Fyade 4

   


  *Page 4*

           Shafi na hudu 


Littafin na kuɗi ne kaman yanda kuka sani a next page Free page zai ƙare sauran na kuɗi ne maza hanzarta kiyi payment don a cigaba da tafiyar dake , The journey is so far 😻 ga yanda Tsarin yake... Regular group ₦500

Vip group ₦1000

Special ₦1500 

Via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 idan VTU transfer ne sai ki tura ta Wannan MTN number 0906146609

*DON ALLAH WANNAN LITTAFIN KAR UNDER  🔞 TA KARANTA PLEASE*

_____________________


Ban yarda Wani ko wata su ɗaura mun littafin nan a ko wani irin website nasu ba tare da izini na , haka masu ɗaurawa a YouTube channel don Allah bana buƙata ,idan kuma kayi hakan duk abun da ya biyo baya kayi kuka da kan ka 🚫 Ga masu buƙatar Audio na littafan mamanteddy zaku iya searching YouTube channel nata#MAMANTEDDY YOUTUBE CHANNEL https://youtu.be/BF6fZ7iNMzg a can zaku samu duk Wasu littafan mamanteddy na sauraro mun gode . Kar ku manta Wurin yi mana Like da subscribe . 



Kama Ƙugu Mama Lantana tayi cikin mamaki take bin iyayen Lauratu da Kallo ,kana tace " Sannu Laminde Wato akan faɗan yara ne kika yo lulluɓi na baki Farida ki daka ? Tun da Ita Lauratu nada gata , ita kuma A'isha Farida bata dashi . To baki isa ba kin yi kaɗan Wallahi . Naga Ɗan tsiyan da zai taɓa A'isha ina Cikin gidan nan . Au tare mata kika yi kenan , kalli yanda ta kumbura mawa Lauratu Goshi? Wallahi ba zan ƙyale ba . Sai dai idan A'isha bata fito ba . Yanda take taƙama da Ƙarfin ƙashi ta mauje mun yarinya wallahi itama sai na Haɗata da Dai dai ita . To ina nan ina jira Laminde Ki haɗo duk wanda zaki haɗo inanan ni  a inda kika sanni .. Gida ne ya cigaba da Hargitsewa da Hayaniya kaman za'a ɓaɓɓake unguwar Tuni mutane sukayi dafifi Yayin da Mama Lantana da Inna Hansai sukayi mawa Mahaifiyar Lauratu caaa da Cin mutunci tana yi suna yi . Itako A'isha Farida tana can kasuwa sam bata San Ma Abun dake faruwa a cikin gidan su ba .  


Hankali ƙwance take sayan kayan Yaji duk inda taje cikin sauri ake Sallamar ta saboda fitinan ta da jaraba . Ta Kamo Hanya ne zata dawo Gida ta tuna da Bata sayo mawa Mama Lantana Maggi Ba wannan yasa Farida tsayawa tana dafe kai . Ohhhh Ta furta tare da rintse ido don a yau ta yawatu itane Shopping Mall ita ne kasuwa duka a ƙafa sam taki hawar abun Hawa da Mama Lantana tace ta hau . Ta rike Kuɗin a dole Zata ci A waran Lauratu da Daddare . Don ita sam ta manta wai da sunyi faɗa da Lauratu . Humm motsa bakin ta tayi tare da cewa " Bara ki gani Yanzu Zan yi sauri na koma kasuwa na Sayo Maggi don jaka guda Mama tace na Sayo . Juyawa zata yi kawai a bakin hanyar Kasuwar taga Wani Babban Trading Company ana sauke buhunhunan Shinkafa Sugar Talia gasu nan da Kwali² na Maggi . Alhamdulillah Komai yazo Gidan Sauƙi ba sai ma na Tsaya komawa ba .  Zaf-Zaf ta nufi hanyar Companyn don Ita har yanzu Ganin kan ta take yarinya yar shekaru 9 ko goma ,don bata ganin kanta a yammata😁 wannan yasa take komai kan ta tsaye kayi mata magana kuma ta rufe ka da Tsiya . Da shigan ta masana'antan ne ta Ɗaga Kan ta tana karanta rubutun saman benen Companyn wanda aka Rubuta NAAWAZ TRADING COMPANY. Humm Wai Nawaaz Wannan wani irin suna ne haka? Ta faɗi magann tana taɓe baki tare da Saka ƙafarta tana shiga cikin inda ma'aikatan suke . Ma'aikata ta gani rutu bayan yan dakon Companyn da ta gansu a waje suna ta aikin ƙwasar kayan da ake saukewa . Me kike so Ƴammata? Taji Muryar Wani Saurayi daga Bayan ta yayi mata magana . 


