Saran Boye 61


 No. 61


...........Da Solomon sukaci karo a jikin wata dalleliyar mota tsaye. sai baturen dake cikin Uniform ɗin hotel ɗin. Da girmamawa Solo yake gaisheta da sake tambayarta ƙarfin jiki. Cike da takaicin zamantowarsa tamkar jelar Yoohan ɗin ya sakata amsawa a taƙaice.

Yoohan ya buɗe mata da kansa ya taimaka mata ta shiga. rufewa yay, ya zagaya inda baturen ya buɗe masa shi kuma ya shiga. Baturen ne ya shiga a matsayin driver, Solomon kuwa gefensa. wannan abu ya zafi Nu'aymah a rai. Kenan duk inda mijin nata yake dole wannan basamuden sai ya kasance da shi?. Dolene tasan matsayin wannan bibbinin kuwa. Galla masa harara tayi lokacin da drivern ke harba motar a titi suka fice daga harabar hotel ɗin.

        Idanu Yoohan ya lumshe da jingina kansa da kujera. Ya saki ajiyar zuciya, a ransa yana ayyana ‘hakan shine kawai mafita a gareni. idan ba ɗan fitar mukaiba bazan iya barin yarinyar nan ba. komai zan iya aikatawa kamar yanda zuciyarsa ke bani ƙwarin gwiwar game da ita’.

          Nu'aymah dai ta fahimci motar hotel ɗince ya ara. Sai dai batasan ina suka nufaba. Dan haka ta ware idanu da ƙyau tana sake kallon tsarin garin na Vienna da ya gama haɗuwa da ababen more rayuwa kala-kala. Duk da ranta cike yake da taikaicin tafiya tare da Solomon, kai harshi kansa Yoohan ɗin haushinsa takeji akan Solo.

         Sun fara zuwa wani haɗaɗɗen wajen Saloon, bata fahemci hakanba kuwa sai da suka shiga ciki. Ta kallesa tana yamutse fuska, “Mi zamuyi anan?”. Kallonta kawai yake shidai fuska a tsuke shima. Dan shi kaɗai yasan a halin da yake ciki. Sai dai yana mamakin miya ɓata mata rai haka? Ya fahimci tun fitowarsu cikin hotel ɗin wajensu Solo ta ciskule fuska, saɓanin farko da kunyarsace kawai tattare da ita.

      Bai bata amsaba, sai ma ma'aikatan wajen da sukazo musu tarba ta mutuntawa. Da Garman language yay musu bayanin abinda suke buƙata. Hakan yasa Aymah bataji komaiba. Saima mamakin dama yanajin yaren data fahimci mafi yawan ƴan garin sunfiyi kenan?. Bata da mai bata amsa, sai jan hannunta da ma'aikaciyar tayi zuwa sashen mata. Binsu yay har ciki, shine ya zaɓa duk abinda za'ai mata. Nu'aymah dai ta zubama sarautar ALLAH ido tana kallonsu. Shiko yaƙi yarda su haɗa idon. Yana gama zaɓa ya biyasu kuɗinsu. Sai shi kuma ya nufi na maza dan yana buƙatar gyaran fuska da yankan farce.

         Haushi ya hana Aymah yin magana har aka fara wanke mata kanta. Ganin babu kitso dai yasa bata damuba. An mata wankin ƙafa da gyaran farce, sannan aka kaita wani ɗaki wai na gyaran jiki ne. Nu'aymah dai taga abinda ya girmeta, har tsoron shiga waɗan nan injina ta ringayi, a ganinta idan aka ɗauke wuta mutum na ciki kuma ai shikenan labarinsa ya ƙare. ‘Kai wannan mutumin ba kawoni yay kuwa a markaɗeniba ma?’ ta aiyana a ranta tana ƙunƙuni da hausa. Su dai ma'aikatan ba jinta sukeba. Hakan yasa suketa aikinsu kawai. Anyi mata gyaran jiki na musamman da ita kanta tasan eh ta gyaru ƙwarai da gaske. Aka kuma kaita wani waje wai tausa nankuma za'ai mata. ‘Babbar bala'i’ ta faɗa a fili cikin suɓutar baki. ‘Amma wannan mai jajayen kunnen ya gama sakamin rayuwa a gaba. Yoni nace masa ina buƙatar duk wannan ne ko mi?’. Haka taita zuba mita ana mata tausa. gashi kuma sai faman lumtse idanu takeyi alamar tanajin daɗin jikinta. Bayan kammala tausan an maidata wajen gyaran jiki, daga haka aka ƙarasa gyara mata kanta. Haɗaɗɗun wando da riga aka kawo mata ta saka ƙyautar da shagon ke badawa kenan idan suka maka aiki mai tsada irin haka. Badan taso ba ta amsa ta saka. Ta yana gyalen jallabiyar ta akai suka fito inda Yoohan ke zaune yana jiransu. Dan shi tuni an kammala masa.

