Saran Boye 6-10

 

No. 6


................Baba malam na tsaka da sallamar abokan arziƙinsa kira ya shigo wayarsa. Kamar zai share karya duba sai kuma ya cirota daga cikin babbar rigarsa. Ganin Number da akai kiran da ita yasashi ɗagawa da sauri ya ɗora a kunne yana faɗin, “Assalamu alaikum. Innah!”. Batare da Hajjo ta amsa masa sallamarba cikin kuka take faɗin, “Duk inda kuke ku taho gidan nan babu lafiya ɗan Malam”.

       “I...in...innah miya faru halan?”. A zafafe Hajjo tace, “Sai kaji abinda ya faru zaku taho? To Firdausi ce aka fita da ita babu rai”.

      Ba ƙaramin bugun ƙirjin Baba malam wannan kalma tayi ba, kafin ya samu damar yin magana Hajjo ta yanke kiran. ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ Baba malam ya fara ambata akan laɓɓansa, atake damuwarsa da yaketa ƙoƙarin dannewa take ƙoƙarin fitowa fili, ya share zufar data taru masa a gaban goshi yana busar da iska mai zafi. lumshe idanunsa yay na wasu mintuna yana ambatar addu'a. Sai da yaɗan samu nutsuwa sannan ya juya zuwa cikin hall ɗin. Ruwa ya samu ya sha zuciyarsa ta ƙara nutsuwa kafin ya tattara su Abbah da samarin gidan suka bar wajen.

        Suna fara tafiya sai ga kiran Omar, shine ya sake sanar masa da abinda ke faruwa, tare da asibitin da suke a yanzu haka. Kai tsaye can suka nufa, inda suka tarar da Addah da yayun Umm sun haɗe kai sunata sharɓan kuka. 

         Hankalinsu Baba Malam sai ya sake tashi fiye da farko, amma da yake shiɗin kamilin mutum ne sai fuskarsa bata nuna yanda yake a rikice ba. Addu'oi ya keta ambata a ransa yana cigaba da miƙama UBANGIJI kukansa.


      Sun kai tsahon mintuna arba'in suna jiran fitowar Doctor kafin ya fito. A kusan tare suka sauke ajiyar zuciya ganin fuskar Doctor ɗin da ɗan sassauci ba kamar ɗazunba. Kallonsu yay cike da girmamawa yace, “Alhmdllh ta farfaɗo. jininta ne ya hau sosai, ALLAH ma ya taƙaita mata wahala, dan irin wannan faɗuwar ga mai hawan jini babbar matsalace, musamman yanda jininta yay ƙololuwar hawa”.

        Sake sauke ajiyar zuciya duk sukayi, Baba Malam ya kauda kansa gefe tare da ɗauke ƴan ƙwallar da suka taru masa a cikin ido.


           Baba malam ne kawai aka bari ya shiga ya ganta, tana kwance idanunta rufe an saka mata ƙarin ruwa. Tai masa wani irin masifar haske a ido. Ya jima yana kallonta tausayinta na sake faɗaɗa a zuciyarsa, ya kai hannu ya shafa kanta yana magana a hankali. ‘ALLAH ya baki haƙuri Jannat kinji, ALLAH ya bamu ikon cinye jarabawar nan, kiyi haƙuri ki daina damuwa’. Ya ƙare maganar da sumbatar goshinta.

       Ya kai tsahon mintuna goma yana cigaba da kallon ƙyaƙyƙyawar matar tasa kafin ya juya ya fita a ɗakin. 


Gaba ɗaya kan baba malam ya ƙara ɗaukar zafi, gashi dama shima yana da hawan jinin. Gudun kar gazawarsa ta bayyana ya sashi samun Doctor ya nema a sallamesu su koma gida da Umm. Family Doctor ɗinsu zai cigaba da kula da ita.

       Doctor baiyi musu ba ya basu sallama, dan yasan su ɗin manyan mutanene, bazasuso cigaba da zama a asibitinba kodan yanayin da ƙasar yake na rashin tsaro.


     Bayan kammala duk abinda ya dace aka saka Umm a Ambulance. Addah ta shiga tare da Nurse ɗin da aka basu, su kuma suka shiga motocin da sukazo a ciki.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


__________________

________________________


            Sosai hankalin mutanen gidan da ƴan biki ya ƙara tashi ganin Ambulance har cikin gida. Da yawan gwiwoyin wasu ya sare a zatonsu ko Umm ta rasu ne. Sai da sukaga an fito da ita zuwa sashensu harda ƙarin ruwan da ake mata sannan aka fara sauke ajiyar zuciyoyi da ambaton Alhmdllh.

            Bayan an shiga da Umm Bedroom ɗin Baba Malam dangi suka shiga jajantama juna da addu'ar samun lafiya a gareta tare da fatan dawowar Nu'aymah gida cikin ƙoshin lafiya. Daga haka dangi na kusa suka fara zare jiki suna barin gidan, dan kam ko masu gidan basuce dasu komaiba sunsan suna buƙatar a basu wuri suji da abinda ya damesu.

       Kafin sallar magriba gidan ya ragu sosai. dan irin dangi na katsina, kaduna, jigawa ma duk sunyi sallama sun tafi tunda ba wani nisa bane mai yawa. Balle kuma ƴan cikin kano da ƴan gayyar aci shinkafa asha zoɓo😏🤐.

         Yayun Umm su Maman Nanah dai suna nan basu tafi ba sukam duk da anan cikin kano suke aure su duka. Sai kuma wasu a cikin dangin Momyn Abdallah da suma sukaƙi barin gidan.


       Har bayan sallar isha'i Umm nata barci, yau Baba malam ko wajen karatu bai zauna ba, sai Abba Mustapha ne yayma magidantan dake ɗaukar karatu bayan sallar isha'i ƙari. Shima daga ƙarin ya sallami kowa ya shigo gida. 


★★★★


        Zuwa bayan isha'in ne hankalin kowa ya koma kan sanin ina Abdallah?, dan duk wannan rugun tsumin da akeyi babu wanda yaji ɗuriyarsa. Nemansa aka shigayi a waya amma bai ɗagaba. Hakan yasa samarin gidan suka fara didduba ɗakunansu. Har hankali ya fara tashi na rashin ganin nasa sai gashi Abubakar ya samosa a ɗakinsa yana barci.

      Fita yay ya sanar musu. A tare duk suka ɗura kai cikin ɗakin, inda suka sami Abdallah kwance cikin matsanancin zazzaɓi. Da yake Doctor yazo sake duba Umm sai aka kirasa yazo ya duba Abdallah shima. Shikam damuwace ta saukar masa da zazzaɓin, sai kuma yunwa. Magunguna Doctor ya haɗa masa harda wanda zai sakashi barci, yace a bashi abinci ya ci kafin yasha.

     Haka kuwa akayi, Hajjo ta basa abinci da kanta duk da yanata cewa shi ya ƙoshi. Da dai lallashi da ban baki aka samu yaci kaɗan yasha magani. Ahmad ne ya taimaka masa yay wanka sannan aka maidasa ɗakinsa da Hajarah ta gyara ya kwanta.

     Ganin barci ya ɗaukesa sai duk suka fito, aka barsa da Ahmad kawai da zai kwana tare da shi dan ba'asan mi dare zaizo da shiba.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


___________________________

___________________________

             WASHE GARI

        ___________________

             

       Daga Umm har Abdallah sun tashi jikinsu Alhmdllh, sai dai damuwa irin ta zuciya da fitarta farat ɗaya bazai yuwuba. Bayan kammala karin kumallo aka haɗu aka tsaftace gidan, sauran baƙi duk suka kama gabansu. Su Sumayya kawai ne duk suna nan basu koma gidajensu ba.


         Bayan sallar azhar Baba malam da su Abba suka zauna tare da Hajjo, sun daɗe suna tattaunawa kafin su buƙaci ganin matan gidan suma da Abdallah.

      Cikin nutsuwa Baba Malam yay musu bayanin da zasu fahimcesa akan wannan canjin da yayi, da kuma dalilinsa na aurama Abdallah su Yusrah. Ya kuma sake nuna fushinsa sosai akan abinda Nu'aymah ta aikata. Har saida takai ƙannen nasa da matansu na bashi haƙuri.

     Umm dai batace da kowa komaiba har aka gama aka sallami kowa. itace farkon tashi ta fice a falon. Dan haka duk suka bita da kallon tausayawa. Banda Baba malam da yay kamarma baisan mi sukeyiba, yanata ƙoƙarin cigaba da danne damuwarsa a rai.


____________________

BAYAN SATI ƊAYA

____________________


              Bayan sati ɗaya da faruwar komai gidan ya koma normal a zahiri. A baɗini kuwa kowa shi kaɗai yasan damuwarsa da matsalarsa. 

     Kasancewar ita Adawiya sun kammala secondary baba malam ya yanke hukuncin Abdallah zai tafi da ita can ta cigaba da karatunta, ita kuma Yusrah saita ƙarasa watannin da suka rage mata sai yazo ya tafi da ita. Kowa yayi na'am da wannan magana, dan harma an kammalama Adawiya duka shirye-shiryen tafiya.

     Kwatanta muku irin farin cikin da Adawiya take cikima ɓata lokacine, sai dai tanata ƙoƙarin dannewa saboda tsoron Addah data sanyama duk wani motsinta idanu yanzun, sannan ta daina sakar mata fuska gaba ɗaya..     

        Ganin yanda Addah taketa share Adawiya daƙin yin komai game da ɗan gyarata yasa Umm ta maidota sashenta. Gyaran da bazai cutar da itaba ta shiga mata. Musamman fatarta da kuma maganin sanyi. da koya mata dabarun zaman aure. Ɓangaren girki da aikin gidan tasan bata da matsala, tunda su duka tsaye suke akan yaransu ta wannan fanin duk da kowane sashe akwai ƴan aiki. Dan danan cikin sati guda ta canja tai fes abunta. Idan tana ɗaki ita kaɗai tata kallon kanta a mirror kenan tana tiƙar rawa da gwada yanda zata kasance da Yah Abdallah. Duk da kuwa a yanzu ko kallo basu ishesaba daga ita har Yusrahn. Ko yarda ya haɗu da suma bayayi sam, idanko yaga ɗaya daga cikinsu a waje yata fama haɗe fuska kenan tamkar an aiko masa da saƙon mutuwarsa. Hakan bai dametaba, dan tasan lokaci zaizo da sauyi wataran, kamar yanda a yanzu yazo da shi a garesu suka kasance matansa batare da mafarkinsu ya taɓa hasaso musu hakanba. 

      Tana tsananin takaici a ranta na haɗata da Yusrah da akayi matsayin matansa, amma ta wani ɓangaren hakan bai damunta, musamman da akace itace zata fara binsa, ta barma kanta yanda sauran aikinta zai kasance tsakaninta da kishiyar tata (😖Adawiya!!!!!💣).


          Yusrah kam dai tana cikin damuwa sosai. kullum cikin kuka take da roƙon Abbanta a warware auren ita bataso. Sai dai kowa yaƙi saurarenta, Amminta ce dai take tayata kuka dan tasan da gaske Yusrah bataso ɗin. Amma yaya zasuyi da ƙaddara?.


        A washe garin da aka cika kwanaki goma da faruwar al'amarine tafiyar Adawiya da Abdallah ta kama.

      Umm da kanta ta samu Addah har ɗaki tai mata ƙorafi akan yanda take share Adawiya. Sai da ta nuna mata ɓacin ranta akan hakan sosai sannan ta ɗora da mata nasiha akan ta yarda da ƙaddara mana.

        “Addah Minene laifin Adawiya tunda ba itace ta saka a ɗaura mata aure da Abdallah ba. Ba kuma itace tabama Nu'aymah shawarar ta gudu ba. A ganina addu'a ya kamata mubi yarannan da shi tare da fatan alkairi bawai tsangwama da hantara ba dan su basu da laifi”.

        “Umm bazaki ganeba wlhy, ke dai kibar......”

      “Naji bazan ganeba Addah”. Umm ta dakatar da Addah da sauri. Ta cigaba da kallonta tana faɗin, “Baki da wani abinda zaki faɗamin da zaki kare kanki, ni dai kawai ki dawo rayuwa da yaran nan kamar yanda kikeyi da. Ki kuma yima Adawiya fatan alkairi kodan sabuwar rayuwar da zata fuskanta a yau dan girman ALLAH”.

      Shiru Addah tai tana sake jinjina ƙyawun zuciya irin na Umm, haka take ita komai tana ɗaukarsa da sauƙi a rayuwarta bata zafafama kanta. Tunda abinnan ya faru babu wanda ya taɓajin furucinta kosau ɗaya akai. Ko a fuska ƙoƙarin ɓoye damuwarta takeyi. Tausayin aminiyar tata kuma ƴar uwarta sai ya sake kamata fiye da da can.


     Umm da kanta ta fita taje ta shigo da Adawiya, zaunar da ita tai kusa da Addah itama ta zauna. Su biyu suka shiga yima Adawiya nasiha kamar yanda sukeyi a duka sauran ƴaƴan Addah uku da aka aurar. Sumayya, Maryam, Badariyya. Sai da sukai mata nasiha sosai kafin Umm ta tashi ta fita ta bar Adawiya da Addahn.  


★★★★


        Kamar yanda tsari da al'adan mutanen gidan yake bayan sallar la'asar iyayen suka sake haɗuwa aka rufu kan Adawiya da Abdallah akai musu faɗa da nasiha sosai. Tare da gindaya musu sharuɗa masu tsauri akan duk wanda wani al'amari mara ƙyau ya ɓullo daga wajensa a cikinsu to lallai zai fuskanci ɓacin rai da fushinsu sosai. Daga ƙarshe aka sake musu doguwar addu'a aka sallami Adawiya da ko sau ɗaya batai hawayeba da iyayensu mata.

     Umm ta tafi da Adawiya sashenta danta kimtsata, suka bar Abdallah tare dasu Baba Malam da Hajjo da suka sake ɗora masa da Nasiha kasancewarsa shine babba.


        Ƙarfe 7:30pm gayyar yaran gidan harna ma'auri su Aysha sukaima Abdallah da Adawiya rakkiya airport dan jirgin 8:30 zasu bi zuwa ƙasar Dubai. Sai sunyi kwanaki goma acan kamar yanda Abdallah ya tsarayi da Nu'aymah sannan su wuce Saudia.

       A yanzuma dai idanun Adawiya ƙifi-ƙifi babu ko ɗigon hawaye a cikinsu. Hakan ba ƙaramin ƙona ran Addah yayiba. Hakama Momyn Abdallah al'amarin ya bata tsoro, taita kallon Adawiyar cike da alamomin tambaya a ranta, sai dai bata furtaba.


            Ko kaɗan Yusrah bataji komai a rantaba, dan ko kusa bata kawo Adawiya ma a cikin matsalolinta saɓanin Adawiyar dake jin zafin Yusrah babu gaira babu sabar. Ita Yusrah dama za'a warware nata auren da tayi matuƙar farin ciki. Amma ta ɗauka alwashin cigaba da addu'oi tana gayama ALLAH kukanta akan hakan kafin lokacin da akace zata tare.