Cike da Gadara tamkar wanda ta riƙo dubu ɗari ta kalle shi tana Harɗewa tare da cewa ' Maggi Star guda Ɗaya . Shiko Nafi'u Jin tace guda Ɗaya ya Ɗauka Ƙwali ɗaya take nufi Nan take yasa Aka kawo mata Ƙwalin Maggi Star . Hannun ta tasa tana farke Ƙwalin tare da Ɗaukar Ledar Maggin Guda daya . Miƙa ma Nafi'u Ɗari Uku da Sittin Tayi tana cewa " Ga kudin ku .! 



Ware ido kowa na Wurin yayi cikin mamakin raunin hankalin Wannan Yarinya . Wata ce mai zafin Rai ta miƙe a zafafe don ta lura A'isha Farida zata ja masu sallama da kora gashi a gaban Aminin Mai Companyn take wannan Aikin ,suma duk a tsorace yau suke , don daga mai Companyn har abokin nasa Sir Aslaaam ba mutunci ne dasu ba . Duka iskancin da A'isha keyi a idon sa . Amma kaman bai ga komai ba ,kallon ta kawai yake bai nuna ko in kula ba . 



Amma ke wacce kalar Jakar Yarinya ce ? Cewan  Gift Dake ƙara tighting belt ɗin ta . Juyowa A'isha Farida tayi cikin Wani irin kallo don Har ga Allah bata san ba'a siyayyar Ɗaiɗai A Company ba . Cike da Mamaki A'isha Farida tace " Ke Me nayi Miki zaki zage Ni ? Bani kika zagaba Uwar ki wacce kika bari a gida kika zaga.! Wani irin yunkuri Gift tayi tana Shirin damƙo Wuyar A'isha Farida wanda ko gyezau bata nuna tsoro ko ɗarrr Ba .wannan yasa Aslaam ƙara Sakin baki yana mamakin wannan Wacce irin tsilalliyar Yarinya ce ,bin ƙirjin ta yayi da kallo kamin ya kalli Fuskar ta ,mtswww Small Kid Yarinya ƙarama sai Rashin kunya abun da yace kenan a zuciyar shi kamin ya dakatar da Gift yana cewa " A ba A'isha Farida Kayan taje dashi zai biya . Juyowa A'isha tayi cike da mamaki kamin ta wangale baki tana cewa "Lahhh  Wai na tafi da kuɗin duka ? Ka saya mawa Mama ta Maggi ? Gyaɗa kan sa Yayi Alamun Eh don baya cika dogon magana .Kai wai dama ya'yan masu kudi suna da kirki irin ka ? Na gode Yaya na , na gode halin ka ba iri ɗaya da Wannan Shegiyar Kafurar ba , baƙa ƙirin fuskar ta har duhu yake tun kamin ta jita a wutan .....Shiiii Enough please.! Ya katse ta cikin hanzari jin tana shirin cin ma Gift mutunci . Ya isa Ɗauka ki tafi . Ai gashi nan a hannu na ,A'isha tayi maganan tare da juyawa tana kokarin ficewa daga Companyn . A'a Ai Duka Ƙwalin zaki dauka . 



Wani irin farin ciki ne ya lulluɓe A'isha Duka Yaya na Zan dauka , Allah ya baka abun da kake so na gode . Murmushi yayi har ta gama addu'an ta,ta fice daga reception din . Tare da barin Companyn da Ƙwalin Maggi Star .


**

Abuja

3:20pm . 

