Bakar Inuwa 47


 Chapter 47

47


............So take tabi umarninsa ta buɗe amma ta tabbatar bazata iya kallonsa ba riga ba. Sai tayi kamar zata buɗe sai ta maida ta rumtse da ƙarfin tsiya. Tayi haka kusan 3times amma ta kasa. Cike da mugunta ya saki murmushi yana saka hanunsa guda ya janye nata data tokaresa da shi. 


   Wani irin ƙuuuu! Cikin Raudha ya bada sautin da har Ramadhan sai da yaji lokacin da taji saukar lips nashi akan nata daketa ƙyallin lipsgloss mai ƙamshin strowbarry. Shi kam da yayi da niyyar tsokana duk yanda yaso janye nasa lips ɗin sai yaji bazai iya ba, cikin rashin ƙarfin jikin da ke tare da shi ya sake manneta da mirror ɗin tare da rumtse ɗayan hanunta dake cikin nasa ya manne jikinsu waje guda yanda har numfashinsu ke fita da ƙyar....


     Ya riga ya mata matsewar da rawar jikin nata ma baya tasiri, sai zuciyarta dake mugun gudu a ƙirjinta har yana iya jiyowa. Randa su Anne sukazo yayi kissing nata sai dai ba irin na yau ba. Na yau babu sassauci, kai tsayene, cike da salon daya sata shagala tuni tsoronta ya gudu saƙonsa ya fara shigarta ɓargo da jini. Itama tanada lafiya, duk da abinda takeji sabo ne gangar jikinta bataƙi amsaba, dan ta kai shekarun da zata iya buƙatarsa. Sai dai rashin sabo ya sake tabbatar da ruɗaninta, dan lokacin daya janye bakinsa kasa tsaiwa tai a kan ƙafafunta. Babu shiri ta sake ƙanƙamesa. Bazata iya ɗagowa ta kallesa ba, sannan ƙafafunta ma bazasu iya tsayawa akaran kansu ba, dan jikinta babu abinda yakeyi sai mazari.


    Duka hannayensa biyu ya dafe kan mirror ɗin da suke jingine, kansa na bisa kafaɗarta, idanunsa duka a rufe suke saboda abinda ke faruwa a cikin nasa jikin. Lallai yasan ya takaloma kansa, ya kira ruwa yau. Yana zaman-zamansa da lallaɓa yanayinsa gashi nan ya takaloma kansa ruwa wajen neman tsokanarta ya tsokanoma kansa abinda ke kwance shekara da shekaru.


    Sunayen ALLAH ya shiga ambata a zuciyarsa da son janye jikinsa da sauri, sai dai Raudha data dabaibayesa sam ta hana yuwuwar hakan garesa. Sai ma ƙara ƙanƙamesa tai dan bata fatan ya ganta a yanayin da take. Sake gwada janyewa yay itama ta sake ƙanƙamesa. Dole ta sashi buɗe ido yana kallon kansa da bayanta ta cikin mirror. Murmushi ne ya suɓuce masa, sake duban idanunsa da suka kaɗa sukai jajur yayi alamar fitinace kwance a cikinsu. Hannunsa ɗaya ya ɗaga da jikin miron ya kaisa kanta ya ture hular data saka, a take gashinta dake ɗaure ya bayyana. Yatsunsa ya tura ciki baki ɗaya ribbon ɗin ta fice duka.


   Babu abinda ke fita a bakin Raudha sai kalmar innalillahi.... Har ƙarshe, ga hawayenta na zarya a kan ƙirjinsa. Murmushi ya saki da sake yamutsa gashin nata da yakeji kamar su yini yana wasa da shi. Cikin wata irin shaƙaƙƙiyar murya da bata taɓa cin karon ji da ga garesa ba ya fara magana...


     “Ustaza wannan ba mafita bace, idan kika bari naje matakin ƙarshe sam bazan saurarekiba sai na tabbatar da sadakina bisa kanki yanzun nan harda ribar baby insha ALLAH..”


