Min Qalb 6-10


MIN QALB 6_*

Wani 'dan murmushin mamaki haj Maryam tasaki tana miqewa tsaye bayan ta ajiye qaramin pillow din kujera data dauka ta Dora a cinyarta bayan zamanta,ta tsaya gaban umme din ta kelleta tanason Bata qarfin gwiwa da Abinda take Shirin yi tace'

Aisha Idan har wannan mafitar kike tunani zata bullar damu ga Abinda mukeso to haqiqa Ina taredake ako wane mataki dazamubi Wanda zai kaimu ga nasa,

Saidai Abu daya anan shine abin dubawar,shi Mahmud din tayaya zai zauna yana kallo ya karbi wannan false accusations din Wanda zaiyi tarnishing image dinsa a idon duniya.


Kallon haj Maryam umme tayi tareda sakin murmushin farko a ranar ta yau tace'"


Mune zamuji Masa ciwo Kuma mune zamu zuba Masa gishiri a ciwon Kuma mune zamu hanasa sosawa,

Abinda kenan wato shine Kinga Maryam narigada nasan weakness din MAHMOUD wato duk duniya rauninsa biyu ne wato mahaifinsa da Khalil,


As long as Modibbo zai zuciya akan wannan alamarin to tabbas MAHMOUD yagama yawo sbd duk wani cigabansa rushewa zaiyi.


To wani hanzari ba gudu ba ta Ina zamu Fara wannan Shirin?

Ma'ana ta Ina zamu Fara neman me wannan aikin? musamman fa Kinga aikine me tsananin hadari sbd 6atawa mutum kamar MAHMOUD suna a duniyarnan babban risk ne ataqaice ma kamar mutuwace kake kirawa rayuwarka sbd kamar yanda yake dinnan a natse zuciyarsa a bushe take,

Duk Wanda zaiyi Mana wannan aikin dole Muna buqatar Wanda zuciyarsa tagama mutuwa akan kudi.


Karuwa,,,,,,


Mene??? umme tafada da 'dan sauri tana kallon haj Maryam din sbd qyamar ma sunanda tafada.


Yes karuwa nace sbd karuwace kawai zata iyayin komai akan kudi,

Ita kadaice zata iya wasa da mutuwa akan kudin sbd sunanta matacciya daga lokacinda wannan alamarin ya lalace.


Dafe goshi umme tayi tana cewa'"


Maryam daina fadar sunan karuwa acikin zabeera sbd fadar sunanta kawai babban laifine a cikin ahalin Nan,

Kawo karuwa acikin zabeera shine laifi mafi Muni dazamuyi Wanda yafi Abinda muke Shirin aikatawa.


Aisha Idan har zamu iya qetare duk wata iyaka mu aikata irin wannan abin to inaga kawo karuwa ba komai bane,

Wannan zancen ma bai kamataba munayinsa acikin zabeera ki shirya gobe muje gyaran qafa zamu tattauna acan kafin Nan kin yanke shawara.


Ficewa tayi tana ayyanawa aranta dole Khalil yazama zabeera na hudu sbd 'yarta nuratu da ita su samu kyakkyawar gaba me kyau.


Umme kuwa kasa zama tayi palon ta wuce dakinta tana dafe kanta dake sarawa sbd damuwar data sawa kanta  ga mafita na neman gagararta

Duk abinta bazata iya kawo karuwa ba a zabeera sbd sanin tsananin alada da Matsin dokoki irin nasu Wanda sune asalin zabeera da Abinda yasa suka fita dabam acikin mutane,


Familyn ZABEERA family ne dasukeda  wani irin tsatsauran raayi da dokoki Wanda suka zame musu tamkar addini,

Basa auren bare,basa zama da bare,basa barin 'yayansu Mata suyi karatun jamiaa a qasar Nigeria saidai qasashen qetare na laraba sbd karsu barsu anan kowa yagama sanin 'yayansu wainda suke tamkar suna musu kulle ne sbd ko muamala basa barin yayansu suyi da mutane sosai,


Asalinsu Hausa Fulani ne saidai yanayinsu yasa ake musu kallon Fulani sbd yawancinsu farare ne masu 'yar doguwar fuska kalar Fulani,

Sarauta tasa dokokinsu da tsaurin raayinsu yin yawa saidai Kuma babban Abinda yasa suke buka mulki da iko shine Babu wani Dan ahalin daya taba karya doka ko qetareta,

Suna tsananin tsoro da bin umarnin manyansu musamman ZABEERA na daya acikin 'dakinsu asalin dahir zabeeran farko MUHAMMAD USMAN ZABEERA wanda suke Kira da ANDI,

Andi shine mahaifinsu Modibbo mahaifinsu MAHMOUD Wanda yake amatsayin zabeera na biyu Wanda yayi shekaru akai kafin yayi murabus ya sauka yabaro asalin zabeera dake cikin babban birninsu ya barwa qaninsa mulkin Wanda shine amatsayin zabeera na yanxu Kuma shine zabeera na uku Wanda ayanzu ne zaayi na hudu.


Andi shine shugaba mafi tsanani da duk zabeera ake tsoro ake Kuma gudun bacin ransa dagashi dai Modibbo daya kusan zartashi fiyeda komaima na tsananin zafi da dokoki,


Babu wani abu magi qyama agurinsu irin cin Amana da Abinda zai taba martabar ahalin,

Duk babban attajiri tareda manyan Yan siyasa abokanan hurdar familyn ZABEERA ne shiyasa ake matuqar giramamasu da mutuntasu,


Kaf familyn Babu wani sakewa atsakanin iyaye da 'yaya sai bin doka da oda sbd Sam basa Wasa ko sakewa 'yayansu shiyasa 'yayansu ke tsananin shakkar manyansu Dan kaf familyn Babu wani 'da dazaice yataba ganin dariyar manyansu iyaye maza saidai iyayensu Mata,


Modibbo keda Mata uku kowacce tanada Yara hudu Mata Banda mahaifiyar MAHMOUD wadda keda shi shikadai ta Haifa ta rasu tun yanada shekaru bakwai a duniya sai umme datake da Khalil bayan 'yaya Mata hudu,


Umme itace tafi kowacce mace zuba iko da Isa agurin Modibbo sbd zamanta uwargida itace Kuma uwar manyan 'yayansa da duk sunyi aure kusanma wasunsu sunkusa aurarwa Suma.


Umme Bata qaunar 'dan daba nataba saidai Kuma bazata iya cutatar dashiba 'yayanta su kadaine 'yayanta bayansu ba ruwanta da 'dan kowa Koda kuwa zataga masifa ta tunkarosa ne,


MAHMOUD shikadaine yataso a cikin iyalan Modibbo baida mahaifiya,

Yataso ne acikin wani irin kadaici ya rayu acikin kadaicin,

Tun Yana yaro baida Wanda yataba janza ajiki harya girma,

Shi kadai yake komai nasa na rayuwarsa iyakacinsa da mahaifinsa gaisuwa da bin umarnin baitaba jansa ya tambayesa Yaya rayuwarsa take tafiyaba tunda mahaifiyarsa ta rasu bama shi kadaiba kaf duniya baida Wanda yataba jansa ajiki yaji ya yake ba,

Baida kowa aganinsa,

Baitaba shiga cikin 'yan uwansa ba sbd basayi dashi,

Shi kadai yake kwana,

Shi kadai take tashi,

Ahaka yayi rayuwa ahaka harya girma,

Da kansa ya koyi faduwa da yanda zai tashi kansa,

Da kansa yasan yayiwa kansa fada ya tsaya ya nemi ilimi dan yin rayuwa dashi,

KHALIL shikadaine 'dan uwansa dayake dashi Wanda yake tsananin qaunarsa duk da yanda umme ke hanasa muamala dashi saidai Sam qaunarsa Khalil ke Masa Babu Mai iya kwabarsa akan shifa alamuransa,


Khalil na tsananin kaunarsa fiyeda wainda suke daki 'daya Wanda kowa yasan da hakan shiyasa tare sukai karatunsu tun primary har secondary  saidai kasancewar Khalil din ba lafiyayye bane asthmatic ne Kuma irin chronic din Nan shiyasa daga secondary suka rabe MAHMOUD Modibbo ya turasa Sudan karatu shikuma umme taqi yarda yaje koina.


