Fulani 1

 


Jihar Katsina jiha ce daga cikin jihohin Nijeriya guda talatin da shida (36), tana yankin arewa ta yamma na kasar Nijeriya. Ansamar da ita ne daga cikin jihar Kaduna, Mutanen jihar Katsina mafiya yawansuHausawa ne, sai kuma Fulani kuma sana'o'insu noma ne da kiwo. suna da halsuna Hausa, Fulani, Turanci. Tana da kananan hukumomin 34 sune :-


Bakori

Batagarawa

Batsari

Baure

Bindawa

Charanchi

Dan-Musa

Dandume

Danja

Daura

Dutsi

Dutsin-Ma

Faskari

Funtua

Ingawa

Jibia

Kafur

Kaita

Kankara da sauransu, GARIN BANDALO (garin bandalo da sunan garin duka na kirkira ne) babban gari ne da ke cikin karamar hukumar Kaita, garin bandalo garin Fulani ne da ke da fadi da yalwan arzikin noma da kiwo. Ya wacin mutanen garin da suke kiwon shanu a yammacin gari da kewaye, wa su kan shiga birni yin fatauci, matan su kuma na shiga birane tallar nono da danyen manshanu, yawacin fulanin da suke garin ba asalin yan garin ba ne, irin fulanin nan ne makiyaya, masu yada zango a duk garin da suka tarar yana da albarka da ruwa. Wani abun da zai burge duk wani bakon garin shine yadda fulanin suka kawata garin da bukkaken fulani, a tsakanin wacan bukkar da wata akwai tazara sosai, domin kowa ya yi gidansa ne a cikin gonarsa, masu wadata da arzikin cikinsu ne suke zagaye gidansu da zana su killace kansu kamar masu babban gida. 


MALAM JAURO SAMA'ILA Shine Sarkin Fulanin wannan yankin, sarki mai adalci da kamanta gaskiya a tsakanin Fulanin da yake mulka, sarki ne daya kafa tarihin da babu wani bafullatani a yanki da ya kafa irin tahirinsa, ta hanyar bawa yarsa Faɗime ilmin boko da na muhammadiya, shi ne kai da mutumen da yake daukar yarsa ya shiga da ita birni a duk safiya ta Allah idan zai je fatauci ya aje a makarantar bokon da ke garin Kaita shi kuma ya shiga cikin garin gurin harkokinsa.....


FAƊIME 

Ya daya tillo a gurin Malam Jaure, kuma ya daya tillo a gurin Tumba, yar da ta kafa tahirin shiga makarantar boko a garin Bandalo. Yar da kowa ke gudu yar da kowa ke kyama yar da kowa ke fargabar arba da ita, yar da Tumba tai mata alkunya da FULANI. 


FULANI POV


Hawaye ne ke fitowa daga lussasun idabuwanta da take sharar bachi da su, fuskarta kuma na kawatuwa da murmushin dalilin mafarkinta. 


"Fulani Fulani Fulani"


Firgigit ta bude ido ta tashi zaune tana kallon mahaifiyarta wacce ke tsaye a sanye da riga da zane na Atamfa, kwayar nono a hannunta.


"Dun Allah Dun hanyar hillacin ki tashi ki kai shanun ga yamma su sha ruwa su yi kiwo, hay Fulani rana hwa ta na ga yi kuma kin san ba su ci komi da safe ba"


Wacce aka kira da Fulani ta saka hannunta na dama da na hagu ta share hawayen bachinta.


"Amman Inna yau ba Hajjo ce da zuwa daji ba?"


"To Inna Hajjo ta hana ta ta ce ba zata je ba, hadda ta turata bunni gurin talla dawo da nono tun dazun suka tafi tare da Mairo, dan haka ke sai ki tashi ki tahi kamin Malam ya dawo, kin fi kowa sanin cewar baya son a bar mai nagge da yunwa"


"To Inna zan tai yanzu"


"To tashi yar albarka, idan kin hito sai ki sha sabon kindiro yanzu na taso shi"


Inna Ladi na fadar hakan ta juya ta fice rike da kwayar sabon nonon da ta taso yanzu, nonon da ko manshanu ba a cire masa ba. 

Mika Fulani tai tana sauraren busar Sarewar da take yawan jin a cikin bachinta, ba kuma dan ana burar a Sahiriba sai dan sabo da tai da ita a kowa wane bachi, ya'alan na safe ne ko na rana ko dare, indai har ta kwanta sai ta yi mafarkin wannan mutumen da ya bata baya yana ta burar sarewa a saman dotse, busar da ke sakata hawaye da murmushi a lokaci daya kuma a cikin duniyar mafarkinta, sai dai murmushin da hawayen har a zahiri ana ganinsu, yayinda busar sarewar kuma ita kadai take jin abarta a cikin bachinta. Mikewa tai tsaye ta nufi gurin jakar kayanta ta dauki littafinta da buro ta zauna a gurin ta soma rubutunta kamar yadda ta saba. 


