Min Qalb 11-15


 







MIN QALB 11*_


_mamuhgee_

Babban palone na alafarma irin tsarin sarautar zamani daya dauke setin royal kushins hudu golden and red sbd girmansa ga kalar dasuka qara qawata palon,

Shine palon da dukkanin familyn ZABEERA ke meeting acikinsa qarshen kowane wata to wannan watan ma hakan ce tafaru dukkanin daukacin zabeeras dake jahar suna cikin palon kusan su sama da arbain kowanne yasamu guri ya zauna ana tsimayin fitowar me kankat wato Modibbo Wanda fitowarsa tayi daidai da tsit da gurin ya dauka sai gaisuwa kawai dake tashi Yana amsawa ta hanyar 'daga Kai batareda ya bude baki ba.


Zama yayi Yana bin kowa da kallon jinjinawa na riqe wannan al'adar dasukayi har idanuwansa suka sauka akan MD ZABEERA wanda ke zaune can bayani iyayensu dukkanin hankalinsa gabaki daya Yana Kan waya dayake karanta email din saqo daya shigosa,


Kallon zamansa Modibbo yayi har zuwa fuskarsa dake daukeda wani irin kwarjini da haiba ya jinjina Kai Yana cewa'


Tabbas Babu wani zabi daya wuce akan mulkin zabeera ayau taron naka ne.


ZARAH kuwa duk da ta shige cikin 'yan uwa da qawayenta 'yan uwanta Amma hankalinta na kansa akai akai take satar kallon gefen dayake sbd ganin yauma dai kamar ko yaushe arayuwarsa ya kebe ne daban duk da yanzu duk Wanda yashigo cikin qanne da tsaransa ma harma da wainda suka girmesa zuwa sukeyi suna gaidashi Wanda Shima yawanci daga Kai ne kawai bai cika bude bakinba Yana amsawa musamman sbd rashin sabo da Yan uwan duk wasu da dama baisansuba.


Khalil ne abokin zamansa akowane meeting tun quruciya Amma yau Khalil din baishigo da wuri ba Abinda baitabayiba ranar meeting wato latti.


Khalil kuwa yanacan ne hanyar gidansu amatu data Hana rayuwarsa da zuciyarsa sukuni,

Tsawon kwanakin Nan bayan haduwarsu da ita bincike yayi me kyau akanta sbd shigo da ita a rayuwarsa Dan sauya musu ingantacciyar rayuwa dakuma tunaninta daya kasa fita ransa da kansa,

Tabbas yasan babban laifine a zabeera neman aure a waje wanda bama ataba yiba asai yanzu dazai Fara shigo da tsarin karya dokar manya sbd bayajin zai iya hkr da maganar amatun a shirye yake daya tallefi yarinyarda zuciyarsa ta riqe a gani na farko Koda hakan na nufin barin zabeera ne barema yasan zai shawo kansu da taimakon MD.


Babban rashin sa'ar dayaci shine bayan isarsa kawu yayi Masa bayanin aiki tasamu ta tafi training Amma dai yabasa numbernta Dana usi din duk da shi Usin Rakata kawai yayi dawowa zaiyi.


Koda ya karba lambar agogo ya duba yaga yayi lattin meeting ga umme Bata gansa ba sai kiransa takeyi 

sai bai tsaya Kiran numbrn ba yayi saving tareda dawowa zabeera cikin sauri sbd yasan zuwa yanzu anfara meeting din.


Yana qoqarin shiga gate din zabeera yaga motar 'yan jarida na tsayawa ta gate suna qoqarin gyara cameras dinsu ya Dan tsaya Yana kallonsu cikin mamakin meya kawosu musamman ma da zabeera basa muamala da duk Abinda zai hadasu da 'yan jarida sbd tsira da mutuncinsu da sunans ahalin,

Ganin yayi latti sauri yakeyi yasa bai tsayaba yashigowarsa,

Yanayin parking harabar gidan Kiran nuratu nashigowa wayarsa ya saki siririn tasaki Yana dafe kansa dake Masa ciwo sbd rashin bacci kwana biyun yayi rejecting kiran ko Ina bai tsayaba Kai tsaye ya nufi palonsu na meeting dasuke Kira da zabeera hall.


Yana shiga yaga har anyi nisa yayi saurin yin gefenda ya hango md zaune Ya lumshe fararen idanuwansa ya kwantarda kansa ta baya jikin kujerar dayake Yana sauraron Abinda ake fada cikin nutsuwa.


Qoqarin miqewa alhaji qarami yakeyi zaiyi mgn suka Fara jiyo hayaniya me 'dan qarfi tana tashi daga wajen qofa,

Sharewa sukayi alhaji qaramin yafara bayani Amma sai gaba hayaniyar keyi

Alhaji qarami ya kalli yakub babban 'dan alhaji qaramin yace"


Yakub dubo meke faruwa ne.


Miqewa yayi ya fita Dan dubowar sukuma suka cigaba da meeting din.


Mintuna biyu da fitar yakub sai gashi yadawo da sauri yazo gefen babansa yayi qasa da murya yafada Masa abin dake faruwa da sauri ya kallesa Yana cewa'"


Mene?


Kowa najin haka yayi tsit suna jiran jin abindake faruwa.


Je kashigo dasu""alhaji qarami yace Yana qoqarin cigaba da bayanin dayakeyi.



Sallama sukayi wadda tasa kowa juyawa hadda Shima dazaiyi maganar duk suka kalli qofar wadda ke seti tana kallon center inda Modibbo yake zaune Shima sbd ba'a taba barin wani shigowa ba idan suna taron yasashi dakowa ya kalli qofar.


Baba Jamila ce agaba amatu na bayanta fuskarta rufe da doguwar hijab dinda tasaka fuskarta da idanuwanta a kumbure sosai sunyi jajir tsabar aboniki dasuka Sha kamar wadda tayi wata biyu tana kuka.


Tsit sukayi kowa palon na aika musu da kallon mamaki da jiran bayani Amma sai qif qif baba Jamila keyi da idanuwanta tana sunkuyar da Kai.


Alhaji qarami ne ya kalleta tareda kallon amatun dake bayanta kafin ya kalli qafafunsu har zuwa zamansu ya gyara murya yace"


Malama Yaya dai??

Lafiya??

Daga Ina??


Saurin zubewa qasa tayi tareda sauke kanta qasa cikin rawar murya tanason fashewa da kuka tace"


Ranka ya Dade adalci nazo nemarwa 'yata...,


Kowa kallonta yayi wasu Kam Kai tsaye kallon mahaukaciya suke Mata mamakinsuma yanda akayi tashigo zabeera harta iso Nan din.


Cikin mamaki alhaji qarami ya miqe ya qaraso gurinta ya tsaya Yana cewa'"


Malama adalci kike nema ai banan ake zuwaba,

Mu Nan Kinga Muna wani taro ne me mahimmanci kinyi batan hanyane kije security zasu nuna Miki qofar fita......


Girgiza Kai tayi wannan karon tana fashewa da kuka Mai shiga zuciya tana bubbuga kanta.


Yanxu Kam mamakinsu yafara cirewa sai fargaba

Kamar daga sama taji saukar muryar dattijo me ran qarfe,

Muryar data saka 'yan hanjinta kadawa Dan tsoro da firgita da wani irin amo yace"


Idan da kanki a hayyacinki kikazo Nan kifadi Abinda yakawoki kokuma ki hadu da hukuncin kutse da datse mahimmin Abu acikin zabeera.


Jan hanci tayi tana shage hawayenta dasukaqi tsayawa murya na rawa tace"


Ranka ya dade 'yatace gatanan cikine a jikinta......


Cikin tsawa me qarfi alhaji qarami ya e"


To Nan asibitine ko gidan aurenta dazaki......


Uban cikin Yana Nan"""ta katsesa cikin rawar murya tana sake bulbulo da ruwan hawaye.


Atake gurin yayi tsit kamar ruwa ya cinyesu musamman Modibbo daya gyara zama Yana kallon matar da kyau kafin ya dago ya kalli amatu dake tsaye har lokacin tana matso hawaye cikin hijab.


Kallon amatu yayi cikin wani irin amo yace"


Ke yarinya bude fuskarki kiyi bayaninda mahaifiyarki keson fada saidai duk Abinda zaki fada kifara tunanin a inda kike.


Qarar wayar Dr khalil ce ta katse maganar Modibbo wadda tasa kowa juyowa ya kallesa da sauri ya Danna wayar tareda miqewa ya fita da sauri Yana magana qasa qasa sbd daga asibitinsane ake Kiran wasu takardune da ake buqata emergency yace suzo su karba Nan gida.


Harabar gidan ya nufa gurin motarsa yana tareda budewa ya dauko takardun cikin Burnet din motar ya nufi bakin gate ya fita Dan miqawa Dr ashir.


Sama sama yayi Masa bayanin takardun sbd hankalinsa dake Kan 'yan jaridar da har lokacin suna gurin take yaji yakasa samun nutsuwa da hakan,


Meke Shirin faruwane?

'yan jarida a qofar zabeera,

Ga Kuma wasu baqi aciki suna maganar anyiwa 'yarta ciki.....


Da matsala yafada Yana sallamar Dr ashir ya juya ciki da sauri Yana tunanin Dole da akwai inda matsala take,

Me zaisa wannan matar su gayyato 'yan jarida??anshirya hakan ne Dan idan baa karbi cikin bane kokuma me??

Something is definitely fishy mezaisa tazo da masu jarida ita Bata damu da mutuncin 'yarta bane idan Yan jaridar suka watsa to kodai tanada wani manufa be??? Oh no.." yafada da sauri tareda yin ciki da sauri haryana hadawa da gudu gudu...


Karo yayi da mutum Wanda yasashi yin baya zai Fadi USI yayi saurin rikosa Yana cewa'"


Dr.


Da sauri Dr khalil din ya dago Ya kalli Usin mamakinsa a bayyane Dan komai nasa ya nuna mamakin cikin sauri yace"


Usman?