A Sudan yaqara samun cikakkiyar rayuwar kadaici Wanda ta hade da rayuwar kadaicin daya baro sai hakan yazame Masa wata sababbiyar dabia wadda yazama rayuwarsa,


Baya fira sbd baida abokan fira,

Yayi gwagwarmayar karatun degree a Sudan na tsawon shekaru shikadai batareda yazo gida ba kokuma wani daga gidan yazo gurinsa,

Babu wani Wanda yataba kiransa yajisa tsawon shekarun bayan khalil sai Modibbo Wanda shine yake kiransa badai shi yakirasaba,


Baitaba damuwa da kadaicin rayuwarsaba da baida kowa sbd ahaka yataso

Hakan shiya kashe duk wani walwala ko muamalarsa da mutane sai kadaici yafi Masa Dadi da nutsuwa fiyeda komai,

Bayasan hayaniya ko shiga jamaa sosai sbd yafi samun nutsuwa a inda kadaici yake.,

Ahaka rayuwarsa ta nitsa inda yasamu nasarori bayan cikakkiyar gwagwarmayar rayuwa dayayi a cikin neman ilimi me zurfi,

Gwagwarmayarsa tazo da nasarori da dama wanda yasa yayi fice cikin manyan mutane da qusoshin qasa,

Zamtowarsa wani qusan Shima sai sunansa yaqarawa zabeera family suna da martaba sosai,

Ya mallaki abubuwan arziki da dama wanda kaf zabeera yanzu Babu abokin karawarsa idan ba Modibbo ko Andi ba wainda sukafi kowa dukiya,

Nasararsa tasa yanzu kusan kowa dangi binsa yakeyi saidai kasancewar bai Saba da a jasa ajikiba yasa baya sakewa da kowa ataqaicema baya iya rayuwa cikin mutane yafison zamansa a Sudan inda acan nasarorinsa suka Fara acan yafi samun nutsuwa idan ya kadaice abinsa

Yana daukar lokaci baidawoba Dan yanafin shekara wani lokacin kafin yazo Wanda duk zuwansa sbd Khalil ne kawai yake zuwa sai Modibbo Wanda yake matuqar giramamawa fiyeda komai arayuwarsa,

Ta bangaren 'yan uwansa kuwa sosai yake sake musu kudi duk da Babu wani sabo ko sakewa a tsakani Amma yakan Basu duk wani abu musamman umme dayake ganin qimarta sbd Khalil batareda yaduba yanda yataso ba sbd idan yace yaduba yanda yataso to zaitsani kowa arayuwarsa.


Ganin kamar MAHMOUD din yayi musu nisa sosai Wanda yanzu suke alfahari dashi amatsayin Dan zabeera sbd mutunci da girma tareda qimarda yake sake kawowa zuriar sai suka yanke shawarar nemar Masa auren 'yar qanin Modibbon Wanda yake kan kujerar zabeera ayanxu ZARAH,


Zarah ta auri MD ZABEERA cikeda alfahari da auren sbd samun miji yanxu kamarsa dibbin nasara ce arayuwa,

Tana tsananin qaunarsa saidai sanin yafi karfinta yasa ko a mafarki Bata tunanin aurensa saigashi Allah yayi shidin mijintane Wanda taqara haukacewa a tsananin qaunarsa,


Baya musu arayuwarsa sbd baisaba doguwar mgn ba ko ta fannin business dinsa ko deals dinsa Abune nayi ko bari bayasan dogon Bata lokaci shiyasa baibi wani dogon sawa Kai ciwon kaiba ya amince musamman da akayi saa zarah mace ce me tsananin nutsuwa da hkr ga biyayya da fahimtar Abu Sam Bata cusa kanta gurinsa tunda akayi auren

Rayuwa suke ta mutunta juna da kiyaye gudun shiga haqqi.,


Shi mutum ne marason damuwa da hayaniyar mutane akusa dashi shiyasa idan har yananan ko volume din tv bata sawa sosai sbd karta damesa,


Bata taba yin wani abu Dan damuwarsa ko sakasa ciwon Kai ba shiyasa yake respecting nutsuwarta musamman dayake dama baya shaawar mace arayuwarsa saidai sbd girman Modibbo da Andi dakuma qimarta yasa yake qoqarin bawa auren nasa haqqin.



***

Yau amatu Bata fita aikiba Saida tagama hutawarta a gida kafin tayi Shirin aikin ta fito tareda usi Dan dama kullum tare suke zuwa aikin


Suna Isa tun a harabar gurin suka fahimci da masu kudi a gurin saidai rashin saar dasukayi gefen VIP saloon dinsu sukaga motocin Wanda sunsan Babu rabonsu yau acikin aljihun masu wainnan motacin masu kama da tarwadar ruwa sbd sheqi.


Direct gefen restaurant suka nufa usi na cewa"


Juyawa zanyi amah zanje gurin insfector Garba naji uban me zaimin dayake nema na tun Daren jiya.


Tana shigewa tace' idanma ni yakeson katayasa lallashi kafada Masa duk yabari nayi Ido biyu dashi Aina sace Masa shegen cikinsa me kama da tayar motar Mai.


Juyawa yayi Yana cewa' nizan Fara nuna Masa kalar rashin mutuncina kawuma nacan Yana jiran ganinsa.

#mamuh#

______________________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauƙi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________




#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/11, 6:12 PM] Zafafa: *_MIN QALB 7_*

_mamuhgee_



Kai tsaye change room dinsu ta nufa ta sauya kayanta zuwa na aiki ta fito tana gyara zaman qaramin Rolling dinta a wuya tana Dan yamutsa fuska tace,


Ni wannan aikinma harya Fara isata sbd wannan kayan aikin kullum mutum atakure bazan iyaba aje aikin zanyi na huta kafin daga baya zanda usi yasamomin wani yanzu dai kafin na ajiye zansamu kudinda zasu riqemu kafin asamo wani.


Tana isa reception dinsu manager  dinsu na isowa 

Shigowarsa kenan Yana waya yayi Mata hannu cewar ta tsaya yagama wayar

Wani harara tabisa dashi tana dauke Kai sbd manager dinnan nasu tafara gano take takensa akanta bazai shiga hankalinsaba sai ranar data sanfe duk wani arzikin dake aljihonsa,

'daga Masa qafa takeyi sbd kudaden datake sanfewa na restaurant Dan kullum saita diba son ranta take tafiya gida Bari tayi yaringa ji da 'daya Amma yakasa Kama kansa,


Kullum sai ayi rikici gun lissafin yanda kudi ke ba'ta Amma ankasa ganewa har so biyu ana sauya cashiers din aje kudin Amma 'yanda kasan 6era ne me satar ko clue bata bari bare amayi zargin mutum ne me satar.


Kallon qeyar kansa tayi tana sakin murmushin qeta tace"


Manager tashi aiki zakayi kwanan Nan...

Maganarsa ta kwasheta ta 'dago tana kallonsa tana 6oye murmushin gayyar datakeyi tace"


Barka da zuwa manager,

Kazo lafiya?


Washe haqora yayi Yana gyara zaman medical glass dinsa cikin son nuna shi wani ne yace"


Yawwa lfy klau amah 

Dama sbd matsalolin damuke fuskanta na 6acewar kudi a bangaren restaurant namu yasa na yanke shawarar maidaki gefen saloon sbd zamu dauki mummanan mataki akan maakatan restaurant din banason asaki acikin Abinda baima shafekiba,

Dukkaninsu maganinsu zamuyi saisun fitar Mana da 6arawon cikinsu.


Kallon Wawa taqare Masa kafin tayi fuskar marayu taredayin qasa da Kai cikin nuna maraicinta tace"


Nagode da hakan Dan ni ko yanda alamarin kudi dake gudana agurin banma saniba,

Banmasan meke faruwa a gunba da azo adauki alhakina abatamin suna kawuna ransa ya baci ciwonsama na hawan jini zai iya tashi idan yaji hadda ni acikin wainda zaa tuhuma da sata Kai Allah dai ya tsareni ya rabamu kalmar sunan satama batada Dadi.


Sake washe baki yayi ganin kamar yayi Abinda ya burgeta taji Dadi ya sake gyara tsayuwa Yana katse Kiran dake shigowa wayarsa yace"


Ai dama shiyasa naga yakamata a sauyaki saga gun sbd kada sunanki ya baci gashima Kinga Ashe kawunmu zai iya samun damuwa.


Tana qaqalo murmushi tace'


Eh dama gashi Muna fama dashi yau ciwo gobe lafiya ko tashi zaune baya iyayi" yaqarasa fada tana soke kanta kasa.


Subhanallah Ashe dai alamarin sosai ne to Allah ya sawwaqa inshallah yau ko gobe idan nabar office zanje nadubasa.


Zakasan me ake nufi da asalin sunan sata idan kaje duba kawo ka laluba kaji usi ya sanfeka tass""tafada qasa qasa tana Masa kallon sakarai....


Me kikace????


Eh cewa nayi akaini inda aka sauyamin din manager.


Yawwa muje'' yafada yanayin gaba tana binsa abaya tana sake 6ata fuska sbd Sam ita Bata wani son wani canje canje ita dake Shirin barin aikin ake Mata wani yaje Jaye Amma dai bangaren saloon din idan taga yamata zata zata Dan jima Amma yanzu babbar damuwar shine kafin ta 'dan gama gane Nan bangaren harta Fara samun damar sanfesu za'a dauki lokaci qila gashi komai nasu yayi qasa na abinci iyami kasuwancinta na Saida garin 'dan wake baya tafiya da albashinta suka dogara yanzu sai Abinda tasamo ko usi yasamo.....


Katsewa tunaninta yayi daidai lokacinda suka iso bakin qofar saloon din dake cikin blue fox din sbd wasu manyan hamshaqan Mata data hango ta cikin glass,

Sake 'daga wuyanta tayi tana 'dan leqawa tasake hango wasu 'yan Mata daga dayan gefen take tasaki ranta tana cewa"


Yauma ranar sa'atace kenan

Nakusa zamowa shiyasa Allah yasa aka daukeni daga Inda mutane basa ajiye jakarsu Amma anan dole mutum ya ajiye jakarsa tunda aiki zaa Masa,

Numfashi ta aje tana cewa"


Inshallah usi nakusa samun kudin karatunka Dan Banda buri yanzu dayafi kayi karatu sbd Kaine namiji qarfinmu zaifi qarewa akan naka kawuma ga manyanci na rufarmasa.


