Abokin Aikina Book 1 Page 5


 LAMBA TA BIYAR.*


Hawayen da suka gangaro mini na share, sannan na miƙe na yi ɗaki domin na yi sallah. Na daɗe kan sallaya ina addu'o'in waraka daga halin da nake ciki. Shigowar yaran ya sa na ɗaga kai ina kallon su, rige-rigen gaishe ni suke yi ina amsawa cikin

sakin fuska, Ummu Salma ta ajiye abincin da ta zubo mini shaƙe da plate. Sai da na yi murmushi sannan na ce "Wannan abinci ina zan kai shi ni kaɗai...?"

    "Ki ci ki ƙoshi Mama. Umma ta ce mu dinga saka ki kina cin abinci mai yawa, kuma mu dinga ba ki haƙuri kada mu bari ki yi kuka".

    Abin da Haidar ya faɗa kenan tare da ɗebo tuwon yana ƙoƙarin kai mini lomar a bakina. Baki na buɗe ya saka mini murmushi ɗauke a kan fuskar shi yana jin daɗi. Ganin hakan ya sa dukansu suka dinga ɗebo tuwon suna ba ni, ban hana su ba kuma ban ƙi karɓa ba. Sai da na fara jin amai sannan na dakatar su. Ruwa Ummu Salma ta kawo mini na Sha, cike da jin daɗi har cikin raina na yi musu godiya kuma na saka musu albarka. 

    Na ba su umurnin canye sauran tuwon sannan na ce da su mu je falo, a can ma tare muka ci ɗan waken kuma sosai na ji daɗin shi a bakina. 


***

Daren ranar na yi bacci sosai kuma na ji sauƙi dangane da ciwon kan da ya addabe ni. Mukhtar kuma bai dawo gidan ba sai sha biyu da rabi, kamar yadda ya saba yin daren shi a waje koyaushe. Ina jin lokacin da yake rufe gida tare da rufewar ɗakin shi, ajiyar zuciya na sauke a raina na ce, 

'Ni kam dai ba ni da bambanci da bazawara. Wai me ya sa wasu mazan suke kasa gane abin da mata suka fi so a wurinsu? Shin ta ya ya mace za ta ji daɗin kyautata wa mijinta bayan shi ba ita ce a gaban shi ba..?'  

Katsar da marata ta yi na yi hanzarin dafe wurin ina faɗin,

 "Wash! Allah!"

Gumi ya fara karyo mini saboda kartar da marar take yi mini, bayan ta dunƙule wuri ɗaya tana zugi. Saboda wani feeling da nake ji wanda nake da tabbacin sha'awa ce ta janyo mini ciwon marar. Na jima cikin halin kafin ta lafa bayan na samar wa kaina waraka, ta hanyar da na saba a duk lokacin da na shiga irin wannan halin. Kuka na fashe da shi cike da ƙyamar abin da nake yi, wanda nake jin takaicin abin a raina amma kuma na kasa dainawa.

        Saboda ganin ba ni da wata mafita mai sauƙi idan ba ta wannan hanyar ba. Duk da na san hakan laifi ne kuma illa ne gare ni ga lafiyata, amma na zaɓi bai wa kaina natsuwa ta wannan hanyar domin ba zan iya aikata zina ba, haka ma ba zan iya zuwa wurin Mukhtar ba. Sanin ko na je babu abin da zai iya tsinana mini balle ya warkar mini da ciwon, illa ya ƙara mini damuwa da takaicin da zan kwana ina tsaki tare da jin haushin kaina. Ban bari na kwana da najasa ba, na tashi na yi wankan tsarki sannan na dawo na kwanta raina a cunkushe kamar ko yaushe. Amma na yi bacci mai daɗi saboda samun natsuwar da na yi ta hanyar gamsar da kaina.


    Tun da safe na miƙe na taimaka wa Ummu Salma suka shirya cikin kayansu na makaranta, sannan suka karya agurguje suka nufi ɗakin shi ya ba su kuɗin tara da na abin hawa. 

     Daga nan inda nake ina jiyo sautin shi yana yi musu faɗa.  "Ni fa wallahi ban da kuɗin da zan ba ku yau. Don ko wurin aiki ba zan je balle na ba ku kuɗin tara, karɓi ɗari ku yi maneji da ita idan za a kai ku hakan.."

   Suka fito fuskokinsu a haɗe suka yi mini tsaye, cikin ƙunar rai na miƙe na ɗauko musu kuɗin tara sannan na ƙara musu kuɗin da zai kai su ya dawo da su. Don daman can kuɗin zuwa kawai yake ba su idan an tashi su dawo ƙasa. Sannan na ja kunnuwansu sosai a kan kada su je ko'ina idan sun dawo ba ba nan, matuƙar ba lokacin islamiya ya yi ba su tafi. Saboda asibitin da zan je ganin likita, kuma ban san lokacin da zan dawo ba.  

