Saran Boye 64


 No. 64


............Motar ta ajiyesu a wani ƙauyene dan iya nan kawai zata iya shiga saboda uwar zaizayar ƙasar dake damun ƴan kudancin ƙasarmu duk ta cinye titunan. Ruwa mai uban sanyi na kwatami madam Rebecca ta samu ta sheƙama madam Chioma saboda sunyi-sunyi ta fita a motar ita da drivern madam Chioma da giya ke aiki a kanta taƙi fita.

      Firgigit ta kawo numfashi tana wani bada faɗi tamkar zata make mutum. Duk baya sukaja kam suka bata fili. Sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta share fuskarta tana hararsu. 

     “Rebecca minene haka kuma?”.

Dariya Rebecca tayi tana miƙama yaron data ari roba a wajensa. “Inda ba hakan nai mikiba zaki tashi ne. Lokacin da ya bamu ya kusa cika kuma kinsan halinsa”.

      Zabura kuwa madam Chioma tayi ta wawuro handbag ɗinta tana ambaton Jesus. Haka yasa itama Madam Rebecca ɗaukar tata handbag ɗin suka zagaye zaftarewar ƙasar suka koma kan titi sosai. Suna tafiya suna ƙoƙarin tare mashin dake wucewa. Amma kowanne sai kaga da mutum. Sai da sukai tafiya mai nisan zango sannan suka samu mashin ɗaya. Badan zai ishesuba suka hau, dan madam Rebecca balaifi tanada jiki. Tafi madam Chioma ƙiba. Haka suka shirma cikin jejin da korayen ciyayi suka ƙawata suna nishin matsuwa. Tafiya sukai sosai kafin su isa wani ƙauye again. Anan mai mashin shima ya saukesu dan zasu hau kwale-kwale ne. Ga madam Chioma da tsoron ruwan masifa. Duk sanda sukazo wajen bokan nan a tsorace take. Shiyyasa wani lokacin tafi buƙatar Rebecca tazo mata sai ta biyata kuɗin da duk ta buƙata. Haka suka shiga kwale-kwale tanata faman ƙunshe kanta a cikin cinyoyi. Tafiyar mintuna ashirin ta kaisu gaɓar ruwan. Daga haka kuma suka kwashi ƙafafunsu suka nausa cikin jajenin da bazaka taɓa ɗauka akwai mutum mai numfashi a wajen ba. Amma da yake zukatansu sun bushe ko tsoro basaji. Sun iso ƙauyen da bokan yake a galabaice. Kamar yanda ƙa'idar shiga wajensa take suna isowa ƙofar fadarsa suka cire duka suturar jikinsu. Haka masu tsaron ƙofar suka basu hanya suka shiga tsirara haihuwar uwarsu (😱🤦🏻). Ba wannan ne ya firgitaniba. Dan su nasan komaima iya aikatawa zasuyi. Shigarsu wajen ne ya rikita tunanina da ɗarsa tsoron duniya a raina. Dan kuwa mutanene cike da wajen suna jiran layi kowanne tsirara yake. Abin kaico da takaici da ALLAH wadai harda musulmai a wajen, kai harma Hausawa saika samu ma'abota son duniya da ruguza lahirarsu. Manyan mutane ƴan siyasa da hasashenka bai taɓa baka ganin irinsu a wajenba sai gasu tumɓur suna zazzare idanu a fadar boka. Manyan mata masu neman duniya da gudun kishiya suma gasu nan ba'a magana. Wannan ya ƙara tabbatar min da sutura na rufawa bawa asiri a idanun mutane. Dan da yawan mutane munana ne idan ka gansu tsirara wlhy🙄.

        Sai da suka tsaya gaban wasu ƙartai akai musu wankan ƙa'ida kafin su ƙarasa su hau layi inda sauran suke. Suna nan zaune masu shiga na shiga suna fitowa har layi yaxo kansu suka shiga suma.