Tana cikin tunanin taji muryar manager na cewa"


Shikenan amah kuje ga shugabarku Nan zata baki Abinda zaki ringa yi

Sai akula please amah.


Gyada Masa Kai kawai tayi sbd tuni hankalinta yayi ciki a matse takeda tashiga ai madam bell na cewa tazo sushiga tayi gaba

Tana tura qofar glass din wani sanyin qamsh ya dameta ta lumshe ido tana qurewa gurin kallo daga sama taji madam bell na cewa"


Oya amah kije gurin anny gatacan tana sawa wata Rolex ki riqe Mata tana sawa idan kungama saikizo kiyi kallon yanda zan gyarawa waincan baqin namu qafafu.


To tace tana ajiye Jakarta a inda aka nuna Mata cikin haushi ta nufi anny din ta karbi robar Rolex din a karkace ta riqe tareda dauke Kai sbd yanda daga zuwanta ko Dan mutuntawar Nan Babu adai nuna maka Kai ba kowa bane face 'dan aiki.


Yini tayi aiki ranar sbd kowane aiki madam bell sata takeyi ayi da ita sbd ta iya gabaki daya Bata zaunaba tundatashiga gashi aranar taga asalin  ire iren Mata masu kudi wainda suke cikin kudi,

Matane sai masu arziki da wainda suka fito gidan arzikin sune kawai ke shige da fice agurin wasu na fita wasu na shiga shiyasa gabaki daya taji yanxu zatayi kudi wato ma a restaurant bataga komaiba sbd can iyajacinsu Kai abinci su dawo.

Sai yamma sosai Takoma gida a matuqar gajiye dan haka tana dawowa ta tarar ana fada hadda dambe da anty salamatu da maman basiru gasu maman junior a gefe anata qara zugawa kawu dai na zaune a shimfidarsa yaqi ko kallonsu bare ya matsa jira yake wani shegen ya fado Masa ya dauko musu motar yansanda ayi me kankat.


Kota kansu batabi ba ta wucewarta daki tana cewa'"


Allah yasa ayiwa maman basiru dukan sakwara muga qarshen qaryarta.


Washe gari ma da wuri sukaje aikin bayan ta biya cafe din kusada layinsu tabada cikon kudin scratch card din usi dazai zana waec Wanda shi baima sani ba.


Koda ta Isa gun aikin yauma Babu sauqi aiki tayi sosai ha lokacin tashi,

Kwanaki kadan tayi a saloon din ta iya aikinsu ba laifi Dan dama daurewa takeyi tana aiki sbd samun sanin Yaya kan gurin yake kafin tafaracin ubansu da halinta musamman madam bell databi ta addebeta da aiki sai janta ajiki takeyi tana yabonta ita kuwa sai sake musu kwantan 6auna takeyi Amma dai abokan aikinta sunfara sanin halinta sbd ba sauqi a tsakaninsu qaniyarsu takeci har mamakinta sukeyi yanda madam ke yabonta sbd batasan waye amah din ba.


Yau hakanan ta tashi da annashuwarta shiyasa batayi lattiba kamar yanda tasaba ta Isa blue fox din tana zuwa ta sauya cikin kayan aikinta suka hau aiki,

Customers biyu yau ta tsamewa kudi a jaka Kuma dukkansu Babu Wanda ya lura bare yagane harsuka tafi ta qirge kudinta tsaf kusan dubu goma sha biyu ta maida jaka tana cewa'


Saura dubu talatin da daya su cika kudin jarabawar usi ya Allah kabani ikon hadasu kan lokac......


Bata qarasaba wasu manyan hamshaqan Mata guda biyu suka shigo gurin tareda wata kyakkyawar budurwa tana biye dasu,


Kallo 'daya tayi musu tasaki baki tana cewa' Masha Allah da ganin wainnan hajiyoyin da hutu ya bayyana ataredasu.


Cikin gaggawa madam bell ta rude jiki na rawa take musu sannu da zuwa kamar zata kwanta su zauna akanta tsabar rawar jikin tarbonsu.


Cikin girmamawa aka wuce can qurya dasu spa room dinsu madam bell nacewa"


Welcome ma,

Welcome ma I've arranged komai da Kika bugo zakuzo kuyi in no time za'a kammala.


Suna shiga suka zauna tareda ajiye manyan jakunkunansu 

Haj Maryam dake waya har lokacin ta ajiye Tata akan kujerar bakin qofar shigowa tareda tsayawa jikin window tana sake bude muryarta gurin yiwa 'danta Salman fadan karya dawo yanxu sbd wani banzan nadin sarautar MAHMOUD dinda basuma wani San juna ba sbd ita din qanwace ga Modibbo ta Dade a gida sakamakon mijinta daya rasu shekaru goma kenan yabarta da manyan 'yaya biyu rak da nuratu da Salman din.


Umme kawai aka farayiwa gyaran sbd sanin idan haj Maryam tafara waya saita share awanni tanayi itakuma nuratu dama gyaran Kai ne zaayi Mata so tanacan guri daban.


Cikin nutsuwa anny keyiwa umme gyaran itakuma tana dudduba wayarta ahaka harsuka gama qafa daya 

Amah dake tsaye tana jiran haj Maryam tagama ita zatayiwa taja boyayyan tsoki yafi so ashirin harta gaji da tsayuwar ta Dan zauna gefe kan kujerar aikinsu kamar ance ta kalla saikuwa idanuwanta suka sauka kan jakar dake Kai wasu sabbin bunch na dubu dubu na leqota batasan sanda ta saki siriyar dariyar farin cikiba a boye tana sauke numfashin farin ciki tace"


Sa'a sa'a wlh saina fanshe zaman jirana danayi akan jakarki.


Fakaitan haj Maryam din tayi taga har lokacin waya takeyi tabada baya ta dawo da kallonta kan umme datayi nisa a taba wayarta ta 'dan matsa tana  zirara hannunta ahankali sai akan kudin ta janyosu batareda tsoroba ta cusa cikin robar hannunta ta kayan aiki saita miqe tareda ficewa.


Wani tsalle ta daka tareda kallon kudin tana washe baki tace' 


Hummm.


Cikin Jakarta tasaka kudin tareda kaiwa ta boye cikin kayanta kafin tadawo sparoom din tana wani basarwa annashuwa na fita a fuskarta Takoma tana zaman jiranta tana cewa'"


Ko darema kikai kina waya zanjiraki Dan nagama cire kudin zaman jirana.


Anny nagama yiwa umme ta miqe ta ficewarta.


Sai bayan fitar anny tagama wayar tazo ta zauna amah din tafara yimata har aka gama tas ta ficewarta.


Tsabar zumudin kudin kasa Bari tayi atashi taje gurin madam nema alfarmar tafiya gida da wuri sbd uxuri ana Bata dama ko kayanta Bata sauyaba ta tattaro su ta fito zuwa gida tana tafe tana lissafi cikin ranta fal farin ciki.


Wayarta ta fiddo tareda lalubo numbern usi taji switch off taja tsaki tana cewa'"


Dama nasani tun ahekaranjiya na lura ka Saida wayarka sbd kudin daka bawa iyatu na garinta da jarin ya karye

Karka damu kaida kawu duk saimun siya waya yau yaqarasa fada tana sakin murmushi itakadai a hanya.


Ganin napep yaqi samuwa yasa tadan Fara takawa tana tafiya a gefen hanya

Tayi nisa sosai wata qatuwar baqar mota Tasha gabanta tayi saurin matsawa tana qoqarin zubawa ko waye zagi.


Parking motar tayi aikuwa itama cikin tsananin masifa ta matso taga uban waye yake neman kassarata adaidai gabar datake ganin tayi kudi.


Cak ta tsaya lokacinda Glass din motar ya zuge tayi Ido hudu da matarda tabaro blue fox dinsu.


'dan hadiye fushinta tayi tareda 'dauke Kai zata tafiyarta tana damqe jakar kudinta.


Kudin dakika dauka nabiyoki karba ko"""""kamar daga sama taji saikar zancen ta tsaya cak tareda rintse ido tana damqe Jakarta tace'"aiko wlh banyarda Naga samu Naga Rashi bazan bayarda kudin nanba kome zaayi.


'dan qaqalo sakin fuska tayi tareda juyowa tace'"


Hajiya Dani kike???


Murmushin takaici umme tayi tareda cewa shigo muyi mgn idan bakyason Tarawa kanki abin kunya anan gurin.


Murmushi tayi tareda Dan matsowa jikin motar tayi qasa da murya tace"


Haj aini bana gudun abin kunya sbd acikinsa nake

Banda kowa Dan haka Babu Wanda zanjawa abin kunyar yi mganarki hajiya.


Kallonta umme tayi cikin tsananin qyama da mamakinta amatsayin mace ta yamutsa fuska tace"


Kudin dakika dauka nakeson kidawo dasu kokuma na miqaki hannun Yan sanda su rufeki har sai anmanta da sunanki.


