Jinkirin Aure Complete Hausa Novel

 


AM OUM HAIRAN: *_JINKIRIN AURE_*

*_Ƙalubale ga ƴammata_*




*By


*Oum Hairan*

*Dedicated to*

Dr Mass Agadas son so for ever.

*P 1-2*



Iska ce ke kaɗawa ta damuna me cikakken sanyi da sanya zuciyar da take cikin kwanciyar hankali a nishaɗi, yayin da zuciyoyin da suke cike da zullumin damuwa suke kasancewa da sassaucin yanayi.

Saidai a gurinta itan wannan yanayi yafi mata kowanne yanayi zafi, rayuwarta ta ƙuntata hawayenta ya yawaita ƙuncin zuciyarta ya ƙaru a yayin data keɓance kanta ita kaɗai a madaidaicin office ɗin nata me ɗauke da table me kujera ɗaya, gabanta cike yake da files-files na petiant ɗinta na yau data gani inda gabadayan hankalinta yabar gangar jikinta a zaune saman kujerar lokaci zuwa lokaci hawayenta ba diga saman takardar dake gabanta.

Ƙwankwasa ƙofar akayi har karo uku dake hankalinta baya jikinta batasan anayi ba, jin shirun ne yasa me neman izinin turo ƙofar tare da sallama ta shigo cikin office ɗin ta tsaya ta zubawa Mamallakiyar office ɗin idanu tana mamakin abinda yake sanyata shiga matsananciyar damuwar da har hankalinta yake gushewa haka.





Dukan Table ɗin Dr Zaheera tayi abinda ya dawo da wadda ke zaunen cikin nutsuwarta tayi saurin sa handcap ta share idanunta ta ɗagosu ta zubasu kan Dr Zaheera itama ita take kallo harta isa ga wata kujerar ta zauna suna facing ɗin juna.

Dr Zahira ce ta kawar da shirun da cewa “Kullum kin kasance cikin damuwa kin takuri kanki kin tsawwala kanki Dr Madinah meye yasa hakan ne? Meyesa kike mantawa duk abinda ba'a fareshi akanka ba bazaa ƙare shi akanki ba?" 

Manyan fararen idanunta ta lumshe ta kwantar da kanta saman kujerar da take kai hawaye na tsiyaya daga kwarmin idanunta tasa tisue ta goge dogo hancinta

“Meye ne matsalata meye ne aibina meye yasa kyawuna ya kasa samar min da mijin aure, meyesa kullum al'umma basamin adalci suke ganin cewar nice naƙi aure bayan Nima nafi kowa son na ganni cikin dausayin sunnar ma'aikin Allah???

Tambayar da kullum nakewa kaina kenan"




Cewar Dr Madinah dake ɗagowa tana zuba idanunta akan ƙawarta Dr Zahira, shiru Dr Zahira tayi na ɗan lokaci sannan ta buɗe baki tace.

“Dr Madinah ba jama'ar gari da suke ganinki daga nesa ba ni kaina da nake da kusanci dake lamarinki yana bani mamaki gani da sani a damuwa da tunanin meye dalili? Madinah kyawunki yakai ace kina juya ragamar maza a hannunki sai kuma ya kasance maza sune ƙaddararki, ta yaya zan yarda ace mu da bamu kai ba maza na zumuɗi akanmu ke da kika wucce kice babu wanda ya taɓa cewa yana sonki?"





Murmushi me ciwo Madinah tayi tana kai dubanta ga agogo ta miƙe ta fara harhaɗa files ɗin ta sanyasu wajen adanasu ta ɗauki jakarta ta dubi Dr Zahira tayi gaba tana cewa “duk sanda na tsaya tuntuntunin abinda kike tunani yanzu Zuciyata zafi takeyi Zahira ni kaina na fara tsoron kaina ina tunanin to ko wani abune ke gareni abin gudu da Ni na kasa ganewa, Zahira shekaruna sun fara tafiya a matsayina na ɗiya mace ba namiji ba ace na zubar da shekaru talatin da biyu batare da aure ba wannan abu da cin rai yake....."

Isa sukayi bakin titin suka tari ɗan sahu suka hau ya fara sauke Zahira a kwanar unguwar su sannan ya wuce da Madinah tasu unguwar ya sauke ta ta fito tana gyara mayafin data yafa saman uniform ɗinta na aiki ta nufi unguwar tasu lokaci zuwa lokaci suna gaisawa da dattijan unguwar dake zaune a ƙofar gidajensu.




Gidansu ta shiga da sallamarta babu kowa a tsakar gidan hakan ya bata damar nufar ɗakin mahaifiyarta ta daga labulen tana cewa “Ammi sannu da gida" Ammi dake zaune  a tsakar ɗakin ta ɗago tana duban tilon ɗiyar tata mace tace “Yawwa Munau Jaɓɓama" guri ta samu ta zauna tana yage mayafinta tace “Yau na gaji da yawa Ammi me kuka girka mana?" Numfashi ta sauke tace “Abinda kika tsana" dafe kirji tayi tace “Nashi na Ammi don Allah meye yasa kukayi alale?" Tana maganar tana kwalawa me aikinsu kira Bintalo ta ta rusuna a gabanta tace “meye kikeyi Binta?" Tana wasa da yatsunta tace “bsbu abinda nakeyi Uwarɗakina" fasali taja tace “ki samamin abinda zanci insjin yunwa gashi ku kun tashi kunyiwa mutane Alele" miƙewa Bintalo tayi ta fita bata jima ba ta dawo ɗauke da tire shaƙare da kwanuka ta ajiye mata a gabanta ta fara budewa tayi murmushi tace “wato wanani Ammi kikayi niyyar yi ashe ma My Favorite kukayi" murmushi Ammi tayi ta zuba mata ido tana kallon yanda take cin abincin a nutse da alama yunwa ta yini da ita yau.





“Munau" Ammi ta kira sunanta ta ɗago tana ajiye cokalin ta mayar da hankalinta ga mahaifiyar tasu Ammi tace “Wato Madinah kullum da wannan tunanin nake kwana nake tashi kullum da tunanin lokacin aurenki nake bacci nake tashi  Madinah kullum shekarunki tafiya sukeyi girma ƙara sauko Miki yakeyi ke kuma abinda yake aranki shi kikeyi baki tunanin gobenki kin kasa tsayar da hankalinki ki samarwa kanki abokin rayuwa ki inganta kanki, Munau meye ne a gabanki daya danni sunnar ma'aikin Allah da tunaninki baya baki dacewa da cancantarki na kiyi ta? Aure shine martaba da mutuncin kowacce ƴa mace aure shine daraja da ƙimar kowacce mace ke ba iya mace ba hatta namiji aure shine ƙimarsa"





Idanunta da suke tsiyayar da hawaye ta sadda ƙasa taci gaba da kukanta me tafasa zuciya, wannan ya tashi hankalin Ammi tace “Ina mamakin yanda da zaran nayi Miki magana akan ingancin rayuwarki kike sanyani a gaba kinamin kuka Munau idan har maganar da nakeyi Miki ce bakiso zan iya tattarawa na daina amma ki sani da gaske ganinki a gabana bayamun daɗi kamar kowacce uwa Nima nafison ki rinƙa zuwar min da yawo kina komawa ɗakinki"

Hannu tasa ta tsane hawayenta ta ɗago cikin raunin murya tace “Wlh Ammi kullum ina addu'a mafarki da fatan zuwan wannan ranar amma taƙi zuwa, Ammi ya zanyi wannan rana tazone? Nima na zama matar aure cikakkiyar mace me ƴanci sannan me ji da alfarmar aure, Ammi ki daina ganin laifina kiyimin addu'a don Allah kema gani kikeyi kamar nice banason aure bayan auren ne yaƙi zaɓata Ammi kinsani tun kafin wannan lokacin wallahi tallahi bansan wani namiji ɗaya daya taɓa tarata ya buɗe baki yacemin yana sona koda wasa ba bare da aure, wai Ammi ya akeyi ake samun mijin auren nan ne Nima nayi ko na samu ki daina kallo na a me laifi...." 





Ta ƙarashe maganar tana sakin wani kuka me gunji tare da kifa kanta a kafaɗar Ammi, cike da tausayawa Ammi ta shiga bubbuga bayanta da sanyin yanayi na mahaifiyar da taga ɗanta cikin halin tsanani tace “Shikenan Munau na fahimceki ki daina kukan haka Allah yanaji yana gani zai kawo mana mafita da yardarsa zanci gaba da yimiki addu'a kema karki gajiya wannan ita ce ƙaddarar mu, yawwa ɗazu baffan ku Sunusi yazomin da maganar haɗin aurenki da ɗan uwanki Khamal..."

A firgice ta ɗago tace “Ni kuma Ammi habadai Khamal kin manta waye Khamal Ammi ƙungurmin ɗan taba sannan ɓarawon kaji da awakin unguwa ace shine mijina? A'a nikam wannan zaɓin baimin ba nidai a tayani da addu'a nasan Allah bai manta dani ba Ammi"

[6/2, 9:15 PM] AM OUM HAIRAN: *_JINKIRIN AURE_*

*_Ƙalubale ga ƴammata_*




*By*




*Oum Hairan*




*Dedicated to*

Dr. Mass @gadas son so for ever.




*Free P 3-4*



_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank._





Tashi tayi ta nufi ɗakinta ta cire kayanta ta nufi bayi ta watsa ruwa tayi alwala tayi sallar magrib ta zauna tana karatun Kur'ani tana sharar hawaye, a wannan yanayi taji an buɗe ƙofar dakin nata an shigo an nemi guri an zauna bata ɗago ba Saida takai aya sannan ta rufe Kur'anin ta shafa addu'arta ta juyo  tare dayin kasa da muryarta cikin girmamawa tace “Yaya Mus'ab  kaine a daren nan ga gari yanata cida alamun ruwa zai sauka"

Fasali yaja yana cire hularsa yace “To ya zanyi Madinah kece kinƙi barinmu mu huta Baffa Sunusi ne yaje ya dameni   da maganar aurenki da Khamal kuma yacemin lallai kafin azumin bana sukeson ayi komi a gama shiyasa nazo naji meye kike ganin zai yuwu?" 





Tunda ya fara maganar take kallonsa tana girgiza kai batare da ta katseshi ba har ya gama sannan tace “Yanzu Yaya Mus'ab wannan shirmen maganar har takai ka hana kanka kwanciya cikin iyalinka ka fito da wannan tsohon daren?" 

Murmushi yayi yace “Kullum ke raayinki bambam yakesha da mutane Ni abinda yasa naga dacewar nazo mu tattauna naga ba duka abinda rai keso take samu ba musamman a wannan bigiran Madinah kinsani ni bana cikin mutanen da zasu kawo Miki mafita domin cutarwa a gareki, nayi ɗawainiya da rayuwarki tun yarinta kawo lokacin da kika zama mutum kike iya yiwa kanki abubuwa da suka shafi rayuwarki.

Inason ki tsaya ki ɗauko hankalinki ki tattarashi waje guda ki duba yanda rayuwar take tafiya kiyi hƙr ki karɓi wannan zaɓin kiyi addu'a wata ƙila shine alkhairin daya hana wani zuwa ke kuma kikaƙi karbarsa tun kina ƙarama"




Idanunta ta ɗago daya ciko da kwalla tace “Shikenan ashe dama idan Allah ya jarabci bawa da wata ƙaddara saiya manta da faɗin ma'aiki (S.A.W) da yake horonmu da mu zaɓawa ƴaƴanmu iyaye na kwarai, Yaya Mus'ab wanne ɓangare zan nuna idan na karɓi Khamal a matsayin miji nace shine alfahari na? Please Yaya Mus'ab na rokeka a matsayinka na gatan daka tsayawa rayuwata kayiwa girman Allah ka shigemin gaba wajen bijirewa auren Khamal baiyimin ba bayan haka Nima banyi masa ba Yaya Mus'ab abinda Khamal yake faɗa min kullum shine shifa duk da lalacewarsa yanaji a ransa taimakona zaiyi idan ya aureni saboda naje na zubar da darajata irin mazan da nakeso na tsaya ruwan idanu nayi musu tsufa bazasu iya aurena ba Yaya Mus'ab kullum haka yake faɗamin Ni ban kalleshi da aibinsa ba sai shine yake cusguna min da naƙasun da bani nayiwa kaina ba...." 





Ɗaganta hannu Yaya Mus'ab yayi yace “Shikenan ya isa Madinah Allah yayi zaɓi na alkhairi yanzu ya batun komawarki karatun? Dr Shafi'u abokina yace akwai wata jami'a a Rasha da suke bada horo na musamman akan duk wata matsala data shafi ƙwaƙwalwa to ke kuma naga kinada interested akan wannan ɓangare shiyasa nace zanyi Miki magana ko zakije ki ƙara samun gogewa" 

Ƴar ƙaramar dariya tayi tace “Shiyasa nake sonka Yayana duk abinda da zai kawowa rayuwata haske shine burinka Yaya Mus'ab Allah yaja kwana ya ƙara arziki, ka bincika min shi abinda tafiyar zataci da inason na biya kudin aikin hajji amma tunda hakane bari na tura gaba tunda dai Ammi tayi Ni daga baya naje nayi, Yaya nifa Research kawai akan abinda ya shafi brain yana mugun sani nishaɗi" 

Dariya Mus'ab yayi yace “Autar Ammi kenan waye zaiƙi farin cikin Ammi ai dole mu ƙarfafa Miki gwiwa munyi waya ma da Khamis shima ya bada goyon baya Salees ne dai da Aminu suke ƙorafin wai mune mukeja ake zaginmu ana cewa mun ɗaure Miki gindi kina yawo da sunan karatu ni wani lokacin gwiwata har sanyi takeyi"





Kwantar da kanta tayi jikin bedside tace “kuyi hƙr No condition is permanent Ya Mus'ab wata rana sai labari Allah shaida ne bana aikata abinda mutane suke zargina dashi Yaya duk wata mace da wannan ƙaddarar ta faɗa mata dama sociaty dinmu kallon ƴar iska gantalalliya watsattsa sukeyi mata hatta da Allah ya hukunta zai aureta bayajin a ransa budurwa zai aura, nifa da wannan surutun da nakeja muku wlh ko za'a bani sadakin bazawara indai nagartar mijin takai gara na karɓa indai yayi albarka Shikenan"




Murmushi yayi ya miƙe cike da tausayin ƙanwar tasa yace “Insha Allahu komai zai wucce ki kwanta goma ta wucce gashi gobe talata" fatan alkhairi tayi masa ya fice tare da ja mata ƙofar ta miƙe tayi mata key ta shiga bayi ta dauro alwata ta kwanta daidai lokacin da aka kece da wani ruwa me ƙarfi ta kunna MP tana sauraron ƙira'a tare da tsunduma duniyar tunanin rayuwar baya.

Kamar yanda ta saba yauma ganin zata raba dare bacci yakasa ɗaukarta tana hasaso lkcn da zata kwanta kusa da mijinta ta tayi matashin kai da ƙirjinsa ta shafa sumarsa taja gemunsa, wannan rana ji takeyi dama zata iya kissimo irin nishaɗin da zata kasance dama tazo mata nan kusa dama zata buɗe idanu taga ba ita ce Madinan da abu ɗaya ya zamewa tsaiko cikin rayuwarta ba.





To wai meyene abinda ya zame mata katanga da samun abokin rayuwa ne? Tambayar da kullum takewa kanta da makusantanta kenan amma ta kasa samun amsa saidai ace mata tayi hƙr lokaci ne idan ta hƙr ta cire komai a ranta kuma sune waɗanda zasu fara cewa da ita “Madinah wai yaushe zakiyi aure ne?" Wannan tambaya tana dagula lissafin ta da ace mutanen duniya zasusan ƙuncin da take shiga a dalilin wannan tambaya da sun daina yi mata ita.

Zuwa yanzu abubuwa sun fara yi mata nauyi sha'awar kasancewa da namiji abokin ɗebe kewa tana yawan bijiro mata takan raba tsayin dare bata iya bacci ba saboda ciwon mara idan abin ya ta'azzara har fita takeyi daga hayyacinta sai likita ya tsaya a kanta sannan take dawowa daidai.

Sai bayan sallar asuba sannan ta koma ta kwanta bacci me nauyi ya dauketa dake yau ba itane da dutyn safe ba tanada isasshen lokacin bacci ba ita ta farka ba sai 12:21pm ta farka shima tashinta akayi ta buɗe idanunta kan Ƙawar tata kuma abokiyar aikinta Dr. Zahira murmushi sukayiwa juna Zahira tace “Tunda nayita kiran wayar ki najita a kashe nasan kinanan kina sana'ar saiki tashi mu fita inaso zaki rakani unguwa"





 Miƙa tayi tare da salati ta diro a katifar Zahira tabita da kallo tana cewa “Kaga manyan mata masu manyan kaya matan me rabo wato Dr. Komanki abin sone ga kowanne lafiyayyen namiji wlh Ni kaina da nake mace halittarki na birgeni an baje fasaha wajen ƙeraki ke gani kin zamewa mazaje ƙwalele ya Allah karka kasheni sai naga wannan me rabo da zai huta da jikin nan" 

“Amin ta amsa dashi tana shigewa bathroom ta sakarwa kanta ruwa ta sulla wankanta ta ɗauro towel ta fito ta tsaya jikin mirror tana shafa ta bata kusan rabin awa wajen shafa mai fesa turare gyara gira sannan ta koma ta ɗauki wata baƙar atamfa tasa abinka da kyakkyawar nandanan ta ƙara wani kyau na musamman ta ɗauki mayafi Milk kalar zanen jikin atamfar da takalminta da jakarta duk kalar mayafin ne ta dauki system nata da wayoyinta suka fice.

A tsakar gida suka ishe Ammi tana gyaran ƙumba ta dubesu tace “Ai dake kece kinga ta fito Zahira ni tun asuba rabona da Munau tanacan tana sana'ar bacci kamar kasa" dariya tayi har Saida dimpli ɗinta ya lotsa tace “Ayyah Ammi wlh banyi bacci da wuri ba jiya don Ni a yanda na kwanta ma sai biyu zan fita a gdannan to wannan uwar ƙwarzabar tazo ta tasheni wai zataje unguwa kuma saina rakata" 





Tsugunnawa tayi tace “Ammi na tuba wlh na horu a taimakeni da key ɗin motar Allah bazan kuma bige kowa ba" harararta tayi zatayi magana tace “Wlh Ammi tsautsayi ne bazan kuma ba da abin hawan kafi kwarjini kinsan yanayin aikin mu....." 

Cilla mata mukullin tayi tana cewa “Yar ƙaniya jeki nikam Allah nunamin ranar aurenku na daina ganinku kuna shigemin gaba" addu'a ce Ammi tayi amma Saida ta sanyaya mata jiki, har suka isa kango jikin gidan nasu dake dama tun jiya tace da maigadin ya wanke mata motar shiga kawai sukayi ta sallameshi suka fice suka dauki hanyar asibitin da suke aiki.

Dr. Zahira ce ta kawar da shirun da cewa “Na fahimci kinsa damuwa kwana biyu a ranki Dr. Meye yasa Ni da nake bazawara bana damuwa kamar yanda kike damun kanki?" Dr. Madinah akwai arhar hawaye nandanan suka shiga zarya a idanunta ta buɗe ƙaramin bakinta tace “Saboda ke kin taɓa yi kinada yaranki ko yanzu kika mutu kinada masu ɗaga hannu suce Allah ya jiƙan Umman mu Dr. Ni banyi ba banida kowa sai Ammi, kwana biyun nan ta matsa da maganar aurena sai nakejin dama zan iya aurar kaina kodan na faranta zuciyar mahaifiyata" 

Cikin tausayawa Dr. Zahira tace “Dole zata damu Dr. Ko kinsan yanzu a unguwar nan taku shafinki aka buɗe jiya Husain ƙanina yazo yake cemin wai ke meye ya hanaki aure ne? Na dubeshi da mamaki shine yake cemin yaji a majalissar Bala me Youghut anata zaginki wai karuwanci kikeyi har wani dillali yana cewa shi yama taɓa kaiki gurin wani mai gidansa....."

[6/3, 7:14 PM] AM OUM HAIRAN: *_JINKIRIN AURE_*

*_(Ƙalubale ga ƴammata)_*




*By*




*Oum Hairan*




*Dedicated to*

Dr. Mass @gadas son so for ever.




*Free P 5-6*



_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. Shaidar payment ta wannan number 09013718241_





Murmushi takeyi wanda da ka gansa kasan na ciwo ne irin wadannan ƙananun sharrikan suna damunta amma yanzu sun rage yi mata zugi a zuciya ta saduda tunda ita dai ta tabbatar da bata taɓa aikata abinda mutane suke kallonta dashi ba, ta sani Allah zai wanketa tsaf idan lokacin wankewar yayi.

Da wannan suka isa sukayi parking bata iya cewa komai ba suka fito kowacce ta wucce office ɗinta da wuri tayi ƴan aikace-aikacenta ta sallami petiant ɗinta yawanci duk waɗanda zasu ƙara karɓar magani ne da kuma ganin yanayin jiki dake azumi ta ɗauka yau ɗin sai uku ta fito daga nata office ɗin ita dama Dr. Zahira ta jima da tashi a aiki suka kuma ficewa, lalle sukaje da kitso Zahira aka yima kitso Madinah ba ma'abociyar kitso bace tafi ganewa ta gyara sumarta ta daure dake Allah yayi mata baiwar sumar.





Biyar suka ɗauki hanya wannan karon Zahira ke jan motar suka shiga unguwannin cikin gari ƙofar nasarawa sukaje wani gida Zahira ce ta kira wata number bugu biyu aka ɗaga suka gaisa ta sanar dashi suna ƙofar gidan yayi musu izinin shiga Madinah na mita tana cewa ta gaji da yawon zuwa gurin ƴan tsubbu da Zahira ke sata ita ta barta taji da damuwarta basai ta ƙara mata wata ba.

Da wannan suka shiga cikin gidan a aljihun zauren suka ishe babban mutumin malami ne babba da tarin littafai a gabansa yana duba wani littafi a hannunsa ya dago ya amsa sallamarsu tare da nuna musu gurin zama suka zauna da gaisawa Zahira ta fara yi masa bayani tace “Mal wannan ita ce Dr. Madinah wacce jiya na fara baka labari wato Mal wani abune me bam mamaki da ɗaure kai yake faruwa nikam abin yana bani mamaki matuƙa, Mal babu muni babu matsalar tarbiyya babu jahilci babu gigita ta talauci amma rayuwar taƙi tayi haske kullum cikin damuwa take hatta Ni kaina abin ya fara sani a damuwa, Mal mijin aure ya gagara ga Dr. Madinah gashi shekaru har sun fara nauyi kullum abu sai ƙara nisa yakeyi Ni raina ya fara faɗamin anya babu sa hannu ko na mutum ko na shaiɗanu?" 





Zubawa Dr. Idanu yayi kanta na ƙasa tana wasa da yatsunta can ya numfasa yace “Allah ya shiga lamarin Madinah" shiru ta tsawaita can ya dago yace “Babu matsalar jinnu cikin lamarin nan kuma babu sa hannun kowa Madinah kawai lokacine baiyi ba amma insha Allahu zamu duƙufa tayaki addu'a Allah ya jinkirta zama ya kawo abokin rayuwa na kwarai yanzu abinda nakeso daku ga wata addu'a da zan baki yau daren Laraba ƙarfe biyu ki tashi kiyi alwala kiyi sallah raka'a huɗu kowacce ki karanta mata fatiha ƙafa ɗaya da kulhuwallahu 40 kowacce raka'a har ki idar kiyi istigfari adadin 100 kiyi salatin annabi ƙafa ɗari shima kina me tawassali ga Annabi Muhammad (S.A.W) bayan kin gama ki faɗi bukatar ki ta zaɓin miji na kwarai abin alfaharin kowacce mace sai ki rufe da istigfari 100 salati 100 saiki tashi ki koma ki kwanta kiyi haka na tsayin kwanaki bakwai bijahi Rasulullah sai Allah ya waiwayi lamarinki domin kin haɗa shi da wanda bazai iya juya baya ga bukatar wanda yaje masa dashi ba wato Muhammadur Rasulullah, Madinah idan kinyi haka duk abinda alƙibla ta nuna to dole ki karɓe shi koda kuwa ɗan uwan naki Khamalu ne idan kuma akasinshi ne to dama fatan da mukeyi kenan, aje a dage Allah zai duba buƙata"





Gdy tayi masa sosai suka ajiye masa sadakar Naira dubu goma suka tafi hakanan taji malamin ya kwanta mata domin a kalaminsa akwai tawali'u sosai cikin lamarinsa, suna tafe ne tafiya irin ta kurame can Madinah tace “Dole zan bar ƙasar nan cikin yan kwanaki Dr. Saurin cin birki tayi tace “What happen Dr. Madinah da zakice zakibar ƙasa bayan kinsan yanayin da muke ciki yanzun?"  Numfashi ta sauke tace.

“Shine dalilin da zaisa nabar ƙasar Dr. Zahira yau ina zaune a office Baba Sunusi ya kirani zagin da yayimin akan nace banada ra'ayin aure da Khamal ko karen gidansa baitaɓa waba har yana kirana ƴar matsiyata taka hayen arziki......" Kukane yaci ƙarfinta ta rushe da kuka tace “Wai meye laifina ne da Alƙasim ya haifeni da Adiyyah? Dubanta Zahira tayi tace.

“Na dade da fahimtar family ɗinku kuna rayuwa a cikinsu ne kawai amma basa kaunarku Dr. Don Allah yau dai ki bani labarinki ko a takaice ne wala Allah ta yiwu inada rawar takawa Dr tun muna school of nursing na fahimci halin da kuke ciki amma abin baiyi tsamari irin yanzu ba don Allah Please Dr. Ba'a ɓoyewa abokin kuka mutuwa"





Ajiyar zuciya ta rinƙa jerawa sannan tace zan baki labari na Zahira kiyi hƙr tun a baya ba rashin cancanta ce tasa nake basarwa ba rashin lokaci ne yanzu kuma inada lokacin da zamuyi amfani dashi yanzu muje gidan Mama mu ɗauki izini saimu kwana a gdanmu" 

Haka akayi gidansu Zahira suka fara zuwa Mama bata hanasu ba don tasan shakuwarsu musamman da sukace zasuyi wani aiki ne suka dungumo suka taho Sheka lokacin Ammi ta gama haɗawa autarta kayan shan ruwa suka baje a tsakar gida suka huta lokacin sallah yayi sukayi Saida sukayi Isha sukayiwa Ammi sallama sukayi shirin kwanciya dake katifar ta Dr Madinah babba ce by six ce me tudu, duban Dr Zahira tayi tace “kin shirya jin labari na?" Jinjina kai tayi Madinah tayi murmushi tace “kin shirya zubar da hawaye kenan zan baki labari kamar yanda kika buƙata  amma idan bukata ta samu zan tashi" amincewar Dr Zahira yasa Madinah gyara zamanta ta kurɓi coffee ɗin hannunta ta fara da cewa.



***    ***    ***    ***



Madinah Alƙasim, shine cikakken sunana  Wadda a yanzu duniyar likitoci musamman wanda suka shafi ƙwaƙwalwa a ƙasata Nigeria sukafi sani da Dr. Deenah,  Mal Buba shine wanda yayi silar tsatsona domin shine ya samar da Alƙasim da ƴan uwansa Sunusi Nuhu da Kabir sai mata biyu Gwaggo Hajara da Yakumbo Harira, Baffana Wato Alƙasim shine daban a cikin  biyar ɗinnan kuma shine ɗa na uku a wajen Mal Buba ya kasance Sunusi da Nuhu sune kawai a samanshi sauran duk ƙasanshi ne.

Mahaifina ya taso da rangwamen gata saboda mahaifiyarsa ta rasu ne tun yana shekara uku a dalilin haihuwar ƙanwarsa inda suka tafi tare ita da jaririyar data haifa, saiya kasance ruƙon Kasim ya koma hannu Inna Mai koko wadda ita ce uwar su Sunusi. Inna mai koko batason Kasim ko kaɗan hakan yasa suma yaranta suka taso da aƙidar ƙiyayyar Kasim inda shi kuma Mal Buba ganin yanda suke nunawa ɗan marayan zakin nasa kyara da tsangwama yasa ya ɗauki kulawa da soyayyar duniya ya ɗora masa.





Sai ya kasance duk inda zasuje tare suke zuwa dake Mal Buba bafulatanin Gwangola ne dake cikin taraba a yanzu  ya taso da yawon kiyo da fatauci har kawo lokacin da girma ya fara riskarsa, yaso ya ɗora Babban ɗansa Sunusi akan wannan tafarki amma sai Innan mai koko tayi tsalle ta dire tace ƴaƴanta karatun boko zasuyi ba gantali ba shima da yake ya jima da zare lissafinsa akansu yasa yaci gaba da rainon Kasim akan harkarsa har Kasim ya saba fita kasashen Afirka shine Chadi Ghana Cameron Mali Senegal Togo kai dama kasashe da yawa na Afrika irinsu Rwanda da dai sauransu.

Daga baya ne kuma karatun bokon yaƙi ga ƴaƴan Inna taso su koma harkar fatauci abin ya faskara domin ba'a rainesu a cikinta ba Baffa Kabir ne kawai ya ɗan yi abin arziki lokacin da Mal Buba ya dawo ya zauna su kuma sukaci gaba da fafatawa a zahiri  Kabir ba irin zuciyar yan'uwansa ne dashi ba shi yanason Kasim musamman yanzu da kusancinsu yake ƙaruwa suke yawon kasashe tare.

Kasim baiyi ilimin boko mai zurfi ba iyakarsa Firamare irin ta wancan lokacin bata yanzu ba amma yanada ilimin muhammadiyya fiye da yan uwansa dalilin da yasa komansa ya zama cikin nutsuwa da dattako,  Wata shekara harkar kasuwancinsu takaisu Ethiopia a hanyarsu ta shiga garin Ethiopia ne sukayi kicibis da wani ayari na ƴammata sun dauko ruwa dake suna kusa da wani ƙauye ne. 

Nan suka isa garesu suka rokesu su sammasu ruwa su sha su wanke fuska kasancewar tafiyar Sahel ga rana duk sun galaɓaita, sai waɗannan ƴammata sukaƙi basu wannan ruwa guda ɗaya cikinsu da tafi kowacce kyau ita ce ta tsaya bayan yan' uwanta sun tafi ta basu ruwan nata sukasha sukayi alwala suka bata tulun ta juya ta koma.