Kaine anan?

Me kakeyi anan??


Kallonsa Usman yayi Yace"


Aiki amatu tasamu anan......


Saurin gintse bakinsa yayi sbd shaf ya manta Abinda ya kawosun.,


Ya shafo kansa Yana waskewa yace"


Dr kaima me kakeyi anan din???


Kafa Masa Ido Dr khalil yayi ba Wasa a fuskarsa yace"


Wane aiki ne amatu tasamu anan din??

Ina amatun take????


Shiru yayi Yana shafa Kai Yana qoqarin hado qarya Dr khalil ya katsesa da cewa"


Ina amatun?


Rasa yanda zaiyi yayi yace"


Tana ciki tashiga da wata Mata.....


Wattt???

Yafada da qarfi cikin firgici da tashin hankali yace"


Meke faruwa?

Me sukaje yi?

Infact meya kawoku Nan din nakeson ji""zuwa lokacin yafara hasala yace"


Kuma wlh karka kuskura kamin qarya.


Kame kame usi yafara Yana neman yanda zaiyi saidai gskia zai fadawa Dr khalil idan yaso qila shi zai taimakesa ya shawo Masa Kan amatun kar tayi Abinda zatayin

Kallonsa yayi tareda jansa gefe yace"


Dr Dan Allah kayi alqawarin zaka taimaki amatu bazakayi Abinda zai jefata hadariba Dan Allah kayi wannan alqawarin.


Cikin zaquwa Dr khalil din yace"


Koba Dan alqawarinka ba bazan taba Bari amatu tashiga hadariba zan tsaya Mata ako Inane just tell me.


Cikin fargaba Usin yafada Masa yanda amatun tayi da hajiya aisha saidai ya boye Masa da yardar amatun nuna masa yayi kamar tursasata hajiyar tayi sbd amatun ta daukar Mata kudi.


Tsit yayi kamar ruwa ya cinyesa 

Har wani duhu duhu idanuwansa ke gani sbd tsananin tsoro da firgicin zancen,

Ita umme ko tunanin hadarinda zata jefa 'yar mutane batayi da kantama tunda komai jimawa dai wataran gaskia zata fito,

Idan ita amatu hankalinta bai Kai ba ita meyasa zatayi hakan??

Qarin tashin hankalinsa MAHMOUD za'ayiwa wannan mummunar 6ata sunan

Haqqinsa bazai bar umme ba hattasu yayanta sai haqqin MAHMOUD ya shafesu Dan haka bazai Bari tadau wannan alhakinba dazai ja Mata azaba gaban Allah hakama bazai Bari rayuwar 'dan uwansa ta lalace ba hakama amatu rayuwarta nacikin mugun hadari.....


Da sauri ya kalli usi yace"


Usman Yi sauri kabar Nan katafi gida namaka alqawarin dawo da amatu Babu Abinda zai sameta maza katafi karka fadawa kawu komai..


Da gudu ya nufi ciki yayi hanyar palon Yana adduar Allah yasa amatun Bata bude fuskartaba Yana Isa ya fada palon da qarfi daidai lokacinda amatun tariga ta bayyana fuskarta akace ta fada cikin waye ajikinta,meye alaqarsu dame cikin?¿


Bude baki tayi hannuwanta da qafafunta na rawa zuciyarta na harbawa da qarfi zatayi magana tana kallon inda MAHMOUD ke zaune har lokacin idanuwansa lumshe Kuma duk yana jin abindake faruwa kawai dai ba huruminsa bane shiyasa ko hankali bai badaba,

 cikin wani irin sauri Dr khalil ya dako tsalle ya fado tsakiyar palon tareda cewa"


Allah ya taimaki Modibbo nine.


Wattttt????umme tafada da sauri tareda miqewa tsaye tareda haj Maryam

Nuratu ma da antynsa juwairiyya duk miqewa sukayi cikin tsananin firgici

Take palon yadauki hayaniya cikin rasa abin fada alhaji qarami yace kowa yatafi antashi meeting.


Hayaniya aka Fara saidai yanayin Modibbo yasa kowa yin tsit suka Fara sulalewa suna ficewa.


Kaf kowa ya fice Banda uwayensu maza da 'yannansu maza sai iyaye mata hatta MAHMOUD na gurin bai fitaba lokacinda yaji muryar khalil amatsayin me cikin yasashi bude Ido ahankali ya sauke Kan amatu dake gefen Khalil din tana kallonsa cikeda mamakin daga Inda ya fado.


Kallonsa takeyi tanason Kiran sunansa Amma ganin yanayinsa ta tana hango tsananin 6acin Rai da takaicinda yake ciki,


Idan har da khalil da MAHMOUD yayan hajiya mama ne kamar yanda tafada mata to acikinsu duk Wanda tace shine me cikin ta cecesa daga hawa mulkinda zaa salwantar da rayuwarsa to kenan duk dayane koba komai zatafi farin cikin kubutarda Dr khalil sbd kurkinsa akansu.


Da hanzari umme ta qaraso gabansa ta kalli cikin idanuwansa cikin 6acin Rai tace"


Me kake fada?

Maza maza fice wannan ba Abinda ya shafeka bane...ba magana nake maka ba""ta fada cikin tsawa da firgici.


Gyaran murya Modibbo yayi akaron farko bayan shock din daya samu na daqiqu ya kalli khalil tareda kallon amatu dake kallon Khalil din cikin rashin Jin Dadi qunci da bacin ran datake hangowa cikin idonsa.


Khalilu ta Yaya kazama uban cikin jikin yarinyar na???


Hadiye wani yawu me mugun daci yayi sbd dai gskia bazata faduba Dan idan yafada gski umminsa da amatu duk suna cikin hadari Dan umminsa har zamanta cikin zabeera saiya ware.


Rintse ido yayi ya budesu suna kadawa jajir take jijiyoyin kansa suka firfito sbd qarya ba halinsa bane bare wannan qaryar datafi kowace muni.


Muna sauraronka Khalil kafin fushinmu ya sauka akanka kayi bayani"cewar alhaji qarami.



Sauke Kai yayi daga kallonda Modibbo ya tsaresa dashi me girgiza jarumtarsa yace"


Mun jima muna qaunar juna tsawon shekaru uku 

Nasan bazaa Bari na aurotaba shine mukaje wani guri aka daura Mana aure.....tassssssss


Umme tasakar Masa wani gigitaccen Marinda Saida ya zube Kan gwiwoyinsa tareda sauke Kai.


Cakumo amatu tayi cikin tsananin 6acin Rai tace"


Modibbo ba gskia yake fadaba Khalil bazai taba aikata wannan qazamin aikinba wannan ita zata fada ubanda ya Mata ciki Amma badai Khalil ba....hannu ta daga zata kaiwa amatun Modibbo ya daka Mata tsawa da cewa"


Aishatu ki dawo hankalinki ciki ne ajikinta kada hannunki ya sauka jikinta..


Ke matso fili ki fada Mana Abinda yafada gskia ne kokuwa??


Fitowa tayi daga bayan Khalil din tana kallon idanuwan umme dake fitowa da ruwa tace"

Eh gskia ya fada.


A Ina kuka hadu??


A asibitinsa.


Shekara nawa yanxu da auren??


Rawar murya tafara tana neman dufewa tace"


Daya.


Aikuwa take kowa yaqarin tsit cikin tashin hankali.

##mamuh#




______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899[3/16, 1:57 PM] Zafafa: *_MIN QALB 12_*

_Mamuhgee_




Kasa riqe hawayenta umme tayi suka gangaro Kan fuskarta ta shafa cikin firgici ta dago hannunta ta kalla taga tabbas hawayene,


Yau ni Aisha mezan gani ne??

Wace masiface wannan yarinyar na gayyatowa kaina ranar farko data sako kafarta gidana hawayenda na manta ya akeyinsu tun quruciya yau sune a fuskata,

Wlh shirina bazai lalace ba Koda kowama zai rasa saidai kowa ya rasa...


Juyawa tayi Kan khalil cikin tashin hankali da rudewa tace"


Khalil karkayiwa kanka haka ka 6ata rayuwarka kafada gaskia wannan yarinyar bakada alaqar komai da ita,


Rintse ido yayi Yana danne tsananin 'dacin da zuciyarsa ke Masa 

Ummin ta girgizasa da qarfi tana sake Marin fuskarsa tace"


Kafada gaskia Khalil wlh bazan yadda a maqala maka cikin qaryaba wannan yarinyar 6arauni.....


Katseta Modibbo yayi da cewa"


Aishatu ki nutsu kisan a inda kike,


Shiru yayi Yana nazari cikin tsananin baqin cikin da takaicin Abinda ke faruwa ya dago ya kalli khalil 

Khalil din yayi saurin sauke kansa

Yace"


Khalilu Abinda kayi a tunaninka meye shi??


Modibbo a musulunce shi aure idan har an daurashi Akan yanda sharuddan aure sukace to banyi laifi ba,

A tsakanina daku iyayena Kuma laifi ne sbd na boye Muku nayi bada izininku ba saidai nayine sbd girmamaku Dan inajin tsoron kawo muku zancen sbd tsoron bazaku Bari,

Dan haka na aikata laifi babba Kuma Ina neman yafiyarku dakuma amincewarku da amatun kodan Abindake cikinta baida laifin komai kada a hukuntasa ko mahaifiyarsa nine me laifin Kuma na dauka a shirye nake da dukkanin wani hukunci saidai Allah ya huci ran Modibbo ina fatan itama amatu abata adalcin datazo nema duk yanda akayi hukuncin zamu dauka.


Tsit sukayi suna kallon bakin Khalil din cikin girgizuwa da kalamansa,

Dukkanin Abinda yafada jin sukayi kalmomin na son tabasu,

Shi cikin babu ruwansa to meye mafita ga wannan alamarin?


