Min Qalb 21-25

 _MQ 21_

**********

Seat din gaba yasakata ciki tareda 'dan kwantar da seat din ya rufe ya zagaya yashiga motar ya tayar yabar gurin cikin gudu sosai,

Cikin mamaki securities suka firfito Amma suna ganinsa sukai saurin bude Masa gate din suna Masa adawo lfy kota kansu baibiba ya fice.



Anty zarah sai alokacin ta tsaya sake da idanuwa tana cewa"


To Ina zai iya da ita shi kadai daya Bari nabiyosu,

Kiran khalil ne yashigo wayarta cikin sauri ta dauka tana fada Masa MD ne  yatafi Kai Amatun asibiti.....


What????""""yafada da sauri cikin firgici Yana cewa'"


Me umme tace?

Yaushe suka tafi??


Umme Bata daga wayarba gashi jini yafara balle Mata shine yatafi kaita da kansa,

Dr Ina fatan kada wani Abu yasamu cikin Nan Dan Allah ka Kira asibiti tun kafin su Isa kafada musu suyi duk iya qoqarinsu Dan Allah karsu Bari cikin Nan yasamu matsala.


kasa Magana yayi ya kashe wayar tareda Kiran Dr Fatima dayasan asibitin na hannunta yanzu tunda bayanan cikin tsananin damuwa da tashin hankali yayi Mata bayanin abindake faruwa.


Cikin sauke numfashi tace"


Karka damu Bari su iso Ina asibitin yau zanyi call(night) ne Inshallah za'ayi yanda aka Saba Mata duk wata,

Problem din dai shine sunriga sunga cewa tafara bleeding ya zamuyi da wannan?


Just handle everything please Dr Fatima 

Nabar Miki komai ki kula dashi nidai kawai please Dr Fatima Amatu azaban datake ciki nakeson kifara bi takai 

Inaji ajikina tana cikin azaba sosai Dan Allah Dr Fatima ki kularmin da ita gobe zan biyo jirgin Rana nadawo bazan iya daukaba 

Tafiyan kwana daya harta Fara shiga abubuwa iri iri.....


Calm down please Dr khalil komai zai zama daidai Inshallah Babu Abinda zai samu Amatun zanyi iya dukkanin qoqarina gurin ganin Babu Abinda zai sameta.


Thank you Dr""yace Yana kashe wayar sbd Jin ana buga office din datake.


Tun kafin ta aje wayar nurse Abida tashigo tana cewa'' 


Dr Fatima ga MD ZABEERA nan matar Dr Khalil ya kawo it's emergency mun karbeta ke ake jira.


Medical glass dinta kawai ta dauka ta miqe suka fito sister Abida nasake Mata bayanin taimakon gaggawar dasuka Bata.


Tana zuwa taga halinda Amatun take ciki take tasaki wani guntun murmushi sbd ganin yanda Dr khalil ya daga hankalinsa akan alamarin ba haka bane menstrual pains ne kawai.


Nan tahau dubata tareda Bata allurai Dan samu 'dan relief tareda qarin ruwa sai paracetamol data Bata.



Tana fitowa daga cikin emergency din sister Abida ta biyota tana cewa''


Dr Fatima zamuyi shifting nata ne zuwa Amenity ko kuwa?


Yes u can shift her Amma kafin Nan kufara taimaka Mata ta gyara so that kar jinin ya qarasa Bata Mata jiki,


Ok zamu Bata pad ne kokuwa abata cotton tayi amfani dashi,

And dose na injection dinta after 2 hours ne zamu sake Bata parainject din??


Yes after 2 hours ko Kuma 3 hours tunda menstrual pains ne kawai.


Ok.


Sister Abida na barin gurin Kiran Dr khalil ne yashigo wayarta saidata saki numfashi kafin ta dauka tana cewa''


Kafin kace komai Dr  khalil please listen to me

Maganar gskia Dr yarinyar Nan tunda har kasan kowane wata irin wannan matsalar ta al'ada na damunta Kaine kawai zaka iya magance Mata matsalar sbd kada wata Rana abin ya zarce ya zamar Mata matsala babba,

Mu'amalar aure ne kawai zai kawo Mata qarshen wannan monthly pains din.


Zata sake Magana ya katseta da cewa"


Dr Fatima lafiyanta kalau yanzu dai ko??


Eh komai ya daidaita zuwa asuba zasu iya tafiya gida..


Ok thank you Fatima

Sauran maganar please mubarta idan nadawo zamuyita.


To kawai tace tareda kashe wayar ta wuce tabar gurin batareda ta juya taga MD dake zaune a bayantaba idanuwansa ne kawai ba'a kanta ba Amma hankalinsa gabaki daya akan zancen datayine tunda nurse Abida har Khalil dasuka Gama Magana yanzu,


Shiru yayi Yana qoqarin nazarin fahimtar zancen sbd idan har yayi amfani da iliminsa na 'dan Adam Koda baitaba haihuwaba ko samun ciki da amatarsa yasan dai Mai ciki Bata period,

Hakama Mai aure harda ciki baza'a ce Yana buqatar rayuwar auratayyaba kafin yasamu saukin cramps,


Bude idanuwansa dake lumshe yayi ahankali Yana tunanin Khalil na boye wani Abu gameda yarinyar Nan wanda yake da matuqar mahimmanci ko hadari,

Koma dai menene ba huruminsa bane Abu dayane zai fadawa Khalil yasan Abinda yakeyi.


Dakin da aka maidata ya qarasa yashiga lokacin ta bude idanuwanta daidai shigowar tasa sai idanuwansu suka shiga cikin na juna 

Ita tayi saurin yin qasa da idanuwanta sai kawai idon nata ya sauka kan farar jallabiyarsa da jini ya Bata daga gaba gurin cikinsa take tayi saurin rintse ido akaro na farko wata irin kunya me tsanani ta kamata saita samu kanta da kasa bude Ido ta kallesa.


Shi kuwa dauke Kai yayi tareda kallon inda yaga ta kalla din kafin ta rintse ido 

Idonsa ya sauka kan abindake rigarsa 

Saurin dagowa yayi ya kalleta yaga itama shi take kallo tana jiran reaction dinsa

Sai kawai shima yaji abin wani iri sbd shi ko so daya Koda Wasa baimasan ya kalar jinin Mata yakeba Dan ko amafarki baitaba ganin na matarsa ba bare gashi yanzu Yana ganin wannan ajikinsa ma......


Fuskewa yayi tareda juyawa yabar dakin tanajin wani irin yanayi kamar yanajin kunyar kansa.



Itama Jin tayi kamar qasa ta tsage ta shige har batasan lokacinda ta Dan daki kantaba tana cewa''


Wannan abun kunya yayi Miki yawa amatu.



Daga shi har ita kowannensu kasa hada fuska yayi da Dan uwansa sosai ya hade fuska har aka sallamesu suka dawo gida zuwa lokacin Tama fisa Jin kunya ganin yanda ya fuske ko nuna yanani baiyiba.


Har suka Isa bame motsi cikinsu ita tafara fita tayi ciki da sauri tana gyara zaman hijabin da Dr Fatima ta Bata ta sanyo.


Anty zarah dake safa da marwa a Palo sbd rashin sanin ya ake ciki gashi yabar wayoyinsa gida 

Tana ganin Amatu tayo kanta da sauri tana riqota zatai Magana kenan sai gashi shima yashigo fuskarsa na Kan agogo zatayi Masa gamana idanuwanta suka sauka akan rigarsa dake daukeda stain din jinin Amatu Wanda ta tabbatarda daga jikinta ya fito sai ta dago ta kalli fuskarsa dayake qoqarin rabata ya wuce 

Sai kawai taji wani irin yanayin kishinsa ya Dan shigeta 

Ta juyo ta kalli amatu da kunya qarara ta bayyana Kan fuskarta har tana sauke Kai 

sai ta watsar kawai da tunanin komai cikin kulawa tana Jan Amatun zuwa daki tace"


Amatu ya babynki?

Ina fatan Babu Abinda ya samesa??


Daga Mata Kai Amatun tayi zata sake mgn Kiran Dr khalil yashigo wayarta data Bari gida Kan gadonta.

##Mamuh#


Please Dan Allah kuyi manage inada uzuri ne yau🙏🙏🙏




ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899[3/31, 10:57 PM] Zafafa: *_MQ 22_*


*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*


*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*


*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆🏾♀️🙎🏽♀️


*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaɗa ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯🏽♀️👯🏽♀️


*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*

*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*


*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*


*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾🤞🏾



************

Cikin kulawa yake tambayarta ya jikin nata itama cikin kulawar take amsawa tanason fada Masa komai na Abinda yafaru tun zuwansu asibiti tanajin nauyin anty zarah 

Ganin hakan yasa anty zarah miqewa tayi toilet Dan taimakawa ta hada Mata ruwan wanka tana hamdalar cikin dayake lafiya kalau Babu Abinda ya samesa.


