Saran Boye 72

 


No. 72


...........Washe gari bayan sallar asuba Nu'aymah ta ɗorama Yoohan karatu kamar yanda suka saba. Daga haka ya shiga ɗakin motsa jikinsa. Ita kuma sai tayi amfani da wannan damar ta shiga ɗakinta domin ɗakko hoton nan. Duk da ta jima bata shigesaba ta fahimci an canja mata zaman wasu abubuwa da dama. Wasuma babusu. Bata bar hakan ya dametaba ta nufi Wadrobe direct inda ta ajiye hoto.

Sosai gabanta ya faɗi ganin yanda kayanta suka koma a harmutse ba yanda tasan sukeba. Cikin gigita ta shiga tiɗosu ƙasa tana faman zazzagewa. Sai dai kamar da wasa babu hoto babu labarinsa. Hankalinta ya tashi, har takaita da duba indama tasan bata ajiye ɗinba amma ko mai alamarsa babu.

        Jagwab ta zauna a bakin gado tanabin ɗakin da kallo daki-daki, dan sai a yanzune ma harmutsewarsa ba yanda ta barsaba yake dawo mata a zuciya daki-daki. Yoohan ta fara kawowa a zuciyarta. Sai kuma ta girgiza kanta dan bata tunanin zai mata bincike. Can ƙasan zuciyarta yace, ‘Omar ne. Bashi kika sanarma maganar hotonba’. Nanma da sauri ta girgiza kanta alamar a'a. Gebrail. ‘Kai bazai zama shiba. Dan shi manufarsa daban data masu hankali. Wannan bashi da man kai akan hakan’. Madam Chioma. Nanma a fili tace, ‘Kai ina bana sata a wannan layin dan kanta baya ja tacika kidahumanci kamar kifi’. ‘To wa zan zarga?. Ko dai papa ne?’. Mikewa tai da sauri tana kaɗa kanta hannayenta duka biyu a saman cikinta. ‘Lallai tabbas shine abin zargina, musamman daya kasance ya riga yabi diddigina akan shigar masa ɗaki da nayi, zai iya kasancewa tunaninsa ya basa zuwa nan yamin bincike. Shin minene wannan mutumin ke ɓoyewane akan mijina? Lallai ya kamata na sani kafin na sake barin ƙasar nan’. Sai kuma ta dafe goshi cike da damuwa. ‘Hoto shine kawai hope ɗina. Gashi yanzu ɗan barahazar ya sace min, bayan na gama baza bayani wajen Abbana da wannan Umar ɗin. Kenan dolene na sake satowa. (Idan bai ƙonaba ko?) zuciyarta ta ayyana mata. Karan farko da matsanancin tsoro ya risketa. Da sauri ta fita a ɗakin zuwa can cikin gidan. Gidan shiru alamar masu gidan babu wanda ya tashi kasancewar weekend ne. Kitchen ta nufa. Tako iske Blessing kawai tana haɗa breakfast kamar yanda tayi hasashe.

       Ko gaisuwar Blessing ɗin bata amsaba taja hannunta suka shige cikin store. Sai da ta leƙa ta tabbatar da babu kowa sannan ta tura ƙofar store ɗin ta rufe ta juyo ga Blessing da jikinta harya fara rawa. “Please ki nutsu, ba wani abu bane tambaya zan miki, ina fatan kuma zaki bani amsa kamar yanda kike bama Omar... Oh sorry Richard”.

      Cike da tsoro Blessing zata fara rantse-rantse Aymah ta tsaidata......

      “Karki wahal da kanki wajen mani rantsuwa nasan komai daga wajensa. Inason nasan zuwan Richard nawa gidan nan?”.

     Da tsoro sosai a fuskar Blessing tace, kusan bakwai”.

          “Dama can anan yake sauka kenan tunkan aurena da Yoohan kokuwa a yanzune yake sauka anan?”. 

      “Eh dama yana sauka gaskiya, amma sai Oga yana ƙasar”.

     Jimm Nu'aymah tayi alamar tunani, sai kuma tace, “Mikike tunanin yana zuwa yi nan gidan?”.

    Cike da tsoro sosai Blessing ta buɗe ƙofar kaɗan ta leƙa, hakan yasa Yoohan daya biyo Aymah yake a laɓe saurin komawa ya lafe a bango. sai da ta sake tabbatar da babu kowa sannan ta dubi Aymah murya can ƙasa sosai. “Na yarda dake sosai Aunty na, dan tun a zuwanki gidan nan na fahimci ke mutuniyar kirkice wlhy. dan haka zan sanar miki komai duk da nima ba komai ɗin na saniba”.

     “Okay ina saurarenki”.

