ko Yana wanne hali ban sani ba,Ayusha mukus tayi tana Jin tsoro haka Cele ta gama masifarta ta fice ta koma dakinta.


       Kakan Cele kuwa tunda Agent ta kwashe su har garin Makkah unguwar Shari mansir inda dandazon bakake suke inda mutanen mu sun gama kashe musu unguwar, Kaka sai Alfarma ya roka wajen Zama dakinsu su wajen mutum goma a nan ya samu ya raba,karfinsa ya Kare bazai iya sana'ar komai ba,yayi zaune yayi tagumi Allah yasa ma Cele ta bashi wasu kudin a hannunsa da su yake lallabawa Yana cin abincin takari, yau ko wanne matashi ya fice Neman kudinsa sai shi Daya a daki ya zuba tagumi yace Ina amfanin Zama na a kasar nan babu Jikata gatana itace komai nawa mene amfanin zuwana kaddara ta kawoni gashi an sace min Rufaida ta maganin Kuka na,na gama Shan kaddarata tun Ina yaro har na tsufa na Gama amsa jarabawata ta rayuwa gashi yanzu kaddarar Cele ta shafeni Ina Zan Sa kaina me zanyi da ya wuce bara bai sai Sanda ya Fara hawaye ba yace Allah yasa a kamani a maidani kasata Najeriya Banga amfanin zamana ba,tashi yayi ya fito da katuwar rigar shaddarsa ya mike titi Yana tafiya sai ya samu inda yaga askarawa Yan Sanda sai yaje cikinsu ya tsaya Wai Dan a kamashi a dawo da dashi Nigeria amma sunki kula shi, Kuma Yana kallo zasu bi wasu takarin da gudu su zuba tsere amma shi basa kulashi,a haka Kaka yake gararinsa a kasar har ya samu ya sauke Umrah Cele ta Sha Addua a dakin ka'abah Allah ya bayyana Masa ita,ba Wanda ya Kama Kaka kamar Dan kasa haka yake harka har kudinsa Suka Kare ya Fara bara a hanyar zuwa Harami wato dakin Allah a hanyar yake zama ana ta bashi sadaka da haka yake ci yana Sha,so yake a kamashi a dawo da shi Nigeria amma anki ga Wanda basa son a Kama su amma sai kamasu ake banda shi.


    Mairo cikinta ya girma tunda taje kasar take sana'ar tuwon shinkafa tana kaiwa gidajen Baki masu zuwa aikin hajji Hausawa, ita kuwa Sadiya tana zuwa taji hausawa takari ana samo musu mazaje suna aura,duk aure daya za a baka kimanin dubu dari biyar wasu sana'arsu kenan sai kiga mace a kankanin lokaci tayi aure goma ma Sabo da wannan kudin, Sadiya tace ita baza ta iya siyar da abinci ba aka samo Mata Balaraben Yemen aka daura aure ta samu dubu dari biyar cas ta tura da kudin gida,babarta sai Murna take daga zuwa arziki ya zo bata ma San aure tayi ba,Sadiya wani wulakantaccen gida ya ajiyeta me dauke da daki Daya tal komai a ciki toilet da kitchen,sabo da ya dauki bakakenmu Basu San me suke ba sannan kudi suke biya suna auren dandane da su, ana Kai Sadiya ya Fara sassakarta ba ji ba gani,gashi bata Saba ba,bata hutawa da Antaina ko 2 weeks bata cika ba ta fito Amma tana yin Idda ta sake auren wani Dan kasar Siriya,shima dubu dari biyar,Ashe shi Kuma burinsa Kawai ya auri bakar fata ya dinga kallo Yana dariya shike nan burinsa, Sadiya ta tare ya shigo yace tayi tsirara haka yake so ya ganta,haka tayi to tasan kudi ya biyata ta tube Kaya ya zurawa surarta Ido Kamar Yana gidan zoo sai ya sheke da dariya yace ta juya ta juya Nan sai dariya hahaha Yana muzantata,yafi karfin ya taba nononta da hannu sabo da haka ya jawo sandarsa ta karfe da yake yawan rikewa dake ya Fara manyanta ya zauna da sandar yake sawa Yana zungurar dukiyar Fulanin Sadiya,kullum aikinsa kenan Yana shigowa gidan zai hau dariya Yana kallonta Yana nunata da yatsa,Sadiya abin ya isheta ta Fara Masa rashin mutunci tunda tana Jin turanci shima Yana ji,dama abinda Basu fiye so ba ka zagi uwarsu Indai ka zagi uwarsu to har abada su da kai,ko dai su koreka ko kaci ubanka,ta zagi uwarsa da larabcin data Fara koya,domin ita Sadiya ita da Mairo suna zuwa cewa Suka Yi zagi Kawai za a fara koya musu,takari Suka koya musu zagi da larabci iri iri,da su Sadiya tayi amfani sabo da son kai shi duk abinda yake Mata na cin mutunci bai gani sai shi sabo da ta zagi uwarsa,ai Kuwa anyi rashin sa'a Sadiya sai da taci dukan tsiya sannan ya saketa ya koreta.

