In Bani Complete Hausa Novel


 _🌹IN BANI🌹

  _DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI_ 

 _Wanan littafin nakine Fauzy, you're very Special, I love you so much, Allah ya raya three plates_ . 


M. Shakur 


1..... 


 Mata ne makil a babban compound din gidan dayasha simenti duk sun sanya anko iri daya, yara da manya sai hayaniya ake anacin shinkafa, wasu nashan pate, wasu nacin tuwon shinkafa da miyan taushe, wasu nacin fried rice da zobo, daga gefe kuma wasu tsofaffi ne daketa rera waka suna buga kwarya, wasu mata na rawa ana shewa ana manna musu kudi, ana guda kana gani kasan gidan biki ne.


Babban gidane mai fadin gaske wanda saika wuce inda ake bikin sanan kabi wata kofa kaje dayar sasan dasuke kira da sasan kaka. 

Kasancewar sasan kaka baida girma sosai babu mutane a tsakar gidan, saidai ko ina fess simentin kasa sai kyalli yake tsabagen neatness din wurin saikuma pampoo dayake diddiga da ruwa dil dil dil da alamu duk wanda yay amfani dashi na karshe bai rufe da kyauba, flat daya ne a sasan kaka dake dauke da wani babban fankacecen falo da akalla zai iya daukan mutane hamsin, falon na dauke da wasu irin hadaddun kujeru maroon color, sai ledan daki mai shegen kyau shima maroon, sai wayansu hadaddun kwaryaye da ake jera ajikin bangon dakin, kana ganin dakin kaga dakin tsohuwa. wani magidanci ne ke zaune yasha fararen shadda inda akamai malum malum sai wata tsohuwa wacce akalla zatakai 79 agefenshi taci atampa daketa gyalli kaman an shafa mai ajikinta, an mata rigan kayan buba da zanin data daura akan rigan, sai kafanta da gabaki dayanshi yasha jan lalli tai lallin da akafi sani da dungulmin tsohuwa, farace tsohuwar, gashin idanunta dana giranta sun koma fari sabida tsufa, sai hancinta daketa uban zufa, dudda tsufanta bai hana kamanninta da magidancin dake zaune kusa da ita bayyana ba alamun mahaifiyarshi ce, cikin muryanta na tsofaffi kuma cikeda masifa tace "Sama'ila, Sama'ila, Sama'ila kaga dai sau uku nakiraka ko, wlh to nagaji, kodai ka tsawatar wanan karan, kona tattara yinawa yinawa nabarma gidanka nakoma chan kauye abina, aikin banza kawai" yanda take masifan yasa mutumin data kira da sama'ila ya sassauta murya yace "kiyakuri Umma na" "bawani zancen na yakuri" ta mishi ihu akah tana nunashi da yatsa tace "iskanci Hamida yay yawa kuma uwarta ke daure mata gindi inba hakaba iskokai ne mutane datake jin tsoron taro iyye? Mayune jama'a? Cha nayi duk yan uwane da abokan arziki suka cika gidan, yau bikin yayarta, yayarta fa Sama'ila amma ace tun safe ba'aga yarinya ba tasaci hanya ta sabe tafice, yo kajimin yar bazan yarin..." shiru tayi sabida sallaman da akayi wata kyaykyawan mace mai jiki doguwa tasa hadadden paper lace doguwan riga pitch da akamai stone work, ta shigo dakin fuskarta ba yabo ba fallasa ta karaso ciki ta gaida tsohuwar. "sannu da hutawa Umma" hararanta tsohuwan tayi batare data amsaba hakan yasa matar ta dubi mutumin dake kallonta tace "gani Alhaji ka aiko akirani" cikin fushi yana girgiza kafa yace "ina Hamida?" shiru tadanyi tana kallonshi kafin ta sauke ajiyan zuciya cike da damuwa tace "Alhaji nima bansan inda take ba" "karya takeyi na rantse maka Sama'ila, matar nan makira ce, itake kara lalata Hamida, wlh, wlh Sama'ila kajini na rantse maka na sake rantsewa in bata nemo Hamida ba saina bar gidan nan nakoma kauye abina dama nafi samin kwanciyan hankali achan" takarashe maganan tana uban huci kaman tana filin yaki, kallonta mutumin yayi cike da takaici yace "haba Umma, to kibari nai magana mana, nace kiyakuri babu inda zaki, kiyakuri kinji" kwafa tayi tawani juya ido tana karkada kafa tace "nayi, yi maganan ka" kallon matar yayi datai shiru tana kallonsu, anatse yace "Halimatu ina Hamida taje?" ahankali tace "wlh Alhaji nima bansani ba, bansan inda tayiba, ina fama da jama'an biki ban masan bata gidan ba saida Ihsan tazo ta fadamin" cikin fushi da tsananin takaici yace "to kije koma ina take ki nemota kindaisan Umma tace da ita za'akai yayarta chan legas gidan mijinta ko, na fadamiki kinemota ta dawo gidan nan right away" dan ajiyan zuciya ta sauke tana kallonshi kafin ta girgiza kai kawai cike da takaici ta juya zata fita daga dakin saikuma ta juyo ta kalleshi da idanunta da sundan chanza kala tace "amma Alhaji kasan matsalan yarinyar nan batun yauba ko, batun yau mukasan matsalan Hamida na Agoraphobia ba, batasan mutane, tanada tsoron shiga taro, tun tana yarinya haka take, yanz..." cikin fushi ya katseta ta hanyar cewa "yanzu yarinya ce? Me amfanin ki amatsayinki na mahaifiyanta? Kinga kisan yanda zakiyi kinemo Hamida kindaiga ran Umma abace yake kina kara bata lokaci ne karfe biyar za'a zo daukan Habiba yanzu karfe uku harda kwata" juyawa tayi ahankali tafita daga dakin, da kyar ta iya saita fuskanta ta amsa gaisuwan da mutanen tsakar gida ke mata amatsayin ta na uwar amarya ta wuce ta shiga bangaren su inda falon ma ke cike da jama'a makil, corridor su tayi tabude wani daki ta shiga mace dayace a zaune a dakin tana hada kayan akwatin amarya data ciro kana ganin matar kaga kamaninta da matar data shigo, maida kofar tayi ta rufe ta shigo ta zauna kan gado dabas da sauri tasa hannu tana goge kwallan daya zubo mata, da sauri matar dake hada kaya a akwati ta saki kayan hanunta tazagayo tazo ta gabanta tace "menene kike kuka Maman Ayush?" share idanunta tayi tanadan nishi alamun kuka nacinta tace "Yaya narasa yanda zanyi da Hamida, kullum, kullum dakika sani saita jamin cin mutunci daga wurin Alhaji da Umma, laifinane Yaya? Nina hallice ta? Munanan dake ai inata trying number ta baya shiga, natura yan uwanta duksunje makota kiramin ita ba'a ganta ba, Yaya ya zanyi? Narasa yanda zanyi na chanza Hamida, narasa wace irin yarinya ce, imagine fa Yaya yau bikin yar uwarta ma ta gudu tabar gidan, ni yanzu a ina zan ganta, yaya zanyi da raina?" takarashe maganan cikin daga murya sosai hawaye na gangarowa daga idanunta, da sauri Yayar tata mai suna Yaya Lami wacce take her only sister a duniya ta rungumeta ta daura kanta acikinta tana shafa bayanta tace "ya isa, ya isa dena kukan, bari na gwada kiranta kozai shiga, is okay."


 _Kukkuruku old train station._


Babban train station ne that has been abandoned for years yanzu, ba'a amfani dashi sabida sabon da aka bude, wajen shiru babu mahaluki ko daya sai wani tsoho baba mai gadi dake kwance kan wata yar katifa yakafa babban radio dinshi a kunenshi yaja antenna waje yana sauraran labaran rana.


Zaune take akan dan danddamalin dake kusada railway, tana sanye da bakin hijabi har kasa daya rufe har takalmin kafanta, gefen fuskarta nake hangowa, farace sosai tana sanye da farin eye glasses, gashin idanunta bakin kirin dogaye, lips dinta kananu sunyi pink sosai sun bushe danko mai bata shafa akansu ba, gefenta wani karamin black and white jakane na MK sai wasu duwatsu yan kanana dake gefenta da akalla zasukai guda hamsin, ahankali ta zare hanun damanta dake cikin hanun hijabi data kankame ajikinta ta  daura hanun akan duwatsu, farine hanunta sol da dogon yatsun ta sirara inda farcenta ke dauke da jan lalli, ahankali tai picking one stone tana kallon railway ta sauke ajiyan zuciya mai sauti cikin wata irin siriruwan murya nai bala'in dadi tace "Kakan mu!" jefa dutsen tayi akan railway tabi dutsen da kallo harya sauka akasa dutsen ya hargitsa duwatsan wajen ahankali tace "dutsen nan is just like Kakan mu, duk inda take saita hargitsa komi, Kakan mu! Kaman zakaran dawaki ce kukanta ba na alheri bane, Kaka! she's the definition of Iska ba nauyi gare kiba sai kada itace" wani dutsen ta dauka ta jefa ya sauka kusa da wanda ta jefa dazu ahankali tace "wanan ne Baba, duk inda Kakan mu take yana wurin, baya tsalleke abinda tace, in kana neman sa kanka a bala'i a wurin Abba ka batama Kaka rai, hausawa sunce, Allah ya sauwake wahala, tsohuwa ta ga ajalinta ya kusa" wani dutsen ta dauka ta jefa ya sauka kusa da wanda ta jefa dazu tace "Mama! Mamana! My everything" shiru, ahankali tace "Mama kaman rake take, tanada zaki amma batada tau..." shiru tayi sabida ringing din da wayarta yafara dake cikin jaka.

_🌹IN BANI🌹_ 






2....


