Jiddatul Khair 26

 


Har karfe daya da wani abu na dare Jiddah bata yi bacci ba, abu bai ta6a tsaya mata rai irin abubuwan da Abuturrab ya gaya mata ba, gashi har sannan ko digon hawaye bata yi ba, amma abun ya ki barin xuciyarta, da yake a kasan darduma ta kwanta kuma bai bi ta kanta ba yyi kwanciyarsa saman gado, ta mike xaune a hankali ta daura kanta bisa gwiwanta, sai a sannan hawaye ya shiga sauka idonta, gaba daya taji da ma ta hakura da aurenta da Iliya, taji ta gwammace gwara ta koma gidansu komin abinda xae faru, taji gwara ta gudu kawai, daga kai tayi hawaye na sauka idonta ta kallesa, duk da wutan dakin a kashe yake, tana ganinsa kwance saman gado. Da safe bayan ya gama shirinsa haka ya fita ba tare da yace mata komai ba, tun bayan da ta gaishesa bata ma san ko ya amsa ba har ya fita bata kalli inda yake ba ita ma, sae dai bata ga ya dau jakar laptop dinsa ba. Bayan fitarsa da minti kusan talatin ta mike ta dau Hijab dinta ta saka ta bude kofar dakin ta fita, a reception din hotel din ta gansa xaune da shayi a kan table din gabansa idonsa a kan screen din wayarsa, sosai gabanta ya fadi tayi still a inda take, dago kai yyi suka hada ido, tana ganin haka ta nufi kofar fita da sauri, da ido ya fara bin ta da mamaki, lkci daya kuma ya mike ya bi bayanta, fita tayi compound din hotel din, ya fara kalle kalle sbda baya son attention, luckily babu mutane haraban hotel din, hakan ya kara masa kwarin gwiwan bin ta ya fixgota ta fashe masa da kuka tace "Ni ka kyaleni in yi wucewata, wllh baxan xauna a nan ba wajen Baabarmu xan koma" Bai saurareta ba ya ciro makullin motarsa a aljihu ya ja ta xuwa parking space da motarsa yake ya bude back seat, turata ciki yyi ya kulle motar, sannan ya jingina jikin motar ya rungume hannunsa yana imagining... assuming baya xaune downstairs tafiyar xata yi da gaske, Jiddah ta dinga rusa kuka cikin motar, ya fi minti 7 a tsaye kafin ya bude motar ya shiga ya kulle, can gefe ta koma tana shessheka taki kallonsa, yana kallonta fuskarsa a daure yace "Ina xa ki tafi kika ce?" Cikin rawar murya tace "Gidanmu mana" Yace "Auren xa ki je a maki da mashayin saurayin naki?" Tace "Ehh" da mamaki yake kallonta, tace "Ni kawai ka mayar da ni, na yarda xan auresa din" Dauke kansa yayi bai ce komai ba, bayan few seconds ya kalleta yace "Toh ba kaduna muke ba yanxu, nan kano ne, ki jira idan mun koma kaduna sai in mayar da ke gidan naku da kaina ba sai kin tafi ke kadai ba, kin ji?" idonta ta fara gogewa tace "Yaushe xa mu koma kadunan?" Yace "Aiki nake yi a nan, sai ranan alhamis" Wani hawayen ya taru idonta, yana kallonta yace "Kin ji abinda nace?" Hawayen ya xubo mata tace "Har sai alhamis kuma?" Yace "Jibi ne alhamis din ai" Ta sunkuyar da kanta tana goge hawayenta, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawa babu, a hankali tace "Toh" Bai kuma cewa komai ba, ya juya ya bude motar ya sauka yana dubanta yace "Sauko" Ba musu ta sauko daga motar tana wani kumbure kumbure, yana kallonta yace "Wani man kike shafawa?