   Mairo ma Allah Allah take ta haihu ta fara aure auren kudi,tana da ciki sha'awa tana damun Mairo gashi ta Saba da namiji,a cikin takari da wasu bakin larabawa suna Neman Mata me ciki akwai Wanda su sai me ciki suke zina da ita suna biyanta makudan kudade,Tuni Mairo ta fada Harkar tana dafa tuwonta na siyarwa tana Neman maza da cikinta ana biyanta kudi musamman da taga bata da girman ciki idan tasa babbar Abaya ma ba a ganinsa sai ka zaci kiba ce kawai.


    Cikin matan da suka Zo da Cele Kuwa gidan Samira da Wasila aka kaisu yaran Mata ne Suma hausawa sunfi su talatin a gidan duk matasan Mata ne gaba dayansu Harkar lesbian suke madugo har matan larabawa suna Neman su suna biyansu aikinsu kenan, Samira tuni Suka jata cikinsu Suka fara Yi da ita,Wasila Kuwa sunyi sunyi amma taki yarda sannan Allah ya tsareta,tace Neman kudi nazo ba lalata nazo ba na rasa inda zan Yi sabon Allah sai nazo har dakin Allah,dama ta iya lalle iri iri ta iya kitso Kawai ta Fara sana'arta ta siyo kayan yi ta Fara Neman kudinta Kuma Allah ya sa Mata Albarka tana mugun samu kudi har ma ta tashi ta bar gidan inda su Samira suke Alfasha ta koma gidan takari mutanen kirki Wanda su dama kudin suke nema sun maida Kai Kuma ta hanyar halak suke nema dama wasu ke bata wasu.


    Bangaren matasan Mazan da suka Zo tare da Cele Abdul,da Naziru bread suke sarowa suna siyarwa bakin gidajen Alhazawa sosai suke abinda ya kaisu,Musty kuwa Wanda ya taba kaiwa Cele hari shi tuni daga Neman Mata sai ya shiga kungiyar Yan luwadi,an samu lalatattun larabawa da suke Yi da su suna biyansu kudi yanzu zaka ga mutum ya Zama me shegen kudi layin Musty ya dauka shi.


     Ni Kuwa Rabi laulayi nake yi sosai,aiki ma ba komai nake yi ba,ga Nawwar bai zama aiki ya rike min shi kullum sai dai waya Yana tambaya ya jikin,Mami ce ke kula dani,ko Riga bana so na saka sabo da jikina ji nake kamar ana rura min wuta kullum da kyar nake saka vest da skert kullum Ina cikin toilet Ina shiga cikin ruwa na Zama Kamar kwaduwa ko nace agwagwa,Mami bata sanin wani abin Dana ke aikatawa bata San har akan kankara kwanciya nake ba, yau ma tunda na samu Nawwar ya fita na dakko Kankara katuwa a fridge dama ruwa nake samu na zuba a bowl din silver da wuri take min kankara,na dawo bedroom dina,na cire kayan jikina sabo da tsiyata ko pant babu na zuba kankarar na barbazata a kasan tiles da ruwan sanyin ga wata Ina Sha sannan na kwanta a Kai Ina malelekuwa a saman kankara Ina Jin dadina Ina tauna wata kankarar Ina lumshe ido, Nawwar ne ya dawo yayi mantuwa ya kamani a Haka kankara ba kadan ba, Innalillahi wa Innailayhirraju'un ya furta tare da Dora hannaye a Kai ni ya tsoratani ma da katuwar kankara a bakina nace lafiya? yace kashe kanki zakiyi shi yasa kullum mura taki Kare Miki kin San idan sanyi ya kamaki wlh munga ta kanmu shike Nan dana Nimoniya ta kamashi Allah ya tsare Hannu yasa ya dagani Yana fada yace dan Iskanci harda yin tsirara ki kwanta haka,Allah ya shiryeki,kankarar dake bakina ya kwakwule da hannunsa,nace ni gobara akeyi a jikina kullum sai naji wutar ta Kama a jikina ko ina, Fitowa yayi yasa aka kwashe gaba Daya fridge din gidan ya maida su bangaren Mami ya fada Mata,yace karki bari Rabiah ta dauki ko ruwan sanyi a fridge,Mami tace haba shi yasa kullum sai naga ta saka ruwa a silver sau biyu sau uku a Rana Ashe kankarar take dauka bata San Illar hakan ba,ganin su Mami sun gama da matsalar sai na koma na samu Kaya me kauri na jikata da ruwa sharkaf na saka kayan haka Ina Jin dadin jikina,Nawwar yana sake kamani sai ya tasa keyata tare muke shiryawa ya tafi dani Office, a can din ma fada muke Yi a tiles nake kwanciya,ga karatunmu Muna Yi duk mun Fara gogewa Kawai sai ya kaini makaranta ya sani a Ss3 kuka wiwi nake yi, yace tunda kullum bakya Jin magana ke sai kin shiga sanyi ai gwara na saki a makaranta ki godewa Allah ba Jss1 na kaiki ba, kuma idan baki karatu ba ki ci duka,a Dole nake saka uniform harda Hijab na tafi school,sai gashi an kawo su Sera dukkanmu ajinmu daya banda Wise ita tana da degree ma