“Tun bayan wucewarku Austria nakeji wasu maganganu masu gidan nayi a kanki. Dan akwai randama na taɓajin an bada kwangilar kasheki ta hanyar likitan da zasu miki aiki. To sai dai kwanan mutuwarki bai rigada yazoba dan ke ƴar baiwane. Sai akazo baki mutuba. Su boss sunje dubaki, bandai san miya faruba bayan dawowarsu Uncle Richard naga ya nacema zuwa gidannan. Sanan yakan sani na masa wasu abubuwa akan boss ko madam ɗin gidan nan. Sannan ko baya gida zai kirani yaji mi akayi ko mi ya faru. Badai komai nake fahimtaba gaskiya, tunda banida hurumin yin komai. Sai dai matsalar dana fuskanta shine randa su papa suka shiga sashenku ita da Solomon da Madam. Sun miki bincike a ɗaki sai dai basu sami komaiba suka fita. Bayan hakan Uncle John yazo ƙasarnan yaga yanda akai miki da ɗaki shine ya zane Gebrail a tunaninsa shine ya shigar miki. A zahiri papa baicema Uncle John komaiba akan dukan Gebrail. Amma bayan barinsa gidannan ba ƙaramin rikici akayiba tsakaninsa da maman madam dama madam ɗin. Shima kuma papan naji yana wasu maganganu tsakaninsa da Brothers ɗin nan nasa wanda ban ganema kansuba sam. Wanann rikicin ne ya saka su Maman Destiny barin gidan nan. Dan sun nuna goyon bayan Uncle Yoohan fiye da Gebrail. Shine yasa akai rikici duk suka wuce. Bayan nan kuma sai Uncle john ɗin da yazo last time madam ɗin gidan nan ta shigar masa ɗ.........”

      Da sauri Yoohan dake a laɓe ya rin tse idanunsa tare da shiga kiran sunan Nu'aymah tamkar ya shigo nemantane. Rikicewa sosai Blessing tayi, amma Aymah ko'a jikinta saima ɓata fuska tayi ta buɗe ƙofar bayan ta ɗebo noodles guda biyu. 

       “Oh Sweet boo ganinanfa a store. Nazo amsar noodles ne a wajen Blessing shine take nunamin inda take”.

            Cike da mamaki yake jinjina wayonta. Amma shima sai ya waske yana mai dafe kansa da faɗin, “Kinsa duk na ruɗe na fito ban gankiba a gaba ɗaya sashen”.

      “I am sorry Hubby”.

“Silly girl yana iya dake. Yanzu yaya za'ai da Noodles ɗin?”.

     “Zan dafa ne anan”. Ta faɗa saboda son ya barta ta ƙarasa jin zance a wajen Blessing.

     Fahimtar hakan da yayine ya sakashi hayewa saman kitchen cabinet ɗin yana cewa, “Okay dafa to mu wuce. Dan kinsan akwaima fa inda zamuji ga lokaci nata ƙurewa, Omar ma jiranmu yakeyi tuni. Koma kibama Blessing ɗin ta dafa miki muje ki shirya data gama sai kici kawai”.

     Duk da Aymah bataso hakan ba sai ta amince kawai. Dan ita bama cin noodles ɗin zatayiba sam. Blessing ta ƙwalama kira. Sai gata ta fito da sauri hannunta ɗauke da abinda zata dafa da rana irin dai shi ta tsaya ɗebowa. Sai dai kallo ɗaya Yoohan ya mata ya fahimci tsoron dake tattare da ita.

    Bata dahuwar noodles ɗin tayi suka fice. Gaba ɗaya hankali Nu'aymah akan Blessing yake. Amma Yoohan yay mata tsayuwar sojan badakkare aka komai tare sukayi. Koda suka fito Blessing ta kawo noodles ɗin catai ta ƙoshi. Sai Yoohan ɗinne yaci tare da Omar. Dama yasan baci zataiba ai. Dan tunda ta samu cikin nan tabar cin indomie sam.

      Koda suka gama ficewa sukai a gidan batare da sunbi takan kowa ba. garama mama debora sun haɗu da ita a falo tana shan shayi. Tako hanasu fita saida akaima Aymah addu'oi ita da cikinta. Dan tace ita yanzu ta daina yarda da madam Chioma a gidan sam😂🤣.


     Ita dai Aymah yanzu tsohuwar birgeta takeyi. Dan har suka bar gidan batabar murmushi ba akan abinda ya faru.

    Tafiyarsu ta ɗanyi nisa Omar ya fahimci ana binsu a baya. Shima Yoohan ya gani amma baice komaiba. Dan babu abinda zuciyarsa ke masa sai tariyar zancen Aymah da Blessing. Tunaninsa wane abu ne Aymah ke zargin an shigar mata ɗaki akansa ana nema? Sannan kuma ashe papa ne da madam Chioma suka shigar masa ɗakin mata hardama Solomon?. wane bincike Umar keyi akan iyayen nasa?  Mi Aymah ta shiga yi ɗakin papa a wancan karon daya dage kareta a wajensu amma hardayin ƙaryar taga wanda ya shiga ɗakin ashe itace?  Miyasa mahaifinsa yasa a kashe masa mata? Dolene yasan waɗanan tambayoyi a lokacin ƙanƙani insha ALLAHU.