Dariya amatu tasaki tareda dafe bakinta tace'


Haj canza dai Amma amatu Bata tsoron 'yansanda ataqaice Babu station dinda basusan niba.


Qarara mamakin umme ya fito tana sake kallon amatu din qyamarta na sake shigarta Dan tuni taji yarinyar ta sake fita ranta Sam Bata ko qaunar magana da ita Amma tun yanda ta lura tana kallon jakar  haj Maryam cikin kwadaituwa da yanda ta dauki kudin cikin tsananin kwadaituwa dasu da yanda take kallon kudin ta fahimci soyayyarta da kudi ba 'yar kadan bace shiyasa taqi tonata Kuma ta mayarwa da haj Maryam kudin ta biyota sbd ganin qila itadin zata iya aikinsu.

#mamuh#


_____________________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/13, 5:49 PM] Zafafa: *_MIN QALB 8_*

_mamuhgee_


Kallon tsantsan mamaki da firgici yanzu takewa amatu din tana kallon qafafunta zuwa hannunwanta dasuka Saba dauka da zuwa stations takeyi mamakinta na qara girmama musamman shekarun amatun datake ganin bazasu haura ashirin da uku ba,


Gyara zamanta tayi cikin motar tana 6oye mamakinta tareda 'dan kallon amatun datake qara damqe jakarta sbd kudin dake ciki alamar bakin Rai take da kudin ta saki wani guntun murmushi tana nazari wani abu kafin ta kalli fuskar amatun tana cewa'"


Ta yaro Mai takeyi Bata qarko

Idan har kinawa kudi wannan son ta tabbas zan baki kudinda kaf zuriarku bazaku iya qirgasuba,

Sake kallon amtun tayi tareda sakar Mata murmushi kafin yace"


Amatu idan da zaki bude idonki ki kalli Abinda nake qoqarin yi zaki fahimci Abinda nafada bashi nake nufiba sbd danaso kamaki da yanzu kin jima da sauya kammani a cell and banyi Miki Kama da wadda kike tunanin zaki fadawa bakya tsoron yansanda,

Amatu akwai rayuwa me kyau danake Miki fatan samu Wanda zaki manta da yanda ake sata,

Zaki samu rayuwarda ko a mafarki bakiyaba tunaninta,

Zaki samu duk wani Jin Dadi da kudinda saikin rabawa 6arayi 'yan uwanki ta yanda Suma bazasu qara tuna sunan sataba.


Wata siririyar dariya amatu tayi tareda sakin jakarta datayiwa riqon Gam Gam tana gyarawa jakar zama a kafadarta tareda gyara tsayuwarta tace"


Hajiya mama Allah ne kawai zai iya cike gurbin kwadayin samu kudi danake dashi Dan gurbin me mugun zurfi ne cikesa ba qaramin aiki bane

Kiyi hkr da wannan kudin Dana dauka tunda dai kinsan ba komai bane acikin arzikin da kike dashi to Allah ki barmin kawai sbd Nima dai bazan iya bayarwar ba.


Bude jaka umme tayi tareda ciro wasu bunches din guda biyu ta miqa Mata tana cewa'"


Ungo ki hada Dana hannunki ki hau abin hawa gobe zandawo spa dinku muyi mgn.


Tana gama fadar haka tace'"


Hafiz muje.


Jan motar yayi suka bar gurin da speed me qarfi suka barta da baki a bude tana kallon kudin hannuwanta da qafafunta na rawa sbd wannan ne karo na farko data taba ganin kudi a fili haka irin Wainnan Kuma ma a hannunta da sauri ta turasu jaka tareda fadawa ckin napep dinda ya tsaya gabanta Yana tambayar Ina zuwa malama?¿


Tunda tashiga napep din take share zufan dayaqi tsaya Mata gaba 'daya kanta ya shiga lissafi Bata taba tunanin kudi irin wannan zasu rudataba duk tsananin samu kudinta dubu talatin ne zuwa qasa albashinta ma duka duka dubu goma sha uku be duk wata saina mutane idan ta sanfo Amma yau itace keda kudi dubu 'dari uku a hannunta amatsayin nata bama na sata ba""wayyo Allah" tafada tana dafe gashi.


Kasa wucewa gida tayi direct ta kalla me a daidaita din tace yabiya da ita ta bakin Luna inda tasan usi na can.


A daidaita din na tsayawa bakin Luna ko fitowa batayiba ta hango bakin gurin cike an taru Kuma daga gani rigima akeyi babba sbd har mitar 'yan sanda ta iso gurin.


Da sauri ta fito tana cewa me napep din" Ina zuwa

Ta qarasa gurin da sauri sbd hango usi da ake kokuwar sakawa cikin motar Yan sanda Yana cijewa su Kuma sai dukanda sukeyi.


Tana isa ta qwacesa da qarfi tareda shiga gabansa tana karesa tace'"


Lafiya meyake faruwa??


Cikin sa'a Allah yasa insfector falalu ne a shugaban tafiyar Wanda tunda dadewa yayi sonta Amma ganin batamasan meye rayuwa ba batada mahimmanci agareta yasa ya qayaleta Dan dole Amma Allah yagani yaso aurenta.


Kallonta yayi Yana cewa'"


Amatu kibari idan munje can office zamuyi magana saiki San Abinda yayi.


Juyowa tayi ta kalla fuskar usi da harsun fasa gefen bakinsa taji wani mugun 'daci ya sauka zuciyarta ta juyo tana cewa'"


Idan zaa kamasa meyasa sai andakesa?

Laifin meyene da bazaku Bari sai anje can dinba kafin kufara hukuntasa?


Kallonta yayi tareda matsowa yayi qasa da murya yace"


Amatu karki Bata Mana aiki Kinga mutane na kallonmu kiduba can kiga kudin me gurin Luna din aka dauke daga tuhumarsa saiya Kama fada da yaran gurin gashinan yanzu an fasa kan 'daya acikin gurin Dole zamu tafi da usi.


Akaro na farko dataji ta tsani falalun cikin fidda 6acin ranta tace"


Duk cikin wainda akayi fada dasu usi ne kawai Wanda zaa Kama kokuwa Dan shi bashida kowane?


Kinga ba anan zamuyi wannan zancen ba sbd wannan laifin babban laifine yanzu haka yaron Yana asibi antafi dashi Babu me tabbacin kozai tashi Dan haka matsa muyi aikinmu 

Ku kamasa mine.


Kallonsa tayi da sauri zata tareda yayi saurin fitowa bayanta tareda miqa kansa sbd ganin idan bai miqa kansaba zasu iya ture amatun.


Yana kallonta yashiga motarsu Yana cewa' amah kije gida ba Abinda zai faru.


Tana kallo suka tafi dashi ta dafe Kai tana rintse ido cikin takaicinl ta juya takalla gurinda akayi fadan duk jini da kwalabai an faffasa ga kujerun gurin duk ayi jefa dasu.


Adaidaita ta nufa ta fada da sauri tana cewa yabi bayan motar yansandan.


Koda ta isa station din harsun cike Masa casefile da cewa yayi attemptin kisa take a qarfafa alamarin tini sukai masa mugun duka,


Duk yanda taso ganinsa ba dama abin wannan karon yayi qamari gashi ankira asibiti yaron har lokacin bai farfadoba gashi ya rasa jini sosai haka tayita yawo tsakanin asibiti da station a yinin ranar har kusan qarfe goma Bata koma gidaba qarshe ma dai kawu yazo sukaita yawon fafutukar case din Amma 'yan sandan sun shafawa idonsu toka sunqi sauraronsu.


Sai dare sosai suka dawo gida itada kawu ko abinci bataciba ta shige daki saidai iyami tabita daki da abincin ta takurata taci kadan.


Washe gari tunda safe suka koma station din gaba dayansu harda iyami amma ko abincin dasuka kawo Masa anqi karba itada iyami suka kwasa sukaje asibiti gurin yaron sbd falalu ya tabbatar Mata da ko yaron yatashi sai iyayensa dashi  sun janye qara zaa saki usi.


Kwana uku suna Abu 'daya duk wani cin hanci tabawa shegun sunkasa sakin usi ga asibiti andaura musu nauyin lalurar qaton saurayin Wanda taci alwashin cin ubansa idan ya warke.


Kwanansu biyar suna wahala kafin aka sallami kabiru din tun a asibiti taja ta tsaya ta kalli yayan kabirun da innarsu tace su janye qara tunda dai yasamu lafiya.


Qiri qiri suka qi janye karar Dan wata sabuwar rigima ta qullu tsakaninsu dasu kabirun kawu tas Saida ya 'debe musu albarka Amma sukaqi.


Station suka dawo tasamu falalu tayi Masa bayani ya kalleta bayan sun kebe kebe"


Amatu ki dage su janye qarar Nan sbd kowane lokaci yanzu kotu zaa iya tura case din Kuma wlh ana zuwa kotu gidan yari usi zaije hakan qara tabarbarewar kawai zaiyi gwara ya tsaya a iya sata kar abin yamasa yawa.


Oga falalu yanda kasan kafiran farko haka mutan Nan suke tsabar taurin Rai,

Munyi munyi sunqi janyewa ni wlh banmasan ya zanyi musu ba Dan dai tabbas bazan bari akai usi gidan yari ba akan wannan Dan laifin da Babu tabbas din shine yayi.


