Babban Goro 9

 


BABI NA TARA___9



             BAYAN KWANA UKU....... 

Zaune take a parlor tana shan wakar Rahama _(you can in the emergency room)_

Sai ruwan hawaye take tana shafa gashin kanta, 

Bugun kofar da taji anayi ne yasa ta  share hawayenta ta tashi ta nufi kofar, ta buɗe. Ganin Saif yasa tayi juya zata rufe kofar, 

   Cikin wani irin zafin nama ya tura kofar ya fisgota abun ka da marar jiki haka ta tafo suww ta faɗo saman faffaɗan kirshinji, 

Da sauri ta ɗago tana kallon shi gabanta sai bugawa yake da karfi, cikin ɗaga murya tace, 

“Mi ya kawo ka nan bayan duk abunda kake so ka samu ko ko kazo kaje da raina ne?”

Glasse ɗin idonsa ya cire suna haɗa ido tsigar jikinta ta tashi, da sauri ta kawar da nata idon tana haki,

Cikin sanyayyiyar murya ya soma magana, 

“Minal banyi duk abunda nayi dan na cutar dake  ba nayi ne dan kawai na taimake ki da kuma mahaifiyarki, 

Minal tun lokacin da kuka faɗa min dalilinki na yin haka sai tausayinki ya kamani na kasa samun sukuni, ban laifin abinda kika aikata ba dan nima kaina idan haka ta same ni kwatankwacin abinda zan aika ta kenan” 

D'ago kai tayi ta kalle shi idonta cike. Da kwallah, 

Handkerchief ya ciro ya mika mata yana faɗin, 

“Am ready to help you ki gane ko kuwaye iyayen ki Minal nayi miki alkawari zan shige miki gaba har sai kinsan suwaye iyayenki” 

Yanayin kalaman shi yasa ta kalli kwayar idonshi, duk da kwarjinin da idon nashi suke mata bai hana ta ganin tsantsa gaskiya dake shinfiɗa cikin idon ba, 

Babu alamar wasa ko yaudara a idon shi balle a kalaman shi shima ɗin baiyi kama da masu irin wannan halin ba, 

Hakan yasa ta karɓi handkerchief ɗin ta share hawayenta tace, 

“Thank you Saif amman am sorry bazan iya ganin Mummy a yanzu ba” 

“I know Minal kawai ina son ki je ki tambaye ta yadda akayi kika zo hannunta, kiyi tunani Minal har ba wadda zaki aura ya guje ki saboda haka miyasa ba zaki so sanin wacece ke ba! Ya akayi kika zauna hannun Dr. Salamatu miyasa iyayen ki suka barki wace ce Dr. Salamatu a wajenki duk baki son waɗannnan amso shin Minal?” 

Da sauri tace “Ina so Saif ina son sani wacece” 

Ajiyar zuciya ya sauke, 

“Fine jeki chanja dress ɗinki muje gurin Dr. Salamatu” 

Kallon jikin nata tayi wata t-shirt ce jikinta yellow ta rufe mata jiki sai dai bata da dogon hannu, sai saket ɗin atamfa wadda ya kai mata har kasa, 

Juyawa tayi ta koma ciki, a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya jingina jikin kofar, 

Bata daɗe ba ta fito sanye da gown ɗin atamfa sosai tayi mata kyau sai dai kanta ba ɗankwali, tsaye tayi bakin kofar tana kallon shi kamar mai tunani hakan ya tabbatar mishi da kwankwanto take, 

Hannunshi ya mika mata, 

“I can trust me Minal” 

Sai da ta haɗi muyau sannan tace “Ina bukatar nayi shawara da Deen” 

Kai Saif ya girgiza mata, “Baki bukatar kowa a yanzu kina tare da Saif just trust me” 

Shiru tayi tana kallon hannun nashi kamin ta mika mashi tana hannun,

Sai da yasa a front seat sannan ya saki hannunta ya zagayo ya shiga driver seat, 

Hannu ya kai ya kunna wakar TAYLOR SWIFT _(the story of us)_, ya fara driving.




A hankali take satar kallonshi a zuciyarta tana mamakin abunda yasa yake son yi mata wannan taimako ko kuma sanya kanshi cikin sha'aninta, 

  Wannan duk plan ɗin Mummy ne dan gata na dawo a gareta, haka wata zuciyar tace mata,

Can kuma ta jefama kanta wata tambayar, amman taya Saif zai bar Mummy tayi using dashi? Bayan mutum ne mai akida ɗaya kuma babu wadda ya isa ya sa shi abinda bai tashi ba babu kuɗin da Mummy zata nuna mishi har yaja ra'ayinshi ya mata wannan aikin Saif mutum ne mai zaman kanshi da kanshi how.... 