      Basufi zaman mintuna talati da huɗu ba aka sanar da tafiyarsu. Sai yanzune Adawiya taɗanji babu daɗi a cikin ranta na kewar ƴan uwanta. Amma saita fuske ta shiga binsu ɗai-ɗai tana rungumarsu. Da tazo kan Yusrah saita wuce batace mata komaiba. Ba ƙaramin mamaki hakan ya bama kowaba, duk suka bita da kallo har Yah Abdallahn. Tsarguwa da tai ne ganin yanda ƴan uwan nata ke binta da kallon tuhuma ya sakata buɗe jakkarta ta ɗakko wani abu ta nufi Yusrah, hannunta ta kama ta saka mata abin sannan ta rungumeta kamar yanda taima kowa. 

      A kusan tare duk suka sauke ajiyar zuciya, dan da da yawansu abun yay musu cak a ƙirji hatta da ƴan uwanta da suka fito ciki ɗaya. Musamman Hajarah da taga abinda ya faru a ranar ɗaurin auren tsakanin Addah da Adawiyan.

     Sallama suka sakeyi da juna. Kafin tabi bayan Yah Abdallah da yay gaba abinsa batare da ya saurareta sun jera tareba kamar yanda taso.


“Hummm!! Wasa farin girki Adawiya👁👎🏻”.


___________________

NU'AYMAH

______________


              Tun randa aka barota daga gida bata sake sanin halin da take a ciki ba sai washe gari da yamma. Farkawa tai a tsananin firgice. Sai dai nauyin masifa da kanta yay mata na azabar ciwo ya sakata sakin ƴar siririyar ƙara da dafe kan nata da hannu bibbiyu tana sakin numfashi a wahale.

        Sake ƙoƙarin buɗe idanunta tai da ƙyar saboda nauyin da sukai mata suma. Tabi ɗakin da take ciki da kallo mai ƙaracin haske, sai dai ba dunɗum yakeba. Katifa ce kawai a ɗaki da wasu lalatattun akwatuna guda uku kalar ruwan ƙasa. Sai takalma na maza da aka jera a gefe kusan ƙafa shidda. Sai hanger a jikin bango anyi hanging farar jallabiya ta maza guda ɗaya da wanduna uku duk baƙaƙe. Sake lumshe idanunta tai ta buɗe a hankali dabin jikinta da kallo. 

     Hijjabin tane dai a jikinta har ƙasa da ta saka lokacin da zata fita neman wayarta. Ta kai hannu da ƙyar ta laluba jikinta. Towel taji wanda shima shine tasan ta ɗaura a jiyan, sai dai yanzu ya kwance duk ya zazzame daga ƙirjinta ya dawo saman cikinta.

      Juya mata da garin ya farayine ya sakata yin baya ta sake kwanciya a katifar hawaye masu a zabar zafi na silalo mata a saman kumatu. A haka ta cigaba da kwanciya tana zirarar da hawayen jikinta duk babu wani ƙarfi. Tafi mintuna talatin da kwantawa sannan aka buɗe ƙofar.

    Kasa buɗe idanu tai balle taga wanene ya shigo ɗin, tsahon mintuna biyar kafin ta buɗe idon kaɗan ta saukesu akan wanda ke tsaye jikin ƙofa sanye da baƙaƙen kaya, hatta da hannunsa akwai safar hannu baƙake. Hakama fuskarsa da facemask, idanunsa kawai take iya gani. Suma ganin kallon da take masa ya sashi ciro glasess ya toshesu. 

    Basket ɗin dake riƙe a hannunsa ya tako gaban katifar ya ajiye batare da yace da ita uffanba ya juya ya fita. Maida idanunta tai da ƙarfi ta rumtse zuciyarta na zafi. Kukanma yanzu sai ya kasa fita mata. Haka ta cigaba da zama a wajen har bayan mintuna kusan goma da fitarsa. Sai kuma ga mace ta shigo sanye cikin dogon hijjab har ƙasa. Itama fuskarta sanye take da niƙaf. 

     Batare da tama Nu'aymah magana ba ta kamata ta tayar. Bata da wani ƙarfi ko iya yin magana, dan haka ta cigaba da bin matar kawai a yanda taso. Ƙofa ƙwara ɗaya ƙarama dake a cikin ɗakin suka nufa, sai da suka shiga Nu'aymah ta fahimci toilet ne. Fas yake babu ƙazanta a cikinsa, saima ƙamshin omo da hypo daketa tashi.

      “Kiyi wanka”. Matar ta faɗa a taƙaice batare da ta jira amsar Nu'aymah ba ta fice abinta. Da kallo kawai Nu'aymah ta bita, sai dai bakinta ya mata nauyi ta gaza cewa uffan a yanzunma. Kamar bazatai wankanba sai kuma wani tunanin yazo mata. Rabonta da salla tun ta isha'in jiya. Ga shi a yanzu da alama har anyi sallar la'asar ma. Tana buƙatar ƙarfin jiki sosai, hakan kuma bazai yuwuba sai tayi wankan.

     Cikin ƙarfin hali ta zare dogon hijjabinta da towel ɗin, duk da tsaftar banɗakin a ɗarare tai wankan. Taji ƙarfin jikinta sosai, sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi a jajjere. Alwala tayi ta fito tana daddafa bango, dan akwai yunwa tattare da ita.

     Da mamaki ta kalli kayanta da aka ɗaura a saman katifar, ta bi ɗakin da kallo kamar ɗazun, babu kowa sai kayan a ajiye da kuma kwanikan abincin dake cikin basket ɗin suma an fiddosu ƙasa an ajiye.

        Bata da wani zaɓin daya wuce canja kayan tai sallolin dake kanta. Harta kammala rama sallolin babu wanda ya sake shigowa, ta kwanta saman abin sallar tana hawaye da tunanin ko wane hali yanzu Umm da Abbanta da Muh'd dama duka sauran ƴan gidansu suke ciki a yanzu na rashin ganinta?. Yah Abdallahn ta, tasan zaifi kowa shiga tashin hankali bayan Umm da Abbanta. ‘Minayi suka kawoni nan? Su wanene su? A ina nake?’. Ta faɗa a fili tana sake fashewa da kuka. Taja tsahon lokaci tana ribzar kukanta, har kanta yana masifar sara mata fiyema da ɗazun. Barcine ya fara figarta na wahala. Jin motsin shigowar mutum ya sakata tashi zaune zumbur. Matar ɗazunce, yanzuma batai mata magana ba ta ɗakko kwanikan abincin ta kawo gabanta da mata alamar taci.

      Yunwa Nu'aymah takeji sosai, dan haka batai musu ba taja abincin tahau cinsa. Taci sosai har matar tai mamakin hakan. Matar ta miƙe zata fara tattare kwanikan Nu'aymah ta kalleta cike da rashin tsoro tace, 

       “Su wanene ku? Miyasa kuka kawoni nan? Minai muku kuma?”. 

     Kallonta matar tayi sosai, amma sai batace da ita komaiba ta tattara kwanikan tai ficewarta. 

        Tashi Nu'aymah tayi ta nufi ƙofar da sauri, sai dai tana taɓawa tajita a kulle, fashewa tai da kuka ta koma saman katifar ta sake kwanciya tana sambatun kiran Umm da Abbanta da Yah Abdallah.


        Tun daga wannan ranar kullum hakan ta cigaba da faruwa, zasu kawo mata abinci sau uku a rana, matarnan zatazo ta gyara ɗakin ta wanke mata bayi da kayan data cire. Sannan ta haɗa mata ruwan wanka ta sakata cin abinci. Tambayar duniya tai mata bama bata amsa, haka shima namijin idan zai shigo sau goma tai masa magana baya ko mata tari. Iya kacinsa ya leƙo ya ganta ya koma.


     Haka Nu'aymah ta cinye kwanaki goman nan cikin matsanancin damuwa da tashin hankali. Babbar damuwarta halin da ahalinta zasu shiga na rashinta. Musamman ma Umm ɗinta da Abbanta da Yah Abdallah da Hajjo. Tayi kuka harta gaji ta bari ta koma gayama UBANGIJI kukanta. Dan tasan shine mai rahama mai jinƙai. Ya fita sanin dalilin da yasa ya jarabceta da wannan al'amari a daren ɗaurin aurenta da yayanta masoyinta.


       Ranar data cika sati biyu a ɗakin bayan sallar la'asar sai ga matar nan, kamar kullum yauma batai mata magana ba, saima kwashe kayanta data cire tai ta fita dasu. Bayan kamar mintuna goma sai gata ta dawo ɗauke da hijjabi wankakke gogagge. Miƙama Nu'aymah tai da mata alamar ta sanya. Babu musu Nu'aymah ta fisgi hijjabin daga hannunta tana watsa mata harara ta sanya. Ita sam bata wani jin tsoronsu, damuwarta kawai family nata.

      Matar bata kulataba, bayan ta saka hijjab ɗin ta zagaya ta bayanta ta riƙe mata hannaye. Fisgewa Nu'aymah ta fara ƙoƙarin yi amma ta kasa saboda ɗaure hannayen da matar tayi. Kafin ta samu damar magana namijin ya shigo shima. Gaban Nu'aymah yaje ya tsaya tare da fiddo baƙin ƙyalle a aljihunsa ya ɗaure mata idanu.

     Duk tsiwar da take masa bai kulataba balle ya tanka. A haka suka fita da ita a ɗakin batare da tasan ina za'a kaitaba.............✍


_____________________

SAHFAT PREORDER!

______________________


        Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.


SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.


Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.


*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*


_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.


Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.


Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.


*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*



_____________________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 

Hafsat miss xoxo🥰

KIBIYAR AJALI......!

      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

   

          Mamu gee🥰

MIN ƘALB!!😋🤗


        Hafsat rano🥰

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


         Bilyn Abdull🥰

SARAN ƁOYE🤗😋


    Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.


*_Typing📲_*


No. 7


................Sosai gazawar Umm take ƙoƙarin bayyana ga kowa. Dan gaba ɗaya yinin yau da Nu'aymah ta yisa a ranta. Tun tana kukan zuci kamar yanda ta saba har hawaye suka kai ga fara sakko mata daga idanu. 

        Wajen misalin biyu da rabi na rana Baba malam ya shigo gidan. Kamar yanda al'adarsa take inhar ya dawo daga wajen aiki sai ya fara zuwa sashen Hajjo yaga lafiyarta. yauma haka ne. Zaune ya isketa a falo Imran na tausa masa ƙafa yana kumbura baki dan ta sakashine dole.

     Murmushi Baba malam yay da zama a ƙasa gefenta kaɗan da ajiye mata ledan kayan fruits idonsa akan Imran ɗin da shi sam hankalinsa bai kai kansa ba.

           “Imran ya naga fuskar a kumbure? Ko dai aikin innah ne ba'a son yi?”.

     Kallonsa Imran yay da sauri, sai kuma ya saki ƙafar Hajjo ya nufi baba malam ɗin yana sake tunzura baki gaba. “Baba sannu da dawowa”. Kafin Baba malam ya bashi amsa Hajjo ta katsesa. “Dan gidanku dawo ka cigaba, inba hakaba kasan ALLAH nasan ta inda zan rama mai ƙwalelen ƙeya kawai”.

      Dariya Baba malam yayi yana kallon yanda Imran ɗin ya cika yay fam, sai kuma ya kalli Hajjo da itama ta kumbura farar fuskarta da duk tai tamojin tsufa tana zubama Imran ɗin harara......

       “Ni wlhy na gaji Hajjo, kumafa Momy jirana take zan mata aika”.

     “Oh! Uwarka ta fini kenan?..”

Baba malam yay saurin haɗiye dariyarsa da matsawa kusa da ita gab ya kama ƙafar tata ya aza saman ƙaramin filon kujera. “Kinga Inna manta da shi kinji, idan shima yana tsoron ɓatama mamarsa nima ai gani tare dake ko?”.

         Murmushi tayi kamar ba itace da fuska a kumbure ba. Sai kuma ta watsama Imran ɗin harara tana faɗin, “Tashi ka fitarmin a falo to kirikun banza, indai nice ai inada ranata yaro”.

     Tashi Imran yay da sauri dan ganin Hajjo ta kwakuso filon kujera da alama dukansa zatayi. Sai da yaje bakin ƙofa sannan ya juyo. “Ai dai gobe idan ALLAH ya kaimu zamuyi komawarmu Abuja.......”

     Kafin ya rufe baki ta tilla masa filon, kwasa yay da gudu ya fice yana ƙyalƙyala mata dariya.

        “Wlhy Ɗan malam ƴaƴanku sun fetsare musamman ma ƙarshe-ƙarshen nan. Kaga akace maka Imran da Muhammadu da Jafar sunfi kowa rainanima a gidannan”. Hajjo ta faɗa a ƙufule.

      Cike da girmamawa da lallashi baba malam yace, “To kiyi haƙuri inna zan musu faɗa kinji, yanzu dai ƙafar ciwo take miki ne?”. 

        “Kaɗan take ciwon dai, na neman man zafin daka siyomin shekaranjiya na rasa inda yake, na tabbata cikin ƴaƴanku wani ya ɗaukesa. Ƙilama Zainabu c.......” sai kuma tai shiru ta kasa ƙarasawa saboda tunawa da tai Nu'aymah ma bata gidan. To ita kaɗaice ke mata yanda ta gadama a cikin jikokinta a zauna lafiya a gidan. Dan suna mugun ɗasawa da Nu'aymah saboda duk aikin da ta sakata yimatashi take. Hatta da wanki Nu'aymah ce kema Hajjo. Hakama gyaran sashenta. Sai ko Adawiya itama sunaɗan shiri, amma ƙa'ida kullum sai sunyi faɗa.

      Ɗan murmushi baba malam yayi mai ciwo, dan shima a kullum ɗiyar tasa tana a ransa. Ya sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Karki damu innah insha ALLAH zansaka Abubakar ya saya miki idan zai baro company. Sannan zanma Doctor Kabir magana yazo ya duba ƙafar, idan kuma asibitin zamu koma to”.

      Jikinta a sanyaye ta ɗaga masa kanta, harya miƙe bata iya sake cemasa komaiba. Sai da yaje gab da fita sannan ta kira sunansa. “Ɗan malam!”. Juyowa yay da sauri yana ƙoƙarin haɗiye abinda ya tokare masa maƙoshi da amsawa da “Na'am Innah”.

         “Har yanzu babu labarin Zainabu dai ko?”.

     Murmushin yaƙe yay mata wanda yafi kuka ciwo, ya ɗan girgiza mata kansa da faɗin, “Innah tasan inda taje ta ɓoye kanta ai. Randa ta buƙaci ganinmu da kanta zata nememu, ki kwantar da hankalinki wannan yabar damunki”.

     Bata iya cewa dashi komaiba yanzuma. Dan damuwa ƙarara ta hango a saman fuskarsa da cikin idanunsa. Amma dan ƙarfin hali sai yay mata murmushi sannan ya juya ya fita.


          Tamkar wanda aka zarema lakar jiki haka ya isa sashensa. Da tsarabar da yayo ta fruits ya fara cin karo a falo alamar driver baiga kowaba ya ajiye a nan. Ya ɗanbi ledojin da kallo kafin ya ida shigewa cikin corridor ɗin da ɗakunan barcin su Umm suke. Kansa tsaye ɗakinta dake can ƙarshen dogon corridor ɗin ya nufa, yay sallama kusan uku a ƙofar ɗakin babu amsa, sai kawai ya tura ƙofar ya shiga da sallama.

       Tsaye yay cak a ƙofar ɗakin riƙe da handle ɗin kofar yana kafe Umm dake zaune a saman gado, Muh'd na kwance ya aza kansa bisa cinyarta yana barci. Kan yaron take shafawa a hankali, kanta na kallon p.o.p idanunta na tsiyayar da hawaye. 