Amatu duniyarce ahaka 

Yanzu wainnan dakuke fama dasu Dan sunga duk kune marasa qarfi da ace case din da manya akeyinsa da yanzu case din ya mutu

Kusamu wani abu kubawasu yaron Inshallah zasu janye.


Numfashi ta sauke ahankali tace''


A rayuwa meyasa kudi sune masu mahimmanci,

Meyasa kudi zaifi rayuwar 'dan Adam mahimmanci,

Shin Dole masu kudi sune suke rayuwa yanda sukeso su huce takaicin komai a duk lokacinda sukeso.


Kiyi hakuri amatu Babu yanda zanyi be Dana taimaki Miki akan case din Nan.


Karka damu oga falalu Inshallah zasu janye badai kudine matsalar ba??daga  yanzu kudi bazasu Kara zama matsalarmu ba arayuwa,

Munga mummanan banbancin da akoyaushe ake nuna Mata fificin me kudi shine mutum mukuma muda dabba duk daya,

Ako yaushe muna qoqarin taka matsayin mutane kamar kowa Amma koyaushe ana sake durqushemu Alan hakan,

To idan hakane kudi sundaina zama matsalarmu zamu nemesu ta duka hanyar data dace matuqar hakan zaisa musamu daraja kamar kowa,


Ada mun dauka maraici rashin kowa shine matsalarmu data saka bamada daraja agun mutane sai yanzu nake gano kudin dai sune komai,

Idan bakada kowa matuqar kanada kudi ko bolace ta haifeka mutane zasu bika.



Akaro na farko a rayuwarta tundata girma hawaye suka ciko idonta ta maidasu tana girgiza Kai tace"


Karka tashi aiki oga falalu zanje nazo dasu ayau zasu janye qararsu a shirya takardun.


Tana fitowa tace kawu ya jira zataje tazo da masu qarar.


Gida tafara biyawa ta dauko kudin daya rage cikin kudaden ta qirga dubu dari da talatin da shida ta zuba jaka ta fito ta fice iyami ba batasan tashigoba.


Gidansu kabirun ta nufa cikin sa'a har yayansa da innar duk sunanan suna ganinta kowanne ya tsuke fuska alamar bazasuyi Mata alfarmar datakesoba murmushin takaici tasaki tana qarasowa tsakar qaramin gidan ta zauna gaban innar tana cewa"


Inna barka da yamma,

Kabiru ya jikin?


Ciki ciki innar ta amsa saidaima kabirun ne ya amsa da sakin fuska.


Bata tsaya batawa kanta lokaciba ta ciro dubun dari ta ajiye gaban kabiri tana murmushi tace"


Kabiru maganar janye qararku haryanxu bazaku janyeba kodan ana tare...


'dan washe baki kabirun yayi Yana kallon kudin kafin ya kalli innarsu da yayansa yaga yanda Suma suke yiwa kudin kallon qurulla suna zazzare idanuwa ya kalli amatun Yana qaqalo murmushin Shima yace"


Nifa dama usi abokina ne su innane suka dage da qarfafa qarar ni dama ban riqesa ba na yafe Masa tun ranardana samu kaina.


Cikeda mamaki innar tace"


Au kabiru hakama zaka fada?

Duk Abinda mukayi badan Kai mukayisaba shine yanzu tsabar rashin godiya zakace haka

Shikenan tinda haka kace ai saimu cire kanmu muma a janye qarar tunda kaida mukeayi danka baka ganiba.


Yayansa ma matsowa yayi Yana cewa'"


Inna qyalesa yayi maganin gobe Babu shegen dazai qara shige Masa gaba idan haka takuma samunsa Nima nacire kaina zuwa zanyi yanzu na janye qarar tunda abin nasa yazama raini.


Numfashi amatu ta sauke tareda rintse idanuwanta ta bude tana qara jinjina alamarin mutane.


Miqewa tayi tana cewa to tunda dai can kayi gurin janye qarar Bari nabika muje tare Amma Bari na tafi da kudin idan ya janye saina basa yadawo muku dasu ko??  Tafada tana dauke kudin tana sakawa jaka ta zura takalmanta tana cewa''


Acikin minti biyar kudi yayi aikin dana fi sati inayi Amma sun kasa fahimtata.


Adaidaita 'daya suka shiga suna Isa station din atake ya janye qarar tabiya kudin beli da tarar me shago dubu talatin kafin aka Basu usi din sukayo gida.


Tun a hanya tafe suke cikin adaidaita Amma batace qalaba tayi nisa sosai cikin tunani,


Ta gaji da wannan masifar ta kullum suna police ko gidan yari,

Duk yanda taso Hana USI rigima takasa sbd da rigimar sukeci suke Sha suke rayuwa,

Baya tunanin kansa sai nata danasu kawu,

Dukkanin aikin datakeyi tana ajewa shine yake samo matasu shi ya gammaci rigimar Amma dai ita yafison tayi aiki,

A iya saninta usi ya fison shi yayi satar a rufesa akan tayi shiyasa yaketa shiga rigingimu Yana kawowa gidan kafin lokacin albashinta

Ga kawu maganarma ace yayi sanaa Bata tasoba sbd tsufa daya taso Masa bama zai iyaba musamman tun zamansa gidan yari wahala ta cinye Rabin qarfin qafafunsa shiyasa yanzu yake Dan fama dasu,


Babban mafitar datake gano musu ayanzu itace usi dayake namiji yasamu yayi karatu yasamu damar daukar dawainiyarsu Nan gaba itadai karatu baya gabanta shiyasa duk burinsu itada kawu ya qare akan Usin yayi karatu Amma Abu ya gagara komai sai qara lalace musu yakeyi.


Koda suka Isa gida jiki a sanyaye kowannensu yashigo ita dakinta ma ta wuce Kai tsaye 

Kawu ma haka

Usin ne dai iyami ta zaunar tareda dauko ruwan zafin data Dora na jiran tsammanin Abinda zaa dafa suci ta gaggasa Masa fuskarsa da wuyansa da bayansa dasuka kukkunbura sbd duka da tsamin dasukayi.


Haka suka kwana dukkaninsu Babu Wanda yaci abinci bayan usi da maman junior takawowa taiba yaci sbd lurada basuda abincin ci

Dama Kuma dabi'ar jama'ar gidance taimakon juna duk da irin zaman fitinar dasuke yi idan sunga juna a matsi suna taimakawa junansu sai dai idan masifar ta tashi akwana a yini anayi.


Washe gari sauran canjin hannunta dasuka rage dubu biyar da dari uku  su ta bawa iyami dubu biyo aka siyo musu waina sukaci sauran Kuma ayi dubarar abinyi tayi Shirin fita aiki tasa  Usin ya shirya tafadawa iyami idan kawu ya tashi asibiti zata Kai usi sbd dukkanin raunikansa sun kumbura sosai ga yankan kwalba a gefen cikinsa gwara suje asibiti tun wuri.


Ganin kudin hannunta nada dama Dama yasa suka nufi wani babban private asibiti dake hanyar gurin aikinta ta baya cikin sa'a kuwa suna zuwa ba layi aka Basu izinin shiga.


Usin ne a gaba tana bayansa fuskarta fayau ba wata walwala ayau sbd tunanin raunikan na Usin kada wata matsala ta biyo baya.


Doguwar rigace a jikinta irin ta gwanjon indiyawa din Nan sbd tana doguwa sai sukai Mata kyau gashi Dan hijabinta na iya wuya ne na uniform din aikinta.


Sanyin AC da qamshin office din yasa ta lumshe ido tareda sakin murmushi tana kallon Usi dashima dadin sanyin AC din yasashi sakin murmushi Yana kallonta qasa qasa tace"


Usi karkayi saurin bashi amsa idan ya tambayeka Dan mu samu mu more sanyin AC dinnan na kwana biyu bansamesa ba sbd banje aikiba

Kodan AC bazanyi saurin aje aikin blue fox ba.


Gyaran murya doctor din yayi sukai saurin kallon inda yake zaune cikin fararen kaftans dasukayiwa kyakkyawar fatarsa kyau fuskarsa daukeda wani sahirtaccen murmushin dayasa amatu bude baki akaro na biyu dataga kyakkyawan namiji Mai wata irin Kamala da kwarjini saidai wancan din nasu insfector Garba ba murmushi a fuskarsa saima wani irin izza Mai bada tsoro sabanin wannan da kyakkyawan murmushinsa yaqara kyakkyawar fuskarsa kyau,

Tasaba da ganin irinsu insfector Garba dasu Sargent salisu da manager dinsu dasukeda fuskoki kamar tuwon daya tashi shiyasa yanzu take ganin wannan amatsayin kyakkyawan dayafi kowa.


Fadada murmushinsa yayi har haqoransa suka bayyana Yana kallon fuskarta sbd yaji Abinda suke fada yace"


Bismillah to Nima bazan tambayeka da wuri dinba.


Sosa Kai usi gayi Yana cewa''


Kyaleta Wasa takeyi likita.


Kallonta yasakeyi akaro na hudu yana qara fadada murmushinsa yace"


To kema Bismillah zoki zauna.