Kallon mahaifiyar amatun Modibbo yayi yace"


Ina mahaifin yarinyar??


Ya rasu tun tana yarinya qarama.


Ina danginsa?


Daga maiduguri mukayo Nan munrasa kowa bamuda kowa nanma amatsayin 'yan gudun hijira muke har mahaifinta yasamu aikin sanaar Saida  kayan Miya harya rasu daga Nan ne muka hadu da......sai tayi shiru tana satar kallon hajiya aisha sbd Abinda zata fada itama ba yanda ta iya Dole tabi tsarin yanda al'amarin ya juya kodan fita da ranta tace"


Daga Nan ne muka haduda likita shine yake taimaka Mana harya sanyata makaranta shine yakawo maganar son aurenta nikuma na amince saidai bai fada Mana cewar iyayensa Basu aminceba yakawo Mana wani amatsayin mahaifinsa aka daura auren yanzu shekara daya kenan,

Mu Kuma kusan wata biyu kenan bamu sake ganinsa ba munyita zuwa asibiti bama samun ganinsa saigashi ciki ya bayyana atareda ita

 mutane harsun Fara binmu da gori da maganganu marasa Dadi shiyasa mukazo...


Faduwa ummi tayi Kan kujera tayi zaman 'yan bori tana kallon baba Jamila tayi wani kukan kura tayi kanta tana cewa''


Qarya takeyi Modibbo wlh taron maqaryata ne....


Saurin riqeta hajiya Maryam tayi cikin tashin hankali take itama tace"


Modibbo Sam wannan matar qarya takeyi wlh daga gani sharri ne zuke qullawa sbd kudi......kallonda Modibbo yayi Mata yasata yin shiru baqin cikin future din 'yarta dake Shirin lalacewa na cinta kamar ta rufe amatu da bugun mutuwa.


Khalilu duk Abinda tafada gskia ne kokuwa? 


Gyada Kai yayi kansa na qasa Dan duk duniya bai ta6a Jin tsanar wani lokaci 'daya ba kamar baba Jamila.


Bsyan dogon nazari da tunanin irin rashin 'da'a da wulaqanta zabeera da Khalil din yayi take yafita ran Modibbo da kusan kowama a gurin kai tsaye cikin nuna qyamarsa ga khalil din da halayyarsa Modibbo yace"


Ban karbi wannan auren naka ba likita haka Kuma kaima na cireka daga iyalina ka dauki matarka kuje kibar Nan karka sake Kiran kanka da zabeera har abada,

Kuma kuje ga adalcin dakuke nema Nan anbaku,

Anbarwa 'yarki mijinta har abada duk ranarda qafarku ta tako zabeera aranar ne zakusan asalin hukunci da zafin Zabeera.........


Kuka ne qarfi umme ta fashe dashi tareda riqe Khalil din da idanuwansa suka qarasa rinewa jajir Yana Mata kallon kece Kika jawo..


Girgizasa tahauyi tana kuka Mai qarfi tace"


Dan Allah Khalil kafada musu gskia bakai bane

Wlh bazan yardaba nizan fada gskia..


Girgiza Mata Kai yayi tareda zamewa daga hannuwanta yayi qasa da murya cikin qunci Yana cewa'"


Ummi kema kisani idan har kina Sona da 'dan sauran farin cikin daya ragemin bazaki taba fadar gskia ba sbd zata saki keda amatu cikin hadari Wanda bazan iya daukaba,

Umme kece rayuwata gabaki 'daya amatu kuwa itace zuciyata

Meyasa zakiyi haka ummi....??


Mutuwar tsaye tayi tana kallonsa cikin tsananin tsoro da tashin hankalin Abinda yafada,

Me Khalil ke nufi?

Amatu zuciyarsa,

Dama sunsan juna da gske kokuwa ita yakeson rainawa hankali,

Amatu dama tasan 'danta shine ta karbi aikinta kenan ita take rainawa hankali tabbas zatasan tayi Wasa da wuta.


Gangarowa wasu sabbin hawayenta sukayi ta girgiza Kai tana cewa'"


Khalil wlh bazan iya gani na rabu dakaiba,

Ka saketa saki uku,

Cikin ma a zubar kabawa Modibbo hkr Amma Dan Allah Khalil kada katafi yaqarasa cikin kuka tana sake riqesa.....


Cikin tsawa wannan karon Modibbo yakira sunanta Yana kallon Khalil yace"


Ko bayan kabar Nan duk ranardaka saketa daga ranar zakasan ainihin fushin mahifinka,

Haka cikin dake jikinta.


Zubewa qasa umme tayi da sauri Yana cewa'"


Na roki Modibbo daya taimaka ya sassautawa Khalil wannan hukuncin.


Miqewa Modibbon yayi Yana cewa'"


Taro yaqare kowa ya tafi.


Kamar daga sama sukaji security din bakin qofar shigowa na bada sanarwar isowar Andi Wanda yasa kowa miqewa cikin tsananin firgici sbd Abinda andin yafi shekaru ashirin beyiba wato zuwa meeting palon.


Hajiya Maryam data yiwa amatu text din takira andin tafada Masa halinda ake ciki ta saki ajiyar zuciya tana riqo umme data miqe da sauri itama ganin Andi yau da kansa take ta shiga taitayinta tana shanye kukanta saidai hawayenta dasukaqi tsayawa ta kalli hajiya Maryam tace"


Kin kyautamin Maryam sbd Andi ne kawai zai iya ceton Khalil Dina yanxu.


Modibbo da kansa ya miqe yabawa mahaifinsa dake tattareda wata irin izzar mulki da cika Ido tareda razanarda mutane da kallo 'daya idan yayi maka Wanda kaf cikin zuriar zabeera mutum biyu ne suka 'daukosa sak alqasim zabeera mijin haj Maryam daya rasu sai MAHMOUD ZABEERA wanda beyi mulki ba Amma Yama wucesa a mugun miskilancin da kwarjini me ban tsoro.


Shigowar Andi tasake saka kowa cikin tsoro da firgici Saida yayi zaman minti biyar tsit bayan gama amsa gaisuwar kowa kafin ya bude muryarsa me amsa amo yace"


Khalilu da kanka zakayi bayanin abindake faruwa daga farko.


Ba inda inda Khalil yasake koro Masa bayanin komai tareda hukuncinda Modibbo ya yanke Masa ya 'dora da fadin"


Na aikata babban kuskure Kuma na amsa laifina nakuma karbi hukuncina Andi,

Zanyi nesa da Nan Kuma bazan taba Bari maganar ta fitaba bare sunan zabeera ya baci,

Nayi alqawarin daga lokacinda zan fita Nan zan aje sunan zabeera Dan kada gaba nayi Abinda zan kawo batanci gareku ba da......


Cikin firgici ummi tayi saurin zubewa qasa tana cewa'"


Allah ya taimaki Andi Dan Allah Andi ya tausaya a sauqaqawa Khalil tsaurin hukuncinsa kada arabasa da sunansa da zuriarsa indai akan laifin wannan yarinyar ne Andi abasa dama yayi Mata saki uku bayan ancire cikin.......


Maganar ummin yasa Andi dagowa ya kalli Modibbo 

Modibbon yayi saurin qasa da Kai Yana cewa'"


Ayi Mata afuwa Andi uwa ce dake cikin firgicin rabuwa da 'danta.


Kallonsa andin yasake hakan yasashi yin shiru Yana cewa"


Allah ya huci zuciyar Andi da Abinda aishatu tafada.


Kallonta Andi yayi tareda kallon baba Jamila yace"


Aishatu matsayinki na mahaifiya kikeson a cutatarda 'yar wata sbd naki 'dan wannan ba adalcin Andi bane.


Kallon baba Jamila yayi cikin sautin dayasata rudewa qafafunta suka hau rawa yace"


Kinxo neman adalci anbaki adalci

Kin aminta da auren 'yarki Dan haka 'yarki zatayi zaman sure bayan munyi bincike akan auren,


Zaki bar 'yarki anan Kuma zata zauna cikin gata da aminci

Zata raini cikinta a hannun matar 'dan uwansa MAHMOUD ZABEERA bayan haihuwarta anbawa mahaifiyarsa halak malak saimu sake daura musu aure,


Aishatu kinason kashe abindake cikin tun baizo duniyaba to kece zaki rainesa har girmansa bayan zuwansa duniya an mallaka Miki shi halak malak.


MUHAMMAD""fada sunan Yana 'daga sautinsa.


Sai alokacin MAHMOUD ya dauke idanuwansa daga Kan Khalil da amatu sbd jin a hannunsa yarinyar zatayi rainon cikinda bai gama yadda da akwaisaba sbd aduniya shine yafi kowa sanin wannan ba halin Khalil din bane ya kalli inda Andi yakira sunansa ya taso cikin nutsuwarsa dake qarawa Andi ganin kwarjininsa ya qaraso ya tsaya gaban andin tareda sauke kansa cikin girmamawa yace"


Allah yaqarawa Andi tsawon Rai.


Matar 'dan uwanka zata zauna a hannun matarka har tsawon lokacinda zata haihu,

Cinta da Shanta duk na hannunka,

Ciwonta da maganinta na damqasu hannunka Dana matarka,

Na damqa maka tsaron lafiyarta Dana Abindake cikinta sbd aishatu ta tabbatar Mana da AMATULLAH da abundake cikinta na cikin hadari a hannunsu Dan haka Kaine kawai Wanda na yarda dashi nabaka amanarsu a hannunka.


