Abokin Aikina Book 1 Page 31

 


*TALATIN DA ƊAYA.*


       "Innalillahi Sajida! Lamarinki da girma fa! Shi kenan kin saka wa yarinya ido komai nata kin kushe."

       Zancen da na yi kenan ina ƙoƙarin danne dariyata, saboda iskancin Sajida a kan amaryar Mukhtar ya shalle tunanina. 

        "Tsakani da Allah ni ma dai na raina ganin ta! Sai ka ce wanda ya hango ta idonsa rufe?" Amina ta ƙare maganar tare da tagumi, bayan jimamin da ya bayyana kan fuskarta a zahiri.

      "Hmmmmm! Ni gaskiyar ma ta yi mini yawa walla..." 

      Kiran da ya shigo wayar Firdausi ya datse sauran maganar da ke ƙoƙarin fitowa daga bakinta.


 "Yawwa! Bari na fito!"


     Abin da ta faɗa kenan ta miƙe tare da saɓa jakarta a kafaɗa ta ce da mu, "To ni zan wuce, sai gobe kuma idan mun dawo tarbar amarya." Sallama su Amina suka yi mata ta fice, na raka ta har bakin ƙofa. Zuciyata a cunkushe na ce da ita,

      "Wai kin san Mukhtar bai ba ni komai na faɗar kishiya ba?"

       "Cabɗijam! Hmm! Ki zura masa ido kawai, don babu inda cin amana take zuwa wallahi! Ko an yi gaba sai haƙƙi ya dawo da mutum baya. Idan ban da ya rasa mafaɗi; wannan ƙazamar yarinya me zai yi da ita?"

      Shiru kawai na yi saboda hawaye masu zafin da suke malala a kan fuskata. "Ki daina damar da kanki a kan Mukhtar! Na sha faɗa miki tun ba yau ba, saboda kuka bai da amfani a wurin da ba za a share maka hawaye ba. Da yardar Allah sai haƙƙinki ya fita a kan wannan auren takaicin da ya ɗebo wa kansa. Dauriyar da kike yi ki ƙara ƙaimi, domin salon takun kisa da mummuƙe ne daga kan shi har amaryar da danginsa duka. Marsiyatan banza azzalumai, marasa tsoron Allah..."

      Odar da maigidanta yake yi ya sa ta fice da sauri fuskarta a haɗe cikin ƙololuwar ɓacin rai. Domin tana matuƙar jin haushin halayen Mukhtar da matsin lambar da Umma take yi mini a kansa. 

     Abin da na sani ne, da ace tana da iko; da tuni ta raba aurena da Mukhtar. Saboda ƙawata ce da ba na ɓoye mata komai nawa, wani lokaci ma idan ta zo gidan tana gani da idonta. A wasu lokutan baya da suka shuɗe ma; ita ce ƙashin bayan ɗauke kwatar lalurorin da Mukhtar ya bar ni da su a cikin gidansa.


      Sai da motarsu ta tashi sannan na koma cikin gidan bayan na daidaita natsuwata. Shiga ta ɗakin ke da wuya Amina ta miƙe tana faɗin, "Ni ma zan tafi, ga shi can a ƙofar gida ya zo!"

      Ita ma na raka ta tare da yi mata godiyar karamcin da ta yi mini. Na dawo muka dasa wata sabuwar hira da Sajida, inda take nuna zallar takaicinta a kan auren Mukhtar. Na dinga nuna mata komai nufi ne na Allah kuma babu wanda ya isa ya kauce wa ƙaddarar shi.


    Bayan kowa ya yi bacci tsakanin Sajida da su Haidar, na yi shiru ina nazarin makomata ta gaba idan rayuwa ta ci gaba da shura mini a haka. Ƙarar shigowar saƙo ya sa na janyo wayata na duba, alert na yi tozali da shi wanda ya sa babu shiri na tashi zaune. 

       Dubu talatin na gani ɗauke da sunan MD na asali ALIYU S. NOMA, a matsayin wanda ya turo mini da kuɗin. Shiru na yi ina nazarin waɗanni irin kuɗi ne ya turo mini, saboda ban san wata ajandar da muka yi da shi ba, wadda kuɗin za su zo mini da yawa haka.