Qarasowa tayi ta zauna tana kallon sunansa da aka maqala a table dinsa DR KHALIL ZABEERA.


murmushi tasaki tana fadan sunan a hankali sbd hada kalmomin Dan karatun nata sai ahankali.

#mamuh#


_________________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899[3/14, 12:09 PM] Zafafa: *_MIN QALB 9_*

_mamuhgee_



Gabaki 'daya hankalinsa nakan fuskar amatu da ita Kuma hankalinta nakan usi da akewa dressing raunikansa bayan an wanke Masa hadda 'dinki Saida akai Masa a inda kwalba ta fasashi.


Sakin murmushi ganin yanda takeyi kamar ciwon ne ajikinta tanata yamutsa fuska tana cewa"


Usi daga yanxu ko sunan Luna nasake ji abakinka nice zanmaka dukanda ko kawu bazai iya ganekaba bare iyami,

Yanxu duba kaga yanda kakejin azaba

Shima wancan kabirun nasa Amin maganinsu Dan na aika buge katangar bayinsu ta  bayan gidansu ta yanda duk kudin dasuka karba zai qare a gyara kaikuma....


Cikin 'yar qaramar dariya ya katseta Yana kallonta cikin burgewa yace"


AMATULLAH antyn Usman ki kwantarda hankalinki Usman is perfectly fine,ba gashinan angama dressing ba shikenan kawai magani zai ringa Sha yanzu daganan raunikan zasu warke Suma.


Kallonsa tayi tareda kallon Usi dake cewa'"


Likita bafa antyna bace qanwatace.


Duka takai Masa da Jakarta tana cewa"


Kaine zakaita zama qani ako yaushe Dan haka kayi Mana shiru agurin 

Ina sake ganinka da kabiru nice zan dawo maka da duka raunikan nan sababbi.


Dafe dinkinsa yayi da sauri Yana cewa'"


Wayyo amah jini na fita dinkin ya warwa.....


Da sauri ta durqusa cikin firgici tana qoqarin Kai hannu tana cewa"


Dagaske?

Mun shiga uku,


Likita Zo ka duba Mana...


Dariya Dr Khalil zabeera yayi Yana kallon firgicinta dayasa takasa tsayawa ta lura usi din tsokanarta yakeyi ya kalli usi Yana cewa'"


Usman ka daina 'dagawa AMATULLAH hankali ko na saka a warware dinkin Nan ayi maka sabo yanzu.


Dariya usi din kewa amatun Yana qoqarin miqewa sbd dukan datake Masa da Jakarta sbd sosai ya fifgitata Dan sanin Babu Abinda take tsananin tsoro kamar wani abu ya samu Usin.


Takardar maganin daya rubuta musu ya miqawa amatun Yana cewa'"


Ga maganin dazai ringa Sha Nan bayan sati daya saiku dawo mu warware dinkin ko?¿


Karba tayi tareda kallon fuskarsa dake yalwace da murmushin dake qayatar da ita tace"


Mungode likita.


Girgiza Mata Kai yayi Yana cewa'"


Ki kula da kanki ba USI kawai ba AMATULLAH.


Qoqarin fitowa sukeyi nurse dinda yayiwa usi dinki na shigowa ya miqa musu takarda yana cewa"


Yawwa ga wannan zakuje ku biya kafin ku wuce.


Karba amatu tayi suna kallon juna da USI ta duba ita batama gane Abinda ke rubuce ba ta miqawa Usin tana cewa"


Duba kaga Abinda sukace aje abiya din.


 Karba yayi yana duba takardar Yana qoqarin hada kalmomin turancin Amma sunqi jaduwa ya duba gurin da akasa kudin yaga anyi 9 da zero hudu ya zato Ido da sauri Yana rawar murya yace"


Dubu casa'innn....


Mene?????ta fada da qarfi tana fizge takardar da sauri ta duba gurin kudin taga 9000 ta hadiye mugun yawu tana cewa"


Basuda hankaline??

Kuskure dai sukayi muje yayi Mana bayani

Dubu casa'in saikace fatarka suka sauya maka gaba daya tsabar gyara raunika.


Dr Khalil dake jinsu tun ayanda ya lura basuda wani ilimin bokon yasan ansamu rashin fahimta gurin duba kudin yaji sun sake burgesa ya taso yabi bayansu zuwa gurin biyan kudin.


Suna Isa amatu ta ajiyewa cashier takardar tana cewa"


Oga wannan dubu casa'in din da aka rubuto ta waye??

An Mana musayar takarda duba kagani.


Yanda tayi maganar yasa saurayin dagowa ya kalleta a wulaqance yace"


Malama takarda indai Kai aka bawa to Babu maganar kuskure idan biya zakuyi ku biya,idan kuna mamakin Abinda aka rubutane to wayace kuzo Nan da saiku tafi asibitin gwamnati.


Yanda yayi Masu maganar yasasu quluwa dama amatun a qule take da kudin cikin takardar kallon walaqanci tamasa tana cewa'


Kai Karen asibiti karkace zaka gaya Mana magana anan gurin 

Da kake maganar asibitin gwamnati idan har irinku zasuzo Nan suyi Karen asibiti mezaisa muma bazamu zoba???


Miqewa yayi tareda fitowa ya zagayo gabansu Yana nunata da yatsa Yana cewa'"


Kisan Abinda zaki fada Nan bama tolerating 'yan iska irink.....


Saukar mari yaji daga sama kafin yakai qarshen maganarsa

A gigice ya dago usi ya cakumosa Yana cewa"


Bayan wannan Marin har kamanni zan sauya maka duk bakinka yasake furtawa 'yar uwata wannan kalmar.


Da sauri mutane dasuka Ankara sukayo kansu ana qoqarin rabasu Koda Dr Khalil ya iso gurin harya 'dan cika abin ya girmama da sauri ya qaraso gurin Yana zuwa ya kalli usi cikin tausasa murya yace"


Usman sakeshi.


Dakinda USI yayi Yana cewa'"


Ka iya bakinka wannan tafi qarfin ko uwarka.


A harzuqe saurayin ya taso Dr Khalil yayi Masa wani mugun kallon dayasashi dakatawa Yana huci yace"


Dr wainnan 'yan iskan.....


Shut up""Dr khalil yace da Dan fada Yana cewa'"


Jafar koma gurin aikin and everyone should leave from here please.


Da sauri kowa ya watse Yana mamakin Dr Khalil daya marawa wainnan baya maimakon staff dinsa.


Bayan kowa ya watse ya kalle Usman da har lokacin ransa zafi yake da kalmar 'yar iskar da aka Kira amatu da ita yace"


Usman this is not how to behave with people musamman wainda kasama gurin aikinsu,

Meye abin fada anan infact meyema matsalar??


Kallon Usi amatu tayi tareda sakin murmushi danta saka ya sauko tace"


Kai usi meye na wani fada tun bamu biya wannan kudin da ake fada akai ba zakayi wani fadan kaji rauni kasa kawu ya cinyeni 'danyata.


Kallonta yayi a raunane zaiyi magana tasaki murmushi tana ce Masa"


Karka damu ka manta bama saka maganar kowa aranmu sbd bamuda abin damuwa,

Duk sunanda zai kirani dashi tunda dai banida Wanda hakan zai zubar Masa da mutunci to meyene aciki?

Kawu ne Kuma Shima zagi da maganar kowa Bata tabasa Dan haka barsu su kirani da kowane suna baya damuna,

Usi Kaine damuwata Dan Allah ka daina shiga rigimarda zata saka a hadari,

Ka manta munada burin cikawa na zama alhazai" ta qarasa fada tana dariya sbd Shima ya sake.


Sakin fuska yayi Yana cewa'


Muje nidai.


Tunda suka Fara magana yake kallonsu cikin wani irin yanayi yanason fahimtar zancensu dakeson nuni da su din marayune.


Gyaran murya yayi tareda gyara tsayuwarsa Yana miqa Mata hannu yace'"


Bani takardar kudin mugani.


Miqa Masa tayi tana shafawa idonta toka tace"


Dr mudai wannan kudin da aka rubuta mu biya bazamu iya biyansu ba sunyi yawa ni banma taba Kai qirqen casa'in ba a lissafin kudi

Ni ko inadasu bazan bayarba wlh ba kawuba koni bazan iya barciba duk ranarda nabayar dasu.


Murmushi yasaki sbd dama yasan za'a Rina ya kalleta yana cewa"


Basaikin kasa bacci ba AMATULLAH dubu Tara ne a rubuce ba dubu casa'in ba.


Kallonsa tayi da sauri tana karban takardan da sauri tana sake dubawa tana bin numbobin dakyau tace"


Eh hakane kuwa..


Dagowa tayi tana kallon Usi cikin masifa zata Fara magana yayi saurin cewa'"


Yi yi hakuri da masifar Inaga banduba daidai bane kokuma ban fahimta bane.


Hadiye masifar tayi tana cewa'"


Usi rashin karatun Nan saiyasa an dauremu wata Rana.


Dariya sukayi atare kafin ta kalli Dr khalil tace"


Dr ai maganar gskia ko dubu Taran Nan bazan iya biyaba zandai biya dubu biyu idan zaa karba.


Kallonta ya shagala da yi tana sake burgesa yace"


Usman kanada 'yar uwa anan,

Kawun Nan Shima yanada 'ya anan.


