Saran Boye 60


 No. 60


 ..........Koda Yoohan ya dawo ɗakin bayan awanni kusan biyu da fitarsa bai tada Aymah dake kudundune cikin bargo tana barci ba. Wanka yayi, yay shirinsa tsaf na fita asibiti. Turaren hannunsa ya ajiye dai da ring ɗin wayarsa. guntun tsaki yayi tare da ɗaukar brush ya nufo inda take yana kwantar da sajensa. Sai dai kuma ganin wanda yay kiranne ya sakashi ɗan waro idanu waje ya dafe goshinsa.

Zama yay a bakin gadon dai-dai da katsewar kiran. Shine ya kirashi zuciyarsa fal takaicin tsakin da yayi. Koda baba malam yaga shigowar kiran da ga can murmushi yayi kawai ya ɗaga suna kallon juna da Umm dake a kusa da shi. Cike da girmamawa Yoohan ya shiga gaishesa. Shiko yana amsa masa da kulawa. Sunɗan taɓa hira da duk Yoohan ke ƙarajin ƙaunar Baba malam. Dan duk akan abinda zai amfani rayuwarsa ne suke tattaunawar. Daga bisani suka dawo da firar tasu akan Aymah. Hannu Yoohan ya kai ya janye bargon data rufe har fuskarta a hankali, dan ya gama fahimtar wannan ɗabi'artace na lulluɓa da bargo har kanta. Lumshe idanu ya ɗanyi ya sake buɗewa a kanta, dai-dai yana amsama baba malam da cewar, “Uncle babu wani damuwa yanzun kam. Gata nanma tasha magani tana barci. Sai nan da kamar awa uku zata tashi insha ALLAH”. Murmushi yayi mai ƙayatarwa saboda jin abinda baba malam ɗin yace daga can. Ya sake kai hannu akan girar idon Aymah ya shafa yana sakin murmushin da har haƙoransa suka bayyana. “Uncle ai zata daina watarana. Yanzunma ƙuruciya ce kawai, kowa dama da irin tasa. A dalilin aikin ma gashi yanzu tayi sanyi sosai. Duk ta zama shiru-shiru”. Faɗaɗa murmushinsa ya sakeyi sosai saboda amsar da baba malam ya sake bashi. Daga haka suka gaisa da Umm sannan yay musu sallama ya kashe.

        Ranƙwafawa yay akan Aymah ya sumbaci kuncinta da saman ido. Bargon ya sake gyara mata yanda bazata rufe fuskarba sannan ya miƙe ya karasa kimtsawa yaɗan mata short note ya ajiye mata da wayar ya fice. 


                    X★x*x★X

      

Sosai Nu'aymah tasha barcinta. Bata farka ba sai bayan a wanni uku da fitar Yoohan kamar yanda ya ambata. Taji daɗin barcin sosai. ta miƙe tanata faman ɓata fuska irin ta wanda ya tashi a barci. Wanka tayo da ruwa mai ɗumi. Ta buɗe Wadrobe zata ciri kaya tajita gam. mamaki ya kamata da takaici ganin rufewa yayi. ƙunƙuni ta fara tana faɗin, ‘Gaskiya wannan mai jajayen kunnuwan yama rainani. Nasan maganinsa ai ALLAH kuwa. Sai yasan yayi da ƴar Umm da baba malam’. Ta ƙare maganar tana huci kai kace wani uban laifi akai mata. Har ta nufi gado da fushi sai kuma ta dawo da baya. Ɗayan murfin Wadrobe ɗin ta buɗe. A mamakinta sai taci karo da akwatin nasu anan. Shi ta buɗe tana ƙwafa da faɗin, ‘Na rantse akan kayanka zan huce takaicina. Dan sakasu zanyi naita birgima a ƙasan ɗakin nan har sai sunsan niɗin Zainabu ce jikar Zainabu Abu hajjaju Hajjo matar malam Hashim ɗan jibiy.......’ ta kasa ƙarasawa sabida cin karo da wata leda da tayi a gefen akwatin. Ɗauka tayi ta buɗe ledar tare da zazzago kayan ciki. ‘Ikon ALLAH sai kallo. shiko wannan bawa mi yake nufi dani dazai ajiyemin waɗannan kayan kamar ɗiyar tsuntsuwar sama jannati? Shin wai nufinsa ni jikar ɗan jibiya ce zansa wannan a tsokani shari'ar komi?, dama shiyyasa yaƙi ɗakkomin kaya sai wani jallabiya guda biyu dan tsabar ya maidani doll’. Tai maganar tana ɗaga wandon da bazai wuce rabin cinyarta ba. Ajiyesa tai ta cigaba da ɗaga sauran ma. Duk da bawani na fidda tsiraici bane sun bata haushi. Dan ba saba saka irin waɗanan ƙananun kayan tayiba a gida. Wani lokacin ko wando da riga ta saka sai Umm ta korata ta ɗora after dress a sama inhar zata fita daga sashensu. Mansa ta ɗauka ta shafa tanata cika baki da iska. Sosai takema man shafawar matsar mugunta. Wai shima sai yaji a jikinsa tunda ya saya mata waɗanan fingalallun kayan kamar wata ƴar tsana. To wlhy tunda ya raina mata jiki saita ta narkar abinci ta zama ƙatuwa kafin subar ƙasar nan. Sai tama aljihunsa ɗibar karan mahaukaciya (Danƙari. To kaji Yoohan talautaka za'ai a ƙasar Austria🤣).