Shiru yayi bai motsaba sbd Abinda andin yafada yaxo da wani al'amarine da kansa yake kasa dauka,

6arauniya a gidansa?ta Yaya zai iya Bari wannan yarinyar ta zauna acikin inda yake rayuwa 

Khalil dinma haryanxu yakasa yarda da shidin ne uban cikin wannan yarinyar

 ahankali yadan dago ya kalli gefen datake tsaye riqeda rigar Khalil sbd zuwa lokacin tafara firgita da abindake faruwa Jin hukuncin da aka yankewa Khalil daga farko taji bazata iya Bari tazama sanadin batawarsa da rabuwa da iyayensaba saiga zuwan wannan Andin Wanda ganinsa kawai yasa taji tsoro da firgici ya kamata gashi ana maganar riqeta ta haihu

Ta Ina dakuma ta Yaya zata haihu

Kasa riqeta qafafunta sukayi tsabar rawa shiyasa ta boye bayan Khalil din.


Taro ya tashi kowa ya watse nagama magana abubukar a aika mahaifiyarsa gida tareda kayan abinci da jarin sana'a me kyau sbd itace kakar Zabeera na shida Inshallah.


Modibbo a qarqashinka zaa kula sosai matuqa da AMATULLAH Ina fatar Nanda watanni kadan za'a bani zabeera na shida a hannuna.


Kallon amatu yayi akaro na farko data saki fuska dukkaninsu Saida suka bude Ido sbd ganin murmushi akan fuskar tasa yace"


AMATULLAH ni Andi nine gatanki keda Abinda yake cikinki acikin zabeera nayi Miki alqawarin baki kyakkyawar rayuwa keda Abindake cikinki sbd zalincin da khalil yayi miki da Wanda mahaifiyarsa ke shirin Yi na cutatar dake da Abinda ke cikinki Dan haka na Miki alqawarin idan har Ina Raye Kika haihu indai namiji sai yayi mulkin zabeera wannan shine babban adalcin dazan baki,

Kece mace ta farko Kuma mutum ta farko data shigo zuriar zabeera a tarihi ki riqe wannan a ranki Dan haka karki Bari har abada Nasameki da illa ko laifin dazai sakani takaicin hukuncina sbd cin Amana,yaudara da qarya ba abubuwan da Andi ke yagewa bane.


Kai Kuma Khalil hukuncinka na ranardazan daura maka aure da ita.


Kowa yatafi nagama mgn.


Hannu umme take Shirin dorawa akai tasaki kukan baqin cikin wannan alamarin Modibbo ya aiko Mata da mugun kallo Haj maryam ma dake Shirin fasa ihu Andi ya nuna musu qofa sunaji suna gani suka hadiye cikinsu bame iya Jan wani suka fito Babu me ganin gabanta tsabar tashin hankali.


MAHMOUD ma ficewa yayi batareda yaqara ko second dayaba.

Baba Jamila da Sha Taranta ta arziki aka kaita gidanta inda suka tsara komai Koda anxo bincike.


ZARAH aka kirawo ita tazo aka damqa amatu hannunta wadda atake alokacin amatun tashiga ranta ta kalli amatun dake qara damqe rigar Khalil sbd hankalinta daya tashi gaba daya da alamarin sbd ita yanzu Tama rasa Ina aikin data zoyi yaje Sam sun rikita 'yar qaramar qwaqwalwarta.


Kallon Khalil tayi tana sake matsesa tana girgiza Kai tace"


Dr gida zani nafasa bana......


Hannu ya Dora a bakinta tareda girgiza Mata Kai Ya bude bakinsa daya gama nauyi muryarsa na nauyi a karye yace"


Kije kibi ZARAH komai zai daidaita bazan Bari komai ya sameki ba na Miki alqawari,

Kuma zansamu kawu nayi mgn dashi zan Masa bayani yanda zai fahimta Inshallah.


Qura Masa Ido sosai take kallonsa sbd yadda dashi datayi dari bisa dari kafin ta daga Masa Kai tasakesa ahankali tareda kallon zarah dake Mata murmushi suka wuce.


Bayan fitarsu Kai tsaye motar zarah din suka nufa suka shiga ta jazu sukabi ta bayan gefens Modibbo zuwa  part dinsu dakeda nisa cikin zabeera din sbd kusan sune na qarshe.



Umme nashiga palonta ta zube qasa tareda Dora hannu akai zata saki ihu juwairiyya tayi saurin rungumeta tana Kiran sunanta itama muryarta na karyewa dason yin kuka.


Haj maryam ma kuka takeyi wiwiwi itada nuratu dake wani irin kuka tana  kwantawa jikin momyn Tata sukam yau wace irin baqar ranace agaresu.

##mamuh#




______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/17, 4:00 PM] Zafafa: *_MIN QALB 13_*

_mamuhgee_



ANNUR PERFUMES ANNUR PERFUMES!!!!!!


JAMA'A MA'ABOTA SON QAMSHI DAN SANYAYA ZUCIYA Ina kuke kuzo ga sabuwar duniyar turare sabon tashe ANNUR PERFUMES sunkawo muku,

Turarensu qarshene,

Qamshinsu na daban,

Kayansu tabbataccine,

Aikinsu ingantacce ne

shin kataba/kintaba amfani da ANNUR PERFUMES kuwa?

To maza qarzayo karki Bari ayi badakeba dankuwa kayansu lamba dayane Kuma amintaccine masu guarantee domin kuwa mun tabbatar.



ANNUR PERFUMES donjindadin customers  munkawo muku dadadan turaruka na musamman  masu nishadan tarda Amarya da uwar gida harma da angonta kamar haka turaren wuta humra kala daban daban kwalaccha  Dana matsi na infection biki ko suna dyadya ko sari  ina kano gaida layin  massanlachin imamu malik koku kira number waya kamar haka 07086341096 ko 07069037534 muna munamaraba daku saikunzo.


ANNUR PERFUMES


TURAREN WUTA

KHUMRAH. 

KULACCAM

MUSK(AL MISKI THAHARA/AYSHA/BLACK AND RED MISKI)

DECORATIONS ..

KAYAN INFECTION DANA MATSI (STEAMING)


TANA KANO: GAIDA LAYIN MASALLACIN IMAMU MALIK!




Koda zarah tayi parking bakin flat dinsu motat MD na gurin tabbacin Yana ciki,

Fitowa tayi tareda zagayowa ta budewa amatu qofa tana murmushi tace"


Muje ko amatu.


Kallon flat din takeyi tana zaro Ido sbd tsarinsa da kyansa tun daga wajen,

Fitowa tayi motar tana zare idanuwanta Kan kusan motaci biyar dake gurin a jere kowacce sai daukar Ido takeyi ta nufesu zata shafa zarah ta riqota tana cewa'"


Muje ciki ki huta kina buqatan hutawa sbd hayaniyar da akayi gashi kinta kuka zai iya taba lafiyan babyn kinji Dan haka please ki kula.


Kallon zarah din tayi tareda shafa cikinta tana cewa''


Wannan cikin zaki kula Dani ne har qarshen rayuwarki idan kina Kiran na haifesa Dan Babu uban komai aciki sai wainar iyami ta safiyar yau danaci.


Magana kike?"zarah ta tambaya tana juyowa daga tura qofar babban palonsu.


Qaqalo murmushi tayi taba cewa"


Cewa nayi harna Fara kewar babata.


Riqo hannunta zarah tayi suka shigo cikin palon tana cewa"


Karki damu Inshallah zakiga jimawa sosai zakiga kin haihu lfy saiki koma gurin babah kafin daga baya saimu sake daukoki kidawo Nan shikenan kinzama ta Dr khalil dinmu.


Dan sunkuyar dakai tayi tana qaqalo kunyar Dole tana Dan murmusawa saidai suna shigowa cikin palon ta fiddo idanuwanta gaba daya tareda Fara jujjuyawa tana sakin baki tace"


Wayyo USI Zo kaga aljannar duniya a gidan Nan.


Kallonta zarah tayi tareda sakin murmushi tana qarasawa ta ajiye gyalenta da keys din motarta tana nufar kicin da kanta ta dauko ruwa Mara sanyi tadawo ta dube robar ruwan ta zuba a cup ta jawo amatun data zage tana taba duk Abinda ya burgeta tana fiddo idanuwa tana Kiran sunan usi.


Zaunar da ita zarah tayi tana miqa Mata ruwan tace"


Sha ruwa amatu Kuma ki zauna kada ki Fadi da wannan zagayen da kikeyi idan kin huta zakiga komai ahankali tunda anan zaki zauna kibari ki huta tukuna.


Kwankwade ruwan tayi ta miqawa Zara cup din idanuwanta nakan dining dataga me aikin zarah din na jere wasu irin manyan kulolin abinci masu daukar Ido da fresh fruits daga fridge sai hayaqin sanyi suke ta hadiye yawu tana satar kallon zarah dake sake zubo Mata ruwan fuskarta na bayyanarda annashuwar datake ciki ta Basu amatun da akayi.


Ganin yanda take kallon gefen dining yasa zarah juyawa ta kalli dining din saita fahimci kamar yunwa amatun keji ta juyo tasaki murmushi tana cewa' 


Muje nakaiki kifara watsa ruwa zakifi Jin dadin cin abinci.


Bedroom 'din dake kusa da nata takaita da kanta tasake gyara Mata shi ta sauya Mata zanin gado tareda kunna AC ta sauyo Mata room fresheners tana cewa'

Duk Wanda kikaji bakyason qamshinsa kifadamin sai a cire Miki shi kada ya sameki.


Toilet ta 'dan wanke Mata sama sama Dan baida dattin komai sbd babuma Wanda yataba amfani dashi dandai ita dana bedroom dinta take amfani batama shigowa Nan dakin gaba daya bare MD dako nata bedroom din baitaba shigaba bare yashigo wannan.


Towel tabata sabo fil tareda kawo Mata shower gel din jaggins da sabbin undies da wata doguwar jallabiya Mara nauyi me dogon hannu ta fice tana cewa' idan kingama zankawo Miki abincinki har daki kibi ahankali a toilet karki Fadi Dan Allah.


Gaba daya hankalinta nakan dakin da ake nufin ciki zata zauna batamaji me zarah din ke fada ba ta fada Kan gadon da qarfi Yana jujjuyawa tace"


Wayyo amatu ko daga Nan aka tsaya  qaramin burinki yacika kinshiga cikin Masa kudi.