_Yau ma na yi mafarkinsu, dayan a gefena mai busar ya ba ni baya, dayan kuma a bayana_ 


Bayan ta rubuta ta rike biron tana ta tunanin yadda mafarkin ya zo mata, a kullum mutanen nan uku mafarkinsu take, sai dai ba zata iya siffanta su ba, domin bata iya shadar fuskokinsu balle kuma wani abun da zai saka ta iya cewa aljanuna ko mutane. A zahiri dai sun fi kama da aljannun domin shi mai busar sarewar kullum baya yake bata, tun tana jin busar a nesa har ta fara mafarkin tana tsinkayarsa ya bata baya, to shi kuma wanda ta bashi baya wanene? Wanda kuma yake gefenta wanene? Su ma duka aljanun ne ko kuma wani abun ne na dabam? Miyasa take yawan mafarkinsu? Miye alakarta da su? 


"Fulani....."


Kiran mahaifiyarta ne ya katse mata dogon tunanin da ta fara, da sauri ta mike tsaye ba dan tana son zuwa kiwon ba, gudun irin abubuwan da suke faruwa wani lokacin, mawuyacin abu ne ta fita ta dawo ba tare da wata saniya ta samu karaya ko kuma ta mutu ba, ko da yake idan ba tai kiwon ba mi za tai? domin a kullum cikin fargabar fita take a cikin jama'a saboda abubuwan da suke samunta ko kuma suke samun jama'ar da take kusanta, kusan ta zama annoba kowa a garin tsoronta yake gudunta yake idan ka cire iyayenta babu mai iya zama da ita ya wanye lafiya........


Omar Abdallah Jari da na biyu a gurin Sarkin Yola wato Sarki Abdallah Jari da Hajiya Kilishi. Mutum ne mai yawan kyauta da nuna kauna da ga talakawa ga yawan murmushi da haba haba da jama'a.


SHATTIMA OMAR POV


Tsaye yake jikin window falonsa yana kallon yadda ruwan sama ke sauka harabar gidan yadda ya kurawa gurin ido sai ka rantse da Allah kirga ruwan yake, babu komai a zuciyarsa sai kewar triples dinsa, saboda suya baro gurin aikinsa sokoto ya zo garin iyeyensa kuma garin haihuwarsa Yola, amman yana fargabar tunkarar Masarautarsu saboda mahifiyarsa wato Hajiya Kilishi. 


Hannu ya saka ya cire wayarsa da ke aljihu ya nemo number Nana ta aika mata kira, ringing biyu ta daga. 


"Hello Ya Shattima"


"Babbar Kanwa ya kike? Ke kadai ce?"


"Eh kuma ina nan Lafiya, ya aikin?"


"Ina son ganin Triples i miss them, dan Allah ki sato min su ki kawo min su guest house, zan ba ki goro"


"Oh Sorry Shattima ka dawo kenan, shiyasa dazun Ammy ta aiko jekadiya ta ce a fada min kar na kuskura na fita da triples"


Ya dan wara ido yana fadada murmushinsa.


"Ta san na dawo?"


"Maybe amman tun da ka ji tace haka kam ai ta san ka dawo"


Dariya yai dariyar da ta bayyanar da fararen hakoransa ya sauke wayar. He wonder how mahaifiyarsa take da basira haka har ta tasan da dawowarsa. Baba Adamu ne ya fado masa a rai a take ya bar jikin tagar ya nufi dayan falon da Baba Adamu yake. Baba Adamu na ganinsa yai saurin mikewa tsaye irin na girmamawa, har sai da Omar ya zauna sannan shi ma ya zauna a kasa.


"Tashi kasa zauna saman kujera"


"Aa ka bar ni nan ranka ya dade"


"Kai ne ka labartawa Ammy na shigo gari?"


Shattima ya tambaya yana dora kafa daya saman daya. Baba Adamu ya kara yin kasa da kansa.


"Ita ce ta bukaci sani, wannan dalilin ne yasa ta maido da ni gurinka saboda ta rika sanin halin da na ke ciki"


Murmurshi Shattima yai mai sauti ya shafa kansa. 


"Amman Baba Adamu ba ni da ikon yin sirri da kai? Ko ruwa na sha sai ka fadawa Hajiya? Ana rayuwa haka?"


Ya tsosa lips dinsa, yana kallon Baba Adamu, Baba yake kiransa duk kuwa da kasancewar karkashina yake sai dai ganin dattijo ne wanda ya isa ace ya haife shi be zai iya kiran sunansa hakan nan kawai ba. 


"Yanzu ga shi ina son ganin yayana amman ba ni da dama saboda ka fadawa Ammy, ni kuma ba son shiga na ke gidan ba daga ita har Mai Martaba ba barin yi min maganar aure suke ba"


Ya fada yana daga kafadunsa. Baba Adamu ya kalleshi cikin Ladabi ya ce. 


"Ranka ya dade suna son kai auren ne, kai kanka za ka fi kima da daraja da aure"


"Haba dai Baba Adamu kamar ba kasan ni ba? Aure nawa zan yi Fisabilillahi? Mace shida ina aure suna mutuwa yanzu idan na kara ta bakwai kenan waya sani ko ita ma iyayenta su rasa ta, ni fa tsoro mana ke kar a fara min zargin maita"


Ya fada yana mikewa tsaye. Baba Adamu ya daga kai yana kallonsa.


"Ranka ya dade ba maita ba, kalmar ba da ka furta a bakinka ina ganin kamar be dace ba, waye be san kaddarar Allah ba?"


