Gidan Aro 28


28*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

A cikin Mota suka had’u da Sabeera, saidai cikin dukansu biyun babu wanda ya fahimci suna cikin motar har saida Sady Ta fad’i

destination d’inta. Sabeera ta waigo suna duban juna, sai kuma ta kauda kanta ba tareda tace komai ba. A haka har suka iso unguwar tasu babu mai cewa k’ala.. 


Da shike waje guda suka sauk’a Sadiya Ta dubi mai motar tace “Malam dan Allah kai hak’uri lungun can kawai zan shiga na amso maka kud’inka.. Akasi aka samu ban fito da Jaka ba.”


Mutumin ya dubeta ya girgiza kai yace “Hajiya Kinsan ba’a haka.. Ki biya kud’in ki kawai ki tafi..”


Zata kuma magana Sabeera ta ciro kud’i ta bawa mai taxi d’in tace “Malam namu ne mu biyu, ‘Yaruwata ce tare muka saba tafiya dama..” Daga haka Sa kai tai zata shige. Sadiya ta dubeta murmushi saman fuskarta “Na gode..”


Sabeeran batace mata komai ba sanda suka soma takowa daga nan bakin babban kwalta yanda aka ajesu.


Sadiya ce ta soma fad’in “Ina fata wata rana ki sami gurbi a zuciyarki ki yafe mun Sabeera.. Nasan Kinsan maganan bashin Hajiya Tabawa dake kanmu wanda Baba yace zai biya mana amma saidai idan zan amince da aurensa.”


Katseta Sabeera tai da fad’in “Basai kin maimaita ba na sani tinda har ya kiraki da Baby a gabana.”


Sauk’e ajiyan zuciya Sadiya tai kafin taci gaba da fad’in “Ba auren jin dad’i nai ba Sabeera. Dan ni ko a labarai ban tab’a karo da labarin irin aurena ba.. Auren Mission nai.. Sannan a GIDAN ARO nake zaune gidanda sam ba nawa bane kuma ko wane lokaci za’a iya sallamata.. Mr Inspector ya aureni ne ba wai dan yana k’aunata ba Sabeera.. Da zaran ya ida mission d’insa zai sallameni daga rayuwarsa Wanda zanfi kowa Farin ciki da hakan..”


Sai sannan Sabeera ta d’an dubeta da mamaki..


Sadiya ta murmusa Wanda yafi kuka ciwo taci gaba da fad’in “Sabeera amfani dani kawai yake domin ya cimma burinsa ya samu wani clue da zai had’asa da abokan ark’allan Sagir.. Yau da zai samu abinda yake nema zai rabu dani.. Amma idan bai samu ba haka zai Ta wahalar da rayuwata.. Kinji irin jarabawar da Sadiya ta sake samun kanta ciki..!” Ta k’arashe gajeriyar hawaye na gangarowa daga idanunta.


Sabeeran ma hawaye ne ya gangaro mata amma Sai batace komai ba.


Sadiya Ta k’ak’aro murmushi ta sakar mata daidai sanda suka iso layin gidansu Sabeeran dan dama sai an fara samun gidansu Sabeera dake sarari kafin a isa nasu Sadiya dake can k’asa.


“Ki gaida Mama Sabeera.” Ta fad’i murya can k’asa.


Juyowa Sabeeran tai ta dubeta kad’an kafin ta jinjina kai. Ba tareda tace komai ba ta shige hanyar gidansu.


A hankali Sadiya Ta lumshe idanunta tana ji can k’asar zuciyarta bazata tab’a bari abinda ya faru ya lalata zumuncinsu da k’awancensu itada Sabeera ba.. Tare suka taso tin suna yara bata da wata k’awa bayan Sabeera.. Tasan Sabeera na k’aunarta deep inside, kawai dai zuciya ce da batada k’ashi amma da yardar Allah zasu koma kaman da. Da wannan tinanin ta nufi layin gidansu.. Zuciyarta fari k’al zataga Umma dasu Ashir da Habeeb. Saidai murmushin nata ne ya tsaya Cak sanda Ta hango Mr Inspector tareda abokan aikinsa ga mutane sunyi cincirindo a k’wanan lungunsu da alama bayanai suke d’auka.


Zuciyarta yai wani irin tsinkewa dan dama tinda ta fito daga makarantar gabanta ke tsananta fad’uwa kaman dai wani mugun abu zai faru da ita.. Saurin girgiza kai Ta soma kafin ta nufi lungun nasu cikin sauri..