Sai data gama juye juyenta akan gadon AC na shigarta tareda qamshi masu sanyin Dadi kafin ta miqe ta cire kayanta ta shiga toilet din Wanda tuni Shima ta rude da haduwarsa Wanda badan tayi aiki agureren masu girma ba kamar irinsu blue fox da bazata San ya ake amfani da irin wannan toilet din ba.


A toilet din tsayawa tayi gaban tangamemen madubin tana duba kanta tana shafa cikinta sai alokacin ta dawo hayyacinta gameda abinda yake faruwa ta lumshe ido tana tunano Khalil da halin dayake ciki,


Ita Sam Abinda Bata ganeba shine 

Haj Mama data aikosu wannan aikin kukan datakeyi na qarya ne kokuwa?

Idan har kamar yanda tace MAHMOUD da KHALIL yayantane to meye banbanci Dan ance Khalil ne ba MAHMOUD ba?

Shin wannan abindaya faru yau din menene ainihin Abinda yake nufi sbd saitake ganin kamar yanda aka tsaro abin kamar ya sauya taku me matuqar hadarin gaske,


Ta Yaya zata haihu bayan batada ciki,

Ta Yaya zata auri Khalil bayan ba ranar haihuwa tunda ba ciki,

Shogowarta fa anan kamar tashigo wani mugun keji ne ta rufe kanta sbd tunda Babu ciki Babu ranar haihuwa,

Babu ranar haihuwa Babu ranar tafiyarta..


Shiru tayi tana jinjina Kai tace"


Ina buqatan ganin Haj Mama naji ni meye matsayina a yanxu.


Wankan tayi tana shaqar gel din me qamshin Dadi tafito ba wani shiririta ta shirya cikin kayanda zarah din takawo Mata tana cikin saka hula akanta zarah din tashigo daukeda tray din kayan fruits hafsatu me aikinta na bayansa daukeda tray din abinci.


Washe baki tayi tana zama qasa Kan qaramar carpet din dake gefen gado tana cewa"


Anty sannu da aiki kinata fama tunda nazo.


Aje tray din zarah tayi tana murmushi tace"


Amatu tunda aka banike nasan hidimarkice yanzu nafara harsai kin haifarmana me kama da Dr dinmu kokuma gwara dai ki haifar Mana me kama da MD dinmu dagani har Dr din saimunfi sonsa sbd MD shine 'dan uwanda Dr yafiso acikin familynsa gaba daya,

As for me nikuma MD shine rayuwata.


Apple amatu tayiwa babbar gutsura tana ci tace"


Anty Dr Yana ina yanzu?


Yar dariya zarah tayi tana zuba Mata Salad Kan dafaffen dankalin da aka dafa matashi da zallar Naman kaza da cabbage tace"


Dr Yana bangarensa Amma nasan tunda matarsa da babynsa na Nan bazamu Kai dare batareda yazoba Dan haka ki kwantarda hankalinki Dr nanan zuwa idanma baizoba zankirasa yazo.


To kawai tace tana cika bakinta da dankali da nama sbd 'dadin da abincin take Mata tace"


Anty idan nagama cin abinci mezanyi Kuma??


Bacci zakiyi ki huta amatu kafin zuwa gobe zanfadawa MD saimu kirawo Dr dina yazo afara dubaki da lafiyar baby.


Sarqewa tayi da qarfi tasaki tari Jin Abinda zaran tace.


Da sauri Zara ta dauki ruwa tana miqa Mata tana Mata sannu tace"


Amatu kodai abincin be Miki bane??


Girgiza Kai tayi da sauri har lokacin tana tari tace"


Ba Dr ne zai ringa dubani ba tunda shine Mijina??


Aje cup zarah tayi tana cewa''


Aa Dr bashi zai ringa dubaki ba munada Dr dinda zai ringa dubaki wato gynecologist Dr likitan Mata Wanda Nima shi nake gani sbd matsalar rashin haihuwarta.


Shiru amatu tayi tana tura abincin kawai sbd tasan ba jimawa asirinta zai tonu duk aka kawo wani likita yadubata zaisan batada ciki 

Andi sakawa zaiyi a harbeta da kibiya sbd da gaskia ta fito.


Tana gamawa zarah tasata kwanciya bayan tayi sallah ta rage Mata sanyin AC ta fice bayan tasa hafsatu ta gyara gurin suka ja Mata qofa.


Shiru tayi tsawon mintuna tana tunanin goben idan likita yazo 

Miqewa zaune tayi tana cewa''


Dole Naga Dr khalil yau nafada Masa kafin goben Amma dai yanzu inason Fara magana dasu usi.


Jakarta da aka saka cikin wardrobe ta bude ta dauko matacciyar wayarta ta lalulo numbrn USI ta Danna Masa Kira.

##mamuh##



______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/23, 1:35 PM] Zafafa: *_MIN QALB 14_*

_mamuhgee_


ANNUR PERFUMES ANNUR PERFUMES!!!!!!


JAMA'A MA'ABOTA SON QAMSHI DAN SANYAYA ZUCIYA Ina kuke kuzo ga sabuwar duniyar turare sabon tashe ANNUR PERFUMES sunkawo muku,

Turarensu qarshene,

Qamshinsu na daban,

Kayansu tabbataccine,

Aikinsu ingantacce ne

shin kataba/kintaba amfani da ANNUR PERFUMES kuwa?

To maza qarzayo karki Bari ayi badakeba dankuwa kayansu lamba dayane Kuma amintaccine masu guarantee domin kuwa mun tabbatar.


ANNUR PERFUMES donjindadin customers  munkawo muku dadadan turaruka na musamman  masu nishadan tarda Amarya da uwar gida harma da angonta kamar haka turaren wuta humra kala daban daban kwalaccha  Dana matsi na infection biki ko suna dyadya ko sari  ina kano gaida layin  massanlachin imamu malik koku kira number waya kamar haka 07086341096 ko 07069037534 muna munamaraba daku saikunzo.


ANNUR PERFUMES


TURAREN WUTA

KHUMRAH. 

KULACCAM

MUSK(AL MISKI THAHARA/AYSHA/BLACK AND RED MISKI)

DECORATIONS ..

KAYAN INFECTION DANA MATSI (STEAMING)


TANA KANO: GAIDA LAYIN MASALLACIN IMAMU MALIK!


**************

Ringin numbern usi din keyi harta katse bai daga ba tasake Danna Kiran tana cewa'


Usi idan muka hadu saina fasa maka baki da kai tunda har zaka iya bacci baka kirani kaji Yaya ta kasancemin ba a wannan zabeerar da kallo daya Andi da Modibbo sukewa mutum sai cikinsa ya mur'da,


Uwa uba arasa gurin ajeni sai anan cikin wannan me bada tsoron da matarsa.


Kira biyar tayi Masa Amma baa daukaba takira wayar iyami cikin sa'a kuwa ta dauka Nan suka jima suna mgn iyamin na maimaita Mata karta taba duk Abinda zata gani na kowa karkuma ta jawowa kanta fitina ko rigima ta jawo musu kafin aka miqawa kawu wayar Shima dai yayi Mata maganar karta taba abun kowa sbd kada 'yan kudin Nan dasuka samu su qare a gun kashe rigima Shima usi sunfada Masa kada ya kuskura ya janyo rigima sbd tanadin kudin Nan zasuyi sbd abinci dakuma qarasa hada takardun komawarsa karatu.


Fadawa lafiyayyan gadon tayi ta kwanta tana lumshe ido bayan tagama wayar

Tai wani juyi tana lulluba da bargon me shegen laushi sbd sanyin AC dake ratsata ta lumshe ido tana cewa'"


Masu kudi wato ko a gurin bacci sunfi talaka samun nutsuwa 

Da agidanmu ne da yanxu radion kawu da qarar dakan turmin maman junior da qarar bude tukunyar maman basiru sun Hana mutum bacci,

Rufe idanu tayi tana sake gyara kwanciya take bacci me dadi yayi gaba da ita ga gajiya ga lafiyyan abinci dataci ga lafiyayyan gurin kwanciyar dakuma sanyin AC ga ba hayaniya ai Dole baccinta yau yayi dadi.


Saida garin ya hantse ta tashi tana wata irin miqa me Dadi fuskarta a sake da farin cikin irin baccin data samu tana qoqarin saukowa gadon ne zarah tashigo daukeda sababbin brushes da toothpaste masu kyau tana kallonta tace"


Amatu Yaya? kintashi lfy? Ya babyn dr?


Qarasa saukowa gadon tayi tana sake yin wata doguwar miqar datasa zarah saurin ajiye kayan hannunta tana riqeta tace"


Amatu zakiwa kanki illa idan kina irin wannan miqar

Idan kinajin gajiya ne za'asa ayi Miki tausa ahankali Amma Dan Allah ki daina kinji??


Kallon sakarai amatu ta Mata Jin hadda miqar ma yanxu wani tsurku zaa kawo sbd ciki...

Amma dai ko yayane bazata Bari banxa ta wucetaba tubda damace tasamu gwara ta dama kafin Takoma inda tafito Dan haka sai ta 'dan yamutsa fuska tana 'dan dafe bayanta tace"


Anty zarah ko Ina jikina ciwo yakeyi na gajiya shiyasa nake 'yar miqar ko zanji jikin ya sake Amma tunda kince za'amin tausa inaga idan anyi zanji jikin ya saki.


Murmushi zaran tasaki tana sakinta Takoma gaban mirror ta dauko toothpastes din different flavors kusan kala biyar tace"


Ga Macleans ki bude kowanne kiji Wanda qamshinsa ya Miki Wanda bazai tayar Miki da zuciyab saiki ringa amfani dashi.


Karba tayi tana washe baki tana duddubasu tace"


Duka ma sunmin abarminsu kowanne  ma qamshinsa zaimin sauran gida zanje dasu idan zantafi.