Tun tanayin wayar a zaune harta Dan jingina da Kan gadon tana rufe idanuwanta tana sauraran abubuwan da Dr ke fada Mata tana murmushi sbd sbd girmqn mahimmancinta a rayuwarsa yake fada Mata Yana Mata fadan ta rage ciye ciyen kayan shiririta.


Ganin ba gamawa zasuyiba yasa anty zarah karbe wayar tareda kashewa Tana cewa''


Tashi kije kiyo wanka yanda jikinki zai qara warwarewa,


Miqewa tayi tana murmushi har lokacin ta cire kayanta tareda daura towel ta fada toilet din.


Ahankali take wanka tana tunanin Rabin ran Anty zarah ta yanda zai iya wanke jinin daba na matarsa ba,

A yanda yakeda tsafta da Shan qamshin Nan Bata tunanin zai iya taba rigar bare ya wanke da kansa,

Duk yanda za'ayi ita zata karbo rigar ta wanke da kanta tunda jinin natane koba komai abin kunya ne gareta wani ya taba jinin al'adarta Wanda ba mijintaba.


Kodata fito wanka anty zarah na dakin tana sauke abincin da hafsatu tashigo dashi Wanda akayi domin Amatun kawai.


Tasamu qarfin jiki matuqa sosai datayi wankan shiyasa cikin walwala ta shirya bayan tafara shafa Mai kadan ta sanya doguwar riga me Fadi sbd ganin anty zarah nata kallon cikinta cikin kulawa itadai lafiyar cikin ce a gabanta.


Zama tayi suka hau breakfast tareda anty zarah din suna 'dan taba firar Dr daya damu da haryana cewa zai dawo yau daqyar ta hanasa.


Suna gamawa ta hau gadonta ta mimmiqe Anty zarah takira hafsatu tana Mata tausa ahankali ahankali har bacci ya dauketa sai alokacin Anty zarah tasaki ajiyar zuciya tareda miqewa tabar dakin.


Dakinta tafara zuwa ta sauya kayan jikinta tareda qara shafawa jikinta body mist ta fito tana gyara zaman qaramin qyalen dake daure akanta Wanda yaqarawa kyakkyawar fuskarta kyau ta nufi dakin mijinta.


So daya tayi knocking tareda bude qofar bedroom dinsa tashiga bakinta daukeda sallama Mai sanyi.


Tsaye yake gaban mirror daureda brown towel iya qugunsa Yana shafawa jikinsa spray din Hugo boss fuskarsa a fuske kamar dai koyaushe.


Kallon budadden bayansa tayi dayake fari tas Babu tambon sai qyalli yakeyi kamar na mace har zuwa wuyansa da faffadan qirjinsa datake gani ta jikin mudubi Wanda tuni yaji ajikinsa shi take kallo saiya juyo ahankali yayi Mata kallo daya yaga yanda take kallonsa cikeda so da qaunarsa saiyaji zuciyarsa ta danyi sanyi sbd yasan zarah mace ce me tsananin hakuri da juriya Wanda yasa yake matuqar respecting dinta akan hakan,.


Gabanta ya qaraso ahankali ya tsaya Yana kallon fuskarta itama shi take kallo tana jin sabuwar soyayyarsa na shigarta ahankali ta matsa ta shige jikinsa tareda zura hannuwanta bayansa ta rungumesa ahankali tana kwantarda kanta akan qirjinsa tareda lumshe ido tana sauke boyayyar ajiya zuciya.


Sai daya jima shiru Yana sauraran bugun zuciyarta dake dukan qirjinsa kafin ya daga hannuwansa ya rungumeta ahankali tareda lumshe ido ya sauke numfashi,

Sun dauki kusan mintuna biyar ahaka  shiru Babu me motsi kafin ahankali ya dagota daga jikinsa ya dauketa gaba dayanta ya nufi gadonsa da ita Yana kallon fuskarta data soke cikin qirjinsa,

Yana kwantar da ita Kan gadon yayi Mata rumfa da fadadden qirjinsa Yana Kai hannu Kan zib din gaban jallabiyarta.



Bayan wasu lokuta haryayi sabon wanka ya fito ita alokacin take qoqarin saukowa daga gadon tayi saurin daukar fadawa toilet din nasa duk da shi mutum ne dabai cikason wani na amfani da toilet dinsaba Amma kasancewar yanzu Basu kadai bane Dole bazata iya fita ahakaba kamar da wani zai iya ganinta.


Wanka tayo tafito lokacin harya shirya cikin farin filtex transparent da hular qube coffee brown Yana fesawa jikinsa turarensa na IMPERIAL MAJESTY.


Kayanta ta maida bayan tagama goge jikinta ta shafa oil kadan tareda turarensa.


Sai alokacin ta tunoda Abinda yakawota ta kallesa Yana qoqarin daukar wayarsa dake Kan bedside cikin taushin murya tace"


Am...amm dama rigar dazu ta jikinka nace ko zaka kawo na bayar a wanke sbd Naga ta samu lalacewa....


Cak ya tsaya daga Abinda yayi niyar Yi hakanan yaji maganar Tata kamar ta ciza ransa,

Idan tunaninsa na aiki daidai yasan me wankin zarah din namiji ne Wanda kusan duka familyn shike yiwa wasu da yawa daga ciki wanki,

Tana nufin shi gardin zata bawa jinin dayake sirrin Amatune ga wani gardin ya wanke???


sake 'dan tamke fuska yayi tareda juyowa ahankali kamar zai kalleta saiya fasa ya juya ya dauka wayarsa batareda yabata amsaba yafara qoqarin barin dakin.


Saurin biyosa tayi tana cewa''


Nace bakajiba rigarka ta yau da safe nakeso kabani zanbawa wa....


Kallon daya dago yayi Mata yasata matsawa baya kadan tana sauke Kai zuciyarta na bugawa da sauri.


Kamar zai wuce baiyi Magana ba saikuma ya tsaya batareda ya juyo ya kalletaba cikin sautinsa me daukan hankali yace"


Karki sake kawo maganan riga da Abinda yasamu riga agabana ok????


Kallonsa tayi tana son sake maganar Amma ganin yanayinsa na Babu Wasa ko sakin fuskarsa yasa ta 'daga Masa Kai tana cewa''


Adawo lfy.


Can qasan maqoshinsa yace"


Thank you"tareda wucewa ya sauko qasa tareda ficewa zuwa office. 

##Mamuh#


Gashinan please yauma kuyi manage gobe Inshallah zamu koma pages dinmu masu tsawo yauma uzurine ya riqeni kuyi hkr da wannan din🙏🙏🙏




ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[4/1, 10:47 AM] Zafafa: *_MQ 23_*


*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*


*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*


*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆🏾♀️🙎🏽♀️


*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaɗa ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯🏽♀️👯🏽♀️


*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*

*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*


*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*


*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾🤞🏾



**********

Yinin ranar cikin farin ciki dukkaninsu sukayisa sbd musamman Andi da Modibbo suka aiko akaje da Amatu gurinsu suka duba lafiyarta qarima Dr Fatima Dr khalil yaturo ita taduba musu lafiyarta taqara Basu tabbacin komai lafiya daga ita har cikin,

Musamman Andi yayowa Amatu kyauta ta musamman Wanda tasake qara Mata baqin jini da qiyayya gurinsu umme da Haj maryam wadda taga Salman dinta na wani rawar Kai akan Amatun tun agabansu Modibbo ta buga tsalle tace"


Wlh Salman karka kuskura kace zakamin kwashe kwashen bacin Rai Dan ni ba dauka zanyi ba.


Ganin basusan akan me take Magana ba yasa kowa tayi watsi da ita saishi uban gayyar datake Magana akansa yafahimci Abinda take nufi sai anty zarah da Amatun dake aika musu da kallon hadarin kaji sbd yanxu daidai takeda kowa kaf cikin zabeera sbd Andi daya tsaya Mata.


Koda suka fito a hanyarsu ta komawa suka hadu da Nuratu tana ganinsu tahau yada maganganu in marasa Dadi Har Amatu zata tankata anty zarah tayi saurin riqo hannunta tajata  sukabar gurin sunaji tana cewa zarah din munafuka Amma Basu kulataba suka wucewarsu.


Da yamma Salman da kansa yazo ya maidata asibiti tasake ganin Dr Fatima suna baro asibitin kamar a mafarki sai kawai tagansu qofar gidansu yayi parking mota


Da sauri ta juyo ta kallesa bakinta da fuskarta daukeda tsananin mamaki da farin cikin dayasa takasa mgn sai kawai ta bude motar ta fito da gudu tayi ciki.