"To ka bincika min wace uwar ce ta son rasa yarta da zata aurawa Omar a samo min ita"


Yana fadar hakan ya nufi upstairs yana murmushi. Baba Adamu ma Murmushi yai duk da kasancewar duk mace da ta auri Shattima mutuwa take wata tana amarya wata bayan ta yi wata hudu zuwa kasa, Maimuna ce kawai tai shekara da wata biyar har ta haifa masa yan uku, bayan ita ya auri Basira ta rasu da wata daya, sai dai hakan ba shi zai saka yarima Omar auren ko wace mace ba a ganinsa sai wacce iyeyensa suka zaba masa ko kuma shi yake ganin ta dace da shi......


WASIM RAU dan sarkin maharba kuma jikan sarkin matsafa na garin GARUK. Mutum ne mai son busar sarewa da zaman dajin, be fiye son harbin ba, duk kuwa da kasancewar shine gadonsa, ba shi da tsoro sai dai ban tsoro. 


WASIM POV


A yau ba saman dotsi yake busar ba kamar yadda ya saba, a saman ice ya hau yana busa sarewarsa, cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake busar, ba mutum kadai ba ko aljani idan ya ji busar sai zuciyarsa ta sosu. Lumshe ido yake yana budewa shi kanshi busar dadi take masa domin tana saka shi nishadi da walwala, idan ka cire abinci da ruwa da rai baya iya rayuwa sai da su to busar sarewa ce abu na biyu da yake kauna a rayuwarsa, busa ce mai dadi kuma mai daidai da yanayin garin da ya hada hadari da iska mai dadi.... 


AHMAD ASHIRU UNCE A A matashin sarauyin da bashi da aikin yi ba dan be yi karatu ba, sai dan aikin a Nigeria ya zama sai wane da wane, sai mai hanya da gata sai kuma wanda Allah ya tsago da rabon abincinsa a gabnatin jiha ko ta tarayyah, a gurin yayarsa yake zaune wacce ta tsaya masa bayan raye uwa da uba, ita ta zame masa tamkar uwa duk wani fadi tashi na karatunsa da hudimar rayuwarsa ita ce take masa duk kuwa da kasancewar ita ma din ba wani abun hannu ne da ita ba, sai dai tana sa'ar siyarda kayan masarufi a cikin gidanta sana'ar ta karbeta sosai a ciki take ci ta ke sha har ma tai ma mijinta wata hidimar kasancewarsa karamin lebara ne wata....



UNCLE A A POV. 


Shinkafa da wanke ce da mai da yaji an yanka tumatur a cikin da albasa, sai kuma ganyen salat da aka yanka a sama shi ma kadan. A hankali yake tauna ragowar shinkafar da ke bakinsa, hannunsa rike da waya yana duba duniyar facebook.


"Uncle A A ba zaka ci abincin ba sai ya sha iska? Ba dadi idan ya huce"


Dauke idonsa yai daga kan wayar ya kalli Jamila wacce ke maganar yai dariya. 


"Zan ci yanzu Jamila"


"Ai ka saba kullum hankalinka yana kan waya"


Cewar Anti Rabi, dariya yai ya ce. 


"Anti abunda ke ban mamaki wai sai ka ji mutum daya ya yi sama da dukiyar talakawa ta miliyoyin nairori, ni har ganin na ke kamar kudin nan karya ne, wai yanzu akwai irin kudin nan muke zaune haka?"


Dariya Anti Rabi tai tana aikin kulla man kulin da take ta ce. 


"Gaskiya ne akwai kudin idan kudi, sai dai masu kula da kudin ne macuta kuma mazanbata"


"Hmm Allah dai ya kyauta, mu ko aikin ya gagare mu samu, da ma degree ne wata kila da za ka fi samu amman ba kowa ke ganinta da daraja ba"


"Karka damu Ahmad wani abun a nesa yake, kuma kowa da irin kaddararsa"


"Haka ne Allah yasa mu dace"


Anti Rabi ta amsa da amin. 


*** *** ***


Kadan kenan daga cikin abunda littafin FULANI ya kunsa.


Best Regards ❤🌹

Khadeeja Candy. 

*🐄🐄 FULANI 🐄🐄*



By Khadeeja Candy 







*Free Page -1*


 ©®Hakkin mallaka nawa ne ni kadai, ban yadda a saffaramin labari ta kowace siga ba balle har a dorashi a YouTube ba tare da izinina ba, yin hakan kuskure ne babba domin zai iya hanyowa mutum matsala a kiyaye ⚠


Ban yarda kowa ya hada document na littafina ba, ni ma na iya idan ina ra'ayi zan iya yi da kaina, ina albishir ga wanda ya hada document din Gobe na da duk wani littafi nawa cewar ban yafe ba ina rokon Allah ya saka min kuma ya mana shari'a da ko waye ne❗️


FICTION.


FREE PAGE. 


FALMATA POV. 


Yola... 


Tun tana surfen da kuzari har ta kai bata iya daga tabaryar da karfi, babu komai a tare da ita sai tarin yunwa da gajiya ga wani uban ciwon kai da ya saka ta gaba. 

Cike da juriya ta

karasa surfen sannan ta risina tana kwashewa tana zubawa a kwayar da ke gefen turmen, sai da ta kwashe shi tas sannan ta hade da sauran da ta surfe, mikewa tai tsaye tana rike da surfen ta nufi gurin tukuyar ruwansu. 