Kaman ance ya d’ago kai nan ya hangota ta nufo lungun.. 


“Oh no..! What’s she doing here..?” ya furta yana k’ok’arin nufota..


Bai tsaya saurarenta ba ya shiga janyota yana fad’in “Mai ya fito dake..? Didn’t I tell to wait for me there.. What exactly is wrong with you.. Baki jin magana koh.. What if something happens to you..!” Cikin fad’a fad’a yake maganar.


Girgiza kai take tana duban lungun nasu “I need to see my Mom and my brothers.. Bazaka hanani ba wannan karon Mr Inspector.!” 


Ya shafi goshinsa kad’an yana k’ok’arin rik’ota. Fuzgewa tai ta nufi lungun nasu a guje tana ambaton Ummanta.. 


“Damn it.! She can’t find out about this.!” Ya fad’i yana mai bin bayanta cikin sauri shima, lokaci guda yana kiran sunanta yana fad’in “Idan kika shiga gidan nan sabon mission zamu fara daga farko..! Just stay right there.!” 


Ko sauraronsa batai ba ta tura k’ofar gidan ta shige a guje tana kiran Umma.. Su Assad tsaiwa kawai sukai suna duban Sadiya da Mu’azzam d’in wanda yabi bayanta cikin sauri.


“Umma gani nan na dawo. Ina kuke..? Ashir.. Habeeb.. Umma wai kuna ina..?” Tana maganar tana bud’e k’ofofin gidan Mu’azzam na biye da ita yana k’ok’arin dakatar da ita..


Cak ta tsaya sanda ta kula ga dukkan alamu babu kowa cikin gidan.. Babu Umma sannan babu Ashir da Habeeb.


Cikin rarrabewar murya tana Ganin gidan na juya mata take fad’in “Umm..Umma.. Umm.. Habeeb.. Ashir... Ina kuke.. Umma wasan b’oyo kuke mun.. Dan Allah ku fito gani nan na dawo gareku.. Babu abinda zai sake rabamu.. Umma dan Allah ki amsa mun.. Kinji na rok’eki..”


Kasa jura Mu’azzam yai ya shafi goshinsa a hankali kafin ya shiga janyo hannunta yana fad’in “Let’s go, we are going home now..!” Ya fad’i a tsare kaman yanda ya saba.


Bama tasan mai ke faruwa ba.. Bata gane mai take ciki ba, batama lura da Mu’azzam dake janyota ba har saida suka fito waje.. Sannan ne ta soma tuna wai babu kowa cikin gidansu. Babu mahaifiyarta sannan babu k’annenta guda biyu... D’agowa tai tana duban Mu’azzam wanda zata iya cewa yau d’in Ta hango tsananin damuwa cikin tsimammen fuskar nan tasa..


Wani irin fincika tai daga rik’on da yai mata, ta soma jada baya ta nufi gidansu tana fad’in “No.. I’m not going anywhere with you.. Ina Mahaifiyata da ‘Yanuwana..? Tell me.. Ina suke..?!” Ta k’arashe cikin tsananin tashin hankali jikinta na wani irin rawa..


Mu’azzam ya shafi kansa a hankali kafin ya k’araso ya kuma kamota “Shige muje nace..!”


Fincika tai tana huci take dubansa “Nace maka bazanje ba..! Ina Umma ta Ina Habeeb ina Asheer.. Ina suke.. Ka fada’a mun Ina suke.. Just tell me.. Tell me now ina suke..?” 


“I don’t know..!! Ki wuce mu tafi nace miki.. Let me remind you, you still owe me.. You are still on your mission.. You must finish your assignment and help me catch Sagir’s accomplices.. Kin fahimta.!” Yai maganar cikin daka tsawa.


Shaye da tsananin mamaki take dubansa, bataga mahaifiyarta da ‘yanuwanta ba but he stills talk about his stupid mission.


Girgiza kai take wasu irin hawaye masu k’una na zubo mata cikin rashin yarda “My Mother and my two little brothers are gone missing.. Yet you still have the audacity to talk about your so called mission..!” Taci gaba da girgiza kai hawaye na zubo mata “You are so Selfish..You are so mean Mr Inspector..!” Daga haka gidan ta kuma komawa a guje tana kirawo Umma da ‘yanuwanta.