Murmushi tayi tana dauke ido daga wallet dinsa daya 'dan fito da aljihunsa daga gani Kuma tasan bazai rasa kudiba aciki Amma sbd kirkin Dr din tanata dauke ido akai sbd hakurinta yakusa qarewa takaiwa wallet din Hari.


Zaro wallet din yayi ya bude yaciro ATM dinsa ya miqawa cashier ta window tareda takardarsu yace acire.


Bayan ancire aka miqo Masa receipt ya miqawa amatu receipt din Yana cewa'"


Shikenan har dubu biyunki anbar Miki AMATULLAH.


Karba tayi ba wata kunya a idonta tace"


Aikuwa ka kyauta Mana Dan akan dubu Taran Nan nafison na kwana 'daya a station da safe na fito nayi gida da dubu Tara ta.


Girgiza Kai yayi Yana murmushi harsuka wuce Yana binta da kallo zuciyarsa na karban baqon yanayin dake shigarta akaro na farko da mace ta sauya bugun zuciyarsa a ganin farko.


Suna fita ya koma office dinsa yasa Akira Masa daya daga cikin nurses dinsu dayaji Yana fadin yasansu amatun lokacinda ake fadan dazu

Yana buqatar sanin inda suke.

##mamuh#



_________________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/14, 12:09 PM] Zafafa: *_MIN QALB 10_*

_mamuhgee_




Suna fitowa daga asibitin gurin aikinta suka nufa ya ajiyeta da adaidaita kafin shi yawuce gida,

Babban Abinda yasa yau tazo aikin shine Jin ko hajiyar Nan tazo nemanta sbd yanzu dai Kam tana buqatar ganinta kodan Abinda yafaru yau na rashin ilimin dasukedashi sosai yasa taqarajin buqatar karatun nasu Amma dai yanzu na usi ne agaba.


Da manager tafara haduwa a reception din blue fox din tana ganin ya washe Mata baki ta tsuke fuska tana cewa"


Wannan Dan wahalar zai Fara damuna yanzu da surutansa wainda basuda amfani aguna,.


Yana qarasowa itama ta washe Masa baki da gayya tana cewa'"


Manager sannu da yawo.


Washe baki yasake yi Yana shaga dogon kansa yace"


Amah 'yan amata ya aikin?¿ Sai yanzu Kika shigo?


Eh sai yanzu nashigo na yagi robana daya wuceni kwana biyu.


Me Kika??


Aa cewa nayi nayi latti Bari naje kafin a nemeni.


Tana fadar haka ta wuce tana cewa''


Kuje kuga gayu da wayewa gurin Dr

Amma kunzo kaida insfector Garba bansan Waye haqoransa sukafi na wani dafewa ba.


Tana shiga saloon madam bell ta kalleta cikeda mamaki tana cewa"


Amah sai yau kikaga Daman zuwa aikin???


Ta gefen ido ta watsawa madam din mugun kallo kafin tace"


Madam lalurace ta hanani zuwa ba ganin dama ba.


Bude Ido madam tayi tana cewa"


Ni kike wa magana haka?


Dauke Kai tayi tai qasa qasa da murya tace"


Ke din uwatace?


Me kike cewa amahhh?


'dan washe baki tayi cikin gatse tace"


Cewa nayi sorry madam.


Qwafa tayi sbd taji Abinda amatun tafada da farko tace"


To ki tafiyarki kawai Dan anyi replacing dinki da wata.


Kallon baibai tayi Mata tana cewa"


Madam korata kikayi ne?


Eh" madam din tafada Kai tsaye tana cigabada da aikin datakeyi.


To Ina tayaki murna madam bansan an maidake manager ba da bana nan.


Aje Abinda takeyi tayi tana yiwa amatun kallon mamaki sbd tasan baqar Magana ce ta jeho Mata wato tunda ba itace manager ba bazata iya korarta ba.


Amatu na ganin ta kunnata ta gyara tsayuwarta zata sake wata maganar aka bude qofar shigowa ana cewa" welcome ma.


Madam ce tayi saurin aje towel din hannunta tana nufar qofar bakinta a washe tana cewa'

Welcome ma.


Gyara tsayuwa amatu tayi batareda ta juyaba Kuma batada alamar juyawar 

Taji ankira sunanta 

Da sauri ta juyo sbd ta 'dau muryar 

Aikuwa ita din ce ta qarasa gabanta tana kallon madam bell tasaki yaqen tura haushi tace"


Madam dama bankwana nazo Miki tareda tayaki murnar samun matsayin manager Dan haka Allah ya sanya alkairi.


Kallon hajiya aisha tayi tana qaqalo murmushi tace"


Haj Mama Ina kwana???


Murmushin mamakinta umme tasaki tareda kallon madam bell tace"


Dama ita nazo nema sai dai next time idan nadawo,amah muje ko???


Gaba amah tayi tana murmushin farin cikin daga yau rayuwarsu zata canja idan har hajiya mama tabata sabon aikin datake cewa.



Motar haj Aisha din suka shiga wani sanyin AC da qamshin ya ratsata ta lumshe ido tareda shafa kujerar motar datajita da wani irin laushi da santsi,

Yaune karo na farko a rayuwarta data taba shiga motar Dana taxi ba ko taxi din tafi shekara goma rabonta datashiga.


Kallon motar takeyi tako Ina tana tabawa ta kasa 6oye farin cikin datake ciki a fili tace"


Hajiya mama ko ahaka Kika barni kincikamin qaramin burina....


Dauke Kai haj Aisha tayi cikin gundura da amatun tun yanzu tace"


Motarma gaba daya zata iya zama mallakinki ko 'dan uwanki usi da Wanda ma ya tsinceku idan har zakiyi Abinda nakeso Wanda a wata biyar kingama aikinki Kuma kin mallaki Abinda zakiyi hannun riga da talauci.



Parking motar tayi daidai kwanar gidansu amatun Wanda yasata juyowa ta kalleta ta yanda tasan gidansu zatayi magana hajiya aishan ta katseta Kai tsaye da cewa"


Zan baki naira miliyan uku tareda makaranta me tsada wa 'dan uwanki harya gama sai gidan zama me kyau ga kawunki da jarin sana'a me kyau ga matar kawunki idan har zakimin Abinda nakeso.


Suman zaune amatu tayi tareda sakin baki gaba daya ta daga hannu tana lissafa abubuwan da hajiyar tace har lissafinta ya 6ata tayi saurin girgiza Kai tana 'dan dukan kanta tace"


Amatu amatu amatu dawo kanki... Dawo kanki.....

Hajiya mama duka abubuwan Nan dakika fada saidai naji kokuwa kunnuwanane????


Qaramin tsoki umme tasaki tareda bude wata 'yar jaka dake daukeda kudi dubu 'dari uku ta miqa Mata tana cewa"


Kije kibawa su kawunki wannan idan kingama aikin zanbaki dukannin Abinda nace

Qaninki kuwa zanbaki takardun makarantarsa ki riqe a hannunki.


Da sauri ta karba kudin ta shafa cikin zaquwa take cewa"


Wannan yanxu duk nawane halak malak??

Hajiya mama na amince zanmiki aikinki koma wane iri ne na shekara biyarma zanmiki bana wata biyar ba.


Kallon takaici umme tai Mata tana mamakinta saidai duba da 'yar tashace Kuma 'yar bola hakan ba wane abin mamaki bane Dan duka tarihinsu tasamu agurin binciken datasa akai Mata akansu Wanda alhaji mande ne yabada bayajin

Shiyasa tasan tsaf amatun zatayi wannan aikin ba gashi indai akan kudi ne.



Zanje dake gidana zaki gabatarda kanki a matsayin wadda akayiwa fyade harda ciki ajikinki,

Ba shaidu,

Duk wasu manyan shaidu na tanadar Miki su tun daga Kan likitoci harzuwa Abinda zai biyo baya,

Aikinki na kammala na tanadar muku gida da sanaar yi a wani guri can nesa da Nan bazaku sake dawowa Nan ba shikenan kunyi bankwana da talauci da damuwa zaku samu damar Fara sabuwar rayuwa.



Duk iya yanda ta rude da Jin abubuwan dazata samu Bata taba kawo hajiyar batada isashiyar lafiya ba sai yanxu datai wannan maganar Amma Kuma bataga alamar hauka atareda ita ba,

Itadai yanxu matsalar dayace ko haj nada lafiya ko batada bazata mayar Mata da kudin nanba.


Yanda amatun ke kallonta yasa ta fahimci tunaninta ta 'dan qaqalo sakin fuska tace"


'dana ne nice na haifesa

Nasa kimin hakan ne sbd banason abawa 'yayana mulkinda zasu cutu Kuma Allah ya tambayesu ranar qiyama,

Mulkin zabeera akwai hadari,

Za'a iya hallakarmin da 'yaya sbd kwadayin mulki shiyasa nakeson kije amatsayin hakan Dan kada abawa 'yayana mulkin da zarar an nada wanda yakamata a nada zan kaiku inda zakuyi rayuwa cikin farin ciki da walwala.


Shiru amatu tayi tareda gyada Kai sbd  soyayyarta da kudi yasa Kai tsaye tayi na'am da hakan Kai tsaye tunda daima ceton Rai ne zatayi koba komai Babu ruwansu da wani abin kunya tunda dai bayi tayiba tasan dai kawu ne bazai yadda da wannan tsarin ba bare iyami.



