Babban Goro 6


 BABI NA SHIDA___6


Cikin yan mintuna suka isa, 

Sara na yin parking ta kalli Munal Minal suka tuntsire da dariya, da gudu suka fita motar suna a rigaggan shiga cikin gidan. 

   Minal ce ta riga kaiwa tsakiyar parlor, tsayawa tayi tana juyi da dariya, 

    “I really don't know how much I miss this place” 

Kai Sarah ta girgiza daidai lokacin da k'arasa kusa da ita, 

“Maybe a million”

“Nope” Minal ta faɗa tana juya ido, 

“Thousands” 

“Nope” 

Sarah ta zauna saman kujera tana faɗin

 “Oops you really don't missed it at all” 

Faɗawa Minal tayi saman kujerar tana dariya,


BAYAN AWA UKU... 

 Minal ce jingine jikin windon kitchen tana kallon flowers,

Wani iska ne maidaɗi yake kaɗawa sai faman sauke ajiyar zuciya take tana. 

   Sarah na jingine jikin kofa, tana kallonta ba tare da ta sani ba, 

“Mil Deen ya faɗa min kinyi kokarin kashe kanki kuma kin gudu kin zo nan ba tare da sanin kowa ba miyasa?” 

Kamar daga sama Minal taji maganar, da sauri ta juyo ta kalleta, 

Can kuma ta ɗauke kai ta ratsa gefenta ta fice daga kitchen ɗin

   Rufa mata baya Sarah tayi tana faɗin, 

“Nima baki son faɗa min ko.?” 

Tsayawa Minal tayi cak. Ganin hakan yasa ita ma Sarah ta tsaya bata k'araso kusa da ita ba, 

“Deen ya faɗa miki komai Sarah” 

Ba tare data juyo ba take maganar, 

Sarah ta ɗaga mata kai

 “Eh ya faɗa min baki son maganar”

Juyowa Minal tayi idonta cike da hawaye, da yaren faransanci tace, 

“Wadda zan Aura ya guje ni, kuma matar da nake zama tare da ita take kulani tana yi min gata ashe ba ita bace Mahaifiyar data haife ni ahalin da nake yanzu ban san waye Mahaifina ba basan a ina iyalina suke ba bani da kowa ni kaɗai nake”

Sanyi jikin Sarah yayi ganin yadda hawaye ke zuba a idon Minal, 

K'arasowa tayi kusa da ita ta rungume ta. 

“Shhhhh ki daina cewa baki da kowa bai kamata ki damu ba har yanzu ba ke kaɗai kike ba muna nan tare a koda yaushe ni ina nan a tare dake Deen ma yana tare dake kuma ba zamu taɓa rabuwa ba” 

Maganar take tana buga bayan Minal alamar lallashi,

Sun daɗe a haka kamin Minal ta sake ta, ta wuce bedroom. 

Fridge Sarah ta nufa bayan ta buɗe ta ɗauki wata farar kwalba ta nufi ɗakin da Minal ta shiga,

  Zaune ta tararda ita tsakiyar godo idanunta a rufe ta dafe kai tana girgiza shi. 

Kwalbar Sarah ta mika mata “U need a fresh brain Mil” 

D'agowa ta fara yi tana kallon kwalbar kamin ta mika hannu ta karɓa, 

“Thank you” 

Ta faɗa tana lumshe idanunta da sukayi ja saboda kuka. 

Murmushi tayi mata “Your welcome” 

Ta kai hannu ta ɗauki car keys dake saman drawer, ta nufi kofa tana faɗin, 

“I'm out” 

Kai Minal ta ɗaga mata, 

“Ok take care” 

“I will” Ta faɗa tana kokarin rufe kofar.

Minal sai da taji tashin motar sannan ta buɗe kwalbar ta dagata sama ta kafa a baki, 

Bata dire ba sai da taji babu gurin iska a cikinta sannan ta sauke kwalbar tana haki, 

  Nan da nan wasu ruwa suka tarar mata idanu, 

Kai ta girgiza jin jirin da ya soma ɗi banta, tafi minti biyar a haka sannan ta sake kai kwalbar a baki ta shanye ragowar. 

D'aga kwalbar tayi sama tana kakkaɓewa daga bisani ta jefar da ita,  

“Oh i need more” 

Cikin magagi tayi maganar kamar mai jin bachi, tana kokarin mikewa tsaye,

   Sai da ta kai tsayen jiri ya ɗubeta ta faɗi kwance saman gadon, 

wani irin numfashi ta rik'a ja tana juya ido har bachi yayi gaba da ita.



21:42GMT......

Saif ya sauka masaukinsa sai da ya huta sannan ya shiga bedroom ya sakarma kanshi shower yayi alwala ya fito,

Wani farin yaɗi ya saka marar nauyi, ya shinfiɗa carpet ya kabbarta sallah,


SOME MOMENT LATER.... 

Kwance take saman gado bayan ya kare cin abinci, sai faman gyasa yake yana shafa ciki, 

Babu wadda ya faɗo mashi a rai sai Huda da sauri ya tashi ya ɗauko wayarshi daman tun cikin jirgi ya chaja sim. 

Nan ya shiga saka number Huda, ringing tayi ta yi sai da ta kusa hankewa sannan aka ɗauka, 

“Hello dear” 

Shiru tayi har sai da ya ɗauka ta katse, sannan tace

“Kaga yarinyar da kaje nema?” 

Cige bakinshi yayi, 

“Wace yarinya kuma? Mi kike nufi ne?” 

ciki da mamaki yayi maganar,

“Oho ni ina na sani Dad dai yana son magana da kai” 

Tashi yayi daga kwance da yake zuwa zaune, 

“Ina Dad ya ganki?” 

“Gidan naje ɗazu bayan fitarka” 

A takaice ta amsa mishi, faɗa ya shiga mata 

“Wa kika tambaya da zaki je? Ba zaki zubar da halinki ba ko? Kuma kinsan... -” 

Shiru yayi jin ta katse wayar, yayi murmushi jin haushi, 

“Lallai yarinyar nan yayi miki kyau” 

Ya daɗe tsaye yana girgiza kai kamin ya shiga danna ma number Dad calling. 

    Cike da fargaba yayi sallama, bayan Dad yayi picking, bai amsa Sallamar ba ya haushi da faɗa, 

“Me kaje yi a new york? Kayi yimin karya kayi ma matarka karya kace nine na aike ka sai ka faɗa min sakon da na aikeka karɓowa” 

Shiru Saif yayi ya rasa abinda zai ce, 

“Baka ji nane kayi min shiru mi kake son maida kanka?”

Nan ma shiru yayi yana jin faɗan har cikin ranshi, 

    faɗa sosai Dad yayi mishi sannan ya bashi umarnin barin kasar gobe da safe, 

Jiki na kwari Saif yayi mishi Sallama, ya faɗa saman kujera yana busar da iskar bakinshi, 

“Ni mi ma yasa na kiraki?” 

Tsaki yaja, 

“Wallahi ba ki da kirki ko kaɗan” 

Nadama yake sosai na kiran Huda da yayi, ya daɗe  zaune gurin yana tunane tunane daga bisani ya tashi yayi shirin bachi.

No comments

Powered by Blogger.