      ‘Wa'iyazubillah’. Ɗakin bokan cike yake da gumaka na dodannin tsafinsa ta kowace kusurwa. Suna shiga suka zube sukai sujida a gaban waɗanan gumaka. Kafin su miƙe zuwa wajen bokan dake hakimce a kujera sai kace sarki. Shima sujidar sukai masa sannan suka miƙe tsaye haihuwar tsoffinsu. Shima dai a tsirarar yake dama🤦🏻. Gashi ƙaton gaske mummuna baƙiƙƙirin matsiyacin sheɗani. Kallon madam Chioma yayi ya kece da dariya, sai da yayi mai isarsa sannan ya haɗe fuska.

      “Yaron da kike tattali da burin mallaka yana neman ƙuɓuce miki ko? Hhhhhhhh!!!!. Ai tun farko kece kikai sakaci. Miyasa kika barsa yay aure?”.

      Kuka ta fashe da shi, “Bangaruta ba laifina baneba. Mijina nane ya cikani da daɗin baki akan ya yarda yaron ya aureta ne dan ya halakata da babanta. Shiyyasa na yarda ni kuma. Tunda nasan ka bani abinda bazai iya taɓa kallon mace da suffar mata ba”.

        “Hhhhhhh!!!!!. Yardarki kuwa ta zamar miki matsala. dan wannan yarinyar daya aura tafi ƙarfinki. A duk inda take tana zagaye da wani haske da ko iya ganinta ni kaina banayi. A yanzu haka bana iya ganin yaron ma kansa a ƙwaryar tsafina saboda kasancewarsu tare. Ke koma basa tare shima bana ganinsa a watannin nan gaba ɗaya.....”

      “Bangaruta ka taimakeni ta tsafemin shi. Na shiga uku shikenan tawa ta ƙare”.

       “Hhhhhhh taki zata ƙarene idan wannan aikin dazan miki yazam bai kamasu ba”. 

      Da sauri ta nutsu tana sharar hawaye. Ya kuna ƙyalƙyalewa da muguwar dariyarsa mara daɗin ji. Kamar yanda na faɗa miki tun farko aikinmu dake kansa bazai taɓa barinsa mu'amula da mataba sai ke. dan haka ki kwantar da hankalinki wannan kam tabbatacciyar maganace hakan bazai faruba. Yanzu zakiyi ƙoƙarin rabasa da yarinyarne kawai. gaba ɗaya hankalinsa zai dawo gareki a wannan karon dan bazamuyi masa da wasa ba”.

       “Nagode Bangaruta, sai dai kumafa igiyar nan ta tukunya ta kwance, wannan shine ya girmama tashin hankalina”.

     “Karki damu da kwancewarta, mu ta wajenmu tana nan a ɗaure. Dan bazai taɓa kwanciya da wata maceba sai ke. Cike dajin daɗi ta duƙe gabansa ta sakeyi sujida🤦🏻😭. A take ya haɗa mata duk abinda zatayi akan Yoohan da Nu'aymah. Ta dire masa maƙudan kuɗin daya buƙata sannan suka fito bayan itama Rebecca ta amshi nata aka abinda ya shafeta.

     A ranar suka sake juyiwa cikin River state a matuƙar galabaice. hotel suka kama zasu kwana sai zuwa da safe su koma abuja.


_____________________


     *_VIENNA AUSTRIA_*


     Su Yoohan da basusan wainar da ake toyawa ba sunacan hankalinsu kwance. Dan wani shagon cin ƙwalam da maƙulashe na kalolon chocolate da ice-creem ya kaita. Ko sha zumamu baya faɗama Aymah shan zaƙi ba. Tako dinga lodama cikinta cike da farin ciki. Duk gargaɗin da yake mata akan tabi a sannu saboda duk zaƙin da take danƙara zai tambayetane a wajen period bata sauraresaba. 