    Baima kai ƙarshe ba tai saurin sakinsa da son tureshi, sai dai hakan bamai yuwuwa ba, dan duk da halin da yake ciki ai goma tafi biyar albarka. Yanda tai ɗin ya bashi dariya, sai dai halin da yake ciki bana dariyar bane, yayi imani kuma da inhar aka cigaba da kasancewa a haka babu makawa a yanzun nan bazai iya ƙyale yarinyarnan ba, duk da ƙoƙarinsa na son yin hakan. Kaɗan ya matsa ta samu hanya, ai da gudunta ta fita har tana bigewa da ƙofa.... Shima zaune ya kai jagwab saman stool ɗin mirror bayan ya ɗauke book ɗinta dake a wajen. Ya dafe kansa zuciyarsa na matuƙar gudu kamar zata fito... (Mike damunka Ramadhan? Mikaje ka takaloma kanka wajen shegen tsokale-tsokalen neman ayi?) a zuciyarsa yake maganar, sai dai sam babu nadamar abinda yay tattare da shi. Sai ma a fili daya furta ‘Oh Ramadhan ka lalace, da sa'ar autarku kake wannan abun ko kunya babu.’


    Sai kuma murmushi ya suɓuce masa, ya kai hannu a wuyansa, “Ni Ramadhana zazzaɓin ma ya dawo” yay maganar a marairaice yana wani langaɓe kai gefe cike da tausayin kansa.... Tuna abinda ya gani ya sashi saurin juyawa ga mirror ɗin, book ɗinta ya ɗauka ya buɗe, sai kuma ya miƙe yana bin rubutun da kallo. “Kai ina..” ya faɗa a fili yana girgiza kansa da miƙewa riƙe da littafin. Bakin gado ya koma, ya ɗauka ɗaya daga cikin wayoyinsa yay snapping rubutun, littafin ya ajiye ya cigaba da danne-dannensa. Tsahon mintuna biyu ya kai wayar kunensa.


     Daga can cikin tsokana Bappi yace, “Ɗan gatan ALLAH ka warke kenan?”.


   Murmushi yay yana sake ƙoƙarin control ɗin halin da yake ciki. “Oh Bappi nida nake kwance cikin ciwo kake kira ɗan gata?”.


     Dariya Bappi ya karayi daga can. “Ɗan gatane mana tunda ciwon naka na ƴan gatane. Bakaji bahaushe yace _mura ciwon ɗan gata ba_”.


     Dariya sosai shima Ramadhan ya sanya a wannan gaɓar Bappin na tayasa. Sai da suka nutsu Ramadhan ya fara magana serious. “Bappi wani abune ya ɗan rikitani yanzun nan. Amma na turo maka saƙo ta email ka duba yanzu dan mu tabbatar”.


    Bappi ma daya koma serious ɗin yace, “To ALLAH yasa dai lafiya?”.


     “Lafiya lau Bappi duba dai”.




     Bayan kamar mintuna uku sai ga kiran Bappi ya shigo, lokacin yana ƙoƙarin saka kaya a jikinsa. Dakatawa yay ya ɗaga wayar. “Ramadhan ina ka samu wannan hand writing ɗin?”.


    “Iri ɗaya ne ko bappi?”.


Ramadhan ya amsa tambaya da tambaya. Daga can Bappi yace, “Tabbas babu wani babbanci, kenan wanda ya turo takardar nan kamar yanda mukai hasashe yanada kusanci damu?”.


    “Bappi kasan rubutun waye kuwa?”.


   “Shi na ƙagu naji Ramadhan ”.


“Ameenatu!”.


  “Aminatu? Kana nufin Aminatu dai matarka?!”.


    “Ita kuwa Bappi. Yanzu naci karo da shi a book ɗinta na makaranta, shiyyasa gaba ɗaya kaina ya kasa ɗauka nima dan na shiga ruɗani”.


   “Uhhm to kaga wannan maganar bata nan bace ba, idan ka fita office gobe idan ALLAH ya kaimu zanzo kawai”.


    “Bappi na sameka a gida mana anjima”.


  “No Ramadhan akwai haɗari. Satar fitarka tayi yawa, ina tsoron magauta su fara fahimta su cutar da kai ta wannan hanyar. Dolene ka canja takunka”.


  Fuska ya ɓata, dan gaskiya akace bazai dinga zuwa gidansu akai-akaiba an cutar da shi. Wannan takura har ina dan ALLAH.