Duka jikinta rawa yafara da sauri ta kalli jakan, kasa taba jakan tayi har wayan ya karasa ringing ya katse, yafara ringing akaro nabiyu, sosai hanunta ke rawa da sauri tajawo jakan tabude taciro wayar tata kirar Samsung A50, Anty Lami data gani a screen yasa kirjinta ya buga da sauri ta dau wayar ta kara a kunenta kafin ma tai magana Anty Lami tace "ina kike Hamida? Nace ina kike?" ta daka mata tsawa, sosai hanunta ke rawa, kirjinta na bugawa dan bamatasan mezatace ba, kasa magana tayi but tana iyajin Maman su nacewa "tamiki shiru halan ko? Ban wayan kigani Anty" karban wayan Mama tayi ta kara a kunenta cike da fushi da takaicinta tace "wlh Hamida inba kinaso ki gamu da fushina da kin dade bakiga irinshi ba ki kamo hanya kidawo gidan nan right this second, dan iskanci ana bikin yar uwan ki kin kama hanya kin gudu, kidawo gida yanzun nan kinajina Hamida?" gyada kai tayi bakinta na rawa sosai tace "t...to Mama" katse wayar sukayi hakan yasa tabi wayan da kallo gabaki daya hankalin ta yatashi cewa da akayi tadawo gida, jakar ta jawo ta saka wayan ciki kafin ahankali ta mike tsaye, doguwar mace ce kyaykyawan gaske, fara ce fat kana ganinta kaga Maman su kaman su harya baci da Mama, tana sanye da fararen eyeglass idanunta ba kawalli saidai eyeliner dataja a saman ido dayama idanun wani irin cool kyau, giranta acike da gashi, gashin bakin kirin, sai dogon hancinta da dan karamin bakinta daya bushe, black hijabi ne jikinta wanda hulanshi ya rufe goshinta sosai dan saura kadan ma yarufe giranta amma dudda haka kana hango kwantaccen gashi a forehead dinta, dogon hijabi ne ajikinta dahar kafafunta ya rufe bama ka hango asalin kayan datasaka, da sauri tadau handbag dinta ta rataya tafara tafiya a natse kaman batason taka kasa ahaka ma wai sauri take tafito wajen da sauri Baba mai gadi ya rage karan radio dayake ji ya juyo ya kalleta yace "har zaki tafi Hamida?" gyadamai kai tayi batare data kalleshi ba tana kakkare fuskarta da hijabi kaman wacce tai laifi tana kara sauri, murmushi yayi yace "shikenan sai gobe tunda baza amin magana ba, gobe ma zaki kawomin tuwon ne Hamida?" gyadamai kai tasake yi still batare datamai magana ba tafice daga wurin da saurin ta, murmushi Baba mai gadi yayi yakomar da kanshi ya daura akan filo yana murmushi ahankali yace "Hamida kenan" yasake yin wani murmushin ya kara karan radio shi yacigaba dasauraran shirin da ake. 



Da sauri take tafiya akan titi tana kakkare fuskanta da hijabi, keke napep ta tsayar ta shiga ciki da sauri tana kallon gefe daya batare data kalli mai keken ba tace "j...jan bulo zani" "naira dari uku ne kudin ki hajiya" gyadamai mai kai tayi tana kara rufe fuskarta da hijabi tace "to" tada keken yayi suka fara tafiya har zuwa jan bulo sosai gabanta yafadi dan sosai anguwan su yacika da manya manyan motoci, da mutane ga maza ko'ina, jitayi hankalinta yatashi tunanin ta shine yanda zata wuce mutanen ta shiga gidansu, ahankali tace "yayi nan" tsayawa mai keken yayi ta zage jakanta taciro dari ukun ta bashi sanan tafito tana kare fuskarta da hijabin ta saukar da kanta kasa tafara tafiya ahankali batare data bari sun hada ido da kowaba kirjinta kaman zai fashe zuciyata kaman zai fito waje, a kofar gidansu ta tsaya chak ta leka ciki uban mutanen data gani ciki yasa ta koma gefe jikinta na rawa duk ta birkice, wata yarinya ce kyakyawa da bazata wuce 10yrs ba tafito sanye da doguwan rigan ankon dayamata kyau sosai, ware manyan idanunta tayi ta kalli Hamidan dabama ta lura da itaba sai kakkare fuskarta takeyi tana sake mammanewa ajikin gate dinsu kaman wacce tai laifi ake shirin kamawa akaita ciki, cikin daga murya tace "laaaa Anty Hamida yaushe kika dawo? Ina kikaje anata nemanki? Kinga anma kusa kai Anty Ayush" dan janye hijabinta tayi back jin muryan kanwarta ta kalli kanwar tata dake kallonta, da idanunta dasuka cika da hawaye cikin rawan murya tace "I..Ihsan jeki fadama Mama nadawo ni bazan iya shigowa ba mutane sunyi yawa" juyawa Ihsan din tayi ta leka compound din saikuma ta dawo wurinta tace "wlh Anty Hamida babu wasu mutane fa, su kawayen Mama ne dana Kaka, saikuma su maman Rabi makotan mu, zomuje ki shirya kisaka ankon ki" tai maganan tana kamo hanunta, sake komawa baya tayi tana zaro mata idanu kaman zatai kuka da yar karaman cool voice dinta tace "Ihsan stop dan Allah kunyan shiga nake" daidai lokacin wata budurwa da bazata wuce sa'an Hamidan ba tazo zata wuce ta shiga gidan dan daga gidan Pharty su na kawayen amarya take taci gayu sosai cikin ankonsu na yan mata wani pink ashobi doguwan riga an mata dauri hadadde tadan yafa gyale a kafada, kwala mata kira Ihsan tayi. "Anty Zainab" da sauri budurwan ta juyo ganin Hamida tsaye tana kakkare fuska da hijabi tana komawa baya yasa ta rike waist takaraso wajensu cike da mamaki tana kallon Hamidan tace "Kinga daman dawowa Hamida?" da sauri Ihsan tace "Anty Zainab kinga wai bazata shiga cikiba, kumafa Mama na nemanta tun dazu dasafe, Kaka ma ta aikani nemota yafi sau dari uku" kallonta Zainab din tayi ta harareta tace "wuce mutafi" da sauri ta share hawayen dasuka zubo mata da hijabi tace "Anty Zainab mutane" "to uban me zasu miki? Cinyeki zasuyi?" kallon wajen tayi cikin tashin hankali tace "nidai zan tsaya anan kucema Mama nadawo" ganin kara makalewa take a bango kuma tasan halin ta tsaf inba ka tursasata ba wlh bazata shigan ba yasa zainab ta karasa  wajen ta finciko hanunta tajata da karfi, fashewa tayi da kuka sosai tana waigen baya tana neman fizge hanunta daga na Zainab din, da sauri Zainab tace "rikemin dayan hanunta Ihsan mu shiga ciki" da sauri Ihsan din ta rike dayan hanun suka jata zasu shiga ciki, fashewa tayi da kuka duka hankalinta yatashi tanason kwace hanunta takasa dan zainab akwai shegen karfi, cikeda tsoron shiga gidan tace "Anty Zainab dan Allah no, please kinji wlh kunyan shiga ciki nake, ai nadawo kusakeni bazan kara fitaba, kunya nakeji" waigawa baya tana neman abinda zata rike dan karsu shiga da ita ciki karaf suka hada ido da Ya Faruk yana zaune kan white Lexus dinshi yaci farin shadda gizna hanunshi rike da waya yana kallonsu, wani mugun kallo ya watsa mata da sauri ta dauke kai tana share hawayen da sun kasa tsayawa suka shiga gidan da ita da karfin tsiya, kara fashewa tai da kuka sabida yanda ake kallonsu ta rufe fuskanta da hijabinta da sauri hankalinta duk atashe, dakin Mama suka bude suka shiga da ita ciki Zainab tace "Mama gatanan tun tuni tana waje taki shigowa shine na jawota" wani irin kallon takaici Mama ke mata gashi ta tsaya tanama mutane kuka aka hakan yasa wani irin zuciya ya debi Mama ta tashi ta zuba mata mari tana huci, ihu tayi ta tsugunna akasa tafashe da kuka sosai, cikin fushi Mama tace "kukan ubanme kike mana iyye?" zata kara kai mata wani dukan Anty Lami ta riketa tace "ke Maman Ayush dena dukanta, addu'a ake ma yara" cikin tsananin fushi tace "wani irin addu'a Yaya? Kullum Hamida saita jamin cin mutunci, meke damunta ne? Yanzu bagata ananba ta wuce mutanen wani abu yasameta? Wlh Yaya kimata magana kotamin shiru kona sassaba mata Allah bazance ta girmaka duka zan kirba mata kaman yar shekara biyu agidan" hanunta Anty Lami ta rike ta zaunar da ita tace "calm down, ya isa haka, kidena bata rai yau babban ranace kina aurar da ya baikamata kina fushi ba" ta juyo ta kalli Zainab dake tsaye itama tana kallon Hamidan data boye fuska cikin hijabi tana kuka tace "ina ashobin nata Zainaba?" "yana dakinmu" tafada ahankali, "yauwa to jeki dauko ki kawomin tai wanka ta shirya taje wajen kakan ku dake nemanta kafin ku tafi" juyawa tayi dan zuwa dauko ashobi, ta kalli Ihsan datai shiru tana kallon Hamidan idanunta sun cika da kwalla itama kaman zatai kukan dan ta tsani taga an taba Hamida tace "jeki taya Zainab dauko kayan" juyawa tayi tafice tarufo musu kofan hakan yasa Anty Lami ta dawo inda take tsugunne tana kuka ta dagota tana murmushi tace "haba Hamidan Maman ta, mai kama da Maman ta" tsakin takaici Mum tayi ta tashi tafice daga dakin, sakinta tayi ahankali tace "oya cire hijabin kije kiyi wanka kizo ki shirya" gyadamata kai tayi ta zare eyeglasses din idanunta ta sauke handbag dinta tasa aciki tana goge idanunta da bayan hannu da hawaye ke zuba ta ijiye jakan ta mike tana kallon gadon ganin ba Mama, ahankali ta zare hijabin ta ijiye akan gadon, kyaykyawan yarinya ce Hamida bana wasaba, gawani irin shape da Allah yamata mai bala'in kyau tana sanye cikin simple riga da skirt na wani poker dot silk material skirt din yabi jikinta yafito da fine curve hip dinta rigan ma yakamata yay mata shegen kyau, kitson shiku ne akanta manya manya dabaza su wuce guda gomaba, gashinta dogon gaske yay tsufa gashi ya kwanta akan goshinta sosai, babu dan kunne a kunenta,looking naturally beautiful, sake goge hawayen daya zubo mata tayi Mama Lami tace "Ya isa kukan haka wuce kije kiyo wankan ki kinji Hamida" gyadamata kai tayi ta wuce tabude bayin dake nan dakin Mama ta shiga bata wani jima sosai ba tafito daure da zani kayanta dasu Zainab suka kawo Anty Lami ta nuna mata akan gadon, daukan kayan tayi bayan tagama tsane jikinta ta shirya cikin kayan doguwan rigan itama aka mata kaman na Zainab bakaramin kyau dinkin yamata ba yafito da shape dinta sosai, zama tayi kan gadon tana wasa da yatsu Anty Lami tace "tashi zakiyi kiyi kwalliya kije kakan ku na kiranki" gyadamata kai tayi tana kokarin danne kukan datakeji taje gaban madubin Mama ta tsaya, tashafa farin hodan data gani awurin, ta shafa man baki, Anty Lami daketa binta da kallo sabida kyan datayi dudda batai gayuba sosai ba amma tai wani irin kyau tace "bayan kin dawo daga wurin kaka kije dakin ku kihada kayan da zakiyi amfani dashi in kinje Lagos din ance kwana uku zakuyi" hawaye ne suka zubo mata da sauri ta share, hararanta Anty Lami tayi tace "ai kyaji dashi lamarin ki ya tabarbare Hamida wuce kibani wuri danni inzan miki nawa wlh saiyafi na wanda maman ki tamiki, kayan takaici kawai mtsww" taja tsaki, ahankali takoma gaban gadon tadau hijabin ta ta zura, baki Anty Lami ta bude tace "kinsa ashobi ki na yan mata saikin saka hijabi kuma? Lallai Hamida nidai wuce kiyi duk yanda zakiyi kekika sani" ta nuna mata hanyar kofa, ahankali tadau jakanta tawuce tafita daga dakin mutanen data sake gani chaa ana hayaniyan biki yasa taja hijabin ta rufe fuskarta tana tafiya ahankali ko ina na jikinta na rawa, kafin takai falo taci karo da mutane sama da goma sha da kyar tasamu ta fice tai hanyar sassan kaka, karo taci da mutun da sauri tai gaba zata wuce batare data dagokai ba taji an wani irin fizgota, a tsorace tadan dago kai hada ido sukayi da Ya Faruk yadaure fuska kaman baitaba dariya a duniya ba, saukar da idanunta tayi kasa bakinta narawa sosai tace "s...sorry Ya Faruk" wani irin matsiyacin kallo yamata hakan yasa jikinta yadau rawa, cikin wani irin kakkausar murya yace "mahaukaciya kawai" yawani irin turata, ahankali ta dagakai ta kalleshi da idanunta dasuka cika da kwalla shima ita yakema wani kallon tsana, cike da dakewa zuciyarta na tsinkewa sosai tace "niba mahaukaciya bace".

