Babban Goro 7



BABI NA BAKWAI___7

SAIF..... 

Yana yin Sallah Asuba ya shirya y nufi Airport, dan yasan halin Dad ɗinshi matukar ya tsallake abunda umarni daya bashi komai zai iya faruwa, 

      Karfe 10pm a gogon ya iso yana sauka Airport yayi ma direba shi waya, cikin kankanen lokaci ya iso suka nufi gida. 

   A parlor a tararda Huda, tana ganin shi ta taso fuska a washe ta tareshi, 

“Sannu da zuwa dear” 

Bai amsa mata ba ya ɗauke kai ya nufi ɗakin shi, yana shiga ya cire kayan jijinshi ya shiga bathroom ya ɗan watsa ruwa, bayan ya fito yayi sallah. ya nufi dining 

    Tana ganin ya fito ta bishi tana mishi magana, nan ma banza yayi da ita har ya kare cin abinci ya koma ɗakinshi, 

Nan ta bishi tana kiranshi tana shiga taci gaban shi tana mishi magana. 

Sai a lokacin ya kalleta, 

“Wai  minene Huda mi kike so nayi miki ne?” 

Cikin ɗaga murya yayi mata tambayar,

  Kamar ta fasa kuka, “Tunda ka dawo kak'i kayi min magana sai fushi kake dani” 

“Ai dole nayi fushi dake halin nan naki bana sonshi kuma bazaki chanja ba, 

Miyasa kika je kika faɗawa Dad maganar tafiyar nan bayan ga yadda mukayi da ke wama kika tambaya da zakije.?” 

Hawaye ta somayi

“Saif saboda ka daina sona kake min haka ko? Shiyasa ka sakeni bayan kuma ka mayar da ni kaki yarda na dawo gidan ka, washe garin dana dawo ka taka jirgi kabar kasar nan dan kuma na faɗawa Dad yayi sanadiyar dawowarka shine zaka hauni da matsifa, saboda ka ga ina sonka Saif ko shiyasa kake son karkata zuciyarka zuwa ga wata ko?, 

Mi yasa kake son wulakanta ni Saif yanzu one year da yin Auren mu amman ace har saki ya shiga tsakanin mu, What is next kuma?” 

Kuka ta saka mashi marar sauti, shikan ido kawai ya sakar mata dan gaskiya ma tayi mishi yawa, 

Kamar da wasa sai gata har kasan carpet tana kuka mai karfi. 

   Sai da tayi mai isarta sannan ya duka ya rikota suka zauna saman gado, fuskarta ya rik'a, 

“Dubi yadda kika bata fuskarki da kuka kamar karamar yarinya, wane Mak'aryacin ne yace na daina sonki?” 

“Haka ne mana Saif” 

“A'a ba haka bane Huda har gobe ina sonki sakin da nayi miki sheɗan neda kuma halin nan naki dan ki chanja, kuma babu wata yarinyar da nake so banda huda” 

Ya k'arasa maganar yana jan hancinta, 

Sai a lokacin ta tsagaita kukan “Toh mi kaje yi new york?” 

“Mamanta ce tace na taimaka mata kar ta rasa yarta” 

“Ni dai na daina bana so” 

Murmushi yayi “Toh shi kenan na daina” 

Da sauri ta kalleshi “Da gaske?” 

“Eh mana tunda uwargida na bata so ai dole na daina abun har da su kuka ba zan sake ba tunda Huda ta bata so”

Murmushi tayi ta shigar da kanta cikin jikinshi, shi kuma ya shiga aika mata da sakwanni yana zolayarta.



MINAL..... 