"To mai kunne kashi ban fada miki idan kika yi surfenki ki rika zuwa bohal kina debo ruwanki ba? Ke wai Fulani sau nawa za ayi miki magana ne?"


A wahale Falmata ta kalli Tumba wacce ke mata maganar, ta amsa mata tana jin kamar ta fadi a tsakar ranar da ke dukan kanta. 


"Umma idan na gama zan je na debo wasu sai na cika"


"Ban yarda ba, kije ki fara debowa ki yi abunda za ki yi wannan wanda kike debo mana na aiki ne bana wankewa wasu banza surfe ba"


Uffan bata sake ce mata ba, sai ta nufi gindin bishiyar dogon yaro ta aje surfen, sannan ta sake komawa ta dauko wani katon bokoti ta riko shi a hannu ta nufi kofar fita jiki ba gwari, tafiya take a hankali kanta a kasa bata kallon kowa sai hanya, gaisuwar girmama ce abunda yake fitowa daga bakinta sa'adda duk tai arba da sa'ar iyayenta. 

A yayinda ta isa bohal din sai ta nemi guri ta tsaya tana ta kallon yadda fanfon bohal din yake cike da mutane yara da manya. Matsawa ta kara can gefe tana daga zanenta kamar mai kyankyamin ruwan da ke zube a kasa.

Kallo daya za ka yi mata ka karancin irin natsuwa da tarbiyar dake tare da ita, sa'aninta na gaban fonfon suna gogoriyon dibar ruwa ita kuma tana tsaye gefe abunta tana kallonsu kamar ba diban ruwan ta zo yi ba. 


"Falmata kawo na baki bokiti daya"


Cewar Khadija kawarta, abun ka da mai nema sai tai saurin cira kafa ta isa gurin da Khadija take tsaye rike da kan fonfon ta mika mata bokitinta. 


"Na gode kawata"


"Karki damu, indai akwai mu ba kya rasa komai kawata"


Khadija ta fada tana daga mata gira, murmushi ne ya fadada kansa a fuskar Falmata ya bayyana fararen hakoranta wanda ya karawa bakar fatarta sheki. 


"Yau ba za ki je gidan Sarki ba? Kin san fa ke ce mai gyara dakin yan uku da kula da su"


Khadija ta tambaya tana daga muryar wai dan mutane da ke gurin su san kawarta na aiki a gidan Sarki. Wata irin kunya ce ta rufe Falmata abun ka da bakauyen mutum sai duk ta ji ta muzanta. 


"Ke Madam ba za ki ba yau?"


"Na tafi, har na dawo sai kuma gobe"


Ta amsa mata kamar ana matso maganar daga bakinta, gaba daya kunya ta gama rufe ta, kamin bokitin ruwan ya cika duk ta tsawwala, bokitin na cika Khadija ta kama mata ta dora a kai sannan ita ma ta dora nata suka kamo hanya tare. 


"Mtswwwww Wallahi Falmata ba ki hadu ba, wai ina son ayi kurin nan ke kuma kin wani noke ba ki ma son amsawa"


Abun nan dai da ya zame mata al'ada ta yabawa fuskarta, wato murmushi sannan ta soma magana da muryarta mai taushi da dadin sauraro. 


"Khadija kunya na ke ji"


Wani banzan kallo Khadija tai mata. 


"Kunyar me? Aikin a gidan sarki? Allah ya kai Khadija Wallahi har tafiya sai na sauya"


Wannan karon dariya marar sauti Falmata tai, tana jinjina lamarin kawarta, daman can indai kaudi ne da iyayi da ba ni na iya ba dai Khadija ba. 


"To ai na ga ni ban wani dade da fara aikin ba, da har za a ce na fara kuri wannan zuwan da nai dazun fa shi ne zuwana na uku, kuma ni na ga..... "


Sai kuma tai shiru bata karasa ba, sai dai karara yanayinta ya nuna akwai damuwa a tare da ita kamar yadda fuskarta take nuna akwai tarin maganganu a kasan halshenta. 


"Miya faru?"


Tsayawa tai tana kallon Khadija kamar yadda Khadijar ma ta tsaya tana kallonta. 


"Sai na ke ganin kamar ba su yarda da ni ba...."


Fuskar Mamaki Khadija tai. 


"Ban gane ba?"


"Kin ga tun da aka dauke ni aikin, har yanzu ban ga yaran ba, sai dai na gyara dakinsu, kuma idan zan gyara sai a saka dogari ko wata baiwa sun tsaya dakin har nai na gama"


"Suna da wulakanci ne?"


"Aa har yanzu ba a taba min ba, ban ga alamun hakan a iyalan gidanba, duk da yake dai ban gama ganin kowa da kowa ba tun da zuwana na biyu kenan, sai dai da alama suna da wuyar aminta da mutum"


Hannu daya Khadija ta saka ta dafa kafadarta. 


"Karki damu, daman su yan sarauta basa saurin aminta da mutun, amman dai da sannu za su fahimci kawata mutuniyar kirkice su aminta da ita"


Ta karasa tana dariya tare da rika fuskarta. 