    Da wnanan tunani da yakene yasa har Omar ya gudama masu binsu shi baisan yaya akaiba. Sai ganinsu kawai yayi a station ɗin su Jay.

         Aymah dai har suka shiga tana maibin wajen da kallo tare da jami'an tsaro. Ko ɗar batajiba duk da ta fahimci wajene bana wasan yaraba. Yau saɓanin ranar Office ɗin Jay aka kaisu direct, acan suka sami Dawood da Little bee da bily. Sai Afrah da adalilin zuwan Aymah Jay yasa akazo da ita. Dan ita karatun lauyanci takeyi batabi ayarin su little bee ba.

      Duk da a hoto sukasan juna ita da Aymah hakan bai hanasu gane junaba. Suka rungume juna kuwa cike da ɗoki dan sunyi sabo sosai ta chart da waya. Daga haka Aymah ta gaida little bee dake zaune tanata danne danne a Computer alamar miskilawan na kusa. Dan duk ihun dasu Aymah sukeyi ko kallo basu ishetaba, aikinta takeyi hankali kwance. Gaisuwarma a haka ta amsata. Sai daga baya ta ɗago ta kalli Nu'aymah sannan suka gaisa dasu Yoohan.

    Nu'aymah dai bata sake bi takantaba itama ta juya ta gaida Dawood da Miemaa data amsa mata da fara'a da kulawa, dan itama ta taimaka mata ta zauna a kujera. Daga haka ta gaida Jay da a kallonsa sai da gabanta ya faɗi. Duk da ba tsananin kamanni suke da Yoohan ba dolene kaga yanayin gittawar jini tattare a tsakaninsu. Duk da ba mutum bane shi mai yawan wasa saida ya tsokaneta kaɗan. Har hakan ya bama su Yoohan mamaki. Dan su dai ba taɓa ganin dariyarsa sukaiba tunda suke mu'amula da shi.

     Sai da aka lafa da gaishe-gaiahe Jay ya fara magana.

       “So ba shirita ne ya taramu ananba. Inason ku bani hankulanku nan gaba ɗaya. Da farko dai kece bakisan dalilin zamanmu ananba duk da mijinki ya tabbatar mana ta hanyarki yasan wasu abubuwan. Sai ko Afrah da sanin nata baida muhimmanci daga tushe duk da itama da taimakonta ne muka samu bayanan sirri game da gidanku. So yanzu little zata miki sabon bayani, ke kuma Afrah jeki waje ki jiramu”.

     Sosai Afrah ta ɓata fuska kamar zatayi kuka. Cikin magiya tace, “Abie Please ka barni dan ALLAH, wlhy nima zan taimaka muku da wani abun kaimafa ka sani. Duk da ba aikin nan nakeba so nawa ina muku aiki ta ƙarƙashin ƙasa”.

    Fuska ya haɗe zai mata magana Aymah da duk kwarjininsa ya cika mata idanu tace, “Abie dan ALLAH, indai hakan ba laifi bane ka barmin Aunty zanfi samun ƙwarin gwiwa nima”.

      Kasa cewa komai Jay yayi, ya kai dubansa ga little. Da wani style na ƙwarewar aiki taima mahaifin nasu alamar roƙon yabar Afrah ɗin. Dan itama tana hasashen tasirin zamanta a wajen.

     Ɗauke kansa kawai yayi ya maida ga Yoohan dake ta kallonsa kamar ya samu television. Sai kuma ya ɗauke ya sake maidawa ga little bee alamar ya bata damar yima Aymah bayani.

    Tsaf ta gama yima Nu'aymah bayanin komai. Dan haka taketa duban Yoohan da Umar cike da mamaki. Da damuwa a harshenta tace, “Amma Yah Yoohan baka gudun Abbana kar yaga ba'a ƙyauta masaba. Sam baya son laifin jama'ar gidan nan namu, shiyyasa yake ƙoƙarin maida laifukansu kuskure dan gudun lalacewar zuminci”.

      “Zeeynab inhar muka cigaba da bama Uncle goyan baya akan hakan tabbas sai an salwantar da ran ɗaya daga cikinsu ko ke ko Muhammad a wannan gidan naku. Dan ni nasan mina ganarma idona a Austria da wasu maban-banta wajaje dangane da ke”.

     Bata iya tace komaiba dan tasan gaskiya Yoohan ya faɗa. Bandama ALLAH yasa tanada sauran kwana a duniya ai da tun tana jinjira an aikata barzahu ɗin. Sannan shima Muhammad ɗin ai ansha gwada rayuwarsa a mabanbanta lokuta Abba na ɓoyewane kawai........