Kasim ne ya dubi Kabir yace “Bantaba zuwa garinnan ba amma naji labarin abinda ke faruwa mubi yarinyar nan kada matasa su keta mata haddi"  babu musu sukabi bayanta ilai kuwa batayi nisa ba wasu matasa su biyu suka fito cikin rairayin Sahel suka tareta sunayi mata dariya ɗaya cikinsu yakai hannu ya dumbuli nononta aikuwa ta ƙanƙame jikinta yana rawa tanayi musu magiya da yanayin tashin hankali kamota ɗayan yayi daidai lokacin da Kasim ya iso da sauri yakai hannu zai ƙwaceta suka kama kokowa da matasan har suna yankarsa daƙyar ya ƙwaceta a hannunsu y haɗata da Kabir shi kuma yaje ya ɗebo mata ruwan ya dawo ya ishe su tana ganinsa ta rinƙa murmushi da kanta tayi musu jagora har gdansu mahaifinta tsoho ne sosai shi kaɗai ne a bukkar tasu sai wata bukkar dake rufe a gefe.





Da mamakinsu sukaji yayi musu magana da fullanci suka amsa masa yayi musu tambayoyi suna bashi amsa can ya dago yace musu  “Adiyyah tayi miji yau zan daura maka aure da matarka ka dauketa ku tafi" Saida gaban Kasim ya faɗi ya ɗago zaiyi magana ya ɗaga masa hannu yace “yaro tsayin lkc ina jiran zuwan mijin Adiyyah baizo ba sai yanzu ka bayyana tabbas kaine zabin da Allah yayi mata kayi hkr ka karɓi al'adarmu a yanda tazo maka zakaji dadi kuma zakayi alfahari da auren Adiyyah gatanan na baka ita halak malak bayan Ni baka da wani gata saikai daga bayyana yanzu"

Kasim baiso karbar wannan aure ba haka Kabir ya rarrasheshi aka ɗaura wannan aure Adiyyah tayi murna shikam Kasim sama-sama ce murnar shi a ranar kaka Hakeem  ya bawa Kasim wannan bukka dake rufe wai ya kwana da matarsa shi kuma zasu kwana da Kabir, wannan shine asalin haɗuwar Kasim da mahaifiyarmu Ammi kenan.





Cikin ikon Allah watansu biyu a wannan ƙauye suna shiga cikin gari suyi sarinsu har suka gama ana saura kwana uku zasu tafi ne ciwon ajali ya riski tsoho Hakeem a daren ya rasu sarai Adiyyah taji mutuwar mahaifinta maiyi mata gata dake su can ba kamar mu ba basa zaman makoki kwana biyu da rasuwar suka dauko hanyar Nigeria birnin Kano kasancewar kasuwanci ya jima da dawo da Mal Buba Kano ganinsu da baƙuwar fuska yasa bayan Oyoyo akayi cirko-cirko ana jiran aji abinda suka zo dashi Kabir ne yayi masu bayanin komai Mal Buba ya jinjina lamarin ubangiji shi nan har yayiwa Kasim mata a can Gwangola ashe matarsa tana Ethiopia, shikam baija da lamarin ba Inna me koko ce dai a lokacin ta rinƙa faɗa tana cewa wannan ai irin tsiya da masifa aka dauko musu ƙasar da akace da karuwanci suke samun kuɗin shiga shine zaaje a kwaso musu don a lalata musu nasaba.

Shi kuwa Sunusi baƙin ciki ne kawai na ganin zukekiyar matar da ƙaninsa ya samu a sadaka yasashi ƙyashi da baƙin ciki gashi shi ya bige da yar tallan shinkafa da wake. Gidan da Mal Buba ya ginawa Baffa Sunusi nan yasa aka gyarawa mahaifina da mahaifiyata Mal Buba da kansa yaje kasuwar Rimi ya siyo musu katifa da pillow da duk wani abu da yasan zasu buƙata, aka fara rayuwa a wannan gida Jamila matar Baffa Sunusi da Indo matar Baffa Nuhu suka hadewa Ammi na kai ya zamana ko fitsari a dole Ammi na take fitowa girki kuwa kafin ta gama tayi kuka yakai sau nawa don sun rinƙa kallonta suna zundenta suna mata habaici tare da dariya suna cewa  da ita karuwa matar cushe ko kuma su rinƙa cewa da ita yar cirani kayy har mayyah sunsha ce mata wai kyawun banza kyan ɗan maciji.....

[6/7, 8:29 AM] AM OUM HAIRAN: *_JINKIRIN AURE_*

*_(Ƙalubale ga ƴammata)_*




*By*




*Oum Hairan*




*Dedicated to*

Dr. Mass @gadas son so for ever.




*Free P 7-8*



_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. Shaidar payment ta wannan Link ɗin👇🏼._

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1





Zahiri irin kalaman da suke amfani dasu wajen cusgunawa Adiyyah sunyi tasirin hanata walwala ta rinƙa rama babu dalili wannan ya ɗaga hankalin Alƙasim musamman lokacin da Adiyyah ta samu ciki me laulayin gaske ya kasance komai sai yayi mata kafin ya fita daga gidan hatta da girki.

Wannan ya ƙara rura wutar ƙiyayya tsakanin Adiyyah da matan yayan mijin nata wato faccalolinta ya kasance ko maganarta babu me amsawa Adiyyah zuciyarta me tsarki ce shiyasa wannan yanayi ya dami rayuwarta a haka a daddafe tayi haihuwarta ta fari ta haifi  Yaya Shamsu koda akazo batun zaman biƙi Inna me koko ita ke daukan duk surukanta amma cewa tayi bazata iya wahala mara amfani ba.

Baffana yaji ciwon wannan magana haka ya tafi Yola dangin mahaifiyarsa ya dauko wata dattijuwar ta kula masa da matarsa lokacin da sukayi arba'in tsohuwar ta tafi ya hadɗanta sha tara ta arziki, rayuwa taci gaba da tafiya babu wani daɗi indai kaga Adiyyah na walwala tsakaninta da mijinta ne ko kuma ɗanta, na manta ban faɗa miki ba a wannan lokacin Sunusi da Nuhu basu haihu ba Sunusi nada shekara bakwai da aure Nuhu yanada huɗu ga Alƙasim shekara ɗaya da rabi an sankato masa ɗansa namiji. 





Aifa sai aka ƙara ɗaukar tsana aka ɗorawa Adiyyah da ɗan ta kinsan abin yaro kuma lafiyayye lokacin daya fara rarrafe Adiyyah na can na aiki saidai ta jiyoshi ya canyare da kuka tana fitowa sai taga ko Jamila ko Suwaiba wata ta make mata ɗa haka zata ɗauki abinta tayi ciki dashi ta rarrasheshi, yaron nan har wuta yasa hannunsa Jamila na girki a Madafi amma bata iya hanashi ba, wannan ta wucce wata rana Adiyyah ta shiga wanka tabar Shamsu na bacci a ɗaki ashe tana fita ya tashi ta yayo waje lokaci an siyowa Suwaiba kalanzir zatayi girki a robar swan kawai yaron ya ɗauka ya kyankyaɗa Suwaiba da Jamila suna ɗaki suna kallonshi yanata kakari da fitar da dafara babu wacce ta fito Saida Allah ya jeho Baffanmu ya ga ɗansa a wannan hali ya isa gareshi da gudu shida Baffa Kabir suka ɗaukeshi Baffanmu yana kwalawa Adiyyah kira ta fito a gigice taga halin da ɗanta ke ciki aikuwa ta fasa ihu sukayi waje a guje kafin suje asibiti rai yayi halinsa.





Sosai wannan abu ya girgiza Baffanmu take ya yanke shawarar barin wannan gida aikuwa bayan bakwai ya samu wani gidan haya shi kadai da matarsa suka shiga ciki babu daɗewa kuwa Allah ya ƙara basu rabo ta kuma haihuwar  namiji shine Yaya Mus'ab ɗina da zakiji ina yawan ambato gatana masharin kukana Yayana kuma abokina me share damuwata.

Zakiji yanda akayi ya samu wannan matsayin da darajar a gurina a hankali, 

           Haka rayuwa taci gaba da tafiya shekarar Mus'ab biyu aka haifi Yaya Salees shima shekararsa biyu aka haifi Yaya Khamis sai yaya Aminu, Ni kuwa Saida yaya Aminu ya shekara tara sannan aka haifeni, Zahira haihuwata tazo da wani irin yanayi me gigita tunani domin tun kafin a haifeni komai ya janyewa mahaifinmu Mal Buba ya karɓe duk wani abu da yake nasa a hannun Baffanmu sakamakon sharrin da Sunusi da Nuhu sukayi masa dalilin siyan wani gida da yayi akusa da wanda muke ciki ya haɗe da namu dake dama ya daɗe da siyen wanda ya kama hayar ya gyareshi, bansan wanne tudu wanne gangare akabi aka sauko ba duk wannan yardar da nasamu labari dake tsakanin kakana da Baffana ta gushe ba ya zamana ko gaisheshi Baffanmu yayi baya amsawa rayuwa tayiwa Baffanmu kunci gashi bai iya komai ba sai fatauci ga babu jarin juyawa sannan ga yan' uwansa duk babu wanda zai raɓa yaji daɗi sai Baffa Kabir shikuma shima ba wata power ce dashi ba domin shima yan uwan nasa da suke ciki ɗaya sun barranta kansu dashi saboda yana tare da Baffanmu.





Tun cikina yana wata biyar Baffanmu ya kama wani ciwo ne kama da hauka sakamakon wani hatsari da sukayi shida Baffa Kabir a hanyarsu ta dawowa daga Gwangola, a wancan lokacin babu wadatar na'urorin bincike  sannan su kansu likitocin kwakwalwar sunyi ƙarancin da ba kowa ne yake da halin zuwa ya gansu ba saboda Ammi na ta sanar  dani a wancan lokacin saidai aje Lagos ko Port-Harcourt sannan za'a sami damar duba mutum indai matsala ce data shafi ƙwaƙwalwa don ko likitocinmu na arewa sunce zasuyi ƙarshe sai sun turaka can.

Tun ciwo yana ƙarami haka Ammi da Baffa Kabir sukayita fafutuka suga abin bai girma ba amma abu yaci tura karshe kan Baffanmu ya rinƙa kumbura yana wata irin firgita ko bacci baya iyawa saidai damuwa kullum cikin kuka yake kamar ƙaramin yaro idan an tambayeshi mene sai yace Adiyyah yake tausayawa ranar da baya raye gashi Mus'ab da Salees da Khamis basu kawo ƙarfi ba bare su taimaketa gata ita ba kowa ba a Nigeria idan tace zata koma Ethiopia ma can ɗin ma ba gatane da itaba tunda shima babanta Hakeem a irin yanayi da Baffanmu ya taso shima ya taso gata ita kaɗai kacal ya haifa kamar rai mace yayyanta biyu maza Daga yawon almajiranci basu dawo gida ba har aka auradda ita Tsoho Hakeem ya rasu.





Cikin dare Adiyyah ta fara naƙudar haihuwata har wayewar gari Baffana da baason shigarsa damuwa kuma dama baa cikin lafiya yake ba domin a lokacin kansa yayi na mutum uku lafiyayyu saboda kumburi shine yaketa kaiwa da komowa sai kuma matar Baffa Kabir da tazo tun daren kiran sallar farko yayi daidai da dirowata duniya zuwa lokacin Baffana ba'a barinsa fita shi kaɗai saboda kowanne lokaci yakan iya samun gushewar hayyacinsa ashe ba'a sani ba ya fita a titin sheka anan wata motar yan sanda ta kwankwatse min Baffana!!

Dakatawa tayi tana sharar hawaye sannan ta ɗora da cewa ashe duk sauran ƴan uwana gata suka samu nice ƙaddarata tazo a juye. 

Zahira tunda Baffa Kabir da Yaya Mus'ab dake da shekaru sha bakwai a lokacin suka fahimci Baffanmu ya fice suka bazama nemansa, basuyi nisa ba suka ishe wannan mugun ganin da bayanin wasu mutane dake gurin sanda abin ya faru suka gane shine aikuwa sun shiga tashin hankali, aka ɗauki gawarsa bayan an shigar da duk wani bayani daya kamata aka wucce da ita gida.

Wayyoh wannan rana zo kaga tashin hankalin da Ammi ta shiga sumanta uku har asibiti ta kwanta yau Shikenan ta fito rana mijinta me ƙaunarta da son ganinta cikin walwala wanda yafita sonsa ya ɗauke wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa ga burinsa ya samu ɗiya mace da yake burin ganin ya haifa ashe bazai ganta ba gatan da yake alwashin bata da ilimin da yake burin bata da muradinsa na ganin ta zama likita duk ba tabbatattu bane......





Wannan mutuwa hatta makota ta girgizasu shi kansa Mal Buba ya kaɗu da jin rashin daya tafka ɗansa mai biyayya a garesa da gudun ɓacin ransa Mal Buba yayi kuka har hawayensa sun kafe ya zama na zuci  yana hasaso daren jiya wajen tara yana zaune a tabarma a aljihun zauren gidansa yaji an shigo, yace waye can ya jiyo shassheƙar kukan babban mutum ya taso ya fito yaga ashe Alƙasim ne mamaki ya kamashi yace “Ƙasim meye ya fito dakai yanzu?" Cikin kukan ya durƙusa ya riƙe ƙafarsa yace “Banida lafiya banida hankali Baffa amma hakan bai hanani jin tausayin kaina ba idan na mutu kana fushi dani akan laifin da zargine sharri ne Baffa kaji ƙaina ka tausaya min kace ka yafemin wlh tallahi inajin kamar bazan kai gobe ba...

Duk sanda yazo yanayi masa wannan magiyar sai yakanji kamar ya yayyafa masa fetur ne to jiyan ma abinda ya faru kenan yana masa kuka yana magiya haka Mal Buba ya tsallake ya shige daki ya barshi shidai baisan sanda ya tafi gidansa ba ashe rabuwar ƙarshe ce.

Kuka sosai Buba yayi yana cewa “Na yafe maka Alƙasim wlh nasan bazaka aikata min ba kuma Kabiru ya faɗa min bakada hannu a cikin wannan sata da akayi ƴan fashi ne suka tareku suka kwashe komai.... Wayyoh Alƙasim ka yafemin Nima na yafe maka!" 





Saida ƴaƴansa suka haɗu suka ɗaukesa a gurin aka ɗauki Baffanmu aka kaishi makwancinsa sannan akaci gaba da karɓar gaisuwa, adalci ɗaya da gwamnati tayi mawa su Ammi ta bawa Ammi jari sannan an ɗauki nauyin karatun Yaya Mus'ab da Salees zuwa jami'a hakanan Ammi ranar suna tasa aka Samun Madinatul Munawwara sunan kakata wacce ta haifi Baffa kenan, nan akaci gaba da raino na kyawu na biyu na haɗa na mahaifiyata Ammi da kuma na Kakata  wacce naci sunanta domin itama waɗanda suka santa suna fadin kyawunta asalin bafulatanar Adamawa ce cikin garin Maybalwa.

Kyau yana jawa yaro farin jini matuƙa musamman ni nawa daya haɗu da tsafta nan a unguwar mu aka rinƙa rububi da tururuwar zuwa ɗaukata Deenah shine sunan da ɗan Baffa Kabir ya raɗamin Shikenan Deenah ta bini Babu jituwa tsakanin yayyena da ƴaƴan su Baffa Sunusi amma ta dalilin haihuwata sai ga Khamal Naseer da Hussain dan Baffa Nuhu suna tururuwar zuwa gdanmu Hussain ne me ɗan banzan karambani har ɗaukata yasha yi ya tafi dani gdansu haka iyayensa zasu koromu karshe Suwaiba tace indai ya ƙara dauko mata wannan aljanar yarinyar irin tsiya da jaraba saita sa an yankashi.

Dake ba wani girma yayi sosai ba haka ya hƙr ya barni saidai yazo gdanmu yayita yimin wasa sai yamma ya tafi, soyyayarsa gareni yasa Ya'ya Mus'ab ɗaga masa ƙafa.





Inada saurin girma kamar kazar gidan gona shekara ta biyu aka sani a makaranta da yake wayona yafi na shekaru na saiya zamana a makarantar ma na samu karɓuwa matuƙa da gaske ina karatuna shaƙuwata da Hamma Hussain na ƙara shiga jikina da koyamin damuwa dashi har takai duk ranar da Banga Hamma Hussain ba bana samun nutsuwa, 

Saida takai duk masifar Suwaiba da  Baffa Nuhu Saida suka sallama lamarin Hamma Hussain gareni, ya garace yaje makaranta a dake shi daya tafi da wuri bai ganni ba.

Inada shekara goma na gama firamare lokacin Yaya Mus'ab ya gama jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya ya dawo gida gadai kwalin amma babu aikin yi dake akwaishi da zuciyar nema haka zai ta buga-bugarsa shine gini shine dako duk don ya samo mana abinda zamuci shida Yaya Salees da wannan suka samamin secondary na ɗora itama ta kuɗi ce kuɗi sosai nake kwasa a wannan makaranta da nakeyi daɗinta dake ba asarar kudin akeyi ba ina  kwashewa.

Inada shekara sha huɗu wata rana muna zaune a tsakar gida nayi matashin kai da cinyar Hamma Hussain yanamin tsifa a lokacin shi kuma yana karatunsa a Bayero University Kano, hira sukeyi suna tattaunawa akan irin wahalar da Baffanmu yasha nan Hamma Hussain yake cewa ai wani lakcaransu yayi musu bayanin yanda ciwon yake samuwa matsalar jijiyoyin ƙwaƙwalwa ne" 





Nan na fara tambayarsa abinda ya shafi ciwukan da suka shafi ƙwaƙwalwa dake yana bawa duk abinda ya shafeni muhimmanci ya zauna yanamin bayanin abubuwan daya sani a matsayinsa na ɗaliban ilimi nan take naji inada soyayyar karantar bangaren kodon na gano yanda za'a magance ciwon daya zama sanadin kashemin mahaifina da kuma wani yaro a maƙotanmu me suna Hashim da shima akace tun wani hatsarin mota da akayi dashi yana ƙarami ya samu wannan matsalar. 

Ina tashi na zura da gudu Hamma Hussain ya bini ban zame ko inaba sai gdansu Hashim, Hashim ya girmeni a haife amma yanayin lalura yasa yake abubuwa kamar yaro ƙarami nan na kama hannunsa muka zauna nace masa “Aboki nice zanyi maka maganin ciwonka zakaji sauƙi zaka warke ka koma kamarni kamar Hamma Hussain" dukkansu waɗanda suke gurin kama daga babar Aboki Hajiya Sakina da kuma Babansa Alh Musa da kuma yayyensa suka kama yimin dariya Hamma Hussain da Yaya Mus'ab sune kawai suka zubamin idanu sun sani a rayuwata banson dariya hakan yasa ina ɗagowa Hamma Hussain yayi sauri cewa “Hakane Dr. Deenah Matar Dr. Hussein insha Allahu saikin zamo silar warakar Aboki" ..........

[6/7, 8:29 AM] AM OUM HAIRAN: *_JINKIRIN AURE_*

*_(Ƙalubale ga ƴammata)_*




*By*




*Oum Hairan*




*Dedicated to*

Dr. Mass @gadas son so for ever.




*Free P 9-10*



_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. Shaidar payment ta wannan Link ɗin👇🏼._

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1





 Tsalle nayi na faɗa jikin Hamma Hussain ina dariya ya ɗagani muka fita duk da shekaruna sun fara nauyi ina da kusan 15 years Amma har yanzu ban girma da ɗauka gurin Hamma Hussain ba baya gajiya da hidima dani baya gajiya da wahaltamin baya gajiya da jiɓantar al'amura na.

Muna rayuwa da taimakon Ubangiji dayake kawo mana ɗauki cikin nasara Yaya Mus'ab ya samu aikin campany ya fara shikuma Yaya Salees yaci gaba da buga-bugarsa shine acaɓa shine kwandastan mota ita kuma Ammi takanyi funkaso da safe da rana kuma tayi lemon  ginger da kunun aya haka Allah ya rinƙa tallafarmu munaci gaba da rayuwa cikin ƙaramin yanayi Ni da yayye ba biyu muna karatunmu wani lokacin kudin school fees ɗinma sai anyi kamar anayi kafin asamu a biya.

Zahira a mafi yawan lokuta ma Hamma Hussain shine yake biyamin kuɗin makarantar, shekarata sha bakwai na gama secondary A wannan lokaci idan kika kalleni zakice nayi shekaru ashirin da biyu saboda cikar zati na da halitta ta.





Tabbas na amince Zahira ni babbar yarinya ce matar manya a hankali mukayi wata shaƙuwa da ta rinƙa rikiɗa tana zama soyayya amma a ɓangaren Hamma Hussain nikam bantaɓa jin so na soyayya tsakanina da Hamma ba saidai kawai nasan duk cikin ƴan uwana inajin Hamma Hussain a raina fiye da kowa.

Lokaci da zamuyi candy Hamma Hussain ya kashemin kudi bana wasa ba domin a lokacin ya gama karatunsa dake zuwa wannan gaɓa Allah ya ɗaga mahaifinsa da Baffa Sunusi sun shiga harkar siyasa gadan-gadan wannan tasa baisha wahalar samun aiki ba, kuma baya ƙyashin kashemin ko nawa ne ga Yaya Mus'ab shima komai ya samo Deenah komai ya shigo hannunsa nawa ne wannan tasa na zama ƴar gata  abu guda ɗaya yanzu daya kutso cikin rayuwa shine masifar son karatun likitanci kamar yanda naci buri itakuma Ammi tunda na taso taga yanda nake girma kamar kazar gidan gona bata da burin daya wucce taga ta auradda Ni.





Muna zaman jiran jarabawa Kusanci na da Hamma Hussain yana ƙara ƙarfi duk dangi kowa yana kallon mu matsayin masoya Mal Buba shine ya shiga cikin maganar dakansa yasa aka kira Baffa Nuhu akan maganata da Hussein tashin farko abinda Baffa Nuhu yace ya girgiza Ammi na sanda taji wai Baffa Nuhu ne yace shi indai shine ya haifi Husain to bai amince masa aure na ba harma da ƙarin cewa shi ai baima yarda muɗin halattatun ƴaƴa bane don har Ethiopia yaje ba'a nuna masa limamin daya ɗaura mawa Baffanmu da Ammi aure ba.

Tun daga wannan lokaci aka jingine maganar auren to dama dake ba wani damuna maganar tayi ba haka naci gaba da harkokina ranar da jarabawarmu ta fito Hamma Hussain ne yaje ya dubo min yazo da murnarsa jarabawa tayi kyau na samu duk abinda ake buƙata ranar Ya Mus'ab har goyani yayi saboda murna ya tsugunna gabana yace “Uktee me kikeso yanzu bayan fitowar jarabawarki?" A dan ɗarare saboda Ammi bata bani da sauƙi idan nace mata karatu nakeso nace masa.

“Hamma Mus'ab don Allah kar ku watsawa muradina ƙasa kune kukace shine burin Baffanmu akaina koda baya raye zaku iya cika masa burinsa, inason nayi karatu burina shine na zama likitar ƙwaƙwalwa please Ya Mus'ab....." 

Ɗaukeni naji anyi da marin da Saida bakina ya fashe Ammi tace “Karatun ubanki zakiyi Munau Ni kwadantaki zanyi inci da zansaki a gaba in kalla Mus'ab na faɗa maka ka daina biyewa shirmen yarinyar nan....." 





Cikin sanyin jiki Yaya Mus'ab ya ɗago yace “Ba haka bane Ammi yawanci tunanin yaro shine nasararsa Kinga yanzu kece da kanki kikace mubar maganar auren Hussain da Madinah to me zamuyi da ita Ammi babu amfani zaman Madinah a gida gara ta tafi makarantar wala Allah karatun shine alkhairin rayuwarta  kuma ai karatu baya hana aure tana karatun ta idan Allah ya kawo mijin sai tayi aurenta"

Barin gurin Ammi tayi Yaya Mus'ab yabita nikuma na nufi ɗakina nasa tisue na goge bakina ina tunanin idan Ammi taƙi amincewa da muradina ya zanyi Allah ya sani ina matuƙar son karatu bazan iya hƙr da karatun ba,  na kusan raba dare ina juyi ranar ko islamiyyarmu ta dare banje ba har na saduda na haƙura da lamarin karatun amma kullum raina a kunci yake banida sakewa damuwa ta aure ni gashi Hamma Hussain ya daina zuwa zuwa gdanmu Baba Suwaiba da Baffa Nuhu sunce idan bai hƙr daniba zasu cireshi cikin jerin yaransu.

A zahiri ya nuna musu ya haƙura saidai a bayan fage yanata yimin hidima  adashi Yaya Mus'ab ya ɗauka a gurin aikinsu yaje ya yankarmin Form na Jamb bansan anayi ba sai saura sati ɗaya za'ayi jarabawar na samu labari murna a gurina kamar anyimin Hajj da Umrah lokacin jarabawa yayi muka zana cikin kokwanto ko mu dace ko mu faɗi tunda mun riga mun san halin ƙasar mu, bayan kammalawa muka dawo sati kaɗan Jamb ta fito komai na cikin nasara na samu abinda kowanne dalubi yake nema, nan aka shiga fafutukar yanda za'ayi a biyamin kuɗin jarabawa a Jami'ar Adamawa aka samamin admission Yaya Mus'ab yasai da machine ɗinsa da system dinsa ya gamamin komai dakansa yakaini makaranta ya kamamin hostel muka fara rayuwar karatu da ɗalubai yan'uwana anan muka haɗu dake in baki manta ba.





Tun a wancan lokacin kyawu na yake firgitani kinsan meye yasa kyawuna yake firgitani? Tunda na taso na mallaki hankalin kaina bayan Hamma Hussain babu wani namiji daya taɓa kallona ya furtamin kalmar nan me tsada a gurina kuma me arha a gurin ƴammatan da suka amsa sunan su mata musamman kyawawa kamata.

Zahira kinsani tun a wancan lokacin Ni dake zamu fito daga makaranta za'a ganmu tare a tsaya ace ana sonki saidai Ni bantaɓa samun wannan gatan ba muna wannan rayuwar kikayi aure kika auri Daddyn Noor har muka gama makaranta mukayi duk abinda ya dace muka dawo garinmu kikaci gaba da rayuwa a gidan mijinki nikuma naci gaba da rayuwata tare da mahaifiyata da ƴan uwana.






A wannan ƙadamin ne kuma idanun jama'a yayo kaina musamman da naje karatu na dawo su Baffa Sunusi sune suka fara buɗe fagen da cewa Ammi ta mayar dani karuwa taki barni bayi aure saboda tana morar kyauna tana samun abin lasawa.

Wannan maganganu sune suka rinƙa tunzura zuciyar Ammi takan cemin Munau ki hƙr da makarantar nan tunda kin samu abinda kika samu kiyi aure ko dangin mahaifinki sa daina zagina da ganin laifina" a duk lokacin da tayimin wannan bayanin nakanyi dariya nace “Ammi kenan duk fa wanda ya zageki haƙƙi ya rage Miki tunda kinsan baki aikata abinda suke zarginki dashi ba kuma ma Ammi shi aure ai mutum biyu akeyinsa Ni kinganni fah wlh tunda na taso babu wanda ya taɓa cewa yana sona shima Hamma Hussain da kuke gani wlh bakina da nasa baitaɓa kallona yacemin Deenah inasonki ba kawai abu daya dana sani zanyi aure idan lokacinsa yayi, kiyi hƙr Ammi banason zaman banza shiyasa kikaji muna zancen juyawata karatu tunda mijin auren baizo ba" 

Jinjina kai Ammi tayi tace “Shikenan Munau Allah ya taimaka ya kawo miji na gari" amsawa nayi da Amin na tashi na ɗauki handbag ɗina dana aje na shige ɗakina na cire kayana na fito na shiga bayi na watsa ruwa na sanya kayan bacci naci abinci na kwanta Zuciyata cunkushe da tunanin ta inda zan fara neman abokin rayuwa raita tana faɗamin to nayiwa Hamma Hussain magana mana aikuwa na daga waya na kirashi ya dagamin babu wani jinkiri kamar yanda na saba nace “Hamma!" Numfashi ya sauke yace “Na'am Ɓingel" yanayin yanda naji muryarsa yasa gabana faɗuwa sai nayi shiru da furta ƙudurina har Saida naji yace “Deenah meye yake faruwa ne yau na yini zirga-zirga akan sharafin karatunki harma an gama komai zaki fara karatu a Skyline university dake nan Kano makarantar tanada kwararrun malamai shiyasa na zaɓa Miki ita kuma shi kinsan wannan ɓangaren da kika ɗauka bangare ne me wahala harkar ƙwaƙwalwa har tafi ta zuciya wahala shiyasa naga gara ayi abin da gaske, to alhmdllh dake Ɓingel ɗin tawa akwai kwazo result ɗinki ya tsallake harma ya zarce kin sami gurbin karatu a cikinta saidai matsalar kuɗi amma karki damu zanji da komai tunda mun gama magana da Yaya Mus'ab komai zai yiwu da yardar Allah"





Numfashi na sauke cikin raunin murya nace “Hamma Ni na hƙr da karatun Ammi aure takeso taga nayi saboda maganganun da aketayi akaina, Hamma kawai muyi aure idan da rabon nayi karatun nayi a gaba...." Wannan magana dana faɗa masa ba ƙaramin jefashi a tashin hankali nayi ba ashe abinda yake addabar zuciyarsa kenan shiyasa farkon kirana naji kamar bashida lfy.

Numfashi ya sauke cikin son kwantar min da hankali yace “Kullum shine burina Deenah karki damu lokacin ya kusa insha Allahu gobe kafin na tafi aiki zanzo gidan muyi magana da Ammi"

Haka mukayi sallama ko babu komi na ɗan samu nutsuwa inaji a raina nakai kukana inda za'a sharemin hawaye, kamar yanda ya alƙawarta min da safe kafin in tashi yazo gdanmu shine ya tasheni da tausasan yatsunsa da naji suna yawo a fuskata yana huramin iskar bakinsa na buɗe ido ina miƙa na manta a yanayin da nake ciki, ya kuwa kafeni da idanunsa ina sauke nawa akansa ai ban gama sauke idona akansa ba na yayumo bedsheet ɗin na rufe jikina ina cewa.