         Haka tasa kayan tana mita. ta ringa zazzagama jikinta turarensa wai shine target ɗin farko da zata fara. A gaban ƙaton mirror ɗakin taje ta tsaya tana kallon kanta. Ta wani riƙe ƙugu tana faɗin, ‘Woow na kumafa haɗu’ tai maganar tana jujjuyawa. ‘Yauwa nama tuna. Bara nayi yanda naga matar jiya tayi’ ta faɗa tana tattare ƙasan farar top ɗin tata ta ɗaure a gefe. Hakanne ya bama ɗingilis ɗin wandon nata kalar blue na jeans damar fitowa sosai. ‘Tab, wlhy su Umm an haifo baturiya ba'a saniba. Hummm inama zan haɗu da hajjo yanzun. Nunawafa zanyi bamma santa ba, dan saina gama folata irin nifa bamma san African ɗinnanba sannan’. Ita kanta abun sai ya bata da dariya. Ta ƙyalƙyale kuwa da ita kamar dai har yanzun kan da motsi😂.

         Haka taita shirmenta ita kaɗai harta gaji ta bari taje ta gyara gadon da kanta. A wajen gyaranne taci karo da note ɗinsa. Koda ta gama karantawa saita murmusa. Wayar daya ajiye ɗin ta ɗauka ta nufi ƙofar da taga sun fita jiya ta danna yanda taga yayi da zai rufe. a take kuwa labulen ya zuge. Ta sake dannawa ƙofar glass ɗin itana ta buɗe. Farar ƙafarta dake a cikin blue Slippers ta zira waje tana wani zuƙar daddaɗar iskan wajen. Barandan ta ɗakinne kawai, hakan yasa taji ta ta sake dan babu ruwan wani da wani. Sannan anyi iyakar da waɗanda ke maƙwaftaka da ɗakin bazasu gantaba, kamar yanda itama bata ganinsu sai ainahin birnin Vienna da kuma harabar hotel ɗin da ƙaton swimming pool yake. Shima sai idan ta miƙene a jikin ƙarfen barandar zata iya ganin masu hutawa na wanka, wasu kuma suna zaune a kujeru ana zuƙar drinks.

      A ɗaya daga cikin kujerar wajen ta zauna, ta ciro buk ɗaya dage cikin ɗan kantan wajen ta ajiye sannan ta hau ƙoƙarin kiran su Baba malam cike da ɗoki. Kamar kuwa jira sukeyi, tana kira ring baifi uku ba Umm ta ɗaga. Dan baba malam yana wanka a lokacin. Cike da ihun murna ta farama Umm magana. Itako daga can sai dariya take da jinjina wauta irin ta ɗiyar tata. Dan ita ta tabbatar ba kuruciyace kawai ke ɗawainiya da Aymah ba. Akwai tsantsar wauta tattare da ita. A dai ƙasar hausa mai shekaru irin nata ai budrwace cikkakkiya kowa ya sani. Biye mata tai ko tanata faman bata labarin haduwar hotel ɗin da suke, da gine-ginen garin Vienna. Harda cewa Umm bara ta katse ta kira video call wai dan ta gani. da sauri Umn tace, “A'a shugabar rawan kai na gode. Nima ai nazo na gani da idona”.