A guje shima ya bita ya fincikota “You will not find them here..Bazaki samesu a nan ba.. Just let the police do their Job..!” Cikin tsananin k’unan rai yake maganar.


Wannan karon da rinannun idanunta take dubansa “Damn the police..!” Ta fad’i tana dukan k’irjinsa.. Lokaci guda taci gaba da kai masa duka a k’irji da duka hannayenta biyu tana ci gaba da fad’in “This is all your fault..! Dik laifinka ne.. Laifinka ne na rasa kowa nawa..! Na tsaneka..! Na tsaneka.. I hate you l..! I hate you..!!” 


Dikda zafin kalamanta da yake ji hakan bai hanasa kame duka hannayenta biyu da take dukansa dasu ba, lokaci guda ya rungumota ya kwantar da ita saman k’irjinsa, ya matseta sosai yanda zai iya hanata bige bige. Lokaci guda yake furta “I’ll find them..! I promise you I’ll find them..!” Yana jinjina kai still tana cikin k’irjinsa crying her heart out yake ci gaba da fad’in “Zan samo Su ko Ina suke..!” Ya k’arashe yana d’aura hab’arsa kad’an saman kanta.


Kuka take kaman ranta zai fice ba tareda tana iya fahimtar komai ba.. A haka ya rik’ota suka nufo waje yanda su Assad ke tsaye suna jiransu.


Mu’azzam ya dubi su Assad da jikkunansu gaba d’aya yai sanyi yace “Take care of things here.. I’ll take her home..”


Assad ya jinjina kai yace “Sure Inspector..”


Bata sake sanin meke wakana ba, bata sake sanin meke faruwa ba.. Farkawa tai kurum ta ganta a d’aki a kwance.. Ta mik’e cikin sauri tana jin kanta na wane irin sara mata.. Dikda rawar d’ari da jikinta keyi hakan bai hanata k’ok’arin fitowa daga d’akin ba ta nufo k’asa. Saidai tana fitowa ta hangesa a kitchen, yana sanye cikin armless shirt ruwan shud’i da bak’i irin kakin da police ke sakawa sai bak’in 3quater.. Ya bada baya da alama aiki yake kitchen d’in..


Cikin sand’a ta soma takawa a hankali da zummar guduwa.. Saidai tana tab’a k’ofar Parlorn ta jita a kulle.. Ta kuma ja da k’arfi taji bata bud’e ba.. Nan Ta shiga dage k’arfinta tana jan k’ofar kaman zata b’alla.


“Let me out please..! Dan Allah ka k’yaleni na tafi.. I need to find my Mom and my brothers.. Dan Allah ka k’yaleni.. Na rok’eka..!” Ta k’arashe sabon kuka na kufce mata tana mai juyowa.


Ido hud’u sukai dashi yana tsaye bayanta rik’e da plate noodles ne cikin plate d’in.


“Kinaso ki tafi..?” Ya tambaya yana dubanta.


Cikin sauri ta shiga jinjina masa kai tana hawaye.


Ya jinjina kai a hankali kafin yace “Come here.” Yai maganar yana mik’a mata d’aya hannun nasa.


Ta girgiza masa kai alamun a’a tana mai ci gaba da hawaye.


Ya fuzar da huci kad’an kafin yace “Idan kinaso na barki ki tafi zakiyi duk abinda nace.. Kinji koh..”


Ta d’ago tana dubansa, sai taji wani kukan na zuwa mata gadan gadan.. Cikin muryar kuka take furta “Umma.. Ashir.. Habeeb.. They need me.. I need to find them.. Dan Allah ka barni na tafi yanzu..!” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka.


K’arasowa kusanta yai kafin ya kamota yace “I know.. But idan na barki kika fita haka bazaki iya komai ba.. You’ll collapse. You need to gain your strength idan kinaso ki samu energy d’in nemansu.. Come with me now..” Ya k’arashe yana janyota cikin jikinsa. Lokaci guda taji wane irin rauni gauraye da tausayin kanta cikin zuciyarta. Rik’eta yai b’angaren jikinsa guda yayinda d’aya hannun nasa ke rik’eda plate na noodle d’in.

A haka suka nufi upstairs tana binsa kaman rak’umi da akala. 


Suna shigowa d’aki ya zaunarta bakin gado kafin ya aje plate d’in gefen bedside.


Kamo hannunta ya kuma suka nufi bathroom. Ya k’arasa wash bowl ya d’auki toothbrush d’inta ya wanke ya zuba mata toothpaste akai.. Lokaci guda ya soma k’ok’arin wanke mata bakin.