Da iyami tafara cin karo a tsaye tana kwashe shanya cikin tsananin farin cikin ganinta ta rungumeta tana cewa''


Iyami wlh bansan haka nayi kewarkuba sai yau Dana ganni a qofar gida Ina kawu da usi???


Kawu dake fitowa daga daki Yana jinta dama ya fito Yana ganin yanda Amatunsa ta koma take ya washe baki Yana cewa''


Maza kuzo mu shige daki kada Ido da baki suyi Miki yawa kinsan gidan harda qarin 'yan bani na iya aka samu.


Dariya tayi tana sakin iyami tace"


Yanzu nasan Ina gaban kawuna.


Kallonta iyami takeyi itama cikin Jin Dadi da farin cikin ganin yanda ta sauya tayi kyau kamar 'yar masu kudi har wani qyallin haske fatarta keyi ga suturar alfarma ajikinta sai annushuwa takeyi.


Dakin suka nufa suka zazzauna Nan aka nude sabuwar fira saiga shima usi dake shirye shiryen tafiya jibi yashigo Nan aka Dora firar ga fankasu da iyami tayi aranar dayaji miyar Naman rago da Ganda Nan aka kawo musu suka hau ci suna Santi musamman Salman dan shima yamasa Dadi matuqa.

Suna Nan saiga Kiran Dr khalil yashigo wayar kawu dauka yayi suka gaisa ckin sakewa kamar 'dansa na cikinsa yakejin khalil sbd shiga ransu da yayi iyami ce madai takejin nauyinsa na sirikantaka sbd tuntuni sunsan Amatu yakeso Dan Yama fada musu Kuma sunyi na'am da hakan jira kawai suke tadawo asa ranar aure,

Sabuwar Hira suka Dora da Dr din a waya su Amatu na fada Masa Abinda suke ci Yana cewa''


Umma iyami idan nadawo Nima shi zakibani wandama yafi nasu Dadi.


Murmushi iyamin tayi cikin Jin nauyinsa tace"


Khalilu duk Abinda kakeso idan kadawo Inshallah duk sainamaka su.


Yawwa nagode umma.


Kawu ke tambayarsa ya aikin dayaje yi dafatar akwai nasara??


Eh yace Masa Yana qarawa da alhmdlh Inshallah muna gamawa zan juyoma.


To Allah yakawo ku lfy.

Amin


Basu bar gidanba sai kusan yamma sosai Wanda anty zarah tayi musu Kira yafi a qirga 

Itama Saida iyami ta hado Mata fankasu suka je Mata dashi.


Kamar kada su tafi hakanan ta fito suka tafi tana sake dagawa Yan gidan hannu kowa nasakejin kamar kadata koma.


Saida suka biya sahad yayi Mata soyayya sosai har abin na Bata mamaki Amma ganin yanda ya dauketa kamar 'yar uwarsa ya nuna bayason godiyarta da mamakinta itama saita daukesa kamar usi Nan suka sake shiriricewa sai magriba suka kamo hanyar gida.


Suna tafe suna fira harda qyaqyata dariyarsu sukeyi Yana tuqi da gudu gudunsa aikuwa Basu ankaraba wata mota tayo Aron hannu a guje itama me motar yake tahowa,


Cikin wani razanannen firgici yaso kaucewa Amma ganin akwai express dayan gefen sai kawai yayi dayan gefen sukai Kan wata bishiya suka daketa Amatu da tuni ta saki ihun sadaqarwa kanta ya daki qofar motar tsananin tsoro da firgici yasata somewa agurin.



Cikin sauri ya juyo Yana qoqarin dagota Yana Kiran sunanta da qarfi cikin damuwa sbd yasan suman tsoroce kawai tayi gashi Babu wani abindama yafaru din sbd bai daki bishiyarba sosai.


Ruwan dayasha ya rage kafin alamarin ya dauka ya shafa Mata saigata tasaki nannauyan ajiyar zuciya a rude tana cewa''


Wlh banason na mutu yanzu saina cikawa Dr khalil burinsa na aurena.


Dariya maganarta ta basa duk da ta daki zuciyarsa Kuma.


Cikin kulawa yace"


Nima banason ki mutu sainaga rabon wace ke a qarshe.


Kallonsa ta juyo tayi cikin rashin fahimta tana qoqarin sake dawowa nutsuwarta.


Murmushi yayi tareda tayarda motar yayi ribas sukabar gurin Yana cewa''


AMATULLAH ki dinga tuna sauran bayin Allah yayin yiwa mijinki na baa dauraba addua.


Sake rudata yayi tasake juyowa gabaki daya tana kallonsa saidai ganin kamar reaction dinta nasake basa damar yadda da hasashensa koma dai yardarsa sai kawai ta basar da zancen tana dariyar tsoron dataji da sumanta tana cewa''


Dan Allah Dr Salman kada anty zarah tasani 

Tana sani zata Fara daga hankali ta fadawa Dr banaso ta daga Masa hankali.


Sai alokacin ya Dan juyo ya kalleta zuciyarsa na wani sarawa Yana maida hankalinsa Kan titi cikin sautin nutsuwa yace"


Idan zuciyarki na tsananin kulawa da qaunar Khalil haka

Meyesa zata so MD ZABEERA???


Cak ta tsaya gabanta yayi mummunan faduwa Amma sbd Bata fahimci zancen nasaba saita saki wani yaqen dolen Dole tana kasa juyowa ta kallesa tace"


Meye hadina da Rabin ran Anty zarah kuma?

Ko gaisuwa Bata hadani dashi bama ya cikin mutanen danake qauna gaba daya sbd halayensa na wulaqanta antyna.....


Baya cikin wainda kike qauna sbd shi sonsa kikeyi Amatu.,

Amatu bansan meyasa shedan yake yawo atsakaninmu ba dayake haifar Mana da wani tunanin dabai kamataba bayan sanin cewa ke amatsayin matar khalil kike,

Amatu nafada Miki hakane Dan kije kiyi tunani kada ki auri Wanda farin ciki ya cancanta a rayuwarsa ba dakon son maso wani ba,


Dr Khalil zabeera shine duk duniya cikin maza ayanzu yafi cancanta daya asameki gaba dayanki daga zuciya har ruhi da ganganr jiki

Dan haka kada ki azabtar da rayauwarsa ta basa gangar jiki da qauna kawai

Yana buqatar dukkanki gaba daya har soyayyarki da zuciyarki sbd koba komai shi din Asthmatic patient Wanda yakeda alaqa da zuciya 

Dan haka AMATULLAH kije ki zauna ki nutsu kiyi tunani ki Fara koyawa zuciyarki soyayyar khalil ba qaunarsa ba soyayyarki yake buqata.


Kallonsa takeyi sosai kanta na neman bugawa da maganganunsa ta girgiza Kai Yana rintse ido cikin rudewa take cewa''


Mezaisa naso Rabin ran Anty zarah ni Dr nakeso, shikadai nake qauna, shikadai nake tunani shikadai nake gani, shikadai nake.......


Mafarki fa???


Tsit tayi tareda kasa qwaqqwaran motsi sbd Jin tambayarsa,

Idan har ba qarya zatayi Masa ba to tabbas 'daidaikun ranakune Bata kwantawa batayi mafarkin Rabin ran antynta ba.


Cikin firgici ta dago idanuwanta na cikowa da hawaye zatayi Magana yayi parking Yana cewa''


Mun iso gida.


Da sauri ta juya ta kalla waje tagansu qofar part dinsu anty zarah din 

Ta sake juyowa gurinsa zatayi Magana cikin rawar murya da sarkewar tunani

Ya katseta da sakar Mata murmushi me sanyi sbd jikinsa da zuciyarsa dasukai sanyi idanuwansa na Dan sauyawa sbd yanayinta ya Gama tabbatar Masa da hasashensa katseta yayi cikin sanyi da cewa''


Kije ki zauna kiyi tunanin Abinda yakamata.


Shiru tayi tana kallonsa kamar bazata fito motarba saigashi kuwa motar MD ZABEERA ta iso gurin yayi parking Dan da kansa yayo tuqin yadawo gida.


Motarsa ta qurawa ido zuciyarta na bugawa da sauri da sauri kamar zata bullo qirjinta ta fito,

Saida yadauki mintuna biyu zuwa uku kafin yafito motar Yana amsa waya fuskarsa a 'dan sake Wanda yasata kusan suman zaune da sauri ta rintse idanuwanta tanaji kamar yanzu ne da Salman yayi maganar ya zuba Mata son MD din me tsanani cikin ranta ta girgiza Kai da qarfi Yana cewa''


Bazan taba son Rabin ran Anty zarah ba.


