Zafin Kai 4


 _*ZAFIN KAI*_

_Mamuhgee_

4

Rasuwar samirah ya taba Annensu sosai fiyeda yanda suka saba hadiye kowane irin yanayi dazai riskesu

Qwaqwalwanta ya sake tabuwa sosai dan haka kusan koda yaushe tana daki a zaune zugum bata komai haka take wuni haka suke kwana da ita,


Sumayyah ma rasuwar ta girgizata tareda firgitata sosai itada safnah ta yanda a yanzu amon muryarsa kawai dukkaninsu fitar dasu hayyacinsu yake jikinsu ya shiga rawar tashin hankali.


Biyayyarsu ta ninku fiyeda baya,

Tsoronsu ya qaru fiyeda baya,

So da kaunar junansu ya karu a zukatansu fiyeda baya haka zalika tausayi da kulawan mahaifiyarsu da suka duqufa yiwa adduar samun sassaucin tabin kan nata sbd qarasa juyewar qwaqwalwanta na nufin Ababa zai iya miqata ga titi ta qarasa haukacewa acan wanda sukuma a yanda sukeji rabuwa da mahaifiyarsu kaman abu ne da mutuwace kawai zata rabasu.


Safnah a yanxu da komai yayi tsanani bata tinanin kowa da komai face kanta,

Mafita take nemarwa kanta koda ta mutuwar ce itama tabi samirah ta huta…


Lokacin rasuwar yaja sosai addua da kulawar dasukewa maihaifiyarsu yasa ta dan dawo daidai lokuta da dama a hankalinta take duk da hakan kusan gabaki daya Ababa yasa dokar karta fito ta ringa zama a daki sbd idan yana ganin yanayinta zai iya kaita gidan mahaukata idan akwai.


Jin hakan yasa suke killaceta a daki sam basa barinta fitowa idan ba bandaki ko alwala zatayiba,


Sauki na samuwarta sosai Hande tasa tadawo Ayyukan da aka saba da ita na wahalar.


Bai taba yarda da kowaba a rayuwarsa bayan kansa

Hande data haifesa bata taba sanin komai daya danganci samu ko dukiyarsaba,

A koda yaushe sune suke masa lissafi a gabansa tas sbd sunada kokari akan ilimin da suka dan samu daga karatun da sikai.


Sun rungumi kaddara sun rungumi rayuwar dasuke ciki sbd suna kiyaye komai girman doka da umarninsa da dukkanin imaninsu,


Abu daya ne yake girgiza jarumta da zuciyar Benazir shine duk lolacinda safnah ta furta kalmar barin gida sai taji zuciyar ta wani irin nauyi da faduwa,

Ba iya damuwa da tsoron abinda zai iya faruwa da safnah din bane idan Ababa ya kamata kaman yanda yakama samirah koma dai menene tasan ba lallai akwai alkhairi tattare da hakan bane.


Dukkanin halaye dake bayyanarda boyayyan son iya kai dake zuciya da jinin safnah yana bayyana ne tun data busar da zuciyarta ga son tserewa kota halin yaya tabar gidan.



********a shekaru yanzu bazasu wuce sha bakwai zuwa sha takwas ba sumayya ce mai sha tara zuwa ashirin,

Dukkaninsu kyawawa ne duk da kasancewarsu ba masu hasken fata ba sosai,

Mahaifiyarsu Anne marainiya ce da Ababa din yayi shaawar aurenta sbd batada kowa batada mai tsaya mata a duk rayuwar da yayi niyar yi da ita,

Batada uwa bata uba sai kakarta bara sukeyi ya aureta ko wata baa rufa da aurenba kakarta ta rasu ya tattara ya baro garinsu da ita da mahaifiyarsa ya dawo birni ya dasa sabuwar rayuwarsa anan inda yake sanaar dabbobi da kasuwancin babban shagon fata da kuma yawon kai manyan shanu da raguna garuruwa,


Bazaa kirasa mai kudi ba hakama bazaa kirasa talaka ba sbd cinsa da shansa da buqatunsa basufi karfinsaba,

Dukkanin masu aiki a karkashinsa basa jin dadinsa sbd mutum ne mara yarda da rashin daukar asara komai kankantarta baya dauka,