     ★Hajjaju Raudha kam tunda ta fice tana can ɗaki duƙunƙune a bargo. Ji take kamar ta tona tsakkiyar gidan kawai ta shige ta huta. Bawai bata san minene aure ba, domin tanada zurfi a ilimin addininta, shiko musilinci ya fiddo mana komai dangane da aure cikin hikima da rahamar UBANGIJI. Matsalar kawai shine komai yana zuwa mata baƙo ne. Bata saba ba, bata taɓa gani anayi ba. Bata karatun littafi sai ranar da Bilkisu ta bata, ko karatun tanayine cike da kunyar wasu wajajen idan tazo a lokacin. Gidansu na hutawa ko tv babu, wama yake da lokacin zaman kallo, yo fitinar Abbansu ma tasa idan rashin kuɗi ya ciyosa ya kwashe ya siyar kona wacece a gidan babu ubanda ya isa yace wani abu kuma. Bata da tarkacen ƙawaye, idan ma kika kasance mai rawar kai a aji bata shiga harkarki, sannan bata zaman fira in group daga boko har islamiyya, hasalima faɗa takema su Safara'u idan taga sunayi. Tasan dole ne ta shiga ruɗani da sabon yanayin da Ramadhan ke son jefasu a tsakanin nan. A wani bangaren kuma tanada gaskiyarta akan shiga ruɗani. Tun farko ta sakama ranta Ramadhan yafi ƙarfinta. Shima kansa ya tabbatar mata yafi ƙarfin nata. Mahaifiyarsa da danginsa harma da mutanen duniya sun tabbatar. A baya babu abinda take gani a cikin idanunsa sai saɓanin abinda take gani a yanzun, duk da dai harga ALLAH tasan bai taɓa muzantata da baki ba, bai taɓa hantararta ko wulaƙantata ba, kawai dai baya shiga sabgarta. Dolene canjawarsa a ƙanƙanin lokaci ta zama abu mai rikitarwa a gareta. Amma tayi alƙawarin hakan bazaisa ta taɓa saɓama umarni ko hani daga garesaba, zatai masa biyayya matsayinsa na miji inhar bai hau turbar sabama ALLAH ba. Zata yi biyayya ga umarnin UBANGIJI akan binyayya ga miji da dokokin aure kodan tabbatar da martabar tarbiyyarta data gidansu a idanunsa saɓanin wadda aka sanar masa da wadda duniya take kallon ahalinta dana iyayenta da shi......


   Ƙarar landline ɗin ɗakin ta katse mata tunaninta, gabanta ya faɗi. Sai dai tunanin ko Mama Ladi ne ya sata buɗe kanta a bargon ta ɗaga.


    “Ustazah! Haka aka koya muki kula da mijinne wai a islamiyyar?”.


    Batama san bakinta ya suɓuceba wajen faɗin, “Wlhy Yaya Ramadhan zaka kasheni da raina!”.


    Murmushi yay daga can, “Idan na kasheki Ustazah dawa zanyi angwancin?”.


    “Na shiga uku”.


Dariyar da batasan ya iyaba ya ƙyalƙyale da ita daga can. Tasa hannu ta rufe fuska tamkar tana gabansa. A zuciyarta ɗunbin mamaki da al'ajab ne danƙare. (Dama haka yake kokuwa yanzune ya canja.....?)


   “Ina jiranki kizo ki bani abinci kar yunwa ta hallakani ga ciwo”. Ya faɗa cikin katse mata tunani yana yanke wayar.


     


     Baki buɗe Ramadhan dake zaune cikin kujera ƙafa ɗaya kan ɗaya lap-top a cinyarsa alamar aiki yake ya saki yana kallon Raudha data shigo bayan tayi knocking ya bata izinin shigowa. (Lallai yarinyar nan kanta da motsi) ya ambata a ransa yana ɗauke idonsa gareta. Sanye yake cikin kaya masu taushi baƙaƙe. Duk da badan kwalliya ya saka ba sun masa ƙyau da sake fiddo hasken fatarsa. Idanunsa dake cike da abubuwa kashi-kashi ya janye yana maidawa ga aikin gabansa. 


    Gabansa Raudha ta ƙaraso bayan ta ɗakko basket abincin data shirya masa tun ɗazun, komai a cooler yake dan haka bata tunanin sun huce. Table ɗin ta kalla inda ƙafarsace fara tas a miƙe, ganinta da abincin kuma baisa ya sauke ba. Kallonsa taɗan sata a ranta tana gulmarsa ganin yanda ya tsuke fuska tamkar bashi ya gama mata abun kunya ɗazun ba (Humm da gaske mutumin nan dai yanada aljanu). A fili kam sai cewa tai “Ga abincin”. 


   Banza yay mata kamar baiji ba. Ta sake maimaitawa cikin marairaice fuskarta dake cikin niƙab data sako. Ganin yaƙi nuna yasan da zamanta a wajen sai takai durƙushe a gabansa tana dire basket ɗin a ƙasa. “Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy tsoro naji ɗazu ɗin”.


   Nanma banza yay mata yana cigaba da sarrafa keyboard ɗin lap-top ɗinsa hankali kwance. Sai dai ya fahimci maganar tata nada alaƙa da tunanin gudun datai ɗazun ne.