    Na raka su har ƙofar gida suka tafi suna ɗaga mini hannu sannan na dawo na nufi ɗakina rai a ɓace. Saboda matuƙar haushin da na shiga dangane da riƙon sakainar kashin da yake yi muna ni da yarana. Wanda hakan ya ƙara saka mini haƙuri da juriya a kan zaman da Umma take so na yi ko don yarana. Domin Mukhtar ko dabba aka bar masa tsaro sai ta mutu bai san ta mutu ba, saboda rashin kula da ko-in-kula irin na shi ta kowane ɓangare. Haƙƙin kan shi ma bai sauke ba balle haƙƙin waɗanda ke tare da shi.


    A gurguje na shirya ba tare da na sake bi ta kan shi ba na fice abina. Kai-tsaye gidan Firdausi na nufa, domin ta raka ni asibitin saboda babu waya a hannuna balle na kira ta. 

       Da murna ta tarye ni muka yi ɗakinta cike da jin daɗin ganin juna, zama na yi a kan gadonta ina faɗin "Wash!" Saboda tafiyar da na yi gabaɗaya jikina ciwo yake yi, domin har lokacin ba na jin ƙarfin jikina. 

    Bayan mun gaisa na sanar da ita abin da ya kawo ni wurinta, shiru ta yi na ɗan lokaci sannan ta ce "Bari na faɗa wa Baban su Mujahida tun kafin ya fita". 

     Da sauri ta fice na bi bayanta da kallo cike da burgewa, saboda suna zaman lafiya sosai ita da maigidanta da yaransu cikin farinciki. Tagumi na yi ina zancen zuci, 

'Ke kam kin yi sa'ar aure, ba irina ba da na rako matan auren duniya'.

     Har raina idan na ga mace da mijinta suna ƙaunar junansu, burge ni suke yi matuƙa gaya. Saboda ni ban ƙaradda komai a cikin aure ba face wahala da tsunduma kai a cikin masifa. Bayan zubewar ƙimar da mijin ya yi mini a idon mutane, tare da janyo mini zagin da ban ji ban gani ba...


    "Yawwa! Ya ce mu je amma fa wallahi ya yi faɗa..."

     "Faɗan me?" Ita ce tambayar da na jefo mata saboda faɗuwar da gabana ya yi babu shiri. 

   "Ya ce ina mijinki da ba zai kai ki asibitin ba sai ni zan kai ki?" 

     Ajiyar zuciya na sauke tare da yin tagumi nan take na ji wani ɗaci ya ziyarci maƙoshina. Cikin sanyin muryar da ke gaf da kuka na ce "Idan kin ga zan takura kawai na tafi ni kaɗai..."

    "Ba fa hana ni ya yi ba, kawai dai haushi abin ya ba shi a ce ni zan raka ki asibiti bayan mijinki ne ya dace ya ɗauki alhakin hakan. Bari na shirya mu je kada mu yi latti da yawa mu tarad da jira" 


     Bayan ta shirya muka fito gidan, abin hawa muka samu muka hau. Muna tafe ina yi mata bitar yadda muka yi da shi a kan zuwa Asibitin. Girgiza kai kawai ta yi cike da takaici ta ce "Ni na rasa wane irin mutum ne Mukhtar! Shi kullum idan bai janyo abin magana ba ba ya jin daɗi. Tsakani da Allah kwata-kwata ba ya kyautawa, domin ita lafiya gaba take da komai".  Shiru kawai na yi ban ce komai ba, saboda tsabar ɓacin ran da na shiga.


    Ko da muka je Asibitin mun taradda jira muka bi sahun masu bin layi. Muna ta hirar matsalolin ma'aurata ni da Firdausi har layin ya kawo kaina, na shiga ofishin likitan cikin sanyin jiki na zauna kujerar da ke gaban shi. Bayani na fara yi masa bayanin abin da nake ji, shiru ya yi mini na ɗan lokaci yana rubuce-rubuce sannan ya ɗago kai yana ƙare mini kallo ya ce 

"Kina da aure?" 

Na ce masa "I" 

Ya sake yin rubutu jikin wata takarda sannan ya miƙo mini ya ce 

"Je ki a yi miki awon, idan aka gama ki kawo mini result". 

    Na miƙe cikin hanzari na fice, wanda nake ji a jikina kallona yake yi ta bayana. Takardar na miƙa wa Firdausi muka nufi ɓangaren da za a yi mini awon. A nan ma jira muka yi har layi ya kawo kanmu, tare da ita muka shiga. Aka ɗibi jinina da fitsari sannan muka dawo muna jiran sakamako. Mintuna a tsakani aka kira ni na karɓi takardar gwajin muka koma wurin Likitan. Na miƙa masa takardar ya duba tsawon minti biyu sannan ya kalle ni ya ce,

 "Kina da ulcer, kuma sannan kina fama da matsananciyar sha'awa a jikinki. Ki yi ƙoƙarin shawo kan matsalar tun kafin ta yi ƙarfi".  

