Abokin Aikina Book 1 Page 33

 


TALATIN DA UKU.*


        Tambayar da na yi wa kaina kenan a zuciya, sannan na yi tattaki a hankali har na isa inda take. Sunanta na fara kira domin alamu ya nuna mini ƙarara bacci take yi

sharkaf!

       Ba ta motsa ba har sai da na duƙa na bugi hannunta tare faɗin, "Barira!" 

      Ta miƙe firgigit tana waige-waige tare da faɗin, "Don Allah Romiyo ka buɗe mini ƙofar"


       "Lafiya kike kuwa?"


       Na faɗi maganar cike da jin haushin banzancin da take ƙoƙarin yi wa kanta. Kallo ta bi ni da shi sannan ta yi hanzarin miƙewa tana gyara zaman rigar barcin da ke jikinta. Soshe-soshen kai ta fara yi tana mayar da hularta bisa kai, ta nufi hanyar ɗakinta ranta a haɗe cikin maƙoshi ta ce da ni,

 

     "Lafiya lau!"


     Bayanta na bi da kallo har ta shige ɗakinta ta rufe, murmushi na yi tare da girgiza kaina ina maimata sunan Romiyon a raina, wanda ta raɗa wa Mukhtar ba tare da ta san bai cancanta da sunan ba. Domin bai san komai a kan soyayya ba balle abin da ta ƙumsa, saboda iya sanin da na yi a rayuwar zamana da shi; ko kiss irin na haɗuwar leɓe da leɓe bai taɓa haɗa ni da shi ba. 

      Kitchen na koma ina ta hada-hadar ɗora mana abin kari. Zuciyata cike da tunanin rashin kawaici irin na Barira, da rashin sanin darajar Mukhtar balle ya sauke haƙƙoƙan da ke kansa.

      Kasancewar muna da sauran kayan tea na soya mana Irish da ƙwai. Ina ƙoƙarin fitowa daga Kitchen ɗin hannuna ɗauke da cups da flack's, na ji sautin muryar Barira a sama tana masifa.

        "Na rantse da Allah sai ka san ni ka wulaƙanta. Babu wata magana da za ka faɗa mini yanzu na yarda, saboda ni ma ba ka ji kalolin kiran da na yi maka ba amma ka ƙi buɗe mini ƙofa."

       Abin da na ji kenan bayan na fito daga Kitchen ɗin, saman carpet ɗin tsakiyar kujeruna na ajiye kayan sannan na ƙwala wa su Ummu Salma kira. Duk da ina jin sautin Mukhtar ƙasa-ƙasa yana magana amma ban ji me yake cewa ba.

        Fitowar su Ummu Salma ta yi daidai da fitowar Barira a fusace ta nufi kitchen. Mukhtar ya bi ta yana kiran sunanta cikin ƙaramar murya kafin ya rufe ƙofar.


      Baki a sake yaran suke bin ƙofar kitchen da kallo, karantar da na yi wa fuskokinsu na gano mamakin da suke yi. Murmushi na yi mai sauti na miƙe daga durƙushen da nake ina faɗin,


      "Ku bari na kawo muku madarar" 


      Kitchen ɗin na nufa na tura ƙofar, cikin sa'a bai rufe da makulli ba. Kai-tsaye na nufi kular da na saka soyayyen Irish ɗin, duk da na tarar da kular a buɗe Barira tsaye tana ci a cikin plate ɗin da ta shaƙe  taf! Ba tare da ta jira na ba ta ba, ko kuma ta tuna da cewa akwai wasu masu haƙƙi da shi a cikin gidan bayan ita. 

     Sai girgiza ƙafafuwa take yi tana cin abinta shi kuma yana faman yi mata magiya. Na so na yi magana, sai na ga duk abin da zan faɗa a lokacin zai janyo wani sabon tashin hankali a tsakanina da ita.

     Kular kawai na ɗauke sannan na ja biredi, wanda shi ma ta fasa ledar ta bar shi a buɗe, na fice ba tare da na ce da su komai. Raina a ɓace na dire kular na koma na ɗauko tire na kasa musu kowa ya ɗauki na shi. 