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Wanda ka siya min mana" Bai ce komai ba, bayan few seconds yace "Toh kar ki kara shafawa" ta kallesa yace "Mu tafi ciki" Ba musu ta fara tafiya ya bi bayanta, ba komai ya sa ya tambayeta ba sai ganin yanda ta kara haske, which he don't like, ko kadan baya son idan mace ta doso waje ayi noticing dinta, haske kuma na daya daga abinda yake sa ayi noticing mace a waje, ita kam Allah ya hore mata wannan, juyawa tayi ta kallesa suka hada ido ta ci gaba da tafiya yana biye da ita, har suka shiga reception din sannan taji yace "Tafi ki shirya ina jiranki, minti ashirin na baki" Bata ce komai ba ta wuce sama ya bi ta da kallon gefen ido, kallon agogon wrist dinsa dake nuna karfe takwas da rabi yayi, he will be piloting around 10:30, shi kuma bai son xama daki tare da ita shi ya sa ya sakko ya xauna reception din. Karfe tara dai dai Jiddah ta sakko, tun da ya kalleta sau daya ya dauke kansa... Abaya ce baki a jikinta, i need not to say yanda kayan ya haskata, sai karamin jaka da takalmin kafarta same color, ta iso table din da yake xaune, lkci daya kamshin turaren da ta saka ya baxa wajen, ya fi minti biyu bai ce komai ba, can dai ya kalleta yace "Baki xo da Hijab bane?" Ta girgixa masa kai kawai, Bai kuma ce mata komai ba, ta xauna d'an nesa da shi, sai a snn yace "Me xaki ci?" Tayi shiru bata ce komai ba, chips and egg ya sa aka kawo mata sai shayi, ya sa ta tafi sama tayi breakfast din, ta mike ta wuce, ya bi ta da kallo, lkci lkci yake duba agogon hannunsa dake nuna after 9, tashi yyi ya wuce sama, ya tarar ta gama, jakarsa ya dauka yace "Kina bata min lkci Malama" Tashi tayi ta bi sa suka fita ya kulle dakin, tana biye da shi har suka iso gun motarsa, ya ajiye jakar a back seat ya shiga maxaunin driver ya tada motar, xagawa tayi a hankali ta bude front seat din ta shiga ta xauna, warming din motar yayi suka fita haraban hotel din ya dau hanyar Airport. Abuturrab ya samu discount wajen yankar mata ticket din Business class, wanda hakan yasa take cikin boarding group na farko, duk wanda ya ga jiddah a lkcn xai xata ba farkon boarding din plane dinta bane, she is so calm, but deep inside her she is so so Afraid, bata ta6a tunanin haka jirgi yake da girma ba, snn bata ta6a mafarkin xata ga jirgi ido da ido ba balle har ta shiga wataran, kuma tunda ta shiga jirgin ta xauna idonta ke kasa, sai ka lura da ita sosai xaka gane a tsorace take, daya daga flight crew member ce ta nufota tana murmushi da ladabi tace "Ina kwana Hajiya..." Jiddah ta daga kai ta kalleta a hankali tace "Ina kwana" Cabin crew din na murmushi ta xauna kujeran gefenta tana kallonta ta buda mata ido sannan ta shiga fastening Seat belt dinta, wanda da alama Abuturrab ne ya sa ta gwada mata yanda zata saka seat belt din, Jiddah dai kallonta kawai take har ta gama sakawa, Flight crew din tace "Toh saka naki haka" Ba musu jiddah tayi yanda taga tayi, matar tayi murmushi ta yi unfasten din nata ta mike tace "Toh ki cire, sai jirgi xai tashi xa ki saka, Allah ya sauke mu lafiya" Jiddah ta cire, matar ta kuma sakar mata murmushi ta juya ta wuce, jiddah ta bi ta da kallo don kayan jikinta yayi mata kyau sosai ba kadan ba, ba