"To Allah yasa"


"Amin, kuma bari na fada miki ba wai saboda wannan bakar Tumba ta tura ki aiki dan ki samo mata kudi ba, ba wai duk abunda aka ba ki za ki bata ba, albashin ma rabi za ki bata ki boye rabi, dan alherin idan kin samo karki kuskura ki bari ta gani, ke abinci wannan ma da ki kawo mata Wallahi kara ki ɓarar dashi a akwata"


Har wani yatsine fuska Khadija take tana jin kamar ace ita ce a matakin Falmata take da step mother kamar Tumba da Allah kadai ya san irin sherin da zata kulla mata. 


"Mahaifina yace idan ban mata biyayah ba be yafe min ba, ko da ace bata san yawan kudin aikin ba zan bata dika balle kuma ta riga ta sani, idan ma na hana ta zata iya duka ko taja Baba da kansa ya doke ni, ba ni da wani yanci a gidan nan Khadija kin sani"


"Hmm ai har da ke Wallahi da kike biye mata, ke ko yar ketar nan ba ki iya ba, Wallahi da ni ce da sai ta sha wuya, shiyasa na tsani shegiyar matar nan bakar Tumba kawai"


Falmata da dai bata ce mata komai ba, ta cigaba da tafiyarta, sanin kanta ne idan zata ce Khadija ta daina kiran Step mom dinta gatsasa sau hansin sai Khadija ta aikata sau dari biyu. 


"Ki duba ki ga fa saboda ki Wahala ta tura ki aiki a gidan, ga yayanta, kuma wai dan tsabar zalinci tace ita zata karbe albashin, bayan babu abunda take tsinana miki"


Tafiya suke Khadija na jifar Tumba da kalamai marasa dadi, Falmata dai bata ce mata uffan ba har suka raba hanya, kowa ya dauki hanyar gidansu. Da sallama ta shigo cikin gidan amman aka rasa mai amsa mata kamar masu gaba da ita ko kuma wadanda ba su ji sallamar ba. 

Ko kadan hakan be dame ta ba, inda da sabo kusan ta saba da wannan rayuwar. Kallo daya tai ma Naja ta dauke kai ta hade wani abu daya tsaya mata a makoshi, yar gata kenan masu yin yadda suke so a gida ba kamar ita ba, wacce aka hana wanke surfen da ruwan da ita da kanta tai aikin jigilar debo su da safe, an bar yar gaban goshi tana wanki da su. 


Sai da ta sauke ruwan sannan ta nufi gurin da surfen yake ta dauko ta wanke, ragowar ruwan ta juye a karamin bokiti ta shiga bandaki tai wanka, dakinsu ta nufa ta shafa mai abun ka da mai son kwaliya sai ta dauko ragaggin kayan kwaliyarta ta tai kwaliya har da su jan baki. Ta yi kyau sosai duk kuwa da kasancewar ta baka sai dai bakin be rage ta da komai ba daga kyaun sura kwarjini ta halitta da kuma cikar sura da zati irin na ya mace. Baka ce amman ba mummuna ba, baka ce kyakkyawa irin kyau ne mai shining. Bakinta mai kyau ne wanda ya kara fito da manyan idonta kuma farare tas, sai dai bayan ido da hakora da tafin hannunta da na kafa babu sauran wani gurin da fari ya bayyana a jikinta. Yana daya daga cikin dalilin da ya saka Falmata bata sha'awar saka bakin kaya, domin ganin take ita da tufafin za su saje ne. 

Bayan ta gama shiryawa ta mike tsaye tana cigaba da kallon kanta a madubi kamin ta maida dan karamin madubin a mazauninsa da ke cikin kayan kwaliyarta. 

Tsakar gidan ta fito ta nufi kitchen dinsu ta dauko abinci da ke rufe a langa (Kwano) ta zauna jikin kitchen din ta soma ci tana ta kallon awakin gidan da ke ta aikin kuka suna fada da junansu, sun ɓata turkensu sun masa kacha-kacha kamar ba dazun ta gama gyara shi ba. Can kuma ta maida dubanta gurin mayan shanun da ke daure guda biyu a gafen garken awakin. 


"Idan kin gama ki taso ga surfen masarar nan ki surfa ko tiya daya ne"


Kam ta gama cin abinci Tumba tai mata furucin, a take yanayinta ya canja tai narai narai da ido kamar ta fasa kuka. 


"Umma ba kin ce sai gobe ba?"


"To masu masarar yau suke son abunsu, kuma da safe ai sai dabobi su samu abunda za su ci"


Kalma daya idan ta kara fitowa daga bakinta ta san ba zata sha da dadi daga hannun Tumba ba.

Bata da wani zabi da ya wuce ta gama cin abinci ta taje tai surfen kamar yadda ta umarce ta. A hankali tai ta cin tuwon marar har ta gama ta tashi ta nufi gurin butarda ke gindin ice ta wanke hannunta sannan ta nufi gurin da masarar take ta dauka ta bude turmi ta fara surfawa. Tsakanin fara surfen da sallamar Maman Baby makociyarsu ba zaka iya tantance wanda ya riga wani ba. Tumba da ke tsakar gidan ta amsa sallamar tare da kallon Falmata da sauri. 


"Kina da son wahalar da kai Fulani, ina ke ina surfe da tsakar ranar nan? Dan Allah ki aje har zuwa anjima ko kuma idan Naja ta gama wanki sai ta surfa"


Kallonta kawai Falmata tai ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfen. 