Saidai bata bari yakai ga hakan ba ta tsaresa da fad’in “I can do it myself.!”


Fuzar da huci yai yana mai kauda Kai gefe “Fine, do it then.” Ya fad’i a d’an hasale shima yana damk’a mata brush d’in cikin hannunta. 


Ta aika masa mugun kallo kafin tace “I need some privacy.!”


Ba tareda ya dubeta ba ya fuzar da huci kad’an yana mai ficewa daga ciki bathroom d’in.


Yana fita ta wanke bakinta kafin ta soma lek’e lek’e ta ina zata iya gudu saidai babu wani hanya da zata iya tserewa.


Silalewa tai nan cikin bathroom d’in tana hawaye tana tina Ummanta da ‘yanuwanta.


Ganin ta jima bata fito ba yasa Mu’azzam matsowa bakin k’ofan bathroom d’in ya kasa kunnuwansa yana tinanin ko tayi collapsing cikin bathroom d’in ne.. Ya d’an saka yatsarsa guda ya k’wank’wasa “Kina lafiya..? Or should I come in..?” 


Cikin sauri ta shiga share hawayenta tana fad’in “I’m almost done..” Ta mik’e tana d’auraye fuskarta da ruwa. Tsaki take cikin zuciyarta tana mamakin Wai duk jimawan nan da tai bai fice ba ashe, yana cikin d’akin yana jiranta.


Tana fitowa ta gansa tsaye gefen k’ofar bathroom d’in ya d’an jinginu jikin garu had’ida d’ingile k’afarsa guda alamun fitowarta yake jira. 

Kallo guda tai masa ta d’auke kai. Shid’inma gajeren tsaki yai yace “Ke Zo ki zauna..” Ya fad’i yana mai k’arasawa had’ida d’aukan plate d’in noodle d’in.. Yai mata alama da ido kan ta k’araso ta zauna saman gadon.


Ba don taso ba ta k’araso ta zauna nan yanda yace ta zauna d’in.


“Eat up now..” Ya fad’i yana d’ebo abincin cikin fork ya mik’o mata saitin bakinta.


Mak’e masa kafad’a tai alamun “A’a.. Ka kaini wajen ahalina na rok’eka.. Suna buk’atata..!” Ta fad’i cikin tsananin rawar murya.


“Zan kaiki amma sai kin cinye abincin nan.. You haven’t eaten anything since morning.. Kinga time kuwa yanzu..?” Ya k’arashe yana nuna mata smart watch d’in dake d’aure hannunsa na hagu.


Kauda kanta gefe tai tana jin wani kukan gauraye da tashin hankali na zuwa mata.


Mu’azzam yai gyaran murya yace “Police are doing all they can to locate them.. Na miki alk’awari zamu samesu.. Nasan baki yarda dani ba.. But please I want you to trust me on this..” Ya k’arashe yana tsareta da idanunsa.


Bazatace ta yarda dashi ba amma ta samu kanta tana mai sadda idanunta k’asa ba tareda taci gaba da duban cikin fuskarsa ba.


Ya kuma mik’o mata abincin lokaci guda yake furta “I cook for the very first time in my entire life. I hope you won’t disappoint me.. Zakici abincin nan koda babu dad’i.. Open your mouth now..” 


Ta d’ago ta d’an dubesa yana mata alama da kansa irin yanda ake ma yara idan basu da lafiya ana so suci abinci.. Gaba d’aya ita gani take ma being nice doesn’t suit him at all gwara ma yaci gaba da zama tyrant d’insa.. Bata iya kauda kan nata ba wannan karon dan Ta kula bazai k’yaleta ba har sai taci d’in.. A hankali ta bud’e bakinta ya saka mata abincin ciki.


Saida tai spoon uku a na bud’u ta kauda kanta gefe alamun ta k’oshi.


“Last spoon.!” Ya fad’i yana tsimewa wannan karon.


Fuzar da huci tai kafin Ta furta a hankali “I’m ok..”


“No you are not.” Ya katse da fad’in haka, kafin yaci gaba da fad’in “Idan baki ci wannan na k’arshen ba bazan kaiki ba..”


Jin abinda yace ya sanyata bud’e baki a hankali ya saka mata.


Lokaci guda taga ya ciro magani pcm ya d’auki bottle water d’in dake gefe ya mik’a mata yace tasha.