Bude motar tayi da sauri ta fito batareda ta sake waiwayo Salman ba Wanda tunda motar MD tashigo fuskarta ya tsurawa ido 

Jan motarsa yayi yabar gurin Yana sauke numfashi me zafi ya nufi gurin mum dinsa da tun rana take kiransa duk tabi ta hargitse ta daga hankalinta akan alaqarsa da Amatu Wanda yakejin da akwai matsala Dan kuwa kome zatayi bazai iya rabuwa dasu Amatu da familyntaba.


A sukwane tashigo ba cikin hayyacintaba tayi nisa cikin tunani da fargaba tareda tsoro taji andafa ta tayi  saurin dagowa sukai Ido biyu da anty zarah tana sakar Mata murmushi tace"


Amatu Yaya dai?

Sai yanzu kuke dawowa tundazu nakira Usman yace kunbaro.


Qaqalo murmushi tayi tana  qarasa shigowa palon tace"


Wani guri mukaje Salman yayi min siyayyar kayan babies da kayan dadi" ta qarasa fada tana qaqalo dariya sbd kawar da banzan tunanin dayake yawo cikin kanta.



Siyayyar ta miqawa anty zarah tareda fankasu din dasuka Zo Mata dashi 

Cikin farin ciki ta karba tabawa hafsatu tace ta zubo Mata a plate 

Ita Kuma dakinta ta nufa Dan yin wanka ta gyara jikinta Amma cewa anty zaran tayi zatayi sallah ne.


Wankanta tayo tareda shiryowa cikin riga da wandon bacci masu Dan kauri ta sanyo qatuwar rigar sanyi akai sbd ana Dan sanyi gashi gidan Sam komai sanyi sunsaba da rayuwar AC ta sanyo hula tareda slippers ta fito tana waya da Dr khalil Wanda yanzu take tsananin Jin kunya da tausayinsa.


Cikin annashuwarta ta fito suna wayar harda 'yar dariyarta sosai sbd labarin abincin dasuka ce na 'yan Chinese yake Bata kamar zaiyi kuka da amai

Ganin yanda labarin ke sakata nishadi yasa yaketa Jan labarin Yana sake fada Mata yanda kalar abincin yake da yanda ake cinsa sbd walwalarta na basa farin ciki da nutsuwa.



Dining ta nufa tana sake qyaqyata dariyarta datasashi tsayawa cak daga cin abincin dayakeyi akan dining din tareda zarah wadda yau duk farin cikinta a bayyane yake sbd gata ga Rabin ranta suna cin abinci tare.


Qoqarin zamata takeyi a dining din idanuwanta suka sauka cikin nasa daidai dagowarsa ya kalleta da idanuwansa dasuka narketa gaba dayanta saita samu kanta da kasa dauke idonta daga kansa zuciyarta na harbawa ahankali.


Sarqewa yayi sbd wani dalili daya kasa sani yafara tari ahankali Yana Kare bakinsa da tissue 

Anty zarah dake Shirin Magana tayi saurin daukar ruwan sanyi zata miqa Masa daidain Amatun ita Kuma ta miqa Masa juice cikin cup.


Kallon juna sukayi itada anty zarah din tayi saurin dire cup din tana barin gurin da sauri ya 'dan bi bayanta da kallo qasa qasa ahankali kafin ya karbi ruwan hannun zarah din yakai bakinsa ya kurba kadan ya ajiye yakai hannunsa ya dauki cup din juice din yakai bakinsa yasha kadan sai kawai ya miqe Yana cewa''


Alhmdlh I'm full.


Binsa anty zarah tayi da kallo harya haye stairs din zuwa samansa tana karantar yanayinsa 

Idan nazarinta yabata daidai MD na wasu abubuwan dabata ganewa kwanakin Nan duk da dai dama can Bata ganewa MD Amma dai yanzu kamar tana nazartan wasu abubuwan nasa.


Bin bayan Amatu tayi tana kawar da tunanin komai tana zuwa dakinta ta sameta Dr khalil na qoqarin cigaba da sata nishadi itama tana qoqarin nuna Masa nishadantuwarta sbd kada ta sace Masa gwiwa.


Palo suka dawo da anty zarah tasata gaba akan saitaci abinci ga cake din datakeso koyaushe Wanda ake Mata duk Bayan kwana biyu Amma ta kasaci komai ko ruwa ta kasa Sha sbd kanta dake daure tamau har wani sarawa yake Mata takasa cire tunanin komai cikin ranta saima wani irin tunanin MD din dayake neman zauta kanta bangare daya ga tunanin Dr da koma me zaije yadawo shi tayiwa alqawarin kanta matuqar suna raye saidai tunanin MD dakuma yake sake rikitata.


Miqewa tayi ahankali tace"


Anty kaina Yana ciwo sosai zanje na kwanta kozai rage.


Kallonta anty zarah din tayi tace"


Dakin daure kinci abinci ko kadan ne Kinga pasta ce aka dafa Kuma me ruwa ruwa ce zuwa anjima kadan lalacewa zatayi kada yunwar dare ta tayar dake ki rasa abincin ci yau ko fruits Babu a gidan Nan baa siyoba gashi rabonki da abinci tun rana da Kika ciyo a can gidanku.


Girgiza Kai tayi tana Dan dafesa tace"


Wlh banajin cin abinci saidai zuwa da safe idan ya warware zanci harda biyan bashin na yanzun din.


Miqewa anty Zaran tayi itama tareda wucewa gaba tana cewa''

Shikenan Allah ya tashemu lafiya Kisha magani kafin ki kwanta Dan Allah.


Hanyar dakin MD ta nufa tana gyara zaman rigarta a jikinta Wanda yasa Amatun binta da kallo idanuwanta na qoqarin cikowa da hawayenda suka sata saurin dawowa hayyacinta tayi dakinta da sauri tareda fadawa Kan gadonta tana rintse ido.



Tunda ta kwanta takasa bacci tana kwance ta qurawa Dan qaramin  hoton Dr khalil dinta Ido dake cikin qaramin frame gefen gadonta Wanda anty zarah ce ta kawo Mata.


Dr Dan Allah kayi gaggawar dawowa sbd Ina buqatar kayi saurin aureni na zamo mallakinka 

Bazan iya jira cikin Nan yakai wata taraba kadawo kasan yanda zakayi dashi nidai aurenka kawai nakeso yanzu fiyeda komai tun kafin zuciyata tafi qarfina.


Har qarfe goma sha biyu da arbain batayi bacci ba gashi zuwa lokacin yunwa tafara hanata sukuni sbd jikinta harya Fara 'yar makarkata 

Ta tashi zaune tana kallon agogo.


Saukowa Kan gadon tayi tareda mayarda qatuwar rigar sanyinta me kaiwa har gwiwa ta zura hula tareda sanyo slippers ta fito tana adduar Allah yasa abincin bai buga ba Dan wlh bazata iya kwana haka ba.


Tana fitowa ta nufi dining Kai tsaye daidai shima yafito daga dining din sbd abincin daya sauko ci Dan duk yinin ranar baici abinci ba sai Daren Kuma spoon biyu kawai yaci yatashi sbd Abinda yafaru gashi yanzu yasauko abincin ya buga.


Kallonsa tayi bayan itama ta bude abincin batasan lokacin datace wlh yunwa nakeji ni bazan iya kwana ahaka ba.


Palo yadawo Yana tunanin zancenta koba komai tunda tanada juna biyu ayanda sukace Dole tana buqatan abinci akai akai.


Shima Dole Yana buqatan abinci bazai iya kwana a hakan ba ya juya zuwa dakinsa ita Kuma tayi kicin ta hau dube dube Babu Abincin ci ta dauko ruwa Tasha taji cikinta na neman qullewa ta fito tana riqe cikin daidai ya sauko sanyeda riga da wando masu Dan kauri kamar na sanyi hannuwansa daukeda mukullan mota da wayarsa batareda ya kalli fuskartaba kamar bada ita yake maganarba yace"


Muje.


Tsayawa tayi binsa da kallo harya fice kafin tabi bayansa da sauri.

##mamuh#



ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[4/2, 11:30 AM] Zafafa: *_MQ 24_*




Tafiya sukeyi ahankali cikin motarsa Babu me Magana sai sanyin AC da qamshin turarensa daya Gama Kama motar dama can yake ratsata Yana Bata wani sabon yanayi cikin zuciyarta Wanda yasata fadawa tunani.,


Tuqinsa yakeyi cikin nutsuwa shima Yana jiyo siririn sahirtaccen qamshin jkinta na Shiga hancinsa ahankali Wanda kusan shima yasashi Shiga tunanin banbanta yanayin qamshinta Dana zarah.,

Istigfari yayi saurin Yi cikin ransa Yana Dan tsuke fuska tareda 'dan qarawa motar gudu.


