Abban Sojoji Takun Karshe Complete


Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


*Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃*



*nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅



Bismillah



Kai tsaye sautin ringing É—in wayar ya daki dodon kunnan Aunty babba dake baje saman gadonsu tana Bacci,a lokacin ko yatsanta bata jin xata iya motsawa saboda baccin dake a idanunta,yatsina fuska tayi alamar an takura mata,

   Ishaq dake tsaye agaban mirror yana gyara jikinshi ya É—an gyara murya tare da cewa"Madam ki daure ki tashi ki É—aga kiran nan!da alama kira ne mai muhimmanci tun É—azu wayar ke ta ringing,"

  Uban tsoki Aunty babba ta buga tare da yunÆ™urawa daÆ™yar ta tashi daga zaune,jikinta na sanye da sleeping dress,riga da wando purple colour,

  Fuskar nan tayi suntum kamar wadda aka nausa,hannu takai tare da É—aukar wayar dake ajiye saman bedside drawer,duba screen É—in wayar tayi ganin sunan Hayaam ya bayyana yasa ta Æ™ara tamke fuska kamar ta shanu,É—aga kiran tayi tare da kara wayar a kunnanta,rai a6ace tace"Meyasa kika kirani fitsararra!ko kin kira ne don ki Æ™arasa yimun rashin kunyar taki don ubanki,"

  on the other hand hayam tace"haba aunty laila,ni harna manta da abunda ya faru atsakanin mu.....'tunkan hayaam ta Æ™arasa maganar Aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"Idan kin manta ae ni ban manta ba,Ki faÉ—amun uban miyasa kika kira ni,idan ba haka ba ni zan kashe wayar,

  Zuba mata ido Ishaq yayi yana kallonta aransa yace"Zagi kamar Æ´ar maguzawa,ko kunyata bata ji,sae faman É—ura ashar take yi,ni dae Allah ya haÉ—ani da Guyaba,'

     cike da damuwa hayaam ta sassauta muryarta,tare da cewa"Aunty laila,na shiga uku,ko ince mun shiga uku,Akwai gagarumar matsala,Gaba daya duk wani plan É—inmu ya tashi aiki,'

  Tunda Aunty babba taji hakan,gabanta ya faÉ—i rasss,Æ™asa Æ™asa da murya tayi tace"Hayaam meya faru?wata irin matsala kike magana akai?

  "Aunty laila,Ashe yarinyar nan mai aikin gidansu,É—iyar uncle É—insu ce Abusufyan!!!!!" tamkar saukar aradu haka aunty babba taji maganar Hayaam aikuwa a matuÆ™ar gigice ta miÆ™e tsaye tana cewa

  "kutumar uba!inji ubanwa!yaushe Abusufyan ya ta6a aure,Wlh Æ™aryane koma wani É—an Æ™aniyar ne ya faÉ—i maki hakan babban maÆ™aryaci ne....'

  Gaba daya hankalin ishaq ya dawo kanta,maganar dayaji tana fadi ta tsaya mashi aranshi,

   "Wani abusufyan din kuke magana akai,"

  Firgit Aunty babba tayi tare da ware ido tana kallonshi sam ta manta da cewar yana acikin É—akin,

  Hankali a matuÆ™ar tashe ta miÆ™e tsaye da nufin ta fuce daga cikin É—akin,Saboda tsabar ruÉ—u ta nufi hanyar shiga toilet,

  gyaran murya ishaq yayi mata tare da cewa"kada fa ki shiga toilet da waya a kunnanki,'

  A zabure ta juya ta kuma nufi wardrobe da alama ruÉ—u yasa ta manta hanyar fita daga É—akin,zuba mata ido yayi yana mai mamakin irin kiÉ—imar da tayi,to ko lafiya?ya tambayi kansa,

   Bata ankara ba sae da goshinta ya bugi jikin wardrobe din kayan nasu,sannan ta gane inda ta dosa,Rai a6ace ta kama hanya ta fuce daga dakin,saukowa downstairs tayi ta miÆ™i hanyar wannan tsohon store É—in data ta6a garÆ™ame su hosana aciki,anan corridor É—in ta tsaya tana sauraran Hayaam,

  "Wlh Aunty laila da gaske ne,Ni shaidace,Naji komai lokacin da Uncle É—in nasu yake korama junaid bayani,bama haka ba Aunty azmee da kanta ta gasgata mun hakan,Babban abunda yafi rikitar dani Yaran fa triplet ne ashe,kuma dukkansu Mata ne kyawawan gaske,kamannin su sak iri É—aya,Kuma kina kallonsu zaki gane cewa Æ´a'Æ´anshi ne......'