         A tare suka zubama juna ido. Kowanne yana zancen ƙyawun da ɗan uwansa yay masa a zuciya. Sake tashi hankalin Yoohan yayi matuƙa, wata sabuwar buƙata da tafi ta farko sai ƙara bijiro masa takeyi. Nannauyan numfashi ya furzar da yin luuu da idanunsa da launinsu na fari ya sirka zuwa ja. Sai da ya lumshesu sannan ya sake buɗewa akanta. Da ƙyar ya iya miƙewa tsaye zuwa gareta. Ita dai kanta a ƙasa tun kallon datai masa na farko da yaba ƙyawun da gyaran fuskar da yay yayi masa, dan an canja masa style ɗin sajensa. bata ƙara yarda ta dubesaba saboda kallon ƙurullar data ga shima yana mata. Hannu yasa a hankali ya zame gyalen daga bisa kanta yana kallon gyaran gashin nata. Ya kama jelar gashin dake ɗaure a tsakkiya ya murza cikin hannunsa tare da shaƙar ƙamshin da gashin keyi. Duk yanda yaso furta wani abu a harshensa ya kasa hakan....

        Maganar ma'aikaciyar wajen ce ta katsesa daga ƙoƙarin kamo fuskar Aymah da yayi niyyar yi. Ya juyo yana kallonta. Bag ɗin hannunta mai tambarin wajen nasu ta miƙama Nu'aymah fuskarta da murmushi tai musu godiya na zuwa masana'antarsu. Guntun murmushi Aymah tayi mata kawai ta amsa. Kallon jikkar yayi ya maida dubansa ga matashiyar matar. Yay mata tambayar da Aymah batasan ta minene ba, kai kawai ya gyaɗa mata da kama hannun Nu'aymah suka fito Reception, wata hanya sukabi bayan taga ya karanta rubutun wajen da ita dai ba ganewa takeba tunda ba turanci baneba. A shagon kaya ta gansu, yanda baiyi maganaba itama batayiba. Sai hannunta daya riƙe yanabin kayan da kallo. Yayinda ma'aikatan wajen ke musu barka da zuwa. 

         Kujera aka bata ta zauna shi kuma yana duba abinda yazo nema. Kallon shagon ya ɗaule mata hankali har batasan dami-dami ya ɗaukaba. Sai da yazo gabanta da riga a hannu ne ta kallesa. ya kamota ya miƙar tsaye yana magana a hankali. “A ƙasar mutane ma sai kin nuna ke bakanuwa ce?”..   

       Harararsa tayi dai-dai yana kamo hannunta ya zura mata hannun rigar coat ɗin ta mata data gama haɗuwa sai wani irin shegen ƙamshi takeyi. Bakinsa ya taɓe ya kamo ɗayan ma ya zura mata ya gyara mata rigar da ƙyau. Takai mata har gwiwa kuwa, hakan yasa ta rufe mata jikin yanda yafi buƙata, dan yaji a ransa bazai iya barinta yawo da kayan da wajen saloon ɗin suka bata ba.

      Ta ƙara ƙyau kuwa sosai masha ALLAH, shi kansa ya kasa ɗauke ido a kanta. Kuɗin abinda ya ɗauka ya biya suka fito a wajen. Inda suka bar su Solomon zaune a harabar wajen nan suka iskesu suna shan coffee. Solomon dake satar kallonsu ta gefen idi yace, ‘Yarinya sai shege ƙyau kamar aljana. Shiyyasa gaba ɗaya oga ya susuce a kanta’.

     Oho Aymah batasan yanayiba. Dan tuni ma ta buɗe mota ta shige ko jiran Yoohan ɗin ya buɗe mata yayi batai ba. Da kallo shima ya bita dan ya fara fahimtar kamar haushin Solomon takeji. Bai dai tabbatar ba, dan haka shima ya shiga motar. Su Solo ma duk shiga sukai suka bar wajen.