Ganin sun kamo hanyar blue fox yasata saurin kallonsa murmushi na sauka Kan fuskarta tace"


Rabin ran Anty Dan Allah muje blue fox akwai abinci me kyau da dadi acan.......


Wani irin kallo ya juyo ya aika Mata Jin sunan data kirasa dashi Wanda yasashi qurawa cikin Idanuwanta Ido Yana son sake tabbatarda Abinda takirasa dashi  _Rabin ran anty_  yanda tafada sunan batareda kulawar komaiba yasashi yimata wannan kallon itama Jin idanuwansa akanta yasata kasa juyowa ta qurawa waje Ido Yana damqe hannunwanta dake rawa zuciyarta na harbawa.


Jin shiru yasata Dan dagowa tareda juyowa ahankali ta kallesa hankalinsa na Kan hanya saita qurawa fuskarsa da fararen hannuwansa dake tuqin motar cikin nutsuwa da qwarewa,

Kan fuskarsa ta tsayarda kallonta tana yaba kyawu da tsarin fuskarda ubangiji yayi Masa me daukeda da tarin kwarjini da Kamala,

Dogon hancinsa ta kalla zuwa manyan idanuwansa batasan lokacinda ta lumshe ido ba hawaye na gangarowa daga cikinsu batareda ta gogesuba cikin ranta tace"


Meyasa zuciyata ta zabi wahalar da rayuwata data Dr ta hanyar son Dan uwa mafi soyuwa agaresa?

Dukkanin kyawu da Abinda MD yakedashi Dr khalil dinta nadasu harma yafi MD din kyawawan halaye masu sanyaya Rai hasalima kusan kamanninsu daya sbd duk mahaifinsu Modibbo suka dauko har Khalil dinta ma yagi MD din hasken fata saidai MD ya nuna Masa gogewa da hutu irin na Boko da yawan qasashe suka hudasa sai kalar fatar mahaifiyarsa daya dauko me sheqi.


A harabar blue fox din yayi parking tareda Dan juyowa ya kalli gefenta tayi saurin share hawayenta tana bude motar ta fito tana washe baki cikin tsananin farin ciki ta juyo daidai ya zagayo tace"


Yau duk abindake restaurant dinnan saina cire kwadayinsa na tsawon aikin danayi anan din.


Bai kalletaba yayi gaba ta biyosa tana sake bayyanar da murnarta ta zuwa gurin.


VIP direct suka nufa inda tuni aka hau sintirin attending dinsu ga mamakinta kusan Rabin ma'aikatan gurin an sauyasu Nan ta bada odar abinci kusan kala hudu da tarkacen su fruit salad harda ice cream da furar blue fox din me shegiyar Madara da Laban yoghurts.


Table dinsu kusan kasa daukan abubuwan yayi sai kawai yayi odar  noodles with veggies salad da power drink yafara ci cikin nutsuwa Yana kallonta tana cin abincin cikin tsananin Jin Dadi Dan harwani lumshe ido takeyi tana cika bakinta da Naman kazar chicken rings dataji carrot da spices.


Yana kallo ta Gama yagalgala kazar ta janye gefe ta jawo shawarma tafara ci itama ta ajiye ta janyo soyayyan dankalin dayaji egg source 

Furarta ta janyo ta kurba ta lumshe ido tana cewa''


Wayyo Dadi" kafin ta aje tacigaba da cin noodles Kuma.


Jingina yayi da Bayan kujera Yana zuba Mata iduwansa masu karya kuzarinta tareda dukkanin nutsuwarsa Yana kallonta kamar ya baby a gabansa.


Saida tayiwa komai ci rabi aje rabi kafin ta qoshi ta dauki ice cream dinta ta bude ta diba tana hadiye yawun matsuwa taji sanyinsa ya sauka a bakinta taji anrike ice cream din

Da sauri ta dago idanuwansu suka shiga cikin na juna ahankali ya girgiza Mata cikin qaramin sauti yace"


This is not good for your health......


Kasa motsi tayi ta harya zare ice cream din daga hannunta ya ajiye idanuwansu na cikin na juna Saida waiter din dake tsaye yayi gyaran murya da qarfi Yana sake miqawa MD din bill dinsu.


Fuskewa yayi Yana Dan tamke fuskarsa ya juyo ya Ciro ATM card dinsa ya miqawa waiter din batareda ya karba bill dinba.


Bayan andawo Masa da atm din anyi clearing bill dinsu suka fito suka Shiga mota sukabar gurin.


A mota shiru tayi tana sauraron karatun Qur'an din dayasa a motar Yana fita ahankali saitaji tana sake samun nutsuwa da yanayin da suke ciki na kasancewa da juna ahaka.


Koda suka dawo zabeera har bacci yafara daukarta cikin motar shiyasa da yayi parking sai bai tayarda itaba hakama bai kashe motarba sbd AC ya zauna ya fiddo wayarsa Yana duba saqon dayaji shigowarsa sunacin abinci.


Ahankali ta bude idanuwanta dake cikeda bacci ta zuba akansa tana lumshe ido ahankali ta furta"


Tabbas Ina cikin tsananin son MAHMOUD ZABEERA Kuma so me qarfi Wanda nakejin kamar ruhina zai rabu da gangar jikina idan nayi nesa dashi,

Lumshe ido takuma Yi tareda budesu akansa cikin sauti me taushi dazai iya jinta tace"


Nagode.


A natse ya juyo ya kalleta da nasa idanuwan dasuka nuna sunfara Jin bacci taji zuciyarta na qara narkewa da sonshi tayi saurin dawowa hayyacinta tareda tashi zaune tabude motar da sauri ta fice hartana hadawa da Dan gudu tayi ciki.


Kai tsaye bedroom dinta ta nufa ta fada Kan gadon tana sakin hawayen dataketa riqewa tace"


Amatu kidawo hankalinki Mana,

Kidawo Amatunki da kowa yasani,

Amatun Dr khalil matar Dr khalil, 

Babu kowa a zuciyarki sai Dr khalil sbd shine Wanda zuciya da ruhinki keson aure.


Ta jima ahaka kafin ta miqe tafada toilet ta wanko fuskarta tayi fitsari tazo ta kwanta tareda lullubewa tana qudurtawa ranta gobe zata amayarwa Salman abindake zuciyarta kafin ta rufe zuciyar gaba daya ta mallakawa Dr khalil dinta Wanda idan har tana Raye Inshallah batada miji sai Dr khalil.


Washe gari tunda wuri ta tashi yau da kanta ita tafara Kiran Dr 

Meeting zasu shiga Amma ganin kiranta Saida ya tsaya ya dauka yaji lafiyarta kafin yace idan yafito zaikirata.


Wankanta tayi ta shirya cikin riga da skirt na atampa kalar blue tayi Mata kyau sosai ta yafo gyalen akanta sbd Bata dauro dankwalin kayanba.


Palo ta fito ta nufi kicin da kanta yau ta dafawa kanta indomie da dafaffen kwai guda biyu sai custard data hado Wanda yaji uwar Madara takoma dakinta acan tayi breakfast dinta tana gamawa ta fitoda kayan ta maida kicin Takoma daki ta sake kwantawa tana tunanin Dr da irin dibbin soyayya da qaunar daya Bata,

Ya juyawa iyayensa baya akanta alokacinda aka koresa ya amince zaibar komai da komai ciki hadda iyayensa da 'yan uwansa da rayuwar daya taso ciki duk sbd ita

To menene Dan itama ta danne zuciyarta ta tauyeta daga Abinda takeso ta bashi koba komai Al'amarin da zuciyarta ta dauko me girma ne sbd mijin anty zarah ta haramtawa kantashi Koda sonsa zai kasheta har abada su biyun Nan anty zarah da Dr bazata taba barin susan halinda zuciyarta ta Shiga akan mutuminda sukafi qauna da komai arayuwarsu.....


Kiran Salman ne yashigo wayarta cikin nutsuwa ta daga tana qoqarin kawar da damuwarta tace"


Likitan qashi na duk Nigeria""ta qarasa tana Yar dariya.


Shima 'yar dariyar yayi Yana gyara zama cikin motarsa yace"


Zakije mukai usi airport kokuwa na tafiyata?