       “Yo Umm ai dai bakiyi yawoba” tai maganar cike da shagwaɓa. Dariya Umm tayi da faɗin, “ALLAH ya shiryeki Nu'aymah. Ga Abbanki nidai barni na hutama raina. Ga autana can kwance yana fama da zazzaɓi bara naje naji da shi”.

        A take kuma sai mood ɗin Aymah ya canja jin abokin faɗa babu lafiya. Duk sai ta marairaice kuma har ma abin ya bama Umm da baba malam dariya. Haka dai ya amsa shima ta zuba masa shiriritarta. Sai da yace ta kashe wayar haka karsu ƙararma Yoohan da kuɗi sannan sukai sallama bayan anbama Muhammad shima sun gaisa, duk da a kwance yake bayajin dadi. Daga haka Hajjo ta kira. Itama suka gaisa. Badan tasoba ta haƙura ta ajiye wayan ta ɗauki buk ɗin data ɗauka ta fara dubawa. 


         Haka Nu'aymah ta kasance ita kaɗai a wannan yini. Duk da gargaɗin karta zauna da yunwa da Yoohan yayta mata bataji ba, sau kusan uku ma'aikatan hotel ɗin na kawo mata abinci amma sau ɗaya taci. Da lokacin shan maganinta yayi kuma tasha kamar yanda ya rubuta mata a note ɗinsa. Novel ɗin data samu ne ya ɗauke duka hankalinta. Dan shi taita karantawa. Salla kawai ke sakata ajiyewa. Bata damu ba da rashin dawowar tasa. Tunda ya rubuta mata uzirinsa zaije ya ƙaraso yau gaba ɗaya shiyyasa. Kuma ya bata haƙuri akan barintan da zaiyi ita kaɗai ɗin. 

      Lokacin shan maganin darenta nayi taci abincin da aka sake kawo mata kaɗan tasha duk magungunanta tai wanka. Kwanciya tai tana cigaba da karatun buk ɗin har barci yay awon gaba da ita.


     A haka Yoohan ya shigo a matuƙar gajiye ya isketa. Ya zauna a bakin gadon yana kallonta. Hannu ya kai ya zare buk ɗin data rungume a ƙirji a hankali. Motsawa tai, tare da buɗe idanunta da ƙyar ta kallesa. Batare datayi maganaba tai luu dasu ta maida tarufe kayanta tare da gyara kwanciya. 

       Idanu kawai ya lumshe shima ya buɗe akan buk ɗin. Batare da yace komaiba ya ajiye ya miƙe domin yin wanka.

        Har ya kammala dukan hidimarsa Aymah nata barcinta. Bai tadataba kuwa yay shirin barci shima tare da sallolinsa da suka rage ya hawo gadon ya kwanta dan a matuƙar gajiye yake. Addu'ar barci yay musu ya rungume matarsa suka lula duniyar barci mai daɗi.


*_WASHE GARI_*


         Yau ma kamar jiya bayan sallar asuba sunyi zaman karatu. Koda suka idan tasha magani shi kuma ya fita motsa jiki. Da ya dawo ma ya sameta tana barcin. Wanka kawai yayi ya fiddo lap-top ya fita ƴar barandar Aymah ta jiya bayan yayi order ɗin abinda zaici. Acan ya shafe tsahon lokaci har Aymah ta tashi a barcinta. Ganin baya ɗakin tai tunanin ko ya fita. Wanka tayo tazo ta shirya cikin sauran kayan jiya. Yau dai wando ne ta saka yellow da black t-shirt. Tayi ƙyau yauma sosai, ta gyara gashinta tana ɗan yatsina fuska ganin yana bukatar wanki. Badai tayi maganaba dan bason a taɓa mata kai takeba daman. Kobi takan abincin data gani batayiba. Ta ɗauki buk ɗin jiya dake a durowar gefen gadon ajiye ta nufi wajen zamanta na jiya. Kasancewar ya rufe yasa bata fahimci yana a wajenba sai da ta fito.

        Yoohan dake zaune a kujerar ya ɗora ƙafafunsa bisa table ɗin, lap-top a saman filo daya sa kan cinyarsa yanata aikinsa ya ɗago idanunsa jin sabon ƙamshin turarensa data bunkuɗa a jiki. Suna haɗa ido ta turo baki gaba tana kauda fuskarta.