Tun da ta ƙara Wayar a kunnen ta take Sauraren maganan nasa da yake mata cike da baƙin izza da Miskilanci . Numfasawa tayi tare da sauke Muryar ta tamkar Wanda take magana da Yaron goye . Aaryaan Ka tabbata gobe zaka sauka a Nigeria?.  Sai da ya dau kusan mintuna uku sannan a takaice ya ba Hajiya Kubrah Amsa da Yeah ". Ok ya....Mum Ina Wani Aiki yanzu i Will call you later. Take care of yourself Okay? . Datse Kirar yayi yana cigaba da Aikin sa ta  laptop 💻 . Dafe kan sa yayi yana tunanin abubuwa . Mum I'm very sorry for what I did . Baa Son Raina bane bana Son zama tare dake , kawai Zuciya ta ce kullum take sakani nake nesa dake wanda ban san dalilin hakan ba . Tun tasowa ta nake jin hakan har yanzu . Buhhh I'm sorry mummy i love You. Maganan yake shi kaɗai Don yana keɓantacciyar Ɗakin sa na Nan malesia . Tsintar kan sa yayi da kallon Hoton Hajiya Kubrah kamin ya rufe laptop ɗin sa yana miƙewa tare da cewa " Inshallah A gobe zan sauka a gida nigeria . I know my mom will be very happy. Ɓangaren Hajiya Kubrah kuwa tana sauke wayan Kallon Ƙanwar ta tayi Hajiya Leela kamin tace "Hajja Leelah  Abun fa na Aaryaan is worst ,zuciya na zata buga . Ina tsoro kar yasan Gaskiya . Cikin Sauri Hajja Leelah ta dafa Hajiya Kubrah tana cewa ":Cool ur mind Mum Aryaan . Kawai nafi ganin girma ne yazo masa Kin san kowa da kalon nasa girman ,wani zaiji ya raba jikin sa dana iyayen sa ,wani kuma A lokacin yake daɗa ɗafa ma iyayen sa .  Kar ki manta Aryaan tun da ya kammala primary school ku ka tafi Abroad baku dawo nigeria ba sai da ya kammala deegre ɗin shi na Farko . SO dole ba lallai ya kasance yana jin dadin zaman Nigeria ba . Kinsan Rayuwar ya'yan Turawa ya sani , Su daga sun kai misali suke barin gidan iyayen su su koma nasu .  


Huhmmm Sauke ajiyar zuciya Hajiya Kubrah tayi kana tace " Ban san ya akayi Allah ya jarabe Ni da Soyayyar Aryaan a zuciya ta ba , tamkar nice na kawo sa duniya , soyayyar da nake masa Ko mahaifiyar sa bata masa irin sa ,don da tana masa Ni Nasan da yanzu ta ne meshi .  Leelah ce tayi saurin cewa " Kin manta mun mata farra'u tsakanin ita da mijin ta da Ɗan cikin ta? Kin manta me mukayi ne? . Na sani Hajja Leelah amma me yasa Aikin ya ki tasiri akan Aryaan ? Me yasa ? Na fara tunanin duka ƙarya ne Leelah . Hajiya Kubrah Wallahi ba ƙarya ,ki duba fa kiga ke kike juya cikin gidan nan . Aaryaan ne dai kawai . Yanda yake nuna mun tamkar ya zauna da mahaifiyar sa ta faɗa masa abubuwan da nayi mata , kuma Nasan fa bai san Ni banice mahaifiyar sa ba . Ƙwallah ne ya fara sauka ma kuncinta tana saka taffan ta tare da gogewa . Ba gobe bane yace zai dawo? A gobe Inshallah zan tafi Jigawa wurin mutumin nan na sanar masa dawowar Aaryaan , Idan kin rufe ido kin sa masa a binci yaci to, idan kuma kin ƙi ke kina tausayin Ɗan ki shikenan, Sai ma Yasan bakyece mahaifiyar shi ba zaki ga sauyi . To Hajja Leelah ki amso wannan karon Abun is to much Wai Har Hajiya Lubna ta fini matsayi akai na , Yafi ganin ta da kima a kaina . Ya dauki Yusraht tamkar Ƙanwar sa ta jini . Ko da yake ai hakan yake Amma mahaifiyar Yusraht Ƙanwar Mahaifin sa ne kaɗai , Alh Abdu Kareem me yasa yake zama a can Gidan Fiye da gidan mahaifin sa ?. Kuyi hakuri Hajiya Kubrah Za'a yi maganin komai , Wallh in so kike yi idan Aaryaan ko wani irin umarni kika basa kar ya kyatara ba zai yi ba . Kawai ki bani daga yau zuwa gobe.

**

9:01pm .