    “Dan ALLAH!”.


Ta sake faɗa a hankali. Idanunsa da har yanzu jan yaƙi kwaranyewa a cikinsu ya ɗan rumtse, ga mura ga fitina da yaketa ƙoƙarin haɗiyewa taƙi hadiyuwa. Iska ya ɗan furzar dakai hanunsa saman goshi ya shafa, tunda tace ALLAH kuma ta gama da shi. Amma hakan bai hanashi yin magana a daƙile ba.


    “Dan kin rainani ni zakizoma da wannan abun a fuska?!”.


  (Oh ALLAH, dama akan niƙaff ne?) ta faɗa a zuciyarta tana lumshe ido. A fili kam hannayenta ta matse waje guda. Cikin sanyin muryarta dake tsumashi batun yau ba tace, “Dan ALLAH kayi haƙuri ALLAH kunyarka nakeji”.


     (Kunya) ya maimaita kalmar a ransa yana ɗan bubbuga yatsansa bisa lips ɗinsa idonsa a kanta. “Okay! Naji ciresa to, inba hakaba kuma ni bashi zan cire ba, wancan zan cire”.


    Kukane kawai ya ragema Raudha ta fashe da shi. Mutumin nan so yake kawai ya zautar da ita a gidan nan, dan sarai ta fahimci abinda yake nufin zai cire. Babu yanda ta iya dole takai hannu tana kwance niƙaff ɗin sai dai ta rumtse idanunta... Hararta yay ya ɗauke idanunsa dan ya tsani ganin hawayen nan.


    Jin bai tanka ba yasata satar kallonsa sai taga hankalinsa baya gareta. Saurin saka nikab ɗin tai ta goge hawayen. Kafin ta ɗaura basket ɗin saman table ɗin ganin ya sauke ƙafafun nasa. Abincin ta haɗa masa ranta cike da fatan ALLAH yasa ya barta ta koma ɗakinta. Sai dai addu'ar tata bata amsu ba. Dan bayan ya gama shan ƙamshinsa lap-top ɗin ya ajiye gefe tare da nuna mata gefensa fuska a tsuke.


    (Nidai tawa ta ƙare) ta ambata a ranta tana miƙewa tabi umarninsa dan har tafara jin nutsuwa ganin ɗan sake mata da yakeyi kwana biyun nan, sam bazataso su koma ƴar gidan jiya ba. Duk da 2seater ce sai da taɗan takura sakamakon yanayin nasa zaman. Lap-top ɗinsa ya ɗauka ya maida a cinya yana faɗin “Ohya bani, dan hukun cinki kenan yau a gidan nan ciyar dani abinci daga nan har dare”. Ya matso da fuskarsa gab da tata. Cikin raɗa ya ƙarasa faɗin, “Inba hakaba kuma na rantse ni zan c....”


   A zabure ta ɗaura hanunta saman bakinsa ta toshe, tsabar rikicewa harda tallafo ƙeyarsa da ɗayan hanunta”.


    “Ni dai gaskiya-gaskiya to nama fasa abotar a kwance wlhy”.


   Kaɗan ya rage dariya ta kufce masa. amma yay dauriyar dakewa yana bin fuskarta da idanun ke rumtse da bakinta dake maganar da kallo. Ga jikinta sai tsuma yake. Sosai yake jin nishaɗi idan ya ganta a yanayi na tsorata ko kunyarsa. Hanunsa yasa ya janye nata hanun daga bakinsa harda ɗan bugesa.


    “Ustazah yaushe kika koma hakane wai? To ai mai raba wannan abotar sai mutuwa mun ƙulla kenan”.


   “To an taɓa dole ne?”.


Ta faɗa cikin waro idanu tana sake ƙwaɓe fuska. Hancinta ya lakata kaɗan da ɗage gira sama ya kashe mata ido ɗaya. “Abota dani dolene yarinya. Dama kika samu na zaɓeki zakimin iyayi”. Yaƙare maganar da wani salon taɓe baki kamar wani mace. Hakan sai yay bala'in saka Raudha dariyar da batai niyya ba. Sosai murmushin fuskarsa ya ƙara faɗi shima. Sai dai tana gama dariyar ta ɗago da faɗin, “ALLAH yanda kayi sai kace mace. Baba Laran gidanmu haka take idan tana faɗa”.


   Fuska ya tsuke da kwaɓeta yana hararta. “Waye macen?”.