Haske ne ya doki fuskanta sakamakon buɗe labulen ɗakin da Sarah tayi, 

Hakan yasa ta farka ta ja bedsheet tana lulluɓewa, 

“Ohhh Sarah I'm not done yet” 

Baki Sarah ta buɗe “You don't done what? Please wake-up baby you already done”

Har ta juya sai kuma ta juyo tana shafa gashin kanta “And before I forget Deen is on the phone” 

Da gudu Minal ta sauka saman gadon har tana kokarin ture Sarah, 

“Oh my Deen” Kamar wata karamar yarinya ta k'arasa gaban wayar ta dauka ta kara a kunne, 

“Hello Deen” 

Daga can cikin wayar aka amsa mata, 

“Ya kike Deen ya enjoyment?” 

“Komai Kalau kaifa?” 

“Nima kalau Sarah tace min kina jindaɗi haka ne?” 

“Eh haka ne ba nida wata damuwa a nan” 

Shiru ya ɗanyi sannan yace “Baki tambayi Mummy ba” 

B'ata fuska tayi kamar yana ganinta “Oh Deen please don't kasan banason maganar ta” 

“Na sani Deen amman fa ta damu sosai kuma kinsan tana sonki” 

Shiru tayi bata ce komai ba jin hakan yasa ya ɗauko mata wata firar, 

Sun daɗe suna waya daga bisani sukayi sallama.



K'arfe 8am Saif ya shigo part ɗin Dad, faɗa sosai Dad yayi mashi sai da yaji ba daɗi daker ya samu Dad ya saurara mishi, 

Hak'uri Saif ya bashi sannan ya tashi ya nufi part ɗin Momi, itama sai da tayi mishi nata faɗan kamin daga bisani ya jata da fita, 

 Sai uku da wani abu ya bar gidan bayan ya gama cin abinci, 

Kai tsaye gidansu Minal ya nufa, da tunane tunane ya isa gida, har ya zauna parlor pictures ɗin Minal dake hannunshi yake kallo, 

   Bai daɗe da zama ba Dr. Salamatu ta fito yadda Saif ya ganta sai duk ta bashi tausayi, duk tabi ta rame kamar ba ita ba, 

    Jiki a sanyaye ta zauna ganin dawowarshi da pictures ɗin Minal a hannu haka ya tabbatar mata da baiga Minal ba, 

Tasowa yayi ya karaso kusa da ita ya mika mata pictures ɗin 

“Ban samu ganinta ba” 

Karɓa tayi tana faɗin, 

“Babu komai Saif kayi kokari Allah ya saka da alheri” 

Hannayenshi yasa aljihu, 

“Babu komai yima kaine ki yi ta mata addu'a shine kawai mafita” 

Kai ta gyaɗa mishi ta share hawayen da suka zubo mata.

“Ba'a sameta ba ko?” 

Budurwar ce ta fito tana tambaya, 

“Eh ba 'a sameta ba Kairat” 

K'araso tayi kusa da ita ta zauna tana faɗin

 “Daman nasan ba za' a taɓa samun Sister ta sai ta hanya ɗaya” 

Daga Saif har Dr. Salamatu kallonta suka, 

“Ta hanyar Deen!” 

“Wanene Deen?” Saif ya Tambaya, 

“A bokinta ne ko kuma nace Amininta duk wani abu nata mai muhimmanci yana hannunshi ta yarda da shi sosai bata kaunar bacin ranshi ko kaɗan ina ganin ma shi ne ya shirya mata yadda tabar kasar nan” 

Dr. Salamatu ta amsa mishi, 

Ido ya tsurawa Kairat ɗin kamar mai karantar abu a fuskarta, can ya ɗauke kai yace

“Yanzu ya za'ayi na same shi?” 

Da sauri Kairat ta tashi ta nufi ɗaki “Ina zuwa” 


Bata daɗe ba ta fito rike da wani ɗan karamin kati ta mika mishi, “Wannan shine address ɗin shi” 

Jimmm ya ɗanyi kamin ya mika hamnu ya karɓa, ya dade yana kallon card ɗin sannan ya tashi ya fice.



NEW YORK..... 