Baya shiga harkar kowa ba ruwansa da duk abinda zakayi koda mutum zaka kashe a gabansa zai iya wucewa bai shiga aikinka ba sbd duk duniya ya tsani a shiga nasa lamarin,


Tunda ya ware kansa daga anguwar dakeda mutane sosai ya dawo irin anguwannin karshe karshen gari inda babu mutane sosai ya kafa iyalansa da rayuwarsa harkokinsa kawai yakeyi,

Babu wanda yasan irin munanniyar rayuwar datake gudana acikin gidansa sbd basa zuwa gidan kowa kaman yanda bayason ana zuwa gidansa idan ba qaruwa yakeyi da kai ba,


Duk tsananim azaba da ukubar da yayansa suke ciki jikinsu baya nunawa sosai sbd kyan fatarsu dakuma fitar da basayi suna killace a gida kullum sai hakan yasa fatarsu take kaman a fresh haka zalika sunada jiki mai kyau,


Baida wanda ya tsana ya bude ido a duniya yagani kamar ‘yayan nan hudu mata da Allah ya basa,


Duk wani tinanin mafita akan yanda zaiyi dasu yayi sbd yanda ciyar dasu kawai kecin wani dan bangare na arzikinsa,

Idan baya qaruwa da kai sam bakada wani amfani ko darajar da zaiyi muaamala dakai,

Komai nasa akan lissafin qaruwa yake,


Anne wadda asalin sunanta yake banazir ita nata amfanin dan yana biyan buqatunsa na aure ne akanta shiyasa baya neman yanda zaiyi da ita din amma a yanda hauka ke neman shigarta daga ranarda ta tabbata ta haukace bazai barta ta qara kwana daya ba a gidansa bakuma tareda ‘yayanta zata tafi ba dan su lissafinsa akansu mai girma ne saiya fanshe komai nasa dasukaci tsaf da yardar Allah.


Dukkaninsu bayan sumayyah datake ta farko babu wanda shine ya rada masa suna a cikinsu

Hande ce take rada musu suna 

Benazir kuwa sbd tsanarta datafi ta kowa ita kanta Hande kasa saka mata sunan tayi shiyasa Annen ta mayarwa ‘yar da sunanta ta saka mata BENAZIR wadda acikinsu itace baa yankawa ragon sunan dayake yankawa sauranba wanda yana yankawa yake siyarda rabi rabin a soya masa yaci abinsa sauran a dan rarrabawa mayun makota masu nacin zuwa idan an haihu din shima hande ce take rabawar sbd itakuma duk wata barna da ‘danta yakeyi tsayawa takeyi ta boye  shiyasa take faran faran da jamaar waje ta yanda babu wanda zai taba sanin halinda Anne da ‘yayanta suke ciki duk da shi rashin gata da rashin kulawar dasuke samu a bayyane yake amma babu me tankawa sbd zafi da tsananin rashin daukan hakuri a lamarinsa.


Duk wanda yasan Ababa da kalmar zafi da masifar son abin duniya zai fara fassara maka shi,

Akan kudi dala babu abinda yake kunya ko wanda yake kunya kai tsaye yake ba kwana kwana ba shakka a takaice zaka iya dorasa a sahun riqaqqun jahilan komai bayan na Nera.



****Ayau sun wayi gari jikin Annensu yayi tsananin tashi ga wani irin zazzabi mai qarfi daya kamata

Kallo daya zakayi mata tausayinta ya kashe jikinka sbd ciwo ne a jikin wanda baya cikakken hayyacinsa,

Bata jin ciwon zazzabi da juyin qwaqwalwar datake samu,ciwo ne a zuciyarta datayi mata wani irin nauyi da sankarewa batajin komai bata gane komai sai fuskar ‘yayanta guda ukun dake gabanta tsananin sonsu na sake toshe kirjinta,


Maqalqale Safnah tayi tareda kafe sauran da ido bata iya cewa komaj sai jijjiga kanta datakeyi da karfi tana murza idanuwata dasukai wani irin ja na azabar ciwon dake cinta amma batasan me zatace ba batama san meyake mata ciwon ba ita.