      Zuciyata a ƙuntace saboda mummunan ganin da na yi musu a kitchen ɗin. Sai da yaran suka cinye sannan na ce da su, 

       "Oya ku tashi ku je islamiyya kada ku yi latti"

      Suka ɗauko jakunkunansu suka wuce, na bi su da addu'ar a dowa lafiya sannan na karya. Na kasa tashi daga wurin na baje saman 3seater tare da rufe idona kamar mai barci, sai hotonsu nake gani a lokacin da suke shagalinsu.


       "Ina nawa breakfast?" 


     Zancen Mukhtar da na ji kenan cikin tsakiyar kwanyata, ban motsa ba kamar yadda ban yi niyyar amsa masa ba.


       "Da ke fa nake magana!"


     Ya sake maimaitawa a fusace cikin ɗaga murya, gyara kwanciyata na yi ba tare da na ce ƙanzil ba.

      "Ni za ki wulaƙanta ina yi miki magana kina sharewa?" 


      "Wane breakfast zan ba ka bayan wanda ka yi a kitchen?"


       "Haƙƙina ne aka ba ni a can, wannan kuma shi kike da haƙƙin bayarwa" 


      Wani ɓacin rai ya taso mini, nan take ya yi mini lulluɓin da ya rufe mini idon gani, domin ban san lokacin da na diro daga kan kujerar ba ina faɗin,

        "An canye haƙƙin ko kana da abin da za ka yi ne idan an hana ka!?"

      "Kwantas Hajiya! Ai kuma yanzu babu kare bin damo! Ki yi yadda kike so ni ma na yi nawa."

     Yana ƙare faɗar hakan Barira ta fito daga kitchen ɗin sum-sum tamkar munafuka ta shige ɗakinta. Harara na wurga masa saboda kallon da ya bi ta da shi yana 'yar dariya. Na danna masa wani kafurin tsaki har sai da na dantse naman ƙasan leɓena. Sannan na bar wurin ina ƙoƙarin shigewa ɗakina ya ce,


     "Sai haƙuri kuma, ni kam na samu inda aka san muhimmancina."


     Baya na dawo saboda ganin idan na yi masa banza bai san kawaici ba,

      "Bari na faɗa maka zancen da ba ya tashi! Wallahi daga wannan karin safiyar; ba zan sake yi mata girki ba. Tun da ta san muhimmancinka ta girka ta ba ka ka ci kai da yaranka."

 

       "Hahahahahh!"


    Sautin dariyar da ya yi kenan har da buga ƙafa ƙasa, sannan ya yage baki yana ƙwala mata kira cikin ɗaga murya.


      "Barcy!!!"


     "Na'am Romiyo!"


Barira ta fito daga ɗakinta cikin sauri ta iso wurinsa da gudu, towel ɗaure a faƙon ƙirjinta da babu tudun komai face na fatar da ke jikinta. 

      

     "Ki shirya yi mana girkin rana ni da yarana. Zan aiko miki da kayan cefane idan an dafa a zuba wa Uwargida nata."


     Tana fari da ido ta ce, "Haba Aunty! Me ya yi zafi ne haka tsakaninki da Romiyo?"


    Baki a sake na dinga kallonsu ɗaya bayan ɗaya, maimakon na ji raina ya ci gaba da suya; sai na ji wata dariya ta suɓuce mini ban shirya ba. Sannan na gyara tsayuwata na ce da ita,


     "To ke Barcy ina ke ina sanin sirrin mata da mijinta? Yana da kyau ki tsaya inda kike da iko da inda ya ajiye ki, ki daina ƙoƙarin shiga hurumin da ba naki ba har sai an kasa da ke. Girki dai ne ya ce ki shirya yi mana saboda yana so na huta da aikin da na sha haka nan, domin tun da aka fara shagalin bikin aurenku ban zauna ba, kullum ina tsaye tamkar haƙori. Don haka idan kin gama ki zuba mana namu a kula ni da yaransa, kamar yadda ya faɗa miki."


     Ina ƙare maganar na juya ba tare da na damu da kallon tuhumar da take aika masa ba. Na je ƙofar ɗakina na ja na tsaya rungume da hannuwa a ƙirji ina musmushin mugunta.