"Aa zan iya"


Sai kuma ta fada kasa-kasa idanuwanta na cika da kwalla, haka take mata a duk lokacin da wani ya shigo gidan ko kuma idan a gaban mahaifinta ne. Kowa a unguwar ya shaidi Tumba akan kaunar da take nunawa Falmata agaban idanuwansu, wani lokacin har da ita ake bada kwacen matar uba wacce ta rike yar kishiya da amana. 


"Oh Tumba ikon Allah, ke dai ba ki kaunar ganin Falmata tana aiki"


Cewar Maman Baby tana dariya. 


"Mahaifiyarta amana ta bar min ita, idan ina ganin tana wata wahalar sai na rika ganin kamar na ci amanar mahaifiyarta"


Daga inda Falmata take tsaye tana surfen ta dago manyan idanuwanta masu kamar madara ta kalli Tumba wacce ta shantake da makociyarta suna fira ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfe idonta tab da kwalla...! 


FADIME POV. 


Katsina State...


Shanun na gaba ita kuma tana biye da su a baya tare da karenta, hannunta rike da yar karamar sandarta ta dukan shanun, tana sanye da tufafin riga da zane na fulani gashin kanta a cinkushe. Sosai hankalinta yake akan ko wace shanuwa da ke gabanta, zuciyarta cike da fargaba da zullumi irin wanda ya saba ziyartar a duk sa'in da ta fita da shanun. Ba ta natsu ba har sai da ta isa da shanun a gurin da ta saba tsayawa da su, sannan ta nemi guri ta zauna saman wani karamin dutse ta zuba musu ido. 

Haka take wuni a cikin tashin hankali da fargaba a duk lokacin da mahaifinta ya tura kiwo, ba tsoron kiwon take ba, ba dan bata saba ba, sai dan fargabar abunda zai samu shanu a duk lokacin da ta fita da su. 

Ba kasafai take zuwa kiwo ta dawo da shanun lafiya ba, wani lokacin a hanyar tafiya wata zata mutu, wani a hanyar dawowa wani sa'in ma har sai ta iso gida.

Tun shanun suna arba'in da uku har sun dawo sauran goma sha bakwai.

   Mikewa tai tsaye tana kallon wata bakar mage mai jajayen indanuwa, wacce ke tsaye saman dutsen da ke gabanta, ba yau ta saba ganin magen ba, kusan kullum idan ta fita kiwo sai ta ganta, tun tana tsorota har ta daina, sai dai su yi ta kallon kallo ita da magen, sai dai a duk lokacin da tai arba da magen sai tsigar jikinta ta tashi, tsakanin ita da magen aka raba mai daukewa wani ido, ba m kamar magen da ke kyakar hakora. 

  Can dai Fadime ta nemi guri ta zauna ta dauke kanta daga kallon magane da take, ta maida hankalinta gurin shanunta. 


WASIN RAU POV. 


As usual, yau ma sai da hasken rana ya fara haska kyakkyawar fuskarsa sannan ya bude idonshi a hankali yana kallon birds din dake saman icen suna rera masa waka kamar yadda suka saba a ko wace safiya. 

Lumshe ido yayi sai kuma murmushi ya biyo baya mafarkin da yai yake kokarin tunawa, jinke hannunsa yai gam yana maida numfashi a hankali tare da dantse hakoransa. 

Kamar an tsikareshi sai kuma yai saurin bude idon yai hanzarin saukowa daga kan icen ya doro kasa, jikinsa ya girgiza har sai da kowace gaɓa ta jikinsa ta motsa. 

Babu riga a jikinsa sai dai hakan be hana shi jin zafi ba, duk kuwa da irin tsananin sanyin da ake kasancewar yanayin safiyar yau a akwai hadari da ya karade ko'ina a sararin samaniya. 

For the first time a yau yaji a kasa yake sha'awar yin busar sarewa abunda be taba ba, a kowace safiya a saman dutse yake yin busarsa mai dadi saurare da kawarda duk wata damuwa. Jingina yai jikin icen ya ciro sarewarsa ya kafa bakinsa ya soma busar cikin kwarewa da shauki, a take duk dajin ya dauka, yanayin haduwar hadarin da kuma busar sarewar, da iskar da ke kadawa sai ya bada wani kalar yanayi na musamman wanda ko wace irin halitta zata so kasancewa a ciki. Sai da yai busar ya gama sannan ya kai hannunsa a gefen walkin da ke jikinsa ya kwance wata yar karamar jakar tsaba ya bude bakinta ya zubo hatsin da ke cikin jakar a hannunsa ya watsawa tsuntsaye a kasa, a take suka sauko kasa suka baibaye gurin suna ta cin tsabar har wasu na hawa kan wasu, kallomsu yake suna cin abinci har sai da idonsa ya gundura da abincinsa sannan ya juya ya kama hanyar shiga cikin burninsu. 

   Safiya ce amman kowa hada hadarsa yake, kai tsaye ya wuce cikin fadarsu, gaba dayan mutane da suke cikin fadar babu mai tufafi kowa walki ne a jikinsu, fuskarsu babu annuri kamar sun yi arba da mutuwa. 

  Kafarsa ya kai kasa dayar kuma ya gurfana da ita ya sirinar da kansa ya gaishe da mahaifinsa. Da mafecin da ke hannunsa ya daga ya dora masa a kai alamar ya amsa gaisuwar sannan ya mike tsaye ya nufi cikin gidan sarautar mai kamar wani karamin burni. 