       Ga shi dare ya yi ƙarfe ɗaya saura balle na nemo shi na ji kuɗin na mene ne. Shigowar wani saƙon ya sa na rarumi wayar da sauri na duba, babu shiri jikina ya yi sanyi ƙalau, saboda wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyata.


     'Ga tawa gudunmawa nan, Allah ya ba ku zaman lafiya'

   

     Abin da na yi ta maimaitawa a zuciyata kenan, kuma na kasa ɗauke idanuwana a kan saƙon. Juya kwanciyata kawai na yi saboda ban san da wace kalma zan yi masa godiya ba.

     Duk da har lokacin ban daina jin haushinsa a raina ba. Haka na yi kwanan daɗi da tunanin abin da zan yi da kuɗin idan safiya ta waye.


****

    Da safe danginsa suka cika gidan ana ta hada-hadar dafa abincin bikin. Duk da na ji zafin rashin saka ni cikin hidimarsa, amma haka na danne zuciyata saboda ba na so a ga kasawa ta.

       Sai dai ko kaɗan ban saka hannuna a cikin aikin ba. Abinci ma nawa na sa aka girka mini a gidan Maman Taufiƙ, da kuɗin da MD ya ba ni na yi komai a wadace.

      Na shiga tarbon mutanena da ke zuwa daga dangin Ummata da waɗanda muke gaisuwar mutunci. Duk da ban yi gayya ba an yi mini kara sosai.

      Wanka kala biyu na ɗauka na safe daban na marece daban, musamman shiga ta biyu da na saka baƙar shaddata kuma ɗinkin ya zauna jikina daram. Sannan na ƙawata kwalliyar da ɗan kunne da sarƙata mai kama da zinari. Don waɗanda ba su san zinarin a ido ba; kai-tsaye za su gasgata ita ce a kunne da wuyana.

       Na saka gyalena ja da takalmina half shoes jajaye da wata ƙaramar jaka mahaɗinsu, bayan agogon fata baƙi da ke tsintsiyar hannuna. 

      Na fito sharr ina ta haske idon maƙiya tamkar sabon wata ɗan daren goma sha biyu, saboda duk inda na doso sai an lalace wurin kallona da sakakken baki. Haka ma idan na juya baya hararar 'yan hassada ta raka ni tare da cizon yatsan ba haka aka so ba; wai ƙanen miji ya fi miji kyau.

      Tsakar gida muka fito ana ta ɗaukar hotuna, saboda mai hoton ma Sajida ta nace a kan sai ta nemo shi. Domin kwalliyar da muka yi kada ta tafi a iska ba tare da an bar wa bikin tarihi ba. 

     Muna tsaka da hotunan ni da su Ummu Salma sun saka ni tsakiya an saka mana rumfar hoton. Sai ga Mukhtar ya shigo yana baza babbar rigar shadda fara da ke sanye jikinsa. Ihu aka saka ana faɗin ga ango nan, saboda ya yi kyau gwanin burgewa don daman can bai da makusa a halittarsa.


      Sajida ta isa wurin shi tana faɗin, "Don Allah Abban Haidar ka zo a yi hoton nan da kai."

       Har ya yi gaba yana 'yar dariya mutane suka fara roƙonsa a kan ya zo a yi da shi, fuskarsa a washe ya zo wurinmu ya tsaya gefen Iman. Mai hoton ya ce ya dawo kusa da ni Ummu Salma a gefensa, Iman gefena Haidar ya tsaya ta gabansa. 

      Ma sha Allah kawai mutane suke ta faɗa saboda babu ƙarya mun ɗauki na kuti. Bayan an gama mana hoton in group aka ce ya tsaya a yi muna ni da shi, yana shan ƙamshi aka yi mana hoton yayin da na ƙawata fuskata da mayalwacin murmushi.