_🌹IN BANI 🌹_ 





 _M. Shakur_



3....


Cike da fushi yawani irin daga hannu zai dauketa da mari daidai lokacin Kaka ta leko, da sauri tace "wlh katabamin ita Faruku Allah ya isa, nitama laifi bakaiba, tamin laifi kaitamawa dazaka fara hukunta? Wanan rapkeken hanun naka mai kama dana basamude zaka zuba mata salon ka nakasamin ita mugu mai zuciyar sojoji, cikata" takaraso wajen tana nishi ta janye hanun Faruk din daga jikin hijabin ta ta ingizata ciki tace "wuce ciki kijirani miskilan yarinya" cikin tsananin fushi Faruk ya fizge hanunshi daga na Kaka yace "dalla chan ki sakeni karki sama fararen kayana datti ni" da sauri ta kalli hannayenta tace "Allahu Akbar wlh babu dauda a hannuna fa Faruku, yi hakuri kaji dena fushin" ta kawo bakinta saitin kunenshi kaman zatai gulma tace "nafiso na hukunta ta dakaina ne, inna bari ka hukuntata aisai ka karasata baka ganta daban bane acikin yaran Sama'ila guda bakwai da Allah yabashi, kabarni da ita nasan maganin ta" hararanta yayi yajanye kunenshi yace "dalla ni kidenamin gulma a kunne, kuma wlh bazan siyomiki namijin goron ba" zata kamoshi yawuce yafice abinshi haba takama tana hararan bayanshi tace "chan ka karata, sojan banza sojan hofi yanda kakeda zuciya inna barka kashe wanan ja'iran yarinyan zakayi" tajuya tashiga dakin a zaune ta ganta akasa jikin dogon kujera tana wasa da yatsun ta, wani mugun kallo ta zuba mata tace "daga ina kike? ina uwarki ta turaki tun safe kikaje kika labe?" girgiza kai tayi tai shiru batare datace komiba, kwafa Kaka tayi tace "nikika maida wawiya ina miki magana kinmin shiru? badai uwarki ke bataki ba to wlh zan gyaraki ne, zan gyara miki zama Hamida, bari zaki gani, kina dawowa daga legas dinan yinaki yinaki zaki tattaro ki dawo nan sasa na dazama ja'iran yarinya kawai, ga furanki chan a fridge inkin ga dama ki dauko kisha" tashi tayi ahankali tai hanyar fridge din ta dauko furan tadawo ta zauna tafara sha, kasama sha tayi sosai sabida yanda Kaka keta jifanta da mugun kallo kaman zata kasheta, ahankali ta ijiye cup din ta mike tsaye, hararanta tasake yi tace "ina zaki? Baki barin sasan nan harsai anshigo da Ayush namata fada sanan zan rike ki da kaina na tura ki a mota, ja'irar yarinya marason mutane, saisa haryau batada mashinshini ko daya, duk yayyinki sunyi aure ga Ayush nan itama tayi, ga Zainaba samarinta har kadasu nake tsabagen yawansu kullum dai kina ganin dakin nan nawa da yar bakan leda samarin su suke shigowa dashi, keko mai bakin jini ko mashinshini kwara daya baki dashi balle nasaran koyar dubu biyu wataran nasamu tasanadin ki, Hamida, Hamida wlh ki chanza hali inba hakaba zaki tsofe a gida ko mahaukaci bazaice yanayi ba balle namiji cikakke mai mutunci, macen dabata shiga jama'a ina zata taba samin mashinshini iyye?" tai maganan tana buga cinya, hawaye ta share tana turo baki tace "salla zanyi" mugun kallo tasake watsa mata tace "wuce ai kinsan hanyar pampon jekiyo alwalan kizo kiyi sallan bance kihadani da Allah ba" juyawa tayi tafita daga dakin ahankali tsugunnawa tayi gaban pampoo ta daura kai akan cinya tana kuka mara sauti tayi minti uku ahaka sanan ta dago kai tashare hancinta dayay jajir, ahankali tabude pampoo tafara alwala tana gamawa ta tashi ta shiga dakin, hanyar uwardakan Kaka tayi Kaka ta nuna mata dadduman dake kan kujera tace "dauko wanan kiyi sallan akanshi bazaki shigan min dakiba" komawa tayi tadau dadduman ta shimfida anan tsakar falon tahau kai tai sallan la'asar, bayan ta idar ta linke dadduman ta ijiye akan kujeran ta zauna akasa ta tankwashe kafa Kaka kuma na ballan namijin goro tanaci abinta, sallaman Mama yasa ta dago kai da sauri ta kalleta, shigowa Mama tayi dakin dauke da karamin trolley da handbag dinta ko inda take batayiba ta ajiye ta kalli Kaka dake kallonta tace "Umma ga kayan nan nata" washe baki Kaka tayi tace "yauwa Haleematu kokefa, kinga inmuna mata hakan  kotanaso kobataso zata dena tsoro da shegen jin kunyan nan, haka zamu dinga chusata cikin mutane dan gaskiya bazan bari tamin kwantai agidaba sonake ayi bikinta tareda Zainaba, amma in kullum tana makale damu, makale a dakinsu bata shiga mutane tayaya zatai mashinshini, daga saman silin din dakinsu Allah zai jeho mata miji? Kidinga sata a jama'a Haleematu kinji" gyadamata kai kawai Mama tayi kaman ba Kakan data mata tatas bane dazuba tace "to Umma in sha Allah zan dinga sata, antashi tafiya yanzu za'a kawo Ayush wurinki kimata fada" sake washe baki tayi tace "to, to shikenan ai, a shirye nake dama dazu rashin ganin miskilan nanne ya konamin rai" juyawa Mama tayi zata fice Hamida takara binta da kallo idanunta sunyi raurau dan ta tsani taga Mama na fushi da ita, dan juyowa Mama tayi suka hada ido watsa mata mugun kallo tayi tasakai tafice daga dakin, nuna mata jakan Kaka tayi tace "zoki kwashesu daganan yanzu za'a kawomin amarya" tashi tayi ahankali tazo taja jakan takomar dasu gefe, matane dayawa suka shigo sasan ana waka ana guda ansaka amaryan datasha alkyabba a tsakiya aka shigo bangaren Kaka da ita, wata kawar Mama tace "kaka ankawo jika kimata fada kisamata albarka" fashewa da kuka Kaka tayi tana soka hannu a lalita tace "Ayush yarinyar arziki, yarinyar kirki ga kwakwalwa wlh ba irin wasu ba kullum nabayan kashi sukeyi a makaranta, Allah ubangiji ya baku zaman lpy da mai gidan ki Muhammadu yaron kirki, Allah yabaku zaman lpy kinji Ayush" kudi taciro yan dubu daidai har dubu ishirin ta kamo hanun Ayush tasaka tace "gashi kina zuwa chan legas din ko albasa ce ki saro kifara saidawa kinji" kashewa akai da dariya awajen sosai danhar Hamida data cusa fuskarta a hijabi saida tai murmushi, hararan su Kaka tayi tace "karki biyema rubabbun nan Ayush dake dariya, aure saida sana'a inka cika tambayan miji bani bani bani gajiya suke afarama wulakanci, zamanin mu babu abinda ban sayar ba, daddawa, kuka, wata tsiya wata tsiyace dukna siyar, Allah miki albarka kinji Ayush dita" gyadamata kai Ayush dake kuka sosai tayi, Kaka tace "to kutashi kutafi karkuyi lattin jirgin saman dazakubi" ta juya ta kalli Hamida data makale jikin kujera tana kare fuska da hijabi tace "tashi kidau jakan ki muje dakaina nan zan saki a mota" fashewa tai da kuka sosai kaman za'a yankata, Zainab taja tsaki tafice daga falon abinta, ta alkyabba Ayush da ake fitarwa waje ke kallon yanda Hamidan ke kuka rabon data sata a ido tun jiya dasafe, tsawa Kaka tamata ganin batada niyyan tashi tace "tashi nace kona kira ubanki nafadamai wlh" da sauri ta mike tsaye, hararanta Kaka tasakeyi tace "ina abin idanunki?" ahankali ta nuna mata handbag dinta, dauka tayi ta mika mata ciro glasses din tayi tasaka kaka tace "dau akwatin mutai" jan akwatin tayi Kaka takama dayan hanunta tajata suka fita daga dakin sukai waje sai sunnar dakai take jikinta narawa sosai ko kadan bataso tai tafiyan nan, har wajen motocin daukan amaryan Kaka ta kaita inda har anma saka amaryan, ihu tayi tana leka jeep din wanda daga Ayush amarya sai Anty Lami dawata kawar Ayush Amina, dawata kawar Mama sai Zainab, da Ihsan da hannu Kaka ta nuna Zainab tace "Zainaba ke da Ihsan ku fito kushiga dayan motan wanan ja'iran nakeso nasa anan dan asaka mata ido ga Lami nan inba hakaba zata iya guduwa tace bazata ba, ku fito nace" tai maganan tana hararan su tana kama kugu, fitowa Zainab da Ihsan sukayi sukai motar gaban su suka shige, Kaka ta kalleta yanda taketa share fuska da hijabi tace "wuce ciki yar tselen uwa" ahankali ta shiga ciki Kaka ta karbi akwatin datake shirin shiga dashi tace "wanan a boot za'a saka" Abokin angon dake sanye da Navy uniform ne ya karbi akwatin daga hanun Kaka ya bude boot ya saka, aka shishiga motar aka tada Kaka ta daga musu hannu, saida taga tafiyar su sanan takoma cikin gida tana murmushi ranta fess.