     Cikin katse mata tunani Jay yace, “Karki damu akan Sheikh, ni zan masa bayanin dazai gamsu akan hakan. Yanzu zamu tafine kai tsaye akan abinda ya taramu anan tunda kin gama jin bayanan farko. Dan dama munsa mijinki ya dawo dake ƙasarnan ne dan zamu ɗanaki a gidanku ne matsayin tarko. Dawood minene bayani akan binciken wayar matar nan da aka sakeyi?”. Ya ƙare maganar da maida hankalinsa ga Dawood.

       Takardun gabansa ya ɗauka ya fara bayani. “Sir bayanan sununa tabbas ana amfani da wayarta batare data saniba. Kamar maganar yin waya da mai aiki da aka turoma matar Yoohan anan Abuja, sam ba Rabi bace ke waya da Uwaliya. Mun tabbatar da hakane ta hanyar binciken ainahin muryar da aka samu a voice recording ɗin nan. Haɗine ta hanyar makirci babba na masu ilimin sani akan na'ura mai ƙwaƙwalwa. Suna amfani da wani app... Ne da aka saka cikin wayar matar, dama kowacce waya idan ta sake sai suke sarrafa wayar tata daga wajensu batare da ita ta saniba, suna barin mata bayanan abinda sukai da tasu wayar, dan ko an tashi bincke ita za'a zarga kai tsaye. Hakan yana nufin kenan tun fil azal da aka kawota gidan dama akwai manufa a ciki, kokuma daga baya aka fara amfni da ita. Waɗanan sune tatattun bayanai akan ainahin contact dake a wayar Rabi wanda suke aiki da saninta. Waɗanan kuma sune ainahin waɗanda ake amfani da ita ta wayar batare data saniba. Kuma insha ALLAHU zasu taimaka mana mu zaƙulo kosu wanene masu aikata hakan kamar yanda Abdurrahman Sameer Saifudden ya bamu tabbaci, dan shine yay wannan bincike gaba ɗaya tun daga ƙasar india. Ya kuma tabbatar mana idan ana buƙatarsa zai iya zuwa koshi ko abokan aikinsa yan uwan tagwaicinsa kenan”.

       Cikin jinjina kai Jay ya amshi takardun yana duban little bee. “Bilkisu! Minene bayanan wajenki akan zaman Afrah gidan?”.

      Juyowa Little bee tayi da kujerar da take a kai tana fuskantarsu. Yoohan ta sake kallo kamar yanda dama tuni shi take kallon a sace bisa ƙyaƙyƙyawan nazari datakeyi akansa tun farkon fara ganinta da shi.

     “Sir! Bayanan dake anan sun nuna wasu sunaye da Afrah ta rubuta akan zarginta, saboda wasu al'amura da suke aiwatarwa a gidan na marasa gaskiya. Akwai Rabi. Mai aikinsu, a yanzu tana a hannunmu. Sai Mai aikin sashen Addah, sai ita kanta Addah da tafi kowa kusanci da Umm a gidan. Sai Nasir wanda asali shi bama ɗan gidan bane yana zuwane lokaci-lokaci. da wasu sunaye a jerin ɗaliban Uncle Soorajidden ɗin. Ta tattara waɗan nan sunayen ne bisa dalilai mabanbanta da suka faru akan idonta da kuma yanda labarin yazo garemu. Zamu iya jin bayani daga bakinta gata nan idan da buƙatar hakan”.

        A yanzu kam bily ce tai wani gutun murmushi tana kallon Jay. Cike da nuna ƙwarewar aiki tace, “Boss niko kaga a duk jerin sunayen nan mutum uku kawai naba ayar tambaya. Sauran kuma inaji a jikina basa zaune a cikin gidan. Abinda yasa nai wannan maganar shine duk lokacin da za'a cutar da ita Nu'aymah akan yine lokacin wani taro a gidan. Hakan na nufin akwai mazauna gidan dake zaune a waje cikin tafiyar. Amma ƙasurgumin azzalumin yana nan cikin gidan tare da su ko akasin haka. 

     Murmushi Jay yayi a karo na farko. Ya sauke numfashi da ɗan buga pen ɗinsa akan takardar gabansa. “Tabbas komai zai iya kasancewa. Dan suma sauran ai hasahe mukeyi, tunda ga Rabi a hashe muka samota kuma sai gashi babu laifinta”.

     “Hakane kuma boss. suspect ɗinmu na gaba sune, Nasir, Ameer, Hamisu, Kubrah, Abdallah. Da iyayen su Abdallah n”.

     Da sauri Aymah tace, “momy!” cikin zaro idanu. sai kuma ta shiga girgiza kanta da sauri-sauri tana cigaba da faɗin, “Bazai kasance hakaba Momy. Uncles ɗina suna matuƙar son Abbana. Hakama Yah Abdallah na matuƙar sona. Bazasu cutar damu ba sai dai idan Nasir ne”.