Wuntsilowa tayi bakin gado tana janyo dankwalinta da gyalenta ta fito tana cewa''


Ai karma kamin haka idan ban takasa a matsayin 'yar uwarsa da bamu taba rabuwaba arayuwa sai yanzu to zan takasa amatsayin matar Dr khalil tunda bayanan Dan shine yafi kowa cancantar ganin wucewar usi Dan shine yakawo wannan murmushin akan fuskarsu na samun cikar buri su samu ilimi kamar sauran 'yaya.



Ganinta kawai yayi tana bude gaban motar ta shigo ta zauna tana kashe wayar tace"


Muje ko¿


Dariya tabasa ya girgiza Kai Yana cewa' 


Amatun likita bokan turai.


Kallonsa tayi tana cewa'' 


Nidai muje tun kafin na huce da zafi zafina nafito Dan yiwa USI huduba.


Jan motar yayi suka fice suna Dan taba fira ahankali har suka Isa gida inda su kadai ake jira suzo dauki usin.,

Tunda tashigo gidan idanuwanta suka sauka Kan 'yan gidan kaf a tsaye cirko cirko tsakar gidan kowanne fuskarsa cikeda yanayin damuwar rabuwa da USI din ta juya ta kalli kawu dake zaune radionsa a kunne Amma yanayin fuskarsa yasa taji idanuwanta suna qoqarin cikowa da hawaye tana kallon iyami sai kawai ta qaraso da sauri Yana sake hawayenta ganin yanda Usin yake tsaye riqeda hannun iyami Yana Bata qwarin gwiwa.


Usman din ta kalla tana share hawayenta tasaki murmushi Dan cirewa kowa damuwa takai Masa duka a baya tana cewa"


Ki yanda kasa kowa cikin damuwar tafiyarka bayan duk hutawa zamuyi da rashin Jin ka musamman maman junior da anty salamatu ko???""tafada tana kallon maman junior da anty salamatun dake qarasowa da jakarsa data fito Masa da ita.


Murmushi maman junior tayi tana cewa''


Usi Allah yabaka sa'a kamaida hankali kayi karatu ko zaka tallafa Mana wata Rana idan lokacin cin amfanin karatun yazo sbd Kaine kasan wahala da gwagwarmayar rayuwa damukeyi anan gwamnati batamasan da ire irenmuba.


Maman junior kada ki damu daya bayan daya dukkaninmu sai usi yakaimu Hajj da umrah da albarkar wannan karatun dazaije Amma idan kuka tsaya Kuna Masa wannan fuskar ta marayu ta Yaya zaije da gwarin gwiwarsa ai kawai ki Masa tashin hankali da hayaniyar da kuka Saba shizaisa yaje Yana tuno kowa ayanda halayyarsa take....


Dariya dukkaninsu suka dauka Nan aka hau hayaniya ana Masa Allah ya kiyayaye shima sai hakan yasashi Jin Dadi ya saki fuska Yana amsa musu kowa ana Masa alqawarin Abinda za'ayi Masa idan akai kudi.


Kawu da iyami dasu akeje har airport inda suka taru su duka da hayaniyarsu suka cikawa Salman motar da hayaniya sai suke qara burgesa musamman Amatun dake qoqarin Hana kowa shiga damuwar tafiyar Usin bayan ita Yana iya hango tsananin damuwa da fargabar rabuwa da Usin a idanuwanta tana daurewa ne kawai.


Suna Isa ko zama basuyiba aka Kira jirginsu Salman ya kallesa Yana basa sauran dukkanin bayanan da Dr yace yayi Masa tareda basa takardun komai Dana atm card na account din da aka bude Masa tareda wadataccin kudi aciki ya miqa Masa tareda Dan rungumesa Yana cewa''


Zaka ringa ganina akai akai inshallah har sai kagama sanin komai da komai just take care brother,

Kuma Ina fatar zaka saka mijin 'yar uwarka alfahari dakai wata Rana.


Kallonsa yayi ya kalla Amatu Yana qirqiro murmushin qwarin gwiwa yace"


Inshallah Dr khalil saiyayi murmushi ga wannan aikin alkhairin nasa.


Gyada Masa Kai tayi tana qoqarin maida hawayen dake subuce Mata 

Suka rungume suna tana sakin hawayenta gaba daya suna zubowa ba tsayawa.

Cikin kunnenta yace"


Amatu Ina Miki fatar samun Abinda kikeso arayuwa Wanda zaisaki farin ciki,

Inaso Kuma kimin alqawarin Babu wani Abu dazai sauya matsayin Dr acikin rayuwarki kimin alqawarin da ke da kanki zaki kirani Dan sanar Dani aurenki da Dr Khalil idan lokacin yayi.


Rintse ido tayi hawayenta na sake gudu ta janye jikinta tana kallon qasa tace"


Usi zuciyata takamu da son wani Wanda ba Dr khalil ba so me girma Amma wlh shima son Dr khalil bai sauyaba a zuciya da rayuwata,

Ba laifina bane sbd bansan yaushe hakan yafaru ba,

Bansan ta Yaya zan kankare wannan son daga zuciyata ba Amma nasan ta yanda zan dannesa dannewar da har abada bazai tasoba bare wani yasan dashi zanbarshi cikin Raina har mutuwata,

Jan kuka tayi ahankali tana cigaba da cewa''


Usman ayau ni Amatu nayi maka alqawarin bazan taba auren kowaba sai Dr khalil,

Nayi alqawarin Dr bazai taba fuskantar sauyawa daga gareniba sbd shi kadai na zaba amatsayin mijina Inshallah...."wani siririn kuka taqarasa maganar dashi zuciyarta na wani irin nauyi.


Baiyi mgn ba ya juya gurinsu kawu yayi musu bankwana ya wuce Yana danne zuciyarsa dake Jin tsananin damuwa da tsoron Abinda Amatu ta fada,

Shin yayi Mata adalci satayin alqawarin auren Dr Bayan tafada Masa akwai Wanda zuciyarta ke tsananin so???


Baya tunanin baimata adalciba sbd a nasa gani da sanin Babu Wanda zata aura ya sota ya qaunaceta yabata farin ciki da kulawa fiyeda Dr khalil zabeera Dan haka koma waye zuciyarta keso farin cikinta da kulawar dazata samu daga Dr yafi matasu ahankali zata manta sonta zuciyarta ta koya son KHALIL din.



Ahanyarsu ta komawa Babu me mgn acikinsu kowa yayi shiru Yana tunani kamar basune suketa hayaniya ba a hanyar zuwa.


Su kawu tunanin rahuwarsu dasu Usin sukeyi sbd dukansu basa gabansu yanzu sai sukejin kamar rabuwa sukayi dasu gaba daya musamman iyami datakejinsu kamar itace ta haifesu gashi yanxu ta tashi Babu ko daya a gabanta.


Shikuma Dr Salman yasan irin ciwo da radadin datake ciki na zabar danne sonta tabi Abinda rayuwarta da 'yan uwanta keso.


Ajiye su kawu sukayi suka nufi gida har lokacin Babu me Magana acikinsu Saida yayi parking qofar part dinsu anty zarah sai ga MD ZABEERA yafito Yana amsa waya fuskarsa sai sheqin kwarjini takeyi ya nufi motarsa ya bude ya shige drivernsa na ciki yaja sukabar gurin idanuwanta na binsa da kallo har motar ta bace Salman na lure da ita ya saki numfashi ahankali yace"


Duk zabin dazakiyi Amatu kisani ni Salman zabeera Ina bayanki dari bisa dari saidai bazanso ki zabi Abinda zai kawo damuwa da qunci cikin rayuwarkiba,

Soyayyar MD ZABEERA Babu Abinda zata baki sai damuwa sbd bazai baki soyayya da kulawar da kike nemaba infact baimasan kinayi ba Koda yasani Babu so agabansa sbd keda idonki Kinga hakurinda matarsa keyi akansa Wanda mu bazamu iya ganinki kina irin wannan rayuwarba so please AMATULLAH for our sake kadaki saka kanki cikin quncin dazaki sakamu muma.


Share hawayenta tayi tasaki murmushi me ciwo tace"


Dr Salman zabeera daga yanxu anan munrufe maganar MD ZABEERA sbd soyayyarsa ba Abu bane Dani Amatu zansamu,

Soyayyarsa wani bangarene me girma a zuciyata da bazan iya cirewa ba saidai Kuma illace ga mutane da dama Dan haka na zabi azabtuwa da ita ni kadai acikin Raina bazan Bari ta azabtarda masoyanaba dan haka daga yanxu Babu mgnar MD ZABEERA da AMATULLAH,

Zuwa yanzu nasan kagama sanin Abinda yake faruwa kasan banida aure da Dr Khalil dan haka idan har ka daukeni kamar Yar uwa wadda kake tsananin qauna to ka nesantani duk Abinda zai cigaba da zurafaf soyayyar MD ZABEERA ka tayani nitsawa da kutsawa cikin son KHALIL ZABEERA sbd na riga na yanke shi na zabarwa kaina.