         Haɗiye tasa damuwar yay ya ƙarasa cikin ɗakin sosai. Harya zauna a bakin gadon kusa da Umm bata motsaba. Ya ɗaura hannunsa saman nata dake shafa na Muh'd. Nannauyan numfashi ta sauke da ɗago kanta. Kallon ido cikin ido sukaima juna ita da baba malam ɗin. Sai tai azamar saka hannunta na haggu ta share hawayen fuskar tata tana maye gurbinsa da murmushi.

       “Sannu da zuwa Abban Nu'aymah. Yaushe ka shigo ban saniba? Gaba ɗaya na gajine shinefa nace bara nazo na.........” hannunsa yay saurin ɗorawa akan bakinta alamar tayi shiru. Yasan ba wani abune ya saka wannan kame-kamenba sai dogon gargaɗin daya gindaya mata akan karta sake masa maganar Nu'aymah koda da wasa ne. Umm macece ita mai biyyaya da gudun ɓacin ran mijinta, duk abinda ya nuna bai masaba ƙoƙarinta shine dainashi tai masa wanda zai sakashi a farin ciki koda ita zai cutar da tata zuciyar kuwa. Wannan yana ɗaya daga cikin abinda ya ƙara mata kima da daraja a gareshi, tare da sake girmama soyayyarta a ranshi.

     Miƙewa yay ya ɗauki Muh'd a hankali ya matsar dashi can gefe ya kwantar. Ita dai tana binsa da kallone har ya dawo ya zauna kusa da ita sosai. Kamota yay ya kwantar da kanta a ƙirjinsa. A tare suka sauke nannauyar ajiyar juciya. Hawayen da taketa ƙoƙarin karsu zubo suka ziraro a guje suna sauka bisa jikinsa.

        Idanunsa ya lumshe tare da sake kwantar da ita jikin nasa da ƙyau, ya zame ɗan kwalinta yana shafa kanta dake cike da gashi dogo mai yarfin furfura ɗai-ɗai alamar girma ya fara kamata. Sake kwanciya tai sosai da cigaba da hawayenta.

    Sunja tsahon lokaci a haka har saida akai kiran sallar la'asar sannan. Itace ta ɗagashi da sauri. Hakan yasa ya farka daga barcin daya figesa shima. Tunda abinnan ya faru bai sake yarda sun kwana ɗaki ɗayaba tun randa ta kwana babu lafiya. Hakan yasa suke tsananin kewar ɗumin junansu. Matsar da fuskarsa yay gab da tata ya sumbaci goshinta da dogon hancinta.

     Ɗan murmushi tamasa da sadda kanta a ƙasa na alamar jin kunya. Shima yay murmushin yana sauke ƙafafunsa ƙasa. Batare da yace mata komaiba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Ki tada Muh'd yay alwala mu wuce massallaci”.

       “To” ta amsa masa tana binsa da kallo.


__________________________________ 


              Ana shiga sallar la'asar jar motar na shigowa cikin layin. Parking yay a ƙofar ƙaton gate ɗin gidan yana kallon gate ɗin massallaci. Kafin kuma ya maido dubansa kan Nu'aymah dake a gefensa hannu da idanunta da baki a rufe tana gyangyaɗi.

       Ɗauke kansa yay ya kashe motar gaba ɗaya. Bai fitaba, saima kwanciya yay jikin kujera ya lumshe idanunsa dake a cikin baƙin glasess ɗinsa.

       Kusan mintuna uku da tsayuwarsu Nu'aymah ta farka. Sai dai kasancewar idanunta da bakinta a rufe suke sai bazaka fahimtaba. Addu'a kawai take jerawa a ranta na nema agajin UBANGIJI. Sai da aka fito massallaci mutane suka gama shashsharewa, sai hayaniyar yara ƴan islamiyya dake cikin harabar massallacin. Kusan biyar na yamma Baba malam ya fito daga cikin massallacin shi da wani maƙwafcinsu suna magana. Saurin tashi yay zaune da kallon Nu'aymah, yay azamar saka hannu ya ɗaye mata salataf ɗin da suka rufe mata baki da shi. Ƴar ƙarar azaba ta saki tana faɗin, “Mugu kawai, ALLAH zai sakamin”. Bai kulata ba ya kwance mata idanunta da hannunta suma. Wani irin farin cikine ya saukar mata a rai ganinta a ƙofar gidansu. Tana zumuɗin fita ya dakatar da ita.

      “Malam ɗauki akwatinki ki wuce da shi”.

     Juyiwa tai da sauri tana kallonsa batare da ta saki handle ɗin ƙofarba. “Bansan kallo, ki ɗau akwatinki nace”.

          “Minene abin kallo a jikin naka banda baƙin hali da zalunci. Ni dai nasan banbar gidanmu da akwati ba mizaisa kuma na ɗauka na shiga da shi...”

        “K!!!” ya daka mata tsawa a fusace. Hakan ya sakata dakatawa daga ƙoƙarin sake buɗe ƙofar ta juya tana watsa masa harara da manyan fararen idanunta masu yalwar gashi. “Minene namin tsawa malam?”. Maimakon ya bata amsa sai ya ɗaga mata yatsun hanunsa biyu dake a cikin safa yana faɗin, “Kinada zaɓi biyu. Koki ɗauka akwatin nan kokuma wlhy na maidake inda muka fito, kuma wannan tafiyar itace zata zamemiki ta har abada keda gida”.

     Kafinma ya rufe baki ta miƙa hannu baya ta sungumi ƙaramin akwatinta ruwan hoda mai ƙyau. Batare data sake jira yace uffan ba ta buɗe murfin motar ta fice abinta.


         

          Sosai gaban baba malam ya faɗi, yabi Nu'aymah dake jan akwati zata shiga gida da kallo harta tura ƙofar ta shiga, kafin ya maido dubansa ga motar data ajiyeta. Akan idonsa mai motar yay reverse yabar anguwar.

    Duk yanda yaso danne ransa suci gaba da magana da Alhaji Mani hakan ya gagara. sai kawai yay masa sallama akan yayi haƙuri anjima zasu ƙarasa maganar.

       Da mamaki Alhaji Mani yabi baba malam da shi harya shige gida da kallo.. Ya ɗanyi shiru alamar tunani. Ganin bai hasaso komaiba sai kawai ya girgiza kai shima ya juya ya shiga nasa gidan da masallaci ya raba tsakaninsu da nasu Baba malam.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


__________________

__________________


             Nu'aymah na isa tsakiyar gidan ta yadda akwatin ta kwasa da gudu zuwa ciki tana ƙwala kiran sunan Umm da Hajjo, dan gani takema tafiyar ɓata mata lokaci takeyi na isa garesu.

        Ba Umm da Hajjo kaɗaiba kowa ma na gidan sai da ya fito, yaran ne kawai da suka wuce islamiyya babu. Samarinma yawancinsu sun dawo daga wajen aiki da makaranta ga waɗanda ke jami'a.

         Wani irin tsalle Nu'aymah tai ta ɗane wuyan Umm dake tsaye a ƙofar sashenta tamkar wata gunki. Hakan yayi dai-dai da shigowar Baba malam gidan a matuƙar fusace.

         “K!! Nu'aymah! K!! Nu'aymah kina ina?”. Baba malam dake shigowa tun daga gate ya fara kwala ma sunanta kira kamar zai haɗiye harshensa.

       Da sauri Nu'aymah ta saki Umm jikinta na wani irin rawa, dan abin yazo mata a yanda batai zatonsa ba. Akwatinta dake yashe a ƙasa ya shura da ƙafa yana faɗin, “Zoki ɗauka ki koma inda kika fito kafin harshena ya furta miki abinda har ki ƙare rayuwarki zai zame miki musiba”.

        Idanu sosai Nu'aymah ta zaro waje jikinta na sake ɗaukar tsuma. Muryarta na rawar fitar kuka tace, “Abba......” Katseta yay a tsawace yana nuna mata hanya da yatsansa. 

     Ba'ita mai laifin kawai ba, kowama yayi tsuru-tsuru a gidan hatta dasu Abba Rudwan sun kasa magana, dan sunsan ran yayan nasu a matuƙar ɓace yake. Hajjo ce kawai zata iya sakashi ko hanashi a irin wannan yanayin. Gashi kuma bata fitoba, ƙila wanka takeyi.

        “Ba dake nake magana ba ne?!!”.

Fashewa da kuka Nu'aymah tayi ta durƙushe ƙasa. “Abbah wajen waɗanda suka sacenin kakeson na koma?”. Tsaki yaja mai ƙarfi, dan yama ɗauka maganarta raini da iya shege.

          “Lallai Nu'aymah kin girma! Ashe wayonki da iya tsara abubuwa har ya kai haka ƙarfi? Ki sanar mana kinbi saurayi saboda kar a aura miki Abdallah sannan ki dawo mana da wani sabon rainin wayon saceki akayi?. To idan saceki akayi uban wanene ya rubuta saƙwannin da kika barmana? Wanene kuma ya sacekin? Wanda naga ya ajiyeki yanzu shima wanene?. Duk sai ki bamu waɗanan amsoshin muna saurarenki?”.

       Kai Nu'aymah ta shiga girgizawa tana hawaye. “Wlhy Abbah bansan komaiba akai. Bansan su wanene ba? Bansan wanene wanda ya ajiyeninba nima? Sannan ban ajiye saƙon komaiba ga kowa wlhy”.

       “Nu'aymah!!!”. A tsananin tsawace baba malam ya kira sunanta. Sai da hantar cikin kowa ta kaɗa da tsawarsa. Itama tai baya ƙasa wanwar jikinta na ɓari na tsabagen tsorata. Dan bata taɓa ganin fushin mahaifinta irin hakaba duk da tasan yanada zuciya.

           Nufarta yay tamkar wani mayunwacin zaki, sai famar huci yakeyi jikinsa na tsuma.

      Da sauri Abban Abdallah da Abba Mustapha suka sha gabansa yana gab da isa ga Nu'aymahn. Kareta sukayi yanda bazai ko iya ganinta ba balle ya taɓata.

         Sake ɓaci ransa yay, ya kallesu da jajayen idanunsa da ƙwalla suka taru a ciki. kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, ya juya zai zagayesu ya damƙeta.

      Caraf aka riƙe masa hannu. Dan haka ya tsaya cak batare da ya shiryaba. Hajjo data fito yanzun nan saboda tsawarsa da taji ta kalli hannunsa data riƙe da tana sake tamke fuska batare da tayi magana ba.

        A take dukkanin jikinsa yay sanyi laƙwas, sai wata irin zufa data shiga tsatstsafo masa a goshi. Sun kai kusan mintuna biyar a haka ana kallon kallo tsakanin duka ƴan gidanma. yayinda Umm tunda Baba malam ya shigo ta sulale ta koma ciki tana hawaye. 

         Da idanu Hajjo tai masa magana da yaren da tun yana yaro ya haddace sa, kafin ta saki hannunsa a hankali ta nufi Nu'aymah dake durƙushe ƙasa tana kuka har yanzun. su Abbah zagaye da ita suma har yanzun suna bata kariya daga baba malam. Kamata hajjo tai ta miƙar da ita ta rungumeta a jikinta. Nu'aymah ta ƙanƙame Hajjo sosai tana jan numfashi da ƙyar. A hankali kuma sai idanunta suka fara lumshewa, kafin kowa ya farga tama sume.

         Hajjo da taji ta mata nauyi tai ƙoƙarin ɗagota amma ta kasa. Gabantane ya faɗi tace, “Kai Mustapha zoku duba yarinyarnan kamarma bata da rai”.

      Ai kafinma ta rufe baki sun kama Nu'aymah da hanzari. Yaraf tai baya jikin Abban Adawiya alamar dai da gaske bata numfashin. Sake tashi hankalin kowa yayi, duk sauranma suka matso suna ambaton Innalillahi....

      Ɗaukarta Abban su Adawiya yay ya nufi sashen Hajjo sauran biye da shi. Yana kwantar da ita bisa kujera Ahmad na miƙo ruwa daya ciro a fridge. Amsa Abban su Abdallah yay ya zuba a hannu sannan ya shafama Nu'aymah a fuska. Ko motsi bataiba balle ai tunanin farfaɗowar ta. Sake tashi hankalinsu yayi. Ahmad da Malam ƙarami suka durƙusa da saurin kama ƙafafunta suna murzawa, suma su Abba hannayen Nu'aymah suketa faman murzawa. Amma abin tashin hankali ko motsi bataiba har lokacin.

          A yanzu kam kowa ya fara tunanin ciwon Nu'aymahr ne ya motsa, dan haka Abba Musbahu da bai jima da shigowa gidanba yay saurin faɗin, “Inaga a kira Doctor ɗinta, kamarfa ciwontane ya motsa”.

        Cikin kuka Hajjo tace, “Kirashi Musbahu, dan ALLAH ka kirashi da sauri. Innalillahi......... Zainabu karki mutu ki barmu kinji”. Kukan Hajjo ba ƙaramin sake ɗaga hankalinsu yayiba, matan ma sai faman share hawaye sukeyi.


        Duk abinda ke faruwa akan idanun Baba malam ne dake tsaye a jikin daga ƙofar falon Hajjo yana kallonsu. Kallo ɗaya zakai masa ka fahimci yana cikin tsananin tashin hankali. Nu'aymah zuciyarsa ce, yana dannewa ne kawai, amma bazai yuwu ya bari son da yake mata ya hanashi hukuntata akan kuskurenta ba, dan yasan icce tun yana ɗanye ake tanƙwarashi, idan ya bushe karyewa yakeyi.


      Sun cigaba da ƙoƙarin ganin ta farfaɗo kafin Doctor ya iso, sai dai fa ko motsi babu wani sashe na jikinta dake nuna alamar zaiyi ma...........✍

      


Tashin hankali😪, kumuje zuwa.



_____________________

SAHFAT PREORDER!

______________________


        Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.


SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.


Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.


*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*


_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.


Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.


Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.


*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*


_____________________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 

Hafsat miss xoxo🥰

KIBIYAR AJALI......!

      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

   

          Mamu gee🥰

MIN ƘALB!!😋🤗


        Hafsat rano🥰

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


         Bilyn Abdull🥰

SARAN ƁOYE🤗😋


    Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.


*_Typing📲_*


No. 8


...................Doctor na isowa aka maida Nu'aymah bedroom ɗin Hajjo. duk fita sukai suka bashi waje yay aikinsa yanda ya kamata. Sai Abubakar da aka bari kawai dan ya taimaka masa da wani abun idan ya buƙata.

        Sunyi jigum-jigum a falon Hajjo, kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa wadda ALLAH kaɗai yasan minene a cikinta.


       Juyawa baba malam yay a hankali ya fice daga sashen. Sashensu ya nufa dan sai yanzune hankalinsa ya kai ga rashin ganin Umm tare da su. Babu kowa a falon, ya nufi bedroom ɗinta canma babu kowa. Fitowa yay ya nufi nasa ɗakin ko tana can. Sai dai kuma nanma babu kowa. A ɗan ruɗe ya dawo ɗakin Muh'd. Muhammad ɗin kawai ya samu yana canja Uniform ɗin islamiyya dan yanzun suka taso. Baima gansaba, sai da yace, “Muhammad ina Umm ɗinku?”

     Jiyowa Muhammad yay da sauri, fuskarsa da ɗan damuwa yace, “Abba nima ban gantaba, na shiga ko ina bata nan kuma yunwa nakeji”.

       Shigowa sosai Baba malam yay cikin ɗakin idonsa akan Muhammad ɗin. “Yunwa kuma Muhammad? Bakaci abinciba ka fita ne?”.