“Wayyoh Oh God sorry please Hamma...." Lumshe idanunsa yayi ya kwantar da kansa jikin bango yana sauke wani wahalallen numfashi na figo hijjab ɗina nasa na miƙe zan bar gurin ya riƙoni na faɗo jikinsa ya saukemin hucin numfashinsa a saitin fuskata a wahale yace “Harda ƙwalele Deenah meye yasa kikeson tsokanata da jikinki wlh kina cutar dani shiyasa na ɗauki matakin ƙaurace Miki saboda banason ayi abin kunya"

[6/8, 2:55 PM] AM OUM HAIRAN: _*JINKIRIN AURE!!!*_

_(Ƙalubale ga ƴammata)_


OUM HAIRAN



Free P 11-12




_Paid book Nrml 300 Vip 500 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1




Zamewa nayi a jikinsa na nufi hanyar da zata sadani da tsakar gidan na ɗauki buta tare da shiga kitchen na tsiyayo ruwan dumi na nufi bayi na watsa ruwa na fito sanye da hijjab dina ina goge jikina da towel na ishesu shida Yaya Mus'ab da Hamma Khamis suna tattaunawa a karshen maganar naji Hamma Khamis yace “Hussain kaje kayi biyayya ga umarnin Mahaifanka itama insha Allahu zata samu alkhairinta munsani kaso Madinah tun tana tsumman goyo ka jiɓanci lamuranta to ba daga kai bane muma badaga mu bane laifin iyayenka ne da suka kasa yima rayuwarka adalci munayi maka fatan alkhairi idan Ɓingel rabonka ce zaka ɗauka Allah shaida banawa Ɓingel sha'awar rayuwa da wani bakai ba domin kai kafi kowa sanin ciwonta"





Jikina ne yayi sanyi Zuciyata tayi ƙunci na koma na zauna sharaf a ƙasa kaina na juyawa na fara tuhumar kaina to meye kenan abin nufin su Hamma Khamis da Hamma Hussain da naji suna tattaunawa?" Banida me bani amsa shiyasa jikina a kasalce na tashi na ɗauki doguwar riga na saka na kwanta nayi likimo bisa katifa ta lokaci zuwa lokaci tunanin ta yanda zan fara shirin wanke zuciyar Ammi na karo na farko yana bijiro min.

Zahira a mind ɗina ƙulafucin karatun boko ya zauna banajin shauƙin son aure saboda ina ganinsa kamar wata katanga ga cikar muradi na, nasani auren zamani ya zamana bana aure baɗi ganda inji Hausawa da yawa ma baa kaiwa baɗin so ina me tunanin zama likitar ƙwaƙwalwa kwararriya ta ƙasa da ƙasa ina batun ɗorawa kanta damuwar iyali?

Wannan gajeran tunanin ne a baya yaki barin Zuciyata kwadaita da samun abokin rayuwa sai a wannan karon da naga Ammi na ta damu Nima saina damu da damuwarta amma ta banza, nidai banji wani bayani ta wajen Hamma Hussain ba in munyi waya kawai labarin cigaban da aka samu ta wajen shirye-shiryen karatuna kawai yake bani.





A wajen Yaya Mus'ab nake samun labarin Hajiya Suwaiba ce tayi rantsuwar muddin ya ƙara furta yana son aurena saita tsine masa kuma tayi masa mata a Gwangola, bansan Zuciyata ta shaƙu da Hamma Hussain ba Saida naji wannan baƙin labari aikuwa ranar nayi kuka kamar zan kashe idanuna daga karshe dai na fawwalawa Allah komai tare da cin alwashin Nima a wannan karon na hƙr da Hamma Hussain badon banjinsa a raina ba saidon inaso ya gama da iyayensa lafiya.

Banci wata biyu ba komai na karatuna ya kammala Yaya Mus'ab yasai da kangonsa daya fara ginawa shikuma Hamma Hussain ya siyar da filinsa suka yimin komai har ɗinki suka ƙaramin na fara zuwa makaranta, A Skyline naga rayuwa da ƴaƴan manya masu damawa a ƙasa Ni kuwa a matsayina ta ƴar Mal Shehu saina kame kaina na fita harkar kowa sai wanda ya shiga tawa abin daya rinƙa bani mamaki mazan da muke karatu dasu sunason yimin magana amma bansani ba kwarjini nakeyi musu basa iyawa saidai idan nice nayiwa mutum magana zakiga har wani happy yakeyi, Nasha jin sunan da suke kirana dashi wanda suka sameshi a bakin wani malamin mu me suna professor Suzan shine mutum na farko daya fara kirana da First Lady Shikenan suka samu suma, mata kuwa kowa so take ace tanada kusanci dani amma Ni naja na janye saboda dukkansu ƴaƴan ƙusoshin gwamnati ne sai yaran manyan yan kasuwa banason raini wannan tasa naƙi basu fuska saidai gaisuwa.






Shekara kwana Zahira sai gashi karatuna ya taho gangara zuwa wannan lokaci damuwa ta fara aurata don nima kuma lamarin na daina ɗaukarsa me sauki inada shekara 25 a duniya ga ilimin addini ga na zamani gashi har an samu wani asibiti babba me zaman kansa sun ɗaukeni aiki da babban matsayi da babban albashi amma kullum lalurata ƙaruwa takeyi takai yanzu idan na shiga taron maza sai kiga duk sunyi ƙasa dakai suna cemin “ranki ya daɗe Allah ya taimake ki" ko kuma kiji suna First Lady meye kike bukata? Zahira shekarun bukatuwa ta ga ɗa namiji sun danno yanzu ba karatu ba ba aiki ba ba girmamawa ba abokin rayuwa kawai nake nema amma na kasa samu, wannan tasa na rinƙa ramewa gashi yanzu a unguwar mu duk majalissar da kika wucce labarin Dr Deenah akeyi wasu suce nayi baƙin jini na rasa mashinshini wasu suce burin duniya ambarni na ganɗame idona ya buɗe nakasa fitar da miji saboda ina kallon kyauna da ilimina na tsaya jiran tsammani, wasu kuma suce karuwanci nakeyi shiyasa naƙi aure an fake da guzuma ana Harbin karsana.





Maganganu dai kala-kala har waɗanda baki bazai maimaita ba, inanan a haka ina aikina saboda surutun mutane Yaya Mus'ab yasa muka Saida gidanmu kuma munyi Sa'a yayi daraja sosai saboda campanyn MTN ne suka siya zasu kafa service a gurin muka matsa gaba mukasai ginanne harma da ƙarin fili babba shine wanda muka zagaye muke saka shirgin da bazai shiga gida ba a ciki, ana haka Bikin Hamma Hussain ya taso dake na cireshi a raina ban wani damu ba akasha biki nayi masa gudunmawa ta ban mamaki naje har wajen dinner ɗin ashe rabon yiwa kaina tambarin ƙaddara ne ya kaini.

Ina zaune a kujerata Ni kaɗai na wanku idanun kowa a kaina ƙannensa da kuma sauran yaran dangin mahaifina sunata yasar min da magana lokaci zuwa lokaci ina ɗauke ƙwallah da tisue ta gefen farin medical ɗina naji an taɓa table ɗin na ɗago idanuna na saukesu kan Hamma Hussain tsaye a gabana Saida gabana ya faɗi da irin kallon da yakemin na yunƙura na tashi da son aro juriya nace “Hamma dama kai nake jira duk na gundura da zaman kaɗaici" ina maganar ina zuge jakata na dauko wani dan ƙaramin akwati na kama hannunsa na zare masa zobe da agogon dake ɗaure a hannunsa na dauko na cikin akwatin na ɗaura masa ina tsaka da sanya masa zoben naji ɗumi ta dokin wuyana na dago da sauri ashe hawayen Hamma Hussain ne suka huda mayafina suka ratsa jikina





Da sauri na dafe kaina nace “Hamma ya haka yau fah ranar farin cikinka ce meye yasa zaka ɓatawa kanka wannan lokacin me girma....?" Rufemin baki yayi yace “Sheeet please Ɓingel muje ki rakani wani guri" zaro idanu nayi nace “Ni Hamma ina? Dare fah yayi kaga goma ta kusa"

Cije leɓensa yayi yace “shikenan tare da juyawa na riƙo hannunsa da sauri nace “Aa ba haka nake nufi ba muje na rakaka...." Juyowa yayi ya  dafa kaina yace “Ranki baiso ba Ɓingel jeki gida kawai" 

Girgiza kai tayi tace “Ba haka bane Hamma...." Ganin idanuna ya kawo ruwa yasashi yin gaba nabi bayansa ashe duk wannan abin da mukayi kan idanun Hajiya Suwaiba, jikin motarsa muka tsaya ya zubamin idanu mun jima tsaye gabana yana faɗuwa shi kuma bazan iya cewa ga abinda yake tunani ba ya buɗe min mota zuciyata babu tunanin komi na shiga shima ya shiga yayiwa motar key muka bar Event center ɗin munyi tafiya me ɗan tsayi sannan yayi parking ya kwantar da kansa jikin kujera yana fitar da wani irin numfashi da bansan dame zan kwatantashi ba.




Can a sama na tsinkayo muryarsa yana cewa “Inajin zuciyata kamar baa jikina take ba tanayimin nauyi tanamin ciwo kamar zata fito a ƙirjina Madinah wanne magani zamu bawa kanmu don ragewa kanmu raɗaɗi tunda kowa ya kasa fahimtar halin da zukatanmu suke ciki?" 

Da rashin fahimta na ɗago idanuna na zubashi akansa nace “Kamar ya fah?" Ɗagowa yayi yasa hannu ya kamo hannuna ya murza tsakiyar hannuna da ƙarfi, karon farko da naji wani abu ya game jikina wanda ya fara tasowa daga tsakiyar kaina, na motsa sa niyyar kwace hannuna maimakon ya sakarmin hannun sai ya janyoni na shiga jikinsa sosai yasa hannunsa biyu ya matseni, faduwar gabana ta tsananta ba baƙuwa ce ni a shiga jikin Hamma Hussain ba amma yanayin na yau baƙone a wajena wani tsoro ya shigeni jin yanda jikinsa ke wata irin kaɗawa kamar yanajin sanyi, ƙamshin turarensa yana ƙara hautsina min lissafi.

Banyi aune ba naji numfashina yana ɗaɗɗaukewa ashe bakina ya jorner a nasa na kuwa datse haƙorana da ƙarfi cikin tsoro da firgici na shigar sabon yanayi, duk yanda naso na ƙwaci kaina na kasa sai kawai na rushe masa da kuka muka rinƙa kokawa dashi yanason dole saiya ciremin mayafin jikina nikuma naƙi bashi dama yakai hannunsa ƙirjina ya cafka kenan nayi wani kukan kura na Angajeshi nakai hannu na buɗe motar ko handbag ɗina ban ɗauka ba na kwasa da gudu shikam bai iya fitowa a motar ba saboda wahalar yanayin dana gudu na barshi aciki.





Inacin uban gudu Allah ya haɗani da me napep na tare na shiga na faɗa masa inda zai kaini har zuwa lokacin ƙirjina harbawa yakeyi da ƙarfi  a kofar gida na tarar da Yaya Salees ya zubamin idanu gabaɗaya yanayina baiyi masa ba ya tako ya kama hannuna yace “Ɓingel yadai" da yanayi na rashin gaskiya nace “Yaya bashi kuɗinsa handbag ɗina aka sacemin a gurin dinner" 

Bayan haka bance masa komai ba nayi gaba ina shiga na kullo ƙofata Zuciyata wani irin bugu take badawa me ban tsoro Ni kaina Saida na firgita da yanayin bugunta hakan na zame a gurin na ɗora kaina saman katifa na rushe da wani kuka me ciwo, abinda bantaɓa tunani ba a gurin wanda bantaɓa tunani ba Hamma Hussain..... 

Hamma Hussain shine da farautar mutunci na? Dama hakan zata yiwu mutumin da kullum yakemin nasihar na kula da kaina mutuncina shine ƙimata yau shine yayi ƙoƙarin rabani da mutuncin nawa? To kodai shima zargina yakeyi da nasan komai kamar yanda da yawa suke ɗauka?? Banida amsa hakan na zame na kwanta raita tanamin wani irin ciwo ranar nayi kukan da bantaɓa yin irinsa ba kuka biyu na rashin madafa da kuma na ciwon abinda Hamma Hussain yayimin, da wannan bacci ya ɗaukeni ko a baccin firgita na rinƙa yi saboda da gssken gaske na razana da yanayin Hamma Hussain nasani addu'a ce kawai ta kuɓutar dani ba karfina ba ba iyawa ta ba.






Ina kwance bankai ga tashi ba da safe naji hayaniya a tsakar gida Muryar Zakiyya da Hajiya Suwaiba sune suka sanyani miƙewa dagani sai rigar bacci a jikina na nufo kofa na tsinkayo Muryar Hajiya Suwaiba tana cewa “Ai dama bazaku amince ba amma ai munada shaida meye ya kawo jakarta da wayarta ɗakinsa idan ba ita bace tayi masa wannan aika²r a gabana fa ta hilaceshi suka fito daga Event center sannan na koma gida na tarar dashi an caka masa wuka a ƙirji an kuma caka masa a gefen ciki wlh tallahi babu abinda zaisa mu yarda Dole taje tayiwa jami'an tsaro bayani idan kuwa dana ya mutu to itama saita bisa"





Da sauri na fito daga dakin na tsaya ina kallon kowa kawai sai naga Ammi ta juya ta shige ɗaki na juya ga Hamma Khamis naga yayi ƙasa da kansa Yaya Mus'ab ne kawai ya Matso gareni ya yayumo hijjab saman igiya yasamin yace “Ya akayi haka My Deenah garin yaya kika aikata wannan mummunan aikin?" Cikin alamu na rashin fahimta nace “Meye yake faruwa ne?" Nan Suwaiba tayo kaina tana cewa “Azzaluma maci amanar ƙauna kin cucemu Madinah kuma saikin girbi abinda kika shuka ashe dana rabaki da ɗana na haramta masa aurenki kyace ya rayu mu gani wlh bazan yafe ba sai anbimin jinin ɗana....." Har yanzu ban fahimta ba Saida jami'ar tsaron ta nufoni da sarƙa a hannunta zata sanya min Yaya Mus'ab ya dakatar da ita yace “Wlh tallahi Madinah bata aikata abinda kuke zarginta ba don haka daganan babu inda zata indai ba gurin aikinta ba haba wannan ma ai haukane kawai don anga jakarta da wayarta a ɗakinsa sai ya zama kuma ita ce ta nemi kashe shi idan so kuke ku tabbatar ku bari ya dawo hayyacinsa mana shi ai zai iya bada shaidar waye makashinsa tunda dai bai mutu ba"





Shigowar Mal Buba da Baffa Kabir ne yasamu mayar da hankalinmu garesu bandani da hawaye yake tsiyaya a fuskata kamar famfo Mal Buba yace “Daga gurin Hussaini muke yanzu haka ya tabbatar mana da ba Madinah ce ta aikata masa wannan ta'addanci ba maza ne su biyu da baisan su waye ba amma yana zargin na gdane........




PAID BOOK

_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. '

Ko MTN card ta wannan number 09013 718241.

[6/10, 4:21 PM] AM OUM HAIRAN: _*JINKIRIN AURE!!!*_

_(Ƙalubale ga ƴammata)_


OUM HAIRAN



Free P 13-14




_Paid book Nrml 300 Vip 500 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1




 Ajiyar zuciya me ƙarfi Madinah ta saki ta juya ta koma ciki zuciyarta na tafasa ranta na suya wai kamar ita duk kusancinta da Hamma Hussain zaace itane taje ta farmaki rayuwarsa, hawaye ta sharce ta juya ta tsaya jikin window tace “Banso furta Miki komi ba amma furucinki na ƙarshe yasa naji inason na fahimtar dake duk da nasan ko kin fahimta girman kai da duhun zuciyarku na ƙiyayyar Zuri'ar Alƙasim bazata bari ki yarda kin fahimta ba.

Mama Suwaiba ba kamar yanda kike tunani bane eh tabbas hakanne abinda idanunki ya gani naje dinner Bikin Bilkisu da Hamma Hussain badon kaina ba sai domin Hamma na, shine ya rokeni alfarmar zuwa gurin taron domin a cewarsa zuwana zai bashi ƙarfin gwiwar gudanar da komai da ƙwarin gwiwa, banso tafiya ni daya ba yanayi yasani dole nayi hakan don wacce zan gayyata tayimin rakiya tana dutyn dare, kuma ba gaskiya bane kalaminki na cewar na yaudareshi na fitar dashi shine yayi amfani da girman darajarsa a gurina ya fitar dani abinda ya faru har yasa na bar masa jakata da wayata wannan kuma sirrinmu ne ni dashi saboda yanada ƙimar da bazan iya fadin komi game dashi ba, wannan shine gskyr abinda ya faru tsakanina dashi, waye ya farmakeshi har ya yanke shi wannan bansani saboda haka Allah ya sakawa mahaifiyata ɗaga mata hankalin da kukayi da wannan nake cewa indai babu kason tsoho da tsohuwa a gidanmu a fice mana daga cikinsa....."





Dafe kuncina nayi da sauri na ɗago idanuna suka sauka cikin na Ammi ta nunani da yatsa tace “Mamanku Suwaiba ba sa'ar yinki bace ki kame bakinki banason rashin kunya bazamu daidaita ba"

Zuciyata a jagule na koma na zauna kan katifa ta ina share hawaye duk da sosai Maganganun mahaifiyar Hamma Hussain sun taɓa ƙoƙon raina amma Zuciyata cike take da son sanin halin da Hamma na yake ciki, yinin ranar sukuku haka nayisa sai dare na fita a gida na tafi gurin aiki kasancewar night duty ne dani, ko a wajen aikin banida walwala sosai  da  safe dana tashi daga aiki raina bai yarjemin wuccewa gda ba Saida na kira Yaya Mus'ab na tambayeshi asibitin da aka kwantar da Hamma Hussain ya faɗa min na ƙarasa gabana yana faɗuwa nurse ɗin suna mutuntani don niɗin ba ɓoyayya bace a asibitin kasancewar nayi wani practical acan, nan na tsmbayesu ɗakin suka rakani na buɗe na shiga da sallamata gabana ya faɗi ganin Hamma Jabir ne a zaune shida Hamma Khamal.






Muka gaisa dasu a ƙagauce kallon da Hamma Jabir keyimin yana damuna na ƙarasa wajen Hamma na riƙo hannunsa tare da shafa kwantacciyar sumarsa nace masa “Ina fatan mijina yanajin sauki?" Shaƙar ƙamshi na dake kashe masa jiki a koda yaushe da kuma jin dirin saukar sautina a dukkan jikinsa yasashi buɗe idanunsa akaina tar yanamin wani kallo na tsantsar ƙauna da tausayin kai.

Raɓawa nayi na zauna a kusa dashi na ɗauki hannu na nakai ƙirjinsa da yake naɗe da bandejin daya ɓaci da ruwan ciwon me haɗe da jini na ɗago na dubeshi cikin tsananin tausayi nace “Sannu Hammana tun jiya raita taƙi sakewa inajin tsoron yanayin da zan tarar dakai shiyasa banzo ba ina fatan banyi laifi ba?" Dagamin kai yayi  nayi murmushi na fara kwance ɗaurin na dauko akwatin dake aje a gefe nasa almakashi na rinƙa yanke masa a hankali ina cire bandejin har naje ƙarshe na sanya safa na cire audugar ya ɗan saki siririyar ƙara nayi saurin ɗora bakina a nasa nayi kissing nasa nace “Haba Dr Mijin Dr. Ba girmanmu bane"





Ina maganar ina sa Spirit ina wanke masa ciwon yana ɗan ciccijewa ina zuba masa sannu har na gama da taimakon wata nurse da tazo take tayani bayan na gama na gyara na cikin nasa shima tare da ɗaukar katin na duba magungunan na sake rubuta wasu a ƙasa na juya na miƙawa Hamma Khamal daya kafeni da idanunsa jajaye da suke firgitani, na buɗe baki zanyi magana yace.

“Madinah ko kinsan nafi wannan yaron dacewa da samunki?....." Ɗaga masa hannu nayi nace “Please adanasu zasuyi maka rana wadannan magungunan nakeso aje a kawomin yanzu" cije leɓe yayi batare daya karɓi katin ba sai Hamma Jabir ne ya karɓa na zaro kuɗi a jakata na basa ya dubeni yayi murmushi ya fice batare daya karɓi kudin ba.

Ban wani damu ba na koma na zauna kusa da Hamma Hussain nace “Hammana kaci abinci?" Girgiza min kai yayi nayi ajiyar zuciya na tashi na cire rigar aikina ya rage dagani sai yar body hug da sikert ɗinta na matsa ga tea flast ɗin na haɗa masa tea me kauri na tasheshi da taimakawar Hamma Jabir daya dawo daga siyo maganin muka jinginar dashi na rinƙa bashi Hamma Jabir yana cewa.

“Ikon Allah Sis Deenah keɗin ƴar baiwa ce ba mu ba har amaryarsa Saida tazo asibitin nan akan ya samu yaci wani abu yaƙi Kinga dake kece ya karɓa" 





Budar bakin Hamma Khamal sai cewa yayi “To kai Kanada abin bashi ne koko ka iya karuwanci ne da zakayi tunanin zai karɓa daga gareka?" Ciwo matuƙa kalaman Khamal sunyi min amma saina shanye naci gaba da abinda nakeyi Shiko Hamma Hussain kallona kawai yake yi lokaci zuwa lokaci yana tsane hawaye a idanunsa, a haka Hajiya Suwaiba Mama Jamila da Bilkisu amaryar Hamma suka zo suka ishe mu hankalina ya tafi wajen kula da Hamma banji shigowarsu ba sai ihun Hajiya Suwaiba naji tana cewa “Yau Ni Asalamiyya naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, Jamila anya yarinyar nan ba mayya bace kiga burinta na kashemin ɗa bai cika ba ta kuma biyosa asibiti don wani kiɗifere da munafurci har wai itane ke kula dashi, to kinsan zaki kula dashi ɗin meyesa kika nemi kasheshi haushin ba'a samu ba?" 

A zahirin gaskiya nutso a duniyar ilimi tasa ba kowacce magana nakeda lokacin tankata ba wannan tasa nayi kunnen uwar shegu da Hajiya Suwaiba da muƙarrabanta sunata subaɗaɗinsu abu ɗaya da nayi bayan na gama kula da Hamma na nayi shirin tafiya shine na sunkuya daidai kuncinsa nayi masa kiss na kusan thirty seconds sannan na janye na ɗauki hannunsa na ɗora a ƙirjina saitin Zuciyata nace “Kaji a ranka Dr. Madinah taka ce da yardar Allah Hammana indai gidanka da gurbin mata to komai nisan zamani zaka sameni badon fitinanniyar soyayya ba a'a saidon halacci" 






Da sauri na fice daga ɗakin nabar Bilkisu shanye da baki tana bina da wani mugun kallo ita da uwar mijinta nikuwa ina fita na tsare ɗan sahu na hau na nufi gda koda naje gidan ban wani bata lokaci ba na hau shirin tafiyata Lagos zamuyi wani taro na ƙarawa juna sani wanda daganan kuma idan mutum yana da ra'ayin tafiya ƙarin karatu zai rubuta idan Allah ya taimake shi manyan ƙungiyoyin lafiya na duniya tare da haɗin gwiwar bankin duniya suka duba cancantarka saisu ɗauki nauyin ka.

Daƙyar na shawo kan Ammi da taimakon Baffa Kabir da Yaya Mus'ab ta amince min wannan tafiya itanma nasani saboda wannan hargitsin auren na Hamma Hussain ne yasa ta barni don na samu sauƙin zuciya.

Hamma Khamis ne ya kaini airport na hau jirgi na tafi dake nasan inda za'ayi taron bansha wahala ba na isa masauki, nayi wanka nayi alwala nayi Sallah sannan na kwanta baccin gajiya.

Ban tashi ba sai tara na dare na gyara jikina na fesa turare mara nauyin ƙamshi na fita domin neman abinda zanci nayi order na dawo na kwanta  babu ɓata lkc aka kawomin na zauna inacin abincin ina tunanin Ammi na, bayan na gama nayi alwala na kwanta bacci me nauyi ya ɗaukeni.





Washegari da safe na fice daga hotel ɗin na nufi gurin taro duk abinda ake buƙata na cika ashe taron na girmama wasu manyan likitoci ne guda Uku Dr. Mansur Hassan Kaltingo, Dr. Labaran Isah da Dr. Maryama Abdi Baye, bayan tashinmu daga meeting ɗin ne na fito domin hawa Abin hawa ya mayar dani masauki naji anyimin sallama a bayana na amsa tare da dakatawa da tafiyar da nakeyi na juya cikin ladabi nace.

“Barka da wannan lokaci Dr. Ina tayaka murnar samun tauraro na ɗaya a jerin manyan likitocin Africa"  Murmushi yayimin yace “Dr. Madinah Alƙasim Gwangola sunanki ya karaɗe duniyar likitocin wannan zamani ba iya ƙwarewa ke haska Miki gabanki wajen laƙantar matsalolin da suka shafi ƙwaƙwalwa ba harda baiwarki wacce take bayyane akan fuskarki"

Murmushi nayi masa nayi ƙasa da gwiwowina nace “Na gde Dr." Zubamin idanu yayi yace “Ni sunana Dr. Mansur Hassan Kaltingo haifaffen Jihar Gombe dake cikin Nigeria, wato na bibiyi tarihinki daga lokacin da Dr. Mu'az na Asibitin Koyarwa ya sanar dani cewa Amatsayina na likitan ƙwaƙwalwa ina buƙatar Haɗin kai daga gareki domin Hausawa sunce Mai laya kiyayi me zamani, Dr. Deenah tun lokacin nasa hankalina akanki,abubuwa da yawa nine nake jefaki a ciki gurare da yawa shurarki batakai a nemeki ba nine nake sawa a nemeki domin ƙarfafar kokarinki na taimakon al'umma.

Dr. Deenah aikinmu yanada wahala mutanen duniya sun tafi akan cewar kudi zai biyamu ladan aikinmu wanda Ni na jima da haƙiƙancewa babu wani kuɗi da yake da nauyin da zai biya likita da Malamin makaranta haƙƙin aikinsu saidai Allah shine kaɗai yake da abin biyanmu, kar na cikaki da surutu A wannan shekarar kina ɗaya daga cikin likitocin da Zasu tafi ƙaro karatu ƙasar Rum wato France domin samun shahadarki ta zama Consultant a ɓangaren daya shafemu wato ƙwaƙwalwa, kuma insha Allahu nayi Miki alkawarin kafin ki dawo daga wannan jihadi zan gina Miki asibiti babba a cikin birnin Kano wanda daga kowanne yanki na Afrika sai an rinƙa zuwa domin kawo ƙarar duk wani ciwo daya shafi ƙwaƙwalwa, ga wannan key ɗin motarki ne da Ƙungiyar likitocin kwakwalwa suka baki kyauta domin tayaki murnar samun gurbin zama a cikinmu"





Da tsananin mutuwar jiki ta ɗago idanunta da suka ciko da hawaye tace “Matuƙa nayi gdy da ƙoƙarinka gareni amma sai nakega kamar bazai yiwu ba...." Da sauri yace “Saboda me?" Ƙasa tayi da kanta tace “Ammi na batason yawace yawacen nan da nakeyi a cikin ƙasata ma ta Nigeria bare kuma naje mata da batun fitata ƙasar waje da sunan karatu Dr. Idan da wani daya cancanci wannan gurbin abashi ni a matsayina na mace basai dole na....." 

“Dole saikin zama Consultant!" Ya faɗa yana gyara tsaiwarsa tare da ɗan takawa yayima motar dake aje a gurin key ya buɗe ta yace  “Dame kama ake ƙota sannan me kamar zuwa ka aika Dr. Deenah dole zaki zama Consultant kizo na saukeki a masaukinki, ki barni da Ammi nine zanji da ita" 

Dr. Mansur Hassan yanada kwarjinin da bazan iya jayayya dashi ba haka na shiga sabuwar motar fil yajamu zuwa Frame Hotel inda na sauka na kwana kenan mun daɗe a receiption muna tattaunawa sannan mukayi sallama da baƙar kafiyata ta fusatashi don yayi duk me yuwuwa yaga na karɓi motar amma naƙi.

Washegari na sake dauko hanyar Kano a gajiye ban wucce gida ba saida naje asibiti n duba Hamma Hussain sannan na isa gda nayi wanka na kwanta Ammi na tsefemin kaina akace ana sallama dani a waje, ke kinji irin muguwar faɗuwar da gabana yayi Zahira! To abune baƙo da bantaɓa samu ba tunda nake a duniya ba'a taɓa aikowa ance ana sallama dani ba, ganin banida niyyar motsawa Ammi ta ƙwalawa Hamma Khamis kira ya fito daga ɗakinsu tace “Khamis dubawa auta wake nemanta?" Shima cike da happy ya nufi wajen ya jima sosai sannan ya dawo yace “Ɓingel yace ace Miki Dr. Kaltingo ne" Zuciyata ta buga da ƙarfi cikin rashin hayyaci nace “Don Allah Hamma kace masa ɓatan hanya yayi banan bane......."



PAID BOOK

_Normal 300 VIP 600 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. '

Ko MTN card ta wannan number 09013 718241.

