Makauniyar Kaddara 58

 


Page 58*


...........Gabanta ya tako a hankali, ya tsaya tamkar zai shige mata jiki. Baice komaiba sai kama hijjab ɗin jikin nata yay ya zare. Ganin yanda ta duƙar da kai ya sashi saka yatsunsa biyu ya ɗago haɓarta. Ba karamin firgita tai ba da ganin yanda ƙwayoyin idanunsa suka canja launi tamkar wani bugagge. Muryarsa a shaƙe matuƙa tamkar mai mura yace,

“Turaren nan naki zai kashe ni kairunnisaa”.

       Sosai jikin Zinneerah ya hau rawa saboda kusanto da fuskarsa da yay gab da tata, ya ɗaura hannayensa duka a kafaɗarta ya fara tafiya dasu a hankali zuwa gaban gadon, gwiwar ƙafarsa ɗaya ya ɗaura a bakin gadon, hakan da yay ya daidaita tsahonsu. Ya cusa fuskarsa akan dokin wuyanta yana wani jan numfashi a fisge dan neman ƙwace masa yake.

       Yanda ƙamshin turaren ke neman zauta masa ƙwaƙwalwa baima san bakinsa ya suɓuce wajen fallasa asirin zuciyarsaba yace, “Ina ƙaunarki da komanki Neerat”. 

    Yay maganar da in ina jikinsa na wani ɗan tsumar da shi kaɗai yake jinsa a jininsa. Dan ita Zinneerah ma ruɗewar datai da salon nasa batasan ta fashe masa da kuka ba. Babu alamar ya jita, dan luuuu yayi dasu suka faɗa saman gadon. Babu shiri ta kanƙamesa jikinta na ɗaukar rawa jin harshensa akan kunnenta.

      “Na shiga uku Yayanmu Please ”.

Ta faɗa cikin muryar kuka tana ƙoƙarin ture fuskarsa dan neman sakata yin fitsari yake. 

    Al'amarinne yazo mata a bazata, gashi farko, gashi da mutum mai matukar girma da daraja a idonta, gashi ta sha gyara na musamman da ita kanta ko yaya akai mata wani salo sai jininta ya motsa.

       “Shiiiiii!!!” 

Ya faɗa a cikin kunnen nata yana zagaya yatsansa saman bakinta. Tsit tai shiru tana haɗiyar zuciya. A nutse ya ɗago fuskarsa yana kallon tata cikin ɗan hasken fitilar ɗakin green.

      Kasancewar idanunta a lumshe suke batasan kallonta yakeba, murmushi yayi mai sanyi ganin yanda take rawar jiki da ƙanƙame hannayenta a ƙirji. Kwanciyarsa ya gayara da kife fuskarsa akan tata, ya sumbaci haɓarta da matsar da lips dinsa kan nata da yatsansa ke kai har yanzun. A bazata taji saukar tausasan lips ɗin nasa akan natan. Sosai ta zabura da neman jan fuskarta sai dai babu damar hakan, dan ya tsare ko ina da ina babu wata damar kuɓuta yau sai alƙawarin ALLAH ya cika da izinin mai hukunci da rahama akan bayinsa masu haƙuri da juriyar karɓar ƙaddara da hannaye bibbiyu batare da raki ko ƙosawa ba.


         Duk da ya haɗa bayanai masu yawa akanta lokacin da yazo babbar gaɓar mallakarta da iyakar jarumtarsa yaje, sai dai samun hanyarsa ɓam ta sakashi jin wani irin zazzafan tausayinta da ƙaunarta mai tarin yawa da tsanani na shigar gaɓɓansa. Ba tare da tuna son binta a matakin tausayawaba ya ji saukar ƙarar kukanta cikin kunnensa, dan a gigice ta ƙwala kiran hajiya iya da Maman Sadiq tana ƙanƙamesa jikinta na wani irin mahaukacin rawa data sakashi ƙanƙameta shima ya manne bakinsa da nata...........