       “Abba lokacin nasha fura wajen Hajjo na ƙoshi, yanzu kuma zanci”. 

     Kama Hannunsa Baba malam yay suka fita kitchen da tsammanin zaiga Umm a can. Sai dai kuma mai aikinta kawai suka samu tana gyaran kayan miya. Cike da girmamawa ta gaida Baba Malam ɗin. Amsawa yay yana cirar tuffah dake cikin fruit tray ɗin da suke sakawa. Ƙarasawa yay wajen fanfo zai wanke Saude tai saurin faɗin, “Baba malam kawo a wanke”. Baiyi musu ba ya miƙa mata tuffa ɗin guda biyu daya ɗauka. Sake bin kitchen ɗin yay da kallo kafin yace, “Ina Jannat ɗin take na ganki ke kaɗai kina aiki?”.

       Saude data wanko apple ta ɗaura a ƙaramin filet tace, “Nima na shigo ban gantaba, dama naje can ƙasan layine na sayo mata daddawa data bada. To nadawo kuma na duba kamar ta fita, shine nace bara na gyara ko kayan miya kafin ta dawo”. Shiru Baba malam yayi gabansa na faɗuwa. Amma sai ya danne ya kalli Muhammad dake saurarensu. Filet ɗin tuffa ɗin ya miƙa masa yana faɗin, “Karɓa wannan kaje kaci muje salla mu dawo saika zauna cin abincin”.

         Kai Muhammad ya ɗaga masa da amsar filet ɗin. Yaron nagaba yana biye da shi har suka fice. Sake komawa yay ɗakin Umm ɗin dai zuciyarsa na bala'in harbawa. Tsaye ya isketa gaban Wadrobe tana fiddo kaya da alama wanka tayo. Ya sauke ajiyar zuciya da faɗin ‘Alhmdllh’ a fili. Hakanne yasata juyowa da sauri dan bataji shigowarsa ba. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru tana kallonsa kawai.

       “Naje massallaci”. ya faɗa a taƙaice yana juyawa ya fita daga ɗakin. Binsa da kallo Umm tayi harya ɓace mata sannan ta ɗauke kanta hawaye na ziraro mata.


★★★★


        A ɓangaren Hajjo Doctor ya bama Nu'aymah dukkan taimakon daya dace kamar yanda ya saba a duk lokacin da ciwon nata ya motsa. Sai dai yau ta jima bata farfaɗo ba. Dan sai da sukaje sukai sallar magriba suka dawo sannan ya ƙarasa ƴan dabarunsa cikin amincin ALLAH ta farfaɗo.

         Godiya yayma UBANGIJI tare da fita ya sanar musu ta farfaɗo. Dan yau ana idar da salla gaba ɗayansu suka baro massallaci, baba malam ne kawai yay zamansa. Matanma suna idar da sallar duk nan suka sake dawowa harda yaransu da dawowarsu islamiyya sukaji komai.


      Bayan Doctor ya kammala komai ya buƙaci tattaunawa da su Abbah. Da ƙyar suka samu Baba malam ya baro massallaci yazo.

        Doctor ya gyara zamansa cikin girmamawa a garesu yace, “Gaskiya wannan karon jikin Nu'aymah yayi tsamari. Kunsan matsalarta ba'aso abu yana firgitata da tsanani. tsawa da duhu suna gaba-gaba wajen girmama ciwonta da ƙarfafa shi”.

        Hajjo ce tai saurin faɗin,  “Hakane likita, duk munsan wannan, kuma ana ƙoƙarin kiyayewa. Yau ɗinma kuskure aka samu kasan ajizanci na ɗan adam. Yanzu minene mafita?”.

           “To Hajjo ALLAH ya kiyaye gaba, amma kam yau abin yaso yin tsamari sosai a gareta, dan yanzu haka zancen da nake muku sam bata cikin hayyacinta, fatanmu dai ta dawo hayyacinta lafiya batare data manta komaiba ma bayan ta farka”.

       Da matsanancin tsoro suke kallonsa, sai dai kowa ya kasa magana. Da sauri yace, “Bamu da tabbacin hakan, komai na ALLAH ne, mucigaba da mata addu'a insha ALLAHU zata farko cikin ƙoshin lafiya. Dama inada shawara ne, dan tun kwanaki naso zuwa da zancen sai nai tafiya kuma, yau kwanana shidda kenan da dawowa ma, zan kuma iya komawa a koda yaushe dan na samu gurbin ƙaro karatu a ƙasar Australia ne”.

        A tare sukace, Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka ya bada ikon karanto abu mai amfani”.

      “Amin ya rabbi, nagode sosai”.

      Abbah Musbahu yace, “Muna surarenka. Wane shawarace da kai?”.

        “Dama akwai wani likita babba kuma ƙwararre, dan kam ALLAH ya hore masa baiwa ta fannoni da dama inhar a ɓangaren likitancine. To wani abokina ya tabbatar min har masu irin ciwon Nu'aymah yana basu taimako. Matsalar ɗaya ce, shine ganinsa. Ganinsa nada matuƙar wahala dan yana aikine a Nigeria da wajen Nigeria. Ko a yau zai iya shigowa kano ya duba marasa lafiya ya fice, zuwa dare kuma kaji bama ya ƙasar gaba ɗaya”.

            “To ai mu Doctor ko biyansa ya kama muyi sai muyi dan yazo ya duba ta”. Cewar Abban Abdallah.

        “Ai anan gizo ke saƙar Malam. Dan ko nawa za'a biyashi bazaizo gida duba mara lafiya ba. Dolene sai dai mutum yaje yay tanadin ganinsa kamar kowa, zai baka date ɗin da zaka gansa idan har ciwonka yakai shi zai dubaka, idan kuma yaga akwai mafita zai haɗaka da wani likitan da zakaje ka gani. Date ɗin da za'a rubuta maka kuma dole a sannan ne zaka gansa babu alfarma. Kwanaki yaron president ya samu wata babbar matsalar da sai shine ake fatan ya dubasa ko za'a dace. Har jirgi aka aika ya ɗakkosa daga wata ƙasar dan kawai yazo ya dubashi amma yace suje su sai kati subi layi kamar yanda kowa keyi shi bazaije ba. Kuma dole hakan akayi”.

      Babu wanda bai jinjina wannan al'amari ba a cikinsu, sukai shiru kowa na tunanin mafita kuma. Ganin haka Ahmad yace, “To Doctor idan babu damuwa ai muma sai kai mana hanya mubi hanyar data dace ɗin na ganin nasa kawai, ko'a ina yake mu zamu bisa insha ALLAH. Fatanmu dai a dace”.

        “Hakan shine dai-dai. Ga Number ɗaya daga ma'aikatansa zan baku sai ku nemesa, insha ALLAH zai muku ƙarin bayanima fiye da nawa ma, ga kuma ta abokina ma duk zan haɗa muku shima likitane zaku iya neman taimakonsa koda ni na wuce ne”.

      Rubutawa yay ya miƙama Hajjo dake a kusa da shi, ita kuma saita miƙama Baba malan da tun shigowarsa baiyi ko tari ba. Bai musaba ya amsa ya ajiye gefensa da nufin idan ya tashi sai ya ɗauka yaje ya adana. Doctor ya tattare file ɗin bayanan ciwon Nu'aymah waje guda ya sake miƙama Hajjo yana faɗin, “Da wannan zaku gansa dole, dan ƙa'idarsa sai yaga bayanan ciwon mutum na baya inhar ya taɓa ganin likita akan hakan”.

     Nanma godiya suka sake masa. Hajjo ta sake miƙama baba malam. Amsa yay ya saka Numbers ɗin da aka bashi a cikin file ɗin ya ajiye.

     Kasancewar lokacin sallar isha'i yayi duk sai suka fice har Doctor. Bayan an idar da salla Doctor ya sake dawowa tare dasu Ahmad ya shiga ya ƙara duba Nu'aymah. Sai da ya sake tabbatar da komai ya zauna sannan ya fito yay musu sallama akan insha ALLAH da sassafe zai dawo yaga jikin nata. Idan kuma sunga da wata matsala komai dare su kirashi.

     Sun masa fatan alkairi da godiya ya tafi.


_★__★_


      Baba malam bai shigo gidan ba sai kusan goma saura, dan ya tsaya sunyi karatu ne. Sashen Hajjo ya fara shiga ya duba Nu'aymahn. Har sannan barci take, dan haka ya ɗauka file ɗin nata ya fice da shi zuwa sashensu.

      Duk abinda Umm take masa bata fasaba. Yanda kuma bai mata magana akan Nu'aymahr ba itama batace da shi ƙala ba har suka kwanta.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


_______________________

WASHE GARI

_______________


          Alhmdllh Nu'aymah ta tashi jikinta da sauƙi, kuma kamar yanda kowa yay fata bata manta da komai ba kamar yanda Doctor yayta jin tsoro. Hajjo ce ta taimaka mata tayi wanka. Yusrah ta kawo mata abinci tama zauna da kanta ta ringa bata. Ta ɗanci babu laifi, dan Yusrah lallaɓata ta dingayi ita da Hajjo.

     Kamar yanda kowa na gidan yazo ya dubata da safen haka Baba Malam da Umm ma sukazo suka dubatan. Sunji nutsuwa sosai a zukatansu ganin jikin nata Alhmdllh. Sai dai kowansu bai nunaba a fuska, sunma haɗe mata gabas da yamma.

    Hakan ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Nu'aymah yay ba, harta kasa haƙuri ta shiga tambayar Yusrah ko wani abu ya faru bayan barinta gida ne? Dan ita tayi zaton idan ta dawo zataga kowa na murnar dawowar tata. Amma saita samu saɓanin hakan, sai ma kalaman baba malam na jiya keta mata kaikawo a cikin rai.

    Ƙasa Yusrah tayi da kanta hawaye na cika mata idanu, haka kawai ta tsinci kanta da jin kunyar Nu'aymah ɗin mai tsanani. “Yusrah dan ALLAH kimin bayani mana? Ina Yah Ab da Adawiya duk bamma gansu ba”. Nu'aymah tai maganar cikin sanyin murya na alamun rashin jin daɗin jiki.

     Saurin miƙewa Yusrah tayi ta juya mata baya zata bar ɗakin. Nu'aymah ta riƙe hannunta itama da sauri. Hannu Yusrah tasa ta goge hawayen dake rige-rigen sakko mata a kumatu batare data juya ta kalli Nu'aymah ba.

     Dai-dai nan Hajjo ta shigo tare da Doctor da yazo sake zuwa ganin jikin nata.

         “Kai lafiyarku?”.

Hajjo ta faɗa ganin Nu'aymah da Yusrah duk suna hawaye.

         “Ba komai Hajjo”. Yusrah ta bama Hajjo amsa tana zare hannunta daga cikin na Nu'aymah. Kamar hajjo zata sake magana sai kuma tayi shiru suka bama Doctor damar duba Nu'aymahn. Yaji daɗin ganin jikin nata normal, sai dai yanason mata allura yana tsoron rikicinta da zasu kwasa. Nu'aymah ta mugun tsanar allura a rayuwarta, indai akace za'ai mata allura to lallai an taro match kuwa. Dan sai kowa yaji a gidan harma makwafta.

     Kallon hajjo yay murya ƙasa-ƙasa yace, “Hajjo ko za'a kira mana su Ahmad ne kusa. Allura zan mata kinsan kuma sai ansha yaƙi”.

       Sosai hajjo ta waro idanu waje. Taɗan kalli Nu'aymah data kwanta idonta na kallon fanka dake juyawa a hankali. Sake kallon Doctor tayi, itama a hankali tace, “bara dai a dubamin cikin iyayen nasu tunda duk basu fita ba”.

    Kansa ya ɗaga mata ya tashi ya fita falon dan ya haɗa allurar. Itama Hajjo biyosa tayi.


      Kusan mintuna biyar da fitar tasu duk suka dawo harda Baba malam dake cikin shirin fita. Batare da yayi maganaba ya kama Nu'aymah da kansa ya tayar zaune. Kallonsa take cike da so da ƙaunar mahaifin nata. Amma yanda yay kicin-kicin da fuska sai yake ƙara tsoratata. Ganin yanda ya jata jikinsa ya rungumene ya saka ƙirjinta bugawa. Dan tun tana yarinya inhar taga ya mata irin wannan rungumar to lallai allura za'a mata. Saurin ɗagowa tai ta kalli Doctor daya ɓoye hannunsa a baya. Jikinta ne ya fara tsuma, zatai magana Baba malam ya balla mata hararar da ta sakata maida kanta jikinsa ta kwantar.

      Rikici sosai akasha kafin Doctor ya mata allurar, ba ita kanta ba har baba malam da hajjo masu riƙetan saida ta tarama gajiya. Doctor kam har ƴar zufar wahala yakeyi a goshi, a ransa yana sake jinjina daru irin na Nu'aymah.

        Tunda baba malam ya maidata ya kwantar ajiyar zuciya kawai taketa faman saukewa hawaye na zirarar mata da gudu. Hajjo ta zauna inda baba malam ya tashi ta ɗago kan Nu'aymah ta aza bisa ƙafarta tana shafa mata dogon gashinta.

       Sauran magungunanta Doctor ya ajiye yayma hajjo sallama suka fice shi da Baba malam.

        Hajjo ta jima tana lallashin Nu'aymah kafin ta samu tayi shiru barci ya saceta. Amma har cikin barcin tsabar rikicinta ajiyar zuciya taketa faman saukewa a jajjere. Haka dai hajjo ta lallaɓa ta kwantar da ita da gyara mata kwanciya ta tashi ta fice.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


_______________________

______________

DUBAI

________


              Amarya Adawiya da ango Abdallah sun isa ƙasar dubai lafiya, sai dai gaba ɗaya ya canja tsarin daya shiryama kansa da Nu'aymah. Ya dai kama musu babban hotel kuma a ɗaki ɗaya. A randa suka isan kuma ya sace wayar Adawiya ya ɓoye batare data saniba.

     Ita dai duk abinda yake mata bai ɓata mata rai, haɗe fuska da ƙin mata magana tunda suka taho baisa taji haushinsaba balle sonsa ya ragu mata a zuciya. Saima ƙaruwa da ya sakeyi tanajin kamar ta haɗiyesa.

     Gadon ya bata ta kwanta shi kuma yasa bargo a ƙasa yay kwanciyarsa. Da asuba ya rigata tashi, yay wankansa yay shiri tsaf. Sai da ya kammala komai sannan ya tadata. Mamaki ya kamata matuƙa ganinsa cikin shirin fita, sai dai kuma babu fuskar tambayarsa.

       Murya a shaƙe yace, “Duk abinda kike buƙata ki kira zasu kawo miki”. Daga haka bai sake tofa komaiba yay ficewarsa daga ɗakin yaja mata ƙofar. Ta jima zaune a wajen tamkar wata gunki har gari yay haske sosai kafin ta sakko jiki a sanyaye taje tayo alwala. Duk da hakan da yay mata babu daɗi sai bataji haushinsaba. Haushin Nu'aymah nema ya kamata, dan a ganinta zaman dataine cikin zuciyarsa yasa baya ganin kowa da gashin mutunci sai ita. Aiko ta ɗauki alwashin sai ya manta wata banza Nu'aymah a zuciyar tasa har abada balle kuma wata Yusrah da tasan bata a gabansa.


“Hajiya Adawiya, ke dai kike kiɗanki kike kuma rawarki🤣😏”.