su fi ashirin a Business class din ba, kowa kuma harkan gabansa yake, tunda wani mutumi ya xauna gefenta ta xama so uncomfortable, ga kamshinsa da ya cika wajen, shi dai bai kalleta ba sai operating din wayarsa da yake yi attentively, bayan minti ashirin duk passengers din sauran class din suka gama boarding plane din, Nan aka fara announcing ayi fastening Seat belt, ganin kowa na saka nasa ita ma ta fara kokarin saka nata, amma sai ta kasa sakawa sai fama da belt din take, sai a sannan mutumin dake gefenta ya kalleta ta gefen ido, ganin ta rasa yanda xata saka, ya kai hannunsa ya saka mata, bata iya ta kallesa ba kuma bata ce komai ba, a haka jirgin ya fara tafiya, dukar da kanta da yaga tayi na kusan minti 5 yasa ya sake kallonta yace "Are you okay?" Da sauri ta dago, dai dai nan  jirgin ya daga, ta rufe bakinta hankalinta a tashe tace "Amai nake ji wllh" da mamaki yake kallonta yace "Amai?? Ohk hold it for a while" Ita dai hannunta na bakinta tana gyada masa kai, he gets she might be prone to motion sickness... ya jira har sai da jirgin ya tafi can sararin samaniya suka kai cruising altitude, duk da seat belt sign that is still on... hakan bai hana shi cire nasa seat belt din ba sannan ya cire mata nata, And he led her to the lavatory, wata cabin crew ta nufosu tana kallonsa tace "Is she alright?" Yace "Sure she will be" yana tsaye har jiddah ta fito daga lavatory din tana sauke numfashi, banda jiri babu abinda take gani, ga kanta dake juya mata, yace "How are you feeling now?" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yace "Toh mu je" Tafiya ta fara yi ya bi bayanta, har xuwa wajen seat din nasu, ta xauna sannan shi ma ya xauna, kamar ya lura she is so uncomfortable from d clouds she is seeing via the porthole that she is sitting beside, rufe wajen yyi yana kallonta, hakan da yayi ya taimaketa sosai kuwa, bayan some minutes da take off dinsu aka kawo masu snacks with drinks, kallonta yayi suka hada ido, bayan an ajiye masu ya dau nasa ya fara ci, ganin bata ci komai ba har ya gama cin abinda xai ci ya kalleta yace "Ain't you eating?" Tayi shiru bata ce komai ba, bai kuma yi mata magana ba, har ta fara bacci, seeing how uncomfortable she is sleeping yasa ya bata access to his shoulder, a haka kuma ta dinga bacci har aka fadi nan da mintuna nawa xa su shiga lagos, shi ya saka mata seat belt din nata bayan an bada umarnin yin hakan, dalilin da yasa ta tashi daga baccin da take kenan, jiddah bata san lkcn da ta rikesa ba ta rufe fuskarta a jikinsa da xa su yi landing, Cikin kuka take gaya masa amai take ji, ya dago kanta yace "Hold it for a while..." ya bude porthole din da ya rufe yana nuna mata, juyawa tayi ganinsu a kasa jirgin na gudu ta ji hankalinta ya d'an kwanta, amma har lkcn xuciyarta bai daina bugawa ba, shi dai kallonta kawai yake, can ta kallesa, d'an murmushi yyi yace "Ya sunanki?" Ta sauke idonta tace "Jiddah" yace "Jiddah!!" Ta gyada masa kai, yace "Wannan ne farkon hawanki jirgi Jiddah?" Ta gyada masa kai, bai san lokacin da yyi murmushi ba yace "I see, to mun kawo lafiya, hope ur next flight won't be as 