         Sun daɗe sosai a wajen, kafin su fito da ƙafa kamar yanda ta buƙata wai tanason taga gari da ƙyau. Aiko ta gani ɗin. Dan birnin Vienna ya matuƙar haɗuwa da gine-gine masu ƙayatarwa. Sai da ta fara hakkin gajiya sannan ya tsaida musu keken doki suka shiga ya maidasu masaukinsu.


        Suna isowa wanka Aymah ta shiga. Sai faman complain take wai ƙafafunta na ciwo.  Baice mata komaiba shi dai tunda itace ta ja musu shan wahalar ai. Amma da yake ta fisa baki shine take cewa shine.

    Wanka tayo ta fito tana ɗingisa ƙafa wai ciwo take mata. Da kallo kawai ya bita shi dai, ya ɗan girgiza kansa yana miƙewa da faɗin, Silly girl maganinki kenan ai”.

       Juyowa tai tana hararsa. Sai dai shi baimasan tanayi ba dan tuni ya shige toilet ɗin abinsa. Koda ya fito ya iske har tayi shirin barci. Sai dai bata kwanta ba. Tana kwance a sofa tana kallo. Shirin barcin shima yayi. Yana kammalawa wayarsa tai Ring. Miƙewa tai zata kawo masa sai taga ya nufota. Hakan yasa ta koma ta zauna harya ƙaraso. Yana amsa yaga Rich ne, sai ya maida kallonsa gareta. “Please sa hijjab muje mu ƙarasa maganarnan yana jiranmu”.

      “Okay” ta faɗa tana miƙewa. Ta ɗauki hijjabin sallarta ta saka tare da zura Slippers suka fito harabar hotel ɗin wajen swimming pool ɗin nan da mutane keta shanawarsu tamkar rana. Daga can gefen garden ɗin hotel ɗin suka koma. dan shima dai mutane ne keta hidimarsu. Aymah ta fahimci mutanen nan sam basa banbance dare da rana halan. Dan koda yaushe su dai hidimarsu suke hankali a kwance.

       Zama sukai inda suka iske Richard. Ta gaishesa da ƴar sakewa fiye da ko yaushe. Shima fuskarsa da murmushi ya amsa mata harda tsokanar wai ta ƙwace masa aboki. 

      Murmushi tayi kawai batare datace komaiba. Shi dama Yoohan bai saka bakinsa ba, sai dai ya bama Rich ɗin hannu sun gaisa.

      Bayan an kawo musu Coffee ɗin da yay musu order itama Aymah aka kawo mata lipton data buƙata sai suka fara tattaunawa akan yanda zasu ɓulloma lamarin. Suna gamawa da maganar gidansu Aymah Rich ya turama Joseph saƙo akan ya janye masa hankalin Yoohan.

     Haka kuwa akayi, ko mintuna biyu da tura saƙon ba'ayiba kira ya shigo wayar Yoohan. Ɗagawa yay suka gaisa da Joseph batare da ya tashi ba. Sai daga baya kuma ya miƙe saboda magana da Joseph ɗin yace yanason suyi.

           Yana barin wajen Rich ya kalli Aymah data ɗauke kanta daga garesu tana kallon wata mata da yaranta twins da babansu dake gefensu. Sai soyayyarsu suke zubawa da tattalin ƴan yaran nasu. jitai sun bata sha'awa sosai har tana kwatanta kanta da Yoohan ace yaran nasune wai (ƴar baba malam an fara hankali kenan🤣).

      Gyaran murya da Rich yayine ya sakata juyiwa taɗan kallesa. murmushi yayi shima dan haka kawai yay zargin abinda take tunani akan mata da mijin da yaransu. 

       “Inason muyi magana Please, sai dai tsakanina da ke ne banason Yoohan ya sani”.

      Cike da mamaki ta tsura masa idanun tana tsuke fuska. Saurin girgiza mata kai yayi yana murmushi. “Am sorry sister akan gidansu ne karki zargi komai”.