         A yanzunma da suka tafi kanta ta juyar tana kallon garin. Shi dai Yoohan nata kallonta ta ƙasan ido da nazarinta har suka ƙarasa wani garden ɗin hutawa. Wajene da masoya kawai ke kai kawo abin zaƙƙyau da burgewa. Sun bar su Solomon acan wajene, shi da ita kawai suka shiga ciki. Inda ya zazzagaya da ita wajejen abubuwan tarihi, sukai hotuna ta sha kallo kuma. Yoohan bai da kuzari gaba ɗaya. Yanata dauriyane kawai, dan a rayuwarsa bai taɓa jin matsananciyar sha'awa irin ta yau ba. Ji yake kamar idan bai akasance da mace ba zai rasa ransa. Itako Aymah gani take shegen miskilancinsa ne ya motsa kawai. Shiyyasa ta tattarasa ta watsar gefe. Ko abu ya faru sai dai taita ƙunƙuni a ranta da gulmarsa a zuciya. A waje sukai sallar la'asar, magriba da isha'i. Sun ɗanyi ciye-ciyensu da Aymah ke ganin wasu ƙazanta. Duk dan lokaci yaɗan ƙara ja sai da Yoohan ya bari tara na agogon ƙasar yayi sannan suka dawo hotel ɗin su.

        Masifaffen ciwon cikin daya taso masane ya sakashi cemata taje ciki yana zuwa zaije asibiti duba wani maralafiya. Bata damuba. Ta kwashi kayan da suka sayo tai ciki. Can ya samu ƙasan wani rumfar ya zauna dan dama babu asibitin da zaije. So yake taɗanyi nesa da shi ko zaiji sassaucin abinda ya keji game da ita. Sai dai kuma ina, rikicewa ma al'amarin ya sake neman yimasa saboda kaiwa da kawowa da matan turawan keyi ta wajen tamkar tsirara. Bai rufa mintuna ashirinba dole ya tashi a wajen ya nufi cikin ɗakin jikinsa na rawa.  


        Shigowarsa dai-dai da fitowar Nu'aymah da sanin bayama hotel ɗin gaba ɗaya ya sakata fitowa daga ita sai guntun towel iyaka cinya. Daga ita har shi turus sukayi. Aymah dai ruɗanin ganinsa babu zatone ya sakata ƙamewa waje guda ta kasa ko motsi. Shiko tashin hankalin halin da yake a cikine ya sakashi tsura mata idanu jikinsa na wani irin tsuma. Ya rasa wane kalar tashin hankaline yake ciki a yau shi kuwa?. 

     Sum-sum ta wuce gaban Wadrobe batare data ƙara yarda ta dubesa ba. Shima sai ya ƙarasa shigowa ya nufi bayin dan watsa ruwa ko zaiji sanyi a ransa da gangar jikinsa.

        Da sauri-sauri tai shirin barci. Sai dai doguwar riga ta saka ta tada salla dan basuyi shafa'i da wutiri ba. Tana yin sallamar shafa'i ya fito. Bata kallesaba ta miƙe zatai wutiri. Dakatar da ita yayi ta hanyar cewa, “Jirani”.

     Da mamaki ta juyo ta kallesa. Sai dai tayi saurin ɗauke kanta ganin towel ne kawai a jikinsa shima. Jallabiya ya ɗauka ya zura a jikinsa yazo inda take. nuni yay mata data gyara tsaiwarta a bayansa. Zatai magana ya ɗan cije lip ɗinsa na ƙasa da girgiza mata kai yana yin luuu da idanunsa dake jajur kaɗan. Bata iya yin maganarba kuwa. haka ta bisa sukai salla raka'a biyu. Ya juyo ya dafa kanta yana karanta addu'ar da baba malam ya koyar da shi tun daren aurensu, kamar yanda kuma yay masa bayani dalla-dalla akan tsarin aure a musulince tun wancan lokacin,


اَللَّهُمَّ  إِنِّي أَسْأَلُكَ خَيْرَهَا، وَخَيْرَ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهَا، وَشَرِّ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ.