frightening as this?" Ita dai bata ce komai ba, 

yace "Ke kadai kika xo lagos?" Ta girgixa masa kai tace "Aa ni da yayana" yace "Wow, yana ina?" Ta buda masa hannu alamar bata sani ba, yace "Ba tare ku ka

 shigo jirgin ba?" Tace "Toh ni ban sake ganinsa ba" yana waige waigen business class din yace "Ohk, sunana Yousuf.... Yousuf Umar" yana fadin haka ya ciro wayarsa yace "Sa min digit dinki so i can say hi some other time Jiddah" Tayi shiru tana kallon wayar tasa me kyau kirar samsung, can tace "Ni ae bani da waya" da mamaki yace "Baki da waya?" Ta gyada masa kai yace "Ban yrda ba" tace "Wllh, wanda yayana ya bani yana gida" ganin how she is speaking innocently yasa ya yrda, ya ciro Complimentary card dinsa ya mika mata yace "Toh ki min alkawarin xa ki kirani ga number na nan" ta dinga kallon katin dake dauke da number sa kafin tace "Alkawari fa kace" yace "Eh Jiddah" jan fingers dinta ta fara yi bata ce komai ba ya bude jakarta ya sa mata katin dai dai nan kuma jirgin ya tsaya cak, yace "Hakan na nufin kin dau alkawarin" Ta xaro ido tace "Kamar yaya" yace "A yarenmu yanda kika yi da fingers dinki yana nufin kin dau alkawarin" Ta xaro ido tana kallonsa, ya sakar mata murmushi, Cabin crew din da ta gwada mata yanda xata saka seat belt dinta daxu ce ta iso inda take tana murmushi tace "Captain Aliyu yace in taho da ke Hajiya" Jiddah ta kalli Yousuf Cabin crew din ta basu waje ta koma can ta tsaya tana jiran Jiddah, Yousuf yace "yayanki ne yayi tukin jirgin kenan?" Da mamaki take kallonsa tace "Tukin jirgi fa kace? Aa baxai iya ba" yana murmushi yace "Toh tashi ki je... ina jiran kiranki" shi ya rigata mikewa ya dau briefcase dinsa ya fara tafiya ta bi sa da ido snn ta mike ta nufi cabin crew din da tayi mata jagora har Cockpit inda Abuturrab yake xaune tare da Co-pilot dinsa wani black American suna secure Cockpit checklist, da mamaki Abuturrab ke kallon Crew din don ce mata yayi tayi leading dinta outside d plane, hannu black American din da ya kafe jiddah da ido ya mika mata yana murmushi yace "Hello...." Kallon Abuturrab Jiddah tayi, lkci daya taga ya mata wani shegen kallo, amma calmly yace "Juya ki tafi ki jirani ina xuwa..." Juyawa tayi da sauri ta bar wajen, Yana ma American din murmushi yace "We don't do that captain, and she doesn't even understand English" Pilot din na kallonsa yace "Ohh, is she ur sister?" Abuturrab yace "My friend's wife...." Jiddah na sauka jirgin ta dinga kalle kalle ganin jiragai da yawa, mamaki ta dinga yi wai yau ita ce ta hau jirgi, Crew din daxu ce ta sakko suka bar wajen tare, sai bayan kusan minti ashirin Abuturrab suka sauko daga jirgin da Co-pilot dinsa. Kallonsa Jiddah ta dinga yi ganin ya kuma canxa kaya, daxu da fararen kaya ta gansa kamar uniform da hula a cikin jirgi, yana isa inda take ba tare da ya kalleta ba ya wuceta, ta bi sa da kallo, juyawa yyi ganin bata taso ba yace "Ko in daga ki ne?" Mikewa tayi a hankali ta bi bayansa, hotel din da ya ke sauka a lagos not too far from Murtala Muhammad Airport ya nufa tare da ita cikin taxi, Tana biye da shi bayan sun sauka taxi din sun shiga hotel din, bin sa take kamar xata shige jikinsa ganin mata 

kusan tsirara suna yawo 

hankali kwance, garin kallon wata da ta gani da wando iya cinya ta kusa fadawa kansa, ya juyo yana kallonta, kamar xata yi kuka tace "Ina ne nan ka kawo ni?" Ci gaba yyi da tafiyarsa ta bi bayansa, har ya amshi makullin daki a reception tana makale da, shi dai bai sake ce mata komai 