               Haka ta yini ita kaɗai, daga kallo sai cin abinci da kwanciya. Gashi ta nema wayarta ta rasa, sai kawai tunaninta ya bata kota barta a gidane kokuma ta yaddata a jirgi Yah Abdallah ya ɗauke mata. Ta barsa akan idan ya dawo zata tambayesa.

         Abdallah bai dawo hotel ɗinba sai kusan 11 na dare, harkokin kasuwancinsa ya yini yi hankalinsa kwance. Baiyi zaton iske Adawiya ido biyu ba. Amma a mamakinsa sai ya sameta zaune dirshen tana kallo. Sannu da zuwan data masa kawai ya amsa ya ɗauke kansa. Ya ɗauka kayan barci ya nufi bathroom. Tana nan zaune ya fito tsaf da shi. Nanma bata ishesa ko kalloba ya zauna a ɗaya daga rukunin kujerun ɗakin yay kira a kawo masa tea. Babu jimawa akai knocking ƙofar. Adawiya ta miƙe jiki na ɓari zataje ta buɗe ya ɗaga mata hannu. Da kansa ya tashi yaje ya amso ya dawo yay zaman sha bayan ya kunna laptop.

       Sunja tsahon lokaci zaune, Adawiya nata faman kallonsa kamar ta samu television, shiko aikinsa yakeyi tamkarma ya manta da ita a cikin ɗakin.

      “Uhhm Yah Ab dan ALLAH ko kaga wayata?”. Cak ya tsaya daga aikin da yake yana sake tsuke fuska batare da ya kalleta ba. Ba komai ya jawo hakanba sai Yah Ab datai kiransa da shi. Dan Nu'aymah itace ta fara kiransa da suna har kowama ya ɗauka. itace kuma ke kiransa hakan a koda yaushe. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ya girgiza mata kansa kawai ya cigaba da abinda yakeyi.


★★★★


        Haka suka cigaba da tafiya a kwanakin da duk suka gabata na barinsu ƙasarsu. Adawiya duk a takure take, dan Abdallah kullum da sassafe yake fita, bazai dawoba kuma sai sha ɗaya. amma soyayya ta rufe mata idanu ta kasa jin zafin hakan da yake mata.

     Shiko gaba ɗaya ya ɗauketa yasa a kwandon shara ya maida hankalinsa ga kasuwancinsa kawai, dan a maimakon kwana goma da ya shirya yi a ƙasar ya maidashi kwana shida zasu wuce.


         Tun a randa Nu'aymah ta dawo gida yay mafarkin hakan da daddare, aiko tunda asuba yay kiran Number Ahmad. Cike da farin ciki Ahmad ɗin ya sanar masa komai, dan dama shima yana da shirin kiran nasa, so yake kawai jikin Nu'aymah aga yanda zai kasance a washe garin.

            Karan farko da tun faruwar al'amarin nan Abdallah yay sassanyan murmushi hawayen farin ciki na cika masa ido. Jiyake tamkar an tsundumasa aljanna yau. Yana katse kiran ya kira Momy itama. A lokacin dawowarta kenan daga sashen hajjo taje ta duba Nu'aymah itama.


        Bayan sun gaisa cike da so da ƙaunar juna irin ta ɗa da uwa, ya tambayi lafiyar kowa a gidan sannan cike da zumuɗi yace, “Momy ashe Nu'aymah ta dawo?”.

       Jimm tayi kamar bazata amsa masaba, sai kuma tace, “Uhmm! ta dawo jiya”.

        “Kai Alhmdllhi Momy, yanzu zanje na saya mana tickets kuwa mu dawo, in ALLAH ya yarda wannan karon bazan sake ta sake kuɓuce minba Momy, a yau ɗin nan ina durowa koda magriba ne sai an ɗaura mana aur......”

         “Kai! Shashasha dakata min. To idanma mafarki kake maza ka farka ka dawo hayyacinka. Wai kai Abdallah wane irin sakaran banzane halan? Ka fita idanuna tunkan na rufesu da kai a ciki wlhy. Bara makaji na maka mai kankat. Wlhy tallahi idan naga ƙafarka a ƙasarnan batare da ni nace kazoba ALLAH ya isa ban yafe maka ba.....”

         “Momy!!” ya faɗa cikin tsananin tashin hankali.

     “Yes! Abinda kaji shi na faɗa. Idan zakai haƙuri da waɗanda aka baka kayi. Hauka akeyi da za'a manna maka mata har uku ƴan family ɗaya uban ƴan son zuminci? Itama Yusrahn ina nan ina nema maka hanyar barinta wlhy. Adawiyar dai ta tsira tunda ALLAH ya sota ka baro ƙasar da ita da wuri. Idan suma sunada nasu zaɓin nima inada nawa ai, amma aka nunamin fin ƙarfi da ƴan uwantaka. Kai kuma shashasha da yake baka kishina hakan ko damunka bayayi. To wlhy kama cire wannan tunanin a ranka. Kuma ko a waya ka kira wani cikin iyayenku kace a ɗaura maka aure da Nu'aymah shima ban yafe makaba. Idan wannan maganar tasa ka kirani karka sake kirana”.

    Ta katse wayar batare da ta jira cewarsa ba.


      Sosai jikin Abdallah ke tsuma. Haƙoransa har wani bada sautin ƙara suke saboda rawar da bakinsa keyi. So yake ya faɗi sunan Momy amma ya kasa haɗa kalmar waje guda dan tsabar rikicewar da yayi.

      “Yah Ab lafiya kuwa?”. Adawiya ta faɗa tana ɗaura hanunta saman kafaɗarsa. A fusace ya ɗago ya hankaɗe hannun nata tai taga-taga ta faɗa saman kujera. Ko kallonta baiyiba yay wurgi da wayarsa ya nufi bathroom da sassarfa. Yana shiga ya sakarma kansa shawa ruwan na saukar masa a jiki batare da ya cire kayaba.

     Kalmar ALLAH ya isar Momy ce keta masa kai kawo a zuciya har kana hango sama da ƙasan da ƙirjinsa keyi na.


       Adawiya kam tana ganin ya shige ta miƙe idanunta cike da hawaye. Da ƙyar ta ɗangyasa ƙafarta data buge da centre table ta isa inda yay wurgi da wayarsa. Addu'a take ALLAH yasa babu lock. Cikin sa'a kuwa babun, sai dai hoton data fara cin karo da shi a fuskar wayar ne yasata jin wani irin zafi tamkar an soki zuciyarta da mashi.

       Hoton Nu'aymah ne da sukayi ranar walimar gama makarantarsu. Tayi masifar ƙyau a hoton, dan ɓakar doguwar rigar data saka na Material ɗinkin yay masifar zama mata a farar fatarta. Ga idanun nan sun bala'in fitowa cikin kwalli har wani ƙyalli suke saboda haske. Tayi ɗan murmushinta loɓar kuncinta data gemunta ta fito raɗam. Sosai Adawiya ke faman taunar lips da ƙarfi tamkar zata hudasu, duk da tasan hoton tunkan shi Abdallah ma ya gani hakan bai hanata jin zafi mai tsanani ba. Da kyar ta iya danne ranta ta shiga dan son ganin dawa yay waya. A fili tace, ‘Momy!. To mita gaya masa daya fusatashi haka har yake neman karya ni a banza?’. Bata da mai bata wannan amsar, gashi kuma batasan inda wayarta takeba balle ta kira wani ta tambaya. Tanajin tsoron yin amfani da tasa kuma yazo ya kamata. Da sauri ta ajiye wayar inda ya jefar jin za'a buɗe ƙofar bayin.

       Tsaye yay cak a ƙofar bayin yana binta da kallon tuhuma fusatar zuciyarsa na daɗa bayyana saman fuskarsa.............✍


   

        Kuyi haƙuri, jiya man kaina ne ya tsiyaye tas yasin na kasa typing😖.



_____________________

SAHFAT PREORDER!

______________________


        Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.


SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.


Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.


*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*


_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.


Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.


Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.


*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*


_____________________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 

Hafsat miss xoxo🥰

KIBIYAR AJALI......!

      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

   

          Mamu gee🥰

MIN ƘALB!!😋🤗


        Hafsat rano🥰

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


         Bilyn Abdull🥰

SARAN ƁOYE🤗😋


    Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.


*_Typing📲_*


No. 9


.................Sosai Adawiya ta tsorata da mugun kallon da Abdallah ke jifanta da shi. Jan jikinta ta farayi baya a hankali ganin ya fara takowa yana nufota. “Y...y..Yah Ab wlhy babu abinda nayi da wayarka, Please dan ALLAH karka dak......”

     Ta kasa ƙarasawa saboda kiran wayar da akayi. Shima cak ya tsaya daga bin nata yana kallon wayar. (Sweet Momy) ya hango ɓaro-ɓaro yana yawo akan fuskar wayar kamar yanda yay saving. Iska mai zafi ya busar daga bakinsa yana lumshe idonu. Tsinkewa wayar tayi aka sake kira. Yanda bai motsaba haka ma Adawiya ta kasa motsawa. Kallon wayar take kawai daga nesa tamkar yanda yake kallonta shima. Sai ka ɗauka gamo sukai da bomb.

      Sai da Momy ta jera ma Abdallah kira har biyar bai ɗaga ko guda ɗaya ba a ciki. Daga ƙarshema saiya nufi wayar a fusace ya takata da ƙafarsa. A take screen ɗin ya shiga bada sautin fashewa.

        Baya Adawiya tai da sauri tana mugun waro idanu da buɗe bakin mamaki. Al'amarin bai ƙara firgitataba sai da taga ya ɗauka wayar ya zare sim card ɗin ya karyashi biyu. ya kuma nufi toilet ya jefashi yay flushing a take.

     Da sauri Adawiya ta koma inda take da ta tsaya zuciyarta na mata wani masifar bugu, ga wani irin tsoron Abdallah daya sake shigarta mai ƙarfi. Sam batai tunanin yanada zuciya irin hakaba. Duk da tasan ƴan gidansu kowa yanada wannan shegen zuciyar amma tazata tashi mai sauƙice ganin yanda bata cika ganin fushinsa ba. Ta gabanta yazo ya fice ko kallon inda take bai sake yi ba. Ya bugo mata ƙofar da ƙarfi har saida ta zabura jikinta na karkarwa........


*_NIGERIA_*


             Cike da mamaki Momy ke kallon wayar tata tamkar idanunta zasu zubo ƙasa. A ranta take raya ‘To miya samu wayar Abdallah? Ta shiga bai ɗagaba, daga ƙarshema wayar ta jita a kashe’.

       “Momy lafiya?”. Omar daya shigo falon ya faɗa idanunsa akan Momy dake tsaye tana ta faman juya waya.

     Saurin ɗagowa tai ta kallesa, sai kuma cikin sanyin murya tace, “Omar yayanku ne wlhy, ya kirani bana kusa inaga ko cikin su Amal wani ya ɗaga, shine yanzu dana fito naga alamar ya kira an ɗaga saina kirashi. Amma har missed calls biyar na jera masa bai ɗaga minba, yanzu daga ƙarshema wayar a kashe take”.

        Murmushi Omar yayi yana zama da faɗin, “Oh Momy ƙila to baya kusa ne, kinsan hidimar Yah Abdallah ba ƙarewa takeba. Nasan zai kiraki shima”.

       Kai Momy ta girgiza masa, “Omar ba rashin ɗaga kiran bane damuwata, jin wayar a kashe bayan kuma duka kiran danai sun shiga”.

       “Momy Please ki kwantar da hankalinki, nasan insha ALLAH babu wata damuwa. Koma baida cajine kokuma network”.

    Kamar zata sake magana sai kuma tai shiru taɗan jinjina kanta. Tashi tai ta maida wayar a caji dan fama cajin ta saka ta shiga kitchen tun ɗazun. Yanzuma tana maida wayar a caji saita koma kitchen ɗin suka cigaba da aiki ita da masu aikinta su biyu tabar Omar daya kwanta cikin kujera yana canja chennal a falon. Sai dai kuma abin yaƙi barin ranta sam.


        Har dare Momy na jiran kiran Abdallah shiru, ta kuma sake nemansa itama amma har lokacin wayar switch up. Tun tana danne damuwarta harta bayyana fili. Abbah da tun ɗazun yake kula da yanayinta ya tambayeta ko lafiya?. Batai nauyin bakiba tai masa bayanin abinda ya faru.

     Shi dariyama ta bashi ganin yanda duk tai wani iri kamar ance Abdallahn ya rasu ne, dan haka yaɗan murmusa yana girgiza kansa, batare da ya ce mata komaiba ya cigaba dacin tuwonsa. 

        “Abban Abdallah dan ALLAH ko zaka kira min shi da wayarka?”. Sake kallonta yayi da ƙyau, sai kuma yay gyaran murya da ɗauke idonsa. “Khadija ki rage ruɗiyarnan taki, yanzu dan ALLAH Abdallah ƙaramin yarone halan? Maybe baida caji ne kokuma ya shiga wata sabgar. Kiyi haƙuri kiga zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu idan bai kiraki ba”.

       A sanyaye tace masa “to” kawai badan hakan ya mata daɗiba. Sai ma ta tattare kwanikan daya kammala cin abincin ta fice da su. Saida takai kitchen sannan ta nufi ɗakin su Amal. Zaune ta iskesu suna karatu, Amal na ƙarama su Imran. Duk shiru sukai suna kallonta. Itama kallon nasu takeyi.

      “Amal wanene a cikinku ya ɗaga kiran yayanku ɗazun?”.

      “Kira kuma Momy? Wlhy bansan Yayah ya kira wayabama ni, dan tun ɗazun danace miki zanje na sake duba Nu'aymah ina can wajenta ɓangaren Hajjo ni da Yusrah. Amma wani abune ya faru?”. Kai momy ta girgiza mata tana kallon su Imran suma. Da ɗai-ɗai suka shiga bata amsar suma duk basu baneba.

     Kanta taɗan dafe zuciyarta na neman faɗawa a ruɗani, lallai yaran sunada gaskiya, dan idanma tai dubi da lokacin da Abdallah ya kira ai duk basa gidan ma suna islamiyya. Kasancewar yau lahadi sunayin harta safe zuwa uku a tashesu, to indai suna garin suma yaran suna zuwa anan ma. Kuma tunda safen duk suka fita. Amal ce kawai batajeba saboda ta tashi da ciwon mara, daya ɗaga matane tace zataje ta duba Nu'aymah. Sai da ta fita da kusan awa ɗaya ma Abdallah ya kira.

      Ficewa tai taja musu ƙofar tanason tunano ko wani ya shigo a wannan lokacin, to amma kuma babu wanda ya shigo ɗin, daga ita sai ƴan aikinta. Abba ma baya nan, Omar ma ganin datai masa bayan kiranne ya shigo gidan, dan tare suka fita da baba malam tunda safe.


              Momy da taga tunaninta na kaita wasu nazari daban sai kawai ta ajiyesa gefe, ta barsa akan uzirine yayma Abdallah yawa. Waya kuma ƙila sanda yake kira cikin sauran ƙannensa yaran gidan wani ya shigo ya gani ya ɗaga. 

     Washe gari da safe batabi takan kiran Abdallah ba ta cigaba da hidimominta kamar yanda ta saba. Abin mamaki kuma har dare bai kirantanba, sai itace dai da dauriyanta ya gaza ta nemesa kusan taƙwas na dare. Switch up dai ɗin yauma.