*_Allahumma innee as-aluka khayraha wakhayra ma jabaltaha 'alayh, wa-a'oothu bika min sharriha washarri ma jabaltaha 'alayh._*

       _Ya ALLAH ina rokon Ka laherinta da alhrin da Ka dabi'antar da ita a kansa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinta da shaarrin Da ka dabi'antar da ita a kansa._

        Ya kuma ɗorawa da wasu addu'oin gwargwadon saninsa sannan ya miƙe yay shafa'i da wutiri da ƙyar. Itama wutirinta tayi. Bayan sun idar ne ta fahimci bashi da lafiya. Ƙulle masan da cikinsa yayine ya sakashi kwanciya ya ɗora kansa bisa cinyarta yana matse fuska. A rikice ta waro idanu waje tana tambayarsa, “Baka da lafiya ne?”.

        Bai iya ya bata amsaba. Sai hannunta daya riƙo ya matse cikin nasa jikinsa na ɗan rawa. Ruɗewa ta sakeyi ganin yanda yake zufa a goshi jikinsa na wani irin tsuma. Rungumo kansa tayi da ƙyau ajikinta ta fashe da kuka tana faɗin, 

      “Na shiga uku ni Nu'aymah. Yah Yoohan miya sameka? dan ALLAH ka tashi muje asibiti, ka tashi dan ALLAH ”.

        Duk da a halin da yake a ciki sai da ta bashi tausayi, yanda ta fashe da kukan kuwa har cikin ransa. Hannunta dake a cikin nasa ya ɗago da ƙyar ya ɗaura akan mararsa datai wani irin ɗaukar zafi dayin tauri ya danna. Zata ƙara magana ya manne bakinsa akan nata.

         Da farko Aymah tayi tunanin zafin ciwo ne ya sakashi aikata hakan. Dan jikinsa ƙara ƙarfin karkarwar data fi ta farko ya kamayi lokacin daya fara kissing nata. Sai dai fa ganin lamarin yana neman zarta wayonta ta fara ƙoƙarin turesa. Sosai hakan ya gagareta, ya bala'in birkice mata a namijinsa. Daga ƙarshema ɗaukarta yayi gaba ɗayanta zuwa gado. Duk kukan da take masa da son sauka a jikin nasa da alama ma bayajinta. Dan duk wanda ya duba Yoohan a wannan lokacin yasan sam baya a cikin hayyacinsa. Idanunsa kansu a rufe suke gam yama kasa buɗesu balle yaga halin ruɗani da tashin hankalin da Aymah take a ciki. Fincike kayan jikinta ya shigayi tana ƙoƙarin hanashi cikin kuka.

         Roƙonta shima ya shigayi cikin wata irin murya mai ban tashin hankali. “Please karkice a'a. Idan kika hanani kanki zan iya mutuwa Zeeynab. D....da....dan ALLAH N...u...ay...mah”. Duk da tashin hankalin da Nu'aymah take a ciki na fahimtar abinda yake shirin aikata mata sai da yanayinsa da yanda yake magana ya nema tarwatsa mata zuciya. Gaba ɗaya ya birkice mata kamar bashiba. Yanda take hawayen neman ceto da son ya barta haka shima hawayen neman agaji da taimakonta matsayin halalinsa ya keyi. A gefe kuma yana mata abinda tunda uwatata ta kawota duniya wani bai taɓa mata koda makamancinsa ba. Duk da ƙarancin shekarunta da shiririta tasan minene aure. Duk da bawai komai da akeyi a cikinsa ta sani gatse-gatse ba saboda yanayin tarbiyyar data tashi a ciki ta kulawar iyaye da rashin tarkacen ƙawaye.

        Duk da baya a cikin hayyacinsa sai da UBANGIJI ya bashi dama da ikon karanta,

         بِسْمِ اللهِ اللّهُمَّ جَنِّبْنَا الشَّيْطَانَ، وَجَنِّبِ الشَّيْطَانَ مَا رَزَقْتَنَا.