  Hannu É—aya Aunty babba tasa ta dafe tsakiyar kanta,yayin da dayan hannun ke ruÆ™e da wayarta data kara a kunnanta,

  "Hayaam bazan ta6a yarda da zancenki ba,Taya hakan ma zata faru!mutumin da bai ta6a yin aure ba,Shi za'ace yana da Æ´a'Æ´a har Æ´an uku!Cikin shege kenan ya ta6a yima wata harya same su!Ni ban yarda da kalamanki ba,Hayaam kinsan cewa babu kyau tsoratar da musulmi,Idan wasa kike mun ki daina!!!!!

6acin raine yasa hayaam ta kashe wayar 

  Fashewa da kuka tayi saboda Æ™ululun baÆ™in cikin daya tokare mata maÆ™oshinta,ga zuciyarta dake ta faman tafarfasa,Gaba daya bata jin daÉ—in jikinta,

  Zubama wayar ido Aunty babba tayi tana kallonta,

  Tsoki taja tana jinjina kai tace"dama saida raina ya bani cewa Æ™arya take yi mun,tayi mun hakan ne saboda ta tsoratar dani don in saukko,Shashasha kawai,

    "Mommy kin farka kenan"

Muryar hafsat ce ta katse mata zancen zucin nata,

  Juyowa tayi tana kallonta,atsaye take fuskar nan É—auke da murmushi jikinta na sanye da riga da wando na jeans,ta É—aure sumar kanta da ribbom,yayin da hannunta ke ruÆ™e da Cup mai É—auke da Tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,

  Tunda Aunty babba taga hafsat na murmushi tasan cewa akwai matsala,hakanan dae ba zakaga fuskar hafsat da murmushi ba tunda farar safiya,

  Æ™aÆ™alo murmushin yaÆ™e Aunty babba tayi tare da cewa"Lafiya naga kina murmushi"?

  "Lafiya lou mommy,kawai wani abun farin ciki ne ya faru,nasan cewa muddin kema kika ji,zaki yi farin ciki sosai,'

  Murya asanyaye aunty babba tace"FaÉ—amun daughter har na Æ™osa naji wannan abun farin cikin?halan an Æ™ara maku albashi ne?ko matsayi aka Æ™ara maki wurin aiki"?

  Dariya hafsat tayi tana girgiza kai tace"Mommy baki canka dai dai ba,wannan albishir É—in da nakeso inyi maki yafi Æ™arfin duk waÉ—annan abubuwan da kika lissafo,kar6i tea É—in nan ki fara korawa kafin na faÉ—a maki,"

  Hannunta na kerma ta kar6i kofin da hafsat take miÆ™a mata,a hankali takai cup din  bakinta ta kur6i Tea É—in,kusan sau uku tana kur6arsa,kafin ta É—an jinkirta bayan ta janye kofin daga bakinta tace"daughter dan Allah ki faÉ—amun wannan wani abun farin ciki ne!wlh duk na Æ™osa naji,'

  "Zan faÉ—a maki mommy amma mu shiga daga cikin palour mu zauna,'

  "Ba inda zanje,idan zaki faÉ—amun ki faÉ—amun kawai,Sae ja mun rai kikeyi," tayi maganar tana faman tamke fuska,

  Hafsat tace"bada jimawa ba,Na kira Aunty azeema,don in gaishe da ita,Anan take sanar dani cewa Æ´a'Æ´an uncle abusufyan Sun bayyana...!