       "Wallahi ba haka muka yi da ita ba Allah ma ya sani."

 

     Maganar da ya yi kenan  yana ɗaga manunansa duka biyu a ƙoƙarin son ta yarda da zancen shi.

       "Daina rantsuwa zan yi girkin kamar yadda ka saka ni, amma wallahi sai ka biya duk wata wahalar da na sha yau." 


    Ɗakinta ta nufa karaf ta dantse ƙofar, ya fara aiko mini da harara yana nuna ni da hannu yana cewa, 

      "Ko shaiɗan sai ya shafa miki lafiya a wurin ibilisanci. Don haka ki je kawai akwai Allah!"


    Dariya na fashe da ita sannan na yi masa gwalo, ƙwafa kawai ya yi sannan ya tsaya bakin ƙofarta yana faɗin,


      "Ki yarda da ni Barcy! Wallahi ba haka muka yi da ita ba."


     ****

  Tun da na shige ɗaki ban sake fitowa ba, sai da su Ummu Salma suka dawo na ce su je su yi wanke-wanke. Bayan na yi wanka na haye gado ina ta faman chatting da na gaji na koma kallo har bacci mai ƙarfi ya yi awon gaba da ni.

     Ƙarfe uku lis na fito ɗakin, saboda hayaniyar faɗan da yaran suke yi. Kokawa sosai suke suna dambacewa tsakanin Haidar da Iman, Ummu Salma tana raba su Haidar bai bari. Ganin Barira a kan kujerarta zaune tana latsar waya ko a jikinta; hakan ya sa na ji raina ya ɓace.


     Fakar Haidar na yi cikin fushi na fara yi masa faɗa sannan na dawo kan Iman. Ummu Salma ce ta fara yi mini bayanin abin da ya haɗa su faɗan.

      "Wai don ba a ba mu abinci muka ci ba, shi ne ya ce dole sai ya je ya ɗauko. Kuma amarya ba ta ce mu ɗauko ba, ta ce mu jira har Abbanmu ya dawo shi ya ce zai ba mu."

      "Ban gane ba! An gama abincin shi ne ba za a ba ku ba sai ya dawo ya ba ku?"


   Ummu Salma ta ɗaga kai alamun tabbatarwa, 

       "To ai shi ne zan je na ɗauko mana mu ci Iman tana riƙe ni. Ni Ko da na gaji haushi na dinga kai mata duka, daga nan muka fara kokawa."

      Kitchen kawai na nufa ba tare da na ce da su komai ba balle Barirar, kulolin da na gani ajiye na fara buɗewa. Shinkafa da miya na gani a cikin kuloli biyu, ban tsaya neman bayani a kansu ba na ɗauki wadda ta fi girma na fice.

     Ina tsaka da zuba musu abincin na ji muryar ta a saman kaina tana faɗin,


      "Kan ubancan! Abincin Romiyo kike zuba musu?" 


       Ban fasa juye musu abincin a tire ba, na bi abincin da miya tare da zuƙa-zuƙan namun da na gani duk na juye musu. Ina ƙoƙarin tura musu gabansu ta fara faɗin,

      "Gaskiya Aunty wallahi ba ki kyauta mini ba! Saboda Allah yaushe zan yi wa mijina girki ki zube wa yara su cinye?"


     "Abincin daga gidanku kika zo da shi ne? Ina ga ai har yanzu ba a kawo miki kayan garar da ake kai wa kowace amarya ba. Ki jira idan aka kawo ki yi iko da abin ki, amma wannan ba ki da halin hana wa yara abincinsu. Domin ubansu ya sayi shinkafar kuma shi ya yi cefanen da aka yi gurkin." 

          "Haka ma za ki ce?"


"E, haka na ce!" 


     Kuka ta fashe da shi wiwi tamkar wadda aka daka, saboda sallamar da Mukhtar ya yi tun kafin ya shigo falon. Wurinsa ta yi da gudu ta faɗa jikinsa tana rera sani sabon kukan, a ruɗe ya fara tambayar,


      "Lafiya? Me aka yi mata?" 

     

    Kallo ma bai ishe ni ba, na zauna ina faɗin su yi sauri su gama su tafi. Isowa ya yi wurinmu tare da ita a jikinsa yana faɗin,


    "Wai me yake faruwa ne!?"