     “Relax Nu'aymah. Muma bamun tabbatar bane hashene kawai. Dan dolene mu alaƙanta laifin nan da mafiya kusanci da iyayenki dake kanki, shiyyasa zamuyi amfani da wannan lokacin da mukasan duk ahalinki zasu taru a gida saboda bikin aure da saukar yaran gidan marayunku mu ɗana musu ke a matsayin tarko wajen damƙesu batare da sun fargaba.....”

        Yoohan ya katse Bily da cewar, “Humm tabbas Momy bana tantama akan hakan. Musamman akan Abdallah. Dan ta dalilinsa na sakama sauran ayar tambaya. Abdallah yayi fushi yabar Nigeria saboda ba'a aura masa itaba. Amma kuma a bayan fage yana a cikin ƙasar, dan yana yawan shigowa akai-akai. Sannan kuma yana bibiyar al'amarinta dani kaina. Dalilina na biyu a kansa shine wani business da yakeyi a ɓoye batare da sanin iyayen nasaba. Dalili na uku akwai harƙalla akan aurensa da yara biyu na gidan da aka aura masa dalilin sace Zeeynab da akai ranar wancan auren nasu. Ya saki yaran batare da ɗaya ta tare ba. Wadda ta tare ɗin bincikena ya tabbatar min da tasha wahalar zama da shi. Zargi na uku. Akan hotona da aka kai gidansu ni da ita. A yanda labarin yazo kakarsu bata bari su Abdallah sunga hotunanba a waccan ranar, amma daga baya sai hotunan suka zo hannun Abdallah harya kaisu office ɗina. Hakan na nufin bayan na hannunsu akwai wasu kenan dama a wajensu komi? Zargi na biyar, Abdallah yafi kowa ɗaukar zafi akan hotunan a gidan, duk da kuwa nasan Uncle da Umm sai sunfi kowa jin raɗaɗi da zafin hakan game da tilon ƴarsu. Amma sai ya nuna zaƙewa akan hakan harda kawomin abokinsa wai yay Arresting ɗina. Zargi na ƙarshe, miyasa a duk lokacin da akai tunanin ƙulla aurensu sai wani dalili ya ruguza shi?......”

       “Please Yah Yoohan ya isa haka mana. Miyasa dukanin zarge-zargenka zai ƙare akan Yah Abdallah? Kana kishi da shi ba shike nufin komai ka yaya ka aza a kansaba”.

      Sosai zantukan Aymah suka zafi zuciyar Yoohan, dan gani yake matar tasa tana goyen bayan tsohon saurayin natane kawai. Sai dai kuma uffan baice akan hakanba, yama ɗauke kansa daga gareta kawai.

     Karan farko little bee ta saki murmushi tana kallonsu. Sai kuma ta taɓe baki da faɗin, “Wannan faɗane da ya shafeku a gidanku Mrs and Mr”.

    Hararta Yoohan yayi, dan dama tunba yauba yana jin haushin yanda take zaman yimasa kallon ƙurilla a fakaice. Yana nuna bai gani bane kawai saboda kunyar iyayenta.

     “A'a bar hararata malami, ni yanzu saina sassafa ka a gaban sahibar taka babu ruwana”.

       “Ashe kuwa mijinki ma zai sassafu a hannuna tare da wannan miskilar fuskar taki mai ƙinyima mutane dariya”.

      Harara itama little ta zuba masa tana tsuke fuska. “Oh kace dama kullum cikin takaicina kake bana maka murmushi, to ƙwalelen kare da hantar kura”.

     Baki Yoohan ɗin ya taɓe da ɗauke kansa gefe yana cije lip. Dan saiya saita yarinyarnan akan layi kafin a gama case ɗin nan. shi babu ruwansa da wani ƴar-sandancin ta ehe. (Kuji ƙarfin hali irin na Yoohan. Da alama mafa little bee ɗin zata bashi shekara ɗaya a duniya, amma wai yarinya😂lol)

      Babu wanda drama ɗintasu baisa dariyaba. Sai Jay da Bily basu dara ɗinba a fili sai a zuciya. Sundaita kallonsu cike da nazarin suɓutar harsunan nasu. 

        Kai jay ya girgiza kawai yana katse little dake son ƙara magana. “Kunga ku aje wannan shirmen naku sai kun fita can sai kuyi, idan kunso ku sassafa kawunan naku munada likita a kusa da zai duba ku. Yanzu dai Yoohan dole a yau ɗin nan Nu'aymah ta wuce kano. Dan aikin nan banason ya shige satin nan bamu kammalashi ba. Maganar Abdallah kuwa na tabbatar jin Nu'aymah na Nigeria zaizo shima koda a ɓoyen daya saba ne. Yanzu zan baza jami'ai da zasu fara bibiyar lamarin motsin kowa na gidan idan ya fito. Shima Nasir ina buƙatar a jawomin hankalinsa yazo kano. Babu sanya a aikinmu, duk wanda mukaci karo da rashin gaskiyarsa zamu kamasane mu tuhumesa kamar Rabi. Za kuma mu maida Rabi itama dan wayarta zata taimaka mana sosai wajen zaƙulo abubuwa”.