            Ganin yanda ta zuba tagumi yasa Abba jin tausayinta. Wayarsa yasa ya kira Abdallahn, amma sai yaji layin a rufe. maida kiran yay a ɗayar Number Abdallah ta business. Bugu biyu kuwa ya ɗaga. Bayan sun gaisa yace masa ga Momy.

       Jimmm Abdallah yay kamar bazaice komaiba, sai da Abbah yace, “Nace ga Momynku ko bakajiba?”.

         “Amm sorry Abbah network ne, bata to”.

      Miƙama Momy Abbah yayi, ta amsa zuciyarta na mata sanyi, dan tana matuƙar ƙaunar Abdallah sosai a cikin ƴaƴanta, sai dai tana ƙoƙarin dannewa gudun saka ruɗani a tsakanin ƴaƴanta.


______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   


            Da ƙyar Abdallah ya danne zuciyarsa ya gaida Momy da fuskarta ke shimfiɗe da murmushin farin cikin jinsa. Ta amsa masa cike da kulawa tana tambayarsa yaya suke? Ina Adawiya?.

           Muryarsa a ɗan cinkushe yace tayi barci, shima shirin kwanciya yakeyi.

           “To Alhmdllh tunda dai lafiya kuke. amma jiya miya samu wayarkane? Na kira har sau biyar baka ɗaga ba, daga baya kuma saima naji switch up”.

           Ba ƙaramin haushine ya kama Abdallah ba dajin maganar Momy, bayan sharaɗin data gindaya masa mai ƙarfi akan abinda yake tsananin so shine kuma zata kirasa?, yanzu kuma dan taga tana kusa da Abbah take nuna kamar batai komaiba. To mizata faɗa masa bayan wanda ta faɗa masan kuma?............ 

       “Abdallah lafiya kuwa?”. Momy ta katse masa tunani. “Babu komai Momy, wayarce ta faɗi a cikin ruwa bayan mungama waya jiya shiyyasa”.

         “Abdallah ai ni bamuyi way.......”

Zare wayar Abba yay daga kunnen Momy yana faɗin, “Haba Khadijah tunda kinji lafiyar tasu ya isa haka. Bakiga dare yayiba ne? Yanzu kuma Abdallah yanada iyali”.

          “Afuwan Abban Abdallah na shafa'ane wlhy. Ni saima naji muryarsa kamar wanda bayajin daɗi”.

      Kallonta Abba yay sosai, sai kuma ya matsota jikinsa ya gwargwaɗa mata magana a kunnenta. Idanu ta ɗan zaro waje, sai kuma tai saurin miƙewa tana kare fuska da hannu alamar maganar tasa ta bata kunya.

     Murmushi Abba yay yana binta da kallo harta shige toilet. Yaɗan girgiza kansa yana gyara kwanciyarsa.


________________


          Jikin Nu'aymah yayi sauƙi sosai Alhmdllh, sai dai har yanzu bata koma sashensu ba tana sashen hajjo. Tana dai zuwa ta gaishesu da safe, ta kuma taya Umm aiki kamar yanda aka horesu. Babu wanda yay mata maganar Yah Ab a gidan, itama tayi ƙoƙari ta danne tana jira taji daga garesu kamar yanda Yusrah ta bata shawara data dameta da tambayar yanda akayi.


       Kwana biyu da samun lafiyar Nu'aymah su Momy sukai shirin komawa Abuja saboda karatun yara. A wannan karon Nu'aymah jitai batason tafiyar su Yusrah da Amal, dan suna ɗauke mata kewar Adawiya sosai. Tasan kuma idan suka wuce zata koma ita kaɗaine babu wani abokin ƙiriniyarta kamarsu a gidan, daga yayu sai ƙanne sai iyaye.

        Babu yanda ta iya, a washe gari su Amal suka fara wucewa Lagos da safe. Da yamma kuma su Yusrah. Nu'aymah harda hawaye. Hajjo da taji tausayinta har tayi tunanin ko Nu'aymah tabi cikinsu Yusrahn, sai kuma ta tuna ashe akwai shirin zuwa ganin Doctor da sukeyi. Zama tayi taita lallashinta harta saki jikinta, yayinda su Hajarah da sukazo sashen Hajjon suka ɗan rage mata kewar tafiyarsu Amal ɗin.


★★★★★★


           Kwanaki sun shuɗa, jikin Nu'aymah yayi garas, gidan ya koma kamar da sai su kaɗai. itama harma ta tattara ta koma ɗakinsu ita da Adawiya dake a sashensu. Sosai takejin kewar Adawiya, musamman ma idan tazo kwanciya ko zata shiga toilet. Dan ƙa'idane kullum sai sunyi faɗa akan bargo da filos, hakama shiga wanka sai sunyi faɗa. Haka sabo yake turken wawane.

       A yanzun kam sai Muhammad ƙaninta ya zame mata abokin hira. Daya dawo makaranta koda yaushe suna tare, duk da dai ta dage wajen maida hankali a karatunta na islamiyya itama. Dan a ɗan tsakanin nan ba ƙaramin ƙoƙari takeyi akan haddar Qur'aninta ba. Ga sauran littatafai ta dage sosai suma.

      Wannan karatun shine ya ɗauketa busy matuƙa. Tunma rashin sakewar da su Umm suke mata yanzu yana damunta har abin ya fara raguwar mata a rai. Dan tasha tambayar Umm ɗin kota musu wani laifine?. amma sai Umm ta shashantar da zancen taƙi bata amsa, haka shima Baba malam baya cemata komai akan hakan. A yaran gidan ma duk wanda taima tambayar ina Adawiya taje? Sai suce mata makaranta, Yah Ab kuma ya koma Saudia.

      Takanyi shiru taita tunanin miyasa  za'akai Adawiya makaranta ita kaɗai a barta? Bayan kuma tunda suka taso komai tare sukeyi, makaranta da komai da komai tare ake sakasu, kuma tare ake musu komai. Wannan tafiya makaranta da taji na Adawiya saida ya sakata kuka, daga ƙarshe ta haƙura da fatan ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Tana kewar Yah Ab sosai a zahiri da baɗini. Gashi yanzu bata da waya, ta kuma kasa aron ta wani ta kirashi koda ta Umm ce. Dan da idan tanason suyi magana wayarta babu caji data Umm take amfani. Shima daya kira yaji bai sametaba zai kira Hajjo ko Umm a bata. Amma a wannan karon ganin shima ko sau ɗaya bai nemeta ba sai al'amatin ke ɗaure kanta da bata mamaki. Da taga dai zuciyarta na neman ƙuntata sosai sai taje ta tsare Hajjo da tambaya tana kuka.

       Hankalin Hajjo ya tashi sosai. Ta zauna tana lallashinta amma Nu'aymah sai taƙi saurarenta. Tana cikin darzar kukan Baba malam ya shigo sashen hajjon da daddare bayan ya taso daga wajen karatu a massallaci.

         Tsawa yayma Nu'aymah amma ba wadda zata sakata firgitaba. Tai saurin nutsuwa hawaye na sake rige-rigen sakko mata a kumatu.

       “K wai kin koma jaririyane a gidan nan yanzu? Da zaki zauna kitama mutane kukan banza da wofi. Ki fita idanuna Nu'aymah tunkan na saɓa miki. Bake kika zaɓama kanki hakanba da kanki? To daga yau na baki sati biyu kima shi wanda kika gudu dominsa magana ya turo iyayensa”.

         Cikin tashin hankali Nu'aymah ke kallon Baba malam. Bakinta na rawa tace, “Abbah wlhy ban guduba, dan ALLAH ka saurareni na faɗa maka yanda akayi”. “Bana buƙatar jin komai daga gareki Nu'aymah, dan saƙwannin da kika bar mana sun isheni dukkan amsa. To kin samu yanda kikeso. Kinso tozartamu ALLAH kuma ya hana faruwar hakan ya rufa mana asiri. Abdallah ne dai kince baƙyaso, ALLAH kuma ya canja masa da waɗanda suka fiki alkairi, sai kima wanda kikeson magana ya fito a aura masa ke kuje ku ƙarata”.

      “A....Ab....Abbah!” ta kira sunan Baba malam bakinta na rawa da jikinta. Sosai kalamansa suka nema zautata. ‘Yah Ab ɗinta ne yay aure da wata ba itaba?. Kai ina bazai yuwuba ma’. Tai maganar a fili tana kallon Hajjo dan baba malam tuni yay ficewarsa ma.

      Kamota Hajjo tayi ta rungume tana lallashinta. Tausayinta na ratsata. “Hajjo dan girman ALLAH kimin bayani, wlhy na kasa fahimtar kalaman Abbah gaba ɗaya. Da gaske yake Yah Ab yayi aure? Ya auri wata ba ni Nu'aymah ba?. Hajjo faɗamin dan ALLAH, taimakeni ki faɗain dan girman ALLAH hajjo”.

          “Ya isa haka Zainabu. Ki nutsu na miki bayanin komai to kinji”.

     Da sauri Nu'aymah ta shiga ɗaga mata kai tana share hawayenta da hannaye biyu. Hajjo ta ruƙo hanun nata, cikin nutsuwa tai mata bayanin komai daya faru a ranar bayan an wayi gari babu ita a gidan. Saƙwannin data ajiye musu akan ita ta tafi batason Abdallah sai Ameer.


_

_______________________


                 “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Mike shirin faruwa dani ni Nu'aymah? Hajjo wlhy kinji na rantse miki bani nabar saƙon nanba. Kuma Ameer da ake magana akansa ni babu abinda ya taɓa haɗani da shi sai sako da Yah Abdallah ke bashi yana kawomin. Rabon kuma dana sake ganinsa wlhy anfi wata huɗu Hajjo”.

        “Ah ah! To amma shi kuma Abdullahin yace bai san Ameer ɗinba, bai kuma taɓa aiko wani wajenki ba sai Ahmadu”.

           “Bai taɓa ba Hajjo? Shi Yah Ab ɗin da kansa yace haka kuma?”.

          “Sosaima kuwa, a gaban kowama ya faɗa a randa al'amarin ya faru. Amma kwantar da hankalinki, Zainabu nima dai al'amarin nan ya ɗaure min kai matuƙa, yanda nasan kike da Abdullahi tayaya zaki aikata wannan abun? To amma iyayenki duk sun kasa fahimtar akwai wani ɓoyayyen al'amari daya faru a wannan ranar, musamman ma ɗan malam daya ɗauki zafi sosai akan al'amarin”.

         “Hajjo dan ALLAH ki taimakeni, wlhy inason Yah Abdallah fiye da yanda kowa yake tunani, dan ALLAH ku tausaya mani karna rasashi hajjo. Idan na rasashi mutuwa zanyi......”

        “Bazaki mutuba Zainabu kinji, ki kwantar da hankalinki muyita addu'a ALLAH na nan, yana sane da komai kuma shine maiyin maganin komai”.

       Kai Nu'aymah ta ɗagama Hajjo dake share mata hawaye, ta kwantar da kanta a jikinta saboda kanta dake wani irin bala'in sara mata kamar zai tsage. “Hajjo kaina”. Hankalin hajjo ne ya sake tashi, dan sam ba'ason ciwon kai ga Nu'aymahr, daboda ciwonta. Saurin tada ita tayi daga jikinta ta kwantar da a kujerar tana faɗin, “Ina zuwa, bara na amso miki maganinki kisha”. 

        Hajjo da kanta ta nufi sashen su Nu'aymah dan yaran duk basu shigoba daga ita sai Nu'aymah ne kawai. Baba malam da Umm suna zaune a falo ta shigo, Muhammad na gefe yana homework.

        Da sauri suka shiga tambayarta ko akwai abinda take buƙata?. Fuskarta babu ko ɗigon walwala tace su bata maganin Nu'aymah kanta ke ciwo. Ba ƙaramin faɗuwa gaban Umm yayi ba, amma saita danne ta tashi taje ɗakin Nu'aymahn ta ɗakko ɗan box ɗin da magungunanta ke a ciki ta kawoma Hajjo. Tanason taje taga mike faruwa da ɗiyar tata amma tanajin nauyin hakan. Ga baba malam yay kamar abin bai damesabama, ya cigaba da shan fruit salad ɗinsa hankali a kwance.

     Hajjo dai batabi takansuba ta amsa tai ficewarta. Da kanta ta bama Nu'aymah maganin, sannan ta kamata ta kaita bedroom ɗinta ta kwantar. Cikin amincin ALLAH babu jimawa barci yay gaba da ita.


          Washe gari da zazzaɓi Nu'aymah ta tashi ga ciwon kai. abinda ya tada musu hankali Doctor ɗinta yayi tafiyar da yace, gashi kuma basu nema wancan likitanba. Andai kaita asibiti wani likitan daban ya dubata, yaɗan mata abinda zai iya ya turasu asibitin dawanau. Kamar koda yaushe Baba malam yaƙi yarda a kai Nu'aymah dawanau, dan acewarsa yarinyarsa ba ciwon hauka take ba. Yasan dai ance tanada matsala a ƙwaƙwalwa. Hakan yasa ya ɗakko file ɗin Nu'aymah da shirin neman wancan Doctor ɗin. Amma abin mamaki da al'ajabi babu takardar da Numbers ɗin take. Anyi ɗai-ɗai da file ɗin babu ko alamar takardar. Kamar wasa aka bincike littatafan baba malam dake tare da file ɗin tas babu takardar dai.

     Wannan al'amari ba ƙaramin ɗaure kan kowa yayiba a gidan. Musamman da ya zam agaban kowa Doctor ya bada takardar da file ɗin. Wannan al'amari ya sake ɓata ran baba malam matuƙa, amma jarumar fuskarsa taƙi nuna hakan. Sai Hajjo ce keta masifa kamar zata haɗiye harshenta. Dan wannan ɗauke takardar ya sake tabbatar mata da akwai mai yin ƙulle-ƙulle a gidan da gaske. Sai dai yanda kowa ya nuna damuwarsa akan al'amarin baka isa nuna zarginka kai tsaye akan wane ne ɗin ba.


_____★_____


               “Maganar gaskiya al'amarin gidannan ya fara bani tsoro Abban Nu'aymah. Anfa daɗe ana ruwa ƙasa na shanyewa, dolene a wannan karon nasan wanene ke mana SARAN ƁOYE. Tunda har aka iya toshe hanyar neman lafiyar Nu'aymah lallai za'a iya kashe mana ita ma”. Umm tai maganar hawaye na zuba mata masu zafi.

          Zama baba malam daketa kai kawo a ɗakin yay kusa da Umm, ya kafeta da idanunsa da sukai jajur shima saboda damuwa. “Jannat idan munce zamu ɗauki mataki, akanwa zamu ɗauka? Akan kuma mi?”.

       “Amma Abbah Nu'aymah karka manta musabbabin ciwon Nu'aymah fa faɗo da ita akai daga kan gado tun tana jaririya, kanta ya bugu ta samu ciwo a ƙwaƙwalwa. Badan ALLAH ya taƙaita wahalaba da zata tashine cikin halin rashin hankali kamar yanda Doctor ya sanar mana. Addu'a da hikimar UBANGIJI ce ta cigaba da jagorancin lafiyar Nu'aymah hartakai wannan lokacin cikin hankalinta, sai dai idan ciwon ya motsa tasha wahala. Tun Nu'aymah batasan ma'anar magani ba ake ɗura matashi a ciki, kanaji kwanaki badan ALLAH yasa Doctor ya farga ba hantarta fa harta harbu da ciwo saboda yawan shan magani. Abban Nu'aymah baka tunanin game da al'amarin aurenan akwai wani abu da bamu hasasoba kuwa?”.