A hankali take Gyara ƙwanciyar nata tare da Kallon Mum Lubna dake rufe ta da Blanket . Yusraht Sleep well . Mumy Good Night. Juyawa Mom Lubna tayi zata fita taji Yusrah ta riƙo Hannun ta , Wannan yasa ta juyowa tana kallon ɗiyar nata .! Mummy Wai me yasa tun tasowa ta Baƙwa jituwa da Daddy? Kullum kaman akwai wani Abu a tsakani ku amma kuma ɓoye mana , a tunani na a da don ina yarinya ce ki shiyasa kike ƙin faɗa mun , Amma mai yasa ba ki faɗa mawa Ya Nawaaz ba ? Idan shi namiji ne ai Ɗan ki ne ,to Ni a yanzu na isa rufe ko wani irin sirri ne dake tsakanin Iyayena , please Mummy ki faɗa mun a yanzu shekaru na ashirin da Huɗu na cancanci Nasan damuwar ki dana Daddy . Wani irin bugawa zuciyar Hajiya Lubna yayi cikin ƙaƙaro murmushin dole ta sa hannun ta tana haɗawa dana Yusrah , Yusraht babu komai tsakanin mu me yasa kike Wannan tambayar , Kawai dai kin Daddyn ki ba mutum ne mai yawan surutu ba shi yasa zaki ga Bama fira tsakanin mu . Amma mum ai muna fira idan muna a tare , Tsakanin ku ne nake ganin tamkar akwai wani Abu . Babu komai Yusrah ki yarda da abun da na faɗa Miki . Shiru Yusrah tayi kana tace " Na yarda Momy good night . Rage hasken Fitilun Ɗakin tayi kana ta fito tare da rufo ƙofan Bedroom ɗin nata . 

**

Bayan A'isha Ta koma gida a lokacin iyayen Lauratu sun bar Gidan ,don haka babu kowa sai masu ba Mama Lantana haƙuri . Anan ne A'isha take jin gorin da Laminde tayi ma mama Lantana tare da cin mutunci wai ba'a san A salin su ba . Farin cikin Maggin da Ta samu kyauta ne ya koma ciki . Ɗaki ta nufa ba tare da ta ce komai ba ,jikin ta yayi sanyi tausayin kansu ya kamata . Zama A'isha tayi tana tunanin yanda Mama Lantana ke shiga Wani Hali duk idan ta tambaye ta ina ne Asalin su . Wannan kuma yasata yanke hukuncin har abada ba zata kara kuma tambayar ta komai ba . Wuraren Yammacin ne A'isha ta fito daga Dakin su . A Madafi ta samu mama Lantana tana Aikin girkin yamma  . Mama Sannu da Aiki . Cikin fara'a mama Lantana ta juyo tana cewa " A'isha kin tashi barcin , Yau baki je islamiyya ba , Kina ta barci yanzu nake shirin na tashe ki bakyau barcin yamma . Shiru Aisha tayi a tunanin Mama barci nake yi kenan ? Tunanin Rayuwar mu nake yi . Kallon Fuskar mama Lantana tayi ganin yanda ta nuna uwa duniya ba'a yi wani Abu ba ɗazu na rikici . A'isha ta lafiya tunanin me kike yi? Abinci ne zaki ci? . Mama Lantana ta jero mata Wannan tambayoyin tana jirar Amsan A'isha wanda gani tayi A'isha Farida ta rungume Ta tsam tana fashewa da kuka . Mama na amince mu bar garin nan A yau zamu tafi ,zan je Aikatau ɗin , Ina so na zama Kaman saura masu gani da idanun su a ko wani lokaci , ina so nan kusa na fidda ki cikin damuwar da muke ciki tun tuni . A hankali Mama Lantana tasa Hannu tana Ɗago Fuskar A'isha . Murmushi tayi mata cike da son kawar mata da damuwa . A'isha kwantar da hankalin ki ,bakina Son zaman nan ba ?. Mama A yau zamu bar Garin nan mu tafi can , Kibar Inna Hansai ta sai gidan da komai kawai . Tana Gama faɗin haka kamin ta ji na bakin Mama Lantana ta juya tana shigewa ɗakin ta don harhada kayan su . 

Cikin Sauri mama Lantana ta nufi Dakin don ta rarrashi A'isha ta bari sai zuwa Safe su nufi Tasha su hau moto da kayan su a yammacin nan kuma ta samu dalallin gidan ya basu kudin . 

Ɓangaren Aryaan kuwa da Hajiyoyin sa biyu Nahila da Bie-bie Tun bayan keorar sa da Mom Kubrah tayi ya wancakalar dasu , a ranan babu mutum guda da ya iya Saduwa da ita da sunan sex . A daddafe ya kwana yayin da Safe ya shirya tare dasu don su dawo gida nigeria daga nan kowa tayi ta kanta. Sai kuma sun haɗu a ɗaya daga Gidajen sa na nigeria su cigaba daga inda suka tsaya .