     Cike da gamsuwa kowa ya amsa masa. Duk da kuwa Yoohan dai da alama baiso yin nisa da matarsaba. Amma ya fahimci hakan zai taimakesa gameda ƙudirin papa kuma a kanta. duk da kuwa a kanon ma wasu kurayen zata tarar. amma gara can akwai jami'ai masu sanya ido a lamarinta.


________★


     Koda su Aymah suka dawo gida bata ga Blessing ba. Hakama Madam Chioma da papa da alama basa gidan ma. Yara kawai suka tarar da Mama debora. Joy ta wuce makaranta, Miracle kuwa mama debora ke basu labarin wai ta haɗa kayanta ta koma gida.

     Ko a jikin Yoohan. Aymah kuwa yar dariyar shaƙiyanci tayi abinta ta wuce sama cike da tunanin ina Blessing ta shiga. Ɗakinta ta nufa direct, ta fara zame kayanta zuciyarta taf damuwa akan maganar hoton nan. Agogonta data cire ne ya faɗi ƙasa. ta ɗan matsa baya tana dubawa ta tillesa da ƙafa yay ƙarƙashin gado. Abin ya bata haushi, dan harta barsa akan yayta zama sai kuma taji tanason ɗakko kayanta dan Yoohan ya batashi matsayin ƙyauta a ranar da suka cika shekara ɗaya da aure. Fita tai ta ɗakko mopping stick dan Yoohan bai shigoba har yanzu yanacan tare da mama debora. Durƙusawa tai gaban gadon batare da damuwa da cikin dake gabantaba saboda wauta. Ta kunna fitilar wayarta ta haska. Da ƙyar ta iya hango agogon ta saka mopping stick ɗinnan ta turosa a hankali. Sai da yazo dab da ita ta fahimci harda wani abu take jawowa. Hannu ta miƙa danta jawosu duka ta kasa. Dole ta sake zungurowa da iccen mofa ɗin sannan suka fito. Jikinta har rawa yake wajen fara ɗaukar envelope ɗin ta buɗe. Tai wani irin waro ido na al'ajabi da mamaki. Batama san sanda ta ƙwaƙume hoton a ƙirjiba saboda murna. Jin an taɓa ƙofar za'a buɗe tai saurin sakin hoton ƙasa, kafin Yoohan daya shigo ya ƙaraso ta tura hoton ciki yanda bazai ganiba.

       Duk da ta masa alamun rashin gaskiya sai bai nuna yama fahimcetaba. Yay baya da fiɗin, “Oh ashe kina nan, bara na watsa ruwa saiki shirya kema zuwa biyar na yamma zamu wuce kano. Amma mi kikeyi ma a durƙushe anan? Bayan kinsan bake kaɗai bace?”.

     Miƙewa tai tana nuna masa agogon data ɗakko. “Kaga abinda na yadda nan na ɗakko”.

     “Ki kulafa, dan na fahimci har yanzu wautanki na nan”.

    Baki ta kumbura da iska batare datace masa komaiba. Shima sai ya juya abinsa ya fice kawai ya barta batare daya sake maganaba. Sai dai bai rufe ƙofaba. Da wannan damar ya samu zarafin laɓewa kozaiga mitakeyi. Aiko tana ganin ya fita ta sake duƙawa ta ɗakko hoton tana ambaton ‘Alhmdllh ya ALLAH. Da banga hoton nanba da bazan taɓa yafema duk wanda ya ɗaukesaba. Dolene nasan wacece wannan mai kama da mijina ɗin insha ALLAHU’.

     Dukkan maganganun Aymah a cikin kunnen Yoohan ne. Hakan yasa zancen tsaya masa a rai tare da son jin ganin hoton nan shima. Yayi kamar zai dawo sai kuma ya fasa. Akan idonsa ta maida hoton a Wadrobe. Tafiya yay ɗakinsa tunda yaga inda ta ajiye. Sai dai kamar tasan yana kallonta. Yana barin wajen ta ɗauke hoton ta sakashi a ƴar jikkar data haɗa kayan tafiya kano wai dan kar wani ya sake shigo ya sace mata. Tana shiga wanka Yoohan ya dawo duba hoton. Sai dai kuma komai kama da shi bai ganima. sai ma kamashi da Aymah taso yi ALLAH dai ya taimakesa ya gudu. 