         Da ƙyar take fitar da numfashi hawaye masu matuƙar zafi da tausayin kanta na sakko mata. Bata taɓa sanin Yayansu mugu bane sai yau, ita kanta batasan adadin kuka da roƙon datai masaba, zata iya rantsewa har suma tayi na wucin gadi ta farfaɗo amma bai shirya barintaba sai da yakai inda yake buƙatar zuwa. Hannunsa dake damƙe da nata ya ɗan matsa da mirginowa ya rungumeta gaba ɗayanta a cikin jikinsa yana bata wasu irin hort kissis da ita kanta tasan na tsantsar ƙauna ne a gareta.

      “Thanks you, thanks you, thanks you” kawai yake jera mata hawayen tausayinta na taruwar masa a idanunsa. Dan duk da kasancewarsa mutum mai tsananin jarumta da kakan daɗe bakaga kuka daga idaniyarsaba yau yaji tausayi mai tsanani akan Zinneerah, saboda abubuwa masu yawan gaske dake zuwa masa arai game da haihuwa da rainon cikin Little da tayi. Sunanta ya ɓaci ta yanda ba lallai kowa ya yarda da ita ɗari bisa ɗariba koda yayi ƙoƙarin fallasama duniya gaskiyarta. Tayi kuka, tayi wahala, tayi ciwo, ta rabu da garinta, ta rabu da mahaifinta, ta rabu da ƴan uwanta, ta rabu da farin cikinta duk a dalilin cikin ɗansa da batasan mafarinsaba. Dolene ya godema ALLAH daya ƙaddara yarinyarnan kasancewa matarsa ba wani daban can ta auraba. Yayi alƙawarin zai jiyar da ita daɗin duniya gwargwadon ƙwazonsa har sai ta san itaɗin ta musamman ce a garesa kuma mutum mai daraja. Dolene ya sanarma duniya wacece ita? Dolene ya wanketa ga mutane koda bazasu yardaba ya tabbatar musu da *_MAKAUNIYAR ƘADDARAR_* data jefa rayuwarta cikin hajijiyar rayuwa badan ta shiryama zuwanta ko karɓartaba itama. “I'm so sorry Neerat”.

     Ya sake faɗa a cikin kunnenta hawayenta na sauka har bisa fuskarsa suna gaurayuwa da nasa na tsananin tausayin da yake mata dajin zafin zalunci mafi muni da akaima rayuwarta.

        Cikin kuka tace, “Yayanmu ruwa. Ruwa zansha”.

     A hankali ya ɗago kansa yana kallon fuskarta data kacame da hawaye, idanun sunyi luhu-luhu yana kallonta. Goshinta ya sumbata a hankali yace, “Ruwa kike so?”.

     Kanta ta ɗan juya masa a hankali itama tana matso wasu sabbin hawayen. Hannu yasa ya share mata su. “Tom ya isa haka kinji, banason kukannan zai saki ciwon kai. ALLAH yay miki albarka uhmyim”.

        Kanta ta maida gefe tana ƙoƙarin haɗiye kukan amma ta kasa. Raba jikinsa yay da nata da ƙyar ya jawo rigarsa ya saka, sakkowa yay daga gadon ya fita ɗakko mata ruwa dan yau ko shigowa dashi baiyiba ya manta. 

      A yanda ya barta haka ya sameta. Zama yay ya jingina da gadon sannan ya ɗagota jikinsa, ta saki karamar ƙarar azabar da wajen ke mata. Ruwan ya saka mata a baki yana ambaton, “Sorry sha ruwan muje ki shiga ruwan zafi”.

      Sosai tasha ruwan wata sabuwar zufa na keto mata. Ta lafe a jikinsa tana lumshe idanu da sauke numfarfashin wahala. Idan zata iya tunawa bayan rainon cikin little da naƙudarsa data sha kafin ai mata cs bata taɓa jin abu mai azaba makamancin wanda taji yau a hannun Yah Abdul-Mutallab ba. Ta jigatu matuƙa irin jigatuwar da mantata gareta abune mai wahalar gaske. Tana tausayin mace a rayuwarta, da ace mata zasu nutsu su ajiye duk wani shirme da ruɗanin huɗubar sheɗan da tabbas wasu abubuwa ƙalilian dake zama wajib a rayuwarsu kawai sun isa zama sanadin kaisu aljannah. Yanzu da irin wannan daren kawai aka barka ai ba ƙaramin abin tashin hankali bane, balle akwai rainon ciki, uwa uba naƙuda da babu abinda za'a iya misaltata da shi. Ga fitar rai, Raino, hidimar gidan aure da ƙalubalensa.