Malesia Airline 9:00am

Da misalin Wannan lokacin ne jirgin su ya ɗaga zuwa Gida nigeria sai dai muce Allah ya sauke su lafiya .

**

NAAWAZ kuwa Tun da ya amfa Taskon Hajiyar sa ya faɗa hannu kwanan su uku sam taki barin shi ya fito . Niko abun mamaki yake bani , banda jaraba da iskanci Allah ya rufa maku duk son Iskancin kuyi aure mana ku huta . Amma duka sun gummaci su rinka biyan buƙatar su a hannun matan banza da Wofi har da iyayen su . Suyi ta sukwanan yan banza . Yau jin Aminin nasa yana Hanya kuma Ɗan Uwan sa cousin din sa Wato Aaryaan yasa shi tattarawa don dole yana kimtsawa don ya dawo Abuja .  Gentle Guy ƙyaƙyƙyawan matashi shi dama shigan sa bai wuce track suit baya son kayan nauyi sam.  Fuskar sa cikin baƙar tabarau yake Wanda yaƙara ƙayatar da kyawun sa . A tsakiyar compound din gidan Hajiya Nafeesa take riƙe da hannun sa ,a bakin Moton sa sam taƙi rabuwa dashi . Hannun ta tasa tana Kamo Kaciyar sa tare da shafa tana murzawa tare da kumshe ido tana masa Wani irin kallo . Zan yi kewar ka sosai . Tana maganan tana cigaba da mutsikar Ƙatuwar Buran sa , tare da Karkaɗa Twins ɗin sa tana wani lasar labɓan ta . I Will come back soon inshallah . I'll be waiting Nawaaz ,ka dawo da wuri don Allah. Girgiza kan sa yayi yana sakar mata Murmushi don shi kan sa ya ji dadin mu'amalar tasu in a just two days ta shayar dashi mamaki ,bai taba gani mace Harija data amsa sunan ba kaman Hajiya Nafeesa . A haka daƙyar kaman ba zata bar sa ba ya fito gidan . 

**

Kaman yanda Mama Lantana tace tun safe suka bar garin da komai nasu tare da Tarkatawa zuwa Garin Abuja .wanda tun kamin su isa Da yake ita mai jama'a ce aka saya mata gida dan dai dai karami . A daga Waje kuma wani babban Shago ne wanda zata rinƙa sana'ar Sayar da Abincin ta kaman yanda ta saba . Da sauran rana Suka isa Abuja tun shigar su gidan A'isha ke bin gidan da kallo a lokaci guda tunanin sa ya fara dawo mata Ƙwallah ne ya ciko idanun ta a zuciyar ta cewa take " Shikenan Yanzu ba zan ƙara Ganin ka ba ? Amma kai kace mun zaka dawo.! Kana ina ne ,kana ina ne ɓoyayyen Masoyi na?. A wannan rana a ɓoye ba tare da Mama Lantana ta lura ba A'isha Farida tayi kuka iya kuka har ta gode Allah . A haka ta fara sabuwar rayuwa a garin da Batasan Yaya yake ba. Satin su guda ta shiga Islamiyya , ana haka kuma Inna Hansai ta taho ,anan ne take sanar da Mama cewa Hajiyar Gudan ta amince da aikatau ɗin nata . Wannan yasa a washe Gari Inna Hansai ta dauki A'isha Farida da kayan ta tana ma Mama Lantana sallama . Wannan shine rabuwar su ta farko tun da suke a rayuwa . Kuka A'isha Farida take yi mama Lantana na kukan itama tare da rarrashin ta ,kana tayi mata Alƙawarin rinka zuwa Tana dubata duk idan ta samu lokaci, rarrashin ta take yi tare da cewa " Aikin wata shida ne Hajiyar ta Ɗauke ta . 


Gidan Alh marshal Abdu Kareem Gida ne mai mahaukacin Girma ga ma'aikata kowa da aikin sa , kuma uniform suke sakawa a dokan Hajiya Kubrah kenan don tace bata son tana ganin tsummoki wannan yasata ko wani ma'aikacin ta yake saka uniform ,kalon na masu shara da  goge goge da ban ,na masu girki da ban . Tun da A'isha Farida ta fara Aiki a gidan Take ganin tijara wanda bata taɓa ganin irin sa ba . Amma haka tasa hakurin da bata dashi don dole . Yanda Hajiya Kubrah ke ma yan Aikin ta tamkar bayin ta . Har da Ma'aikata masu yi masu massage ( Tausa) . Ke yanda take mulki ko sarauniyar Ingila Albarka .