Wani irin kuka sumayya ta fashe dashi mai ciwo da rashin sauti tana riqo hannuwan Annen datake sake matse safnah da karfi kaman zata illatata,


Safnah ma hawaye takeyi tana hana kukanta sauti kaman sumayya din tanajin zuciyarta na nauyi sbd tasan kila Anne taji a jikinta itama rabuwa zasuyi wata kila ta dawo ta fanshe su da kudi a hannun mahaifin nasu idan har ta tsira wata kila kuma rabuwarsu ce ta har abada bazasu sake haduwaba…wasu hawayen ne masu zafi suka gangaro mata tana kallon Annen wadda  itama ita take kallo amma bata iya magana sbd daman idan abin ya motsa bata iya magana.


Sunkuyar da kai sumayyah tayi tana tsananta kukanta hannuwanta na toshe bakinta ganin hawaye na gangarowa daga jajayen idanuwan Annen,


Benazir datakai hannu ahankali ta share hawayen annen jin tsananin zafinsu yasata fashewa da wani irin kuka mai tsananin ciwo sbd zafinsu ya tabbatar mata da dole a tsananin hali Annensu take amma bata iya fada.


Kukan benazir yasa dukkaninsu sake fashewa da kuka a tare mara sauti hadda Annen data ga ‘yayanta na kuka cikin kunci musamman ganin kukan Benazir yasa kukansu qaruwa dan ba qaramin qunci kesa Benazir din kuka ba.


Sunaji suna gani suka baro Annen a daki tareda safnah dataqi saki suka fara ayyukansu sbd basason Hande tasan jikin annensu ya tashi Ababa na dawowa zata fada masa dan haka suka ringa boye boye dan karta gane.


A dakin kuwa Safnah kai tsaye ta bude baki ta sanar da Annensu tafiya zatayi idan ta mutu kaman Samirah ta yafe mata.


Gabaki daya rikicewa jikin Annen yayi da kalaman safnah wanda ya sata fita hayyaci haukar ta taso tuburan dan haka ta kirawa sun benazir suna zuwa hankalinsu ya tashi take suka daddaureta a dakin suka hanata motsi sbd Hande naji zata kira Ababa a waya 

Idan ya taddata a wannan halin a yau zai rabasu da ita

A yanzu da baisan gidan mahaukataba wani gurin zai iya kaiita ya saki tabi duniya ta yanda bazasu taba ganinta ba ko Allah yasa sun tsira a gaba.


Fizge fizge takeyi sosai tana hawayen radadin zuciya duk da tana cikin hali na gushewar hankali radadin uwar da zata rasa yarta cin zuciyarta yakeyi gashi su benazir basusan abinda Safnah din ta fada mata ba jikin nata ya rikice hakan,


Har dare suna cikin tashin hankali da boye boye dan zuwa lokacin har bakinta suka rufe suna kukan wannan azabar ta dauretan da sukayi ba dan ransu ya so ba amma basuda zabin daya wuce hakan tunda suna tsananin son abarsu ko me zata zama.


Safnah kuwa shedan samun damar tsayar mata da zuciya yayi akan Amafani da ciwon Annen ta gudu sbd a yanzu takai gabar da itama ta rasa nata hankalin qwaqwalwarta na gab da juyewar kaman ta Anne koma fiye,


Kusan dukkaninsu idan aka cire Benazir qwaqwalwarsu kaman ta dade ta tabuwa baa ganewa ne sbd basa tareda kowa haka basuda yanci ko na haukar.


Yanda suka rana haka suka ga dare sbd a zaune dukkaninsu suka kwana sbd yanayin jikin Anne daya kasa sauki ko kadan

Duk wani qarfinta ga qare a fizge fizge takai har bata iya motsawa sai hawayen dake bin gefen idanuwanta

Idanuwanta kuwa kaman zasu fado waje tsaban ja da fitowarsu.


Koda sukai sallar Asuba basu saketa ba dan bazata iya sallah ba a halinda take ciki saidai idan tadawo daidai tayi rankon salloli,


Koda suka fito babu mai iya bude idanuwansa har karshe sbd kumburin kuka dan haka duka aikin  sukayi kansu a qasa kada a gane.

#MAMUH#

#DEEP

#LIFE

#PURE

#LOVE

#MARRIAGE

#BILLONAIREROMANCE

#BENAZIR


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-FURAR DANKO

Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at

09033181070

09032345899


Zafafa🫶🔥🔥

No comments

Powered by Blogger.