        (Kai jama'a mata masu duniya, mata sarakan duniya, mata na gaisheku, na gaisheku gaisuwa irin ta girma da mutuntawa dan kun cancanci a yaba muku, ku ƙara haƙuri jaruman duniya, ku cigaba da haƙuri taurarin duniya, kuzama masu haƙuri ALLAH zai sakanka muku da aljannarsa😍😘).


        Ruwa AK ya shiga da kansa ya haɗa mata a toilet, sannan ya fito da kansa ya taimaka mata ta sauka a gadon hawaye na rige-rigen sauka mata, ganin tafiyar tasu babu sauri yasashi ɗaukarta kawai. Ajiyar zuciya ta sauke mai haɗe da kuka, dan hakan da yay mata ba ƙaramin taimakonta yayi ba.

         Koda suka shiga ba kai tsaye ya tsundumata a ruwanba, cikin dabara da lallashi yay mata. Zinneerah nada dauriya sosai, koshi ya shaida hakan dan ta nuna masa jarumta yau duk da taci kuka, amma tun ihun farko datai lokacin isarsa gareta bata ƙara buɗe baki domin yin kwakwazo ba, sai dai hawayene kam da suna ƙarewa yau da sun ƙare gareta. A yanzunma hawayenne kawai sai ƙanƙamesa da tayi amma ko uhum batace ba.

        Hakan ya masa daɗi, dan ya tsani kwakwazo a rayuwarsa da hayaniya, yafison komai a silent kuma da nutsuwa, wannan yana ɗaya daga cikin hallayarta data fara jan hankalinsa gareta batare da ita ta sani ba. Kanta dake kwance a ƙirjinsa ya rinƙa shafawa yana hura mata iskar bakinsa cikin kunne. Hakan ya matuƙar shagaltar da ita har ruwan ya ratsata yanda ya kamata ya ƙara mata wani kuma. Sai da ya tabbatar taji daɗin duka jikintama ba wajen kawai ba sannan yace mata tayi wankan.

         Duk da tanajin nauyinsa ga zazzaɓi dake neman rufeta haka tabi umarninsa tayi, dan tsaye yay a kanta da alama yana son tabbatar da ingancin abinda zatayin. Yaji daɗin ganin yanda tayi komai dai-dai, sai kawai ya ɗauka mata bathrobe ya saka mata. Zai ƙara ɗaukarta cikin dasashshiyar muryarta tace,

     “Zan iya”

   Baice komaiba ya matsa ya bata hanya, cikin dauriya ta fice a toilet ɗin, saida ta fita gaba ɗaya ta cije bakinta da jingina jikin bango tana maida numfashi, tayi hutun kusan minti ɗaya sannan ta ƙarasa kaiwa gadon dake a hargitse. A ranta tace, ‘Dole ka hargitse gado dan nima an hargitsani’.

       (😂🤣wayaga mai cikuykuya an zinni😆😝).

       Ƙarasawa tai ta fara ƙoƙarin ganin ta gyara don buƙatarta kawai takai kwance. A dai-dai nan boss ya fito yana tsane jikinsa. Ƙarasowa yay inda take yana murmushi tausayinta fal ransa. Batare da sanin fitowar tasa ba taji an rungumeta ta baya da amshe bedsheet ɗin hannunta. “Uhm-uhm waya saki wannan aikin?”.

     Sosai tsigar jikinta ta tashi saboda yanda yay maganar a cikin kunnenta. Bai damu da amsawarta ba ya ɗauketa ya dire a saman sofa. Shi kuma ya juya gaban gadon ya kimtsa musu shi, gabanta ya dawo ya durƙusa, tai saurin yin ƙasa da kanta saboda matsananciyar kunyarsa dake neman halakata, gashi yanzu babu riga a jikinsa sai towel daya ɗan yafa a wuyansa ƙarami bayan wanda yake ɗaure da shi. Lallausan murmushi ya saki yana lumshe idanu da sake buɗewa akanta lokacin da yake warware towel ɗin data naɗo gashinta dan ya tsane. Towel ɗin ya warware yana ƙara tsane mata gashin da ƙyau gudun kamuwa da mura.