[6/11, 7:22 PM] AM OUM HAIRAN: _*JINKIRIN AURE!!!*_

_(Ƙalubale ga ƴammata)_


OUM HAIRAN



Last Free Page 15-16



Nan na kawo karshen free Page na wannan littafin ki biya domin karatu cikin salama Nrml 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya 

Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1




 _____________________________




Zubamin idanu Ammi da Hamma Khamis sukayi da tsananin mamaki nidai banason tuhuma wannan tasa na miƙe na shige ɗakina na kullo ƙofata na haye katifa na kwanta gabana ya sake faduwa jin Ammi tana cewa “Bawan Allah ka baƙuncemu a bazata koda yake kace gurin Munau kazo ita kuma na fahimci kamar batayi lale da zuwanka ba" 

Murmushinsa na dattako yayi yace “Nasani Hajiya ba lallai Dr. Tayi farin ciki da zuwana ba Ni wakili ne daga ƙungiyar likitoci ta duniya WHO Hajiya wani albishir ne nazo Miki dashi game da Dr. Deenah duk da dai naga ita batayi murna da wannan alkhairi danaje mata dashi ba, Am dama sakamakon tacewa da zaƙulowa da wannan ƙungiya takeyi na fasihai kuma jajirtattun likitoci yasa muka zaƙulo Dr. Suka bata damar zuwa ƙasar Faransa domin ƙara samun gogewa a ɓangarenta me muhimmaci na ƙwaƙwalwa, bayan nan sunyi mata kyaututtuka na karramawa bisa ga jajircewarta wajen kawo ci gaba a wannan fanni babbar kyautar da sukayi mata itane waccen motar dake waje sai system da kuma gurbin karatu na shekara guda domin zama ƙwararriyar likitan ƙwaƙwalwa a ƙasar Nigeria, ina fatan Hajiya ke kin fahimceni Ni wakili ne daga WHO" 





Shiru sukayi gabaɗayansu kowa da sakon dake sauka a zuciyarsa banda Ni da bansan meye yake faruwa ba a haka Yaya Mus'ab yazo ya ishesu suna zaman kurame babu wanda ya samu damar magana saishi dake shigowa gidan ne yace “Ammi waɗanna manyan bakin mukayi ne haka a gidan naga wata kafurar mota a ƙofar gida"

Ammi ce ta ɗago ta dubeshi tace “Gara da Allah ya kawo ka Mus'ab kaina ya kulle na rasa abin tofawa nabar bawan Allah ƙurar hazo sai ƙare masa takeyi aka" 

Zama Yaya Mus'ab yayi yace “to meke tafe dakai bawan Allah da farko dai Assalamu alaika don naga motar lambar WHO ke gareta" murmushi Dr. Kaltingo yayi yace “Ai motar ma nan zan tafi na bar muku ita" nan ya zayyane masa komai Yaya Mus'ab yaja dogon numfashi ya sauke yace “Danƙari maƙari wannan lamari da girma yake yanzu dai ƙwarai munawa WHO godiya ne matuƙar tarin yawa alhmdllh ko iya haka Ɓingel taci moriyar nacinta gashi har duniya ta fara sanin da ɓurɓushin tsirarta a ban ƙasa maganar zuwa Faransa ƙaro karatu kuma Dr. Kaje nidai Amatsayina na wanda nake magana da yawun Madinah na amincewa tafiyarta muna fatan tafiyarta tsanin nasararta ce......"





Ammi ce ta ɗago tace “Anya Mus'ab hakan kana ganin zai yuwu kasan fa yanayin da Munau take ciki kowa bayama rayuwarta uzuri gani sukeyi kamar itace ta tsarawa kanta ƙaddararta Mus'ab inajin tsoron kada tafiyar yarinyar nan Faransa ya sake janyo mata wata masifar da bayan ta dawo zata hanata kwanciyar hankali"

Khamis ne ya magantu da cewa “Yanzu Ammi zaman nata meye ya rage nifa ina ganin tayi tafiyarta kawai shine yafi mata alkhairi...." Dr. Kaltingo ganin ya samu goyon baya yasashi saurin cewa “Kuma babban abin sha'awar inta dawo da aikinta zata dawo domin lokacin da zasu gaba karatun lokacine da WHO take daukan sabbin ma'aikata tare da gwaggwaɓan albashi Hajiya tuntuɓe daɗin gushi akwai asibitin da muke ginawa anan Kano da Gombe cikinsu ne Wannan ƙungiya zata bata jagorancin ɗaya Kinga kenan wannan dama ce da bai kamata ayi wasa da ita ba" 





Murmushi Ammi tayi tace “Yaro duk naji wannan amma nikam a son raina naga Ɓingel ɗina tayi aure suna zuwarmin da mijinta suna gaisheni suna tafiya....." Da sauri Dr. Kaltingo yace “Shima auren Lokacine idan lokacinsa yayi za'ayi Ammi ayi ta addu'a ba gaggawar ba samun mafi alkhairi" da haka wannan zama ya tashi nikam ina ɗakina bansan inda aka kwana ba sai magrib ina zaune a ɗaki naji sallamar Hamma Hussain gabana ya faɗi sosai inajin a raina kamar in tashi in fita wata zuciyar tana hanani amma nayi mamakin yanda aka bari ya fito yanzun da ɗanyen ciwo a kirjinsa bai warke ba.

Kasa dannar ruhina nayi na miƙe na fito mukayi karo dashi yana niyyar shigowa ɗakin nawa na matsa na bashi hanya ina buɗe bakina nace “Ya akayi wannan wanne irin kulawa likitanka yake baka da zai baka damar yawo a wannan lokac....." Ban rufe bakina ba naji nayi flat a cikin jikinsa yasa hannunsa biyu ya zagayeni ya ɗora kansa a saman kaina cikin zafin fitar iskar numfashin dake nuna wannan zuciya tana cike da ƙunci yace “Wlh babu wata mace da zan iya yima kyautar samartaka ta indai bata kasance keba Ɓingel zanyi nesa da kowa dominki a yau na gama komai nawa na barin ƙasar nan zan tafi Italian domin yin wani course ina tunanin zai ɗaukeni watanni takwas insha Allahu kafin na dawo zanyi duk me yiwuwa na daidaita komai muyi aure kafin na rasa rayuwata ta dalilinki......" 





Yana rufe bakinsa na janye a jikinsa nace “Duk da nasani Zuciyata taka ce Hamma amma inason don girman Allah muyi biyayya domin muma ayi mana Hamma rayuwa fah tana taka rawar ne kayi ne me za'ayi maka tunda iyayenka sunƙi duba kusanci da zumunci su karɓeni matsayin suruka ka haƙura dani ka zauna da Bilkisu da zuciya ɗaya ina maka fatan ta zamo alkhairinka indai nice inanan akan bakata ban janye ba idan har Allah ya hukunta aure tsakaninmu to ko a mace ta huɗu zan shiga gdanka na amince, Hamma nima akwai yiwuwar zanyi tafiya zuwa Faransa duk da bansan ya mutane zasu ɗauki abin ba, Nima da farko ban karɓa ba yarjewar Yaya Mus'ab yasani yarda domin shiɗin furuci nane indai ya aminta Nima ina aminta da amincewarsa"

Ina maganar ina isa saman akwatin kayana na ɗebo masa takardun da aka aikomin dasu da magarubar nan kafin na tada sallah ya karɓa yana kallona Nima shiɗin nake kallo ya ɗauke idanunsa akaina ya mayar kan takardun yaci gaba da dubsnsu a nutse Saida ya gama dubawa sannan ya ɗago fuskarsa babu wata walwala yace “Congrats" daga haka ya juya ya fice tun daga wannan rana alaƙa tsakanina dashi ta janye bansan dalili ba kuma nayi duk me yuwuwa naga na sani amma yaƙi bani dama koda alaƙata dashi ta dawo saita dawo a wani yanayi yawanci ina office ina aiki zai kirani yace idan na tashi yanason ganina a guri kaza" 





A farko banjin komai haka zan ɗauki mota na naje duk inda yacemin tun daga lokacin daya fara bijiromin da abubuwan da hankalina bazai ɗauka ba daga lokacin na daina amsa kiransa nakance masa inada meeting ko inada uzurin yi a gida.

Wata tana ban mantawa naje Aiki na dawo na gaji ga kaina dake ciwo saboda shirye-shiryen tafiyata da muketayi babu zama babu nutsuwa hakan yasa banida lokacin kaina, wannan rana na ɗebo gajiyar gaske kayana na cire na ɗaura towel da nufin shiga wanka gashi gidan Ni kaɗaice Ammi ta tafi gidan Hajiya Mabruk wata yar ƙasarsu, gajiya ce ko tsautsayi ne nidai bansani ba naji wayana na ring ina dubawa naga Number Dr. Kaltingo na ɗaga da girmamawa ta da nakeyi masa domin mutumin yanada ƙimar gaske a gurina mun gaisa yacemin kiyimin snapping na Passport naki ki turomin sannan ki zama cikin shiri jibi in Allah ya kaimu karfe 1:00pm zaku tashi Don Allah a kula dakai sosai kada ki biyewa sakarkaru su ɗauke Miki hankali daga abinda kikajeyi" 





Godiya nayi masa mukayi sallama na dauki hoton na tura masa na kishingiɗa ya'akayi ya akayi bacci ya ɗaukeni naji kamar an tasheni na zabura ina ƙoƙarin tashi kawai naji an kwanto kaina tare da ɗora hannu a ƙirjina abinda ya sabbabamin buɗe idanuna tarwai cikin firgici kiɗima da tashin hankali nace “Hamma Huss....." Numfashi nane ya ɗauke nayi wani kukan kura ina ƙoƙarin Angajeshi towel ɗin jikina ya suɓale ya rage dagani sai pant nasa hannu na ƙanƙame jikina ko dukkan gaɓɓaina suna rawa nace “Innanillahi wa Inna ilaihirraji'un Ham... Hamma....." Nufoni yayi da wani yanayi da bantaɓa riska ba a rayuwata na miƙe ina ƙoƙarin yayumo hijjab ɗina nasa ya cafkeni ƙarfinmu ba ɗaya ba kawai naji wani ɗumi da zugi saman nipples ɗina na buɗe idona na sake rintsewa na saki wata ƙara tare da dafe kansa cikin tashin hankali nace “Ham...Hamma Ka bari banaso ya hayyu ya ƙayyumu innanillahi hasbinallahu wa ni'imal wakeel......... Ɗagowar da zaiyi na samu na Angajeshi na shige bayin cikin ɗakina da ba'a gama gyarawa ba na datso ƙofar ƙirjina na duka irin na dakan garin tuwon mutanen da haka naji yanata bugan ƙofar yana kiran sunana da wata wahalalliyar murya da na kasa gane wacce iri ce nikuwa naƙi buɗewa na zauna a ciki na haɗe kai da gwiwa ina kukan baƙin ciki karo na biyu kenan da yake ƙoƙarin ketamin haddi na meye yasa yakemin hakanne?





" Tambaya mara amsa da wannan tunanin naji alamun fitarsa naja ajiyar zuciya na miƙe na buɗe kofar a hankali ganin babu kowa na fito na dannawa ɗakin key na koma na zube ilahirin jikina har yanzu rawa yake ranar inajin shigowar dukkan yan uwana har Ammi na inaji suka dawo ita da Hamma Aminu dake a mota ta suka fita har ɗakina ta ƙwanƙwasa zata bani mukullin amma firgici ya hanani buɗewa gani nakeyi kamar zasu fahimci abinda ya faru.

Washegari kuwa daƙyar na fito kiran duniya Hamma yayimin da saƙonni naƙi buɗewa saboda matuƙa ya ficemin a raina na fahimci farautar mutunci na yakeyi so yake ya cikawa duniya burinta na kirarin da sukeyi mana budur bazar.

Ina office aka kirani a waya na ɗaga kawai sai naji an kece da dariya nayi shiru ina hasaso waye can naji yace.






 “Madinah kenan jiya dai sai akai walƙiya akan idanuna naga halin kowa ashe dama shaƙuwar nan Ni nasan bata Allah bace ashe lalubar juna akeyi am na manta ban faɗa miki waye ba duk da nasan zaki iya daukar murya to mijinki ne da zai taimakeki ya aureki amma fah in kinso rufuwar asirinki wato Khamal, kafin na sauke layi ina Miki albishir da ki buɗe data akwai kyakkyawan tukuici da nakeson yau na farayi Miki saboda inason kisan nasan keɗin wacece ashe lulluɓin biri ne ta ciki fanko ne koda yake nima na haɗiyi yawu........."

Datse layinsa yayi batare da bawa shirmensa muhimmaci ba na buɗe data sakonni suka fara shigowa baƙuwar number dana gani kawai na duba na zabura na miƙe kaina yana juyawa jiri na neman kayar dani na saki wayata, kinsan meye na gani? Video na da Hamma Hussain jiya an cire murya da komai an daddatse wasu guraren sai inda ya kwanto jikina inda ya sanya nipples ɗina a bakinsa da inda na ɗora hannu na akansa da niyyar tureshi iyanan kawai aka bari wani hawaye me ɗumi ya satatomin ba jikina ba hatta Zuciyata rawa takeyi inda kikasan sabuwar kamun ciwon jijjiga ta masu naƙuda......




_Normal 300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank. '

Ko MTN card ta wannan number 09013 718241.

[6/12, 8:57 PM] AM OUM HAIRAN: 17-18


_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1






Bansan tsayin lokacin dana ɗauka zaune a gurin nan ba Saida naji an buɗe office ɗina an shigo shima ba shigowar naji ba ƙarar dukan table ne ya dawo dani hayyaci na dago idanuna da suka kaɗa sukayi jawur tare da cije leɓe na ganin me shigowar yana nufoni yasani saurin miƙewa na nunashi da yatsa sai naga ya tsaya shima jikinsa na rawa da murya me nuna alamun tashin hankalinsa yacemin “Ya akayi kikayi mana video jiya har kika fitar dashi......." 

Bansan inada fushi ba sai ranar Allah ɗaya bansan lokacin dana ɗauke Hamma Hussain da wani nagartaccen mari da ya sanyashi dafe kunci ba, cikin kuka nace masa “Azzalumi mayaudari dama shirinka kenan akan rayuwata shiyasa kaketa bibiyata ashe jiran damar da zaka canzamin lissafin rayuwa kakeyi Hussain ni ka tallatawa surata a duniya saboda cin mutumci da tozarci akan abinda bantaɓa nema ba bantaɓa aikatawa ba Hamma meye nayi maka daka zaɓi fitar da bad video na....." 

Rufemin baki yayi da hannunsa jikinsa har yanzun rawa yake yi na tureshi nace “Karkace min komai ɗon girman Allah kaje kawai Allah ya bimin haƙƙina ya sakamin wannan tozarcin daka shirya yimin" 

Ina faɗin haka na zari jakata da key na nayi waje ya biyoni yana kwalamin kira banko bi takansa ba bare na saurareshi nayi ma motata key na fice da mugun gudu na nufi get ɗin maigadin ya buɗe min cike da mamakin yanda nakejan motar a fusace.





Gida na nufa dama dai ikon Allah ke kare bawa amma kariyar ranar ta musamman ce, inayin parking na kifa kaina a sitiyarin na rushe da wani kuka me dukan zuciyar makusanci banji sanda aka buɗe ƙofar ba saiji nayi ansa hannu an ɗago fuskata yasa hannu ya sharemin hawayen yana girgizamin kai yace “Ɓingel ya akayi haka?" Da sauri na ɗago ina ja baya ina kaɗa masa kai yayi saurin damƙar hannu na yace “Please Lovely sis baa ɓoyewa abokin kuka mutuwa kuma ko kowa yaƙi fahimtarki nikam zan fahimceki garin yaya haka ta faru videonki nata yawo tsakanin wayoyin dangi harma suna iƙirarin fitar dashi duniya muddin baki yarda da ƙudurinsu ba?" 

Sai yanzu na samu damar furuci na buɗe bakina Harshena na sarƙewa na zayyane masa komai yaja gwauron numfashi yace “Allah shine kawai zai fitar dake Hussain yayi kuskure kuma ya ha'ince ke Madinah koda ace da yardarki hakan ta faru bai kamata yayi Miki video har yayi sakacin da videon zai tantsama duniya ba, yanzu dai karki shiga gdannan saboda Ammi nakan tsini wlh duk wani bayani daya kamata nayi mata nayi mata taƙi fahimta muje na kaiki gdansu Ja'afar ki zauna tare da Mamansu duk yanda zanyi sanyi na haɗo Miki komanki kiyi tafiyarki Faransa ki barmu da Ammi zamuji da ita"

Ɗagowa nayi ina ƙoƙarin dakatar da kukana nace “Bazan iya tafiya bansan matsaya ta a gun Ammi ba Hamma Mus'ab....." A fusace yace dole saikin tafi domin kuwa hakan shine kawai zaisa komai ya batare da rai ya ɓaci ba"





Naso gardamewa kafiyar Yaya Mus'ab yasa na amince ya kaini gidansu abokinsa dake Inna Saude tasanni bamu samu matsala ba ta rinƙa bani kulawa har zuwa dare wajen Goma Yaya Mus'ab ya kawomin trolly na kayana dana haɗa da sauran tarkace na na killace washegari raina babu daɗi haka Dr. Kaltingo ya kirani yazo ya ɗaukeni shida Yaya Mus'ab suka kaini Airport Saida suka jira tashinmu ina kuka ina ɗagawa ɗan uwana hannu karon farko da zanyi tafiya me nisa a rayuwata bantaɓa zuwa ko Niger ba iyakar yawona a cikin gidane Nigeria sai gashin zan sauka a birnin Rum da sunan karatu tabbas wannan wani Babban ƙalubale ne daya farmaki rayuwata dole nasan irin naɗin da zanyi don ɗaukar cece-kucen sociaty ɗina.

Ƙasar France ƙasace me ban sha'awa da burge idanu gani na fara fuskantar hakan ne tun daga Airport ashe abin na gaske ne ko anan ɗin ma motar WHO ce tazo ta daukemu ukune Ni kaɗai ce mace kuma bahaushiya a cikinsu ɗayan Ucche yazo daga Ogun Dayan kuma yazo daga Benue, aka kaimu masauki kowa aka damƙa masa key na dakinsa a hotel ɗin da aka saukemu.





Na daɗe ina kallon tsarin ɗakin da zanyi rayuwar shekara guda a cikinsa gashinan dakine tangameme sai parlour shima babba yayi biyun ɗakin dakin gadone kawai da wardrobe sai dressing mirror falon kuwa ƙatuwar TV ce ta bango sai kujeru set sannan gefe dinning table da kujerunsa tsakiyar kujerun akwai Center table sai wani guri da aka ware aka zuba littafai a cover alamar da take nuna gurin karatu ne aka tanada numfashi na sauke tare da komawa ciki na cire kayana na shiga bathroom nayi wanka na ɗaura alwala dake sun sanya hoton da yake nunawa mutum ƙibla nasa doguwar riga nayi Sallah ina azkhar naji ana taɓa kofa ta na tashi na buɗe wani ma'aikaci ne ya gaisheni tare da miƙamin SCHEDULE nasu na abinci na zabi wanda nake tunanin zan iya ci na koma bai jima ba ya kawomin na karɓa Saida na gama abinda zanyi sannan na bude wayata da son kiran Yaya Mus'ab sai naga su lokacin dare yayi musu nisa dole na hƙr na kwanta.





A chat nake sanar dasu Yaya Mus'ab na sauka lfy tare da ɗaukar masaukina na tura masa baya online saboda haka Nima na sauka na kwanta, satinmu ɗaya muka fara ɗaukar darasi akwai yan Afrika da yawa a ajinmu musamman yan Nijeriya anan muka sake haduwa dake munyi mamakin ganin juna sosai kike tambayata yarana nawa nayi murmushi nace Miki banmayi auren ba nan kike cemin yaranki biyu Noor da Ayman babansu ya rasu tunda cikin Ayman na tausaya Miki sosai daganan amincinmu yaci gaba da hauhawa ya kasance kin baro masaukinki kin dawo nawa muna rayuwa da yarda da juna da kulawa kinsha tambayata meyesa banyi aure ba ke s tunaninki boko ce ta hanani aure sai daga baya kika fahimci ashe niɗin wata cukurkuɗaɗɗiyar ƙaddara ke kaina babu wani abu dana nema na rasa dangin kyau duk wata halitta dake cika zatin mace Allah ya gama zubeta a wajena harma da ƙari ga ilimi amma mijin aure ya gagara samuwa a gareni.

Haka mukayita gungurawa har muka gama karatu na fito da kyakkyawan certificate wanda yabawa kowa mamaki kamar kuwa yanda Dr. Kaltingo yayimin alƙawari haka ce ta faru bayan mun gama shagalin graduation namu a wannan ƙasa muka ɗungumo Nigeria a Abuja muka sauka banyi tunanin Ammi zata halacci wannan taro ba amma sai na ganta, murna farin ciki bansan sanda na rungumeta ba harda Hamma Hussain yazo gurin wannan shagalin da Baffa Kabir tunda shine matsayin uba a gareni bayan komai ya nutsa ne aka fara kiran manyan likitocin duniya suna jinjinawa kwazona da har ƙasar France ta amince ta bani shahadar zama Consultant ta ƙwaƙwalwa tare da kyakkyawan yabo, amma fah munci wuya kafin faruwar hakan Allah ne kawai ya dubeni ya bani Sa'a don duk waɗanda mukaje dasu Ni kaɗai ce na tsallake jarabawar ƙarshe wayyoh Allah Dr. Zahira mutum aka kwantarmin nayi masa aiki na ƙwaƙwalwa tsayin sati biyar ana wannan aikin dukkan abokan karatuna nasu majinyatan basa wucce aikin farko zuwa na biyu suke mutuwa nice nakai ƙarshe da taimakon Dr. Kaltingo na samu wannan petiant nawa ya miƙe wannan abu ba ƙaramin daɗi yayiwa masoya na ba wannan shine farkon nasarata ta duniya gabaɗaya.





A wajen taron aka bani Offer na ta ɗaukar aiki a Word health organization  sannan aka ware ranar da za'a rakani office ɗina na Asibitin da suka gina na masu matsalar ƙwaƙwalwa dama sauran cututtuka anan Kano tare da kyautar wata arniyar motar saman wacce suka bani a farko, ranar baniba hatta Ammi tayi kukan farin cikin yanda taga kowa a wannan waje Idan ya buɗe baki Dr. Deenah yake ambato.

Na sake rungumeta na fashe da kuka nace “Duk wannan baya gabana Ammi nafison na wanke Miki zuciya ta hanyar yin aure Ammi wannan millions of dollars ɗin da suka zubamin a acct ɗina zaki tafi Saudiyya bana keda Yaya Mus'ab da Yaya Salees da Hamma Khamis da Hamma Aminu dani kaina inason don Allah kuyimin addu'a idan ciwone Allah ya yaye min yayimin zaɓin abokin rayuwata na kwarai ya bayyana mana shi da gaggawa kodan samun cikakken farin ciki....." 

Rungumeni tayi tana hawaye tana cewa “Zaizo Ɓingel zaizo insha Allahu  Allah ka jiƙan Alƙasim ka haskaka makwancinsa burinsa ya cika akanki da ya jima yana fata samun ɗiya mace ta zama likita gashi ya samu amma bai gani ba Ɓingel ki ginawa mahaifinki masallaci da rijiya ko makarantar islamiyya da niyyar sadaƙatul jariyyah nasan zaiyi alfahari dake....."






Da wannan taro ya tashi muka taho gida jirgi muka biyo nida Ammi da Baffa Kabir Yaya Mus'ab da Hamma Hussain da Khamis suka tuƙo motocin suka taho dasu, ƴan unguwar mu sukayita shigowa yimin sannu da zuwa wasu domin Allah wasu kuma gulma ke kawosu bayan lafawar abubuwa na shiga office ɗina na fara gudanar da ayyuka cike da ƙwarewa kema nayi Miki office a asibitina mukaci gaba da gudanarwa kinsani albashina ba kaɗan bane duk watan duniya a canjinmu na Nigeria ina ɗaukar 1.8 million hakan yasani bige gidanmu nayi mana gini na alfarma na siye kangon  dake kusa da namu kangon duk na haɗe mana muke rayuwa da mahaifiyarmu sannan na bawa Yayye na jari me kaurin gaske suka fantsama kasuwanci dake sunada nasibi dukkansu gasunan suna rayuwa cikin rufin asiri Yaya Mus'ab ne ya koma karatu bayan ya gama ya samu aikin banki yanzu dukkansu babu wanda bashida iyali hatta Hamma Aminu da nake bi yayi gida da yaransa biyu niko gani a gida kullum cikin jiran tsammani nake Allah bai kawo karshe ba.

Zahira zuwa yanzu wlh Nima babu abinda nake buƙata sai miji abokin rayuwa shawara da ɗebe kewar juna amma abu kullum kamar daɗi na fara cutuwa har shaiɗan da zuciya sun fara yawo dani musamman yanda yanzu kuma wata fitina ta bijiro min namiji zai shiga jikina sai mun saba ya fara bijiro min da wasu ɗabi'u saidai idan na fahimta na gocewa buƙatarsa kasancewar inada burin ƙaddarata ta tsaya iyakar JINKIRIN AURE karta haɗa da karuwanci, Zahira wannan shine kaɗan daga cikin tarihi na ina fatan hakan zaisa ki gane cewa Ni bani nake gudun aure ba shine yake guduna".........




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1



[6/19, 8:28 PM] Am Oum Hairan: 17-18


_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1






Bansan tsayin lokacin dana ɗauka zaune a gurin nan ba Saida naji an buɗe office ɗina an shigo shima ba shigowar naji ba ƙarar dukan table ne ya dawo dani hayyaci na dago idanuna da suka kaɗa sukayi jawur tare da cije leɓe na ganin me shigowar yana nufoni yasani saurin miƙewa na nunashi da yatsa sai naga ya tsaya shima jikinsa na rawa da murya me nuna alamun tashin hankalinsa yacemin “Ya akayi kikayi mana video jiya har kika fitar dashi......." 

Bansan inada fushi ba sai ranar Allah ɗaya bansan lokacin dana ɗauke Hamma Hussain da wani nagartaccen mari da ya sanyashi dafe kunci ba, cikin kuka nace masa “Azzalumi mayaudari dama shirinka kenan akan rayuwata shiyasa kaketa bibiyata ashe jiran damar da zaka canzamin lissafin rayuwa kakeyi Hussain ni ka tallatawa surata a duniya saboda cin mutumci da tozarci akan abinda bantaɓa nema ba bantaɓa aikatawa ba Hamma meye nayi maka daka zaɓi fitar da bad video na....." 

Rufemin baki yayi da hannunsa jikinsa har yanzun rawa yake yi na tureshi nace “Karkace min komai ɗon girman Allah kaje kawai Allah ya bimin haƙƙina ya sakamin wannan tozarcin daka shirya yimin" 

Ina faɗin haka na zari jakata da key na nayi waje ya biyoni yana kwalamin kira banko bi takansa ba bare na saurareshi nayi ma motata key na fice da mugun gudu na nufi get ɗin maigadin ya buɗe min cike da mamakin yanda nakejan motar a fusace.





Gida na nufa dama dai ikon Allah ke kare bawa amma kariyar ranar ta musamman ce, inayin parking na kifa kaina a sitiyarin na rushe da wani kuka me dukan zuciyar makusanci banji sanda aka buɗe ƙofar ba saiji nayi ansa hannu an ɗago fuskata yasa hannu ya sharemin hawayen yana girgizamin kai yace “Ɓingel ya akayi haka?" Da sauri na ɗago ina ja baya ina kaɗa masa kai yayi saurin damƙar hannu na yace “Please Lovely sis baa ɓoyewa abokin kuka mutuwa kuma ko kowa yaƙi fahimtarki nikam zan fahimceki garin yaya haka ta faru videonki nata yawo tsakanin wayoyin dangi harma suna iƙirarin fitar dashi duniya muddin baki yarda da ƙudurinsu ba?" 

Sai yanzu na samu damar furuci na buɗe bakina Harshena na sarƙewa na zayyane masa komai yaja gwauron numfashi yace “Allah shine kawai zai fitar dake Hussain yayi kuskure kuma ya ha'ince ke Madinah koda ace da yardarki hakan ta faru bai kamata yayi Miki video har yayi sakacin da videon zai tantsama duniya ba, yanzu dai karki shiga gdannan saboda Ammi nakan tsini wlh duk wani bayani daya kamata nayi mata nayi mata taƙi fahimta muje na kaiki gdansu Ja'afar ki zauna tare da Mamansu duk yanda zanyi sanyi na haɗo Miki komanki kiyi tafiyarki Faransa ki barmu da Ammi zamuji da ita"

Ɗagowa nayi ina ƙoƙarin dakatar da kukana nace “Bazan iya tafiya bansan matsaya ta a gun Ammi ba Hamma Mus'ab....." A fusace yace dole saikin tafi domin kuwa hakan shine kawai zaisa komai ya batare da rai ya ɓaci ba"





Naso gardamewa kafiyar Yaya Mus'ab yasa na amince ya kaini gidansu abokinsa dake Inna Saude tasanni bamu samu matsala ba ta rinƙa bani kulawa har zuwa dare wajen Goma Yaya Mus'ab ya kawomin trolly na kayana dana haɗa da sauran tarkace na na killace washegari raina babu daɗi haka Dr. Kaltingo ya kirani yazo ya ɗaukeni shida Yaya Mus'ab suka kaini Airport Saida suka jira tashinmu ina kuka ina ɗagawa ɗan uwana hannu karon farko da zanyi tafiya me nisa a rayuwata bantaɓa zuwa ko Niger ba iyakar yawona a cikin gidane Nigeria sai gashin zan sauka a birnin Rum da sunan karatu tabbas wannan wani Babban ƙalubale ne daya farmaki rayuwata dole nasan irin naɗin da zanyi don ɗaukar cece-kucen sociaty ɗina.

Ƙasar France ƙasace me ban sha'awa da burge idanu gani na fara fuskantar hakan ne tun daga Airport ashe abin na gaske ne ko anan ɗin ma motar WHO ce tazo ta daukemu ukune Ni kaɗai ce mace kuma bahaushiya a cikinsu ɗayan Ucche yazo daga Ogun Dayan kuma yazo daga Benue, aka kaimu masauki kowa aka damƙa masa key na dakinsa a hotel ɗin da aka saukemu.





Na daɗe ina kallon tsarin ɗakin da zanyi rayuwar shekara guda a cikinsa gashinan dakine tangameme sai parlour shima babba yayi biyun ɗakin dakin gadone kawai da wardrobe sai dressing mirror falon kuwa ƙatuwar TV ce ta bango sai kujeru set sannan gefe dinning table da kujerunsa tsakiyar kujerun akwai Center table sai wani guri da aka ware aka zuba littafai a cover alamar da take nuna gurin karatu ne aka tanada numfashi na sauke tare da komawa ciki na cire kayana na shiga bathroom nayi wanka na ɗaura alwala dake sun sanya hoton da yake nunawa mutum ƙibla nasa doguwar riga nayi Sallah ina azkhar naji ana taɓa kofa ta na tashi na buɗe wani ma'aikaci ne ya gaisheni tare da miƙamin SCHEDULE nasu na abinci na zabi wanda nake tunanin zan iya ci na koma bai jima ba ya kawomin na karɓa Saida na gama abinda zanyi sannan na bude wayata da son kiran Yaya Mus'ab sai naga su lokacin dare yayi musu nisa dole na hƙr na kwanta.