Kallon kudin tayi ta kalla hajiya aishan tace"


Kinada tsarin fadawa kawuna ya amince???

Dan nidai nariga na amince.


Murmushi umme tasaki tareda tayarda mota suka qarasa shiga layin gidansu amatun tace"


Kawunki bazaisan gskia ba sbd gudun samun matsala agaba,

Kidai saka aranki aikin kudine zakiyi domin samun ingantacciyar rayuwarsu kawai zan aiko a sanar dashi kinsamu aiki a zabeera tareda albashi me kyau zaki ringa zuwa duk sati kina ganinsu har tsawon wata biyar.


Kawu bazai yadda ba"tafada tana tunanin mafita.


Karki damu zai yadda idan wadda zanturo tazo saiki qara da dubarunki ta yadda zai yarda.


Kallonta amatu tayi kafin ta kalli kudin tsawon daqiqu tana nazari zuciyarta na son yin rawa a alamarin Amma burinta na hana hakan.


Rintse idanuwa tayi tareda sauke ajiyar zuciya me qarfi ta furta na amince saitazo nikuma Ina fatan wannan alqawarin yacika.


Gyada Kai kawai hajiya aishan tayi tareda nuna Mata qofa.


Fita tayi tareda kudin tabi motar hajiya aishan da kallo harta bace mata ta sauke ajiyar zuciya tana cewa'


Amatu wannan sa'a ce ko rashin sa'a???


Tana shiga gida Kai tsaye gurinsu kawu taje Allah yasa duk suna dakinsu kawun harda USI dayashigo yanashan magani kawu Kuma na gefe yanashan waqar 'dan indo,ta qaraso ciki tana sallama tareda qarasawa ta zauna gefen iyami dake ballowa usi magani ta ajiye Daurin kudaden tareda sauke boyayyan numfashin zancen dazata qirqiro.


Idon kawu na sauka kan kudin yatashi zaune da sauri daga kishingiden dayake Yana qarar radionsa Dan kada aji Abinda zai fada yace""kudi" Yana sake bude idonsa akansu.


Iyami ma dakatawa tayi daga bude maganin ta kalli amatu da sauri,


USI ma kallon amatun yakeyi zaiyi magana ta rigasu da cewa"


Duk nasan tunani kukeyi dabam dabam 

Iyami wlh tallahi ba kudin wasu bane na dauko,

Kawu aiki aka koreni sbd nayi kwanaki banje ba to, to ,to shine dama inawa wata babbar hajiya mama aiki a saloon dinmu shine tace ita zata daukeni aiki zata budemin gurin aiki irin fire fox me sassa dabam dabam wanda nice zanzama managan gurin Amma....


Amma me????iyami ta tambaya da sauri zuciyarta naqin gasgatuwa da zancen..


Amma Wai sai nashiga training dinda zaayiwa manyan ma'aikatansu a can inda aka kebe na tsawon wata biyar zuwa shida.


Tsit sukayi a dakin duka kowa na qoqarin fahimtar zancen saidai ta Yaya??


Kallonta USI yayi dakyau yaga itama shi take kallo yace"


Amah idan har cigabanki ne me kikeso yanxu to.


Kallon kawu da iyami tayi Shima kawun kallonta yake yace"


To wannan kudin fa???


Kai tsaye tace kudin albashinane aka bani na watannin Dan daukar nauyin Kai kafin mu fito training din.


Iyami ta kalla tace"


Wlh iyami aiki zanje Yi ba qarya nakeyiba na rantse Miki...


Duk shiru sukayi kafin kawu yace"


Naji kuje zanyi tunani akai.


Miqewa tayi ta fito usi ya biyo bayanta suna fitowa yafara watso Mata tambayoyi tajasa zuwa dakinta da sauri Dan kar kawu yajisu suka zauna tafara yimasa bayani komai Kai tsaye yace wlh bai amince ba.


Hayaniya suka Fara tayi saurin rufe qofa tana cewa"


Idan baka gaji da yawon cell ba ana maka dukan wulaqanci to ni nagaji da ganin hakan,

Rayuwa me kyau nakeson muyi kamar kowa Usman,

Idan har kanason farin cikina danasu kawu wannan maganar mungamata,

Banyi Dan Jin dadinaba sai Dan wainnan bayin Allan dasuka sadaukar da komai saboda mu,

Babu uqubar dabasu shigaba amma suka riqemu da Amana,

Kaima inason ganin kasamu ingantacciyar rayuwar sbd ka tallafesu a gaba Dan ni nasan rayuwata acikiku taqaitacciyace kobanaso nasan Dole wata Rana kawu saiyamin aure..


Usman mubar maganar Nan kawai qwarin gwiwarka nake nema.


Kallonta yayi idanuwansa na cikowa da hawaye yanajin inama ya mutu ya rage Mata 'dawaimiyar datake ganin itace akai,

Maimakon yazama jagora Amma yazama wani irin koma baya itace jagorar.


Ficewa yayi Yana share hawayen fuskarsa dasuka saka jikinta yayi sanyi matuqa Amma batajin zata fasa sbd tariga takai qarshe zasu bar Nan din sbd karatun Usman din.



Kwana biyu ana rigima sosai a tsakaninsu kafin iyami da Usin suka  amince akan aikin nata bayan dattijuwar da aka aiko tayi zuwa kusan hudu tukuna.,


Kwana uku masu zuwa zata tafi Amma duk sai jikinsu su hudun hakanan ya mutu sosai suka shiga damuwar tafiyarta duk da dai Basu fadaba sai hakan yataba 'yan gidan Suma sbd su kawun dadu amah sune hayaniyar gidan dake qara Raya gidan shiyasa Suma duk sai sukaji ba Dadi,


Amatun ma hakanan takejin kamar zata rabu dasu kawun ne rabuwar har abada Wanda usi ne ma tadawo Yana qoqarin cire Mata damuwa,


Iyami da kantace ta hada mata duk wani abin buqata a 'yar Jakarta ta goyawa ranarda akazo tafiya da ita iyami duk hakurinta saidatayi hawayen rabuwa da amatun sbd zuciyarta takasa samun nutsuwa da tafiyar,

Kawuma kasa rakiyarta waje yayi saidai Usman ne aka tafi dashi Dan yaje yaga inda take.


Su maman junior hadda rungumeta sukayi sunajin kewarta tun Bata tafiba.





****

Wayarta data gamayi ta kalla tareda kallon haj Maryam dasuke zaune a palon tace"


Su amah ne gasunan a hanya isowa zasukai mintuna ashirin kafin su iso zuwa lokacin an halarta gurin meeting din familyn ZABEERA daza'ayi  yau

Yau komai zai qarewa MD ZABEERA.


Murmushi haj Maryam tasaki tana miqewa tsaye tace"


'yan jaridar Dana gayyatoma suna daga baya suna jiran kirana suzo ya sakarwa duniya wannan labarin da dumi duminsa.


Dariyar farin ciki suka saki atare daidai lokacinda nuratu tashiga cikin kyakkyawar adonta na wata Kuwait jallabiya datayiwa fatarta kyau sai qamshi takeyi tace"


Momy kusan kowa fa ya halarto dan gasu anty bahijja nacan sun iso taredasu anty juwairiyya dasu baba qarami.


MD ZABEERA ma Naga shigowarsa yanxu tareda ZARAH.


Kallon juna sukayi tareda cewa"


Shikenan muje.




***

_40 min later_


A bakin babban qaton gate din ZABEERA motarsu ta Parker Wanda akayi juyensu da ita zuwa wata matacciyar golf baqa.,


Akaro na farko ta 'dago hoton MAHMOUD ZABEERA da aka Bata bayan anmusu bayani wasu abubuwa akansa ta kalli hoton zuciyarta tayi wata irin bugawa akaro na farko...


Rintse ido tayi zuciyarta na wani irin tsalle tayi saurin rufe hoton tana dafe zuciyarta dake bugawa da qarfi tace"


Ya Salam..

Meyasa zuciyarta ke bugawa da ganinsa a hoto???

Kallon Babar dasuka Zo tare tayi tana qoqarin Hana zuciyarta bugawa Amma sai qara bugawa tayi tayi saurin miqa Mata hoton tana cewa'"

Ki riqe a hannunki nariga Naga hotonsa zan ganesa da kaina.

Kallonta baba Jamila tayi tana cewa'"

Ki nutsu fa.

Gyada Kai tayi tana yiwa qatoton gate din zabeeran kallon kwadayi da qauyanci.

Shima usi kalle kallen yakeyi baki abude sbd tsananin girma da kyan gate din kafin suka nufo gate din Babu dogon musu sbd babban security in charge yasan da zuwansu yasa aka Bari suka shigo suna kalle kallen baki asake 

Amatu tace"

Usi kana ganin Abinda nake gani kuwa????

Kasa magana yayi yafarabin manyan motacindake harabar gidan da kallo Yana cewa'"

Wlh amatu wannan gidan aljannar duniya ce muka shigo.

Itama motacin tahau shafawa tana cewa'"

Aikuwa sa'a takawoni Nan ni amatu.









No comments

Powered by Blogger.