      Mere na yi musu daga shi har ita, sannan na ci gaba da bai wa su Ummu Salma umurnin su yi sauri su gama su tafi.

      "Wai fa abincinka ne ta ɗauko ta zube wa yaran, bayan kuma sun ci abincin tun lokacin da na gama girkin."


     Kallo na kawai ya dinga yi fuskarsa a haɗe sannan ya ce, 

     "Wai ke don Allah har abada ba za ki bari a zauna lafiya ba? Yanzu wannan abin da kika yi miye ribar shi?"


     "Daga kai har ita ban da lokacinku! Don haka idan ta gama shirya maka zance ka haye, to ka zuba mini fetur ka ƙone mu duka mu kama da wuta daga ni har yaran."


      Wata zabura ya yi tare ƙoƙarin kai mini duka, ta yi hanzarin riƙe shi tana faɗin,

      "Don Allah Romiyo ka ƙyale ta a bar ta da halinta. Idan ma sun ci ai 'ya'yanka ne ba na kowa ba. Mu je na ba ka wanda ta bar mana ai gobe ma rana ce!" 


     "Da ba ki hana shi ba! Tun da ba ki ji kunyar yin ƙaryar da za ki haɗa ni da shi ba. Na rantse da Allah duk ranar da ka yi gangancin taɓa jikina da sunan duka sai na illata ka. Ke kuma baƙar Munafuka annamimiya sai kin gwammace ba ki san shi ba a faɗin duniya, don sai kin yi kukan da ko uwarki ta mutu iyaka kenan. A dai juri zuwa rafi watarana tulun zai fashe."


     Ba su ce da ni komai ba, ta ja shi suka shige kitchen na ce da su Ummu su tashi su je tun da sun ƙare.

      Na zauna ina ta huci tare da girgizar ƙafafuwa, saboda na zo wuya komai zan iya aikatawa a lokacin. Su Ummu Salma suka fice gidan tamkar ƙwai ya fashe musu a ciki, su kuma tsuntsayen soyayya suka fito aka baje tsakiyar kujerunta. Shwagaɓa ta dingà yi masa tana ba shi abinci a baki suna hira ƙasa-ƙasa, idan abin ya yi musu daɗi su fashe da dariya.

    Komawa ɗaki na yi na ɗauko wayata na kwanta, na fara waya tamkar gaske cikin kashe murya ina faɗin,

      "Haba dai ai kai ma ka san bayan kai babu wani a faɗin duniya. Daina zancen wannan lusarin, wanda bai ajiye komai ba face masifa da hargowa tamkar zai cinye mutum da ransa."


    Shiru na yi kamar yadda su ma suka yi tsit tamkar ba su cikin falon, dariya na yi mai sauti sannan na ce,

     "Cabɗijam! Ai ka yi shiru kawai abin ba a cewa komai. Fankam-fankam ai ba ya kilishi, ita ma kwana biyu za a jone mu bi sahu. Ai na rantse da Allah da ta san kowane ne ba za ta yi gangancin raɓarsa ba. Saboda muddin ya ƙyalla ido ya hango wata ƙawarta sai ta sha mamakin abin da zai aikata mata. Yo nawa aka yi wai an yi wa ɓarawo kashedin sata?" 


       Wayar na ji an fisge ba tare da na ji lokacin da aka zo a kusa da ni ba. Da sauri na miƙe fuskata a haɗe na ce da shi,


     "Ban wayata!"


     "Sai kin faɗa mini da uban wa kike waya? Kuma wane ɗan iska ne ya kira ki?"


     Raina fes ba tare da shayin komai ba na ce da shi,    

       "Da uban da ke so na yana dakon aure na! Sannan da ɗan iskan da ka ajiye mini ina lalata da shi a waje."


Kallona ya dinga yi bakinsa yana rawa, na yi 'yar dariya sannan na ce,

      To ba ni wayar tun da na amsa tambayar ranka shi daɗe! Romiyo mijin Barcy!"







Kai jama'a🤭Ni dai babu luwana yasin🏃🏻‍♀️



No comments

Powered by Blogger.