“Minal tun lokacin dana barki nan kika kwana?” 

Tambayar daya jefa mata ne ya katse mata tunani, 

Sai da ta shafa wuyanta sannan tace “Eh a nan nake” 

“Kuma shima Deen ɗin a nan yake kwana?” 

“A'a baya kwana a nan sai dai yana tayani fira sai dare ya raba sannan yaje ɗayan gidanshi ya kwana wani lokacin kuma ya kan kwana nan” 

Shiru yayi wani abu ya tsaya mishi a wuya duk sai yaji ba daɗi, ko babu komai yar uwarshi ce musulma yana kishin yadda take sakin jikinta tana mu'amala da maza yana bakin cikin yaga mace musulma a irin wannan halin, 

    Kallonshi tayi “Miyasa ka tambaya?” 

Shima kallonta yayi ya ɗan sakar mata murmushin gefen fuska “Babu komai” 

Daga nn bai sake cewa komai ba ita bata sake cewa ba har suka isa. 

    Yana yin parking gabanta yayi dakan uku-uku, bai ce mata komai ba ya buɗe motar ya fita, 

Bayan kamar minti biyar ya fito ya nufo motar, koda ya buɗe motar baiga kowa ba, nan ya rufe motar ya nufi wajen gidan, sai da ya fita harabar gidan gaba ɗaya sannan ya hango ta jinkine da bangon gidan tana kallonshi. 

K'arasa yayi kusa da ita “Mi yasa kika fito? Baki yarda dani bane?” 

“Na yarda da kai kawai dai am not ready to meet her” 

Ajiyar zuciya ya sauke, 

“Minal karki manta badan taji daɗi zakije ki ganta ba no saboda kina bukatar wasu amsoshi ne right?, 

Ko bayan haka matar nan bata chanchanci haka daga gareki ba she's take good care of you for more than twenty years duk wani jindaɗi ta baki babu wata ya mace da zata nuna miki gata kina ganin idan kika mata haka kin kyauta kenan after that baki san uzurinta ba”

Kasa tayi da kanta, tana lumshe ido,

“Wannan dama ce a gareki Minal karki bari ta wuce ki”

Hannu ta mika mishi tana ɗaga kai, 

Badan yaso ba ya mika mata nashi hannun ta rik'e gam sannan suka nufi cikin gidan,



Rike take da hannunshi har suka isa cikin parlor, 

    Dr. Salamatu na ganinta ta tashi tsaye da sauri, 

“Minal my child” 

Bayan Saif Minal tayi ta taɓe kamar wata karamar yarinya da taga abun tsoro, 

Hakan yasa Dr. Salamatu ta tsaya bata k'arasa kusa da ita ba ta rungume hannayenta, 

Saif ya kalleta “Da kin zauna da yafi” 

Ba musu ta koma ta zauna tana kallon Minal, shima Saif a kujerar dake kusa dashi ya zauna, ganin hakan yasa ita ma Minal ta zauna a kujerar daya zauna jikinta na gogar nashi, da yake kujerar zaman mutum biyu cikin dabara ya matsa aka samu space tsakanin su, 

Mummy ce ta fara magana “Na sani Minal i hurt....” 

Da sauri Minal ta tari numfashinta “Mummy I'm not here to tell me love me or hurt me I'm here to tell me who I really am who is my father and who is my real mother?” 

 A takaice Dr. Salamatu ta bata amsa “I'm your real mother Minal nina haifeki” 

Ido Minal ta sakar mata alamar bata gamsu ba, 

A hankali hawaye suke saukowa a fuskar Dr. Salamatu cikin rawar murya tace “Minal zan faɗa miki ko wacece ke a yau zan tona asirin dana shekara ashirin da uku ina boyewa” 

Shiru tayi ta noce kai, ganin haka yasa Saif ya tashi tsaye da niyar fita, dan a tunaninshi bai dace yaji sirrin su ba,

Nan itama Minal ta rik'e mashi hannu ta tashi tsaye, Mummy kamar tasan abunda yake ranshi sai ta kalleshi, 

“Zauna Saif duk abunda zan faɗa ma Minal zan iya faɗa maka” 

Kai ya girgiza zaiyi magana Minal tace “Please Saif for me” 

Kasa magana yayi sai ya koma ya zauna ita ta zauna, Sit parlor yayi kamar babu mutane har na kusan minti biyar, sannan Mummy ta ɗago ta kallesu ta fara magana........... 

No comments

Powered by Blogger.