      Dariyar dake yalwace da fuskarta ta sake ƙyalƙyalewa da ita tana kai hannu ta danne bakin. Yayinda shi kuma ya kai hannu ya mangare mata kai ransa cikeda nishaɗi. Ganin taƙi daina dariyar ya sake bata ranƙwashi....


    “Wayyo Mommyna zai ɓararmin da karatu na”.


  (Kan uban nan) ya faɗa a ransa dariya na kufce masa shima. cak ta tsaya da tata dariyar ta zuba masa ido batare data sani ba. Dan wani irin ƙyau dariyar tai masa. haƙoransa duka sun bayyana ba kuma yana yinta a haukace bane...


   “Sharri kika koma kuma Ustazah?”. Ya faɗa da sake kai mata ranƙwashi yana dariyar har sannan sai ta duƙe kan nata ya sauka bisa cinyarsa hularta na zamewa ta faɗi ƙasa. Ƙoƙarin ɗagota ya shigayi amma taƙi yarda. cakulkulo ya fara mata a wuya, cusa kanta take sakeyi tana dariya da ƙoƙarin ture hanunsa. 


   Jinsa yake a wani irin nishaɗi daya jima baiyiba a rayuwarsa. Zai iya rantsuwa tun bayan rasuwar Haseenahr sa da Amnah bai sake farin ciki makamancin hakan ba da yake a kwanakin nan musamman yanzu. Yanda gashinta data ɗaure ke reto ya sashi kama ribbon ɗin ya zare gashin ya tarwatse. Da sauri Raudha ta ɗago dan batama san hulan ya zame kansa ba. Sai kuma kunya ta kamata jin ya tura yatsunsa a ciki. Tai ƙoƙarin matsawa ya riƙeta. Shiru tai tsigar jikinta na tashi, kamar yanda shima yakejin jininsa na haurawa da gudu a kowanne jijiyar jikinsa....


    “Ina son gashin nan sosai”.


Yay maganar yana matso da kansa a kafaɗarta da kamo gashin ya kai hancinsa yana shaƙar ƙamshin haɗaɗɗen turaren *YERWA INCENSE AND MORE...* da yakeyi. Sai kuma ya saka maida yatsun nasa cikin gashin ya tallafo kanta ya ɗaura goshinsa akan nata suna musayar shaƙa da fesawa juna numfashi... Murya a matuƙar shaƙe duk da akwai mura dama tattare da shi ya ce, “Ƙawata!”.


    A yanda ya ambaci kalmar ba ƙaramin tada tsigar jikin Raudha yay ba. Da ƙyar ta iya faɗin. “Uhhyim”.


   “ALLAH yay miki albarka”.


Sosai taji daɗin wannan addu'a tashi da batasan dalilin yinta ba. Muryarta a raunane tace “Amin nagode”.


   Kansa ya ɗan jinjina mata da cigaba da motsa yatsun hanunsa cikin gashin nata. “Ni kuma fa?”.


    _“Kaima ALLAH yay maka rahama da rahamarsa. Ya kareka da kariyarsa. Ya baka ikon sauke hakkin ƴan ƙasa dake bisa wuyanka, ya baka nutsuwar ayyuka da har abada da baza'a manta da kai ba. Ya hanaka cin hakkin kowa koda bai kai girman ƙwayar gero ba”._


    (Ya ALLAH yarinyar nan zata hakalani) ya faɗa a ransa yana mai rungumeta tsam a jikinsa. Wannan shine karo na uku da hakan ta faru tsakaninsu. Amma yau an samu cigaba dan itama tayi luf duk da jikin nata naɗan tsuma kaɗan-kaɗan.


   “Insha ALLAH ke ƴar aljanna ce *_AMEENATU!_*”. 


   Murmushi mai sanyi da yalwa ta saki domin jin furicin nasa. Itama cikin rawar murya tace, “Tare da kai da iyayenmu baki ɗaya”.


   Ɗagota yay daga jikin nasa yana ɗan murmushi. “Uhhm an samu jiki mai daɗi an lafe. Ƙawa kemafa naga kina buƙatar ɗumin mijinki gsky”.


    Hannu tasa ta rufe fuskarta tana murmushi. 


  “Gulmammiya ni bani abincina. Kinzo kinatamin kwarkwasa yana hucewa”.


    “Kai Yaya Ramadhan dan ALLAH”.


“Kam kujimin yarinya da kalan dangi, yaushe na zama Yayanki nikan daga ƙawance kuma? Koda yake kije na yafe miki dai bani abinci cikina ya fara kiran Taura”............✍


No comments

Powered by Blogger.