  Ni idan naje makarantar ma bana ganewa sabo da laulayi kowa yana sit ni Ina kasa a zaune a haka nake karatun Yan aji suyi ta kallona, gajiya wasu matan Suka Yi Suka ce Rabia kalau kike kuwa ke kullum a kasa,nace ciki ne da ni mijina nane ya min ciki,Yan aji sai dariya suke suna Jin kunya wata a ciki tace ai ba sai kince mijinki ne ya Miki ba,a'a ai karku kaini inda banje ba kuyi zaton na shege ne to da ubansa Ina da aure ku Kuna ganina kun San ni ba sa'arku bace,babban Kai ce ni na ja tsaki na kwanta a kasa sosai Kamar ina dakina har aka tashi ni yau na kasa tashi ma Sabo da kwailo irin nawa,Star sun gaji da halina sun kyaleni tafiyarsu Suka yi, Nawwar daukana yazo yi da Kansa yaga har Yan school sun Kare bai ganni ba,wata Yar ajin mu ya tambaya yace Rabiah fa? Tace a aji muka barta ta kwanta a kasa kullum a kasa take kwanciya ko ta zauna ka tambayi ma kawayenta su Star kaji ,motar ya bude ya fito duba ajujuwan har ya hangoni a ajinmu a kwance jakar makaranta tana gefe Ina ta bacci na, Yana zuwa ya tashe ni yace Wai me yasa ke gaba daya baki da dauriyar wahala Kamar a kanki aka Fara ciki,tashi mu tafi kalli uniform dinki duk yayi dirty Kamar Yar pre nursery, tashi nayi Ina harararsa nace wlh da Zan iya sai na dawo maka da cikinka jikinka duk waye ya jawo min wannan halin da nake ciki idan ba Kai ba,Ni na taba lalura irin wannan ma Sai a gidanka,dariya yayi yace nima da Zan iya kwace yarona zanyi karki kashe min shi da sanyi,Jakar tawa ya daukar min na fito Muka tafi,Muna komawa gida komai shi ya min har wanka,ana wanka sai dadin ruwan nake ji ruwan sanyi ne nace dan Allah Kar a gama wankan nan, sabo da muguntar Nawwar sai ya danna ruwan zafi ya sirka ruwan ya dawo me dumi da wuri nace an gama ya Isa na fita tas, a toilet din ya rikeni ya dinga aika min da sakosa na soyayya dukkanmu ba Kaya a jikinmu ya rungumeni tun bana maida Masa martani har na saki jiki sosai Muka jiyar da junanmu Dadi sannan Muka sake wanka tare da tsarkake kanmu muka fito.


    Kwanan Cele biyar a gidan larabawan Maheerah matar gidan tsakaninsu sai harara da kyama, Ahsan ne kadai yake saurarenta shima Kuma ba zama yake Yi ba a gida, ko me aikin Ayusha itama wariyar launin fata take nuna mata,mamakin da Cele take Yi me Suka ajiyeta suke Yi da ita a gidan Kuma game da abinci sai abinda taga dama take dafawa abin Yana daure Mata kai a haka Cele ta cika wata guda cif bata taba ko leka tsakar gida ba kullum tana kulle a gidan kofar ma baza ta budu ba tayi tayi ta Gane amma abin ya gagara,tana haka Kawai sai taji ba abinda take bukata sai Namiji bata San tana da ciki ba,sannan ga kwadayi dake damunta abinci sai ta zaba,sha'awar tafi  takura mata,sannan turaren Ahsan da yake sawa ji take idan bata shaki kamshinsa ba kamar zata mutu sai yawan bacci da kasala da Suka taru Suka Mata yawa,ta kasa gane kanta ta rasa me ke damunta, ana haka sai Cele taji tafiyarta ma ta canja tana Jin wani nauyi a jikinta tafiyarta kamar agwagwa haka take Jin tanayi amma a fili babu me ganewa,ita kadai tasan me take ji Kawai tafiya tayi nisa kwanaki na ja sai ta Fara jin kamar anyi motsi a cikinta ai da gudu ta fito,wani wawan birki ta ja ganin Yan uwan Maheerah suk zo ganin me cikin da aka yiwa dashen ciki su biyar da su Mata uku maza biyu a matan akwai dattijai guda biyu daya itace Maman Maheerah sunanta Fatima suna ce Mata Ummu Omair,Su Uku ne yaran data Haifa Omair shine Babba sai Maheerah sai kanwarta Jasmin wacce tana cikin Wanda Suka zo,Daya macen Kuma Babba ce itama kanwar Maman Maheerah ce Najwa.