ba suka shiga dakin da ya amsa, bayan ya kulle kofar kamar xata yi kuka tace "Su basa jin kunya ne?" Juyawa yayi ya kalleta pretending not to know what she is talking about yace "Su wa?" Ta sunkuyar da kanta, yace "Tambayarki nake su wa?" Still ta ki cewa komai, ya ajiye wayoyinsa yace "Ke me ya aike ki kallonsu?" Bai jira cewarta ba ya fita dakin ta bi sa da kallo, a hankali ta karasa ta xauna gefen gado tana bin katon dakin da kallo, ya ma fi wanda suke ciki a kano kyau sosai, Ba a dau lkci ba ya dawo dakin, fried rice with chicken, jollof rice with beef and plantain, sai pepper soup da ruwa with drinks.... abubuwan da ya bude kenan tsakar dakin ya xauna kan carpet yana nannade hannun shirt din jikinsa, ita dai kallonsa kawai take, sai da ya fara cin fried rice din sannan ya daga kai ya kalleta yace "Idan xa ki ci ki sakko" A hankali ta girgixa masa kai, ya hade rai yace "Sakko...." Bata sake cewa komai ba ta mike ta dawo ta xauna daya side din carpet din, abincinsa kawai yake ci, ganin haka ta dau spoon dake nannade cikin tissue ta saka cikin jollof rice din ta fara ci, ya gama cin abinda xai ci ya mike ya shiga bandaki ya wanke bakinsa sannan ya fito ya kwanta, ta d'an saci kallonsa ta dau sauran naman kazan da ya rage ta daura kan abincinta, hada ido suka yi lkci daya ta daburce ya mike xaune yace "Maida shi, ai nace baxa ki sake cin kaza ba" Da sauri ta mayar da kaxan kan abincin da ya rage, ya koma ya kwanta, bayan ta gama cin abincin ta gyara wajen ta hade takeaways din cikin leda, ruwan da drink ta ajiye su gefe daya, sannan ta mike tana kallonsa taga idonsa a rufe, can gefen gadon ta tafi ta xauna a kasa. Karfe biyu saura Abuturrab ya koma Airport tare da Jiddah, don he will be piloting to Abuja, hankalinta ya tashi ganin jirgi xa su kara shiga tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Don Allah mu hau mota, wllh bana son jirgin nan" Lkci daya hawaye ya kawo idonta, yace "Baki so saboda me?" Tana goge idonta tace "Amai nake yi, kuma ina ganin jiri, don Allah kar mu shiga tsoro nake ji" Yace "Daxu kin yi amai kenan?" Ta gyada masa kai yace "A ina kika yi aman?" Tace "Wani mutumi ne da ya xauna kusa da ni ya kai ni bandaki" Abuturrab ya juya da sauri yana kallonta yace "Ya kai ki bandaki??" Ta gyada masa kai, maimaitawa ya sake yi, ta kuma gyada masa kai, yace "Sai aka yi yaya?" Tace "Ya jirani nayi aman sannan muka dawo, da jirgin xai sauko kasa ma shine ya kamani wllh tsoro nake ji" Sake baki yayi yana kallonta yace "Ya kamaki a ina?" Tayi shiru bata ce komai ba, ya rungume hannunsa yace "Ya mutumin yake???" Tace "Yana jin hausa, kuma dogo ne kaman ka, sannan yace min sunansa Yousuf" Ya xare glass din idonsa yana kallonta, can yace "Ohk har hira ku ka yi kenan" Tace "Aa bamu yi hira ba" Bai kuma ce mata komai ba ya ci gaba da tafiya ta bi bayansa gabanta na faduwa, ticket din da Abuturrab ya yankar mata sai da ya tabbatar the person next to her is a female, exactly abinda tayi daxu daga kano xuwa Lagos shi tayi daga Lagos xuwa Abuja, Bayan jirgin ya sauka Abuja ta fita tana kare ma jirgin kallo tana fatan babu abinda xai kaddara mata sake shiga jirgi, har suka isa gidan Abuturrab wajajen la'asar jikinta a sanyaye yake, duk yana lura da ita bai ce komai ba, xaunawa tayi kan kujeran parlon tana bin parlon da kallo, yana kallonta yace "Yanxun ma kinyi aman a jirgi kenan?" Ta gyada masa kai kamar xata yi kuka, hararanta yyi ya wuce bedroom dinsa don yin alwala ya wuce masallaci dake layin, Har ya dawo tana nan yanda ya barta yace "Bakya sallah ne?" Mikewa tayi tace "Ban san inda xanyi alwala ba" Ya nuna mata dakin dake parlon, ta nufi dakin, ya bi ta da kallo sannan ya wuce dakinsa. Bayan ta idar ta fito parlor ta xauna tana sake kare ma parlon kallo, a haka bacci ya dauketa bayan ta jinginar da kanta jikin kujeran da take xaune, wajen karfe biyar da rabi aka kwankwasa kofar parlon, hakan ne ya farkar da ita, jin an kara kwankwasawa ta mike ta nufi kofar ta murda key din ta bude kofar, komawa baya tayi tana kallon warce ke tsaye bakin kofar kamar yanda take kallonta ita ma, dai dai nan Abuturrab ya shigo parlon, Jiddah ta juya tana Kallonsa....


No comments

Powered by Blogger.