'yar dariya zarah tayi tana girgiza Kai rashin damuwar amatun na sake burgeta musamman data 'dan Fara lura tun jiya inda amatun tafito tana tareda yunwa gskia Dr be kyautaba barinsu su wahala haka tana matsayin matarsa bayan duk arzikin dayakedashi.


Fita tayi Takoma kicin ita Kuma amatu toilet tashiga tafara yin brush da kusan toothpaste kala hudu kowanne saidata fasa ta 'dan lakata tayi dashi take bakinta suka ringa bada wani qamshi masu Dadi dasuka sakata yin wanka cikin nutsuwa da annashuwa.


Tana fitowa saidatayi sallah kafin ta shirya cikin doguwar rigar jallabiya Mara nauyi Wanda duk zaran ce takawo Mata daga gani duk nata ne Amma suka sabbi ne Babu Wanda ta taba sakawa.


Tana cikin fesa turare tana lumshe ido cikin jin Dadi tace"

wainnan turaren dasu zankoma gida idan zankoma ma komai saina dauka naje dashi bazanga irin wannan Batinba nabariba.


Turarukan ta kwashe duka tabude wardrobe tazubasu cikin Jakarta daga can qasa ta rufe zip din tadawo gaban mudubin tana gyara zaman rigarta a jikinta saiga zarah tashigo tana kallonta Jin dakin yacika da qamshin turaruka yasata Dan 'yin tari tana cewa'"


Amatu wannan turarukan bazasu cutatar dakeba kuwa¿

Qamshin yayi yawa Zo muje dining muci breakfast idan Kuma akwai Abinda kike buqata ba Wanda akayi ba sai hafsatu ta Dora miki ga Dr khalil ma yazo Yana palon MD suna Magana.


Ba qaramin Jin Dadin zuwan Dr khalil tayi ba sbd sanar dashi Abinda su zarah din ke shirin Yi na Kiran wani Dr shiyasa ta farayin gaba tana cewa''


Ni komaima aka dafa yamin zanci Amma Dr nakeson Fara gani anty zarah Dan Allah kinji.


Biyota tayi tana cewa''

Wannan rashin hkr haka amatu bazaki jira yagama yazo yasameki har dakin ba.


A palon ganin Dr khalil baida lokacin fitowa daga gurin MD yasa ta marairaicewa zarah fuska tana taba cikinta 

Take zarah ta tashi da kanta ta hado Mata nata abincin a tray sbd kada yinwa tai Mata illa sbd cikin dake jikinta bazata iya jiransu ba.


Dakinta Takoma acan tayi zaman Yan bori akan carpet tafara cin lafiyayyan breakfast din tana bude plate din farfesun kifin da akayi kawai sbd ita dayaji kayan qamshi da 'dan yaji batasan lokacinda tasaki dariyar farin cikiba tana diba takai bakinta saiga Dr khalil yayi knocking yashigo fuskarsa tayi wani iri na yanayin damuwar dake tattare da ita.


Tsayawa yayi daga bakin qofar ya qura Mata ido yanda take cin abincin sosai cikin Jin dadinsa dakuma bayyanarda baqone agareta sai yaji jikinsa yasake yin sanyi ya rintse ido Yana Jin zafin zuciyarsa na qaruwa sbd baisan ta Ina zaifara da wannan qaqqarfar rigimarba sbd Nan ana Magana ne akan ciki da aure Wanda baa Wasa dasu sbd komai dadewa gskia zata fito idan akwai idan Babu,

Ta Yaya zaifara neman mafita?

Ta Yaya zaifara neman inda mafitar cikin amatu zata fito?

Gasu usi yanxu da Dole nauyinsu zai dawo kansa sbd inganta rayuwarsu su duka din ta yanda har abada komai zai faru bazasu Yi shaawar sake komawa rayuwar dasuka fito ba,

Idan har amatu zata iya saka kanta acikin irin wannan masifar me hadari akan kudi to tabbas zaiyi amfani da kudi da qarfinsa ya wadatasu da dukkanin abin buqata har sai amatu ta cire kwadayin kudi a ranta,

For now Abindake gabansa shine mafitar cikin jikinta da ake zaton akwai Amma bazai Yi rushing abubuwan ba tunda tana Nan hannun MD yasan Babu abin dazai sameta she's morethan safe anan Dan haka zata cigaba da zama anan zaije gurinsu kawu zaifara aikin kulawa dasu daga yanzu.


Gyaran murya yayi Yana sake gyara tsayuwa tayi saurin dagowa tana ganinsa ta miqe tana qarasa kwankwade sauran kakkauran tea din dake hannunta cikin cup tace"


Dr tun jiya kaina ke neman bugawa da son ganinka na.....


Quite amatu""yafada cikin 'yar tsawa ransa a 'dan bace.


Cak ta tsaya tana kallonsa ganin yanda bacin Rai ya bayyana a fuskarsa sosai sai hakan yasa jikinta yin sanyi tayi qasa da Kai tana kallonsa fuska a marairaice.


Ya dauke Kai sbd ganin zata sa zuciyarsa saukowa yace"


Kinsan zaman da kikeyi acikin zabeera?


Saurin matsowa tayi tareda katsesa da cewa"


Wlh dr aiki Na....


Amatu just keep quiet please,

Wane qarya kike tunanin zakimin bayan duk abin daya faru jiya gaban kowa and yanxu Ina tambayanki kinason kawo min wani different story

Ki saurara kiji usi yafadamun komai Wanda yasa nake mamakinki har yanzu

Amatu har kudi yayi mahimmancin dazaki 6ata sunan wani akansu,

Rayuwarsa kike neman batawafa gaba daya

Shin kinsan shi Wanda kikaso batawa rayuwar shine Wanda nafiso a rayuwata fiyeda kowa bayan iyayen dasuka haifeni???


Tsit tayi tana sake yin qasa da kanta cikin rashin Jin dadin yanda yake maganar cikin tsananin 'daci da bacin Rai 

akaro na farko a rayuwarta dataji nauyin wani mutum.


Juyowa yayi Yana kallonta yacigaba fa cewa"


Amatu wannan duk Abinda kike tunani ya wuce Nan

Wannan alamarin babbane bazaki ganeba sbd tunaninki kawai ya ta'allaqa ne kawai akan kudin dazaki samu 

Meyasa kudine kawai Abinda kike gani amatu wannan alamarin babbane meyasa bazaki ganeba,

Umme mahaifiyatace duk Abinda tasaki kizo kiyi tayine sbd rashin mafitar datake gani tana ciki 

Gashi yanzu kunsani a tsaka me wahala bansan yazanyi da kowannenku ba,

ku duka bazan iya barin wani Abu ya sameku ba kokuma wani mummunan hukunci ya hau kanku sbd kowaccenku nada matsayi me girma agurina gashi yanzu ta kowane bangaren nine zansan Yaya zanyi.


Kuna tunanin MD sakarai ne daza'a Zo Kai tsaye afadi wannan alamarin ace shine ya zauna ya dauka kawai sai  sunansa ya baci?

Tabbas dakun aikata babban kuskure sbd ilimi da matsayin MD yawuce inda umme ke tunanin ke bakyama ciki sbd komai ma qaramin kanki bazai ganeba gameda waye MD Dan haka ki saurareni da kyau kiji,


Daga yanzu dakike cikin zabeera duk Abinda zakiyi da Wanda yake faruwa ki tabbatarda kina sanar Dani,


Karki kuskura Koda Wasa kiyi maganar Abinda yake ainihin gskiyar maganar Nan da kowa Koda kuwa zarah ce ko a waya karkiyi maganar da USI sbd kadama wani yaji,


Kince kinada ciki Dan haka zakici gaba da zama a me cikin harsai na samu mafitar fita cikin wannan shirmen da kuka faro,


And bayan zarah karkiyi muamala da kowa acikin zabeera batareda izininaba lastly Kuma karki yarda kiyi Abinda za'a zauna meeting akanki kokuma asan asalin waye ke acikin zabeerar Nan hakama karki yadda kiyi Abinda zaisa a fahimci bakida ciki idan nace karki kuskura I mean kada Koda Wasa ki kuskura


Duk Abinda kike so kifadamin zan kawo Miki shi Kuma kullum zan ringa zuwa Nan dubaki kafin na wuce office da idan nadawo and you better behave yourself duk da MD baida lokacin batawa agurin matarsa bare ke to yanada lura sosai zai iya ganoki a lokaci daya hakan Kuma na nufin samun matsalarmu..


Kin fahimci dukkanin abubuwan Dana fada right??


Gyada Masa Kai tayi ahankali tana Dan satar kallonsa sbd ganin yadauka zafi yanda yaketa fadan.


Ajiyar zuciya ya sauke tareda kallonta Yana sassauta fushinsa yace"


Shikenan karki saka damuwa ko tsoron komai aranki Ina Nan Babu Abinda zai sameki,

Usman ma tun jiya ninace kada ya dauka wayanki Koda kinkira sbd nasan zakuyi Magana Kuma wani zai iya jinku idan nafita zan Masa Magana yadauki wayarki tun jiya nasan labari Yana bakinki Wanda zaki basa.


Sai alokacin ta saki murmushi tana kallonsa Jin ya sauko gaba daya ta washe baki tana cewa"


Duk da haka saina fasa Masa baki idan nagansa tunda yaqi daga wayar.


Kallon fuskarta yayi Yana sauke wata ajiyar zuciya sbd gaba daya tagama sauke fushin dayazo dashi ya sakar Mata murmushi Yana cewa'


Shikenan basai idan kingansa ba zaki fada bakin

Makaranta zai tafi Kuma hostel zai zauna infact idan yatafi bazai dawoba saiya Gama karatun Amma dai zai dawo Daurin aure inaga.


Kallonsa tayi baki sake tace'


USI zaije makaranta?

Haj Mama ta biya ne???