      Ajiyar zuciya ta sauke a ɓoye da ɗan shafa gefen wuyanta alamun taji kunya. Shima sai ya ƙara murmusawa dan ta birgesa. Hakan na nufin a duk inda take zata karema ɗan uwansa mutuncinsa. Wayarsa ya miƙa mata tare da miƙewa yabar wajen. Can ya koma inda Yoohan ke zaune yana waya dan ya fahimci shima hankalinsa na kansu.

      Binsa da kallo Nu'aymah tayi. sai kuma ta buɗe video ɗin data gani akan wayar, da alama shi Rich ɗin ke buƙatar ta gani. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yayi ba, saboda cinkaro da kanta a ranar data shiga ɗakin papa ta ɗakko hoto. Sai dai iya falone. har shigowar Papa da Andrew falon. Shigarsa bedroom ɗin da fitowarsa da sake komawarsa. Harma fitarta da kayan harƙallar papa da suke magana akai shi da Andrew. Cocaine ce da wasu ƙwayoyi, sai abinda ke cikin ɗayar jikkar dai bai buɗeba, hakan yasa batasan minene ba. Hannu tasa ta sharce zufar data tarar mata a goshi. Ta ƙara playing ɗayan video ɗin dake a ƙasan wancan shima. Shi kuma papa ne da wasu mutane yana bada kwangilar a kasheta duk sanda suka dawo Nigeria. Randa aka kashetan kuma a kashe baba malam shima. ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ ta shiga maimaitawa tana kallon inda Yoohan da Rich suke zaune. Ganin Rich nata jan ra'ayinsa ga barin kallontane ya sakata kauda kanta tana taunar lip ɗinta. A ranta kuwa sake jinjina lamarin papa take da jin tsanarsa a ranta. Lallai saita tona dukkan sauran sirrin mutumin nan duk da kasancewarsa mahaifin mijinta. To amma shi wannan Richard ɗin mi yake nufi da bata video ɗin ta gani?.

     Kafin ta nemo amsar tambayarta taga sun miƙe sun nufota. Fita tai daga cikin folder ɗin da sauri ta ajiye masa wayarsa da ƙoƙarin control ɗin kanta dan kar Yoohan ya gane.

        Rungumeta Yoohan yayi cike da tsantsar farin ciki yana faɗin, “Oh my Sweetheart ke haske ce a rayuwarmu. Rich yace yanason zama musulmi”.

       Cike da razana Aymah tace, “What?!!”. Sakinta Yoohan ɗin yayi yana dariyar farin ciki da jinjina mata kansa. kafin yace wani abu Rich yace, “Tabbas abinda X-man ya faɗa ashine gaskiya Sister. Zama da mahaifinki ya ƙwaɗaitamin son kasancewa musulmi. Hakan ya ƙara tasiri ne a raina a ɗazun dana ganku kuna salla abin ya birgeni”.

      Kallonsa kawai Nu'aymah take cike da tuhuma. Dan gani take wani ƙullinne kuma yake shirin musu ta hanyar shiga musilinci.

     Fahimtar hakan da yayine ya sakashi girgiza mata kai idanunsa na kawo ruwan ƙwalla. “Na rantse da ALLAH ni Richard inason shiga musilinci ne da zuciya ɗaya bada wani daliliba. Ki yarda ke haske ce a garemu kamar yanda mijinki ya faɗa”.

        Numfashi Aymah ta sauke tare da furzar da iska ta lumshe idanunta hawaye suka gangaro mata a hankali. Sai kawai ta faɗa jikin Yoohan ta rungumesa tare da rushewa da kuka. “I love you so much Yah Yoohan”. Ta faɗa a bazata tana ƙanƙamesa da ƙyau. 

       Da sauri Yoohan ya ɗagota yana kallon fuskarta. “Cikin rawar muryar zuwan bazatan maganar yace, “Really? Please sake faɗa naji dan ALLAH”.

       “Babu ƙarya ko yaudara a maganata. Da gaske ina SONKA Yah Yoohan. Na rantse da ALLAH ina sonka da gaba ɗaya zuciyata”. Ta kuma rungumesa.