  Tunkan ta Æ™arasa maganar a gigice Aunty babba ta saki kofin dake hannunta,Ya tarwatse Æ™asa,Ruwan tean dake ciki ya fallatsar masu a Æ™afa,

  ja da baya hafsat ta É—anyi tana kallonta tace"haba mommy,so kike ki Æ™onamin Æ™afa ta,daga faÉ—in abun farin ciki?

  Rai amatuÆ™ar 6ace tace"Ki 6ace mun da gani sakarya kawai,MaÆ™aryatan banza,bazan ta6a yadda da kalamanku ba,duk bakinku É—aya da Hayaam,'

Ta faÉ—i hakan tare da kama hanya fuuuuu kamar zata tashi sama,ranta duk a jagule,bin bayanta hafsat tayi da kallo harta haye upstairs,ta6e baki tayi tare da watsa hannayenta tace"I don't care, Ni dae farin ciki nakeyi,Daddy ma nake jira in tambayeshi yaushe zamu je gidan saboda a qagare nake dana ga Æ´a'Æ´an uncle É—inmu Abusufyan,tunkan na gansu har naji ina sonsu sosai,in ma na tashi tafiya hada tsaraba zan tafin masu dashi,'

  Cike da farin ciki hafsat take maganar,zuÆ™unnawa tayi tana tattare kofin da aunty babba ta fasa,


Lokacin da Aunty babba ta Æ™arasa bedroom É—in nasu,har ta É—aga Æ™afarta zata zura acikin É—akin taji muryar ishaq yana cewa"Alhamdulillah!Alhamdulillah!Alhamdulillah!Abba nayi farin ciki sosai,Meyasa tun jiya ba'a sanar dani ba,ae da tunda sanyin safiya zanyi maku dirarr mikiya,Amma ina taya uncle murnar ganin Æ´a'Æ´anshi,kuma ina tayamu murnar samuwar Æ´an uku acikin zuri'ar mu,gaskiya bazan ma iya jurewa ba,Zan shirya nazo ne kawai,saboda na qosa naga Æ´an ukun mu bayin Allah....   

    Abba yace"wani abun ma sai kayi tozali da yaran,kyawawan Æ´an mata dasu,Yadda kasan photo copy É—in abusufyan haka suke,kamanninsu sak iri É—aya da nashi,'

  Murmushi Ishaq yayi tamkar yana agabanshi yace"Abba kafin na Æ™araso,dan Allah a isar musu da saÆ™on gaisuwata,Ace yayansu General ishaq yana gaishe su sosai da sosai,kuma saboda suma zaiyi zuwa na musamman,'

  "Insha Allah zan sanar masu yanzun nan,Allah ya kawoka lfy,"

  "Ameen Abbana,"

Sun jima suna waya kafin sukayi sallama ishaq ya ajiye wayar,

  tashin hankalin da ba'a sama shi date!!!!!!!

  Magana dae ta tabbata da gaske ne zancen da hayaam da hafsat suka faÉ—a mata,TabÉ—ijancan,

  Dakyar ta iya shiga cikin É—akin,lokaci guda ta rasa kuzarin jikinta kamar wadda tayi Zazza6i na sati É—aya,

  Jin takun tafiyarta yasa ishaq juyawa yana kallonta fuskarshi a washe har ya kammala shiryawa cikin haÉ—aÉ—É—iyar shadda,

  Ganin yana Æ™oÆ™arin buÉ—e baki yayi mata magana yasa tayi saurin katse shi da cewa"Naji abunda ya faru,Hafsat ta sanar dani komai,ina tayaku murna,'ko amsar shi bata tsaya ji ba,ta faÉ—a cikin toilet,

  Tana juyo muryarshi daga cikin bedroom É—in yana cewa"Ni yanzu zan wuce Abuja ne,inyaso kun biyo ni daga baya ko zuwa gobe ko jibi haka,duk dae yanda kuka yanke shawara keda hafsat,

  daga cikin toilet tace"Allah ya sauke ka lpy,in anje agaishe mana da mutanen gidan,"

   "zasuji insha Allah," ya amsa mata tare da kama hanyar fita daga É—akin.

No comments

Powered by Blogger.