A chat nake sanar dasu Yaya Mus'ab na sauka lfy tare da ɗaukar masaukina na tura masa baya online saboda haka Nima na sauka na kwanta, satinmu ɗaya muka fara ɗaukar darasi akwai yan Afrika da yawa a ajinmu musamman yan Nijeriya anan muka sake haduwa dake munyi mamakin ganin juna sosai kike tambayata yarana nawa nayi murmushi nace Miki banmayi auren ba nan kike cemin yaranki biyu Noor da Ayman babansu ya rasu tunda cikin Ayman na tausaya Miki sosai daganan amincinmu yaci gaba da hauhawa ya kasance kin baro masaukinki kin dawo nawa muna rayuwa da yarda da juna da kulawa kinsha tambayata meyesa banyi aure ba ke s tunaninki boko ce ta hanani aure sai daga baya kika fahimci ashe niɗin wata cukurkuɗaɗɗiyar ƙaddara ke kaina babu wani abu dana nema na rasa dangin kyau duk wata halitta dake cika zatin mace Allah ya gama zubeta a wajena harma da ƙari ga ilimi amma mijin aure ya gagara samuwa a gareni.

Haka mukayita gungurawa har muka gama karatu na fito da kyakkyawan certificate wanda yabawa kowa mamaki kamar kuwa yanda Dr. Kaltingo yayimin alƙawari haka ce ta faru bayan mun gama shagalin graduation namu a wannan ƙasa muka ɗungumo Nigeria a Abuja muka sauka banyi tunanin Ammi zata halacci wannan taro ba amma sai na ganta, murna farin ciki bansan sanda na rungumeta ba harda Hamma Hussain yazo gurin wannan shagalin da Baffa Kabir tunda shine matsayin uba a gareni bayan komai ya nutsa ne aka fara kiran manyan likitocin duniya suna jinjinawa kwazona da har ƙasar France ta amince ta bani shahadar zama Consultant ta ƙwaƙwalwa tare da kyakkyawan yabo, amma fah munci wuya kafin faruwar hakan Allah ne kawai ya dubeni ya bani Sa'a don duk waɗanda mukaje dasu Ni kaɗai ce na tsallake jarabawar ƙarshe wayyoh Allah Dr. Zahira mutum aka kwantarmin nayi masa aiki na ƙwaƙwalwa tsayin sati biyar ana wannan aikin dukkan abokan karatuna nasu majinyatan basa wucce aikin farko zuwa na biyu suke mutuwa nice nakai ƙarshe da taimakon Dr. Kaltingo na samu wannan petiant nawa ya miƙe wannan abu ba ƙaramin daɗi yayiwa masoya na ba wannan shine farkon nasarata ta duniya gabaɗaya.





A wajen taron aka bani Offer na ta ɗaukar aiki a Word health organization  sannan aka ware ranar da za'a rakani office ɗina na Asibitin da suka gina na masu matsalar ƙwaƙwalwa dama sauran cututtuka anan Kano tare da kyautar wata arniyar motar saman wacce suka bani a farko, ranar baniba hatta Ammi tayi kukan farin cikin yanda taga kowa a wannan waje Idan ya buɗe baki Dr. Deenah yake ambato.

Na sake rungumeta na fashe da kuka nace “Duk wannan baya gabana Ammi nafison na wanke Miki zuciya ta hanyar yin aure Ammi wannan millions of dollars ɗin da suka zubamin a acct ɗina zaki tafi Saudiyya bana keda Yaya Mus'ab da Yaya Salees da Hamma Khamis da Hamma Aminu dani kaina inason don Allah kuyimin addu'a idan ciwone Allah ya yaye min yayimin zaɓin abokin rayuwata na kwarai ya bayyana mana shi da gaggawa kodan samun cikakken farin ciki....." 

Rungumeni tayi tana hawaye tana cewa “Zaizo Ɓingel zaizo insha Allahu  Allah ka jiƙan Alƙasim ka haskaka makwancinsa burinsa ya cika akanki da ya jima yana fata samun ɗiya mace ta zama likita gashi ya samu amma bai gani ba Ɓingel ki ginawa mahaifinki masallaci da rijiya ko makarantar islamiyya da niyyar sadaƙatul jariyyah nasan zaiyi alfahari dake....."






Da wannan taro ya tashi muka taho gida jirgi muka biyo nida Ammi da Baffa Kabir Yaya Mus'ab da Hamma Hussain da Khamis suka tuƙo motocin suka taho dasu, ƴan unguwar mu sukayita shigowa yimin sannu da zuwa wasu domin Allah wasu kuma gulma ke kawosu bayan lafawar abubuwa na shiga office ɗina na fara gudanar da ayyuka cike da ƙwarewa kema nayi Miki office a asibitina mukaci gaba da gudanarwa kinsani albashina ba kaɗan bane duk watan duniya a canjinmu na Nigeria ina ɗaukar 1.8 million hakan yasani bige gidanmu nayi mana gini na alfarma na siye kangon  dake kusa da namu kangon duk na haɗe mana muke rayuwa da mahaifiyarmu sannan na bawa Yayye na jari me kaurin gaske suka fantsama kasuwanci dake sunada nasibi dukkansu gasunan suna rayuwa cikin rufin asiri Yaya Mus'ab ne ya koma karatu bayan ya gama ya samu aikin banki yanzu dukkansu babu wanda bashida iyali hatta Hamma Aminu da nake bi yayi gida da yaransa biyu niko gani a gida kullum cikin jiran tsammani nake Allah bai kawo karshe ba.

Zahira zuwa yanzu wlh Nima babu abinda nake buƙata sai miji abokin rayuwa shawara da ɗebe kewar juna amma abu kullum kamar daɗi na fara cutuwa har shaiɗan da zuciya sun fara yawo dani musamman yanda yanzu kuma wata fitina ta bijiro min namiji zai shiga jikina sai mun saba ya fara bijiro min da wasu ɗabi'u saidai idan na fahimta na gocewa buƙatarsa kasancewar inada burin ƙaddarata ta tsaya iyakar JINKIRIN AURE karta haɗa da karuwanci, Zahira wannan shine kaɗan daga cikin tarihi na ina fatan hakan zaisa ki gane cewa Ni bani nake gudun aure ba shine yake guduna".........




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1

[6/19, 8:28 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan 19-20_*





_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1





************



Wata gwauruwar ajiyar zuciya Dr. Zahira tayi ta cire hannunta a kuncinta tace “Wato komai naki abin taajibi ne Dr. Madinah haƙiƙa duk da nasan abubuwa da yawa game dake amma yau na ƙara cika da tausayin rayuwarku kuna rayuwa da ƙaunar juna tsakaninki da ƴan uwanki saidai duniya taƙi maku adalci Dr. Kiyi hƙr wataran komai zai zama tarihi me bada tarihin ma bazaa samu ba, amma meye yasa kika yanke shawarar sake tafiya Rasha domin sake wasa kwakwalwa?"

Iska ta fitar daga hancinta da bakinta tanakai dubanta a agogo tace “Saboda na bawa 9ja iska zarge-zargen mutane a kaina sun fara yawan da kaina yake neman gaza ɗauka Dr. Zahira kina gani wahala nakeyi nakecin gumina Gashi dai permanent office ɗina amma Ni kenan a yawo yau ina wannan jihar gobe ina wannan asibiti tara ne a ƙarƙashin kulawata Ni kaɗai ga damuwa da take neman fasamin kwakwalwa a ƙalla idan na matsa zan samu sauƙi na kwana biyu" 

Tana maganar tana shiga bathroom ta ɗauro alwala ta fito lokacin 1:57am ta tayar da sallah kamar yanda Mal Hamza ya umarce ta haka tayi harma da addu'o'in da bai sata ba sannan ta kishingiɗe a kan praymate ɗin bacci ya ɗauketa.





Kiran asuba ne ya tasheta ta tashi Dr Zahira sukayi sallah itadai sake kwanciya tayi ita kuma Zahira ta shiga gyaran gidan kafin Ammi ta fito ta gyara komi ita da Bintalo, koda Ammi ta fito ta gani ba ƙaramar addu'a sukasha ba sukayi break Ammi tace “ita Sarkin baccin bata tashi bane?" Murmushi Dr Zahira tayi tace “kusan kwana tayi tana ganawa da ubangiji yau kuma tace azumi takeyi amma Ammi Madinah tana buƙatar kulawa sosai saboda a ƴan kwanakin nan na fahimci matsalarta ta dameta saboda ina yawan kamata cikin dogon tunani wani lokaci harda hawaye Ammi kici gaba da tausarta da nuna mata lokacinta ya ƙarato insha Allahu"





Jinjina kai Ammi tayi tace “To Zahira ubangiji ya amince" miƙewa tayi tace “Ammi bari naje gda na shirya na tafi aiki" fatan alkhairi tayi mata ta fita ita kuma taci gaba da ƴan aikace-aikacenta na gda sai rana sosai ta fito ta gama shirinta tsaf suka kuma gaisawa da Ammi ta zauna tana nazarin ta inda zata fara Ammi tace “yauma da tafiyar ne?" Ajiyar zuciya tayi tace “wlh Ammi zan shiga wani ƙauye can cikin Garum Malam bana fatan nakai dare bare kwana ya kamani bazan tafi da mota ba saboda bansan yanayin hanyar ba kinsan hanyar ƙauyuka sai a hankali" 

Fatan alkhairi Ammi tayi mata ta fita ta hau ɗan sahu Saida ta biya office ɗinta ta dauki wasu takardu sannan ta fita ta nufi Kano line ta hau mota tasha wahala kafin takai ƙauyen haka dai tayi abinda ya kaita ta fito ta kuma nufo Kano ko asibitin bata koma ba ta wucce gida ana kiran Isha saida tayi sallah sannan ta samu damar shan ruwa bayan tasha ruwa ta kwanta tayi muguwar gajiya batako son ta motsa bacci ya ɗauketa cikin bacci taji ana knowking ƙofar ta tashi ta zauna a gefen katifar tana tattare gashinta tace “Waye?" Ba'a bata amsa ba sai turo ƙofar da akayi aka shigo tayi saurin miƙewa tsaye ya tsaya jikin ƙofar tare da saƙale hannunsa a ƙirjinsa ya kafeta da idanunsa dake cikin farin tabarau.





Saurin saita nutsuwarta tayi tare da ɗaure fuska tace “Mal lafiya a wannan lokacin?" Takowa ya farayi cikin takunsa na isa yana matsota batare da yace komai ba har Saida ya isa ciki sosai ya ɗora ƙafarsa saman stool ya sake saita idanuwansa akanta yace “Dr. Deenah ko kuma nace Ɓingel sunan da kika saba dashi daga gareni" kawar dakai tayi tana juya masa baya tace “iyakar abinda ya kawo ka kenan?" Murmushi yayi na gefen baki yace “Nazo ne naji matsayata a gurinki domin naji wani sabon labari da brain ɗina ya kasa tantancewa Madinah meye matsayin Hussein a wajenki yanzuuu...."

Ya faɗa da ƙaraji yana hautsinota gaba da karfi ya ɗago kanta tare da zuba idanunsa kan fuskarta, takaici ne yasata tureshi taja dogon tsaki ta juya zata fice ya fincikota da ƙarfi yace “Wlh tallahi Madinah Hussain ya ƙuna yanzu baya tsoron ƙauri indai a kan lamarinki ne banyi ba ance nayi garama muyi ɗin musan munyi in kika cika nunamin rashin daraja zan gwada Miki nafiki ɗiban albarka domin komai kikayi zai kasance horona ne....." 

A hassale tace “Hakane Hussain Ni horonka ce ta fanni da yawa na rayuwa amma ka sani a baya nake horonka yanzu Ni horon duniya ce ina iya bawa me tunanin wacece Dr. Deenah mamaki saboda haka inason ka riƙe a ranka babu wata alaƙa tsakanina dakai a yanzu course ka saremin tun kafin wannan lokacin na tsaneka tun lokacin da ka fara fitomin da asalin kalarka banida wani hope akanka yanzu da wannan nake roƙonka ka fita a rayuwata..........."





“Ƙarya kike Madinah" ya faɗa yana nufota kamar wani mayunwacin zaki taja baya da sauri ya ritsata a jikin bango ya rufota ta rintse idanunta yayo ƙasa da kansa daidai kunnenta yace “Ban zaci wannan zai zama sakayyar ƙaunar dana nuna Miki ba Ɓingel ki ɗauka ma nine na fitar da wannan videon da yasa kika yanke wannan hukuncin akaina shin na cancanci wannan butulcin daga gareki? A gurin duk wanda yasan halacci zaice a'a koda yake babu mamaki goyon ɗan mage nayi saidai inaso ki riƙe a ranki zan aureki in har Allah ya ƙadarta keɗin matata ce Madinah banma taɓaji a raina keɗin ba matata bace, sannan maganar aurenki da Khamal na rushe ta babu ita........





Juyawa yayi ya nufi ƙofa ya fice ta bishi da wani mugun kallo tace “Aikin banza sai kayi da wata idan na bar muku ƙasar sai kaci kanka" komawa tayi ta kwanta Hamma Hussain ya fara bata ciwon kai batajin zata iya jurewa wannan baƙin halayen nasa dole ma ta nemawa kanta mafita kodai ta karɓi appointment ɗin da WHO suka bata zuwa German?" Ita kaɗai taketa tufkawa da warwarewa ta rasa tudun dafawa a daren ta shiga Gmail ta cike takardun appointment ɗin da aka turo mata ta gama ta tashi tayi alwala yauma kamar jiya abinda Mal Hamza ya faɗa mata shi tayi sannan ta sake kwanciya washegari da wuri ta fice a gidan ta nufi gidan Yaya Mus'ab suka gaisa da Kharimatu matarsa suka zauna suna taɓa hirarsu Mus'ab ya fito daga ɗakinsa ya zauna suka gaisa yace “Tace Ka bincika min abinda tafiyar zataci kuwa?" Shafa kansa yayi yace.

“Eh mun fara magana dashi yau zanje mu ƙarasa ina fatan lfy dai ko?" Numfashi ta sauke tace “Inaso ne kawai nayima ƙasar nan nisa" dubanta yayi da rashin fahimta yace “Meye yake  faruwa ne ke ba ma'abociyar son zuwa gidan mutane bace Ɓingel akwai abinda yake damun zuciyarki fah banson ki fara ɓoyemin abubuwan da suka shafeki zaki ciremin ƙwarin gwiwa" 





Ƙasa tayi da kanta hawaye ya zubo mata tasa hannu ta share tace “Hamma Hussain ya takuramin ga fitinar su Baffa Sunusi ga Ammi kullum damuwarta ƙaruwa takeyi Yaya Mus'ab da wanne zanji, shiyasa nakeson barin ƙasar idan na kaucewa ganinsu ƙila su barni na sarara itama Ammi ta samu sururi" “Ammi bazata samu sururi ba har sai kinyi aure wanda nasan shine burin ta, kawai zan shiga maganar ne don ki samu nutsuwa" murmushi tayi tace “Gdy nakeyi abin ƙauna dama wani appointment na samu zuwa Germany so nan da sati biyu ne shine nakeson kafin wannan tafiyar na gama komai na waccan kaga saina tafi gabadaya tunda na fadawa Dr. Kaltingo kuma yace yayi na'am da tafiyar domin yanada labarin course ɗin yanada amfani matuƙa musamman yanzu da duniyar likitoci take ƙara samun ci gaba a duniya"





Murmushi yayi yace “Wannan ogan naki yanada kirki Ɓingel Saidai fatan Allah ya saka masa da alkhairi ke kuma Allah ya ƙara Miki ƙarfin gwiwar yin biyayya a garesa yanzu ina zaki naga shirin kamar bana office bane" darawa tayi tace “Kamar ka sani asibitin Dawanau zan shiga zan duba wasu marasa lafiya akwai wasu Sabbin petiant da na samu labarin akwai yiwuwar aiki za'ayi musu sana su sami salama"  

Miƙewa yayi yace “zaki iya zuwa dani nifa inajin bantaɓa shiga wannan asibitin naku ba" dariya tayi tace “Sai kazo muje ai Ni kaina ba son shiga asibitin nan nakeyi ba sau tari indai ba babban aiki ba Turawa nakeyi to yau ance saidai naje da kaina" suna tattaunawa suka fita har suka isa asibitin hirarsu sukeyi ta nishaɗi office na shugaban asibitin suka isa suka gaisa ta zaro ID card nata ta nuna masa suka sake gaisawa cike da girmamawa nan yayi mata jagora har cikin asibitin ɓangare ɓangare suna duba marasa lfy kawo kan marasa lafiyar da tazo gani ta dubasu tana duba magungunan da ake basu ta zaro wani  katin ta rubuta wasu magungunan ta bawa shugaban asibitin ta dubesa tace “a daina basu magungunan da ake basu aci gaba dayi musu amfani da waɗannan abinda ke akwai sai a sanar da asibitinmu akwai jerin kalolin cututtukan da aka ware za'ayi masu aiki nan da watanni shida idan da buƙatar aikin shan maganin nan dana rubuta zai nuna"





Sallama sukayi yanayi mata gdy har mota ya rakasu daidai inda sukayi parking suka tarar an parker wata babbar mota ƙirar sama daidai zuwansu daidai buɗe ƙofar motar, takaici ya rufe Madinah ganin yanda mamallakin motar ya rufesu kuma ko a jikinsa shirin fitowa ma yakeyi daga motar ta dubi Mus'ab kafin ya bata amsa ta nuna wanda ya fito a motar tace “Yallaɓai idan zai yiwu ka gyara parking zamu fita" wanda ya fito a motar ya juyo matashin saurayi ne baƙi faffaɗa irin matasan nan yan wanka.

Wani kallon wulaƙanci yayi mata yace “Idan babu halin fah Hajiya?" Zuba manyan idanunta tayi kan motar ta buɗe baki zatayi magana Dr. Jadda ya tako ya dafa saurayin yace “Ranka shi daɗe wannan baiwar Allah da kake gani Nima a ƙarƙashinta nake kayi hƙr ka gyara parking tazo ne domin ta duba marasa lafiyar da muke dasu masu babbar lalura......" A hassale matashin ya zame hannun Dr. Jadda a kafaɗarsa yace “kaine kake ƙasanta ni a ƙasana take koma wace ita, ita a haka takai matsayin da za'a zama a ƙarƙashinta batada ladabin magana....." 






“Nazeer!!!" Sukaji wata murya daga bayansu ta furta dukka suka waiga, wani matashin attajiri ne wankan tarwaɗa dogo ƙirar sarakai harɗe jikin mota sanye da farin boyal me sheƙi, idanunsa akan Dr. Deenah yace “Gyara parking banason faɗan rashin gaskiya da talakawa su ba jin kunyar cin mutuncin mu zasuyi ba, tsakaninka da talaka kawai ka taimakesu idan ka gansu a wani hali amma ba musayar yawu ba, kasani tun kafin kayi parking Saida nace karka rufesu" Ba ƙaramin duka kalaman mutumin sukayi mata ba a fili tace “Talaka?" Bai ko sake kallonta ba ya ɗauki wata ƴar yarinya ƙarama da bata wucce shekaru takwas ba ya saɓa a kafaɗarsa ya nufi cikin asibitin tabisu da kallo tare da taɓe baki a ranta tana raya irin maganar da zata mayar musu Mus'ab ya kama hannunta ya shigar da ita mota  yanda Zuciyarta take a kusan nan yasan idan ya barta komai zai iya faruwa Madinah bata iya fushi ba kuma bata ɗaukar wulaƙanci, ba itaba shima kalamin mutumin sun daki zuciyarsa dauriya kawai ya fita.

 Udanunta ne ya sauka akan number motar taga number ce ta musamman an rubuta AA Waziri taɓe baki tayi sukaci gaba da hirarsu da ɗan uwanta har sukaje Office ɗinta ta shigar da bayanan da zata shigar Yayi mata sallama ya fita Dr. Zahira ta shigo sukaci gaba da hirarsu lokaci zuwa lokaci kalamin wannan yaron na ɗazu da take kyautata zaton zata iya girmansa suna dawo mata tare da kalamin wannan mutumin da farkon fitowarsa a motar tayi masa kallon me hankali “AA Waziri" ta furta tare da furzar da iska aranta tana raya Allah ma ya sake haɗasu a gaba..............

[6/19, 8:29 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan 21-22_*




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment ta 09013718241_




Da mamaki Zahira ta dubeta tace “Waye kike fatan sake haɗuwa dashi a wannan duniyar?" Murmushi tayi ta tattare kayanta tace “ba haɗuwar alkhairi bace Zahira amma ina fatan Allah ya sake haɗani dashi ta hanyar da zan nuna masa ba talaka ne wulaƙantacce ba wanda ya raina talaka shine wulaƙantacce" 

Bata bawa Zahira damar sake magantuwa ba ta juya ta fice  a office ɗin dole itama Zahira ta fito suna tafe suna tattaunawa har sukaje ƙofar gdansu Zahira ta sauketa sukayi sallama ta nufi nasu gidan ranta a jagule, a tsayin shekarunta 35 an faɗa mata maganganun da sukafi wanda wannan mutumin ya faɗa mata zafi amma tashi ta tsaya mata a rai harma tanajin meye yasa bata rama ba tun a lokacin?

Hatta Ammi saida ta fahimci bata cikin walwala da dare da suka zauna Ammi ke tambayarta ta sanar da ita abinda ya faru Ammi Murmushi tayi tace “To banda ma abinki wannan har yakai ki damu kanki ita rayuwa ai kowa da irin fahimtar da yayi mata su a yanda suka fahimci tasu rayuwar kenan talaka ba abakin komai yake ba kuma bakida wata dama ta fahimtar dasu ba akan daidai suke ba saboda haka sanya damuwa akan abinda bakada ikon canzawa yakan zama rashin hankali da gajarce tunani kije kiyi abinda ke gabanki ki manta da babinsu shine zai faranta min rai" 





Tashi tayi tana murmushi tace “Amma Ammi kinsan ba'a taɓayimin abinda naji bazan iya yafewa kamar wannan ba? Ina fatan kada Allah ya sako wata dama tasu a hannuna wlh sai sun yara wahala kafin nayi Inma zanyi ɗin kenan"

Daƙuwa Ammi tayi mata tace “Shidai Allah yanason mutum me yafiya akan abinda akayi masa ya baƙanta ransa har yayi ƙunci" bata sakeyin magana ba ta nufi ɗakinta ta ɗauki system ɗinta tana daddanawa lokaci zuwa lokaci tana duba agogo ganin dare yaja ne yasata kwanciya har zuwa lokacin zuciyarta bata gama sanyi ba.

Cikin kwanakin da suka gabata abubuwa da yawa sun faru masu daɗi da akasinsu kamar yanda Mal Hamza ya umarce su bayan sati guda da zuwansu suka koma tayi masa bayani kamar yanda ya buƙata yayi shiru na dogon lokaci can ya ɗago ya dubeta sosai yace “kuma Munawwara cikin satin nan bazaki iya tuna wani da kuka haɗu ba kodai daɗi ya haɗaku ko kuma akasin haka, ko s gurin aiki ko a kasuwa ko a kan hanya?" 





Shiru tayi tana nazari can ta ɗago tace “Wlh na kasa tunawa Mal" Murmushi  yayi yace “Shikenan Ni na hango abinda baki hango ba kije kici gaba da addu'a saura ƙiris nasan idan lokacin yayi zaki tuna da komai" gdy tayi masa suka tafi iyakar tunaninta ta kasa tuno wani abu, daga nan gurin shirye-shiryen tafiyarta ta wucce ta gama komai sannan ta dawo gida zata fara zuwa Germany ne tayi wata biyu daga can zata wucce Rasha.

Tayi wata shida ranta wasai farin ciki takeyi da tafiyar domin tasan zata huta da jarabar danginta da suka sanyata a gaba ga Hamma Hussain daya ƙaro wulaƙanci kullum cikin tuhumarta yake tare da ƙalubalantar watsin da tayi dashi ita kuma Allah ya sani bawai sonsa ne ta daina ba a'a sabuwar rayuwar daya tsiro da ita bayajin kunyar taɓa jikinta kullum burinsa ta bashi dama ya nuna mata kalar tasa ƙaunar practical ita a tunaninta koda zatayi wannan rayuwar shikam ba abokin yinta bane bare ma bata taɓa fatan hakan ga waninta  ba bare ita kanta.

Da wannan ta tattara ta sauka a ƙasar Jamus ƙasa me cike da albarka saidai sanyin da yaso ya takurata amma tanajin daɗin rayuwa a ƙasar babu ruwan wani da wani, ta rasa meye yasa turawan suke matuƙar bata girma idan sukaji matsayinta musamman sukan raina ƙananun shekarun da suka kaita wannan matsayi, Seminar da ta kaita Garman sati huɗu ta ɗauketa.





Ta huta na sati biyu sannan ta wucce Rasha ta fara abinda ya kaita hankalinta ya kwanta duk ta sauke layukanta na 9ja saboda ta samu damar yin abinda ya kaita ko sabuwar number data saka daga Amminta sai yayyanta sukeda ita sai Dr. Kaltingo da Dr Zahira da tabar asibitinta a hannunta ta gurinta takejin yanayin gudanarwar, hankalinta ya kwanta sosai batada damuwar komai.

Kullum da safe zata fita taje asibitin da take course ɗin ta dawo da yamma ƙwarai hukumar asibitin suka yaba da kwazonta sun jima basu samu likita me kaifin basirarta a wannan asibiti ba aikuwa nan sukayi mata cahhh suka fara zawarcinta suna aikawa da shugabancinta cewar suna buƙatar abar musu ita, to itama ta ɗan kwaɗaitu da son zama dasu saidai Amminta tana ranta bazata iya barin Amminta da zaman dindindin ba, ko a cikin ƙasar tana ganin yanda Ammi take shiga damuwa idan taga bata kusa da ita bare kuma ace ta tafi tafiya doguwa irin wannan ta ba yau ba ba gobe ba dole da damuwa.

Wannan shine ya hanata karɓar tayinsu ta dai ci gaba da lallaɓawa ya rage saura wata ɗaya ta gama course ɗinta ne suka bata wani aikin bincike da zai dauketa wata biyu steel bataji dadin karin lokacin ba saidai babu yanda ta iya wai a haka ma sunyi mata da ƙauna.





Tayi nisa cikin wannan aikin bincike ne wani dare ta dawo daga hospital ta gaji sosai saboda sunyi yawo sosai a ranar, tana kwance tayi ruf da ciki tana duba yanayin yanda project ɗin nata yake kasancewa  wayarta ta soma Ring bata ɗauki abinda wasa ba ta jirkito ta ɗaukota tasan ɗayan uku ne kodai ƴan gdansu ko kuma aminiyarta ko Dr. Kaltingo kodai ɗan nacinta Hamma Hussain da a yanzu lamuransa suka fara bata tausayi Bilkisunsa ta rasu a dalilin haihuwa gashi ta barsa da yara biyu shi kuma tayi masa wulaƙancin ya barta ya kasa barinta zuciyarta ta fara ayyana mata kodai bashi dama zatayi a karo na ƙarshe? 

Wata zuciyar kan gargaɗeta kwana biyu ta samu salama daga ƙwarzabar dangi idan ta kuskura ta dawo da maganarta da Hamma Hussain sabuwa to zata koma ruwa ita kuwa da wancan yanayin daya wucce ya dawo gara ta ƙarshe kwanakinta babu auren duk da tana tsananin buƙatar mijin musamman a wannan lokacin da take jin tabbas tanason namiji feeling ya fara cutar da rayuwarta kullum ita kenan shan ƙwayoyin da zasu rage mata zugin azabar da take ciki amma kullum lamarin kamar kara ta'azzara yakeyi.

Kara wayar tayi a kunnenta da sassanyan sexy voice ɗinta tayi masa sallama ya amsa da walwala yace “Dr. Deenah ina fatan kina cikin aminci waɗannan Rashawan basu takura Miki ba don nason so da masifar son African women"





Murmushi tayi tace “Allah dai yana tsallakar damu kamar yanda ya saba tsallakar damu a nan ɗin ma Dr. Ya Nigeria ina missing chakwakiyar ƙasata duk sai nake jina wata daban nan ba hayaniya babu sa ido ba ruwan wani da wani rayuwar dai gwanin daɗi amma ta ƙasata tafita daɗi tafita ƴanci" 

Dariya yayi yace “Dr. Kenan kinada abin dariya Am wato Dr. Wata petiant muka samu take neman bawa kaina ciwo, yarinyar wani Sanata ce me wakiltar Gombe central ta samu wani irin ciwo na ƙwaƙwalwa me wuyar sha'ani da wuyar magani an fita da ita ƙasashe sunfi goma amma kullum babu wani sauƙi a ciwon shine nace bari na kiraki don nasan kinason irin wannan isue ɗin"

Gwauron numfashi ta sauke ta tashi zaune tana gyara bra ɗinta tace “Meye asalin samuwar ciwon na haihuwa ne ko kuwa daga sama ta sameshi?" Fasali ya sauke yace “Wato shekara bakwai baya sunyi tafiya da mahaifiyarta Nasmat daga Gombe zuwa Abuja a mota a wannan tafiyar ne suka samu gagarumin hatsarin mota wanda yayi sanadiyar mutuwar Nasmat da Drivern su ita kuma yarinyar Nusaiba ƴar shekara uku a lokacin ta samu karaya biyar a jikinta wanda hakan ne ya hana asalin wancan ciwon bayyana sai daga baya aka ga kanta yana kumbura tana firgita nan hankalin mahaifinta ya tashi domin ya ɗauki son duniya ya ɗorawa wannan tilon ɗiyar tasa ko kaɗan baison abinda zai taba nutsuwar yarinyar, sake gyara zamanta tayi tace “Waye mahaifin nata kuma wanne asibiti da wanne aka kaita?" Jin ta  bawa abin attention yasashi cewa “Senetor Abdurrahman Abba Waziri Wato AA Waziri..........."