      Ai gaba ɗaya yama manta da wani Rich dake wajen. cikin sauri yaja hijjab ɗin jikinta ya shige ciki tare da zame mata fuskarta itama ta koma ciki. lalubar bakinta yayi ya manne da nashi. Duk da kunya da tsoron abinda ya faru dake cikin ranta hakan bai hanata tayasa abinda yakeyiba batare da tasan ta zurma ba.

        Dariya Rich ya sanya musu tare da miƙewa yabar wajen, can inda suka baro da Yoohan ya koma ya zauna yana kallon wani wajen daban, zuciyarsa fal da wani irin farin ciki da shi kansa baisan na minene ba.


         Da ƙyar Nu'aymah ta ƙwaci kanta daga hannun Yoohan da ke neman sakin layi. Ta sauka daga jikinsa tare  tabar wajen da gudu. Kasa motsawa yay saboda kasala data saukar masa. Ya kife kansa a table ɗin kawai yana sauke numfarfashi a jajjere.

      Ganin wucewarta da gudu ya saka Rich tasowa inda Yoohan yake. Damtsen hannunsa yaɗan buga da faɗin, “Mara mutunci, a gabana ma babu ɗaga ƙafa”.

        Gani kawai yayi Yoohan ɗin ya miƙe ya rungumesa yana faɗin, “Thanks you Rich, thanks you so very much. Gashi a dalilin gane gaskiyarka ta faɗamin kalma mai tsada dana fidda ran samu daga gareta. Wlhy ina sonta fiye da zaton mai hasashe Rich. ashe itama zata soni. ALLAH na gode maka. Rich ka zama sanadin farin cikina”.

      Dariya sosai Rich keyi ta jin daɗin ganin farin cikin Yoohan ɗinsa da yake tsananin so da ƙauna. Suka zauna kowanne fuska ɗauke da murmushi. Cikin ɗage gira Rich yace, “Dama makauniyar soyayya kakeyi kai ashe?”.

       “Makauniyar da ko idanu ba'a yanka mataba kuwa Rich, amma yanzu ta sanadinka gashi har numfashi ta samu”.

      “To Alhmdllh, dama ni na fahimci tana sonka wlhy. Kawai dai akwai yarinta tattare da itane. But ko dai yayane ma kun dace. Dan na jima banga masoyan da suka dace da junaba irin ku. Dan haka Mr Lover Congratulations joooh”.

        “Thanks you dear. Congratulations too. Nayi farin ciki da kai saurin gane gaskiya. Ya rabbi ka karɓi tubanmu ka gafarta mana”.

     “Emen dear. Yanzu nawane zan biya? A wajenwa kuma zan biya”.

     Fuska Yoohan faɗaɗe da murmushi yace, “Shi muslinci ba'a biyan komai a wajen shigarsa. Kalmar shahada kawai zaka faɗa. Amma bara na kira Uncle first”.

      Kai Rich ya jinjinama Yoohan. Ya ɗauka wayarsa yay kiran baba malam cikin sa'a kuwa ya ɗaga. Bayan sun gaisa yay masa bayanin komai cike da jin kunyar da Aymah ta sakashi a ciki tun ɗazun. Dan duk yau ma ya kasa kiran baba malam ɗin. Yanzun ma shaf ya mantane saboda ɗokin musulintar Richard.

        A take baba malam yace, “Ina mamana? Duk bayanin dazan muku itama zata iya yinsa insha ALLAHU Yahya”.

     Cike da jin kunya Yoohan yace, “Tayi barcine Uncle. Gashi kuma Rich ɗin zai dawo gida nan 9ja gobe. Idan kuma ya bari sai yazo wajenka to”.

        “A'a Yahya. Gara dai ya cikasa niyyarsa dan ranmu ai ba'a hannunmu yakeba. Nasan kaima zaka iya masa bayani akai. indai zaka iya tuna duk yanda kayi lokacin daka musulinta”. 