Sosai take share hawaye a mota hanunta har rawa suke, ahankali Ayush dake zaune kusada ita ta mika hanunta ta daura kan nata ta rike, da sauri ta dago rinanun idanunta ta kalli Ayush din hada ido sukayi itama idanunta sunyi ja ta girgiza mata kai, da baki tamata alamun "stop crying" hakan yasa ta share hawayen ta damke hanunta gamgam ahaka harsukakai airport suka fiffito daga motan kanta akasa ta rike Ayush gam har suka shiga jirgi jirginsu yadaga jitake kaman zata kurma ihu. 




 _Lagos_

Misalin 7:25 jirginsu ya sauka a Lagos, wasu manya manyan hadadun cars ne sukazo dukansu har lokacin tana rike da hanun Ayush kanta akasa kaman zatai ihu, suka shiga mota, abokanan ango suka kaisu gidan Ayush dake cikin Navy Barrack, gidane mai kyau hadadden gaske, sai alokacin hankalinta ya kwanta ta natsu ganin su kadaine agidan, barin musu dakin da aka aje Ayush din tayi tafito ahankali tana kalle kalle Ihsan biye da ita ta shiga dayan dakin dake corridor, dakin katifa ne da ledan jikinta kejiki, ko shimfida gadon ba'a yiba dayake ba'a gama jere ba, hand bag dinta ta ijiye ta wuce ta shiga bayin dakin tadauro alwala daidai lokacin Ihsan ta bude kofan ta shigo tace "salla zakiyi Anty Hamida?" gyadamata kai tayi tace "inane gabas?" karasowa cikin dakin Ihsan tayi bayan ta kulle kofan tace "bansaniba nima Anty" "daukomin wayana muduba compass" da sauri Ihsan taje kan gadon wurin jakanta tabude taciro wayar ta kawo mata bude wayar tayi kasancewa ba key tabude compass ta nemi gabas sanan tai murmushi tamikama Ihsan wayar tace ajiye kiyo alwala kizo muyi salla to tace tawuce bayin, kabarta sallan tayi Ihsan tafito ta zauna gefen ta saida ta idar tace "to Anty kiban hijabin ki nibanzo da hijabi ba" hararanta tayi tacire hijabin ta mikamata ta tashi ta koma kan gado tadau wayar nata tabude tana dube duben hotunan su, Ihsan na idarwa tai tsalle  tafada bayanta hakan yasa tasaki kara. "wash Allah na, Ihsan zaki karyaniii" tai maganan kaman zatai kuka, dariya Ihsan tayi tana kallon hotunan su datake kallo awaya tace "kawo wayanki kiga Anty Hamida" hararanta tasake yi dayawani irin karama fuskanta kyau tace "bazan bayarba salon ki kara batamin waya kaman wachan lokacin ko" "Hamidaa!" Anty Lami ta kwala mata kira da sauri ta tashi daga kan gadon tace "na'am" fita tayi da sauri Ihsan tabi bayanta da kallo tace "yes, ai yanzu na iya waya har chatting na iya bakaman da ba" facebook dinta ta bude tana murmushi tana dube dube ganin bata da friends banda su Anty Ayush, zainab dasu Anty Rukayya yasa taja tsaki tana turo baki, tace "dukma yan gidanmu ne friends dinta" suggestion din da Facebook ke nuna mata na add friends tashiga tana kallo tasake turo baki tace "ai wlh sainai adding dukansu" d sauri tafara adding mata friends din, tai adding friends yafi dari da hamsin da kanta tagaji da clicking ta saukar da ajiyan zuciya tace "Allah sa suyi accepting I will check gobe kokuma cikin dare yau when she's sleeping" kashe data tayi ta fita daga facebook din ta shiga dialog tana dubawa daga Mum sai Anty Ayush sai Anty Lami yawanci suke kiranta, tsaki tasakeyi tace "wayar Anty Hamida is so boring bakaman na Anty Zainab ba, wai yaushe Anty Hamida zatai saurayi ne" ajiye wayar tayi da sauri tafice sabida kiranta da Anty Lami tayi itama, hadadden abincin da aka kawo musu duk kowa ya dibi cinshi, kadan Hamida ta iyaci ta tashi takai plate din kitchen Anty Lami tabita da kallo tanajin su Zainab da kawayenta na hiran Pharty da za'ayi gobe a ship wanda abokan mijin Ayush suka hada akan ruwa za'ayi Pharty, tabe baki tayi aranta tace aisai kuyi tayi mayun Pharty, alwala tayi tazo tai isha'i sanan tafada kan gadon sai bacci dan ta mugun gajiya.

_🌹IN BANI 🌹_ 






 _M. Shakur_




4.....