           “Kiyi haƙuri Jannat karmu zargi kowa akan al'amuranmu, mu daure mucigaba da ɗaukar komai akan jarabawa ne. Duk abinda yay farko nasan zaiyi ƙarshe. Da ALLAH na dogara game da lafiyar Nu'aymah nasan kuma shi mai jine mai kuma ganine. Indai bamu da haƙƙin kowa ALLAH bazai bama kowa damar shiga haƙƙinmu ba. Ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU zan sake samo Number likitan nata, dan mantawama nai nace masa idan ya tafi ya kiramu”.

           Kanta ta jinjina masa hawaye na cigaba da sauka mata. Ya saka hannu ya share mata yana murmushin da shima iyakarsa laɓɓansa ne kawai. Shi kaɗai yasan mi yakeji a ransa. Yana dai ƙoƙarin dannewane dan yasamu Umm ta kwantar da nata hankalin kodan hawan jininta............✍



_____________________

SAHFAT PREORDER!

______________________


No. 10


________________________

*ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE* 


       *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*  domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._*

     _________________________


.............Yau Nu'aymah ta tashi jikin nata daɗan dama, sai dai rashin ƙarfin jiki. Tunda Ahmad ya tafi raka Hajjo asibiti ganin Doctor saboda ƙafarta saita dawo sashensu ta kwanta. Barci tai sosai dan har sai gab da azhar ta tashi tai wanka. Shiri tai da ɗan sauri-saurinta ta fice zuwa ɗakin Umm, dan wani irin maitan awara takeji. Babu kowa a ɗakin, sai gyara da yasha yanata uban ƙamshi. Tai murmushi da faɗawa saman gadon ta kwanta tana mai sake shaƙar turaren wutar da ƙyau cikin hancinta. Tana masifar son ƙamshi a rayuwarta. Shiyyasa turare kwana kaɗan yake mata ya ƙare. Ga baba malam da Yah Ab sun mugun ɗaure mata ƙugu wajen siya mata. Sam basa gajiyawa. Kafin wani ya ƙare an saya mata wani. Ga khumra da Umm itama take bata ita da Adawiya. Tun Adawiya bata damu da ƙamshiba harta fara biyema Nu'aymah saboda yanda take bulala musu shi a cikin ɗaki kamar shagon saida shi.........

          “K! Kuma yaushe kika shigo nan?”. Umm ta faɗa tana kallon Nu'aymah dake kwance a kan gadonta idanu a lumshe. 

     A hankali ta buɗesu akan Umm dake kallon yanda tai rama cikin kwanaki kaɗan. Tai ɗan ɓata fuska kamar zatai kuka. “Umm dan ALLAH awara zanci”. Kai Umm taɗan girgiza da nufar gaban mirror ɗinta ta ɗauki ƙaramar wayarta da tazo ɗauka. “Indai banda fitina ni ina naga awara yanzu Nu'aymah? Ke dai inhar kikai zazzaɓi sangarta iri-iri kin iyata mara dalili, ko Muhammad baya iya shegenki a gidan nan”.

              “Umm Please!”. Ta sake faɗa cike da shagwaɓa kamar zatai kuka. Zama Umm tai a bakin gadon kusa da kanta. Taɗan shafa goshinta a hankali,  “Nu'aymah banson rigimar nan, yanzu dai kinsan baza'a samu awaraba ko? Sai ki bari sai anjima, bara dai na bama Saude takai kuɗin gidan ƴan awaran”.

      Kai Nu'aymah ta ɗagama Umm tana murmushi, sai kuma ta tashi zaune ta rungumeta tana ƴar dariya. Zame hular kanta Umm tai ƙoƙarin yi. Da sauri Nu'aymah takai hannu zata riƙe dan tasan mi Umm ɗin zata duba. “Umm kainafa ke ciw.....”

        “Ƙaniyarki keda ciwon kan, wai Nu'aymah bazaki daina wannan shegen ƙazantan nakiba na rashin son ƙitso? Kalla kiga fa kanki gashinki duk ya lalace saboda rashin kula. Tashi maza ki wuce wajen Adda ta kama miki kai kafin na ɓata miki rai”.

         Ƙwalla cike da idonta ta kalli Umm, “Umm dan ALLAH ba yau ba”. “Kin rainani ko?”. Umm ta faɗa tana ɓata fuska.

      Muhammad dake ƙoƙarin shigowa ya ƙyalƙyale da dariya yana faɗon, “Umm ALLAH fa ta rainaki, inba rainiba ya zakice taje kitso ta zauna shagwaɓa......”

    Filo Nu'aymah ta ɗauka ta wurgama Muhammad ɗin. Ya goce yana dariya. “Wlhy idan na kamaka a gidannan saina tsiyayar maka da man kai tas. Umm ki faɗama yaron nan nifa ba sa'arsa bace”. Yanda tai maganar idanunta cike da ƙwala ya saka Umm yin ƙaramar dariya itama, tai saurin saka hannu ta rufe bakinta tana haɗiyeta ganin hawayen harsun sakko a guje.

      “Uhghumm!” Umm tai gyaran murya tana haɗe fuska da wurgama Muhammad harara. Hannayensa ya haɗe waje guda fuskarsa da murmushi yace, “Am Sorry aunty N”. Ya ƙare maganar da mata gwalo kaɗan. Harara ta zuba masa ta koma ta kwanta da juya masu baya shi da Umm ɗin.

       Hannu Umm ta bashi suka tafa, kafin ya haye gadon yana faɗin, “Banace kiyi haƙuri ba Noorunnisa”. Juyowa tai fuskarta ɗauke da murmushi ta dungure masa kai tare da ja masa hanci tana faɗin, “Yaro 1-0”.

      Dariya sukayi a tare. Umm ta miƙe tana murmushi ta bar musu ɗakin.


★★★★


       Sashen Addah Umm ta nufa, dan tanason su tattauna game da al'amarin nan na Nu'aymah tun jiya, sai dai rashin lokaci yasa bata shigaba. Tasan itama Addahn bata shigo bane saboda taga baba malam ya wuni a gida jiya, yauma ya daɗe bai fitaba.      

         Kubrah kawai ta iske a falon tana  yankan ƙumba. Ta gaidata cike da girmamawa kamar yanda suka saba. Dan bayan mahaifiyarsu Umm itace mace ta biyu a gidan da suke ɗauka tamkar mahaifiya. Fuskar Umm ɗauke da murmushin itama ta amsa mata, “Ɗiyata saike kaɗai a gidan kenan?”. “Eh Wlhy Umm, daga ni sai Addah kawai. Hajarah da su Jafar sun fita aika”. “To ALLAH ya maidosu lafiya. Ina Addan?”. “Umm tana ɗaki ki shiga mana”.

     Kafinma Umm ta amsa mata Addah ta fito daga ɗaki. “Haba nifa ince kamar muryar Umm, ashe kuwa kece?”. “Ƙyaface haka mana, tun jiya rabon danaga idonki a gidannan Addah. saboda kinga ƴarki ta samu lafiya”.

               “Wacefa lafiya Umm, anason a ganmin bayanta”. Addah ta faɗa cikin ɓacin rai. Murmushi Umm tayi da kama hannunta, dan tasan Addah dama bata barin saita kwana sam. “Kinga nidai muje sarkin hawa”. 

           “Bazaki ganeba Umm. Daga jiya zuwa yau naje sashenki yafi sau a ƙirga amma sai na iske Baba malam na nan. Wlhy na kwana tamkar na ciji kaina dan baƙin ciki. Gaskiya Umm wannan al'amarin bai kamata mu zuba masa idanuba a wannan karon, yanzu dan ALLAH minene na ɗaukar Number wayar likita idanba zalunci ba? Lafiyarta ne ba'ason anema kenan ko minene?”.

          “Humm Addah wlhy nama kaina wannan tambayar yafi sau dubu tsakanin jiya zuwa yau. A a daren jiya har musabbabin ciwon Nu'aymah sai da ya dawomin a rai. Bansan minene laifin yarinyar nanba akeson rayuwarta ta salwanta. Ni harma na rasa wane kalar tunani zanyi Addah, wanene? Miyasa? Mi mukai masa?......”

            “Umm nidai tsakanina da ALLAH na fara zargin jama'ar gidan nan fa, idan har mai aikata wannan abubuwan ba'a gidan nan yakeba to daga ina yake zuwa? Nifa dagama jiya na fara tantama akan barin Nu'aymah gidan nan akan maganar aurenta. Shiyyasa ni dama tun farko ban yardaba. ni dama tun jiyan wani shawarace tazomin akan yanda zamu saka ido akan motsin kowa, na tabbatar insha ALLAH a hankali zamu samo bakin zaren”.

                Kai Umm ta ɗaga mata cikin alamar nuna gamsuwa. Addah ta matso kusa da kunnen Umm ta gwargwaɗa mata hanyar daya kamata subi. Ɗari bisa ɗari Umm ta amince, suka ɗaura da addu'ar dacewa. Daga nan suka cigaba da tattauna al'amarin suna ƙarama juna haske. Umm bata bar sashenba sai da lokacin salla yayi. Ta koma sashenta tana jin daɗi a ranta, koba komai zuciyarta ta rage nauyin da tai mata. Shiyyasa akoda yaushe take sake godema ALLAH daya haɗasu aure gida ɗaya ita da aminiyarta. Su kashe su rufe matsalolinsu babu maiji sai ALLAH.

            

______________________

ZAFAFA BIYAR 2021

_______________________

   

                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


_______________________

_____________

*_DUBAI_*

________


                 Tun randa Abdallah yay waya da wadda yake zaton Momynsa ce ransa ya sake dagulewa gaba ɗaya. Wani lokacin ji yake tamkar ya naɗama Adawiya mugun duka ya cillata jirgi ta koma Najeriya. Sai dai tsoron fushin iyayensa ke sakasa dannewa.

         A maimakon kwanaki bakwai ɗinma da yay niyyar suyi a kwana na huɗu yasa suka wuce Saudia. Adawiya sai jin daɗi takeyi dukda bata ganin koda murmushinsa. Ita kasancewa da shi a ƙarƙashin inuwa ɗaya kawai ya wadatar da ita a cewarta.

       Ba wannan bane karonta na farko zuwa ƙasar saudia, sai dai yanda tazo a wannan karan yanada banbanci da sauran zuwanta na baya. Shiyyasa take wani jin kanta a sama. Wanda kuma takeyi dominsan ma baisan tanayiba. Tunda suka iso gidan da zasu zauna ya nuna mata ɗakinta bata sake ganin koda ƙeyarsa ba. Tsalle ta dingayi bayan fitarsa, dan ɗakin yayi matuƙar ƙyau da tsari. Sai dai kalar komar zaɓin Nu'aymah ne, harda ma manyan frames ɗinta guda uku da aka manna a bango, sai na Abdallah guda biyu shima. Dukansu sunyi masifar ƙyau. Ta taɓe baki da jan wawan tsaki, stool ɗin mirror taja duk ta juya na Nu'aymah dan har cikin ranta ta tsani ganinta, tunda itace sanadin hana tabbatar farin cikinta, saboda Nu'aymah yah Abdallah yaƙi sake mata, saboda Nu'aymah ta gagara daraja a garesa matsayinta na matarsa. Saboda Nu'aymah saboda Nu'aymah..... Komanta yaƙi dai-daita kamar yanda tai fata, tabar na Abdallah kawai tana faman kuka kashirɓan da zagin Nu'aymah da batasanma tanayiba.


           Rayuwarsu ta saudia tana kadaran kadahan ne, baya shiga harkarta bakuma ya takura ma rayuwarta. Sai dai har yanzu ya hanata wayarta, idanma zata gaisa da Addah da Abbanta ko wani a ƴan gidan nasu saita wayarsa. Kuma yay tsaye a kanta har saita gama ya amshe abarsa. Hakanna bata haushi, amma sonsa da tsoronsa ya hanata ta nuna masa koda a fuska.

      A haka suka kwashe watanni biyu a gidan. Shirye-shiyen makarantarta ya gama kammaluwa ta fara zuwa. Da farko bata shiga harkar kowa ta maida hankalinta a karatu kamar gaske. Tana wata na biyu da fara karatunta tai ƙawa mai suna Abida, sai da ana kiranta Maman Aaida, itama matar aurece harda yaranta biyu, asalin Mamana Aaida itama ƴar Nageriya ce, amma yanzu iyayenta na nan Saudia. Ta girma Adawiya da kusan shekara uku zuwa biyar, dan itakam zatai 22years. Maman Aaida irin matan nanne masu shegen iyayi dason gayu, ga Ƙwanƙwanin tsiya kamar jikar ƙaruna, kullum cikin bama Adawiya labarin mijinta take a zatonta Adawiya budurwa ce. Adawiya dataga iyayin Maman Aaida yayi yawa saita fito ta nuna mata itama ai tanada auren. Sosai Maman Aaida tayi mamakin hakan, danta tabbatar saita shirya zuwa gidan Adawiya a wani weekend. Babu wani ja'inja Adawiya ta bata address ɗinta. A kuwa ranar Alhamis saiga Maman Aaida har gida ita da maigidanta da yaransu biyu, da yake Abdallah na gida sai har mijinma ya shiga. Abdallah dai bai wani sake musu ba, bai kuma wulaƙantasuba aka gaisa da ƴar hira suka wuce, bayan tafiyar tasu kuma bai cema Adawiya komaiba akan zuwan nasu ba duk da yasan ya dace ace yayi hakan.

           Sanadin haɗuwa da Maman Aaida fa idanun Adawiya ya ƙara buɗewa. Dan tunda Maman Aaida ta bigi cikinta taji yanda akai aurenta da Abdallah sai ta shiga ɗorata bisa wasu hanyoyi da zata ringa jan hankalin Abdallah, ciki harda abubuwan irinsu turaren jan hankali da sauransu. Tun Adawiya najin tsoron yin hakan harta fara hawa kan network da sha'awar fara gwadawa ko zata dace Abdallah ya manta da Nu'aymah.

      A ranar farko da ta fara buɗe jikinta da turare Abdallah bai kwana gidanba, yamayi tafiya bata saniba. Da yake sai ya gadama take ganinsa sai bata fahimci baya nanba, washe gari ta wuce makaranta. Data dawoma bata gansaba bata kawo komai a ranta ba har dare, lokacin kwanciya ta sake shanana turare ta nufi ɗakinsa. Sai dai kuma wayam. saida ta leƙa har toilet sannan ta lurama ba'ai amfani da toilet ɗinba ma kwata-kwata. A take kuma sai tsoro ya kamata duk ta tsure, leƙe-leƙe ta shigayi cikin gidan kamar wata zararriya. Data ga dai lallai babushi a gidan saita fara kuka, ta koma ɗakinsa ta ƙulle ƙofa ta ƙudundune a bargo. Ta kusa awa guda a haka sannan ta fara jin motsin za'a buɗe ƙofa. Sake rikicewa tayi da kuka catake wanine ya shigi. Cike da mamaki Abdallah daya shigo yake sauraren kukan nata dan baiyi zaton ganinta a ɗakin nasa ba. Ƙarasawa yay gaban gadon ya yaye bargon. Tako dage zata kwarara masa ihu dan ruɗewa ya hanata nutsuwa taga wanene. Saurin hayewa gadon yayi ya rufe mata baki ruf da hannunsa yana kallon yanda jikinta ke rawa. 