      Ana gama ɗaukar hoton ya yi ciki ya bar mu muna ci gaba da hotunan, ba tare da ya yi mini kallon tsanaki ba balle mu haɗa ido ya ga kwalliyata. Mintuna a tsakani ya fito ya fice gidan, jim kaɗan da fitar shi wata Yayarsa ta zo kira na. 


      "Mukhtar ne a ƙofar gida yake so ku gaisa da abokansa."

        

      Mayafina na ɗora a saman kai duk da ɗaurin da aka yi mini mai tozo sama. Ina gaf da fita sabon tunani ya shiga kaina, saboda burin da nake da shi a kan na ɓata masa kamar yadda yake ƙoƙarin yi mini a bikin.

      Mayafin na sauke a kafaɗa, na fara taku irin na isa na doshi inda abokan nasa suka yi dandazo. Fuskata a sake na fara gayar da su, waɗanda suka san ni suna tsokana ta da sunan uwargida sarautar mata. 


     "Gaskiya Mukhtar ka yi sa'ar mata, domin kuwa na kasa tantance ita ce uwargidan taka ko kuma amaryar ce?"

     

     Murmushin yaƙe kawai yake yi yana kallona, fari da ido na yi wa mai maganar, duk da ban waye shi ba na ce, 

       "Ai duk macen da ta yi saurin zama jagwaf daga ita ne. Domin babu inda aka ce shi kaɗai ne da haƙƙin gyara ta koyaushe. Yana da kyau ita ma ta taimaki kanta da 'ya'yanta domin ta rufa wa kanta asiri da mijinta."

      Kallona kawai Mukhtar yake yi, domin ya kasa ɗauke idonsa daga kaina. ni ma idona cikin nasa nake jefa masa murmushin,


 'Ya ka ji kafcen?'


     "Gaskiya abokina ka yi sa'ar aure, domin kuwa ka auri macen da ta dace kuma wadda ta san kanta. Congratulations bros"

     Abin da wani ya faɗa kenan yana bubbuga kafaɗarsa, bai ce ƙanzil ba ya bar wurin, yana ƙoƙarin tare wani mai mashin da zai wuce ta gabanmu. 

      Karantar yanayinsa da halin da ya shiga ya sa na yi musu sallama na juya, zuciyata cike taf da farincikin abin da na yi. Don na san shi ya gano inda zantukana suka nufa, waɗanda ba lalle ba ne su abokansa su fahimci inda na dosa, balle su hankalta da bugun gorar da na yi masa a fakaice cikin siyasa.  


      Har aka watse taron bikin ban daina jin farinciki a zuciyata ba, bayan magriba wasu daga cikin danginsa suka je ɗauko amarya. 

       A lokacin da na ji dirar motocin 'yan kawo amarya, ƙirjina ya buga daram-dam-dum! Kafin zuciyata ta karɓa tana ta harbawa ɓal-ɓal sauri-sauri gudu-gudu. Ga uwar guɗar da ake jerawa wata bayan wata a lokacin da aka shigo gidan


 "Ayyururui!!!!"


   Na daburce na ji ina ma na samu ƙafar tserewa na ɓoye, domin kada na yi kukan da zan fallasa kaina a gaban mutane.  Firdausi ta taso daga mazauninta ta zauna tare da yi mini raɗa a kunne.


      "Ki natsu da kyau kada ki bari a gano ki plsss!" 


     Babu shiri wa'azinta ya shiga kaina na mazge, tare da miƙewa na tarbo amaryar. Jikina na saka ta na rungume tare da riƙo hannunta na zaunar da ita a kan kujera.

     Zama na yi kusa da ita ina faɗin,

 "Yau dai ga amarya a cikin gidanta. Allah ya ba ku zaman lafiya ke da angonki."


     "Amin-amin!" 


Gabaɗaya mutanen da ke falon suka amsa cikin ɗaga sauti. Wata daga cikin danginta ta matso kusa da mu tana faɗin,

      "Ga Barira nan mun kawo muku, sannan mun damƙa ta hannunki amanar Allah!"

      Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "Daga ni har ita amanar junanmu muke, saboda zama ya haɗa mu dole ne mu yi haƙuri da juna. Don haka ni a wurina babu wata damuwa, ina mata fatan alheri, zaman lafiyar aurenta da zuri'a ɗayyiba."


     "Allahu Akbar! Sannu 'yar aljanna!"


     Maganar da na ji wata ta faɗa kenan a cikin matan da suka zagaye mu, ba tare da na ga fuskarta ba balle na gano wace ce. Cike da ƙwarin gwiwa na karɓi kuɗi a hannun Firdausi na ɗora a saman cinyar Barira. 

      "Ga nawa kuɗin sayen bakin, tun kafin ango ya riga ni jin muryar amarya." 


      "Na gode Aunty!"


Ita ce maganar da ta fito bakin Barira bayan ta damƙe kuɗinta a hannu, tamkar wadda aka ce za a yi wa ƙwace. Dariya aka shiga yi da ihun murna, Na riƙa ta har zuwa ɗakinta, bayan na saka ta yin basmala da shiga ɗakin da ƙafar dama.

      Sai da na zaunar da ita kan gadonta, sannan na baro ɗakin da ban gama tantance tsarinsa ba. Saboda ko da wasa ban ji ina sha'awar shiga ba bayan an gama jeren, haka ma duk zaryar da danginta suke yi kawo kaya da gyare-gyare ban bi ta kan ɗakin ba, balle na ga kalar kayan gadonta da su Yaya Maimuna suke gulma.


      Su Firdausi suka ja ni ɗakina, haƙuri suka shiga ba ni sosai irin wanda ya sa na ji kuka ya zo mini babu shiri. Sannan suka tafi kowa ya watse aka bar ni daga ni sai yarana da amarya Barira a cikin ɗakinta.

      Ƙarfe goma da mintuna na ji Mukhtar yana rufe gida, sannan ya turo ƙofar ɗakina ya shigo kamar an jefo shi. Ledar da ke hannunsa ya ajiye a kan bed side, sannan ya zo daidai kaina yana faɗin,

     "Yanzu ke abin da kika yi mini a gaban abokaina kin kyauta kike gani? To wallahi duk abin da kike taƙama da shi na fi ki."


     "Ni ce shaida! Domin kuwa ko rashin adalcin da ka fara da shi; ya nuna mini zahirin wane ne kai a yanzu ko da ban san ka a baya ba."


     Amsar da na ba shi kenan ina ƙoƙarin tashi daga kwanciyar da nake. Duk da a raina ba na so mu yi abin da zai raba mana hali, gudun amarya ta jiyo mu.

      "Idan ma don ban ba ki kayan da aka ce ana bayarwa ba ne kike son tozarta ni; to ki yi duk abin da za ki iya. Amma wallahi ba zan ƙara wa mai ƙarfi ƙarfi ba, don kina da kuɗin albashinki, wanda kaɗan ne za a ƙara a kan wanda nake karɓa. Kuma ina da hidimar da ta fi zama dole fiye da saya miki kayan dannar ƙirjin."


   A harzuƙe na ce da shi,  "To da ba ka saya ba sai me!? Ai dai ba ka gan ni a wulaƙance ba ko?"

      "Kanki ake ji! Ga kazar amarya nan ki sa albarka. Ni na shige! Kuma idan an ga ban fito da wuri ba kada a neme ni, don ba ɓata zan yi a cikin gidan ba."


   Sai da na fashe da dariya sannan na ce,  "Allah na tuba ka yafe ni! Wane dare ne jemage bai gani ba?"


       "Na ranar mutuwarsa!"


     "Idan haka ne kuwa babu abin da zai sa na damu da barazanar da iyakacinta a baki. Da ma a ce kai namijin gaske ne mai iya gamsar da mace ya cire mata kwaɗayin wasu mazan; da zan ji zafin aurenka da wannan daren da kake tinƙaho yanzu. Amma abu kamar lagwani ranar me za ta yi mini balle na ji haushin masu zuwa aro?"


     





     Laaaa!😱🤭🏃🏻‍♀️

No comments

Powered by Blogger.