Kiran salla asuba yatada ita daga bacci mai dadin datakeyi, ahankali tabude idanunta tana karanto addu'an tashi daga bacci ahankali Ihsan tagani sanye da kayan bacci zaune achan edge of bed tana mata danne danne a wayanta, tadage tanayi kuwan harda murmushi da sauri ta tashi zaune cikin cool siririyan muryanta takira ta. "Ihsan!" a mugun firgice Ihsan ta kalleta da sauri ta ijiye wayan tana sauka daga kan gadon tai hanyar kofa tsorace tace "am sorry Anty Hamida, please don't beat me, am looking for a friend for you kiyakuri please Anty Hamida na, wlh bazan karaba kinji sorry" tai maganan tana komawa baya tana kokarin kama handle din kofa, yanda taga ta daburce yasa da sauri tadau wayan dan taga metayi da wayanta akan Facebook messenger taga Ihsan na chatting dawani account mai suna Aadil Muhammad Thani, da sauri ta zaro ido ta daura hannunta ta dafe kirji, tsabagen mamaki ma takasa bude chat din ta kalleta tace "innalillahi Ihsan you are chatting with a man on my phone" ta sake dafe kirjinta, da sauri ta ijiye wayan kan gadon ta sauko tace "saina fadama Anty Lami wat u are doing" da sauri harda gudu Ihsan tadawo ta rike hanunta tafashe da kuka sosai tace "dan Allah kiyakuri, dan girman Allah kiyakuri Anty Hamida, I just wanted to find a friend for you naga baki da friends a facebook dinki, jiya da mukazo duknai adding nasu, and I only tell him my name and your name, I told him we are looking for a friend, and shikadai ne nakeson sunanshi saisa ma namai magana kuma is  yaki accepting friend request dinne shine namai magana, and baima kulani ba, bece komiba, am sorry kinji Anty Hamida" tsayawa tayi tana kallon Ihsan din mamaki ma take ta yanda tasan kan chatting she's just 10 fa, she's sure a wurin Anty Zainab taga tanayi harta koya, fizge hanunta tayi dan kawai ta kara tsorata tace "nidai baruwana, as small as u are har kin iya begging maza suyi accepting friend request dinki, no kinma iya adding dinsu on top of that begging dinsu suyi accepting naki dakuma wayana, my phone ko sabida kin rainani, Allah kaimu gida saina fadama Baba" tana fadin haka tawuce tabude bayi ta shiga ta rufe, fashewa dawani irin shegen kukan tashin hankali Ihsan tayi tadaura hannu akai, a rayuwata tana mugun tsoron Baba, rasa mezatayi yasa tadau wayan da sauri tana kokarin typing dama baimayi replying ba amma yanda hanunta ke rawa sosai yasa tama kasa typing tai pressing voice recorder cikin kuka sosai tafara VN tace "please Uncle kagani I don't know you, please don't accept the friend request again, dama I was looking for a friend my Anty Hamida she's always alone batason mutane, everyday our grandmother use to insult her and she cries, and I hate to see her crying, please kayakuri don't accept d request am just 10yrs old ina basic 1 ne, kaga Anty Hamida tace saita hadani da Baba ina using phone dinta in the night ina magana da maza, please am sorry ai banyi magana dakai bako? Kaima shaidane, and u are d only one danama magana ma because your name is so cute, Maybe ma empty account ne bakama chatting, okay bye bye I will not do it again" tura voice note din tayi tana kuka sosai harda majina abunka da auta kuma shagwababbiya sanan tai deleting conversation din gaba daya ta zauna a wurin tana kuka sosai ta ijiye wayan, bude kofan Hamida tayi tafito daga bayin da sauri ta tashi tafada jikinta tasaki wani kukan tace "please am sorry Anty Hamida i will not do it again" sosai tabata tausayi hakan yasa ta share mata hawayen tace "to dena kukan, waya koya miki chatting?" cikin kuka tace "no body inadai ganin yanda Anty zainab ke chatting ne intanayi saisa nima nayi naga bakida friends a facebook saiyan gidanmu, I want you to be chatting kaman Anty zainab ne saisa, am sorry kinji bazan karaba wlh I've even told him not to accept kuma nai deleting komi" murmushi tayi tace "don't try that again, jikiyo alwala kafinan na idar nabaki hijabi na kiyi sallan kema" gyadamata kai tayi tana matse kwalla tawuce ta shiga bayin, nafila tafarayi kafin tai sallan asubahi ta cire hijabin tabama Ihsan din tana matsawa gefe tana azkar, Ihsan ta karba tasaka takabbarta sallan itama.



Tana cikin lazimi Anty Lami tabude kofa ta shigo, hada ido sukayi hakan yasa tai dan murmushi akunyace tace "ina kwana Anty Lami" hararanta tayi tace "dole kiyi murmushi tunda kin gudo nan kin kwana baki kwana cikin jama'a ba, itakuma wanan data biyoki duk kuka kwana anan kun kyauta ai, tunda kun tashi in kugama kufito mukarasa jeren komi" maida kofan tayi tarufe tafice.

Ihsan na idar da sallan suka fita daga dakin, aiki suka farayi suna gyara gidan dan karfe hudu ne  boat cruise party su, babban boat abokanan ango sukai hiring na Nire prest company, Zainab da kawayen Ayush din sai maganan party suke dan a arewa basu tabajin anyiba, sai wuraren one suka gama da sauri ta gudu dakinsu Ihsan ma tabiyota salla sukayi Ihsan ta debo musu abinci suka ci dan bataso takara fita dan gidan yacika da baki matan abokanayen shi ga makeup artist din da aka dauko dazata musu makeup suna gamaci tahau gado Ihsan tabi bayanta sai bacci.



Wuraren uku na rana Anty Lami ta shigo dakin taci gayu cikin wani hadadden lace baki daja dayay mata kyau sosai, baki tabude tana kallonsu yanda suke bacci abinsu kafin ta karaso wajen gadon ta daka musu duka a firgice dukansu suka tashi bayi ta nuna musu cikin fushi tace "tashi kije kiyo wanka right dis minute kisa ashobin ki ki fito amiki makeup, ke Ihsan tafi bathroom din dayan dakin kiyi wanka" da sauri Ihsan ta sauka daga gadon ta wuce dan bataso tai missing party nan for anything bata taba ganin party da akeyi a jirgin ruwaba ba kuma akan ruwa ba, kallon Hamida tayi dake sosa ido tace "wuce kema" ahankali kaman zatai kuka tace "Anty Lami ni bazani ba zan zauna gida tareda ke" cikin tsananin fushi Anty Lami ta nunata da yatsa tace "koki tashi kije kiyo wanka yanzun nan kiyi la'asar kije amiki makeup ki shirya kutafi ko wlh na saba miki Hamida, yanzu nafara yarda da maganan mamanki iskancin ki is too much stand up and get out of my sight my friend" da sauri ta tashi sabida tsawan data daka mata, bayi ta shiga tayo wankan tadauro alwala Anty Lami tagani a zaune ga trolley ta ta shigo mata dashi ahankali ta tsugunna tadau hijabin ta tasaka tai la'asar tana idarwa Anty Lami ta nuna mata sea blue ashobi ta wanda shine theme din party anmata wani hadadden gown, daukan rigan tayi tasaka Anty Lami ta tasata agaba takaita falo inda mata kenan dayawa anata makeup sunnar dakai tayi Anty Lami tasa aka fara mata, raurau tai da ido zatai kuka da kyar ta iya hadiye hawayen har aka gama mata makeup din, duka matan falon kafeta da ido sukayi sabida wani irin shegen kyau da tayi kaman ita tai kanta, hadadden takalmi Anty Lami tabata navy blue tasaka tabata glasses dinta tasa bakaramin kyau tayiba yanda ake kallonta yasa jikinta yafara rawa, horn da aka fara musu ana cewa su fito dan abokan ango tun uku da rabi suka taho yasa ta mike da sauri zata tafi daki hanunta Anty Lami tarike tana hararanta tace "wuce dan ubanki saikinje wlh, Zainab" ta kwalama Zainab dake kokarin sa hill dinta taci gayu sosai kaman itane amaryan kira, da sauri takarasa sa takalmin taje inda Anty Lami take tace "gani Anty Lami" murmushi Anty Lami tamata sabida kyan datayi tace "samomin gyale ta yafa dan bazata saka hijabin nanba yau" fashewa da kuka tayi jin ance bazata sa hijabi ba,  bakaramin kular da Anty Lami abin yayiba tace "wai ke lamarin nan naki baza'a kaiki asibiti ba kuwa?" tabe baki Zainab tayi tace "Anty Lami wlh haka take ni dama kinbarta ta zauna a gidan inba hakaba wlh kuka zataje tana mana tana sunnar dakai tana neman inda zata labe saikace barauniyar datai sata a kasuwa, yar kauye kawai" hararanta Anty Lami tayi tace "kekuma dena cemata yar kauye wuce ki samo gyalen danace" ta kalli Hamida dake share hawayen cikin muryan lallashi tace "haba Hamida na, mai kama da mamanta, kinga kyan da kikayi kuwa? Bama wanan ba bakiso kije kiga jirgin ruwa yau, kintaba ganin jirgin ruwane ai saidai a tv a film irinsu tatanic, amma yauko zaki shiga cikin jirgin ruwa akan ruwa za'ayi party jirgi na tafiya, dena kuka kinji kije abinki inkin dawo kibani labarin abinda yafaru, kinga karma kibata kwalliyan ki" tai maganan tana share mata hawayen datakeyi daidai lokacin Zainab tafito dawani hadadden navy blue gyale ta warware ta yafa mata a one side aiko tai masifar kyau, murmushi Anty Lami tayi tace "iyye Allah nagode ma wanan kyau irin na yarana haka muje na rakaku wajen" rike hanunta tayi suka fita har wajen tasasu a mota Hamida kaman zatai ihu sabida tashin hankali gabanta har faduwa yake tsabagen tsorata sai sunnar dakai take tana kare fuskarta da gyalen jikin nata, daga musu hannu Anty Lami tayi tana dariya dan abin Hamidan ma looks funny dan yanzu yaga maganan zainab datace tana abu kaman barauniyar datai sata akasuwa.

Tashi motar tayi itakuma ta koma cikin gida tana girgiza kai tace "Hamida, Hamida hmmm Allah dai ya kyauta".