     Baiyi maganaba shi dai. Bai kuma daina mata kallon ƙurilla ba, dan kayan sun matuƙar mata ƙyau, kodan yau ne ya fara ganinta a cikin irinsu oho. duk da kuwa yana bala'in son yaga tayi shigar Hausawa dan tana masa ƙyau. Amma yauma dai tayi irin ƙyawun da yake buƙatar ganinta a ciki.

        Haɗiye abinda ya tsaya masa yay a maƙoshi yana furzar da nannauyan numfashi. Yanda yayi ɗinne ya saka Aymah dake tsaye kamar an dasata kallonsa. da alama kunyace ta hanata motsi kokuma ganin da tai masa a wajen a bazata. Saurin janye idanunta tai ganin har yanzun kallonta yakeyi. Harga ALLAH ita tanajin nauyin ganinsa da kaya irin waɗanan. Rigace armless fara tas a jikinsa, sai wando dako cinyarsa bai gama rufewaba oxblood. Duk da lap-top ɗin daya ɗaura bai hanata ganin farare cinyoyinsa da gargasa suka kwanta ba.. Cikin sanyin muryar da baisanta da ita ba tace, “Good afternoon”.

    Idanunsa yaɗan lumshe ya buɗe a kanta. Sai kuma ya maida ga lap-top ɗinsa yana faɗin, “Same, How are you?”. Hararsa tai ta gefen ido saboda jin yanda ya amsa gaisuwar. Da tamayi niyyar komawa ciki, amma yanda ya amsa matanne ya sakata takowa ta ƙaraso inda yake. Kujerar taja itama ta zauna tanata wani faman haɗe fuska irin batason wargi din nan.

      Duk abinda takeyi Yoohan na kule da ita. Sai faman ƙoƙarin danne dariyar dake taso masa a rai kawai ya keyi. Aikinsa ya cigaba da yi ita kuma ta karatun novel. duk da kuwa bama karatun takeba satar kallonsa kawai takeyi tana gulmarsa a zuciya. Tunda ya fahimci kallonsa takeyi shima sai ya kasa ci gaba da yin aikin. Saboda tsabar neman magana ya tura ƙafarsa ya tanƙwaɓe littafin nata ya faɗi. Ya kuma fiske abinsa yaƙi kallonta tamkar bashi ne ya aikata ɗin ba. 

      Ƙara tsuke fuska tayi tanabin buk ɗin dake yashe a ƙasa da kallo, ɗan bakin kuwa sai motsawa yake amma ta kasa magana. Cike da takaicin daya kumeta ta ɗauki filo ta maka masa a ƙafa harda cije baki.

       “Ouch!” ya faɗa yana saurin janye ƙafarsa. “Silly girl!. Wane mugunta ne haka? Mina miki?”.

        Harara ta balla masa. batare da tace komaiba ta duƙe zata ɗauki buk ɗinta. Sai dai kuma hannunta bazai kaiba dole sai tazo ta gabansa. Fitowa tai tazo har inda littafin yake. ta ɗauko harma ta miƙe zata koma inda take ya saka mata ƙafa. Sai ko gata a kan cinyarsa ɗare-ɗare.

        Mutsu-mutsun ƙwace jikinta ta fara ya saka hannayensa yay mata zobe. Duk yanda taso ta motsa kuwa sai ta kasa. Sake kumbura baki tayi da ƙyau, dan haka kawai ta tuno randa ya taɓa rungumeta a gidansu har Aunty Kubrah ta gansu.

          Kansa ya ɗora bisa kafaɗarta yana busa mata numfashinsa. Cikin magana raɗa-raɗa yace, Silly girl, K ba'a zama lafiya da ke sai kinja faɗa ko?”. Wani shegen mintsini ta bashi a cinya wanda ya sakashi sakinta babu shiri. Miƙewa tsaye tai daga jikinsa tana masa gwalo. Yanda ya ɓata fuska kamar zaiyi kuka ya sakata ƙyalƙyalewa da dariya tana nufa hanyar ƙofa. Yatsu biyu ta ɗaga masa, ɗayan hannunta riƙe da ƙugunta tace, “Wannan na yadda buk ne na maka. Saura na......”