      Haka suka kammala shirin wucewa kano mamakin atsabibancin Aymah na damun Yoohan, shi ganima yake ta gansa shiyyasa ta canjama hoton waje.

     Itako Aymah ranta fal baƙin cikin rashin ganin Blessing da Yoohan yasa tabar gidan har sai sun wuce dan bayason ta sanamar Nu'aymah abinda ya faru tsakaninsa da Momynsa.


*_KANO TA DABO_*


          Ƙarfe bakwai dai-dai jirgin su Aymah ya sauka a kano. Batare da sanin kowa daga ahalintaba har su baba malam. Sai da Yoohan yasa suka fara biyawa sukai shopping na tsarabar da zata kaimusu sannan suka wuce gidan.

        Ganin Aymah da Yoohan ya saka mai gadi buɗe musu gate mai taxi ya shiga har ciki. Nu'aymah zata fita da kwakwazo Yoohan ya riƙota yana girgiza mata kai. “Please kibi a hankali, a ganinama ba gara ki shige babu wanda ya san da zuwanki ba da safe sai kiyi musu surprise”.

    Baki ta ɗan tura gaba. Sai kuma tai saurin sakin dariya da cewa, “Yes Yah Yoohan kayi gaskiya kuma”.

     Murmushi yay mata da bata sumba a gefen kumatu. Daga haka suka fito a motar. Gidan shiru kowa yana a sashensa, hakan yasa Yoohan taya maigadi kaima Aymah kayanta bakin ƙofa. Sannan ya turata ciki ya sulale ya koma taxi ɗin suka fice. Dan hotel yake son guduwa kafin baba malam su fito massallaci su ritsashi.

     Umm na zaune a bedroom tana karatu da jiran lokacin sallar isha'i sai ji kawai tai an rungumeta. A firgice ta juyo dan harga ALLAH ta tsorata. Ta waro idanu sabida mamakin ganin wadda batayi zatoba. 

     “Nu'aymah wai kece da gaske?”.

Kukan murnar ganin Umm ɗinta ta saki tana faɗin, “Nice Ummna, I miss you so much”.

       Rungumeta Umm tayi da ƙyau a jikinta itama ƙwalla na cika mata idanu. Kai ɗa dabanne gaskiya. Sanin ba ita kaɗai bace yasa Umm tadata daga durƙuson da tayi a ƙasa ta zaunar da ita a bakin gado. Gaba ɗaya Aymah sai kuma taji kunyar Umm ta mamayeta, sai ta duƙar da kai ƙasa tana ƙara lulluɓe cikinta da gyale. Dariya abin ya bama Umm sosai. Sai dai bataiba. Saima tambayarta tai ina mijin nata?. 

   Kan Aymah a ƙasa tace waje ta barsa ita dai suna kwaso kaya shi da maigadi. Jin haka yasa Umm fita ta leƙa. Sai dai babu Yoohan babu dalilinsa sai maigadi kawai dake shigo da kayan ɗan barandar falonsu. Shine ke sanar mata Yoohan ɗin ya juya tare da mai taxi akan da safe zai dawo insha ALLAH.

      Kai kawai Umm ta girgiza ta koma ciki, inda ta iske Aymah ta fito daga toilet da alama fitsari tayo. Cike da kulawa tace, “Kinji mijin naki ya tafi wai zai dawo da safe. Dama kunyi dashi hakan?”.

     “A'a wlhy Umm, ni kawai yace na shigo zaije massallaci ne”. Tai maganar cikin ɓata fuska. Murmushi kawai Umm tayi ita dai, tace, “To kiyi wanka kawai sai na samo miki abinda zakici ke tunda shi ya gudu. Cike da kunyar Umm ɗin data aro ta yafama kanta ta amsa da to. Daga haka ta koma toilet ɗin danyin wanka.


         Babu wanda Umm ta sanarma da zuwan Nu'aymah a gidan sai hajjo. Sai ko Muhammad daya dawo massalaci ya ganta a bazata. Baba malam ma sai da ya sallami ɗalibansa ya shigo yaci karo da ita a falo zaune ita da Hajjo da Umm da Muhammad dake liƙe da ita.

     Tuni Nu'aymah ta manta da kunya, ta miƙe da sassarfa ta nufi Abbanta dake kallonta cike da kewa da so da ƙaunarta. Gabanta tai niyyar durƙusawa ya riƙota yana faɗin, “A'a mamana keda ke fama da kanki. Irin wannan zuwa haka na bazata”.

    Hannunta yaja ya maida a kujera sannan shima ya zauna. Kanta a ƙasa ta shiga gaisheshi cike da kewa. Shiko yana amsawa da kulawa. Abakin Umm yaji cewar Yoohan ya gudu. Dariya kawai yayi dan ya fahimci kunya Yoohan ɗin keji da alama.