      “Insha ALLAH Uncle. Amma zanso kana saurarenmu”.

     Dama baba malam ya bashi. Dan haka Yoohan ya maida kiran video call. A take Yoohan ya bama Rich kalmar shahada. Bayan ya maimaita baba malam ya faɗaɗa masa bayanai masu muhimmanci tamkar yanda yayma Yoohan a wancan karon. Sai ga Yoohan da Rich suna hawaye. Sunja lokaci mai tsaho kafin baba   bashi zaɓin suna. A take Rich yace ya bashi dama ya zaɓa masa kowanne.

     Cikin jin daɗi Baba malam yace, “Akwai sahabban manzon ALLAH da sunayensu sukai fice a garemu, bara na lissafa makasu, tare da na Annabawan ALLAH da Yahya ya samu ɗaya daga cikin sunayensu shima”.

    A tare suka jinjina masa kai.

   “Abubakar, Umar, Usman, Aliy.......”

Kafinma baba malam ya ƙarasa Rich yay saurin faɗin, “Uncle inason Omar”.

        “Masha ALLAHU Son. Daga yau kazama Umar. ALLAH yasa ka zama mai koyi da ƙyawawan halayen Umar da gaskiyarsa da jarumtarsa harma da yawan ibada”.

       A tare suka amsa da amin.

Daga haka suka sake ɗan tattaunawa sannan sukai sallama da shi. Masaukin Rich suka nufa. Inda Yoohan ya koya masa wanka da alwala harma da salla. Daga haka ya barsa. Saboda gobe idan ALLAH ya kaimu Omar (Rich) ɗin zai koma Nigeria.

      Sun sake rungume juna suna hawaye da sake godema UBANGIJI. Sannan sukai nafila raka'a biyu a tare ta godiya ga ALLAH. Omar (Rich) yay sallar Magrib da isha'i dan lokacinsu bai gushe ba har sai alfijir ya keto. Musamman ma isha'i.

       Daga haka sukai sallama Yoohan ya nufi nasu masaukin cike da ɗoki da farin ciki.


      Nu'aymah dake kallo tanajin motsin buɗe ƙofar tai azamar kifewa rubda ciki dajan filo ta tura kanta ciki. Murmushi yayi yana ƙarasa shigowa dan ya rigada ya ganta. Television ɗin ya kashe tare da wutar ɗakin lokacin da yake ƙoƙarin hawa gadon. Cikin nutsuwarsa ya kwanto bayanta yana sauke ajiyar zuciya tare da saka hannu ya ɗauke filon data tura kanta a ciki. 

       “Wayyo Hajjo ƙaton nan zai ɓalla miki jika”. Tai maganar cike da rikicin kunya da nauyinsa daya sakar mata.

       Murmushi yayi da rage mata nauyinsa sannan ya birkitota. Da sauri ta kanannaɗe masa jiki dan batason su haɗa ido.

       Hannunsa ya tura cikin rigarta yana ɗora bakinsa akan kunnenta. Cikin raɗa yace, “I love kunyankin nan my sweet angel, my sweetheart my Heartbeat. My everything”. Ya ƙare maganar da ɗan cizar kunnenta kaɗan. 

       Kukan shagwaɓa ta saka mata tana murza ƙafafunta a jikinsa wai saita rama. yanda taketa masa mutsu-mutsu a jikine ya nema susutashi. ƙwaɗayin da yaketa dannewa tun da rana ya kasa dannuwa. Cike da kasala da tsumar jiki ya lalubi bakinta ya manne da nashi. Tun yana tunanin tsayawa iya kiss ya rage zafi har hakan ya nema fin ƙarfin ƙoƙarin nasa. Gaba ɗaya ya birkice mata. Tun tana biye masa da wauta harta koma masa kuka dan bata manta wahalar datasha daren jiyaba. 