        A take yanayin nata ya juye masa tamkar na Nu'aymah, dan duk lokacin da abu ya tsoratata haka zakaga jikinta na rawa duk ta fita hayyacinta, daga haka kuma saita suma. Yanda zuciyarsa ke ƙawata masa Nu'aymah sai tunaninsa ya gushe zuwa gareta harya rungume Adawiya batare daya fargaba. “K malama ki nutsu nine?”.

         Sosai Adawiya ta sake maƙanƙale masa dan a rikice take sosai, amma taji daɗi da taji shine.

            Tun Abdallah na shaƙar ƙamshin turaren data saka matsayin ƙamshi kawai harya fara canja masa yanayi. Hancinsa ya ɗaura bisa wuyanta yana shinshina da lumshe idanu, kafin a ɗauki tsahon lokaci jikinsa ya fara tsuma, sai ya sauya salon riƙon da yay mata. Anan nefa Adawiya ta dawo hankalinta da ƙyau. Da farko nishaɗin abinda yake matan ta farayi. Sai dafa taji al-amarin bawai wasan yara bane sannan ta fara kuka da roƙo da magiya. Da al-amari yay zurfi saiga hajiya malama mandiya ƴar ƙwalisar soyayya Adawiya na tsinema Maman  da jamata ALLAH ya isa🤣😂🤣.

     Oho, Abdallah baisan tanayiba, morewarsa yakeyi dai-dai gwargwado, yama manta dawa yake tare. Iya wahala ya bama Adawiya batare da tausayawaba, kafin ya koma gefe ya barta ko numfashin kirki bata iya yi.


      Tun daga wannan ranar Abdallah ya maida Adawiya abar hutawarsa. Daya samu biyan buƙatarsa kuma ya watsar da ita tamkar bai taɓa sanin daga inda ta fitoba. Sam ta gagara gane kansa balle inda ya dosa. Komai nasa yana yinsane da kulawa da lura. Abincinta dama kam bai taɓa ci ba, zai dai ajiye mata duk abinda ta buƙata ya kuma bata kuɗi. Amma babu wani farin ciki da kulawa kamar yanda Maman Aaida ke faɗa mata. Duk iya dabarun Maman Aaida cikin gwadasu take ga Abdallah amma saiya yi kamarma baisan tanayiba. ba shiga ɗakinta yakeba, ko abu zai bata sai dai yay knocking ta fito ta amsa. Idan yana buƙatar moranta ma zai mata knocking ne idan tana ɗaki yace ta samesa nasa ɗakin. 

     A haka rayuwar auren nasu ke tafiya tare da karatun Adawiya da ta fara saka shiririta saboda damuwarta kawai itace Abdallah ya sota a yanzu.


*_NAJERIYA_*


            Rayuwa ta shuɗa, kwanaki nata gangarawa, inda ake neman watanni na takwas kenan da lalacewar auren Nu'aymah da Abdallah. Tana cikin tsananin damuwa da begensa, kullum dare sai tayi kuka, tana sonsa matuƙa, dan ta rayune da son nasa. Yawan damuwar da take a cikine ya haifar mata da yawan yin ciwo, saboda ciwonta bayason damuwa sam. A duk sanda ta takura kanta da tunani da damuwa yakan yawaita motsa mata akai akai, tana kuma matuƙar shan wahala. 

        Gaba ɗaya a awatannin nan lafiya taƙi wadatarta, haka taketa fama yau fari gobe tsumma. Gashi baba malam kullum cikin mata jan ido yake akan ta kawo Ameer yay musu aure. Tayi kuka tayi rantsuwar akan Ameer ba saurayinta bane amma sam yaƙi ya saurareta. Umm kanta wannan al'amari na tada mata hankali. Amma babu yanda ta iya ta zuba musu ido kawai taga iya gudun ruwan mijin nata. 

    

      Burin Nu'aymah cigaba da karatu a yanzun, amma Baba malam yay banza da maganar karatun nata, bayan kuma kowa a gidan yasan burinta a rayuwa shine ta zama likita ko Nurse tun tana yarinya. Addu'arta kullum itace Baba malam ya haƙura a sake nema mata makaranta kafin ALLAH ya dawo da hankalin Abdallahnta gareta, dan ita duk ɗaukarta Abdallah fushi yake da ita akan ta gudu ran aurensu, shiyyasa yaƙi nemanta koda a wayama. Ta dage da azumin litinin da alhamis da sallar dare tanata gayama UBANGIJI kukanta.

      Ana cikin wannan yanayin su Baba malam suka gama shirya gagarumar walima na saukar Al-Qur'anin yaransu na gidan marayu, tare da aurar da waɗanda suka samu mazan aure. Wasunsu anan cikin gidan suka dai-daita kansu. Wasu kuma a waje suka samu mazajen aure da mata.

    Shirye-shirye ake babu kaman hannun yaro, dan shinema ya ɗauki Baba malam Busy sosai ya samawa Nu'aymah lafiya daga takurar zancen fiddo mijin aure. Duk da dama dai yana matane kawai dan hukuntata ta cikin ruwan sanyi akan abinda ya faru. amma ta ƙarƙashin ƙasa neman hanyar ganin likitan nan kawai yakeyi da nema mata makaranta batare da ko Umm ta san da hakan ba.  

      Ana saura sati ɗaya su Yusrah suka iso, washe gari kuma su Amal. Hakan ba ƙaramin daɗi yayma Nu'aymah ba, koba komai ta rage kaɗaicin da ta tsinci kanta a cikin a waɗannan watanin ai. Abinda ya ƙara faɗaɗa farin cikin natama shine Amal da Yusrah bazasu komaba, dan zasu zaunan zana jarabawar ssce anan. Cikin kwana biyu kacal da dawowar tasu ta fara komawa cikin walwalarta. 

       Tuni suka fara addabar gidan da ƙiriniyarsu da bata ƙarewa, sauƙinma babu Adawiya, amma hakan baisa sun fasa abinda suka saba yiba. tun ana saura kwana uku suka saka Hajjo ta roƙa musu baba malam komawa cikin gidan marayu har sai an kammala komai. Dan yawancin ƴammatan da za'aima auren duk ƙawayensu ne, duk da dai a shekaru gaskiya zasu girmesu da kusan shekara bibbiyu ko ɗai-ɗai.

     Bai hanasu ba, dan gidan marayun nan nada matuƙar muhimmanci a garesa dama family ɗin gaba ɗaya. Yanda suke ƙoƙarin dagewa akan tarbiya da karatun yaransu haka suke dagema yaran gidan marayun nan suma. Shiyasa suma yaran suna tsananin ƙaunar wannan family, su suke ɗauka danginsu da komai a rayuwa.


★★★★★


             “Wai wannan akwatin da kika lodama kaya duk na miye Nu'aymah?”. Umm data shigo ɗakin Nu'aymah ta faɗa tanabin Nu'aymahr daketa shirin kaya da kallo.

     Ɗagowa tai ta kalli Umm cike da ɗoki, “Umm yo na bikine mana, sati guda zamuyi a can”.  “To lallai, ashema kune iyayen bikin kenan?”. Dariya Nu'aymah tayi dajin zancen Umm, Umm kam daga haka bata sake cewa komaiba ta ajiye mata magungunan ta tana faɗin, “Gasu nan, saura kije kita wasa da shansu Nu'aymah, dan ALLAH ki kula da kanki, duk abinda kikasan zai zame miki matsala ki kujesa, ku kuma riƙe mutuncin kanku, na kira Baba Habi a sashenta zaku zauna kafin Hajjo ta iso gobe idan ALLAH ya kaimu, saura naji wani abu mara ƙyau na shegen tsiwanki, ALLAH saina ɓata miki rai”.

        “Umm insha ALLAH bazakiji komaiba ma”. “ALLAH yasa”. Umm ta faɗa tana juyawa ta fice daga ɗakin..


          Bayan sallar azhar su Nu'aymah sukai sallama da kowa suka wuce, Yah Abubakar ne ya kaisu. Da yake shima irinsu ne ɗan taraliya saida ya kaisu sukai shopping sannan ya wuce dasu gidan marayun.

     Ƙaton gaske ne, sannan an ƙawatashi ta ko ina babu makusa. Akwai makaranta da asibiti da duk ma abinda masu rayuwa da iyayensu suke samu. Makarantarsu ta fara tun daga noziri har zuwa sakandire. Ana koyar da boko da arabic, idan kaji yanda yaran ke larabci da turanci sai kasha mamaki da al'ajabi. Rayuwarsu suke cike da farin ciki da jin daɗi wadda ko wasu masu iyayenma basa samu. Gasu da tarbiyya abin birgewa. 

     Ɓata lokacine zama bayyana muku yanda gidan marayun nan ya ginu da tsari mai ƙyau, kusa a ranku kawai ya haɗu. Dan sosai su baba malam ke samu taimakon manyan mutane dama masu mulki game da riƙe gidan. Ga kuma suma kansu masu nemane basu zauna jiran na sadakaba. Kaso mafi yawa na ɗunbin dukiyarsu yana tafiyane wajen tattalin rayuwar marayun nan da kulawa da su. Shiyyasa Alhmdllh da wahala ace sun nema abu sun rasa. Sai dai ace yau da gobe sai ALLAH, komai arziƙinka dama wani abun sai ya gagareka.

       A yanda su Nu'aymah suka sami tarba zai tabbatar maka da sanannune a gidan, kuma ba wannanne farkon zuwansu su kwanaba. Dan rigima aka shigayi musamman ga sa'anninsu, kowa na faɗin sashinsu su Nu'ayma zasu sauka. Bayan ansha taƙaddama dai kowa ya haƙura zasu zauna a sashen da amare suke, wato sashen baba habi da Umm ta faɗama Nu'aymah tun a gida.

        A yau kowa ya kalli Nu'aymah yasan tana cikin farin ciki sosai, haƙoranta sun kasa rufuwa. Tsiyarsu sukaita tsulawa uwa ba kwaɓa uba babu tsanani, dan suna son suga sunzo gidan nan, shiyyasa wani lokacin baba malam da kansa yake cewa suzo suyi weekend ɗinsu anan, dama anan duk yaran gidansu ke karatunsu tun daga noziri har zuwa sakandire, shiyyasa sukeda shaƙuwa sosai da yaran gidan marayun fiye da zaton mai tunani.


     Washe gari Nanah tace suma gasunan zuwa ita dasu Suhailat, hakan yasa bayan sallar la'asar ana tsaka da musu ƙunshi dan ranar itace suka saka ranar ƙunshin, Nanah ta kira wayar Yusrah ta sanar musu gasu a bakin titi suzo su shiga dasu dan baza'a barsu su shigaba kai tsaye.

        Nu'aymah da Yusrah da biyu cikin ƴammatan gidan suka fita shigowa da su Nanah dansu ƙunshinsu harya bushe sun wanke, Nu'aymah ce kawai bata wanke nata ba amma ya bushe. da ƴar tafiya tsakanin gate da gidajen yaran, amma haka suka taka a ƙasa suna hira har suka iso. suna a gab da fitane suka haɗu da yaran gidan maza da bazasu gaza shekaru sha biyu ba kusan su bakwai wai wajen ball suka tilla ƙwallon waje ta katanga shine zasu zagaya ɗakkowa. Security ɗaya ne tare dasu zai rakasu. A tare suka fita dasu Nu'aymah da zasuje tarbar su Nanah.

       Gidan marayun yana akan babban titine, shiyyasa sam ba'a barin yaran fitowa ko ina su kaɗai koda hakan ta kama sai da security.

      

        Dariya Nu'aymah tai ganin su Nanah acan ɗayan tsallaken basu tsallakoba, tasan Nanah matsoraciyace akan tsallaka titi dama, shiyyasa yanzuma abun ya bata dariya data tuna. Su Yusrah ma dariya suka sanya famhimtar dariyar Nu'aymah da sukayi. Bayan sun kalla ɓangare biyu na titin babu mota suka sa kai zasu tsallaka. Da sauri security ɗin daya rako yaran nan yasa hannu ya fisgo Nu'aymah dake ƙarshen tafiya saboda tahowar wasu motoci guda uku a jere cikin masifaffen gudu.

        Ta juya zataima security ɗin masifar taɓatan da yayi dukda tasan hakan na halinsu bane sukaji razananniyar ƙarar ɗaya daga cikin yaran wanda motar farko ta kwashesa yana ƙoƙarin ɗakko gyalen Nu'aymah daya zame ya faɗi lokacin da security ɗin nan ke ƙoƙarin maidota baya.

         “Ƙuuuuuwww!!!” motocin suka bada sautin taka birki a tare, yayinda mai napep dake bayansu ya bugi motar ƙarshe shima.

      A tare su Nu'aymah suka fasa ƙara da rumtse idanu kunnuwansu a toshe da hannayensu, sai da sukaji tsitt sannan suka bubbuɗe ido dan son ganin yaya akayi.

       “Innalillahi.... Suka shiga ambata kusan a tare saboda hango yaron a kwance ƙasa cikin jini. Sunma manta a titi suke, suka tafi da gudu kansa suka rufu masa. Sunkai mintuna uku akan yaron nan suna kuka da jujjuyashi amma ko mutum ɗaya bai fito daga motocin nan uku ba balle kai tunanin sunsan ma abinda suka aikata. Cikin tsananin fushi da zafin zuciyar gado Nu'aymah ta rarumi wani dutse dake a gefen titin ta nufi motar tsakkiya dake a saitinta, wadda kuma tafi kowacce haɗuwa da ƙyau ta buga dutsen jikin glass ɗin. 

      Ko gezau glass ɗin baiyiba, dan haka ta koma na gaba wanda tasan insha ALLAH zata dace ta sake bugawa da iya ƙarfinta. Aiko a take ya shiga tsatstsagewa. Ta sake ɗagawa zata buga aka riƙe mata hannu. Fisge hannun nata tai ƙoƙarin yi ta kasa, dan haka ta juyo bakinta cike da tsiwa.

      Ido huɗu tayi da manyan garada masu suffar ƴan dambe cikin baƙaƙen suit da glasess zagaye da ita su shidda, daka gansu kaga cikakkun marasa imani dan babu alamar sunsan ma minene dariya a rayuwarsu, babu tantama kuma zasu iya halaka mutum batare da sunji koda ɗar ba.

        A mamakinsu sai gani sukai ta ɗaga dutsen ta bugama wanda ya riƙe mata hannu a goshi. Saurin sakinta yay ya dafe goshinsa daya fashe a take ya fara zubda jini.

        Kusan a tare suka fiddo bindigu suka nunata da shi. Duk da Nu'aymah tasan zasu iya harbin nata ta mutu kuma, amma sam cikin idanunta babu tsoronsu, saima masifa dake cinta. Haka take ita sam batasan tsoroba. Idan kaga tsoro ga Nu'aymah to duhu ne ko tsawa, ko allura.

       Ɗasss! Ɗasssss!! Ɗassssss!!!

Sukaji sautin buga yatsu a bayansu. Gani tai duk sunja baya daga kusa da ita amma basu sauke bindugunba, sundai risinar da kawunansu ƙasa na alamar girmamawa ga koma wanene mai buga yatsun.

        Kamar bazata juyaba sai zuciyarta ta bata shawarar juyawa taga wane shahararran ƙwallan mara imanine da mutuncine shiɗin...........✍


Nidai nama rufe idona bazan gansa ɗinba😎🚶🏻.


Yau dai ga dogon page nan ku more harda na jiya na haɗa muku. Saura kuma naji wata tace bai isheta ba😚😏😣🚶🏻🚶🏻🚶🏻


No comments

Powered by Blogger.