Gabaki daya she's not comfortable, gashi sai tafiya suke kaman bazasu kaiba chan lekki sukaje sukai parking a parking lot na Nire prest Boat activities, suka fiffito kafin su karasa waterfront din dukansu suna kallon katoton baban Boat din da akai decorating da flowers seablue, ga mutane maza damata suna kida na tashi, karasawa sukayi suka shiga kirjinta wani irin bugawa yake kaman zai tsage da sauri tarike hanun Zainab hakan yasa zainab ta kalleta daidai lokacin dayake duk angama shiga jirgin yafara gudu a ruwan, da sauri ta rike Zainab gam bakinta har rawa yake tace "An..Anty Zainab wlh am scared, please banaso wanan katon jirgin I don't like water" hararanta Zainab tasake yi dan sosai take jin haushin halin Hamida tace "aisai kiyi tsalle kifada ruwan, look back kiga yanda mukai nisa da wurin da muka bari yanzun nan, jirgi tafiya yake, idan kuma you can swim back there bismilla" girgiza mata kai tayi hawaye zai zubo mata tace "to please hide me kinji, am shy and am feeling somehow, mutane sunyi yawa" tsaki Zainab tayi kafin tajata by fire by force sukai sama jirgin asalin party floor din, ihu Zainab tayi ganin wurin yanda yahadu taciro wayarta zatai selfie tace "Omg this is paradise" Ihsan ma ihu tayi tana tsalle karasawa inda akai arranging kujeru sukayi kida natashi yan mata suka fara rawa, janta Zainab tayi tace "dalla chan zomuyi rawa yar kauye kawai karki kofsani" fizge hanunta tayi da karfi dan sosai kanta yafara juyawa yanda taga mutane dayawa awurin ga karan kida dake tashi ga duman music dahar kwanyanta takeji suna wani irin cika mata kunne kunenta yay wani dumm, duk inda ta juya saita hada ido dawani ko wata ana kallonta, cikin tsananin tashin hankali ta iya bude baki bama tagani da kyau tace "Anty Zainab" sosai idanunta suka fara juyawa hakan yasa ta daura hannayenta kan fuskarta tarufe fuskan kozata dena hada ido da mutane yan rawa na bugeta suna ihu, tai nan tai chan da sauri tace "Ihsan, Anty Ayush, somebody please help me, jiri nake gani" daidai lokacin kuma aka rage kidan wai amarya da ango zasu shigo, ahankali ta janye hanunta daga kan fuskarta ta bude idanunta dake juyawa, gani tayi mutane na komawa kan kujeran wajen suna zama, da sauri kanta na juyawa sosai tafita daga wurin tai baya tana tafiya kaman wacce bata da lafiya, da sauri Ihsan ta tana Zainab dake selfie tace "Anty Zainab kalli Anty Hamida ina zata?" batare data kalleta ba tana selfie ta tace "shareta Ihsan kema kinsan zataje neman inda zata boyene me tsoron mutane, nidai banda lokacin damuwa da lamarin ta am going to have fun and take pictures na nunama yan dept dinmu evidence munyi biki a boat akuma kan ruwa" tai dariya tanajan Ihsan tana hoton da ita.



Da kyar take tafiya tasa hannayenta tasake rufe fuskarta da sauri tafita daga wurin kanta na juyawa tai chan gaban jirgin wurin ba mutane tana kulle ido dan ko kadan bataso ta kalli ruwan dasuke kai da yanda ruwan ke gudu, ihu dataji na jama'a dakuma wani irin duma da sautin music da aka kara kaman zai fasa mata kunne yasa taji duka kanta na juyawa tana ganin jiri sama da dazu kanta na juyawa sosai da sauri ta zare hannayenta daga kan fuskarta ta kalli sama idanunta na kankancewa, sosai saman ke juyamata hakan yasa tafara juye juye itama tana mikar da hannu trying to hold on to something da kyar cikin layi tace "Ma...ma" bayanta ne taji yabugu da karfen jirgi gakida dake tashi ga kanta dake juyawa, wani irin mika tayi kanta yay bayan karfen idanunta suka juya tana kallon ruwan da yanda jirgin ke gudu sosai wani irin iska na walwal da gyalenta dake lilo shima, kara mika tayi hakan yasa glasses din idanunta suka fita daga fuskarta suka fada ruwan yanda take bangara idanunta na kafewa sosai ya rinjayi karfinta kafafunta suka daga tai cikin ruwan itama takai tsundum!.

_🌹IN BANI 🌹_ 






 _M. Shakur_



5.....


 Hakanan Ihsan taji tanajin wani irin, zuciyarta taki natsuwa sai kawo mata Anty Hamida take aranta da sauri ta kutsa kai tafito daga dance floor din tabi hanyar dataga Hamidan tabi tana kalle kalle har itama takai gaban jirgin amma bata ganta ba, babu ma alamunta awajen da sauri tace "to ina taje" sosai taji tanajin wani iri a zuciyarta tashiga wani irin damuwa hakan yasa ta juyo ahankali tana tafiya tana tunani, yar budurwa da saurayinta data gani a wajen takarasa wajensu tana murmushi kafin ma tai magana saurayin yace "cute girl wakike nema anan ki koma ciki karki fada ruwa, small girl doesn't suppose to be here" murmushi tamai tace "please Uncle have you seen my sister Anty Hamida anan?" da sauri dagashi har budurwanshi sukace no, hakan yasa tajuya tana magana ita kadai tace "to a ina kikaje kika boye Anty Hamida?" komawa hall din tayi but still she's not herself karasawa wajen Zainab dake rawa abinta tayi tarike hanun Zainab da sauri Zainab ta kalleta, ganin idanunta sun cika da kwalla yasa ta duko dakai cikin daga murya dan karan waka yay yawa tace "Ihsan leave me alone, if you are hungry dau plate ga wajen abinci chan serve ur self ne babu mai hanaki, kici duk abinda kikeso, am having fun please karki daman da rigiman ki auta pls" sakinta Ihsan tayi cikin fushi tai gaban hall din chan inda Ayush ke zaune da handsome mijinta agefenta sunyi kyau sosai, tana ganin Ihsan suka mata murmushi da sauri ta karasa wajen kaman zata fashe da sauri Ayush tarike mata hannu tace "menene auta?" hawaye ne ya gangaro daga idanunta tace "banga Anty Hamida ba nabi inda tayi banganta ba" dan shiru Ayush tayi tana kallonta hakan yasa mijin Ayush yadan duko dakanshi yace "menene Baby" ahankali tace "wai bataga Hamida ba" shiru yayi saikuma yace "bari nasa a bincikata" ya kalli Ihsan din dake share hawaye yay murmushi yace "cry cry Auta, bari nasa anemo miki ita tunda you are missing her dama gashi kunfi kama" yana maganan ya juyar dakai yama wani abokinshi dake sanye da kayan security alamu da hannu yazo yana zuwa yace "Man please ga Ihsan anemo mata Hamida duk inda, am sure ta buya a jirgin nan ne somewhere just help her find her" ya kalli Ihsan yace "follow him kinuna mai Hamidan inkin ganta" washemai baki tayi tabishi da sauri suka fita daga wurin tanamai surutu tace "Uncle dukna duba saman nan bata, muje kasane" murmushi yamata dan d girl is so cute yace "okay fine girl muje" kasa sukayi dan duba dakunan dake kasan..... 




Wani irin tumble tayi ta shige chan cikin ruwan takai kafin wani wave mai karfi na ruwa yay sweeping dinta with force gaba dawani irin mugun gudu, sanan ruwan yawani irin wuntsulota sama kanta yafito space wani irin nishi tayi tana daga wuya. "iy..yyuuu" tabude baki tana wuntsila kafa da hannu sama tana juye juye tana kokarin bude idanuwanta da ruwa duk suka shiga, da kyar ta bude idanun tana juye juye amma bata hango jirgingu ba tadai ganta a tsakiyan ruwa, gaba ruwa baya ruwa, gefe ruwa ko ina ruwa, gashi sai kasa kasa take kaman ruwan najanta ciki ta nitse, ruwan har habanta, da kyar cikin tsananin tashin hankali gwanin ban tausayi tace "Ma...m" wani irin wave na ruwa yakara zuwa kaman ana aikoshi yahau kanta yay sweeping nata away with force fiye da nada gabaki daya kawai tasadakar ta mutu dan tama kasa bude ido tana kokarin bude baki danta iya numfashi ruwa na shigan bakinta ga ruwan so salty, gawani irin ruwa dake shiga hancinta da kunnuwanta taji kanta yay dumm, yanda take kasa kasa kasa tana bubbuga kafa tana fighting da ruwan dataji gabaki daya yawani irin matseta ya shaketa ya murdeta sosai kaman an kulleta da chain yasa fishes din ruwan duk suka rude suna neman wurin guduwa......




 _Elagushi Beach Lagos_


Zaune yake agaban Beach yana kallon ruwa,  he's d sunset type, there's something about sunset that gives him goosebumps, tun yana yaro when ever he's outside d yamma he always stare at the sun idan yana faduwa, saisa yau ya shigo beach da yamma just to have fun and watch the sun set. 

Sanye yake da summer beach pant dayadan wucemai cinya kadan ya dameshi yabi kakkauran cinyarshi, jikinshi ba riga sai fadaddan huge full kirjinshi irin na maza masu work out, idanunshi sanye da ocean cabaretti sunglasses daya wani irin fitar da dogon hancinshi kaman karas, ga wani round black tabon salla agoshin shi daya karama fuskarshi kyau sosai, gashin kanshi dakeda dan yawa jike yake da ruwa dan ruwan ma diddiga yake yanabin gefen fuskarshi alamun daga cikin ruwan yake hanunshi rike da abinda akafi sani a beach da Aqua de coco (danyen kwakwa da aka fere saman akasa straw aciki) ahankali yake sipping coconut water har lokacin yana kallon beach din cool breeze da feshin ruwa na fesomai.