Batareda ya kalletaba yana duba Kiran dake shigowa wayarsa yace"


Duk wani deal ko aiki ko kwangilane ma dake tsakaninki da umme babusa yaqare so ki cire zancensa completely a kanki Babu wannan zancen.


USI zaije school ne sbd shine burinki nikuma nauyine Dana dorawa kaina na cika dukkanin burinki.


Wani tsallen murna tayi tana Kiran sunansa daidai shigowar zarah tayi saurin kallon amatun tana cewa'


Amatu wannan tsallen fa 

Zaki yiwa kanki illa.


Kansa ta mayarda kallonta zatayi Magana ya rigata da cewa"


Zarah amatu sai kinyi da gske she's stubborn..


Cikin tsananin farin cikinta daya kasa boyuwa tace"


Anty zarah Dr jarumi ne 

 Babu kamarsa.....


Tsit sukayi zarah na dariya cikin Jin nauyin Abinda amatun ta fada shikuma idanuwansa ya zuba Mata jikinsa na mutuwa da qaunar yarinyar.


Atakam batama kawo tunanin komai gameda maganar yataba sai sake sako maganganunta takeyi ganin haka yasa zarah ficewa da sauri shikuma ya fito sbd yayi lattin zuwa asibiti itama biyosa tayi tayi Masa rakiya zuwa mota suna tafe tana Masa sambatun irin farin cikin datake ciki har suka Isa motarsa dayazo da ita har qofar part din nasu zarah ta kallesa tana sake cewa idan kaje Dr Dan Allah Ina sake gaidasu kawu 

Iyami ma kace Mata Inshallah bazan jawo rigimar kowaba.


Harya zauna cikin motar yace"


To nikuma fa Abinda nace?


Dariya tasaki kafin tace'"


Kai duk Abinda kafada narigama nafara aiki dashi tun lokacin.


Murmushi yasaki tareda gyada Kai Yana cewa"


Good AMATULLAH.


Juyawa tayi zata tafi cikin taushin murya yace"


Me zan kawo Miki idan zandawo.


Kallonsa tayi Wanda yasashi Jin wani iri kafin tana 'dan tunani tace"


Duk Abinda masu ciki keci shi zaka siyomin naci Kona rage zafin sunan me cikin da ake Kirana dashi.


Girgiza Kai yayi Yana cewa"


Shikenan koma ciki ki kula Kuma.


Sam yau farin cikinta yakasa boyuwa tana shigowa ciki Palo ta zauna tareda miqewa akan doguwar kujera tana kallon zarah data fito hanyar zuwa saman mijinta tasake bajewa tana cewa'


Anty zarah qafafuwana tsami sukemin sosai Kuma.


Qoqarin kawar da damuwar data sauko da ita daga Daman tayi tana qaqalo murmushi tace' 


Bari na dauko man massaging sai a Dan mammatsa Miki qafar.


Dauko oil din tayi takirawo hafsatu Nan suka zauna tana yankawa amatun manyan gwaiban datace tanaso tana Mata fira ita Kuma hafsatu na mammatsa Mata qafafunta dake miqe Kan glass table din da aka Fara Dora Mata pillow me laushi kafin tadora qafafun.


Sunyi nisa zarah ta Dan 'dago tareda juyawa ta kalli hanyar saukowarsa sbd qamshin turarensa na IMPERIAL MAJESTY data Fara shaqowa Yana doso palon.


Jin zarah tayi shiru daga labarin datake Bata tana yanka Mata gwaibar yasata dagowa ta kalleta saitaga tana kallon wani gefe fuskarta kamar da damuwa ahankali itama ta juya ta kalli inda take kallon Wanda yayi daidai da saukowarsa gaba daya Yana sanye cikin suit din _Alexander vanquish 11 bespoke_  ash kala dasukaiwa fatarsa kyau sosai sai wani irin kwarjini da sirrin kyau dake fita daga fuskarsa da Babu sakewa acikinta.

##mamuh#




#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899[3/24, 10:27 AM] Zafafa: *_MIN QALB 15_*

_mamuhgee_



Jin idanuwa ajikinsa yasashi 'dan dagowa ya kalli inda suke Yana qarasa fitowa palon gaba daya

Su kuwa duk su biyun idanuwansu zube suke akansa Babu ko qyaftawa musamman amatu dake qare Masa kallon tsaf zuciyarta na harbawa sbd yaune karo na farko a rayuwarta datake kallon wani namijin data kasa dauke idanuwanta a kansa.


Ko inda suke bai qara kallaba ya dauke Kai fuskarsa na sake fitar musu da annuri ya nufi qofa zai fice zarah tayi saurin ajiye wuqa da gwaibar hannunta tana miqewa ta nufesa tana  cikin kulawa tace"


Fita zakayine gashi har an jere maka komai na breakfast a dining,

Ko zaka daure kaci ko ka.....


Zanyi a office idan naje I'm late already excuse me"

Rabata yayi ya wuce Yana daukar wayarsa datai ringin batareda yasake waiwayartaba ya fice.


Shiru tayi agurin tareda bin qofar daya fice din da kallo jikinta a matuqar sanyaye sbd a zaman aure kulawa da lokacinsa ne tasan bazai taba Bata ba gashi abin Yana damunta matuqa musamman idan a gaban mutane ne.


Qaqalo murmushi tayi tareda boye damuwarta ta juyo tadawo gefen amatun ta zauna tana kawo wani labarin daban sbd wancan datake Bata na farko ta manta Abinda take cewa.


Tsura Mata ido amatu tayi tana kallon hannunwanta dake yanka gwaibar duk sai taji bataji dadiba 

Sbd me zai dizga anty zarah din bayan ita kulawa ta nuna Masa¿


Dafa hannunta tayi tareda karban wuqar da gwaibar ta aje cikin plate dake Kan table tana qoqarin kawar Mata da damuwa ta saki murmushi tana cewa"


Anty zarah gwaibar Nan ta isheni haka babyb harya Fara zama qato daga zuwanmu jiya sbd ciye ciyen da  kike basa.


Sai alokacin tasaki fuskarta sosai cikin Jin dadin Abinda amatun ta kalla tace"


Ai dama so nakeyi yayi qatoto cikin qoshin lfy ta yanda iyayensa da kakanninsa zasu bani lambar yabo ta musamman.


Hmm anty zarah waye zai baki lambar yabo acikinsu Dan kin kula da renon cikinda ba'a so?

Dr ne kawai ke sonmu sai ke Dan haka Kona haihu ke zanbarwa babyn har sai kema kinsamu nai.


Dariya sosai anty zarah tayi tana cewa''


Waye yake kyautar ciki tun baa haifesaba amatu,

Kuma ki daina cewa ba'a son abin dake cikinki sbd idan har ana maganar gata to na tabbata abin dazaki Haifa gata yagama yimasa yawa,

MD ZABEERA Dr ne Wanda yafi kowa qauna fiyeda komai da duk abin daya mallaka Dan haka Ina tabbatar Miki da Babu wani uba bayan Dr dazaifi MD qaunar abindake cikinki musamman sbd ni ba haihuwar nakeba Kinga kuwa Dole zai qaunaci 'dan Dan uwansa uwa uba Kuma Dr khalil shi yanzu ai bashida kamarku keda cikin Dan hakama ki daina cewa ba'a sonku mu Muna sonku Andi ma Yana sonku hakama Modibbo.


Gyada Kai kawai tayi tana daukar sauran fruits din dake gabanta tana cinyewa tana lumshe ido Dan dai tunda tazo idanba da daddare data kwanta ba bakinta bai zauna a rufeba komaima cin cire haushi take Masa sbd ganinsa kamar ba kudi aka saka aka siyoba komai akwai kamar a banza.



******

Zaune take tana sauraren 'yar guntuwar da nasiha tareda lallashi da 'yarta juwairiyya ke Mata cikin kulawa da tausasa harshe Amma ita Sam hankalinta baya kanta tayi nisa gurin tunanin abindake damunta,


Ganin hankalinta baya kanta yasa juwairiyya yin shiru tareda miqewa tana cewa"


Umme tafiya zanyi ga dadynsu Fatima na kirana Kuma gobene tafiyarmu Lagos sai gaf da azumi zamu dawo Inshallah.


Dagowa tayi ahankali ta kalleta batareda tace komaiba ta gyada Mata Kai tana shafa Kan Ahmad 'dan qaramin 'danta tace"


Allah yakaiku lfy.


Amin tace suka shiga bedroom din umme suna qarasa dauko sauran kayansu suka fice.


Shiru tacigaba dayi tana saqa da warwara,

Yarinya qarama kamar amatu itace tayi Wasa da tunaninta tasakata cikin wannan tunani da halin na baqin ciki har ana cewa itace Zara raini cikinda Babu ubanda yayishi,

Wlh bazata yarda ba tunda shirinta ya lalace na kowama saiya lalace Dan kuwa sai ansan wa aka taba,


Idanma MD ne ya ninkawa wannan makwadaiciyar kudi datake iya komai akan kudi ta kuwa kowa sai yaji ajikinsa wlh,


Amatu cikin dayayi sanadin baki Jin Dadi da gata acikin zabeera shine zaizama mugun sanadin barinki zabeera da mummunan hukunci tareda wulaqancin da sai Yan jarida sun buga,

Zanga yanda za'a haifi cikin da Babu.


Shigowar Haj maryam ce tasata kallon qofa tana sake ajiyar zuciya ganin yanda itama haj Maryam din duk ta hargitse sbd burinsu na shekara da shekaru ya lalace cikin mintuna goma a hannun yarinya qarama.


Zama tayi ummen nace mata'  Yaya nuratu?


Nuratu na can haryanxu kuka takeyi 

Wlh Nima aishatu nakasa yadda da khalil wata yake aure ba nuratu ba,

Yarinyar Nan fiyeda shekara goma take fama da son Khalil sai yanxu da ake maganar aure kwatsam wannan mugun labarin ya fada,

Labarin da mune muka qirqiresa Amma sai asamu wani juyin Masa a zancen

Ni dai wlh Kam wannan Abu ban amince dashi ba nabawa nuratu wuqa da nama nace ta qetare duk wata iyaka ta qwato Khalil dinta mukuma maji da sauran.