  Ta wani bangaren ruwan korama ne ke da guduna ga shukoki a gefenta daga can nesa da shukokin kuma wasu manyan itatuwan ayaba ne, idan ka tada kanka ka kalli gabanka kuma ginar kasa ta zakanin da irinnta kaka da kakkanin, wacce aka kawata ta da fatar damisa wani gurin kuma an kawata shi da gashin tsuntsaye kalakala da suke cikin dajin. 

  Masarautar GARUK babban masaurata ce mai karfi tsafi, tun daga kakannin har jikoki su ba su yarda da cigaban zamani ba, a duk inda za su je a duniyar nan sai dai su taka a kasa ko su yi tsafi ko su hau wani abun hawa daga dabbobinsu ya kaisu, fita su bar garin ma abu me mai wahala, ba kasafai yam garin ke nesa da garin ba saboda yanayin rayuwarsu da kuma suturarsu, kamar yadda ganganci ne wanda ba dan garin ba ya kawo ziyara a garin ba tare da sanin wani a garin ba. Yawancin abincin mutanen garin yayan itatuwa ne sai alkama danyar kwakwa. 


ZAINAB HAJIYA KARAMA POV. 


Yola... 


Kadan ta kurba tea da ke gabanta ta aje karamin kofi a hankali sannan ta tattara dukannin hankalinta da natsuwarta ta maida akan laptop din dake gabanta. 

Hotunan da ta dauka jiya take kokarin gyarawa, tunanin yadda zata banbanta su da sauran take, domin a halin yanzu bata da wani buri da tunani da ya wuce ganinta a matakin da kowa be taba kaiwa ba, tana bukatar sabuwar idea. 

Tunani take tana wani tsuke karamin bakinta, tare da dora kafa daya saman daya. Wayarta ta dauko  ta kunna data, ba da niya ba ta shiga whatsapp, da gangan ta duba sakonin da ake aiko mata na dan ta bada amsa ba, ta saba halinta sai ta bude sako ta bar shi a bude ba tare da ta mayar da amsa ba, ji take ta isa da hakan, kuma ra'ayinta ne dole kowa ya bi. 

  Kai tsaye ta nufi status, sai da ta fara duba adadin mutane da suka duba nata status din wanda ta saka sannan ta fara duba na mutane.


“Wow.......”


Ta furta tana kara zooming wani hoto na wani namiji tare da matarsa da yayansa biyu. 


“Amman mijin nan na ki ya hadu fa”


Ta kara duba hoton da kyau da sauran hotunan da suke biye da shi duka na miji wani guri da yaran wani gurin ita da shi wani gurin kuma shi kadai, sai a lokacin ta lura da matar ta goge hoton ma, sai ita a gurinta be gogu ba saboda tana using GB whatsapp.


“Happy anniversary dear zan zo cin cake”


Ta rubuta mata sannan ta shiga wani sashen tai saving hoton. Wata Dattijuwar mace ce ta shigo dakin tana daure da zane kanta kuma ya yafin atamfa kalar zanen da ke jikinta.

  Ganin matar yasa Zainab kara relaxing akan kujerar tana wani lankwafar da kai. 


“Iya..... ”


“Kyakkyawa, kowa yana can yana karyawa ke kina nan”


“Iya inata tunanin abunda zan yi this week na haska duniya, kuma na amsa sunana na photographer, ina da mabiya miliyan uku da rabi a media, ina yan hamayya ya kamata ace na hara kura na daga musu hankali, kin san mu photographers kullum burinmu mu dara kowa”


Ta karasa tana kai kafarta ta tana wata karamar camera dake gabanta da kafartata. Iya ta yi murmushi irin nasu na manya, sannan ta lasa bakinta ta dan daga jajayen idanuwanta kadan tana kallon Zainab tace. 


“Na fada kullum idan kina bukatar wani abun, ki rika kiran yayanki, shawara kike bukata ko wani taimako ki rika fada masa”


“Iya kin san baya son waya mai tsaye ne, kuma baya gari balle na same shi mu yi magana”


“Yana gari be dai shigo gidannan ba”


Da sauri ta tashi zaune tana kallon mummunar fuskar Iya. 


“Ya akai kika sani?”


Iya ta yi dariya. 


“Kina wasa Zainab, sirrin masarautar nan a hannuna yake, sai ki rika abu kamar a nan aka haife ki ba, ni na fada miki Omar yana cikin garin Yola”


“Idan hakan ne, ba shi da amfani tun da baya bukatar shigowa cikin gidan nan....”


“Kira shi ki fada masa dansa Labib, be da lafiya”


“Ba zai jidadi ba idan nai masa karya”


Ta fada tana dan turo baki tare da komawa jikin kujerar ta kwanta. 


“Ni kuma mahaifiyarki sai nace ki yi karya? Da gaske ne dan sa be da Lafiya, bari na dauko miki shi yanzu nan”


Iya na fadar hakan ta juya ta fice daga dakin, sauka tai kasa gaba daya downstairs, ta nufi wani bangare na masarautar, a tsakanin bangaren da ta nufa da kuma wanda ta baro yayi nisa wata karamar unguwa zuwa wata. 