Ahankali take tafiya sanye da bikini pink tadaura beach hat akan long kitson attachment din dake kanta, tana tafiya ahankali cike da rangwada babu takalmi akafa kafafunta na nitsewa cikin lallausar kasar Beach din, hanunta tana rike da nata Aqua de coco tana sipping kadan kadan ta karaso inda guy din yake zaune, fadawa kanshi tayi ta daura kan akan kafadarshi kaman zatai kuka cikin harshen turenci tace "auch Aabid my feets are aching" shiru yayi kaman baijitaba ya cigaba da sipping  aqua de coco shi yana kallon ruwan, ahankali ta sakeshi ta tankwashe kafa ta cigaba da sipping nata saikuma ta ajiye ta sake kallonshi tana turo baki takai yatsanta dake sanye da dogon kumba irin na arna tace "talk to me love, I have a shoot today but I abondon it just for you Aabid" ganin ko kallonta baiyiba yasa ta ijiye kwakwan nata a gefe ta tashi ta zagayo ta gabanshi ta shiga ruwan bayanta yabi da kallo tsugunnawa tayi ta dibi ruwan ta watsamai tana murmushi tace "you must talk, say something Aabid, say something, you must talk" takara watsamai ruwan a kirji, dan murmushi yayi daya bayyanar da cute one sided dimple dinshi daidai lokacin wani ma'aikacin beach din yazo yadan dukkar dakai alamun respect yace "sir your sport water bike is ready" dawani irin murya chan kasan makoshi kaman anyi forcing dinshi yay magana yace "okay u can go" ya juyar dakai yana kallon bike din dake cikin ruwan da aka daure igiya a jikin wani karfe awater front din gudun karya gudu, ajiye aqua de coco yayi yamike tsaye da sauri tafito daga ruwan tabiyoshi da gudu takama hanunshi tace "am going too Aabid let's water dive together since d bike has two seat" dan juyo dakai yayi ya kalleta da baki yanuna mata yaron beach din akasalance yace "then get a life vest jacket, I don't want you to die before your time" dariya tayi tamai kiss a hanunshi tana wani irin kallon shi cike da so tace "so you care for me" tai maganan tana kallon fuskarshi ganin bai kalleta ba yasa tasaki hanunshi ahankali tajuya da sauri taje wajen yaron beach din karban jacket shikuma yay wurin bike din, there's nothing dat gives him more fun koyana nigeria koyana outside inhar yana beach shine riding bike a ruwa, dan tsaki yayi dan beach din Lagos dinma is not as blue as he wants it to be, is too local for his liking, shiga ruwan yayi harya kaima gwuiwa kana ganinshi kaga wanda ya kware da ruwa sanna yahau kan bike din yajuyo yana kallon Vanessa that's coming towards him tanasa life jacket din data karbo akan dan pininin pant da bra na beach dake jikinta bikini, tana gyara beach hat dake kanta, ruwan itama ta shiga tace "yayy am so excited Aabid this ride is gonna be mad fun right baby" gyada mata kai yayi da sauri ta dane ta rungumeshi ta baya ta daura hanunta akan cikinshi tanaji kaman ta cinyeshi dan so, dan yatsine fuska yayi yadan duko yamika hannu yacire igiyan daga bike din ya kunna bike din dawani irin jarababben gudu yana awizo yaja bike din sukai cikin ruwan wave yawani irin dagasu ihu tayi sosai tana kara kankameshi tace "please Aabid we shouldn't go far okay, am a lil bit scared" cikin husky voice yace "and you shouldn't have followed me, just keep quiet and enjoy d free ride am giving you" kiss tamai abaya cike da murna takara kankameshi tace "I feel honored Mr Cute, sharing a ride with you is a privilege, no is an achievement" kara lankwashe murya tayi breeze din ruwan na neman fadin da hat din kanta tace "am so happy you choose me acikin all d hot hot celebrities damukeda shi a nigeria, thank you handsome" lashe pink lips dinshi yayi yawani irin yin awizo da machine din ruwa ya feso musu a fuska ihu tayi ta kankameshi tace "am having maddd fun, I love you Aabid" tai maganan tana juyawa daidai lokaci ta hango kafar mutum da sauri ta bubbuga bayanshi tana pointing da hannu tace "Aabid look is that a marmaid leg? A think is a marmaid Aabid let's leave here" batare daya kalleta ba yadanyi murmushin iskanci yace "they're no marmaid in Nigeria gurl" ahankali ruwan yadan wurgota sama kadan hakan yasa ta hango fuskan mace, ihu tayi sosai tace "Jesus christ Aabid look is human being, look I think is a girl, Jesus I hope she's not dead ewooo olorun!" da sauri yadan juyo da kanshi yace "stop enchanting rubbish on my ear" ya yatsine fuska, da sauri ta rikemai kafada tace "look Aabid am serious" ahankali cikin tsananin gajiya da ita ya kalli inda take nunamai fuskan mutum ya hango kadan saikuma wave din ruwa yazo yahau kanta hakan yasa ta niste cikin ruwan, ihu Vanessa takara yi tace "how are we going to save her now Aabid, am not with my phone we suppose to alert the beach authority, are you with your phone Aabi...?" bata gama kiran sunanshi ba ya kashe bike din yawani irin mikar da hanunshi up ya hadasu yay wani irin jumping daga bike din yafada cikin ruwan straight takai ya shige chan kasan ruwan shima hangota yayi ta bude hannu sideways jelan gashin kanta  sun mike sun kwanta a ruwan suma tana kasa, kasa, kasa, idanunta a kulle bata numfashi ko kadan, wani irin sauri yayi yana numfashi da baki yana fito da ruwan waje yana swimming kaman fish kafin yakaraso wajen, ahankali ya tsaya ya bude hannayenshi yana wani irin kallon fuskarta tacikin glasses din dake kan idanunshi yanajin wani irin abu da tunda yake in his life betaba jiba, ahankali ya jata da hanun damanshi yahadata da jikinshi ya daura fuskarta akan kirjinshi ya kife fuskar yay sama ya mikar da hanunshi daya sama yana yin kafarshi kaman kifi yay saman ruwan kanshi yafara fitowa kadan saman ruwan, Vanessa dake kan machine gabanta na faduwa sosai sabida tsoro tana hango kanshi nesa da bike dinsu sosai tai ihu tace "thank you Jesus" da sauri ta kwalamai kira. "Aabiddd am right here love" wani irin ciro Hamidan yayi daga cikin ruwan ya daurata akan kafadarshi yana komar da ruwan baya da hannunshi daya yana yin wajen bike din da sauri, tashi yayi daga ruwan yahayo kan bike din da ita Vanessa na kallon fuskarta, zaro ido tayi tace "Jesus she's beautiful Aabid are you sure she's not a marmaid?" kunna bike din yayi yana gyaramata zama a kirjinshi yaja bike din dawani irin fitinannen gudu kirjinshi na bugawa fast fast, ko 1min bai daukesu ba tsabagen shegen gudun dayake yi yakaisu gaban ruwan da sauri ya kashe bike din baima damu da kar ruwa yatafi da bike dinba ya diro daga kai rike da ita da sauri Vanessa ta sauko itama ta biyo bayanshi ahankali ya shimfideta akasa yana kallon fuskarta daidai lokacin Vanessa ta karaso dan dago kai yayi ya kalleta tareda jan glasses din idanunshi  sama cikin husky voice dinshi yace "get d medic" da sauri tace "o..okay handsome" tabar wajen dagudu, ahankali ya juyo da kanshi ya daura cool brown eyes dinshi akanta, ahankali yay placing hanunshi akan cikinta dayay dan kato sabida ruwa yay pressing gently yana kallon fuskarta, sau uku yana pressing cikinta ganin ba response yasa  ya bude bakinta yanadan kallon fuskarta, ahankali yana kallon fuskarta ya daura bakinshi akan nata da sauri ya lumshe ido, ahankali ya hura mata iskan bakinshi cikin nata bakin kafin yadago kanshi ya maida hanun kan cikinta yy pressing but no response, hanunta ya kama yana murza palm dinta sosai sabida yay warming nata yana kallon fuskarta feeling somewhat awkward ahankali yace "hey Jewel, stay with me okay" da sauri ya saki hanun nata yakara dukawa ya daura bakinshi kan nata yasa mata iska sosai this time kafin yakoma adan rude yafara danna cikinta yana kallon fuskarta yace "fight, Jewel don't go just like that precious, stay with me okay".

_🌹IN BANI 🌹_






 _M. Shakur_



6......


 Sake danna cikinta yayi da karfi da duka hannayenshi yana kallon fuskarta cikeda damuwa yace "please Jewel" yay maganan yana sake pressing cikin wani irin nishi tayi tawani bangaro jikinta na rawa sosai ruwa na fitowa ta bakinta da hancinta da sauri ya dagata ya daura kanta kan kafadarshi yana bubbuga bayanta yana kallon yanda ruwa ke fita ta bakinta da hancinta ahankali yace "sorry" sosai take aman ruwa tana wani irin mikewa ahankali yake bubbuga bayanta yadaga kai da sauri yaga Vanessa na karasowa wajen da sauri ita kadai hakan yasa yaja gajeren tsaki ya mayar da kanshi ya kalle fuskarta jintai shiru kuma, ganin ta kara suma yasa da sauri ya dagata kaman wata yar baby yafara tafiya da sauri, adan rude Vanessa tabishi da sauri itama tace "Aabid where are you taking her?" batare daya kalleta still idanunshi akanta yana kallon fuskarta yace "hospital" da sauri tana kokarin cimmishi kafafunta na shigewa kasan Beach din tace "but d medic are coming, they're looking for first aid box" batare daya kalleta ba yana kara saurin tafiyanshi yace "I can't wait for them" daidai lokacin yafito parking lot, bude babban jeep dinshi yayi Brabus da hannu daya ahankali ya kwantar da ita a back sit yaja jacket dinshi black na Gucci ya rufamata in order to keep her warm, sanan yaja dayan plain white shirt dinshi dake jikin hanger anan bayan motan ya saka baimabi takan rufe boturan riganba ya rufe kofan yabude gaba ya shiga ya zauna a mazaunin driver, da sauri Vanessa data karasa saka dan half kimono ta tana daure igiyan gaban ta zagayo ta shiga dayan bangaren tana rufo kofar tana gyara zama tana kallonshi dan cije lips dinshi yayi ya waigo yasake kallonta sanan ya maida kanshi kan wajen key yatada motar, da gudu yabar wajen, da sauri tace "handsome where are we taking her to? Where are we going with her? We don't know her, don't you see she don't look like a human, she looks like a marmaid u know that's how they use to be very fine and beautiful" wani matsiyacin kallo ya watsa mata kafin yamika hannu ya kunna waka a motan na drake yanabi yana wani irin dan iskan gudu harsuka kai wani private hospital mai suna safeguard hospital, parking yayi yafito yabude baya da sauri ya yaye jacket din daya rufamata ya dauketa ya shiga ciki da ita da sauri aka karbeta daga hanunshi a reception din aka kwantar da ita akan gado, bin fuskarta yay da kallo ya tsaya awurin yana kulle boturan riganshi, daidai lokacin Vanessa ta karaso tazo inda yake ta tsaya kaman zata shige jikinshi hanunshi ta rike tashafa soft kumatun shi ahankali tana kallon fuskarshi tace "let's go home baby since we've brought her to the hospital" kallonta yayi kafin ya janye hanunta daga fuskarshi yabi bayan Dr din dayaga suna shigar da ita wani daki, binsu yay cikin dakin yana kallon oxygen din dayaga ana kokarin yimata fixing a hanci da sauri Dr yajuyo ya kalleshi yay dan murmushi yace "don't worry young man, she will be fine, she need oxygen ne sabida state of her lungs right now but for now excuse us let do our work please Sir" fuskarta yakara kallo kafin ahankali ya juyo yafito daga dakin, wata nurse ne tabiyoshi da folder da kuma takardan bill, bill din tafara mikamai ya karba sanan tace "Sir wats her name? And how old is she?" kallon nurse din yayi da shanyayyun idanunshi masu kama dana mijin bacci ahankali yace "name Jewel, age 19 or 20" da sauri tace "okay okay, is all we need for now, then the bill sir, we need to get the things now" tashi yayi yace "1min" fita yayi danba kudi ajikinshi mota yaje ya bude yadau wallet dinshi ya bude most of kudin dake cikima are US dollars Nigeria naira daya gareshi which is a 1000 note, tsaki yayi dan bai chanza kudin ba tunda ya shigo ba, hakan yasa yaciro ATM card dinshi na first bank ya rufe motan ya shiga cikin hospital din da POS yabiya kudin sanan ya kalli nurse din daketa kallonshi yace "take care of her please, zanje gida I wanna shower and change, will be right back" murmushi tamai tana washemai baki dan guy din can speak, his accent kaman nadan amurka tace "okay Sir I will do dat for you" dauke kai yayi yana kallon Vanessa yace "gud" dagama Vanessa data cika tai fam da gira yayi yace "are we safe gurl?" yay maganan yana hanyar fita daga reception din yana taku daidai, binshi tayi da kallo in life halin Aabid na kasheta, tana bala'in son this his C² character, the guy's coded and classic hali na bala'in burgeta, baka taba gane halinshi komin dadewan dakayi dashi, dan juyowa yayi ya kalleta hakan yasa ta tashi da sauri ta biyoshi tana murmushi tana turomai baki.