   Kunya ta rufe ni na haɗe fuska ban ce komai ba. Takardar ya miƙo mini ta magungunan da zan saya sannan ya raka ni da addu'ar samun lafiya, na fito offishin cikin sauri saboda kunyar da ta yi mini lulluɓi. 


    Ban sanar da Firdausi zancen ba, amma na yi mata bayanin ulcer da aka ce ina ɗauke da ita. Chemist ɗin da ke bakin Asibitin Firdausi ta sa muka je, magungunan aka duba mana sannan aka saka leda bayan an yi total. Kuɗin da ke hannuna ba su isa ba sai da ta cika mini, sannan na karɓi maganin muka tafi.  


Abin hawa muka fara nema a bakin titi, kamar an ce na kalli gefena. Sai ga MD da gudu zai wuce ta gabanmu karaf idanuwana suka sauka cikin na shi. Gabana ya ƙire ya faɗi saboda tozalin da na yi da shi ya tuna mini ɓarnar da Mukhtar ya yi masa. Nan take na shiga sunkuyar da kai har ya dawo ya tsaya gabanmu, cikin fara'a yake tambayar inda za mu je. Firdausi ce kawai ta amsa masa da cewa, "Gida za mu je..?" 

Gaishe shi na shiga yi cike da jin nauyin shi a idona, buɗe motar ya yi ya fito idanuwan shi a kaina yana faɗin 

"Ya jikin naki?" 

Kaina a duƙe na ce "Da sauƙi".

"Allah ya ƙara lafiya"

"Amin" Firdausi ta amsa, ni dai kaina a duƙe zuciyata cike da son ba shi haƙuri dangane da abin da ya faru. Motar shi ya koma ya fito da wata leda a hannun shi ya miƙo mini yana faɗin

"Ga wayarki nan da na manta ban ba ki ba ranar. Tsoron wata rigimar ya hana na bai wa kowa ya kai miki gida. Sannan ki yi haƙuri dangane da abin da na janyo miki ranar, ban san hakan zai faru ba da ban je ba..." 

"Babu komai ni ce ya dace na ba ka haƙuri..." Maganar da na yi kenan cikin sanyin jiki, kafin ya katse ni da faɗin,

"No! Kada ki damu. Allah ya ƙara lafiya".


Yana ƙare faɗar hakan ya shige motar shi ya wuce, ajiyar zuciya na sauke sannan na ce da Firdausi. "MD yana da kirki wallahi. Kuma ko a offis ba ya shiga shirgin mata, shi ya sa ban ji daɗin abin da Mukhtar ya yi masa ba..." 

"Allah dai ya kyauta! Amma zargi ba zai bar Mukhtar zama lafiya da ke ba, matuƙar bai sauya hali ba". 


    Abin hawa muka samu, bayan mun miƙa tafiya na buɗe ledar da MD ya ba ni da zummar ciro wayata, kawai sai ga sabon kwalin waya na hango. Baki buɗe na yi hanzarin faɗin,

 "Na shige su!"

Firdausi ma ta kai kallonta ga kwalin wayar tana faɗin "Sabuwa ce!" 

Cikin sauri na fito da wayar a kwalinta har wani sheƙi take yi, sai kuma ga asalin wayata ƙasan kwalin na gani. Jikina ya hau rawa cike da tsoron abin da zai je ya dawo, saboda har ga Allah na gaji da tashin hankali. Musamman irin wanda zai janyo rikicin da za a ji tsakanina da Mukhtar, sannan ba na son zargin da yake jifa ta da shi a banza mutane suna zagi na. 


 "Damuwar mi za ki yi a kan abin da ba ki roƙa ba?" Firdausi ta jefo mini tambayar ganin yanayina ya sauya a lokaci ɗaya.

   "Halin Mukhtar na sani, a kan wayar nan zai iya janyo mini zagin mutane da ɓacin ran Umma". Na ƙare maganar kamar wata doluwa. 

   "To ke faɗa masa za ki yi yadda aka yi kika same ta kenan? To bari ki ji, na rantse da Allah muddin ba ki taimaki kanki da kanki ba babu wanda zai ƙwatar miki 'yancinki wurin Mukhtar. Ban ce kada ki mayar wa MD wayar shi ba idan hankalinki bai kwanta ba, amma ki daina ba da ƙofar da zai dinga ɓata miki suna a banza. Haka kawai don shi laifi yana tudu sai ya dinga tsallake na shi yana hango naki domin ya baza wa a faifai yana rabar wa mutane!?"  

Ta ƙare maganar cikin ɗaga murya cike da jin haushi. Shiru kawai na yi ina nazarin maganganunta, cikin sanyin murya na ce,     

      "Zan mayar masa da wayar shi gaskiya. Saboda ba na son zargin Mukhtar ya tabbata a kanmu..."


No comments

Powered by Blogger.