     Ganin ya miƙe ya sata kwasa da gudu tai ciki batare data ƙarasa faɗaba. Baya ya rufa mata har cikin ɗakin. Nanfa suka shiga zagaye ɗakin. Duk yanda yaso kamata taƙi tsayawa, duk da dai da alama ya barta ne kawai. Ganin yanda yake hakki da nuna matuƙar gajiya ya saka taketa ƙyalƙyala masa dariya tana masa gwalo. Harda yin yanda yara keyi na tsokana. Tana saka yatsunta a kunne da jujjuyasu tana masa gwalo. 

      Shiko ƙara narkewa yake irin shifa ya gaza kamata. daga ƙarshe ma ya faɗa saman gado yana hakki da faɗin, “Silly girl”.

     Zuwa tai har inda yake kwance ta shuri ƙafarsa zata gudu. Dama tarko ya mata. Yako harɗota da ƙafar sai gata a jijinsa. Da dai taga da gaske an kamatan saita fara kukan ƙarya tana kai masa ƙananun duka a ƙirji. Dariya ya farayi ya haɗa duka hannayen ya riƙe tare da juyata akan gadon ya koma kanta. “Wana kama to yanzun?”. Ya faɗa yana busa mata iskar bakinsa a kan idonta dake hawayen ƙarya.

      Baki ta sake kumburawa tana matso hawaye. “To bakai ka fara tsokanata ba. Ni dai dana fita ai banma kulaka ba amma ka takaleni”.

       Ƙanƙance idanunsa yay da ɗage gira sama. Yace, “Yarinyar nan kin iya sharri. A yaushe na tsokanekin?”.

       “Na rantse da ALLAH kai ne ka fara tsokanata, kuma bazan ƙyaleka ba sai na rama”. 

      “Da gaske?”. Ya faɗa a hankali yana sake matsar da fuskarsa dab da tata har hancinsa na gogar nata. Cikin sarƙe idanunsa cikin nata ya sake faɗin, “Yaushe zaki daina rashin ji ne?”.

         Duk yanda taso bashi amsa ta kasa. Saboda goga mata lips ɗinsa da ya farayi akan nata. Tai ƙoƙarin kauda kanta gefe, yay saurin tarewa da nashi yana faɗin, “Uhmyim?. Faɗamin yaushe zaki san kin girma?”. 

     Ba ƙaramin harbawa zuciyar Aymah tayiba saboda jin a yanda yay maganar, kafin tai wani yunƙuri ya haɗe bakinsu waje ɗaya. Tabbas yau kam tamafi ranar shan chocolate, dan Yoohan ya tabbatarma Aymah a matuƙar zalame yake dason kasancewa da ita. Duk yanda yaso sassauta mata ya gagara, sai da ya ɗora mata sabon salon karatunsa mai wahalar haddacewa.

       Gaba ɗaya kukan da taso masama sai ta nemesa ta rasa, sai wani irin tsoro da matsananciyar kunyace da bata taɓa karo da itaba a rayuwarta ta lulluɓe ta. Tunda ta samu ya barta ta tura kanta cikin filos bata sake yarda sun haɗa idanu ba. Sun kwashe mintuna talatin a kwance kafin taji ya sake matsota. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yayi ba jin ya kwanto a bayanta. Amma sai ta daure tana ambaton sunan ALLAH. 

         “Akwai matsala fa”. 

   Ya faɗa a cikin kunnenta yana tura hannunsa a rigarta. Saurin riƙe masa hannu tayi ta zabura zata matsa yaƙi bata space. Dole ta haƙura sai daifa mutuniyar taku tsorone fal cikinta. 

       “Kin jamin sai nayi wanka, kuma ni ban iya ba”.

        “Hu'um. wankan ne baka iyaba? Babu dai ƙyau manya na ƙarya”. Tai maganar da son jan jikinta. Saurin sake ruƙota yayi ya matse. A kunnen nata Yace, “Bafa normal wanka bane, Uncle ya sanarmin a addinin musilinci wanka ya kasu kashi da yawa. *_Fitar maniyyi kai tsaye, ta hanyar jin dadi daga mace ko namiji. 2. Ɓoyewar kan azzkari a cikin farji. 3. Idan mutum ya mutu ya wajaba ayi masa wanka, sai dai in shahiɗi ne. 4. Musuluntar kafiri ko wanda ya yi ridda. 5. Jinin al’ada. 6. Jinin biki (wato jinin haihuwa). 7. Wankan jumu’ah. 8. Wankan shiga harami (da hajji ko da umarah). 9. Wanka ga wanda ya yi wa mamaci wanka,  Wankan idi biyu (na zuwa karamar sallah da babbar sallah). 10. Idan mutum ya farfado daga hauka ko 

farfadiya. 11. Wankan shiga Makkah.