*_Bismil-lah, allahumma jannibnash-shaytan, wajannibish-shaytana ma razaqtana._*

     _Da sunan ALLAH. Ya ALLAH! Ka nisantar da shaidan daga garemu, kuma ka nisantar da shaidan daga abin da Ka azurta mu da shi._

        Kamar yanda aka koyar da shi. Lokacin da Aymah ta sake jin baƙon al'amarin da yafi komai gigitata fiye da duk abubuwan da yay mata a farko tuni sai numfashinta ya shiga neman shiɗewa. Kuka take iya ƙarfinta tana kiran baba malam da Umm suzo su taimaketa. Hajjo kanta da Muhammad sunsha kira. Kai duk ƴan gidansu ma babu wanda baisha kiran neman ceto ba hatta da Yah Ab da Nasir🤣, su Ananah kansu da su Gwaggo (kakarta data haifi Umm) sun sami nasu rabon. Tun tana haɗashi da ALLAH harta koma cemasa “Idan yana ƙaunar papa da Momy (Madam Chioma) yayi haƙuri, ta rantse tabar masa tsiwa bazata sake ba. Duk abinda ya keso zata dingayinsa. Ko ƴan gidansuma ta daina faɗa dasu, idan mutum ya mata abu zata barsa da ALLAH kawai😂😜. Na tabbata da ace Yoohan cikin hankalinsa yake babu abinda zai hanashi shan dariya da sumbatun shiriritar Nu'aymah. Tunma tana iya kukan da roƙo harta gaza bakin ya mutu ta tafi sumar wucin gadi........


Wannan lamari sai da tafiya hutun wucin gadi dan tausayin jikar ɗan jibiya😒😏🚶🏻.


*_ABUJA NIGERIA_*


     A firgice ta farka da ga razanannen mafarkin daya risketa cikin barcin daya ɗauketa bayan dawowarsu wani taron karammawa da akaima papa, kasancewar sa dattijon da akeji da shi a yankinsu. Sannan gashi babban Pastor da ba Nigeria kawaiba har wasu ƙasashen ƙetare yana baza komarsa. Wannan taron karammawa ya gudana ne a Abuja bisa jagorancin ƙungiyar Christians reshen catholic. An karamasu su bakwai. sai dai papa shine yafi kowa ɗaukar wannan jinjinar girmamawa.

       Ɗunbin gajiyar data samo acan ne ya saka suna shigowa gidan kaya kawai ta cire ta kwanta ko wanka bata iya samu tayi ba. A cikin wannan barcine tai gamo da mummunan mafarkin da ko'a labari bata fatan tabbatuwarsa. A zabure ta miƙe zuwa inda ajiyayyen asirinta yake na tsahon shekaru kusan goma sha uku. Rawa jikinta ya kamayi kamar mazari ganin ƙullin da akaima igiyar cikin tukunyar ya warware. Da sauri ta ajiye tukunyar a ƙasa saboda karkarwar da hannunta keyi gudun karta yaddata. Waya ta jawo a ruɗe tai kiran ƙawarta. Bugu biyu Madam Rebecca dake holewarta da wani yaro a gidanta dan mijinta baya ƙasar yana can harkar kasuwancinsa ta ɗaga tana riƙe hannun matashin yaron ɗan shekaru ashirin da uku daga sheɗancin da yakeyi a jikinta. 

     “Sorry Baby. just 5minutes”. Ta faɗa tana masa kiss da kai wayar kunnenta. Duk Madam Chioma tana jiyosu, ta riga tasan ƙawar tata kullum bata rabo da yara ƙanana tare da ita. Sai dai bama wannan bane damuwarta a yanzun. Damuwarta abinda taci karo da shi. Muryarta na rawa tace, “Rebecca! Tawa ta ƙare”.

       Cike da tsoron jin yanayinta da furicinta Madam Rebecca ta tashi zaune tana tambayarta miya faru?. Cikin kuka rurus Madam Chioma ta zayyane mata komai game da mafarkinta da kuma abinda ta gani a tukunyar tsafinta. Wani shegen murmushin mugunta Madam Rebecca tayi. A fili kuwa sai tace, “Kinga kwantar da hankalinki, bara na gama da babyn nan na gabana zanzo gidan”.

     Da matuƙar tashin hankali madam Chioma tace, “Haba Rebecca. ina miki maganar matsalata kina magana irin haka? ki tausaya min mana. Banason na rasa Yoohan a rayuwata ko cika burina ban samu nayiba”.

      “Hah!! Kinada matsala Chioma. Kema kinsan inaa wannan yanayin babu abinda zan iya miki koda nazo. Garama kiyu hakuri ki bani 1hour kawai”. Cike da matsanancin takaici Madam Chioma ta yanke wayar. Maida akalar kiranta tayi ga Number Yoohan. Sai dai harta yanke ba'a ɗagaba. Dan a lokacin bama wayaba har ita kanta dake matsayin uwarsa ya manta da ita a duniya. Nu'aymah kawai ya sani a yanzu, ita kaɗai kuma yake gani.