[6/19, 8:29 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan 23-24_*




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1


Durowa Madinah tayi daga gadon da take kai da sauri tace “Abdurrahman Abba Waziri, AA Waziri?" Jinjina kai Dr. Kaltingo yayi yanaci gaba dayi mata bayanin da bata fahimtar komai a cikinsa  bai san meye yake faruwa ba saida yaji taja gwauron numfashi ta sauke tace “Ya isa Dr." Shiru ta kuma ratsawa can tace “Allah ya bata lfy Dr. Zan kwanta gobe in Allah ya kaimu inada fitar wuri zuwa wani guri banason African time shiyasa nakeson kwanciya da wuri" baiji daɗin yanda lokaci ɗaya yaga yanayinta ya sauya ba yace “Ok Dr ki kwanta mayi mgnr da safe" aje kan wayar tayi sunan da Dr. Kaltingo ya faɗa mata yanaci gaba dayi mata yawo a kwanyarta tana tuno Number motar mutumin da yaci mutuncinta ranar da sukaje Asibitin Dawanau ita da Yaya Mus'ab tabbas Inma ba shine ba to makusancinsa ne a cikin motar, irin wannan zuriyar basu dace da tausaya ba domin suma basa tausayin kansu"





Bawa zuciyarta hutu tayi ta hanyar gyara kwanciyarta washegari babu inda zata don haka ta yini tana research akan irin lalurar da Dr. Kaltingo ya sanar da ita jiya ta jima da sanin ciwon amma bata taɓa bada hankalinta wajen bincike akansa ba domin ba ciwone da yake yawan samuwa ba amma ciwo ne me wuyar sha'ani, bawai don taji tanason duba petiant dinba a'a saidon ta ƙarawa saninta ƙarfi game da harkarta, yini tayi tana abu ɗaya daga wannan shafi zuwa wancan sallah da abinci sune suke dakatar da ita har yamma sannan ta rufe tayi wanka ta fice daga gidan ta nufi wani gurin hutawa.

Anan ne zuciyarta ta rinƙa raya mata tayi ɗan ƙaramin research kan AA Waziri Murmushi tayi ta ɗauki wayarta ta kunna layin ta na Nigeria ta lalubo number Dr. Jadda bugu biyu ya ɗaga yana cewa “Allah ya taimaki likitan likitoci na nemeki har nagaji da cigiya sai daga baya nakeji ashe ƙasar kika bari" murmushi tayi tace “Dr. Kenan ya aiki ya fama da petiant?" Numfashi ya sauke yace “Munata fama ya Rasha?" “Alhmdllh" ta amsa tare da sauke numfashi tace “Ka tuna lokacin da nazo duba marasa lafiya asibitinku nida Yayana kafin barowata Nigeria? in baka manta ba akwai wasu mutane da sukayi bad parking har mukaso yin hatsaniya da Drivern a ƙarshe me gidansa ya fito ya faɗi abinda yakeso suka tafi, shin zaka iya tunawa?" 





Murmushi yayi yace “Ƙwarai kuwa ranki shi daɗe ban manta ba ai ranar Nima naji babu daɗi sosai" ajiyar zuciya tayi tace “Meye abinda ka sani game dasu?" Shiru ya ɗanyi me tsayi sannan yace “Yaron da kukaso kuyi hatsaniyar dashi ƙanine ga wannan mutumin sunansa Nazeer Abba Waziri shikuma wanda ya fito daga bayan Sunansa Sanata Abdurrahman Abba Waziri mutanen Gombe ne a lokacin da kuka haɗu dasu sun kawo wata ƙaramar yarinya ne sakamakon ciwon taɓuwar ƙwaƙwalwa da take fama dashi......." 

“Ya isa ranka shi daɗe iya haka ma ya wadatar" “Amma Dr meye yasa kike tambaya game dasu? Ko case na rashin lfyr yarinyar yazo hannunki ne?" Girgiza kai tayi kamar tana gabansa tace “Eh to yazo baizo ba taimako na gaba shine zaka ɗaukomin hoton file na yarinyar ka turomin inason nayi bincike ne game da ciwonta" 





Tana aje wayar kiran Dr. Kaltingo ya shigo suka gaisa ya tambayeta game da maganarsu ta jiya tayi murmushi tace “Wato Dr. Yarinyar tana buƙatar kulawa matuƙa nayi bincike yau sosai game da ciwon ina tunanin ta samu ciwon (INCREASED INTRACRANIAL PRESSURE) wanda yake samuwa dalilin buɗewar  hanyoyin gudanar jini (BLOOD FLUID & CEREBROSPINAL FLUID(CSF) Dr. Wannan ciwo yanada wuyar sha'ani yanada wahalar magani gsky domin ba kowanne asibiti ne suke da kayan gwajinsa ba, am abu ɗaya da zan iya yi cikin wannan lamari shine ka faɗa musu suje France zan rubuto masu sunan asibitin da suke wannan aiki na toshe hujewar da jijiyoyin ƙwaƙwalwa sukayi amma fah Dr. Kasani aikinmu ƙila wa ƙala ne idan Allah yaso ta tashi zata iya tashi saidai har zuwa yanzu cikin kaso dari da akewa aikin nan kaso uku ne ke iya tashi sauran duk suna mutuwa ne sannan fah Dr. Har yanzu ba'a gano engine da zai yi aikin a warke gabaɗaya ba anayinsa ne duk bayan lokaci, ina ganin wannan bayanin zai taimaka musu wajen shawo kan matsalar"





Numfashi Dr. Kaltingo ya sauke yace “Amma Dr. Zan so a matsayinki na ƙwararriya kuma jajirtacciya data saba taimakawa ki samu lokaci kiga Nusaiba nasan ganinki da ita zaisa ki tausaya mata wala Allah ma kiji a ranki zaki iya tallafar rayuwarta"

Murmushi tayi da yake sanyaya masa gwiwa tace “Banason haɗawa kaina aiki ne Dr. Nan inada wasu manyan project guda biyu da suka sanya lkcna ya ƙaru gashi akwai wasu petiant da nake kula dasu ciki harda me irin ciwon Nusaiba please Dr. Kaima zaka iya nikam gsky banji a raina zan iya wannan aikin ba musamman danasani idan na shiga zanyi wuyar fita saidai ɗayan biyu ta faru ko dai Nusaiba ta dawo Kano ko kuma Ni na koma inda suke nikuma gsky bazan iya barin garina ba.

Bama wannan ba nifa Dr banjin zan iya wannan aikin ne"

Katseta yayi da cewa “Amma Dr. Bansanki da irin wannan ɗabi'ar ba meye yasa zaki tsireta lokaci guda haka aikinmu munayi ne da son abun da kuma hope akai saidai yanzu naga kamar kin cire hope Dr. Meyesa" dogon numfashi taja ta sauke ta buɗe baki muryarta can ƙasa tace “Inada dalili Dr kayi abinda ke gabanka inka samu dama ka taimakawa Nusaiba Allah ya bata lfy koda addu'a na tayata nayi hoɓɓasa basai nakai ga taɓa jikinta ba" ƙitt ta tsinke layin tana ganin ƙimar Dr. Kaltingo amma batajin zata iya tsinka burinta tabbas wannan wata dama ce da Allah ya bata na ta rama abinda ya jima yana kartar zuciyarta saidai kuma dole saita iya takunta batason Dr. Kaltingo yasan dalilinta so takeyi sai ta ja rawanin AA Waziri a ƙasa ta nuna masa tabbas shima talaka yanada rana, 

Miƙewa tayi tana zagaya ɗakin tana saƙa hanyoyin da zatabi wanda dole sai an nemeta, murmushi tayi tace “Insha Allahu zanyi duk me yuwuwa naga baki mutu ba Nusaiba don idan kika mutu shiri na ya rushe kiyi haƙuri naso taimakonki halin mahaifinki ne zaija sauƙinki da nisa.........."





Kuyi hkr da wannan na ɗan shiga busy ne.

[6/19, 8:29 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan 25-26_*




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1




        *BONUS PAGE*




Komawa tayi ta zauna tana Murmushi a ranta tana raya irin ƙudurin dake zuciyarta da wannan ta tashi tayi wanka ta kwanta tare da kiran Ammi a waya sukayi hirarsu sun jima sosai sannan sukayi sallama kiran Zahira ya shigo tace “Dama yanzu nake shirin kiranki meye asibiti yake ciki?" Murmushi tayi tace “komai yana tafiya daidai mun samu ƙarin ma'aikata ma daga UNICEF" jinjina kai tayi tace “Nagaji da zaman ƙasar nan kuma kullum dalilan zamana ƙaruwa sukeyi" murmushi Dr. Zahira tayi tace “kinajin daɗinki Ni yanzu wani abune ya tunkaroni da yake neman fin ƙarfi na Dr. Wani cousin ɗin Daddyn Noor ne ya fito waishi sona yakeyi zai aureni na nuna masa a'a banaso amma kullum maganarsa ƙara ƙarfi tskeyi ke yanzun har yakai kansa gurin Baffanmu shi kuma ya kirani yake faɗa min ya yaba da nutsuwarsa amma me nagani, to kaina ya kulle Naseer bashida matsala gsky a kankin kansa saidai matarsa Samira tanada mugun kishi wanda Ni nake ganin kamar bazan iya auren mijinta ba"





Dariya sosai kalmar ta ta ƙarshe tabawa Madinah Saida tayi me isarta tace “Kinada abin dariya Dr. Zahira mata suna tsorataki toke yanzu kina tunanin samun saurayi ne wanda bashida mata ko kuwa kina tunanin zaki samu matar da bata kishin mijinta ki aure mata? Kema kinsan bame yiwuwa bane dole ne cikin biyu ɗaya ta faru kodai ki auri Naseer ko kuma ki auri waninsa, Dr. Zahira koni a yanzu raina baitaɓa bani cewa zan auri saurayi ba saboda haka duk shirina na zama da kishiya ne mu goga kowa tasa ta fisshe shi, Ni ina ganin indai kinason Naseer to ki bashi damar fitowa kuyi aure kema kya samu nutsuwarki ta dawo sai kuci gaba da tayamu addu'a muma Allah ya kawo mana karshen kaɗaici" 

Jinjina kai Dr. Zahira tayi cikin yarda da kuma tausayin aminiyar tata tace “shikenan na amincewa shawararki zan faɗawa Baffa na amince Allah yasa alkhairin kenan Madinah wlh kullum inayi Miki addu'a bantaɓa rokawa kaina miji na gari batare da nasaki a ciki ba kuma inaji a jikina yana gaf da bayyana yanzu yaushe zaki dawo Nigeria ko kuma mune zamu biyoki?" 





Sunsha hira sosai sai wajen biyu na darensu Madinah sannan sukayi sallama sunayi sallama taga saƙon Dr. Kaltingo ta email kamar ta bari sai Saida safe saidai yafi gaban haka a gunta batasan dame yazo mata ba haka ta buɗe tare da tashi zaune tana karanta saƙon “Likita a kullum burinsa yaga al'ummar da yake cikinta sun rabu da ciwuka sun zauna lafiya, likita a kullum burinshi taimakon al'ummah likita a kullum burinsa sanya dariya da farin ciki a zuciyar me ciwo, shin Dr ki kalli yarinyar nan da idanun Rahma dame zaki iya taimaka mata? Likitoci sun bada shawarar dole ne a samu ƙwararren likita ya kasance da ita a kowanne lokaci domin tana buƙatar kulawa ta musamman don tabbatuwar lafiyarta, mahaifinta Abokina ne ya taimakeni a rayuwa Dr. Inason gusar da ƙuncinsa ta hanyar zama silar samuwar lafiyar gudan ƴarsa ɗaya tilo gashi ni girma ya hauni bayan haka bangaren a yanzu ya girmeni saboda yanayin shekaru ya tabbata sai irinku masu ƙuruciya kune zaku iya wannan sadaukarwar.

Dr. Na bawa Hon. AA Waziri labarinki ya roƙeni alfarmar yi Miki tayin kwangilar so na sanar dashi bakida ra'ayi domin mun fara maganar dake yace na bashi number ki kuyi magana ke dashi don Allah ki bani dama na bashi number ki ina faɗa Miki gsky ne AA Waziri yafi ƙarfin komai a gurina kiyi don ni Dr. Madinah wannan shine karon farko dana nemi alfarma a gurinki....."





Gabanta ne ya faɗi ta rinƙa bin hoton da kallo yarinya kyakkyawa da bata wucce shekaru goma ba amma da ganinta kasan ta tawaya cikin alamun tausayawa ta rubuta masa “ok” ta aje system ɗin ta kwanta kasancewar ba sallah zatayi ba taci gaba da latsa wayar yanayin garin ya fara sabar da ita rashin baccin dare hakana ta cinye daren wajen tufkawa da warwarewa sai asuba ta tashi tayi wanka tai alwala sannan ta samu baccin ya ɗauketa cikin baccin taji wayarta tana ruri ta wawurota ta danna a kunnenta jin Muryar Dr. Kaltingo yasata wartsakewa yace “Sorry na tasheki dama Hon. AA Waziri ne yace ya kiraki baki ɗagaba" Hamma tayi tace “Eh lkcn daya kira lokacin daga wayata baiyi ba yanzun kuma ya wucce zanyi wanka na fita kace ya kirani 8:00pm" shifa Dr. Kaltingo mamaki sha'anin Madinah ke bashi yaja fasali yace “Ok babu damuwa insha Allahu zakiji shi lokacin da kikace" tare suka ajiye wayar ta tashi ta fara shirin fita. 

Lkcn data dawo rututu ta tarar da misscall bata saurara ba Saida tayi wanka ta zauna ta buɗe system ɗinta wani kiran ya shigo ta jima tanabin number da kallo kafin ta ɗaga tare da sallama, a tausashe aka amsa mata ta lumshe idonta duk da ba wani sani tayiwa Muryar ba amma ta gane wani ɓangare nata take wutar dake cin zuciyarta ta ruru sabuwa har taji kamar ta kashe wayar saidai Dr. Kaltingo ne a tsakiya dole ne tayi danshi saboda yayi mata abubuwan da ba wannan alfarmar ba ko tafi haka ya nema sai tayi masa.





 

Batakai ga magana ba yace “Sunana Abdurrahman Abba Waziri nasan sunana bazai zame Miki ɓatacce ba Dr. Mansur Hassan Kaltingo ne ya bani number ki" taɓe baki tayi tace “Ya sanar dani zaka kira" cikin faɗuwar gaba Hon AA Waziri yace “kamar naso nasan Muryar koda yake muna harkar mutane ƙila me irinta ce am yanzu meye kika tsara game da petiant ɗinki?" 

Sake gyara zamanta tayi tace “Naso nayiwa Dr. Kaltingo bayani saidai naga kamar bazai fahimceni ba Hon. Ciwon yarinyarka yana buƙatar kulawa saidai niɗin daya zaɓa don bata kulawa abubuwa sunyi min yawa yana maganar 1 week ne Ni kuma a ƙallah zan ɗauki tsawon 7 weeks kafin na gama abubuwan da nakeyi so bansan yane za'ayi ba....." 

Katseta yayi da cewa “Kada kiyimin haka don Allah ki taimakeni kada Nusaiba ta rasa rayuwarta Dr. Ki faɗamin da wanne irin kuɗi kikeso na rinƙa biyanki Naira, dollers ko......" Dakatar dashi tayi da sauri da kalmar data soki zuciyarsa tace “Abdurrahman Abba Waziri, Sunana Madinah Alƙasim Gwangola talaka ce ni amma kai bakada kuɗin da zaka iya biyana ladan aikina idan nayi saboda haka ka adana ƴan canjikan ka da basu wucce liƙin evant ba nasan zasuyi maka amfani a gaba, zan bar duk abinda nakeyi don Nusaiba da rayuwarta na dawo 9ja nan da kwanaki biyar saboda haka ka zama cikin shiri, abu ɗaya da nakeson ka faɗamin Yanzu haka Nussy tana ina? Abuja gdanka ko Gombe gurin Hajiya Babba...." Dubanta takai ga agogo takwas da rabi ta cire wayar a kunnenta tare da cewa “Lkcn dana ɗauka don saurararka ya ƙare zan koma kan aikina letter"





Ƙit ta yanke wayar yabi wayar da kallo cikin faɗuwar gaba da ƙaruwar bugun zuciya yakebin sensor ɗin da kallo mamakinsa na ƙaruwa zuciyarsa na tafasa ya ɗaga wayar ya kira Dr. Kaltingo yace “Wacce irin yarinya ka haɗani da ita?"

Da mamaki Dr. Kaltingo yace “Meye ya faru?" Ajiyar zuciya ya sauke yace “Waye mahaifinta a Nigeria da takejin kanta haka?" Tashi zaune Dr Kaltingo yayi yace “Wai Dr. Madinah kake nufi? Hon Ba ƴar kowa bace hasali ma marainiya ce da bata taso da gatan mahaifi ba naci da jajircewa sune suka ɗorata a matsayin da take yanzu nasan tanada izza akan aikinta amma tanada sanyin hali akan yanayin rayuwa Hon. Dr Madinah mace ce ta kwatance domin takai kuma ta doke matsala ɗaya cikin abinda ka nema shine ba lallai ta amincewa barin aikinta don aikin Nusaiba ba tana ɗaukar albashin da har yanzu bana ɗaukar kamarsa tana da hanyoyin da suke kawo mata kuɗin da bata ɗauki kuɗi a bakin komai ba, may be kaje mata da maganar kuɗine ita kuma basa cikin abinda suke ruɗarta shiyasa kaga rashin kirkinta"





Numfashi ya sauke yace “Tace zata dawo nan da 5 days Nussy tana Gombe Ni zanyi tafiya ne zuwa Cairo Dr. Na wakiltaka akan komai daya shafi lafiyar Nussy nasan banida matsala dakai insha Allahu"

Duk yanda yaso ya manta da kalaman Madinah ya kasa yawo sukeyi masa a ƙwanya shi kamar shi ta gayawa waɗannan zafafan maganganun shikam zaiso ganinta da abinda take taƙama dashi a duniyar nan.





Kamar yanda tayi masa alƙawari hakan ce ta faru suna waya da Dr. Kaltingo akan duk abinda ya shafi Nussy ita kuma tana ƙara bincike da tattara bayanai, daƙyar ta samu asibitin da tayi course ɗin suka bata certificate ɗin ta tare da kyaututtuka na wasu muhimman kayan aiki taji daɗi matuƙa hakanan basaso suka kawota airport ta hau jirgi tare da alƙawarin duk lokacin data samu free zatake kawo musu ziyara saboda ba ƙaramin sabo sukayi ba.

A filin jirgin saman Abuja ta sauka tana sauka ta hango Dr. Kaltingo tsaye jikin wata mota ta zubansa idanu tanayi masa murmushi shima murmushin yayi mata ya nufota tare da karɓar jakar hannunta yace “Wlcm back Dr." Murmushi tayi tace “Dole mana tunda kun tasoni...."  Maganar ce ta maƙale lkcn da sukayi idanu biyu da Nazeer ƙur ya ƙura mata idanu itanma shi take kallo a wulaƙance tace “Wannan fah Dr." Murmushi yayi yace “Autan Hajiya Babba kenan" sake kallonsa tayi ta kawar dakai ya sake saita Engine idonsa akanta, Dr ya buɗe mota motar ta shiga tana cewa “Dr. Ayimin booking a yau komai dare gdan Ammi na naka kwana" tayi mgnr lokacin da motar take tashi ta sulali titin Asokoro gaban wani babban katafaren gida Nazeer yayi parking tare da horn get man ya buɗe masa ya sunna matar ciki yayi parking a rumfar aje motoci ya buɗe kowa ya fito yanayin gini da tsaruwar gidan yakai ta daga kai ta kalleshi amma ba lokacin wannan bane Nazeer ne yajasu har zuwa cikin babban parlourn gidan ya basu gurin zama tare da dauko musu lemo ya nufi wata ƙofa yana kiran “Hajiya! Hajjaju ki fito kinyi baƙi"





Wata dattijuwa ce riƙe da hannun Nusaiba ta fito tana cewa “Kaikam kira kamar sanƙira to gani baƙi ko nace baƙuwa sannu da zuwa kinsha hanya" murmushi tayi tace “Wlh Hajiya ya gida da me jiki kuma?" Zama tayi suka kuma gaisawa tace “zo Nusaiba" babu musu ta iso gareta ta janyota ta zaunar da ita a cinyarta tace “kina zuwa school?" Turo baki tayi tace “Daddy ya hanani wai banida lfy mommy kema Kinga banida lafiyar?"

Yanda tayi mgnr tana saƙalo wuyan Dr. Madinah yabasu dariya Dr. Madinah tace “Kuma kema kin yarda bakida lafiyar?" Ɗaga kai tayi tace “Daddy na yana yankani yana soyani kuma yana kaini Other country" gabaɗaya sai taji yarinyar tana wani shiga ranta tace “Ok kinashan magani?" Hajiya Babba ce ta katseta da cewa “Dr. Idan kika biyewa shirmen yarinyar nan bazakiyi abinda ya kawoki ba" ɗagowa tayi tace “Shima hakan cikin aikina ne Hajiya"

[6/20, 9:24 PM] Am Oum Hairan: Dr Madinah sake mayar da dubanta ga Nusaiba tayi tace “Amma kamar Naji ance bakison shan magani ko meye dalili?" Turo baki yarinyar tayi tana dafe kanta tace “Mommy sune da wannan da wancan suke takuramin sai nasha kuma suke.... Me mah uhm.... Na manta" murmushi Dr. Deenah tayi ta dubi Hajiya Babba tace “Hajiya ko zan iya ganin magungunan da akewa Nusaiba amfani dasu?" 

Miƙewa Hajiya Babba tayi tace “Meye zai hana likita bari na ɗebo Miki dama shekaran jiya kafin Daddynta ya tafi yaje ya siyo mata su wani likita ne ya rubuta mata su" tana maganar tana shigewa ciki suka kalli juna da Nazeer ya sosa kai yaso ganeta saidai ya rasa inda da kuma lkcn daya santa wannan dalilin yasa yaketa satar kallonta ko zai tunano inda ya taba ganinta.





Bayan ta gama duba magungunan tanayi tana duban Nusaiba ta ɗago tana saita idanunta kan Hajiya Babba tace “Zaa daina bata maganin nan zuwa lokacin da zan gama bincikena game da abinda ya dace ayi mata yanzu zan wucce Kano Ni yau zuwa jibi idan Allah ya kaimu zaku zo za'ayi mata wasu gwaje-gwaje anan asibitinmu" tana faɗin haka ta mike ta dauki jakarta takai dubanta ga Dr. Kaltingo shima ya mike Hajiya Babba tace “Amma Dr. Da kun bari sai gobe kwa tafi wannan tafiya da kika ciwo ne nisa ga yammaci tayi liƙis haka" 

Murmushi tayi tace “na gde Hajiya ai ba'a dare a gida" tana mgnr tana fita ko tayin da Hajiya Babba keyi mata na abincin da suka tanada dominta taƙi amsawa ta fice ta jira Dr. Kaltingo a jikin motar nan ya fito da kaya niki-niki yasa a but ya shiga taja suka nufi airport sukan taɓa hira har suka kai ta kuwa yi saa dake abin da alfarma  lokaci bata wani bata lokaci ba suka tashi zuwa Kano Yaya Aminu ne yaje ya ɗaukota suka rungume juna cike da farin ciki tace “Hamma Aminu kaima ka zama magidanci" dariya yayi yace “Ƙanwata kenan ke bakiga yanda kika zama babbar mace ba" dariya tayi tace “to ya zanyi kun taramin yara sun baibayeni yanzu fah kaima yaranka huɗu oh Ni Munawwara Allah dai ya kaini Nima naga nawa na goya" murmushi yayi yace “Amin Ɓingel in layi naja ai na baya zai samu lokacine"





Da wannan hirar suka shiga unguwarsu an ƙara gyarawa Ammi gidanta yayi masifar kyau ya fito da layin sosai taja ajiyar zuciya yanzu kam burinta ya cika ita da ƴan uwanta sun gyara gidansu babu wanda zai musu kallon raini, parking yayi a gurin parking na gidan ta fito ta shiga da gudunta tana cewa Ammina......" 

Fitowa Ammi tayi da sauri tare da riƙe haɓa tace “Oh Ni Adiyyah dama ashe ke yaron nan zaije ɗaukowa ɗan ƙaniya yacemin zance zashi" dariya sukayi suka baje a tsakar gidan suna gaisawa da hirar yaushe gamo ta kwanta cinyar Ammi tace “Ammi nayi missing cinyarki da yawa fah saidai na rungumi pillow in kaɗaici ya dameni nayita ƙunci ni kaɗai...." Sallamar da akayi ce ta katse mata surutun nata ta ɗago sukayi idanu hudu ta kawar dakai tare da yunƙurawa ta mike zatabar gurin ya riƙo hannunta ta juyo da wani irin zafi ta sauke masa zafafan idanunta da suka sanyashi saurin sakin hannunta yace “Wlcm back My Wyf" kallon data sake watsa masa duk da kasancewarsa dakakken namiji Saida ta faɗar masa da gaba ta juya ta faɗa ɗakinta yanaji tayima ƙofar key.

Takaicinsa har wuya haka ya dawo suka gaisa da Ammi yace “Ammi Ni narasa meye yasa Ɓingel takeda ruƙon masifa takasa yafemin laifin da take zargina akai" Murmushi Ammi tayi tace “Hussaini ai kunfi kusa da Ɓingel kuma zan iya cewa kafini sanin halinta domin kaine amininta kafin tasan kanta inaga kaci gaba da haƙuri zata sauko fah....."





“Bazan sauko ba" sukaji ta furta lokacin da take fitowa tace “Ba fushi nakeyi dashi ba damar biyayya na bashi Ammi Mahaifinsa da mahaifiyarsa basason alaƙata dashi meye yasa bazai nemi wacce ransu zaiyi daɗi da itaba wlh tallahi Ammi Hamma Hussain ya cika naci Hausawa fah sunce idan so cuta ne hƙr magani ne, Ammi nafi Hamma Hussain buƙatar abokin rayuwa saidai son na samu abokin rayuwa bazaisa kuma naƙi yima iyayena biyayya ba wannan dalilin yasa na ciresa a lissafina yaje ya rayu kawai" Miƙewa yayi zuciyarsa a karye yace “Koda kin daina sona Ni zan rayu dake Ɓingel banida burin takura rayuwarki amma ina ƙaunarki ƙauna ta jini saboda haka ki shiryawa zama amarya ko ranki bayaso" dariya tayi tace zanji kuma zangani"





Bai saurareta ba ya fice daga gidan ita kuma ta shiga kitchen ta kunna gas ta ɗora ruwa yayi dumi ta sauke ta koma bathroom na ɗakinta tayi wanka tayi sallar magrib da Isha sannan ta miƙe, bata jima da kwanciya ba wayarta ta ɗauki ruri ta lalubota tana duba number Nussy ta gani kamar yanda tayi saving number AA Waziri da ita kamar ta ajiye tunawa dole suyi communicating tunda ya ɗauki ragamar lfyr ƴarsa ya damƙa a hannunta, a kasalance tayi masa sallama ya amsa tare da cewa “Meye bayani game da Daughter?" Murmushi tayi taja numfashi tace “banfara aiki akanta ba nadai duba yanayinta ne ranar Monday inason a kawota asibitinmu Kano akwai wasu gwaje-gwaje da za'ayi mata sannsn na dakatar da shan magungunan ta har sai anyi gwajin abinda ya nuna sai asan abinyi a gaba am wannan shine abinda ke akwai"





Ya rasa meye yasa yakejin kamar yasan muryarta sannan yanayin sanyin maganarta yake sanyashi kasala, a gajiye yace “Ok tanks" daga haka ya kashe wayarsa bata wani bawa hakan muhimmanci ba ta gyara kwanciyarta bacci me daɗi ya ɗauke ta. Kashegari da safe ta nufi office ɗinta don tana da abubuwan yi masu muhimmanci sai yamma ta dawo duk da cewar ranar ba ranar aiki bace Lokacin data dawo ne ta ishe mutane a tsakar gidan nasu da yawa gabanta ya faɗi suka kalli juna da Ammi ta kawar dakai.

Maryam cousin ɗin ta ce yace wajen Baffa Kabir itane ta nufota tace “Congrats Dr komai lokaci ne yau dai Baffa Nuhu ya amincewa aurenki da Hamma Hussain...." Da sauri ta dubeta tace “Shine me sai akace in shi ya amince Ni na amince?" Dukkan wanda yake gurin Saida yabita da kallo musamman Ammi da take kallon wannan a matsayin wata dama da Allah ya buɗewa Deenah ta samun abokin rayuwa me sonta da ƙaunar farin cikinta. Tsaki taja tayi ciki Abinda Ya ƙara tabbatarwa duk wanda yake wajen Deenah batayi amanna da wannan shiri ba, Kharimatu matar Yaya Mus'ab ita ce tabi bayanta don tasu tafi zuwa ɗaya ta ishe ta ta cire kayanta zata shiga wanka tace.





“Wai Madinah meye ne yake damunki ke kinsan irin murnar da mu masoyanki mukayi da aka sanar damu yau za'a kawo lefenki yanzu fa dakon jiransa mukeyi?" A hassale tace “Zaku karbi lefena dawa? Aunty Kharimatu ina ganin mutumcinki kije ki fadawa duk wani wanda yazo don wannan shirmen yaja tsumman rayuwarsa ya ƙara gaba wlh bazan auri Hussain ba yariga ya gama fita a raina da abubuwa da yawa na tsaneshi matsayin miji ku barni nayi rayuwata Ni ɗaya nafijin daɗinta....."

Tass aka ɗauketa da mari ta dafe gurin zuciyarta na tafasa ta ɗago ta sauke idanunta kan Ammi, Ammi tace “Na daɗe ina zarginki da bijirewa aure kina musamin ashe gaske ne ke wacce irin zuciya ce dake kamar ta kafuran farko Munau meye laifin yaron nan Husaini ya ƙare rayuwa a wahalarki ashe ke butulu ce wlh kin bani kunya meye baya hawa tsanin ƙaddara ne yaron nan yanata binki kina janshi a ƙasa shin ke kinajin akwai wanda zaisoki kamarsa a duniyar nan? To ahir ɗinki ko kinaso ko bakiso indai na isa dake kuma nice na haifeki saikin auri Hussaini...." 

Da rawar murya tace “Idan kuma Allah bai ƙaddara bafa Ammi na rantse da Allah banaƙin Hussain amma a yanzu bana masa son aure Ammi kibarni wlh bazan taɓa auren jinin Hajiya Suwaiba ba matar nan ta ƙini ta cutar da raina lokacin da bankai kowa ba Ni danme yanzu zan......."

“Zaki rayu da ɗana ko? Rasa kunya ɓeran tanka international Karuwa, to ai bari kiji fin ƙarfi na akayi har maganar Nan ta kawo haka amma Ni bazan taɓa amincewa dake matsayin matar ɗana ba saboda ɗabi'a naso takeyi abinda aka gada iyaye da kakanni shine akeyi ake fakewa mutane da karatu Madinah ga lefenan an kawo kuma na haƙiƙsnce  ɗannan ya mallaku kansa na cikin tukunyarki to amma ki sani ba cinya ba ƙafar baya ki jira ranar da zaki tabbatar Suwaiba ba sa'ar karawarki bace tafi uwarki ma makaman yaƙi"...............