12. Wanka domin sallar kisfewar wata ko kuma rokon ruwa. 13. Wanka na mai istiha a kowacce sallah. 14. Ga kowanne jima’i an so a yi wanka._* �kinga kenan yanzunma sai nayi fa tunda kin sakani na fitar da......”

     Wani irin wuntsilowa Aymah tayi ta dafe masa baki tana faɗin, “Na shiga uku ni Zainab, ni dai wlhy babu ruwana”. Ta fashe masa da kukan taɓara.

        Wani mugun dariya ne yaji yana taso masa. Amma sai ya danne da ƙyar dan karya ƙara tunzurata a samu matsala. Hannu yasa ya janye nata dake akan bakinsa. Fuskarta kuma har yanzu tana a ɓoye. “Okay yi haƙuri bake bace nine. Yanzu dai kisan yanda zakiyi dani lokacin salla yayi”.

        “To ni ya kakeso in maka?”.

   “Ki koyamin”.

Tamkar zata fasa masa sabon kuka tace,  “ALLAH ya sani nama fasa zaman hutawar ka maidani Nigeria kawai tunda na warke”.

      Shi dai dauriya yaketa yi dan kar yay dariya matsalar tafi haka. yace, “To naji, yanzu dai tashi muje ki koyamin yanda zanyi wankan”.

       “Ni dai babu inda zanje, idan kanaso na koya maka a haka kaje kayi abunka”. 

       “A'a gaskiya, sai dai fa kiyimin practical zanfi fahimtarki. Haka ake malami yayta ragema ɗalibi mudun koyarwa”.

       Shiru tayi taƙi motsawa, taki kuma tanka masa. ya tashi zaune yana faɗin, “Okay shikenan, bara kawai na kira Uncle saina sanar masa abinda ya faru daga nan ya koyamin yanda zanyi wank.......”. Zaune ta tashi dingangan ta ɗare masa jiki da danne bakinsa da hannunta tana waro idanun dake cike da ƙwalla.

       “Yanzu dan baka da kunya sai ka kira Abbana ka sanar masa wannan abun?”. Hannunta ya ture yana marairaice fuska shima. “To yaya kikeso nayi ne Sweet girl? Kinga dai babu damar nayi salla babu wankan nan? Kema kanki nasan fa sai kinyi”. Ya kai ƙarshen zancensa da kashe mata ido ɗaya. Filo ta jawo ta maka masa a hannu sannan ta sauka masa a jiki tana ƙunƙuni. Duk yanda yaso danne dariyarsa ta gagara sai da yayi abinsa. 

        Itako data sauka a gadon sai masifa takeyi a ranta tana sharar ƙwallan da babu tantama najin kunya ne. Shi dai Yoohan ganin ya samu yanda ya keso tasowa yayi ya biyota inda ta koma ta zauna akan sofa tana sharar ƙwalla. Ɗaukarta yay cak zuwa bayin tanata wantsala ƙafafu da faɗin ita ya sauketa. Tama fasa koyawar yaje yay Searching a Google ai zai gani. Ko jintama shi bayayi sai da ya direta cikin wajen wankan, zata gudu yay saurin kunna shower ɗin. A take tai musu jalab da ruwan data sheƙo. Ya jawo hannunta ta dawo saman jikinsa. Jin santsin ruwa zai jata ta faɗi dole ta rirriƙesa ruwan na sauka musu a jiki. Da wannan damar Yoohan ya kafe gaban rigarta daya jiƙe da ruwa komai ya fito yanda ya kamata da kallo. Bata fargaba sai da taji hannunsa a wajen. Ƙasa tai da sauri tana ture masa hannu. A ranta kuwa al'amarin sake firgitata yakeyi. ƙara ƙarfin shower ɗin yayi, hakan yasata tilas ta sake miƙewa tana sharce ruwar dake sakko mata a fuska ko gani da ƙyau yana neman hanata. Numfashi ma takai da baki take firzarwa. Shi kansa ruwan ya masa yawa. Amma saboda karta gudu yay haƙuri yana saka hannu yana sharcewa kamar yanda takeyi itama. Sai da ya tabbatar sunyi jagab sannan ya kashe shower ɗin. Ya koma hanyar ƙofar wajen wankan ya tsaya. A mamakinta sai gani tai ya fara cire rigarsa. Ƙasa tai da kanta gabanta na faɗuwa. Ganin wandonsa ya saɓulo ƙasa ta ƙara kiɗimewa. Da sauri ta juya bayanta. Hakan ya bashi damar matsawa ya manna bayanta da ƙirjinsa. 