  Mazan biyu kuma baban Maheerah ne Omair sai dayan Wanda kanin Baban Ahsan ne Rayyan zaune zagaye suke da abinci iri daban daban irin nasu na larabawa ai sai ci suke suna labarinsu da larabci akan cikin,Maheerah ce tace tana basu labari da harshen larabci tace ai da amincewarta kafin ma a kawota gidan Nan sai dana biyata wajen million uku sannan idan ta haihu za a biya wasu,Basu sani ba ashe Ahsan ya bata kudi ta cinye sisi bata ba Cele ba,Kanin Baban Ahsan ne yace amma ta taba haihuwa ko na ganta tayi karama ne,da sauri Maheerah tace haihuwarta uku yaranta biyu a Nigeria Daya Kuma a nan ta haife shi a Saudiyya amma da yayi wayo sai ta kaishi Nigeria wajen iyayenta, suna ta Jin dadi suna murna ana ci ana sha,Kanin Baban Ahsan Rayyan shine ya yafito cele taje Wai,ta taka taje har gabansa tare da tsugunawa Kawai to ita bata Jin yarensu,Yana Murmushi ya dafa kanta kallonsa tayi tana Masa murmushi,Dangin Maheerah kuwa in banda hararata ba abinda suke Yi gaba dayansu musamman Ummin Maheerah sai kallon wulakanci suke min,ba boye boye Ummu Maheerah tace me yasa bata sa Hijab da nikaf a gida ta zauna haka tana shiga yanda taga dama ga mijinki a gidan yana kallo,Ahsan yace tunda an dakkota bai dace a takura Mata ba,masu ciki suna yawan Jin zafi ba sai ta sa komai ba tayi shigarta shi bai da matsala ai na Dan lokaci ne zata haihu ta tafi,ita dai Cele bata San meke faruwa ba gaba Daya Bata Jin me suke cewa tashi tayi ta koma bedroom sai yamma likis Suka tafi,Maheerah tana da aikin yamma Kawai Ahsan ne ya kaita ya dawo, Yana dawowa har da su Ice cream ya siyo wa Cele,dakinta yayi knocking ta bude tare da Fitowa ledar ya Mika mata ta karba ta duba Ice cream ne da zam zam da wasu abubuwan na ci,taji dadin ganin ice cream din tana ta murna nan take ta dauki roba daya ta bude ta fara sha,Hannunta ya riko ta fito ta zauna a kujera sannan ya kunna mata kallo tana Shan Ice cream dinta cike da nishadi,ji tayi anyi wani motsi a cikinta zumbur ta mike,da sauri ya kalleta ganin duk ta firgice,ji tayi an sake motsi sai Kawai ta ajiye Ice ream dinta ta fashe da kuka ta rasa ta yanda Zata Masa bayani bata da lafiya, cikinta ta nuna Masa tayi motsi tace da hausa motsi nake ji haka nake ji a ciki ana matsawa ana zamewa ana yin sama sai ayi kasa,sai naji an koma gefe sai naji ana matsawa a hankali ana zullo,Ahsan yace bai gane ba ta dinga gwada Masa yanda take ji tana hawaye tana nuna Masa cikinta,Riga da skert ne a jikinta Kalar na larabawa sai ta dage rigar cikina ya bayyana Ahsan Kansa ya Dora a saman cikin har da sa kunnensa a saman cikinta, a hankali taji Yana shafa cikin shi Wai dansa yake shafawa,dama kadan Cele take jira matsananciyar sha'awa na damunta ta zaci romancing dinta zaiyi bata zaci dansa shi yake tabawa ba Yana gamawa ya jawo rigar ya rufe Mata cikinta ya matsa,kamshin nasa bata so ya bar hancinta kanta ta tura a kirjinsa tana shakar kamshin,mamaki da tsoro ya kamashi sai kace akuya sai tunkuyar Masa kirji take,Ahsan  harda cewa Hajja Haram Haram....Cele tace ni daka taba min ciki fa,ta sake makalkaleshi tana Jin kamshi sai jawo Masa farar jallabiyar take zuwa fuskarta gaba daya.





Ina godiya masu sharhi






AsmaBaffa

No comments

Powered by Blogger.