_Sorry nd manege_

[6/22, 7:45 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan_*




_Kiji tsoron Allah karki karanta baki biya  ki biya ta wannan asusun 300 VIP 600 PC 1k domin jin yanda wannan littafi zai kaya sis abari ya hucce shike kawo rabon wani in baki fara ba ki fara yau JINKIRIN AURE ƙalubale ne dake ciwa al'umma tuwo a ƙwarya_

_Nrml  300 PC 1k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank ko 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank  ko kati MTN ta wannan number 09013718241, Yan Niger zaku turo katin Airtel na 500cf shaidar payment direct Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1




    

Tunda ta fara maganar babu wanda ya kulata sai yanzu da Madinah ta ɗago ta dubeta tayi murmushi ta buɗe baki zatayi magana Ammi ta ɗaga mata hannu tace “Karkice komai Madinah, ke kuma tunda kin gama ɗiban albarkar taki kina iya tafiya" Harara ta zabgawa Ammi tace “Eh kince haka mana to wlh muddin nice na haifi ɗannan to baku isa ku mallake min shi ba dole ku sakarmin kurwar ɗana da kuka kame tun baisan kansa ba, yo Ni na taɓajin wannan masifa ance baasonku kun nace kun liƙe saboda anyi baƙin jini anason a jonawa ɗana masifa gayyar baƙin jini....." 

Zuciyar Madinah har wani zillo takeyi tanada abin faɗa amma Ammi ta hanata magana dole ta koma ta zauna tanaji tana gani Suwaiba ta fice taci bulus, kwarai da Ammi tabarta da sai ta faɗawa Hajiya Suwaiba maganar da har ta mutu bazata manta ba.

Murmushi tayi ta juya ta kwanta ranta na suya Ammi tace “Ki kama kanki kuma ki koyi juriya dole ko don arzikin Mijinki ki rinƙa ragawa Suwaiba domin ta haifeshi tunda kuwa ta haifeshi Kinga kema ta haifeki Munau don Allah banason wata magana mara daɗi ta shiga tsakaninki da Suwaiba" 






Daga kai tayi tace “Insha Allahu Ammi amma ku dakatar da kawo lefen nan a tara wani lokacin" Murmushi Ammi tayi tace “To ya kikeso ayine Munau shifa aure dole ne gareki kiyi hƙr ki karɓi zaɓin nan ƙila shine zaɓin da Allah yayi Miki" 

Zaune ta tashi ta dubi Ammi tace “Idan ya kasance haka ne meyesa bai yiwu tun a baya ba Ammi matakin bata ran juna kawai aka ɗauka amma Ni inaji a jikina bashine zaɓin da Allah yayimin ba Ammi duk da haka na karɓa saidai inaso ki faɗa masa kar ya takurawa shiga rayuwata banaso" 

“Ai Shikenan" Ammi ta faɗa tana ficewa daga ɗakin hakan ya bata damar shiga wankan da tayi niyya ta fito ta zauna zaman shafa mai ta gama tayi sallolinta ta kulle ƙofarta tayi kwanciyarta kira da bugun ƙofar duniya taƙi buɗewa, ashe a wannan rana aka kawo lefen Mal Buba ne ya tsayar da lokacin bikin wata uku masu zuwa shima saboda Ammi tace a dan basu lokacine.





Washegari Litinin wayar Dr. Kaltingo ne ya tasheta ya sanar da ita sun taso ta amsa da “Ok" sukayi sallama ta shirya ta fice, har yamma ba'a gama gwaje-gwajen ba wannan tasa dole sai kwana sukayi washegari aka ɗora sukayi mata sallama suka tafi, taci gaba da bincikenta akan lamarin ciwon na Nusaiba kwana uku komai ya kammala da dare bayan ta nutsu ne ta ɗauki waya ta kira wayar Hon AA Waziri, bugu ɗaya ya ɗaga tayi shiru kamar bazatayi magana ba bayan tayi masa sallama, can ta numfasa tace “Munyi dukkan abinda ya kamata muyi na gwaje-gwaje game da matsalar Nusaiba abu ɗaya dana gano shine za'ayi mata aiki ne a zuƙe jinin da ya taru a cikin kanta sakamakon ɓulewar jijiyoyin ƙwaƙwalwarta amma kafin aikin za'a ɗorata akan wasu magunguna da kuma allurai, za'a aika masu da alluran da magungunan su Alluran za'a rinƙayinsu  ne duk Bayan 2 hour baa fashi kuma ba'a tsallake lokaci idan bakwai daidai aka fara to goma daidai za'ayi wata idan aka fara tsallake tsallaken shine matsala kuma shima maganin duk bayan 3 hour ake shansa sai ku nemi wanda zai kula da ƙa'idar lokacin"





Sosai sharruɗan suka tashi hankalinsa yaja numfashi yace “Amma Dr. Waye zaiyi wannan aikin?" Murmushi tayi tace “Toni ya zanyi in sani kaima baka sani ba wannan dai shine matakin farko na kula da Nusaiba a wannan ƙadamin da muke kai ciwonta yayi zafin da kulawa ta musamman take buƙata" 

Aje wayarta tayi taci gaba da harkokinta kwana biyu tsakani Dr. Kaltingo ya kirata yakeyi mata bayanin yanda sukayi da Hon AA Waziri tare da rokonta alfarmar ta karɓi kwangilar kula da Nusaiba...." Take tace masa bazata iyaba tadai bar Kano ta koma Abuja dominta, sosai hankalin Hon AA Waziri ya tashi yayi mata kiran wayar duniyar nan taƙi ɗagawa saima rejected da tayi a ƙarshe ransa yayi baƙi ya dugunzuma tunda yake a rayuwarsa bai taɓa haduwa da mace mara daɗin mu'amala irin Madinah ba, to wai ita meye takamarta ne? Tambayar daya kasa samun amsar ta ranar kwana yayi da ƙuncin zuciya.





A washegari ya nufo Abuja part dinsa wanka yayi ya fito ya nufi masallaci Saida ya dawo ya ishe Hajiya Babba a parlournta ita da autanta Nussy na kwance na gefe dafe da kanta sai wasu irin abubuwa  ya isa gabanta ya riƙo hannunta cikin tausayawa yace “Sannu Daughter ya jikinki?" Ɗagowa tayi ta zuba masa idanu tana hawaye   tace “Mutuwa zanyi Daddy....." 

Rufe mata baki yayi yace “shiru Daughter bazaki mutu ba insha Allahu zan yi duk me yuwuwa naga an samu wanda zai baki kulawa" zama yayi a gefenta suna duban juna da Hajiya Babba ta kwantar dakai tace “Babban mutum kamar akwai damuwa a tare dakai wani abu ya faru ne?"





Tsumman hannunsa yasa ya share fuskarsa idanunsa sun kaɗa sunyi jawur yace “Ba kowanne irin mutum nakeson shigo dashi cikin rayuwata ba Hajiya saidai yanzu yanayin ciwon Nusaiba yanaso dole saiya rakito wani" nan ya kwashe duk abinda Dr. Deenah ta sanar dashi ya faɗa mata, hatta Nazeer Saida ya girgiza da jin wannan dokoki ya ɗago yace.

 “To wai Bro A canza mata likita mana" ɗagowa yayi ya zubansa idanu tare da girgiza kai yace “Bakada hankali Bro kana ganin irin wahalar da muka rinƙa sha tsayin shekaru indai munason mu ɗan samu nutsuwa saidai mu fita da Nusaiba waje sannan ne zamuyi bacci na ƴan kwanaki, yanzu idan mun canzawa Nusaiba likita waye zai iya Bro manyan likitocin da mukejin zasu iya sune suka bada shawarar neman Dr. Deenah kaga kenan mu hkr ya kama" 

Ɗagowa Hajiya Babba tayi tace “Ita wannan yarinyar matar aure ce ko bazawara?" Batare da sanin ma'anar tambayar ba yace “Budurwa ce Hajiya shiyasa take abu da gadara batasan darajar haihuwa ba" da sauri Hajiya tace “Haba budurwa Babban mutum kodai bakaji daidai bane ai ba yarinya bace" Murmushi yayi yace “To inajin banji daidai ɗin ba amma Hajiya meye solution?" 





Murmushi tayi tace “Idan na baka mafitar zata zama ta dole ne Abdurrahman bantaɓa cewa dole kayi ba tun bayan mutuwar matarka Nasmat saidai yanzu dole ta kama kayi ɗin, kaje ka nemi auren Madinah Cikin sati biyu ayi komai a gama kada kabi ta kanta ka nemi Mansur Hassan Kaltingo abokinka kubi ta sama don inajin yarinyar nan bazata baka haɗin kai ba....." 

Girgiza kai yayi yace “Hajiya....." Ɗaga masa hannu tayi tace “Karkace komai kayi yanda nace" shiru yayi ya zuba uban tagumi, Nazeer yace “Amma fah Bro don baka ganta bane babyn ta wanku na daɗe banga halitta me kyaun wannan  yarinya ba karka wucce tayin wannan mata......

Daka masa tsawa yayi ya miƙe yace “Zaayi hakan amma Hajiya raina bai kwanta da wannan tsarin ba"

[6/23, 8:34 PM] Am Oum Hairan: *_Oum Hairan 31-32_*




Tunda aka sanya bikinta da Hussain take cikin damuwa batada cikakkiyar walwala bawai don batason auren ba saidon gudun fitina tabbas ne akwai ƙura cikin aurenta da Hussain ba iya mahaifiyarsa ce batason zamowarta suruka a gareta ba harda ƴan uwansa sunayi mata kallon kamar wata matsala s tattare dasu.

Bikin saura sati Uku inda ta mayar da hankalinta gabaɗaya akan kulawa da Nussy duk da cewa tanada burin fansa akan mahaifinta da har yanzu taki aminta su haɗu ko ranar da yazo Kano ya kawo Nussy Dr. Zahira da Dr. Nura tasa suka ganshi ita tace tanada uzuri me muhimmanci.

Sosai yaso ganinta amma taƙi ganuwa saima ƙara tabbatar masa da takeyi bazata ganun ba, sati ɗaya ta basu za'a sake dubata bayan magungunan da ta sake musu kafin su bar asibitin ma ita ta fice daga asibitin.





Tunda yake yaga mata iri-iri amma baitaɓa ganin mace me izzar Madinah ba, koda sukaje Office ɗinta shi da Dr. Nura ƙamewa yayi yana kallon taswirar hotonta tabbas babu ko tantama ya taɓa ganinta amma to a ina? Ya manta inane a ya jima yana kallonta kafin yaja numfashi suka fita yaja motar zuciyarsa tab da tunanin inda yasan majigin fuskar yarinyar lallai itan ya sani bamai kama da ita ba, kai tsaye Dr. Kaltingo yayi masa jagora har zuwa gurin Mal Buba suka zayyane masa bukatarsu Mal Buba ya jinjina lamarin kafin ya ɗago ya dubesu yace.

Kunzo da lamari me girman gaske, a zahiri dai Munawwara tanada wanda zata aura ɗan uwanta ne yayanta angama komai yanzu ma saura kwanaki ashirin da ɗaya bikin bansani ba ko ita ce ta turoku tunda dama ba na'am tayi da wancan auren ba musamman dake iyayen yaron masason auren, yanzu dai ina buƙatar ku bani lokaci zan tuntuɓeta zamuyi magana da ita duk abinda ke akwai zan nemeku" 





Jiki a sanyaye Hon AA Waziri da Dr. Mansur suka bar gaban Mal Buba kasancewar basuga alamun nasara ba saidai AA Waziri ya ƙudurce zaiyi duk me yuwuwa don ganin ya samawa ƴarsa madafa bazaiyi saken da Madinah zata suɓuce musu ba ko badon komai ba don lfyr Nusaiba.

Hanyar Gombe suka ɗauka dake Hajiya ta koma can shima kuma kamar yaro yafison zama kusa da Hajiya ko ba komi zai yi hira da ita yaji daɗi tana rage masa kewar matarsa abar ƙaunarsa da shawarwari da kuma nasihohi.

Kamar yanda Hajiya ta sabar masu suna zaune a wani sashi cikin parlourn da aka tanada don ibada tana duba wani littafin addini suka shigo yana riƙe da hannun Nusaiba suka zauna sunayi mata sannu da gida ta ɗago da murmushi ta miƙawa Nusaiba hannu ta kamota tace “Ina fatan andace?" Murmushi yayi yace “Eh to kusan haka ɗin duk wani abu da ya kamata ayi anyi dangane da abinda ya shafi Nusaiba.

Saidai kuma ina ganin kamar bamu dace ba a ɗaya ɓangaren" nan ya kwashe duk yanda sukayi da Mal Buba ya sanar da ita, tayi shiru na  lokaci Sannan ta ɗago tace “Yanzu meye mafita Babban mutum muna buƙatar Madinah cikin gidannan fiye da yanda Wancan yake buƙatarta kada kayi ƙasa a gwiwa ka jajirce ina ganin zaka dace banji a raina Allah zai gaza taimakonka akan wannan niyyar taka ba kaje, Abdurrahman ka dage zaka dace" 





Numfashi ya sauke yace “Hajiya bawai sarewa nayi ba amma sai nake ganin a barta tunda sun riga sunyi mata miji" girgiza masa kai tayi tace “Kaine mijin Kayi abinda nace maka kawai" baya jayayya da maganarta dole ya sunkuyar da kansa sukaci gaba da tattaunawa akan abubuwan daya shafi rayuwarsu.




Itakuwa Madinah anata shirye-shirye magana ta kankama Dr Zahira da sauran mutanenta sai rawar ƙafa akeyi basusan wainar da ake toyawa ba domin tunda aka fara maganar auren basu taɓa waya da Hussain ba ko ya kirata bata ɗagawa idan ya turo mata test bata buɗewa take gogewa gashi ko gidan yazo saidai ya hangeta daga nesa tanajinsa zata kulle ƙofarta yayi nacin Ammi tayi faɗan duk wani wanda ya isa ya faɗa yayi amma tayi kunnen uwar shegu, ranar Alhamis data kama za'ayi kamu ranar ne komai ya bayyana ga Ammi da yayyenta su Mus'ab shi itakam batasan me akeyi ba dake dama ba ɗokin auren takeyi ba batada wasu Yan rahoto iya masifa taki bari aganta bare a kamata, tunda aka fara hidimar bikin kullum sai sunyi faɗa da Zahira.

Yau ɗinma bayan an taso daga Event ɗin da akayi kamu sai uzurin amarya batada lafiya aka bayar suka raba abinda zasu raba kowa ya watse, A ɗakinta ta tarar da ita ta tusa takardu a gaba tana dubawa tare da shigar da wasu bayanan cikin system ɗinta.





Rufe system ɗin Dr. Zahira tayi tace “Amma ke bakida mutumci wlh kawai kisa mu tara mutane domin tayaki farin cikin zuwan wannan rana da aka daɗe ana addu'ar zuwa ta shine zaki jisgani ki watsamin ƙasa a ido ki barni da ƙarya wa mutane na cewa amarya batada lafiya....." Harara ta watsa mata tace “Kece kike murna da wannan auren da ba baki nayi masa ba amma banji a raina zaije ko inaba" Daga mata hannu Zahira tayi tace “Dakata dallah Malama kada ki fusatani ai saiki tashi kije Mal Buba ne yake neman ki yace idan an taso daga kamun Azo masa dake"

Kasaƙe tayi tana mamakin wanne dalili ne yasa Mal Buba yake nemanta? Dole ranta baiso ba ta tashi ta ɗauki mayafinta suka fice a harabar gidan ta tarar da Yaya Mus'ab suka gaisa yace “Kunyi magana da Mal ne?" Girgiza masa kai tayi tace “Yanzu Zahira take cemin Ammi tace idan an taso daga kamu naje yanason ganina" gaba yayi itama ta nufi  motarta ta shiga suka  fice ranta cike da saƙe-saƙen dalilin kiran nasa.

A zaurensa ta tarar dashi suka gaisa yana zolayarta tana Murmushi can ya nutsu ya kira sunanta yace “Munawwara!" Ɗagowa tayi cikin faɗuwar gaba yace “Na canza Miki miji....." Wani dam gabanta ya buga tace “Ni..." Jinjina mata kai yayi yace “Ƙananun maganganu sunyi yawa a lamarinki da Hussain wannan yasa na canza Miki zaɓin abokin rayuwa  ina fatan ya zame Miki alkhairi"




Jikinta a sanyaye idanunta ya ciko da hawaye tace “Waye Mal?" Murmushi yayi yace “Hon Abdurrahman Abba Waziri...." Cikin firgici tace “What?" Jinjina mata kai yayi yace “Kiyi hƙr insha Allahu shine alkhairin ga lefenki nan ankawo ɗazu da safe" Idanunta taf da hawaye tace “Amma Mal waye ya kawoshi gurinka har ka amince masa aure na wlh Mal banason auren Hamma Hussain amma da na auri wannan mutumin gara na auri Hamma...….





Dafa kanta yayi yace “Kije kiyi biyayya wannan zaɓin ba nawa bane zaɓi Allah ne" gdy tayi masa ta miƙe jiri na ɗibanta tana fitowa suka kalli juna da Zahira hawaye ya zubo mata tayi saurin shigewa mota ta rushe da kuka abinda ya ɗaga hankalin Zahira tace “Waye ya mutu Madinah?" Bata kulata ba saida tayi me isarta sannan tace “Meyesa ƙaddarar aurena tazo a haka? Hon Abdurrahman Abba Waziri shine Mal zai canzamin meyesa bazai zaɓomin wani ba?"

Da rashin fahimta tace “Kamar nasan sunan" hawaye ta share tace “Kinsanshi mana mutumin da ya kawo yarinyarsa asibitinmu kwanaki har na baku damar dubata keda Dr. Nura wai shine matsayin mijin da Mal ya zaɓamin to waini ya akayi ma yasan gdanmu"

[6/25, 9:05 PM] Am Oum Hairan: *_33-34_*





Zubawa Dr Madinah idanu Dr. Zahira tayi tace “Ikon Allah yanzu dashi za'a ɗaura kenan?" Jinjina kai tayi tace “Hakane banji daɗin zaɓin ba domin nasani sarai ba don Allah ya kawo kansa gidanmu ba har ya nemi aurena yayi ne don ƴarsa" da sauri Dr. Zahira tace “kamar ya don ƴarsa meye ya kowa ƴarsa cikin lamarin aurenku?" Murmushi tayi me nuna irin ɗacin da yake zuciyarta tayi parking a ƙofar gdannasu tace “Nace bazan karɓi kwangilar kula da itaba kasancewar yanayin ciwonta ya nuna dole sai an samu likita permanent dazai zauna tare da ita kafin a samu lagon ciwon  shine ya ɓullo ta aure Kinga ya zama dole kenan naje na zauna na rayu dasu, eh na aminta zanje na zauna na rayu dasu zan kula da Nusaiba saidai a hankali nufina zan wanzar dashi domin nasami cikakkiyar dama da zan ganar da Hon Abdurrahman Abba Waziri talaka ba wulaƙantacce bane...." 

Da rashin fahimta.





Dr. Zahira tace “Har yanzu na kasa fahimtar komai kiyimin bayani yanda zan gane!" Murmushi tayi ta kwashe komai ta sanar da Zahira, Zahira tayi ajiyar zuciya tace “Kinada matsala wannan har yakai kiyi saving mutum a ranki ni sai naga kamar baikai ba ki ajiye komai ki karɓi zaɓin da ubangiji yayi Miki inba haka ba zaki kuma jefa kanki ciki matsala, Madinah koda ace da manufa ya aureki  to yaji yana ra'ayin rayuwa dake ne shiyasa har ya nema please ki cire komai a ranki" 

Zuciya taja ta buɗe motar tana cewa “Abinda naje na tarar a gidan shine zai haskamin yanda gobena zata kasance.





Cikin gidan suka nufa kowanne da abinda yake saƙawa a ransa tana shiga Ammi ta tareta tace “Garin Yaya hakan ta faru Munau?" Cikin sanyin murya tace “Nima tambayar da nakewa kaina kenan Ammi bansan komai game da wannan lamari ba....." “Kunya muke neman ji shiyasa muka canza Miki da cancanta Alh Nuhu ya kuma cin laya kan cewa bazaa ɗaura auren nan ba shikuma wannan mutumin yanata naci shiyasa muka sauya Hussain dashi shi kansa Hussain ɗin har yanzu labari bai isheshi ba, naso sanar dashi tun yau Mal ya hana yace abarsa dasu" bata ƙarshe jin abinda yake faɗaba ta shige ciki don itadai tasan babu abinda jin zai ƙare ta dashi





Kayanta ta cire ta kwanta kowa yana farin ciki da daren aurensa amma banda ita shauƙi da nishaɗin da kowacce amarya take samu a ranar bikinta ita bata sameshi ba zuciyarta batajin komai game da auren to meye yasa hakane?

Rashin amsa yasata gyara kwanciya a haka Zahira tazo ta ishe ta suka zauna ita da wata ƙawarsu suna zolayarta har zuwa yanzu maganar sauyin mijin nata bata bazu ba to itama baso take tabazu ba shiyasa taja bakinta ta tsuke washegari gidan ya cika ya tumbatsa da dangi anata hidima abu yaji masu abu kuma a ranar ne wajen tara na safe taji wayarta tayi ring tana dubawa taga alert ne na kuɗi masu kaurin gaske bayan alert ɗin anyi mata gajeran sako, _Nasan ba lallai idan na tambayeki ki faɗa min matsalarki ko nawa kike buƙata da zata gama Miki hidima shiyasa na turo miki waɗannan idan sunyi kaɗan don Allah ki sanar dani....._

Taɓe baki tayi ta aje wayar akaci gaba dayi mata gyaran farcen ƙarfe biyu bayan sallar juma'a aka ɗaura auren kamar yanda aka tsara tun farko ko second ɗaya ba'a ƙara ba.

Hussein yana gefe da dandazon abokansa yaji Maroƙin yana shelar ɗaurin auren da  wani bashi ba, tashin hankali da ba'a sa masa rana Koda Hussain ya tsinkayo Muryar Maroƙin baisan sanda ya zube a gurin sumamme ba, bashiba kowa ma yayi al'ajabin yanda  wannan lamari ya faru.





Lokacin da Hamma Khamis ya kirata yanayi mata congratulations batasan sanda hawaye ya rinƙa zarya a Idanunta ba tace “Alhmdulillahi bi ni'imatihi........" Sai kuma ta faɗa jikin Ammi ta rushe da kuka tare da ƙankameta Ammi itama cikin hawayen tace “Komai nada lokaci Madinatul Munawwara yau dai da masu Miki fatan alkhairi da masu yi Miki na tsiya da masu zunɗenki lokaci yayi da zaki gusa ki bar musu unguwar kije kema kiyi bautar ubangiji tabbas wani jinkirin alkhairi ne kekam inaji a jikina kin tsamo alkhairin rayuwarki saidai fatan alkhairi kije kiyi biyayya"





Ƙarfe uku motocin ɗaukar amarya suka zo Tunda Madinah take bata taɓa kuka irin na yau ba, lokacin da Baffa Kabir yakeyi mata nasiha akan biyayya da bayyana mata girman haƙƙin miji akan matarsa matuƙa jikinta yayi sanyi tayi kukan gingimemen nauyin daya hauta sannan tayi kukan rabuwa da Amminta rabuwar da ta zama babu dawowa saidai da ziyara.

Tanaji tana gani aka sata a mota suka sulali hanyar da zata kaisu Gombe suna tafe tana shassheƙarta idan ta tuna da Amminta ta rushe da sabon kuka ita ba yarinya ƙarama ba amma yanayin ya zame mata sabo, haka sukayita zuɗaɗa tafiya basu suka shiga Gombe ba sai bayan Isha suka ɗauki hanyar unguwar da gidan Senator Abdurrahman Abba Waziri yake basuyi wata doguwar tafiya ba suka isa ƙofar get ɗin gidan masu gadi suka wangame musu motocin guda uku sukayi parking a rumfar aje motocin mutane suka fara fitowa, Hajiya Sadiƙa kanwace ga Hajiya Babba ita ce ta fito da Dr. Madinah daga motar suna riƙe da hannunta har ɓangaren Hajiya Babba mutanen dake falon suka taresu da guɗa da fullancinsu suka kamata suka zaunar da ita gurin da aka tanada dominta sunata yi mata Barka da zuwa, bayan komai ya lafa ne Hajiya Babba ta kama zara²n yatsunta tace.





 “Inayi miki Barka da shigowa cikin wannan zuri'a tamu matsayin mata Madinah Allah yayi Muku albarka yasa aurenku ya zamo haske ga wannan gida, Zainab ku rakata ɓangarenta ta huta kafin mijinta ya shigo"

Miƙar da ita sukayi suka fice suka nufi wani ɓangare da yafi kowanne haɗuwa da tsaruwa a gidan aka buɗe ƙofar aka shigar da ita kai tsaye ɗakin baccinta suka shigar da ita Zahira da sauran mutanensu sunata yabawa da baiwar da Allah yayi mawa Madinah ta more gida ta more dangin miji saidai fatan zaman lafiya.





Ƙarfe goma kowa ya watse suka nufi makwanci ya rage daga ita sai Zahira suna zaune Zahira tace “Ni ina mamakin kukan da kikeyi na meye ke ba mutuwa akayi Miki ba ba komai ba aure Sunnah ce kowa da haka ya saba ki daina kukan nan haka don Allah banaso Mijinki yazo ya tarar dake a haka"

Daƙyar ta samu ta rarrasheta tayi shiru ta mike tace “Nima zanje na kwanta Allah ya bamu alkhairi" fita tayi ta barta zaune a gadon tanata tufka da warwara ta kasa miƙewa daga gurin har sha ɗaya aka buɗe ƙofar aka shigo Idanunta na cikin mayafi ya tsaya jikin ƙofar ya zuba mata idanu tare da sauke ajiyar zuciya ya taka a hankali ya isa gaban mirrow ya ajiye ledar hannunsa can ƙasa taji yace “Welcome" sake takowa yayi gabanta yace “Idan kin shirya inason magana dake a part ɗina"

[6/27, 8:52 PM] Am Oum Hairan: *_35-36_*




_Paid book 300 SP 1k view acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank or DM 09013718241_




Shiru sukayi na tsayin lkc sannan taji yaja ƙofar ya fice ta sauke wata ajiyar zuciya me ƙarfi sannan ta miƙe ta shiga bayi ta kalli bayin sosai kafin tayi wankan ta dawo ta buɗe kayanta ta ɗauki rigar bacci mara nauyi tasa ta zura hijjab ta fice daga ɗakin gabanta na faɗuwa ta nufi wani sashi da take hange kusa da nata ta murɗa ƙofar a hankali ta tura ta shiga tare da sallama.

Shiɗin dake fitowa daga bathroom ɗaure da towel ya amsa mata tayi saurin ƙasa da kanta tace.

“Na gama inason kwanciya" ajiyar zuciya ya sauke yace “Ok dama game da Nusaiba ne nace meye tsarinki na fara kula da ita?"

Binsa tayi da kallo irin na  kama rainamin hankali ta juya zata fice ya riƙo hannunta yace “A baya kina da cikakken iko na jana a ƙasa kiyimin duk abinda kikeso amma yanzu dake da aikinki duka a ƙarƙashin inuwata kuke" lumshe idanunta tayi tace “Zanyi tunani akan hakan" tana faɗin haka ta zame hannunta ta fita a dakin yabita da kallo yarinyar akwai jin kai ya rasa meye taƙamarta a duniya





Taɓe baki yayi tare da zura rigarsa ya fita domin yaje ya gano halin da Nussy ɗinsa take ciki mamaki ne ya cikashi ganin Madinah a ɗakin tana dubata ko shigowarsa baisa ta ɗago daga abinda takeyi ba saima sake dauke kanta da tayi daga ɓangaren da yake taci gaba da abinda yake gabanta.

Shiru sukayi na tsayin lkc sannan taji yaja ƙofar ya fice ta sauke wata ajiyar zuciya me ƙarfi sannan ta miƙe ta shiga bayi ta kalli bayin sosai kafin tayi wankan ta dawo ta buɗe kayanta ta ɗauki rigar bacci mara nauyi tasa ta zura hijjab ta fice daga ɗakin gabanta na faɗuwa ta nufi wani sashi da take hange kusa da nata ta murɗa ƙofar a hankali ta tura ta shiga tare da sallama.

Shiɗin dake fitowa daga bathroom ɗaure da towel ya amsa mata tayi saurin ƙasa da kanta tace.

“Na gama inason kwanciya" ajiyar zuciya ya sauke yace “Ok dama game da Nusaiba ne nace meye tsarinki na fara kula da ita?"

Binsa tayi da kallo irin na  kama rainamin hankali ta juya zata fice ya riƙo hannunta yace “A baya kina da cikakken iko na jana a ƙasa kiyimin duk abinda kikeso amma yanzu dake da aikinki duka a ƙarƙashin inuwata kuke" lumshe idanunta tayi tace “Zanyi tunani akan hakan" tana faɗin haka ta zame hannunta ta fita a dakin yabita da kallo yarinyar akwai jin kai ya rasa meye taƙamarta a duniya





Taɓe baki yayi tare da zura rigarsa ya fita domin yaje ya gano halin da Nussy ɗinsa take ciki mamaki ne ya cikashi ganin Madinah a ɗakin tana dubata ko shigowarsa baisa ta ɗago daga abinda takeyi ba saima sake dauke kanta da tayi daga ɓangaren da yake taci gaba da abinda yake gabanta ya ɗauki lokaci yana kallonta kafin ya juya ya fice a dakin ya koma part ɗinsa ya kwanta ransa ya tafi tunanin irin zaman da zasuyi da amaryar tasa s yanda ya lura da take²nta bata ɗaukar wasa.

Da wannan tunanin bacci ya ɗaukeshi ita kuwa Dr Madinah bata samu komawa part ɗinta ba sai sallar asuba tayi sallah tayi wanka ta kimtsa ta kwanta, wajen tara taji ana taɓa kofarta ta miƙe tana mika ta buɗe baƙinta ne da suka kwana suka rankayo parlourn nata suka baje tare da fara bayyana mata irin sha tara ta arzikin da aka hada musu suma kuma sun jibge gararsu ta Fulanin Gwangola, nan suka rashe sunata hira sai ɗaya na rana Bashir driver ya shigo yace.