        Duk yanda Yoohan yaso haƙuri ya bar Nu'aymah hakan ya gagara. cike da fita hayyaci ya fara sarrafata. Yau ma dai an maimaita na daren jiya, sai dai kukanta ya sakashi taƙaita tafiyar batai nisan zango kamar ta daren jiya ba ya tausaya mata dan yasan bata gama dawowa hayyacinta ba.

        A take kuwa jikinta ya ɗime da zazzaɓin wahala. Hardasu rawar sanyi. Yasan ya ƙara laifi mai girma. Dan haka yayta lallashi da ban haƙuri harya samu ya kimtsa mata jiki yau ma yay gashi dan yasan zataji ciwo a wajen balle gashi yayi fami ne.

       Da taimakonsa tayi wankan tsarki, shima yayo sannan ya taimaka mata suka fito. Lallaɓata yay tasha yogurt da maganinta, kafin ya ƙara mata shirin barci. Sai da ya sake kimtsawa shima sannan ya hawo gadon ya rungumeta dan harma ta fara barci. Irin allurar ɗazun da rana ta rage raɗaɗi yay mata. Kuka ta fasa masa jikinta na matuƙar rawa. Yay saurin haɗe bakinsu waje guda. Sai da ya janye allurar sannan ya janye bakin yana furzar da iska tare da rungumeta da ƙyau a jikinsa yana shafa bayanta da faɗin, “Am so sorry sweetheart. Please forgive me”.

         Luf tayi a jikinsa tana zirar da hawayen. A haka barci yay gaba da ita yana faɗa mata kalamai masu sanyi cikin kunne da hura mata iska mai daɗi. Jin ta fara sauke numfashi na alamar barci shima saiya shiga sauke ajiyar zuciya a jajjere. Yana ƙara jin ƙaunarta mai tsanani tana ratsa masa zuciya da dukan jikin sama gaba ɗaya. Ta zama ta farko a zuciyarsa. Ta farko a sirrinsa. Ta farkon haskama rayuwarsa hanya. Ta farko.... Ta farko.... Da yawa harma baisan iyakaba. Insha ALLAH kuma itace zata zama ta farko har ƙarshen rayuwa🤗😍.


*_Muma ALLAH yasa mu zama na farko ta ƙyawawan hanyoyi ga mazajenmu har ƙarshen rayuwa my dear fans. Ba dole sai kin kasance matar farko ba zaki zama ta farko😋😘. Kota huɗu kikaje ƙyawawan halayenki zaisa ki zama ta farko😍. Uwar gida kema dage ki riƙe gam kar a ƙwace miki ta farko😉🤗😅._*

                  Washe gari haka Nu'aymah taita zubama Yoohan shagwaɓa da raki yana faman lallaɓata da lallashinta. Tasa dole ya kira mata baba malam da Umm da hajjo. Inda anan itama hajjon ta fahimci takwararta ta kai mutuncinta gidan aurenta. Hakan ya mata matuƙar daɗi harta kaita da yin sujidar godiya ga ALLAH. Cike da tsantsar alfahari da jin daɗi ta kira Ananah ta sanar mata. Sosai Ananah taji daɗi tana godema ALLAH daya wanke Aymah cikin sauƙi a garesu bisa hikimarsa da rahamarsa. Daga haka sukai gum da bakinsu suna jiran bayyanar gaskiyar ga kowama cikin hikimar UBANGIJIN al'arshi.

      Da ƙyar Yoohan ya samu yaje sukai sallama da Omar (Richard) da zai wuce Nigeria a yau. Daga haka ya dawo wajen ƴar amaryarsa sarkin shagwaɓa da shiririta. Haka suka kasance a gaba ɗaya wannan yinin cike da so da ƙauna. Dan itama tun tana nokewa da ƙunshe-kunshe harta saki jikinta duk da dai akwai kunyar tattare da ita, saboda ta kasance tarbiyyarta tun fil'azal...........✍


No comments

Powered by Blogger.