Cikin quluwa itama ummen tace"


Dukkansu zasu raina kansu ne harshi Khalil din saiyaga bacin raina.




***Da Rana lafiyyan faten dankali da Naman kaza da carrot akayi sbd ita kawai 

Haka ta zauna tacinye Wanda aka kawo Mata tas ta kora da ruwan roba masu sanyi Danma lemu masu sanyi taso Sha anty zarah din ta hanata da cewa saidai Tasha fruits drinks ba lallai su bawa baby lafiya ba 

Haka ta hkr badan taso ba Dan ita wannan cikin badan Shiba da duk abindake gidan saita ringa cinsa ba kakkautawa.


Baccin Rana tayi bayan tayi sallah sai yamma sosai ta tashi bayan tayi la'asar suka Fara waya da USI Nan yake fada Mata Dr yazo gida yafadawa su kawo shine 'dan wadda ta daukeki aiki Kuma zai ringa zuwa Yana dubamu kafin kidawo hakama ya tafi dashi anyi cike ciken makarantar dazashi har ilorin.


Saidatayi sallar magrib tukuna ta fito Palo ya zauna tareda miqe qafafu hafsatu na matsa Mata tana kallo cikin ranta tana cewa"


Amatu kinfa zamo hajiya 

Irin wannan Jin Dadi haka 


Gashi dama ba wani ciwo da qafafunta keyi tsaban son Jin Dadi da wuce wurine yasa take cewa ciwo suke Mata Dan a matsa Mata.


Wata tashar turawa take kallo ana wani film na adventure sai washe baki takeyi tana cin cake din data sa anty zarah tasa hafsatu tayi mata na inibi me laushi yaji butter sai ci take tana lumshe ido tana kallo tana Jan hafsatu da labari itama hafsatun na tayata fassarar qanxon kurege na turancin da akeyi Dan itama ba wani iyawa tayiba Amma ta dage tana fassara Mata.


Anty zarah ce ta fito daga dakinta ta nufosu cikin ado da kwalliya me kyau sai qamshi me Dadi take fitarwa amatu tabita da kallo cikin farin ciki tace''


Anty zarah kinyi kyau sosai

Amma meyasa zakiyi kwalliya yanxu da dare tunda kwantawa zakiyi?


Zama tayi kusa da ita tana murmushi tace"


Amatu MD na hanyar dawowa shiyasa.


Ohhh ohhh nagane anty zarah"

Taqarasa fada tana dariya.


Miqa Mata plate din cake din tayi tana cewa''

Anty zarah kici kiji yayi Dadi sosai.


Har takai hannu zata dauka saita fasa tana cewa"


Idan naji cikina zai cika bazan iya cin wani abincin ba kada MD yadawo nakasa tayasa cin abinci a dining.


Kallonta tana cewa' kici ko kadan anty zarah tunda kinaso.


Girgiza Kai tayi tana gyarawa amatun pillon data jingina dashi tana jawo Mata wani labarin take amatun tahau dariyar labarin datake Bata anty  zaran na tayata sunyi nisa sunata nishadinsu saiga bude qofar palon aka shigo Dr ne hannunsa daukeda qatuwar ledoji da amatu ta ajiye plate din cake din hannunta ta taso kenan saigashi a bayansa Shima ya shigo fuskarsa kawai ta kalla ta janye daga gefen Takoma gefen Dr ta tsaya tana Masa murmushi zatai Magana yace"


Baki gaida MD ba amatu.


Kallonsa tayi kafin ta kalli inda MD din yake Yana qarasa shigowa palon tayi qasa da murya tace"


Ina wuni sannu da dawowa.


Hannu kawai ya daga Mata ya nufi hanyar samansa anty zarah dake zaune ta miqe itama tana Masa sannu da dawowa to ita ya bude baki ya amsa Mata tareda Dan tsayawa ya kalleta kafin ya dauke Kai Yana cewa'


Karki jirani dinner nariga nayi dinner agurin Modibbo.


Kallonsa tayi Yana qoqarin wucewa tace"


Akawo maka ko fruits ne?


No thank you.


Wucewa yayi ya barta a tsaye tana binsa da kallo fuskarta na 'dan canzawa Amma Jin duk idanuwansu akanta yasa ta washe fuska tareda juyowa tadawo inda suke tana cewa"


Dr ko zakayi dinner tareda mu ne to?


Kallonta duk su duka sukeyi girmanta na qaruwa a idon Dr 

Tausayinta da qaunarta na shiga a zuciyar amatu tareda takaicin MD din ta yanda anty zarah ta Hana kanta cin komai sai yadawo Amma ya take hakan ya wucewarsa ko kwalliyar datayi danshi bai tsaya yayi Mata kallon ko mintu biyu ba ko me ya dauki kansa Dan ma yasamu mace me kirki da kyau kamar anty zarah tana sonsa wlh da itace koya Masa hankali zatayi taga qarshen kyau da Jan ajin banzansa.


Kamo hannun anty zarah din tayi suna zama palon tace"


Anty zarah Zo kici cake din Nan kiji Allah yayi Dadi sosai.


Ledojin hannunsa Dr ya miqawa amatu Yana cewa"


Nima a gajiye nake kamar MD shima yau a gajiye yake sosai Nima tunda muka hadu baicemin ko qala ba sbd gajiyar dayake tareda ita zanje na kwanta Saida safenku 

Amatu ki kula ok?¿


Gyada Masa Kai tayi tana cewa''


Nagode Saida safe.


Yana fita zarah tasaki murmushi tana cewa"


Dr kayaushe kanason gyara Abinda MD yakeyi Dan kada aga laifinsa 

Kadaina damuwa Dan Nima Babu ranar dazanga laifin nasa.


Takaicin MD din yasake Kama amatun tasake dagewa Saida anty zarah din taci cake din sosai Tasha apple drink suka cigaba da firarsu 

Ganin hankalin zarah din na Kan hanyar sama yasa amatu sakin tsaki qarami tana miqewa tace"


Bacci zanyi Saida safe anty zarah.


Tana shigewa zaran tasa hafsatu ta kashe komai itama tashige 

Suna shigewa taje dakinta ta shirya ta nufi dakin MD.



Ahankali amatu tasaba da zarah da hafsatu sosai kamar sunyi shekaru atare,

Kulawar dasuke Bata da gatan datake samu daga garesu yasa hankalinta ya kwanta sosai acikinsu musamman ma  da kullum tana waya dasu kawu dasuketa sawa Dr khalil albarkar yanda yake kula dasu sosai Dan yanzu ranakun matsuwarsu sun qare ga USI anata shirye shiryen zuwa makaranta,

A duniya yanzu mutanen datake so a rayuwarta fiyeda komai da kowa sune USI,kawu,iyami,Dr da anty zarah sbd sune mutanenda tasan tabbas qaunarta sukeyi Babu wani qyama ko munafurci.


Dr ya Gina qaunarsa cikin ranta danasu kawu sbd Suma shine mutum daya qwal daya fito ya tsaya musu a rayuwa yake qaunarsu batareda qyama ba ko buqatan wani Abu daga garesu shiyasa dukkaninsu kowannensu ya bude baki Dr ne abakinsa sai anty zarah dinta.


Qaunar data kewa anty zarah din yasa take Jin tsanar MD matuqa cikin ranta sbd yanda tagama lurada Sam baya damuwa da alamarin zarah din kullum shine damuwarta shine kukanta shine jimaminta ko tausaya Mata bayayi da yanda take matuqar qaunarsa/sonsa da ganin girmansa,


Duk yanda zarah din take qoqarin boyewa hakan baya boyuwa ga Wanda yake zama taredasu shiyasama Sam ta tsani ko ganinsa matuqar Yana gida Bata fitowa sbd kar wataran tayi amsa zagin maguzawa akan Abinda yakewa antyn saidai duk Abinda zai faru yafaru ba ruwanta.


A bangaren Jin Dadi kuwa zatace itakam gwara da akayi Dan kuwa rayuwa ta sauya Mata sosai Dan ko jikinta da fatarta sum nuna suna cikin hutu sbd lafiyayyar rayuwar datake ciki,

Banza ta Fadi" kaman yanda take fada

Dadinta takeci ba qaqqautawa duk wani Abu me Dadi cewa takeyi tanaso ba Bata lokaci kuwa Zarah zatasa akawo Mata shi,


Hafsatu kanta ta qararda 'yar ta'addace a gidan Dan kuwa tunda amatu tazo Bata zaman awa biyu batai aikin hada mata wani abuba,

Itace ayi Mata gullisuwa,

Tuwon Madara,

Kwakwameti,

Cake,

Dambun nama,

Dambun kaza,

Furar Madara da Milo

Komaima ci takeyi ita Bata taba ganin me ciki irin wannan na amatu ba da baya tadar komai 

Komai ci takeyi hadda Wanda masu ciki baya shafa musu lafiya

Gashi ko ciwon Kan Nan na banza da masu ciki keyi ita batayi kullum daram dam take

Ga Dr ya Hana asa kowane likita ya duba matarsa yace shine zai ringa dubata musamman da kwanakin umme tasaka fitinar sai Modibbo yasa anyi scanning Dan asan ranar haihuwar cikin su Fara shiri.


Hankalinta bai wani tashiba sbd tasan Dr na Nan shine zaisan yanda za'ayi da Maganar scanning din itadai damuwarta 'dayace shine anty zarah data Fara maganar cikin baya girma sbd ta shanye kusan wata biyu a gidan gashi Koda tazo tace ciki wata biyu wata hudu kenan Amma Babu alamar tasowar cikin shine anty zaran ta daga hankalinta cewar cikin baida lafiya itama tanason ayi scanning.


No comments

Powered by Blogger.