Najma 9-10

 


👄👄👄👄👄👄

      *NAJMA*

💋💋💋💋💋💋

By maman noorul hudah


    Paid book ne

    09090112846


🅿️9️⃣🫦1️⃣0️⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


      Tace"Kai haba karama dani har wani zuwa Hira zakayi "ta Kare da rufe fuska 


Yace"toh Ni ba yayanki bane"


    Cikin Kau da Kai tace"injiwa dangi iya ko na baba"


    Yace"kawai kalan dangi ne irin tawa "


Tayimurmushi ta Fara kiciniyar bude motar tace"muje ka gaida kakana "


Yace"ok"ya bude Mata mota tana fita ta halce a guje ta karasa gun  Abbu ya fito cikin tafiyarsa na kasaita da ji da Kai Kana ganinsa ka gan  naira ya zauna ta 

 Ya karasa 


     Abbu ya kalli uwani yace"ke da wa?"


Tace"wani Dan birninne ya Zo yace Yana son zaman yayanah "


     Ya girgiza Kai ganin ya karaso cikin Ladabi saif ya duka ya gaisheshi yace"Ina yini abbunmu min sameku lafiya"


        Cikin mutuntuka Abbu ya amsa yace"ya ka baro gida?"


Yace"alhamdullilah Abbu"


Abbu yace"toh maddallah Haka Mike sonji kai Dan garin nanne?"


Murmushi saif yayi yace"eh Abbu baka ganeni ba nine fah jikar malam dauda d'an alhaji Musa"


Abbu ya Bude Baki da mamaki yace"Allah me iko badai saifudeen  ba "


Cikin Jin kunya da ya rasa meya kawo sa ya dukar da Kai yace"eh nine saifullahi abbu ya kwana biyu "


Abbu ya Kai hannun Baki Yana mamaki yace"Allah me iko ka zama baban mutum yanzu wani aiki akene "


         Yace"yanzu Ni lauya ne Ina da chamber Dina 


        Kallonsa kawai uwani keyi ta gansa mugun kyakyawan nan...ga fatar jikinsa dake d'aukar Ido idanunsu na shigan na juna ta sakar me murmushi 


      Mikewa yayi yace"toh Ni Zan karasa gida Abbu"


Yace"toh ya kamata ka je ka huta kaji,ai ka Sha hanya dukda babu nisa da cikin gari'"


     Ya mike ya sallamesa Abbu cikin girmamawa ya sake sallamarsa sanan yayi gaba uwani ta bishi a baya 


Yana Shiga mota ta zaga tace"Dan Allah nace ko in shiga muje in gaida Yan gidan naku?"


            Dariya sosai yayi yace"me zai hana Amma je ki Fara fadawa abbu Zaki bini tukkunah sai mu tafi 


Daga gindi motar ta d'aga murya tace"Abbu zanje gaida mutan gidansu "


Yace"sauka lafiya 


    Kallonta yayi yariya ce sosai bazata wuce Sha hud'u ba kamar  shekarunta haka girman jikinta yake yanzu ma ta Fara kirgan dangi Fara ce Sol har hasken ya so yin yawa dan farin nata mai hayaniya ne  ga uban Suma Mai tsayi da Basu da cika ko kad'an sai tsayi dan sai ka dau foreigner ce ita ga fuskar karamin tsam Bata da fadin fuska sai cute bakinta dake d'auke da pinklips dinta sai eyelashes dinta Dake kwance bakake kyakyawa ce ko ta Ina a Haka ya tada motar tana me Hira Yana biye Mata 


Tace"motarka sanyi sai Nike ji ma kamar zazzabi zai kamani wallahi 


            Yace"toh bari in kashe  a/cn,gyara Zama tayi tace"da dai yafi Kam daman kasan inda zaka taba a daina Jin sanyi ka ki kashe salon mu mutu,mu shiga uku 


     Parking yayi dai'dai kofar gidan yace"kina tsoron mutuwan ne?"


        Tace"ba Dole ba Ni din guda nawa ne "yayi dariya ya fito ya bude Mata Suka shiga cikin karamin gidan kakan nasa sai rabtaba sallama take 


          Baaba na ganinsa ta Fara lale marhaba lale su said ne a gidan namu?"


            Ya saki murmushi yace"yau dai nace Bari in zo in gan tsohuwar matan nawa kewarta na niman zautani"


      Ta washe Baki da babu cikakka hakora ta shiga ta kawo Masa tarbama ta shimfida Masa sai a sanan suka Fara gaisawa da baaba tana amsashi cikin so da kauna da Kuma farin ciki sai washe baki take tana nuna farin cikin da ya mamayeta 


          Yace Ina abokin nawa ne"


Tace"ai ya fita gona be dawo ba ai su ba a ganinsu a wanan lokacin 


Agogon hanunsa ya duba ya gan past 12am sai yace"gonar nada nisa ne"


Kafin tayi magana uwani tace"Ina yini baaba 


Sai yanzu baaba ta maida hankalinta gun uwani Dan harga Allah ta ganta but ganin saif ya d'auke Mata hankali 


    Cikin sakin fuska tace"lafiya Lau uwani ya su umma naki da kawata iya"


Uwani tace tana can gida zaune gu d'aya sai zuba mulki 


       Baaba tace"Ni ban tambaye ki wanan ba"


Tace"ai nayi shiru baaba"

Saif yace"kin santa kenan 


     Tace"waye be San uwani ba a garin Nan a Ina ma kuka hadu 


     Yace"a hanya ta had'a fad'a *


    Baaba tace"kad'an da aikin uwani ai"


      Tace"rayuwa kenan Ina zaune ana cin duduniyata ba komai ke baaba in Baki sun  zo ba a basa ruwa ne"



     Baaba ta rike Kai tace"shaf na mance Ina zuwa said"ita saif din ne bata iya Kira ba 


Yace"karku damu baaba Ina ma da ruwa a mota  na Sha "


Uwani tace"Daman Wai ruwan Zaki basa haba baaba ai bakonka annabinka Ina laifin ki siya Mata na kwalba ya d'aga Kuma sai a yanka Masa kaza cikin zakarunki jikanki nefa ba in ya tafi kin San Randa Zaki gansa ne "shidai kallonta yake


Baaba ta mike ta fita ba a Jima ba sai gata ta dawo da wani d'an makotansu saurayi 


     Tace"Kai salisu kamo min zakara mafi girma a kejin nan kafin uwani tasa ni a bakin duniya 


     Shidai murmushi yayi ya mike yace"naj kin San gonar"


Tace"eh na sani "


   Yace"muje "


     Saida ta Kuma  cewa"eh "


Yace"muje gonar nace Miki"


        Tace"na_am


    Yace 



Maman Nur

No comments

Powered by Blogger.