Kallonta ya tsaya Yi zaiyi Magana tayi saurin girgiza Masa Kai tana share fuskarta da tissue din motar tana murmushi tace"


Zancen ya wuce Kuma ai"" dan sake batarda zancen ta Dora da fadin" 

ni yanzuma so nakeyi kafara koyamin wannan turancin naka na turawa idan Dr yadawo so nakeyi nabasa mamaki.


Dariya yayi Yana jinjinawa gwarin gwiwarta na kawo dariya Kan fuskarta da boye abindake zuciyarta Wanda hakan na daya daga cikin Abinda yake burgesa gameda ita.


Fitowa sukayi suna fira sama sama suna dariya kamar Babu Abinda yafaru.


Anty zarah na ganinsu ta daga wayar hannunta tana cewa''


Cikinku fa daya zankira sbd Ina ganin bangantaba nasan Kaine kawai zaka fita da ita.


Ko zama beyiba suka gaisa da anty zarah din ya juya ya fice sbd mum dinsa daketa qwalo Masa Kira.




Fes ta sakewarta Takoma Amatun ta me rayuwarta cikin Raha da Jin Dadi,

Duk wani Abu ko inda tasan zata hadu da MD ZABEERA ta tosheta gaba daya data fahimci lokacin dawowarsa yayi take komawa daki takira Dr ko USI ko Salman suyita firarsu cikin nishadi.


Kulawa kuwa da qaunar da anty zarah take Mata sai ninkuwa sukeyi sbd yanzu kwata kwata ta daina cire cikon datakeyi sbd umarnin Dr khalil ne Dan shima yanzu so yakeyi daya dawo Susan dubarar Yi maganar cikin Nan yaqare su fuskanci reality itakuma anty zarah data qwallafawa cikin Rai har MD ZABEERA yiwa zancen takeyi idan tasamu fuska sai hakan yafara basa tunanin Dole daman Suma wata ran suyi sha'awar samun 'da ko 'ya.



Sannu ahankali sabo da shaquwarta da Dr Salman yayi qarfi Dan shima saitakejinsa kamar usi da baya kusa duk wani gurbi na 'dan uwa me kulawa ya cike matashi Dan dukkanin  shawararta da sirrinta dashi takeyi ta yanda shima baya boye Mata komai sai suka zama tamkar wasu best friends kokuma Yan uwan dasukafi kusanci da kowa.


A bangare daya Kuma yanzu su umme sun Dakota gaba itada Haj maryam sbd ganin dukkanin yayansu sun qare  da rawar qafa agunta sai suka sanyota gaba ba itaba ba anty zarah ba tun abin baya damunsu harya Fara damunsu zancen yajewa ummah mahaifiyar anty zarah tazo tayi musu mgn sai abin yazama fitina akayi tashin hankali tun abin na dagasu sai yayi tsanani akai kusan qaramin yaqi a familyn Wanda yasa akayi taro na musamman Amma duk da haka sai abin yaqara jawowa Amatu baqin jini sbd ganin kamar itace takawo fitina cikin familyn ZABEERA sai aka Fara camfata ga nuratu data sanyota gaba sosai tafara bincike a kanta sbd gano haqiqanin gaskia Dan bazata taba Bari Dr khalil ya auri wata banzar karuwa ba yabarta.



Zuwa yanzu satin Dr khalil uku cikin na hudu da tafiya suna saka ran dawowarsa gobe shiyasa take cikin farin cikin data kwana biyu batayiba sbd tashin hankali sbd wannan fitinar da akayi yasa Andi saka doka me tsanani akanta akan kullum taje ta gaida uwar mijinta Wanda duk taje da  bacin Rai take dawowa.



Blue fox sukaje akayo musu gyaran Kai da qafafu akaiwa Amatun Jan lalle a hannuwa 

Basu bar gurinba sai yamma sosai sukayo gida Salman ne ma ya daukosu suna yin parking motar MD ZABEERA nayin parking akusa dasu ita tafara juyowa daidai shima ya juyo idanuwansa suka sarqe cikin na juna

##mamuh#






ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[4/5, 4:22 PM] Zafafa: _*MQ 25*_



Saurin dauke idanuwanta tayi tana juyar da kanta zuwa wani gefen tana cigaba da dariyarta ta firar dasukeyi da Salman Wanda shima ya lura da yanayinda Amatun tashiga sai ya basar kamar yanda itama ta basar suka fito suna cigaba da zancensu.


Gurin MD din ya nufa ya bude Masa mota ya fito Yana gaidashi tareda fada Masa saqon Dr khalil daya basa sbd yakasa samun wayoyin MD din duka.


Itadai gaba tayi tashigewarta ko Palo Bata tsayaba sbd sanin ciki sukayo

Anty zarah ce ta tsaya tai Masa sannu da zuwa ganin Salman yasata itama wucewa sbd yanda ya amsa kamar bazai amsa ba karya kwafsa Mata gaban Salman din itama bedroom dinta ta wuce Kai tsaye sbd dukkaninsu suna buqatar wankene kawai Dan ko yunwa basa ji Dan Babu  kalar cimar dasuke buqata wadda Salman be siya musu ba Wanda kusan hakan yasa tafarajin qaiqayin ciwon Abinda rayuwarta take ciki na rashin kulawa daga kowa musamman mijinta Wanda shine yakamata ace ya jiyar da ita dadi da nushadin rayuwa amma Bata samu hakan daga kowa ba sai yanzu sanadin Wanda batamasan meye ake Kira gata da arziki ba a rayuwa gashi ta sanadinta suna nishadantuwa da rayuwarsu da Basu San komaiba sai bin umarni da oda.



Wanka tayo ta shirya cikin kayan baccinta ta sanya dogon hijab tayi sallah tana idarwa taje ta dauko yoghurts a fridge ta zuba cikin cup ta qara Masa madarar gari sosai ta juya sosai tadawo daki tana Sha tana daukarwa Dr khalil hotunan lallenta tana tura Masa saigashi yakira.


Daukar wayar tayi tana murmushi qasa qasa tace"


Kai Dr baka shanye rada ba.


Wani siririn numfashi ya sauke Wanda yasata aje spoon din hannunta  cikin kulawa tace"


Yadai???

Lafiya najika kamar kana bacci?


Murmushi me sauti yasako Mata Yana gyara kwanciyarsa da lullubinsa yace"


Lafiya kalau kawai sanyin garin Nan ne yafara tabani tun satin daya gabata  garin qasar ta daina shafamin lafiya Amma ai alhmdlh tunda gobe zamu dawo.


Ajiyar zuciya ta sauke tana cigaba da Shan yoghurts din tace"


To Meyesa zaka zauna harka Dade haka a inda baya shafa maka lfy???

Gwara da gobe zaka dawo da yau saina daga maka hankali kabaro.


Murmushin qarfin hali yayi Yana cewa''


Gobe idan nadawo me Kika ajemin?


Wani juyi tayi tareda kifewa kan carpet tace"


Saika dawo zaka gani.


Fira sukeyi ahankali sbd yanayin yanda yakejin jikin nasa sbd sanyi ya shigesa sosai Wanda yafara yiwa lafiyarsa barazana Dan yanaji ciwonsa yafara tashi ahankali.




****Miqewa Nuratu zabeera tayi daga zaunen datake a cikin restaurant din blue fox tana juya envelope din data karba tana sakin wani irin qyayataccen murmushi tace"


Manager kayimin Abinda zai juya rayuwata nasamu Abinda nakeso kaima kasamu wadda kakeso,

Wannan taimakon naka yabani farin cikin danayi shekaru bansamu ba sbd Dr khalil zabeera shine farin cikina,burina dakuma zuciyata...


Kallonta yayi tareda miqewa tsaye yace"


Ina fatar zan mallaki Amatu kamar yanda kikaimin alqawari??


Karka damu idan ka iya takunka zakayi amfani da damarka ka sameta daga lokacinda aka watsota daga rayuwar farin cikina da zabeera ma gabaki daya.


Barin gurin tayi tana sake riqe envelope din farin cikinta na qaruwa ta nufi motarta tashiga ta rufe..


Bayan ta zauna cikin motar kallon envelope din tayi tana cewa"


AMATULLAH K SALEH wannan shine asalinki tun kina Yar bolarki har zuwa yanzu,

 rayuwar alfaharinki tazo qarshe,

Kinyi kutse a tsakanin masoyanda ba'a iya rabawa sbd son danakewa khalil hankalinkima bazai daukaba bare ki iya rabamu,

Kina alfahari da kanki dakuma gatan da Kika samu daga Khalil, Modibbo da Andi ma gaba daya

Zan ruguza rayuwarki gabaki daya sai nasaka kowa ya tsaneki fiyeda yanda tunaninki zai dauka,

Ki shirya komawa rayuwar sata da dauke dauken da Kika fito bayan kinyi shari'a da familyn ZABEERA na Bata sunan da kikaso yimusu.