Zata masa gardama taga ya tsareta da wad’ann idanun nasa. 


Ta kauda kanta gefe tana amsan ruwan da maganin.. Saida ya tabbata tasha kafin ya mik’e zai fice.. Tai saurin bin bayansa tana fad’in “Nayi duk abinda kace.. Yanzu sai ka barni na tafi please..!”


Tsareta yai da idanu yana dubanta, kafin ya murmusa kad’an yace “And what makes you think zan barki ki tafi..? 

Ya d’an jnjina kai yana dubanta lokaci guda ya had’e rai yaci gaba da furta “Bayan juran duka tsaurin idonki na ‘Yan tasha da kika saba. Mu’azzam Gamji cooks for the very first time in his life.. He feeds a low life like you  with his hand.. Bayan mahaifiyarsa bai tab’a ciyar da wata mace da hannayensa ba.. Kina tunanin mission mai sauk’i kikeyi da zai jure ya miki Duka wad’ann abubuwan..?”


Ya jinjina kai kafin yaci gaba da fad’in “Nayi duka wad’ann ne don na tabbata kin tsaya cikin k’oshin lafiya har dai na ida mission d’ina... Idan kina mafarkin zan barki ki tafi ba tareda nayi accomplishing mission d’ina ba you’re so mistaken.. You are staying right here until the mission is finally accomplished..!” Yana ida fad’in haka ya fice ya janyo k’ofar.


Girgiza kai take tana furta “No please.. Dan Allah kayi hak’uri..!”


Ta k’araso a guje tana tura k’ofar amma ta kasa.. Kuka Ta soma tana rok’onsa ya bud’e mata Ta fice amma a banza.. Ta nufo balcony a guje tana k’ok’arin tura k’ofar amma saidai shima a rufe ta jisa..

Cikin sanyin jiki ta dawo da baya Ta zube nan saman gadon tana kuka mai tab’a zuciya.. Tinawa da tai ko sallar azahar da la’asar da tuni an soma kiraye kiraye batai ba ya sanyata Saurin mik’ewa ta nufi bathroom d’in da zummar d’auro alwala tana hawaye.

Nan tazo ta tada sallah ta soma kai kukanta ga Sarkin da Babu kamansa.


**


Kasancewar isowar yamma lis sukai yasa Aunty Shema basu nufi gidan Safeenar da niyyan gyare gyare da kakkab’e k’ura ba. Dan dama tace da zaran Sun iso a yau d’in zasu d’iba ma’aikata aje a share gidan a gyara tas. Mommy ma tace su bari kawai gobe idan Allah yakai rai da safe sai suje su gyara gidan idan yaso zuwa yamma sai akai Safeenah. Hakan kaw akai basu je gidan a ranan ba saima bada hankali da ‘yan gyare gyare da ake ma Safeenar wanda Aunty Shema’u tai tsayin daka tana fad’in sai Safeenah ta rikita angonta. Safeenah kaw jin hakan sosai yai mata dad’i.. Mommy ma taji dad’in hakan sanin irin abubuwan da d’iyarta tai kafin aure idan mijinta ya tunk’areta a haka sunada babban matsala. (Su Mommy kenan, sun mance ba’ayi ma Allah wayo.. Maganin bari dai shine kar a fara.. Allah ka tsaremu daga fad’awa aikin danasani.. Ameen)


Safeenah Amarya Dikda ciwon dake k’afarta dan da crutches ma take tafiyar hakan bai hanata zumud’in shirye shiryen tafiya gidan mijin nata ba. Meema Ta dubeta tace “Waini Addah Feenah ina Ya Mu’azzam ne.. Tinda muka dawo ko ganin k’yallin motarsa banyi ba balle nayi tunanin ganinsa cikin gidan nan..? Toh kodai baisan kin dawo bane.?”


Safeenah ta murmusa tana kuma kurb’an tsimin da Aunty Shemau Ta tilasta mata shanyesa tas a daren tace “I want to surprise him.. Kema Kinsan yanayin aikinsa k’ila sai dare ki gansa ya dawo.. I’ll wait for him in his room saidai kawai ya shigo ya ganni.” Ta wani k’arashe tana girgiza k’afarta mai lafiyar.


Meema Ta tab’e baki kad’an tace “Toh amma idan kika taresa a d’akinsa ya b’ata miki shirin da akai na tafiya gidanki fah.. Ko so kike komai ya faru a nan gidan tin ba’aje gidan naki ba..?”