“Alh yace wai bakin da zasu tafi su shirya anjima motoci zasuzo" tana kallo suka tashi suka fara shiri haushi kamar tayi kuka, tana gani suka gama shirinsu tsaf Masu aiki na kawo abinci motocin suka zo a gurguje sukayi lunch din suka tafi har hawaye tayi saboda kewa da zasu rabu da aminiyarta Dr Zahira tace “Ai dake zaku koma Abuja Nima can zamu tafi da Angona" 





Tana ɗaga musu hannu suka tafi ta juya zuciyarta a karye ta nufi cikin gidan dangin su Hon Abdurrahman suma duk sai yau suketa tafiya yamma tayi kowa ya watse aka barsu da halinsu, daga wannan lokaci rayuwa ta fara canzawa Dr Madinah babbar damuwarta ita aikinta ba a Gombe ba gashi tazo ta tare a Gombe gashi ya ɗora idanu kan kulawar da take bawa Nussy kusan kullum sai sunyi faɗa dashi ita tana ganin tana bakin ƙoƙarinta shikuma yana nuna mata bata iyaba danma da Hajiya Babba a tsakiyarsu ita ke tsawatar masa wataran idan ya bata haushi ta hana Madinah taɓa Nusaiban har sai ya sauko ya bata hƙr.

Gashi da yawan tafiye-tafiye tunda dai suka samu suka dawo Abuja Allah ya taimaketa ma'aikatarsu ta ajiyeta Headquarter ta Abuja Shikenan ta samu nutsuwa yanzu damuwarta ɗaya lamarin Nusaiba dake ƙara ƙamari da taimakon Allah ta samu aka amince mawa appointment ɗinta data tura ƙasar France suka basu lokacin da zasuje ayi mata aikin farko.

Dukkansu hankalinsu a tashe yake hatta ita Madinan saboda tasani aikin nada hatsarin da ba kowa ake yiwa ya tashi ba amma ya zasuyi gara ayin Allah shine keda rayuwar bawa.





Lokacin ya cika suka nufi ƙasar France Cikin ikon Allah akayi aikin lfy aka gama wannan nasara ba ƙaramin daɗi tayiwa wannan ahli ba saiga Nusaiba kamar ba itaba hakan yasa suka dawo bayan an basu lokacin da zasu koma a kara duba lafiyarta, rayuwa tayi daɗi na wasu takaitattun lokaci.

Wata rayuwa da ke wakana tsakanin Madinah da AA Waziri tunda aka kawota gidan da sunan mata  basu taɓa kwana ɗaki ɗaya ba sukan ɗauki lokaci basuga juna ba tunda Madinah ta kiyaye lokacin dawowarsa idan yana ƙasar Shikenan da zarar taga ya kusa dawowa saita shige part ɗinta ta rufe tayi kwanciyarta ko wani abu yazo dashi saidai yabawa Nussy takai mata, cikin watanni shidan sunyi wata irin shaƙuwa tsakanin Nussy da Dr Madinah komai Mom komai Mom kai zaka zata da gaske ita ce ta haifeta.





Duk bayan wata uku suke mayar da Nusaiba gurin likitanta Dr James da kuma Dr. Madinah, Yau asabar ce hutun ƙarshen sati AA Waziri yana ƙasar a babban parlournsa ya wuni yana ganawa da baƙi har yamma sai biyar sannan ya shigo gda kai tsaye part ɗinsa ya shiga yana shiga ya ishe Madinah a zaune saman kujera tana duba jaridar daya ajiye a saman tables ɗin dake gaban kujerar.

Ɗago manyan Idanunta tayi ta saukesu akansa tare da miƙewa ta nufeshi ta sanya hannu ta zame wayarsa dake hannunsa tace “Sannu Ranka shi daɗe nasan ka gaji...." Mamaki ne ya cikashi ganin ta sake nufosa duk da gaban Madinah faɗuwa yakeyi haka ta isa cikin kwarkwasa takai hannu ta fara ɓalle masa bottle na rigarsa ta zame ta a jikinsa tana shiga jikinsa tace “Meyesa ka gajiyar da kanka haka..." 

Hannu takai saman tazugen wandonsa yayi saurin riƙeta yana cewa “Ya akayi meye ne hakan?"





Murmushi tayi ta karyar dakai tace “Kawai inason bawa mijina kulawa ne nayi hutu me tsayi na aiki gashi Ammi na tayimin nisa Zahira kuma sun koma Kano da mijinta shiyasa nakeson samun abokin  da zai rinƙa daukemin kewa muna hira dashi ya bani lokacinsa na bashi nawa so na duba na dubo kaine kawai taswira ta nuna saboda kaiɗin halali na ne......

[6/29, 9:04 PM] Am Oum Hairan: *_37-38_*




_Paid book 300 PC 1k view acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu first bank or DM 09013718241_




Zuba mata idanu yayi cike da mamaki yace “To ni bana buƙata" Murmushi tayi tace “Haka zakaso" ya buɗe baki zaiyi magana ta ɗora hannunta a bakinsa tace “sheet karka wahalar da kanka Ni nan daka ganni ba wani abu nake nema ba banma san abinda kake tunanin ba bare naji shauƙi a kansa kawai kazo muje nayi maka wanka na taimaka maka ka shirya na baka abinci in kana buƙatar hutu nabaka dama ka huta" 

Surutunta ya fara yi masa yawa shi baima taɓa tunanin a miskilncinta tana magana haka ba"

Sake narkar dakai tayi tace masa “Kasan cewa inada haƙƙi a gunka wanda kayi watsi dashi tsayin watanni? Abinda yasa bai dameni ba saboda bansan me akeji a ciki ba amma dai ka sani ina kallonka ne a mutumin da yake da gazawa wajen sauke haƙƙi, koda yake ashe ba aurena kayi don mu rayu ba ka aureni ne don yarinyarka kaje kayi rayuwa amma ka sani Ni bana da wata mafita bayan kai" 

Juyawa tayi zata fice ya riƙo hannunta ya juyota gaba tayi ƙasa da idanunta ya saketa yace “kije zan nemeki" juyawa tayi ta haura gadon ta kwanta tana miƙa tace “Na gaji da kwanan kaɗaici gsky yau a bayan mijina nakeson kwana" shikam yau ya gamu da gamonsa abinda ya faɗa kenan cikin ransa kafin ya nufi bathroom ya sakarwa kansa ruwa.





Taɓe baki tayi taci gaba da latsa wayarta tanaji ya fito ya fara shirin kwanciya ya dubeta yace “zan kwanta"  kallonsa tayi tare da yin miƙa tace “Ok Bismillah tana matsawa daga inda take tunanin zaiso kwanciyar kallonta yayi 

Zaiyi magana meye kuma ya tuna saiya fasa a ransa yana furta shikam ya shiga uku da wannan yarinya yau salonta mamaki yake bashi, raɓawa yayi kan gadon ya kwanta kamar wanda za'a kama ita kanta a tsorace take da yanayin kawai dai don tanason takura masa ne amma da taji ɗumin jikinsa a jikinta Saida gabanta ya faɗi mazewa kawai tayi ta share dukkansu a ɗarɗar sukayi bacci sanyin dare da yayi sanyi basusan sanda suka manne ba jin yanda ɗumin tattausar fatarta yake ratsashi ya haifar masa da wata kasala da baisan meye ya sabbabata ba sai wani yanayi ya rinƙa shigarsa kiran sallah ne ya tashesu suka janye jikinsu ana juna da sauri kowanne yace “kayy" tare da yiwa juna kallon tuhuma saidai babu me bakin magana haka ta juya ta fice shima ya shiga bathroom yayi wanka yayo alwala cike da shauƙin yanda baccinsa na jiya ya kasance rabonsa da bacci mai daɗinsa ya manta lokacin.





Masallaci ya nufa yayi Sallah sai bakwai ya shigo a tsarin gidan kuku ne yake ciyar da kowa saidai yau yaga sabanin haka ita da kanta taketa shirya dinning ɗin ya tsaya yana kallonta ta ɗago suka haɗa idanu tayi saurin ɗauke nata tace “Barka da safiya" a gajiye don wankan nata na yanzu ya sashi a corner yace “Yawwa ina Salman ɗin" rausayar dakai tayi tace “Hutu na bashi yau Nima inason samun ladan aure" kalmarta tayi masa daɗi yaja numfashi a miskilnce yayi ciki tabisa  da kallo tare da yin Murmushi tace “Zaka shigo hannu ne"





Da wannan ta nufi sashin Hajiya Babba suka gaisa ta shirya mata dinning dinta Nusaiba nayi mata surutu tana cewa “Mommy jiya naje bedroom naki banganki ba ina kika ɓuya" murmushi tayi tace “Ina wanka kikaje" da sauri tace “Lalala mommy nafa daɗe naji banjiki ba na taho" daƙuwa Hajiya Babba tayi mawa Nussy tace “karbi nan sarkin surutu ƴar ƙaniya zo kiyi break a kaiki school" miƙewa Madinah tayi tace “Bari naje na sallami Daddy Daughter" kaɗa mata kai tayi ta fice ta nufi nasu part ɗin a dinning ɗin ta tarar dashi ya harɗe sarai tasan mugun ikonsa nan jiran me haɗa masa abincin yakeyi.

Haka ta cire ganda ta haɗa masa itama ta zauna sukayi zaman kurame ita ce ta gaji da shiru ɗin tace masa  “To ka bani labari mana!" Yanda tayi furucin tana shagwaɓe fuska yasashi kallonta baisan sanda yayi murmushi a rayuwarsa yanason yaga mace tanayi masa shagwaɓa waɗannan abubuwan ya rasa shiyasa ya kasa aure gani yake kamar bazai samu kamar Nasmat iya kula da miji da tattalin ƙauna da kuma shagwaɓa ba......

Baiyi aune ba yaji taja yaji ya buɗe idanunsa da sauri akanta take yayi mutuwar tsaye lkcn da ya ɗora idanunsa kan nipples ɗinta da take matsawa harda hawayenta tace “Please Hon Help me ƙaiƙayi yakeyi......"




_Bantaɓa yi muku ƙaramin typing kamar yau ba._



_Manage don kusan kuna raina tomorrow insha Allahu_

[6/30, 11:26 AM] Am Oum Hairan: *_39-40_*




_Paid book 300 PC 1k view acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu first bank or DM 09013718241_





Kasa ɗauke idanunsa yayi dagakan Madinah ƙirjinsa yana bugawa da ƙarfi shikam yau yaga rayuwa yarinyar nema take ta zautashi, ganin yanda take ƙara zubar da hawaye ne yasashi miƙewa a hankali ya isa gabanta ya tsugunna yakai hannunsa zai ɗora akan nata data riƙe nipples ɗin nata ta kuwa saki wata siririyar ƙarar kirsa tace.

“Wayyoh Allah na zafi ƙaiƙayi ka sosamin please...." Yanayin Muryar da tayi maganar da ita ta ƙara narkar dashi har baisan sanda yasa yatsansa ya fara sosa mata nipples ɗin a hankali ba ita kuwa sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi, Idanunta a lumshe taji wani ɗumi me gusar da yanayi a saman nipples ɗin nata ta buɗe Idanunta a hankali a kansa ashe harshensa yasa yake lasar nipples ɗinta taja ajiyar zuciya tare da janyewa burinta dama kenan ta sanyashi a yanayi kuma ta gama fahimtar ya shiga hakance tasata zame jikinta ta miƙe da niyyar barin gurin ya riƙo hannunta yana kallonta da idanunsa da suke lumshewa.





Miƙewa yayi ya cafeta cak ya nufi ciki da ita bai direta ko inaba sai saman gadonsa yaja musu labule, duk inda Madinah takejin zata iya kwatar kanta a hannunsa abin yaci tura don dole ta bashi kai bori ya hau.

Yawan shekarunta bai hanata shan wahala ba a wannan fagen daƙyar ta ƙwaci kanta bayan ya samu nutsuwa ta koma tana jan numfashi shima yana sauke numfashi shikam nutsuwar daya jima bai sameta ba ita yaji ta dawo masa sabuwa fil yanajin wani shauƙi na shigarsa, lallai ne ya yarda mace rahama ce domin gashi ta bashi nutsuwa Madinah ita kaɗai ta kashe masa ƙishirwarsa ta shekaru.

Yana ganinta ta tashi da dabara ta nufi bathroom ta fara gyara kanta zafin ruwan takeji idan ya shiga jikinta hakanan dai ta gyara kanta ta fito fit ta fice daga ɗakin yanda ta fice ɗin ya bashi dariya ya mike shima ya nufi bathroom ɗin yana cewa “Waike bakyaji dama ai barki nayi" Wanka yayi ya shirya cikin wani blue ɗin yadi abinka da farar fata yayi masifar kyau ya ɗauki key na mota ya fice daga gidan zuciyarsa wasai da farin ciki ya samu nutsuwa yau ya fitar da dattin mararsa.





Itakuwa Madinah tana shiga ɗakinta daƙyar tasa kaya ta kwanta zazzaɓi ya rufeta batasan haka karon zai kasance musu ba da bata fara ba ashe ita keda wuya lallai babu wani daɗi cikin wannan lamari Inma akwaishi to wuyar tafisa yawa, da wannan tunane-tunane bacci ya ɗauke ta ba ita ta tashi ba sai biyu tana tashi wanka kawai tayi tasha magungunan da tasan zata samu relief ta fito parlourn ita kanta ta lura tafiyarta ba daidai take ba badon yunwa da son bawa Nussy magani ba da bazata fito ba haka ta daure ta isa har babban parlourn suna nan dukansu harda Nazeer suka sake gaisawa da Hajiya Babba Nazeer yace “Barka da sfy ko nace rana Dr uwar likitoci" murmushi tayi tace “An gaisheka talakan zamani" sosai kalmar ta dakeshi Hajiya Babba tace “Kamar ko kin sani yanzu nan zuwa yayi zai cajeni wai bashi da kuɗi niko nima ba sune dani ba" kallonsa tayi tace “abin tausayi kuma nawa kake buƙata" shafa sumarsa yayi yace “Ko hundred thousand ne ma ya isheni hajjaju" taɓe baki tayi tace “ka turamin acct details naka kasan babu komai tsakaninmu da talaka daya wucce taimako" 





Yau gabaɗaya kalaman matar yayan nasa wata manufa take nuna masa daban ya dubeta sosai yanason tambayarta amma babu fuska hakan tasa ya sadda kai yace “Gdy nake Likita" daga haka sukaci gaba da hirarsu da Hajiya Babba tana bawa Nussy magani bayan ta gama bata ne sukaci abinci me kula da Nussy tazo ta jata domin yi mata shirin islamiyya.

Itama miƙewa tayi tace “Hajiya bari na ɗan kwanta banajin daɗin jikinnan nawa kai kuma ina jira" tana faɗa ta nufi part ɗinsu a parlour ta kwanta saboda yanayin zazzaɓin da takeji har yanzu bata jima ba bacci ya ɗauke ta.

Cikin baccin taji ana shafa fuskarta tayi tunanin Nussy ce taji dai abin baiyi kama da Nussy ba don abin ya fara zarce fuska yanayin ƙirji ta buɗe Idanunta tana dubansa shima idanunsa a kanta yace “Gajiyar ce" lumshe idonta tayi tana ƙara dunƙule jikinta, da gaske sanyi takeji ya dubeta da mamaki yace “Ke wai meye ne daga ihu ɗaya har murya zata dashe?" 





Hawaye ne ya zubo mata tace “Ni... Ni ka daina taɓani...." Murmushi yayi yace “In na daina taɓaki na taɓa wa? Tashi muje kiyimin wanka ko kyayi aikin lada na biyu" noƙe kafaɗa tayi tace “Ni bazan iya ba ka barn....." Bata gama ba ya sunkuceta gabadayanta ya nufi ɗakinsa da ita ya kwantar da ita.

Tare da ja mata bargo yace “nasan matsalarki ki huta sosai Ni dama haka nake" bata gane meye yake nufi ba ita kuma bata tambaya ba ta lumshe idonta ba bacci takeyi ba saidai yanayin yafi bacci daɗi hakanan tana jinsa yayo wanka ya dawo ya shirya ya kuma fita itadai batace masa komai ba saima bacci daya ɗauke ta.

Sai gaf da magrib ya tasheta tayi sallah ta sulale ta gudu daga ɗakin dazun ta dandana kuɗarta bataga tsautsayin da zaisa ta sake kwana dashi ba don tasani wuya zata kuma ɗorarwa alama ta bayyane ta nuna so yake ya kuma turmusata itakam ta hƙr basai sunyi abotar ba.

Ko abinci sawa tayi aka kawo mata taci ta ture kwanukan tayi brush ta kwanta tana chat wajen goma bacci ya ɗauke ta, can cikin dare taji iska me ɗumi na zaga kunnenta ta buɗe Idanunta a kansa da sauri ya lumshe nasa yace “Nazo na taya ƙawata kwanciya...." 





Da alamun tsoro da faɗuwar gaba tace “Aa kaje banaso...." Maganar gagara fita tayi saboda toshe mata bakin da yayi da nasa ya wani kwanto jikinta yanashan harshenta kamar sweet iya sonta data tureshi ta kasa tanajinsa shine harda zamar mata da hannun rigar baccinta ya janye bakinsa ya dubeta yana kallon kyakkyawan nipples ɗinta yace “Yana ƙaiƙayin?" Girgiza masa kai tayi tace “Zafi yakeyi karka tab....." Kafin ta rufe bakinta ya mayar da bakinsa a nipples nata.

Da haka wasan ya sauya Madinah ta raina kanta sosai a hannun AA Waziri domin tabbas koda batasan ya mazan suke ba shikam tanada yaƙinin jarumi ne domin yana daka mata gumba a hannu tanaji a jikinta sosai.





Tana samu ta zame ta koma gefe ta ƙudundune bacci ya ɗauke ta ya matsa ya janyota jikinsa yana shafa bayanta har bacci ya saceshi shima da washegari da kansa ya haɗanta ruwan wanka ta shiga tayi, duk tabi ta tsargu da irin kallon ƙurillar da yakeyi mata

[6/30, 8:36 PM] Am Oum Hairan: *_41-42_*




_This book is not free Nrml 300 PC 1k view acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank or DM 09013718241_




A ransa yake ƙissima irin baiwar kyawun da Allah yayiwa Madinah komai ka kalla a jikinta sai kaga ya dace da ita babu wani abu na dama ace a jikinta komanta kalarta izzarta tafi komai daukar hankalinsa hatta takunta kaida ka gani kasan na isassun matane takeyi, tun ranar farko daya farajin muryarta a waya zuciyarsa ta karɓi sako game da ita saidai yakan adana yanayin da yake ciki ne karta sani ta kawo masa wargi.

Numfashi ya sauke ya sake gyara kwanciya bayan ta fito ta gudu ɗakinta, duk da yau Litinin ce ɓata tsayin daren da yayi yana kwasar gara yasa yaji bayason fita kwanciya yake buƙata wannan ta sanyashi kashe wayoyinsa duka ya kwanta ransa yana dawo masa da darensa na jiya ya samu nishaɗin da rabonsa dashi shekara goma sha huɗu kenan tun daren amarcinsa da Nasmat sai yanzu Madinah ta dawo masa dashi sabo, da wannan bacci ya daukesa, itakam yau ko part ɗin Hajiya Babba bata iya zuwa ba da gaske ciwon jiki ne da wani zazzaɓi yake dagargazar ɓargonta.





Shiru rashin motsinta yasa Hajiya Babba yo tattaki ta nufo part ɗin nasu ta tarar da AA Waziri a zaune a parlourn ta tsaya yana mamaki tace “Babban mutum yau dama baka fita ba?" Shafa kansa yayi yace “Eh Hajiya wata kasala na tashi da ita shiyasa ban fita ba" nan suka gaisa take tambayarsa Madinah ya kai dubansa ga ƙofar yace “tun safe take bacci" 

Riƙe haɓa Hajiya Babba tayi tace “Baccin sakarai tun safe har la'asar ai a tashi mutum" tana maganar tana nufar ƙofar shiga ɗakin Madinah ta murɗa ta hangota ƙudundune sai rawar ɗari takeyi ta isa gaban gadon da sauri tace “ya Allahu ƴarnan bakida lafiya shine kika shigo kika ƙudundune" tana maganar tana taɓa jikinta tajishi zafi zau daidai lokacin ya shigo ta watsa mai daƙuwa tace “Ashe bata da lafiya shine kacemin bacci takeyi" sunkuyar dakai yayi cike da kunya Allah ɗaya tunda ya tashi ya leƙo bai kuma shigowa ba yace “Bari a kira likita ya dubata" cikin sanyin murya irin ta mara lafiya tace “nasha magani nayi allura zuwa anjima zazzabin zai sauka yama fara sauka tunda gashi na fara gumi" 






A tausaye Hajiya Babba tace “sannu yar nan Allah ya kawo sauƙi bari naje na kawo Miki abinci" fita Hajiya Babba tayi ya isa gefen gadon ya janye mata bargon ya taɓa jikinta yaji yanda ya dauki ɗumi yayi murmushi yace “ke yanzu tun baayi komai ba kika fara karaya da girmanki da komai yanzu me kikeso zakici?" Kawar da kanta tayi tace “Banason surutu ka tafi" rausayar dakai yayi can sukaji an fasa ihu  ta waje ba shiba hatta Madinah da ba lafiyayyiya ba saida ta fice a guje tashin hankalin da suka tarar yasa Madinah sake sakin wata ƙarar ta kwasa da gudu ta zube gaban Nussy tana jijjigata saidai taki motsawa ba komai ne ya sameta ba face zuwa da tayi tana wasa da ƙarafunan dake jikin matakalar benen gidan ko ya akayi oho ta cake maƙogaro dashi har Saida ya hudo gaba jini kuwa kamar an yanka rago.

Iya ƙoƙarin Madinah wannan accident yafi ƙarfinta dole sai babban asibitin Abuja aka kira emergency suka taho sukayi dabaru suka cireta a jiki tun a gurin suka tabbatar da babu rayuwa a jikin Nussy.





Tashin hankali ashe Madinah bata fahimci irin son da AA Waziri yakewa Tilon ɗiyar tasa Nusaiba ba sai lokacin da aka sanar dashi mutuwarta ai yanke jiki yayi ya faɗi cikin wani yanayi na tashin hankali aka daukeshi aka kaishi asibiti ita kuma aka shiryata zuwa makwancinta, ita kanta Madinah wannan mutuwa ta taɓata sosai tayi kukan rashin Nussy domin ta shaƙu da yarinyar shaƙuwa ta gaske gashi yau Allah ya karɓi rayuwarta Nusaiba yarinya me shiga rai ta tafi tabar masoyinta mahaifinta da ƙuncin damuwa.

Kwanaki ukun zaman makokin duka ba'ayi su da AA Waziri ba yana asibiti jininsa ya hau daƙyar Madinah ta samu kansa da bashi hƙr da kuma bashi misalai waɗanda sukafi nashi zafi wannan tasa ya hƙr suka dawo gida, Madina ta mayar da hankalinta a kula da mijinta da kanta.

Cikin lokacin sukayi wata muguwar shaƙuwa soyayya me kwanciya a zuciya ta sarki ruhin junansu kulawa ta musamman suke bawa juna cikin hakan Madinah ta fara laluri ita kenan kullum babu lafiya dakanta tayiwa kanta test saiga shigar ciki a jikinta matuƙa tayi farin ciki da farin cikin mijinta don tasan yanzu duk wani burinsa na duniya ya ta'allaƙa ne akan son haihuwa aikuwa tana ganin gata tattali da kulawa gurin wannan ahli ba shiba ita kanta Hajiya Babba kulawar da take bata ta musamman ce.

Tun cikin yana wata biyar ya fara turowa aikuwa AA Waziri ya tubure shi bazaa wahalar masa da ɗa ba dole abar yawon aiki ta ɗauki hutu to dake suma sunsan matsalarta basu wani wahalar da itaba suka bata hutun tazo ta zauna saidai taci tayi wanka ta fita motsa jiki, cikin na kaiwa wata bakwai suka bar ƙasar gabaɗaya wai ta tafi haihuwa Saudiyya acan ta zauna ta haifo yaronta namiji wayyoh murna gurin waziri kamar an masa kyautar ƙasar Makka.

[7/3, 6:19 PM] Am Oum Hairan: *_JINKIRIN AURE_*



          *_END 43-44_*



_This book is not free Nrml 300 PC 1k view acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu First bank or DM 09013718241_




Ranar sati yaro yaci suna Muhammad a ranar ne kuma suka ɗungumo suka dawo Nigeria jirginsu ya sauka a Abuja  a can suka tarar da Ammi saboda tace itane zata kula da ƴarta da jikanta,

Kwana goma sha huɗu da haihuwar akayi gagarumin shagalin suna  bayan lafawar komai rayuwa taci gaba da gudana cikin jin daɗi da kwanciyar hankali yaronsu yaci gaba da girmansa ɗan yan boko rabin rayuwarsa da nanny danma Hajiya Babba tana gidan tana ɗaukarsa suna yini tare.

Komai ya wuce da haka rayuwa taci gaba da tafiya kamar komai bai faru ba nutsuwa ta samu Madinah anyi gidan kai gashi har iyali sun baibayeta.

Cikin shekaru uku yaranta biyu Muhammad da Nusaiba, irin son da AA Waziri yake nunawa iyalinsa sone da bashida tamka.





Yau asabar ce dukkansu suna gda babu wanda ya fita Nazeer daketa fama da Muhammad ya ɗago ya dubi Madinah dake zaune shirim kamar kayan wanki da tsohon ciki a gaba yace “Wato Dr idan na kalleki sai na rinƙa ganin kamar kafin lalurar Late Nussy ta shigo dake rayuwarmu tun da can na wanku" Murmushi tayi ta zuƙi lemon dake hannunta tace “Eh ba ƙarya bane ba da gaske kasanni kafin wannan lokacin saidai a yanayin daka sanni ɗin ba yanayi ne me daɗi ba, ka tuna wata rana da kuka je Kano asibitin Dawanau bansan meye ya kawoku ba amma kunyimin block mota har nayi maka magana kaso zagina.

Nayi tunanin Da Hon ya fito zaiyi maka faɗan girma amma saiya faɗi wata kalma da har yau takemin yawo a ƙwanya Nazz Allah ɗaya lkcn da kukayimin wannan cin mutumci ya tsaya a raina musamman na Hon saboda shi ba yaro bane saidai tunaninsa a wannan karon yayi kama dana yara wannan tasa naci burin ɗaukar fansa akan Nussy amma tausayi ya gagara barina domin tun ranar dana ɗora idanuna akan Nussy naji tayi bala'in shiga raina" 





Dukkanninsu kallonta sukeyi da mamaki sukace “Kece?" Kada musu kai tayi tace “Zahiri" Murmushi Hon Abdurrahman Abba Waziri yayi yace “Na tuba nabi Allah matata" itama Murmushin tayi tace “na daɗe da yafe maka ai kawai dai ya kamata Ku fahimci talaka ba wulaƙantacce bane kuma bawai sonsa ne Allah bayayi yayisa a talaka ba sannan badon yafi son wanda ya azurta ne yasa yayishi a me arziki ba dukka bayinsa ɗaya ne a gurinsa wanda yafi tsoronsa shine kawai wanda yafi so, Ni zan tashi na koma ciki marata ciwo takeyi master ga yaranka nan kar su zo su dameni su dameka kaida Hajiya" 





Bin ta Hajiya tayi da kallo ganin yanda take riƙe mara tace “Ƙalau kike kuwa Madinah?" Murmushin yaƙe tayi tace “kawai marata ke ciwo nasan idan na kwanta zan samu relief" 

Da wannan ta haye saman ta buɗe ɗakinta ta kwanta ciwon marar na ƙaruwa can taji ya lafa ta miƙe ta shiga bathroom ta tsugunna domin yin fitsari kawai taji an dannota ta rintse Idanunta da ƙarfi jikinta na rawa ta sunkuto ɗanta namiji, ganin yaron yanata wutsil-wutsil yasata sauke numfashi daƙyar ta ɗauki rezar saman wata yar cover da suke zuba kayan wanka ta yanke masa cibiya ta cire ɗankwalinta ta naɗeshi ta lalubo wayarta ta kira Hajiya Babba.





Da gudu Hajiya Babba ta nufo saman tana cewa “Ikon Allah wannan karon haihuwar a sadaka muka sameta" gyara yaron tayi tsaf da mejegon ta kwanta tana hutawa ya shigo gidan bakinsa kamar an masa kyautar duniya ya matsa jikin gadon babbyn ya ɗaukeshi yace “Barakallahu ahsanal khaliƙin wato mazan sukayo kama dani Nusaiba tayo kama dake My life wannan yaron har yafi Muhammad kama dani"




Bayan suna ne kuma rikici ya rincaɓe tsakaninsu ita tace saidai su hƙr da haihuwa shikuma yace bata isaba  rigima har Kano daƙyar aka shawo kanta ta hƙr sukaci gaba da gurgura rayuwarsu da yaransu rayuwar wadata arziki da kwanciyar hankali.

Komansu yana tafiyar musu yanda sukeso da yardar Allah cikin lokacin ne Madinah ta buɗe asibiti nata na kanta a Kano inda AA Waziri ya buɗe mata wani katafaren asibitin a Abuja ta ɗauki ƙwararrun ma'aikata ta zuba.

Tanaci gaba da aikinta da WHO Madinah an zama manyan mata masu aji ga ilimi ga kuɗi ga kwanciyar hankali ga soyayyar miji sannan ga yaranta sun fara ɗagawa, rayuwa a Nigeria tayi musu wahala ita da mijinta yau suna wannan ƙasa gobe suna waccan yaran ne kawai ke zaune a gida 9ja suma kuma da anyi hutu suke dauke kayansu haihuwa daya ta  kumayi ta samu Ummu Adiyyah ga Alƙasim dinta shima ya girma yaranta huɗu ita da kanta haihuwar ta tsaya basu wani damu ba domin yara uku suna ganin sun ishesu rayuwa.





Tammat bih hamdullah





Nan na kawo ƙarshen wannan littafi Mai suna JINKIRIN AURE fatan Allah ya bamu ikon amfana dasu akasin hakan Allah ya rintse idanunmu daga garesu.

No comments

Powered by Blogger.