Cikin handbag dinta ta sakashi ta ajiye jekar gefenta tareda tayarda motar tabar gurin cikin mugun speed Dan amatse take data Isa zabeera sbd so takeyi kafin Dr khalil zabeera ya iso an dade da korar Amatun daga rayuwarsu,


Agogon motar ta kalla taga qarfe biyar  ta yamma takusa gashi guraren yamma jirginsu Khalil ake sakaran zai sauka,gudu taqarawa motarta tana kallon titi.





***Cikin riga da skirt na lace maroon tayi adonta tareda daura dankwalin lace din ta sanya Yan kunne marasa tsawo sosai kalli agogo tana zama bakin gado da wayarta a hannu tana daukar hoto tace"


Kowane lokaci yanzu Salman yace Dr zasu iya saukowa Meyesa yau nakejin wani iri cikin raina kamar inajin kunyarsa ne kokuwa wani abin daban.


Shiru tayi gabanta na 'dan faduwa taji duk batajin sukuni ta miqe tana ajiye wayarta gefen gadon ta miqe tareda fitowa zuwa Palo gurin anty zarah ko zata debe Mata yanayin da fira.



Tana fitowa anty zarah na fitowa daga nata bedroom din sanye da doguwar Turkish abaya red itama tayi kyau sosai sai qamshi takeyi kamar Amatun sai abin yabasu Daria kusan atare suka saki dariyar Zarah na cewa''



Wannan da kishiyoyi muke bansan wa mijin zai Fara kalla ba sbd kalar duk jajaye ne Kuma kalar ja idan ba mantawa nayiba tana cikin kalar da MD ke tsananin so sbd ance kalar kayan mahaifiyarsa kenan kafin ta rasu sbd sarautar da mahaifinta yataba Yi.


Kallonta Amatu tayi tanayin shiru cikin tunanin kalamanta aranta tace"


Anty zarah Allah yasa kada 'yan Amin na kusa su karba Miki zancenki sbd ita Magana ana fadarta ne da fatar 'yan Amin su amsa shiyasa ake cewa kafada alkhairi ko Kayi shiru.


Wucewa gaba anty zarah din tayi Amatu naci gaba da binta da kallo zuciyarta na sake shiga fargaba saita kuma komawa daki zata zauna kenan saiga Kiran wayar Salman da sauri ta dauka Dan dama shi zata Kira ya debe Mata kewar tunaninta..


Salman ka......


Muryan Dr khalil taji yace"


AMATULLAH.


Wani irin sanyi da farin ciki taji ya kwaranya cikin ranta batasan lokacinda tasaki wani irin qaya taccen murmushi ba tana furta" Alhamdulillah ya Allah.


Har cikin ransa yaji dadin hakan ya kashe wayar tareda miqawa Salman batareda yace komaiba suka kamo hanyar gida.



Koda suka iso gida a gurin ummensa ya sauka Dan itama a matse take da ganin Dan nata musamman sbd kwanakin wata sabuwar qauna da kewar danta ke kamata shiyasa itama a matse take da taga abinta Nan aka hau hidimarsa kayan abinci da snacks kala kala anyi Masa taredasu fruits dasu fura duk dai wasu kayan marmarin kewar gida anyi Masa Nan yaci abinci tareda ita da Haj maryam da salman da Nuratu wadda koda ta iso gida kusan ataredasu Khalil din ta shigo Dan motarsu na gaba kafin Tata 

Ganinsa yasa takasa riqe farin cikinta da zumudinta tama manta da Abinda tadawo dashi Nan ta zauna cikinsu anacin abincin tana faman kula da duk motsinsa da Abinda yake so iyayensu kuwa sai washe baki sukeyi sbd dama shine burinsu hada Khalil din da Nuratu.


Bai bar gurin umme ba sai magriba ya wuce gurin Modibbo acan sukai sallah taredashi da salman da MD ma Wanda ya shigo ana magribar.


Bayan sungama sallah anan suka zauna tareda Modibbo Yana tambayar MD Amatu sbd duk yau da jiya Bata Zo ta gaidashiba kamar yanda ta Saba shiru MD din yayi Yana Dan sauke Kai yace"


Inshallah duk suna lfy sbd Nima na kwana biyu bana zama gobe ma insha Allah Nima zanyi tafiya zuwa Germany.


Allah ya taimaka ya tsare yabada sa'a Kuma.


Amin dukkaninsu sukace suna qoqarin miqewa cikin sautinsa me saka nutsuwa yace"


Khalilu matarka Ina saka ran a lissafi saura wata uku haihuwarta ko???


Tsit sukayi dukkaninsu su ukun 

Take zufa tafara Dan tsatsafowa Khalil din MD kuwa fararen idanuwansa ya zuba Masa Yana jiran jin amsar da Khalil din zai bada sbd shidai wadda ake maganar cikin akanta tana zaune gidansa Amma baitaba ganin ciki a jikinta ba gashi ana maganar saura wata uku haihuwa.


Dan gyara murya Khalil yayi cikin girmamawa yace''


Inshallah haka ake saka Rai saidai cikin yazo da tangarda ne sbd rashin girmansa ya bayyana cikin baida lfy inasaka ran ma gobe zanje da ita asibiti musake dubawa.



Cikin watanni da dama baa fada baida lfy ba sai yanxu?


Sarqewa Dr khalil din yayi Yana Dan gyara murya yace"


Ayi mini afuwa Modibbo nayi kuskuren rashin sanarwar.


Shikenan ba damuwa kuje Allah ya Bata lfy.


Amin"Khalil din yace suka miqe suka fito tare suna tafiya zuwa hanyar sashensu dayake direction guda.


Tafiya sukeyi su biyu Banda salman daya wuce ya nufi motarsa yafita zabeera ahankali kowannensu shiru Babu me mgn dama sun Saba haka suke koyaushe idan suna tare saisun jima shiru kafin su Fara mgn Wanda MD ne me wannan halayyar shikuma Dr khalil Yana girmama kowane irin Hali da MD ya zabawa kansa da rayuwarsa.


Tsayawa yayi ahankali batareda ya juyo ya kalli khalil dinba yace"


Bansan wane mataki ka dauki wannan alamarin ba Amma ya kamata kasan kana saka kanka cikin hadari along with her.. 'dan shiru yayi kafin ya juyo ya kalli khalil din cikin wani irin yanayi yace"


Atleast kayi tunanin Hali da Abinda zata fuskanta kafin kasata a irin wannan tight spot din sbd yanxu ku duka Kuna situation dinda only God can help so kafin komai ya fita hannunka kasan Abinda kakeyi ka dawo daidai,the truth doesn't cost anything but a lie could cost you everything.


Kallonsa Khalil yayi tareda sauke ajiyar zuciya cikin damuwa yace"


Bansaniba ko kasan Abinda nake qoqarin boyewa Amma bazaka iya fahimtar dalilina nayin hakan ba sbd komai yazone alokacinda banyi tsammaninsaba Babu mafita bayan wadda na dauka a wancan lokacin da yanzu ma..


Denying the truth doesn't change the fact cewa ka dauki hanya Mara bullewa,

Ka zauna kayi tunani zaka samu wata mafitar wannan batayi ba.


Yana Gama fadar haka ya wuce gaba batareda ya juyoba yayi hanyar sashensa.


Shiru Dr khalil zabeera yayi yana tunanin maganganun MAHMOUD din wainda suka sakashi zurfin tunanin sbd tabbas qaryarsu takusa qarewa wadda idan bai nemo mfitaba asiri ya tonu to daga Ummensa har Amatu dashima suna cikin matsalarne,

Babban burinsa daya dawo dashi shine maganar auren Amatun tukuna sbd duk wasu kayayakin aure na akwati ya siyosu yazo dasu saitin akwatinsa cif ya hado kayan aurensa Wanda ko gidan bai kawosu ba daga airport gidansu kawu suka Fara ajiyesu kafin su qaraso gida.



Ajiyar zuciya ya sauke kafin shima yabi Bayan MD din zuwa ganin Amatu da tun Yana gurin umme take kiransa yaqi dauka sbd kada farin cikin ummen ya gushe.

##Mamuh#



Kuyi hkr kuyi manage da wannan 

 hutun weekend naje dakuma mura dake damuna🤦🤦🙏🙏[


No comments

Powered by Blogger.