      Ta jera masa kira kusan biyar babu amsa. Hakanne ya ƙara rikitata ta koma kiran Solomon. shima dai akai sa'a bai ɗagaba. Dan a lokacin yayi barci saboda gajiyar yawon da sukasha, yana dawowa kuma ya samu wata ƴar baby suka shige da ga ciki. Ai saita sake haukacewa. A ruɗe ta fara haɗa kayan tafiya ƙauyensu Madam Rebecca, dama daga can aka yo mata aikin. Dan bazata iya kwana garin Abuja ba batare data san makomar abinda ta ganiba. Bayi ta shiga ta facaccala wanka ta fito. Yanda take komai a birkice sai ka ɗauka tama zare ne. Sai da ta kimtsa tsaf ta fito jaye da ƙaramin trolly da handbag. Sashen Papa ta nufa, kamar yanda tayi hasashe kuwa ta samesa a falonsa zaune shi da Uncle Godwin suna tattauna mai fishshesu. Da ƙyar ta iya ƙoƙarin control ɗin ruɗaninta suka gaisa da Godwin ɗin. Papa dake binta da kallo ya miƙo mata hannu alamar tazo garesa. Zuwa tayi ta zauna a jikinsa cike da dauriya, ta ɗora kanta a kafaɗarsa. Kiss ya bata a goshi da bakinta yana faɗin, “Are you Ok?”. Kanta ta daga masa. Murya a sanyaye tace, “Yes. I'm. Kirane ya sameni na gaggawa daga office ɗinmu, akwai wani taro wai da zamuyi a Lagos dama tun kusan sati biyu, anata ɗagawa kuma sai yau ne wai sukace gobe za'ayi, gashi yanzun an turomin saƙo ni akeson na halarci wajen wai kuma”.

       Tuni fara'ar papa ta ɓace a fuskarsa. Dan yana tsananin sonta, koda wasa bayason tanayin nesa da shi. Amma kuma bayason ɓacin ranta. Zai yi magana tai saurin ɗora yatsanta akan bakinsa tana faɗin, 

    “Please baby”.

Ajiyar zuciya ya sauke a hankali. Badan ransa nasoba yace, “Okay. Yanzu kina buƙatar wani abu ne?”.

       “No thanks you dear. Basai na ɗaura maka wata wahalaba ma”. 

       “Bakinta ya sake sumbata, da murmushinsa na yake yace, “Babu damuwa zan miki transfer ɗin kuɗin shan ice-creem ”.

       “Thanks you baby”. Ta faɗa tana sumbatar laɓɓansa da mikewa tsaye. Ta sake cewa “Bey”.

    Kusan a tare shi da Uncle Godwin sukace mata “Safe journey”. Daga haka ta fice tabar papa da jimami. Duk da shima hakan wata damace a garesa da zai shanama tashi rayuwar.

     Ko sallama batai da su mama debora ba ta fice abinta. Yaran kuwa suna can garden dama. Tana fitowa harabar gidan motar madam Rebecca na shigowa. Tsaki taja tare da nufar motar. Batare data yi magana ba ta buɗe gefen driver ta zauna. Reverse kawai Madam Rebecca tayi suka fice da ga gidan.

      Sai da suka hau titi suka fara magana. Madam Chioma ta dage akan a yau zata wuce dan bazata iya kwana cikin abuja ba. Lallaɓata Madam Rebecca ta shiga yi akan ta bari su sami jirgin da zai kaisu jihar River state. Dan tafiyar mota ba abune mai sauƙi a garesu ba. Da farko sam madam Chioma taƙi saurarenta. Sai da tai da gaske da tuna mata ka'idojin bokan sannan ta dawo hayyacinta ta amince zata kwana a gidan Madam Rebecca ɗin. Can suka wuce. Sai dai a ranar sukai booking ɗin jirgi. Tare da kiran bokan shima sukai magana da shi ya basu damar zuwa a goben. Da ga haka suka cigaba da tattaunawa akan lamarin Yoohan da Nu'aymah, dama basusan sunayi ba, dan su suna can a sabuwar duniya😉😎.........✍


No comments

Powered by Blogger.