Babu abinda suke sai ciye ciye sun cika ɗaki da waka suna ihu kamar wasu sabbin mahaukata, 

Sam basu lura da Telephone ɗin dake ringing ba, sai da suka je chanja waka, 

Da sauri Sarah ta nufi gurin wayar, 

Tana ɗauka ta kwalawa Minal kira da gudu ta k'araso jin ance Deen ne ya kira, 

Tana kara wayar a kunne kamin tayi mishi magana yayi mata cikin wata irin murya tana karkarwa, 

“Minal kiyi min wani taimako karna rasa raina Please” 

“Miya faru Deen?” 

“Ina son ki bar New York yau yau ki dawo Nijeriya idan ba haka ba zan iya rasa raina” 

“Miyasa Deen mi yake faruwa?” 

“Kawai kizo idan baki son na rasa raina kinji?” 

“Ok gani nan zuwa” 

Nan ta aje wayar ta nufi bedroom, Sarah ta rufa mata baya tana tambayar ba'asi, 

   Cikin yan mintuna ta ɗauki Passport dinta da Atm ta fito, sosai Sarah taso ta hanata zuwan amman sam taki yarda, ganin haka yasa dole tayi Driving ɗinta Airport, 



6:24AM...... 

Ta iso Nijeriya ta tari taxi, bata ajeta ko ina ba sai Gidan Deen, 

Fita tayi tana faɗin “Ina zuwa kaji?” 

Kai kawai ya ɗaga mata ta nufi cikin gidan, 

Ko ina sai da ta duba cikin gidan amman bata ga Deen ba balle alamunshi, 

Tsoro ta soma ji , da sauri ta nufi gurin da tasan ya saba aje wayoyin shi, ɗaya gada cikin wayoyin ta sauka ta danna mushi kira, 

Ringing ɗaya aka dauka amman ba'ayi magana ba, 

“Deen gani gidanka kana ina?” 

Ya ɗan daɗe kamin ya amsa mata “Ok gani nan zuwa” 

“Ok” 

Na  aka katse wayar, ido ta tsurawa wayar, ta zauna saman kujera dan sam ta manta da mai taxi dake waje, 

Bayan wasu tan mintuna taji parking ɗin mota, tashi tayi ta nufi kofar fita, 

Kamin ta k'arasa Saif ya shigo tsaye tayi tana kallon shi har ya k'araso kusa da ita sannan ta shiga leka bayan shi, 

  Ganin ba Deen yasa ta tsara gefenshi da niyar fucewa, 

 Fisgota yayi da karfi ya dawo da ita, 

“Ina zaki.?” 

Yana tambayarta ta tambayeshi, 

“Ina Deen” 

Fuskar Saif a haɗe yace, 

“An salami mai Taxi” 

“Bashi na Tambayeka ba ina Deen?”

Baki ya taɓe yasa hannunshi aljihu ya ciro wayarshi ya danna kira, nan da nan akayi picking, Hands-free yasa ya mika mata wayar, 

   Deen ne cikin rawar murya yake magana, 

“Please Deen duk abinda yasa ki kiyi rayuwata na cikin haɗari” 

Jikinta a sanyaye tace “Ok Saif mi ya faru da kai?” 

Kamin yayi magana Saif ya fisge wayar ya kashe, 

Nan ta kalleshi 

“Mi kayi mishi?” 

“Banyi mishi komai ba yanzu dai zanyi mishi idan baki yi yadda nake so ba” 

Ido ta tsura mishi wani irin tsanar shi take ji amman babu yadda zata yi dashi sai ido, 

  Badan taso ba tace “Na amince zanyi yadda kake so amman Please kada ka cutar dashi”

“Bani Atm ɗinki da passport” Da sauri ta girgiza kai “A'a bazan maka haka ba ask something else” 

Kujera ya nuna mata alamar ta zauna, tana juyawa ya fisgota yasa hannunshi aljihunta ya ciro Atm da passport har da wasu yan kananan takardu, ya jefar da ita saman kujerar.

[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...! 


No comments

Powered by Blogger.