Harara Ta aikawa Meema kafin tace “Na sake miki da yawa Meema.. Yaushe har muka fara irin wannan tad’in dake..?”


Meema tace “Ahap na yaushe kuma Adda Feenah.. Ai bakida aminiyar da ta wuceni dan haka dole nasan komai..” Ta k’arashe tana kashe mata ido guda.


Suka tintsire da dariya a tare Safeenah na fad’in “Of course my sister is my sidekick.. Zanyi missing shishiginki da gulmarki Meema.. Daga gobe I won’t be living here anymore..! Come here give your sister a hug..” Ta k’arashe tana turo baki gaba kaman zatai kuka.


Cikin sauri Meema ma ta k’arasa ta rungumeta tana fad’in “I’ll miss you too Addah Feenah.. And this your Savage Husband  shi zai ke hanani zuwa gidanki.”


Safeenah ta dara kad’an tace “And I love him just like that.”


“I know..!” Meema tace tana d’an tab’e baki.


Lokaci guda Ta k’arada “And I hope he doesn’t surprise you instead..!”


Daidai lokacin glass cup d’in dake hannun Safeenah ya fad’I k’asa ya tarwatse tsimin dake ciki ya zube. Jin abinda Meema ke fad’i mata.


Meema ta zaro ido waje tana kame baki “Oh no.! This is a sign Addah Feenah... It’s a bad omen..! Something terrible is going to happen..!” Tai maganar tana kuma firfito da idanu waje cikin k’ok’arin razana Safeenar.


Jifa mata pillow Safeenah tai tana fad’in “Shame on you Meema.. Fice min a d’aki I need positive vibes..” Ta k’arashe tana k’ok’arin kwad’a mata Sandar crutches d’in nata..


Meema ta fice tana dariya lokaci guda take furta “I’ll miss you Addah Feenah.. I love you..”


Daga nan yanda Feenah ke zaune take fad’i da k’arfi itama “And I hate you little sis.. Ki turo wata cikin maids d’in nan Ta gyara nan..”

**


Har safiya Safeenah bataga Mu’azzam a gidan ba.. Mamaki ya cikata, nan Ta yanke shawarin tambayar Mommy dan ko jiya da daren Ta kirasa yafi abinda yafi amma bai d’aga ba.. Ta fara tinanin ko wani abu ne ya faru dashi sanin irin had’arin dake tattareda aikinsa.


Saidai tana k’ok’arin shiga d’akin Mommy Ta soma sinkayo tattaunawar Mommyn da Aunty Shemau.


Cak Safeenah Ta tsaya tana jin Wai tinda Mu’azzam ya dawo bai kwana a gidan.. Idan ba sharholiyarsa yake waje ba mai zaike hanasa kwanan gida matarsa bata gari.. Sau d’aya ma suka had’u da Mommyn.


Zuciyarta ne yai wani irin yankewa amma sai ta bawa kanta k’warin gwiwa da cewa aikinsa aikin Al’umma ne zai iya kasancewa a ko Ina any moment. Mijinta bazai tab’a cutar da ita ba.. Mata basu gabansa, sannan shima baida lokacinsu.. Bazata saka ma zuciyarta wannan damuwar ba musamman yanzu da ta samu Mu’azzam yake nuna damuwarsa akanta.


Da wannan tinanin ta juyo ba tareda ta shige d’akin Mommy ba. Saidai gaba d’aya jikinta a mace ne.. B’angare mafi girma cikin zuciyarta yafi karkata ga zancen da taji Mommy nayi.. Take taji zuciyarta na son amincewa Mu’azzam ha’intarta yake. Da gaske sharholiyarsa yake a nan.. Toh amma tambayar da su waye yake sharholiyar tasa..? Take taji zuciyarta na bata amsa da matan banza mana.. Ji tai kaman sandar taimak ma tafiyar nata ya gaza d’auakrta.


Tana tafe kaman mutum mutumi K’annenta Meema da Kiki dake haurowa saman suka hangota, Kiki sanye da sch uniform d’inta da safiyace da alama makaranta zata.. Meema kuma sanye da tracksuit da alama morning exercise ta fito. 


Sukai carko carko suna dubanta.


Meema tai saurin zare earpiece d’in dake mak’ale kunnenta Ta k’araso Ta dafata tana fad’in “Addah Feenah lafiya..?”


No comments

Powered by Blogger.