      “Karki zama malama mai yima ɗalibanta rowar ilimi fa”. Yanda yake maganar yana yawo da hannunsa akan cikinta sai ya nema sake susutata. Tama rasa tunanin da zatayi akan wannan al'amarin nasa mai wahalar fashin baƙi. Tanaji tana gani yay amfani da ƙarfinsa wajen zame mata riga da wandon jikinta. Sai dai fa duk yanda yaso cire harna cikin taƙi yarda sam. daga ƙarshe ma sai ta saka masa kuka. Ƙyaleta yayi ganin dai ankai inda ma baiyi zatoba. A haka ta fara ƙoƙarin koya masa wankan duk dan ta samu ta kuɓuta daga wannan dabaibayin da yayma rayuwarta baki ɗaya.

      Sai da tai nisa a koyawarne ta fahimci ya iya, dama ashe kawai danya bata wahala da kallar mata jikine ya sashi cewa ta koya masan. Wannan haushin ya sakata harya ƙarasa wankan ya fita ya barta dan taki yarda tayi ita tana antaya masa harara. Duk da ƙaryar datai masa na cewar babu wani wanka daya hau kanta yana fita kuwa sai da tayisa. Dan duk wautarta tasan abinda takeyi tunda tanada ilimin addini. Aiko dai ansha ƙunƙuni. Tana cika baki da iska ta miko hannu akan ya bata Bathrobe da towel, dan yana a bayin bai fitaba. 

      Hand dryer ɗin hannunsa ya ajiye. Ya ɗauki rigar wankan ya kai mata sai dai babu towel. Hannun nasa ma sai da ya sha harara sannan ta amsa. Ganin babu towel ɗin kuma taita ƙunƙuni. Koda ta fito kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta ganin daga shi sai towel iya ƙugu zuwa gwiwa. Shiko gashinta dake ɗigar ruwa yabi da kallo. A cikin ransa dariya ya sanya mata yana faɗin, ‘Yarinya ashe kinada lafiya tunda saƙona ya isa inda na aikashi?’. A fili kuwa sai ya fuske abinsa. Tai saurin ɗaukar towel ta naɗe kanta wai dan karya gani.

      Ƙarasa hidimarsa yayi ya fito ya barta. Koda ya fito mai ya shafa yay shiri cikin ƙananun kaya. Baƙin wando da pitch color ɗin shirt mai dogon hannu. Yana fesa turare ta fito.  

       “Kiyi shirin fita”. Ya faɗa yana ajiye turaren.

     Bata tanka masaba. Tai tsaye har sai da ya matsa a wajen sannan ta buɗe akwatin nasu ta ɗauki jallabiya ɗaya. Bayi ta koma ta sanyo sannan tazo ya jasu salla. Suna idarwa yace ta ƙarasa shirin yana zuwa.

       Fita yay, ita kuma ta miƙe ta shafa mai, da ƙarasa kimtsawa. Tana gamawa kuwa yana dawowa. Zata fara feshi da turarensa ya amshe yana faɗin, “Silly girl ya isa haka dan ba tallanki nazo yima Austrian ba”.

     Ita dai bata tanka ba. Bakuma ta yarda sun kalli juna ba dan wannan fushin da takeyi tsabar jin kunyarsace kawai ke ɗawainiya da ita.

        Tsaf suka fito abinsu gwanin sha'awa. Tamkar ka sacesu ka gudu. idan ka gansu sai ka ɗauka ƙaramar ƙansawarsa ce ma. Yau dinma bata cuci kantaba sai da taita kalle-kalle har suka fito ƙaton reception ɗin hotel ɗin. Zuwa yay yayi signing kamar yanda dokarsu take. Daga haka yaja hannunta suka fito............✍


No comments

Powered by Blogger.