     “Duk zafinsa naƙuda tafisa ko?”. Ya faɗa yana zame towel ɗin daga cikin kanta.

       Rashin fahimtar tanbayar tata ya sata ɗago kumburarrun idanunta ta kallesa. Ya sakar mata lallausan murmushi da ɗan jinjina kansa. Kanta ta maida ƙasa kawai gabanta na ɗan faɗuwa da tunanin koya san itace ta haifa little ne?.

         Hannunsa ya ziro ta ƙugunta, ɗayan ya ɗago haɓarta sosai suna kallon juna. Duk yanda taso janye idanunta da suka shige cikin nasa hakan ya gagara, dan shu'umin kallon da yake mata tamkar yana zuba mata wasu sinadaraine masu matuƙar daraja da tsada, ta ɗan fara mar-mar da idanunta dake cikowa da ƙwalla. 

     Kansa ya girgiza mata alamar kartayi, kafin ya saki fuskar tata da matsota jikinsa ya rungumeta a haka suna sauke ajiyar zuciya a tare. “Aure jarabawane kuma ibadace, haƙuri a cikinsa nasarace kuma daraja ce. Riƙe mutunci da kame kai martaba ce, mutuntawace ga iyaye da tarbiyyarsu. Dan duk namijin daya sami mace a yanda yay hasashe ba ita kaɗaice ke samun kima a garesaba har iyayenta ma mutunci da kima suke ƙarawa. Kinsha wahalhalun rayuwa amma hakan baisaki yin gaggawa ba wajen ƴanta kanki har sai da ALLAH ya iyakance miki. Daga yau ke sarauniyace a fadar Abdul-Mutallab, ki ɗauka kin mallakesa shi da komansa. Kin bashi ƙyauta mafi daraja guda biyu da bazai manta da itaba. Kin haifamin Abdul-Mutallab, kin daɗamin da tukiycin budurci. ALLAH yayi miki albarka. ya yalwata rayuwarki da tarin farin ciki, ya share hawayenki ya yaye damuwarki, ya ɗaga darajarki ya cigaba da kare mutuncinki fiye da yanda kika kare nawa”.

        Sosai tsoro ya kama Zinneerah jin ya ambaci haihuwar little, sai dai daɗaɗan kalamansa da batasan zai iya kwantar da kai wajen furtasu ga mace ba suna ratsata. Ya ɗago fuskarta yana kallonta. Lumshe nata idanun tayi saboda nauyinsa da kwarninsa.

        Ɗan murmusawa yay da miƙewa tsaye, ya kamo hannunta suka nufi gaban mirror batare datasan mi zaiyiba. Dan barci takeji sosai tanada tabbacin kuma asuba ta gabato, ga zazzaɓi jikinta zau, tasan kuma yanajin zafin. Baice mata komaiba ya zaunar da ita a kujerar mirror ɗin, kanta a ƙasa harya jona handryer dake ajiye, gashinta ya fara busar mata sannu a hankali, sannan ya tufƙe matashi da ƙyau yanda bazai takura mataba. Rigarsa ya juya ya ɗakko cikin Wadrobe yazo ya fesheta da turare sannan ya saka mata bayan ya zame bathrobe ɗin tanata noƙe-noƙe dan kunya. Rigan ya kai mata har cinya dan haka ta saki ajiyar zuciya. Sake kamata yay ya kai bakin gado ya zaunar, ya buɗe drawer gefen gadon ya ciro magani dan yaji zazzaɓi a jikinta. Bata yay, babu musu tasha saboda bukatarsa da takeyi. Tana sha yana shafa kanta harta shanye ta miƙa masa ruwan.

     “Good girl.”

Ya faɗa yana kamata ya kwantar, tare da ja mata bargo ya lulluɓa mata iya rabi sannan ya sumbaci goshinta da cewa “Good night”.