  Da kanta take tafiya hadiman gidan nata aika mata gaisuwa ita ko tana amsa musu baki har kunne, haka take da kowa fatfat kusan ta fi kowa far'a gidan. 

  Sai da ta fakaici idon mutane sannan ta shiga garken dawakai tana tambayar mai gadinsu.


“Yau ka duba su kuwa?”


“Ranki ya dade duba su kuma ai dole ne tunda shine aikina”


Ta yi murmushi.


“Hakan na da kyau bari na duba dokin Babban mutum.... ”


Haka take kullum sai ta fake da sai ita da kanta zata duba dokin ba dan komai ba sai dan ta samu damar shiga ciki, cikin gurin ta shiga tana takawa ahankali tana duba dokuna kamar mai duba lafiyarsu, har ta isa gaban wani farin doki wanda ake kebe can shi kadai aka zagaye shi da katako, bude gurin tai ta shiga, ta kai hannu ta shafa dokin wanda kusan ya saba da ita, sannan ta duka kusa da shi ta fara tonon kasa, wasu abubuwa da fiddo guda uku dane a cikin zare, na tsakiyar ta matsa sai kuma taja zaren da karfi. 

  Daga inda take ta jiyo kukan Labib a kunnuwanta, da kuma maganar Nana wace ta tsorota da yadda yai kyalowa ta nufo shi tana ambaton Allah. Cikin saurin ta mayarda kulolan ta rufe ramen ta nade hannunta cikin zanenta gudun kar a ganshi da kasa sannan ta fito daga gurin. 


SHATTIMA UMAR.... 


YOLA...


Kofin tsamiya ne a hannunsa, dayan hannunsa kuma rike da lemun tsami yana matsawa a karamin kofin, farar singilat ce jikinsa sai farin tawul din da ke daure a ƙugunsa, fafaren kafafuwansa kuma sanye da takalminsa na bedroom. 

Sai da ya gama matsa lemun sannan ya saka tea spoon ya garwaye lemun tsamin da tsamiyar suka hade jikinsu, a take ya daga kansa sama ya hanye, a gurin ya dire kofin ya mike tsaye ya nufi bathroom, he spent more than thirty minutes a bathroom din yana jika kansa da ruwa sannan ya fito rike da wani karamin tawul yana goge kyakkawan jikinsa, gaban madubi ya tsaya yana goge gashin kansa. Fari ne kyakkyawan gaske, irin kyau nan mai daukar hankali, bafulatani gaba da baya amman idan ba sani kai ba sai ka rantse da Allah baasbine ne ko shuwa, ko'ina na jikinsa yana amsa sunansa na namiji kamar yadda muryarsa da siffar zatinsa take haska surarsa. Wani farin mai, mai sanyi ya dauka ya shafa a hannunsa ya murza sannan ya shafa shi a jikinsa, kana ya ware hannayensa yai mika, wacce ta sanarwa dukan jikinsa. 

  Wayarsa da ke kan gado ce tai ringing, sai da ya kwance tawul din jikinsa sannan ya nufi wayar ya dauka. 


“Nana”


“Na'am Labib ba Lafiya yana ta ihu”


“Waya taba shi?”


Ya tambaya sanin cewar daman can ba lafiya ta isheshi ba.


“Babu ina ma dakin, sai kawai na ji yayi kyalowa ya fashe da kuka, jikinsa ma duk yayi zafi”


“Ku kira Doc”


“Ammy ta kira shi”


“Gani nan zuwa”


Ya fada yana sauke wayar daga kunnensa, kiran Nana na sauka na Muhseen ya shigo wayarsa, da murmushi Omar yai picking call din. 


“Shattima kana gurin Ammy? Ko kana Kaduna”


“Ka shigo gari ne?”


“Yeah ina Yola yanzu haka”


“Wow gani zan je fada yanzu”


“Okay mu hadu a can”


Daga haka ya sauke wayar yana murmushi he can't remember when last ya ga Muhseen mutanen Abuja.

  Daukar tawul din yai yaaje shi a muhallinsa sannan ya bude wardrobe ya dauko farin jean and blue t-shirt ya saka, a gagauce ya shirya ya saka agogon hannunsa ya fesa turare ya dauki abubuwan bukatarsa ya fice daga dakin. 

  

“Baba Adamu.... A tashi mota yanzu nn zamu je fada Labib ba lafiya”


Tun kan ya sauko ya fara kwalawa Baba Adamu kira, abunka da mai jira jikin na rawa Baba Adamu ya nufi motar yai mata key sannan ya fito ya budewa Shattima. Tun kan su shiga motar mai gadi ya bude gate Shattima na shiga Baba Adamu ya fisgi motar kamar ba Dattijo ba. 


“Ahaaa haka nake so, a dinga taka mota kamar mu kadai ne a garin nan”


Omar ya fada yana jindadim yadda Baba Adamu ke gudu da motar kamar dominsu kawai akai titi. 


________________________


Did i ever write something about witch? (Mayu) 

Do you remember other family Mama Fulani da suke Yola? The story is about them now 🤗 

*FULANI -it's not free, if you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*

I just published "Free Page -2" of my story "FULANI". https://www.wattpad.com/1104521181?utm_medium=com.fmwhatsapp&utm_source=android&utm_content=share_published



 DOWNLOAD HERE

No comments

Powered by Blogger.