        Haka sukayi murnarsu su huɗu kawai. Ganin dare ya farayi Hajjo taje sashenta danta kwanta. Aymah kuwa a ɗakin Umm zata kwana tare da Umm ɗinta data bar baba malam shi kaɗai.

     Aiko maimakon barci sai suka buɗe sabon babin hira ita da Umm ɗin, sai da suka kusan kai asuba sannan barcin ya kwashi Aymah, daga nan itama Umm tayi.


__________★


        Washe gari kam a bazata kowa yaga Nu'aymah a gidan. Kafin kace mi sun rikice da murna da hayaniya. Tun Aymah na ƙunshe-ƙunshen ciki harta saki jikinta ta shige cikin ƴan uwanta anashan shafta. Zuwa tashin hantsi kuwa sai ga Hajarah tazo gidan, dan ita dama tasan da zuwan nata. Rungume juna sukai cike da farin ciki. Yanda suka nuna ɗin har mamaki ya bama kowa. Dan gaba ɗaya salon shaƙuwar Adawiya da Nu'aymah ne ya koma kan Hajarah a yanzu.


      A ranar da yamma suma ƴan Abuja suka iso. Ganin Nu'aymah kuma ya matuƙar basu mamaki dansu da suke Abujan ko a labari basusan da zuwan nataba. Har Momy ma sai da ta kasa haƙuri tai complain ɗin cewar Yoohan bai ƙyautaba. Suna matsayin iyayen Nu'aymah amma yazo da ita har Abuja bai fara kaita canba sai dai suzo su ganta anan tsulum.

     Daga karshe dai Yoohan ɗinne da yazo gidan ya kare kansa akan wannan tuhuma. Dan Aymah bata iya cewa komaiba tunda itama tunanin zuwa can ɗin baizo mataba. Zumuɗinta kawai azo kano.

     Ya bama su baba malam haƙuri akan rashin tsayawarsa jiya. Acewarsa aikin gaggawa ne ya samesa shiyyasa bai tsayaba. Duk sun masa uziri akan haka. Sannan suka ɗora da godiya akan hidimarsa ga gidan marayunsu daketa ƙara nunkuwa a koda yaushe. Akan bikin nanma kawai da za'ai ba ƙaramin hidima yayiba.


      Washe gari baƙi suka fara cika gidan, ƴan katsina, ƴan lagos da sauransu, kowa kuwa yana sake yaba yanda Aymah ta ƙara girma da canjawa a cikin shekara ɗaya kacal. Gashi daga gani ansan ta samu lafiya yanzu. Sai dai fatan ALLAH ya sa ta sauka lafiya kuma.

    Da yamma sukaje can orphanage akai walima, anan ta haɗu da sauran yayunta su Kubrah. Tayi mamakin ganin yanda Aunty Kubrah ɗin dukta lalace. Harta kasa haƙuri ta tambayi aunty Hajarah. 

    Cike da damuwa Hajarah tace, “Humm Aymah ke dai ALLAH ya ƙyauta, zaman natane babu daɗi daga ita har mijin da kishiyar. Kwanaki ai kusan watanta biyu a Lagos wajen Abbah Musbahu. Sunyi faɗa ya daketa shine taje can”.

     Kasa magana aymah tayi saboda damuwa. Kodai babu komai Kubrah ƴar uwartace duk da a yauma ta nuna har yanzu ba sonta takeba.

    Duk wannan hidima da akeyi kuwa su Aymah zagaye suke da yaran Jay ta ko ina. Motsin kowa akan idonsu yake faruwa. Tun daga orphanage har cikin gidansu.


    Washe gari juma'a aka ɗaura auren amare ashirin da takwas maza da mata. Kowa ya kalli su baba malam yasan suna cikin farin ciki. Sai dai ai fatan ALLAH ya basu ladan hidimarsu ga marayun ALLAH babu gajiyawa.

    An miƙa amare ɗakunansu, daga haka baƙi suka fara raguwa sai na jiki kawai aka bari. Kamar yanda Jay ya samu tattaunawa da baba malam a ranar ɗaurin aure a yau suka yanke hukunci bisa shirinsu. Duk da kuwa da ƙyar baba malam ɗin ya yarda da buƙatar Yoohan, Jay, Omar ɗin. Dan basu ɓoye masa komaiba game da shirin nasu gudun kar a samu matsala.  

      Tun a yammacin ranar baba malam ya fara takalar Umm da batun mallakama Nu'aymah wasu kaddarorinsa dan yasan lallai mai musu laɓe na tare da su saboda tuna Nu'aymah tazo garin ya fahimci mai laɓen ya ƙara ƙaimi wajen yimusu. Ta riga tasan shirinsu, itama sai ta biye masa. Sai dai zancen bai tsahoba suka barshi akan zasu ƙarasa da safe dan lokaci baba malam nada uziri..........✍


No comments

Powered by Blogger.