      Kanta kawai taɗan jinjina masa tana lumshe idanu. Wahala tasa barcin ɗaukarta cikin ƙanƙanin lokaci, sai saukar numfashinta ya rinƙaji a hankali. Lip ɗinsa ya cije yana firzar da wani irin huci mai ɗaci dan tabbas bazai bar duk mai hannu a al'amarin nanba. Matakin farko zai fara ajiye hujja ga iyayensu a safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu, zai kuma saka bincike na kwanaki biyu zuwa uku domin tabbatarwa da kama masu hannu a ciki dumu-dumu.

    Duk da shima barcin yakeji bai kwantaba, alwala yayo da saka jallabiya ya fara nafilfili dan asuba ta gabato ma, yasan idan ya kwanta zasu makarane kawai. Zinneerah kam tasha tarin addu'oi harma da iyayenta, yana a wajen har akai sallar asuba dan bai fita massallaci ba yau bayajin ƙarfin jikinsa sam.

     Badan yaso ba ya tada ita da ƙyar domin yin salla. Aiko yasha langaɓe dan sai faman lumshe idanu take, sai da ya taimaka mata zuwa toilet ɗinma tayo alwala sannan. Tanako idar da salar yau babu zancen azkar ta ɓingire a wajen. Ɗagata yay cak ya maida a gadon ya kwantar shima yabi sahunta dan kansa ya fara masa ciwo saboda barci. Cikin so da ƙauna ya rungume matarsa cikin jikinsa suka lula duniyar barci.


       *_12:5pm_*


    Sai ƙarfe sha biyu da mintuna biyar AK ya farka saboda kiran wayarsa da akayi, ƙaramin tsaki yaja dan barcin sam bai ishesaba. Da ƙyar ya lalubo wayar ya buɗe ido yana kallon mai kiran. Ganin Granny ya sashi gyara kwanciya sannan yakai kunne. 

        “Assalamu alaiki, Granny barka da asuba”.

      “Ai dama barka da dare kacemin, kujimin iya shege da ranar ALLAH kake kiramin barka da asuba. Kai ko moddibo kana lafiya yau kuwa kai da inno? An aiko muku da abinci kusan mutum uku suna zuwa amma an ƙwanƙwasa ƙofa ko motsinku babu”.

       “Oh God! Granny sai kin mana kwakwazo duniya tasan bamu tashi ba? To barci mukeyi”.

      “Eh lallai ai nafaji barci kukeyi ja'iri, sai ka tashi ka buɗe ƙofa ka amsa ka koma ku cigaba da barcin”.

     Murmushi ya saki da ajiye wayar yana faɗin, ‘Hajiyar matsala’. Daga haka ya ɗan leƙa fuskar Zinneerah dake barcinta hankali kwance sannan ya zare jikinsa a hankali ya sauka a gadon. Jallabiya ya ɗauka ya ɗaura saman boxer ɗinsa ya fito.

       Haneef ya samu zaune a saman motar da yazo, yana ganinsa ya duro ya nufosa ɗauke da basket. “Yayanmu barka da hantsi?”. Ya faɗa cike da girmamawa.

       Amsa masa yay da kulawa yana tambayarsa jama'ar gidan. 

    “Kowa lafiya yake yayanmu”.

“Alhmdllh, yanzu daga nan ina zaka?”.

      “Ba ko'ina zan koma gidane”.

“Okay to kabar zuwa gidan, gidan Abba zan aikeka kaje ka ɗakko min Gwaggo Maryama, sai ka biya ta gidan dasu Mammah suka sauka ka ɗakkomin Mahma. Kafin kaje duk zan kirasu”.

         Kai Haneef ya jinjina ransa fal wasiwasin lafiya kuwa?. Rashin mai basa amsa ya sashi miƙa masa basket ɗin kawai ya juya domin cika umarninsa..

     Shima ciki ya koma kai tsaye sashensa. a dining ɗin falon nasa ya ajiye basket ɗin ya koma ciki. Wayarsa ya ɗauka yay zaman kiran Hajiya iya, sun ɗanyi magana ya maida kiran ga Mahma kuma sannan ya kira Abba na gidan mmn sadiq...............✍




*_Aunty Farah kina can wagaga da baki za'a mallake mana AK😖😖😬😬😒😒😏😏😏😾😾🙄🙄😑._*


No comments

Powered by Blogger.