5:pm .

Tun wuraren ƙarfe Uku na yammaci take kitchen ita da Adda Maryama , Itama mai girki ne amma babbace tana da shekaru ba kaman A'isha Farida ba. Ihu take ji da Shashanci irin na ya'yan Hutu yayan gata ,rabi da kwatan maganan su bata fahimta , ta dai fahimci turanci suke yi ,amma kuma American English Kuma ita bata iya ba wannan yasa bata mai da hankali don ta saurara . Kee ke A'isha..! Taji Adda Maryamu ta kirata a hankali . Ɗago idanun ta tayi tana kallon ta kamin tace me ya faru ? . Ki fita ki kai wannan Dinning room suna nan a falo Sir Aaryaan fa ya dawo ,bakiji firar su ba gayi can , ki bi a hankali har ƙasa ki gaida su , basa da kirki ,kuma har da Tsegalallun ƴammatan nan a wurin ,idan kin kammala sai ki masu magana Kinji . To Adda Maryamu amma Ai Nasan shi zai kasance mai kirki ba kaman Mahaifiyar sa ba Hajiya Kubrah . 



Saurin kama baki Maryamu tayi tana cewa " Kee Wane ? Ai wannan ya fita kaman sama da ƙasa ,ga rashin mutunci ga Miskilanci ke halin sa sai mun zauna . Hummm A'isha Farida tace tare da Ɗaukar wani Basket dake dauke da different dishes . Nufo Falon tayi kan ta tsaye fuskar ta a sake idanun ta a sama ita har ga Allah duk ta kosa tazo taga masu magana da American English haka don bata fahimta .  Wow .! Ta furta cikin sauri tare da nufar falon don ƙamshin Turaren wurin yayi mata dadi sosai kaloli daban-daban alamu ya nuna mutane mabanbanta a wurin . 



Cikin sauri ta risina a daga tsakiyar falon tana kallon Hajiya Kubrah dake tsakiyar Falon . Hajiya Sannu da Hutawa.! Duka a tare suka ɗago suna kallon ta jin Sanyayyar Muryar mai zaƙi da daɗin saurara . Juya kai Hajiya Kubrah tayi tana cigaba da Shafa Kan Yusrah tare da cewa " Yanzu ai kuka kuma ya ƙare tun da Cousin ɗin naki ya dawo ko?. Inda sabo A'isha ta fara sabawa da wulaƙancin Hajiya Kubrah wannan yasata juyawa tana kallon ƙasa tare da cewa A'a Aaa A'ammm Sannun ku da Izuwa .! 



Saurin Miƙewa Yusraht suka ga tayi kaman wanda aka mitsina kece?? Tayi magana da ƙarfi tana nuna A'isha Farida da Hannu . Ɗago kai A'isha tayi a lokaci guda ta tuno da Yusra da kuma marin Yusra da tayi .wani irin tsoro ne ya kamata Wannan yasata saurin juyawa tana kallon Gyefen ta Aslaam ta gani yana bin ta shima da kallo . Kai ne ka saya mun me tauraro ko? Tayi maganan kamin ya bata amsa ta juya tana kallon ɓarayin sa INDA Nawaaz yake Shima ita yake kallo ,tuno da rashin kunyar da tayi masa yasa idanun A'isha Farida firfitowa . Gyefen sa Sadeeq ne Wanda a gaban sa Ta Mari Yusra har da hade Moton su da ƙasa . Innalillahi wai'inna ilaihir raji'un Abun da Farida ta furta kenan kana Ta kallo inda Aryaan ke zaune ko Ɗago kai baiyi ba bare ya kalle su ko yaga Abin da suke yi . Mum wannan itace yarinyar da ta mare Ni da nake baki labari .yau zanci Uban ki kuwa dama yar matsiyata ce ke na sani . Jikin A'isha ne ya hau Rawa idon ta na taruwa da Ruwan hawaye . don Allah kuyi hakuri Duka Wallh Ban san anan kuke ba , Wallh da ban maku komai ....!






Tirƙashi😂

Yanzu fa aka fara😻

Free page zai ƙare a page na gaba maza hanzarta Wajen mallakar taki... Regular group ₦500... Vip group ₦1000 Special ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 .

No comments

Powered by Blogger.