Koda tafita wajen harya shiga mota yatada ahankali tabude dayan side din itama ta shiga itama ta zauna yadan juyo ya kalleta murmushi yay kadan yana kallon fuskarta yace "cool down" da sauri ta kama dayan hanunshi tamai kiss tana murmushi tace "I love you Aabid please stop ignoring me okay" dan murmushi yamata yana kallon kwayar idanunta kafin yamata alamu da ido data sakeshi, murmushi tasake yi tasakemai kiss a hanun sanan ta sakeshi ahankali tana murmushi, kunna motar yayi yanadan fuzar da iska yaja motar sukabar asibitin, Victoria garden city VGC yawuce, gaban wani babban hadadden gida yay horn gateman yabudemai ya shiga yay parking motar, hadadden compound ne mai fadi sosai flowers ko ina, fitowa yayi yay ciki batare daya jirataba ya bude kofa ya shiga, falone babba da akai komi off white, dakin yahadu sosai da sauri yakarasa wajen fridge ya bude yadau bottle water na Eva, budewa yayi yasha yana kallonta daidai lokacin ta shigo sai kumbure kumbure take, shareta yayi ya ijiye goran ruwan kan saman fridge yahau stairs yy sama yabude wani daki ya shiga, shima dakin komi off white da akamai sirki da sky blue, dakin yay kyau fiye da misali kaman aturai, jefa wayarshi kirar iPhone 11 yay kan makeken gadon dayaci farin duvet, ahankali yakai hanunshi yanadan lumshe ido alamun gajiya kan boturin rigan shi yay unbutton shirt nashi ya cire yayar nan kasa, yaja summer beach pant din shima kasa sanan ya tsallake kayan ya wuce yana tafiya ahankali yabude bathroom ya shiga.

_🌹IN BANI🌹_ 




 _M. Shakur_


 7....


Ruwa yahada mai dan zafi a bathtub da kyar sabida gajiya ya zuba shower gel nanda nan bayin ya cika dawani irin mugun kamshi ya shiga ciki ruwan ya lumshe ido yanadan tunani, yakai kusan 5min ahaka Vanessa tai knocking kofar rike da wayarshi dake ta haske murya chan kasa tace "handsome your phone is ringing" dan yatsine fuska yayi cikin kasalalliyar murya yace "who is calling?" kallon screen din tayi ganin Dil❤ da emoji heart yasa tace "is Dil" wani irin murmushi yayi daya bayyana set din white hakoran shi yace "rascal keep d phone, I will call him back" murmushi tayi tace "okay love" maida wayar tayi ta ijiye kan bed din, fita tayi daga dakin ta shiga d next room inda yar akwatin LV dinta yake, wanka tayi itama tasa wani hadadden red lingerie tafesa turare tafito daga dakin sanye da white bathroom slippers tabude kofan dakinshi ta shigo tana kallonshi yana tsaye gaban mirror sanye da bathrobe yana kokarin shafa cream, kallo daya yamata ta mirror ya dauke kai, ahankali ta maida kofan tarufe tana wani irin cat working takaraso gaban mirror ta baya ta rungumeshi dudda yafita tsawo sosai abayanshi ta daura kanta tana shafa kirjinshi da hands dinta asaman kirjinshi dakeda gashi ta saukar da hannun dawani irin bedroom voice tace "Handsome lemme help u with the cream, why am I here if am gonna let you do things yourself" tai maganan tanajan hannayen daga chest dinshi zuwa kan navel dinshi, wani irin ajiyan zuciya ya sauke yana kallon kanshi ta mirror, dan murmushi tayi tawani irin zagayo ta gabanshi tahau gaban mirror ta zagaye kafafunta ta bayanshi tana murmushi tana kallon fuskarshi, shima kallonta yake da idanunshi dasuka chanza kala, ahankali takai hanunta kan pink lips dinshi tana shafawa gently tana wani irin kallonshi tace "you are so cute Aabid, I love your skin, your skin is so soft, I love your ebony skin is so sexy" ahankali ta janye hanun nata daga kan lips dinshi ta janyo cream din ta debo a hanunta tana mutsitsikawa tana kallon fuskarshi, gently ta daura hannayen nata akan kirjinshi tafara shafamai mai tana sauka kasa kasa har ta sauka kan V-lines dinshi dan lumshe ido yayi yana cije lips, yanda taga yayi yabata more access na fadin abinda takeso tace, fuskarta takai saitin kumatunshi tana shafawa, cikin low voice tace "Handsome I wanna feel you, am tired of  romance, romance romance, let's have s*x, make me pregnant plss, I wanna be pregnant for a handsome young milloniare like you Aabid, make me your baby mama plss" tai maganan while grabbing his thing gently, da sauri yabude ido yatureta tai baya, dawani irin sauri ya shiga bayi, yakai kusan 10min kafin yafito yana goge jiki ko kallon inda take baiyiba ya shirya cikin wasu hadadun Jean da riga black and white ya feshe jikinshi da hadadun turare, bakaramin kyau yayiba yadau key mota daga gaban mirror yawuce yafita ya sauka kasa, wajen mota ya karasa ya bude motan ya shiga yaja motar yafita, masallaci yafara shiga yay salla sanan ya fito ya shiga KFC take away yay sanan yafito ya shiga mota yaja motar zuwa asibitin, parking yayi a haraban asibitin yafito yana kallon ko'ina yadau take away yarufe motar ya juya ya shiga cikin asibitin yana taku dai dai yakarasa ciki, da sauri nurse din dazu dake zaune kan kujera ta taso  tana washemai baki tace "welcome Sir lemme take you to her room, amma gaskiya Sir your patient tasha ruwa sosai, kaga ruwan da aka cire daga jikinta kuwa" tsayawa yayi chak ya kalleta, murmushi tasake mai tace "don't worry she's fine, we manage to save her, mun fitar da duka ruwan datasha, yanzu  bacci takeyi bama ta tashiba har yanzu but am sure any moment from now zata tashi" cigaba da tafiya sukayi tabude mai kofan dakin da aka kwantar da ita ta shiga ciki bayanta yabi yana kallon gadon tana kwance kan gado ansa mata kayan asibiti an kunna warmer adakin, dakin yay dumi sosai, maida kofar yayi yarufe har lokacin idanunshi akanta ya tsaya awurin tare da folding hanunshi a kirji yana kallonta, dauko wani magani nurse din tayi tazo inda yake tsaye tace "Sir maganin nan once ta tashi kabata 5ml" gyada mata kai yayi takoma ta ijiye maganin tadawo tace "if you need anything from me Sir just ring that alarm" ta nunamai wani jan button, gyadamata kai yayi batare dayay magana ba ya matsa gefe tabude kofa tafice, ahankali ya tsaya a wurin yana kallon fuskarta, tai wani irin haske looking innocent, gashin gaban goshinta ya kwanta sosai tana fitar da numfashi ahankali ahankali an mata fixing drip a left hand dinta, ahankali yadaga kafa kaman bayaso ya taka kasa yana kallon fuskarta kaman wani magnet na pulling dinshi towards her harya karasa jikin gadon ya tsaya akanta yana kallon fuskarta, sai lokacin ya lura da bandejin da akasa a saman goshinta alamun tanada injury a wurin, kujeran gaban gadon yaja ya zauna yana kallonta still ko kyafta ido bayayi shi kanshi baisan mesa yake kallonta hakaba, kawai yasami kanshi da kallonta ne nonstop, saukar da idanunshi yayi kan hanunta da aka makala mata ruwa ahankali ya mika hanunshi ya dauki hanun nata yarike yana yana kallon hanun yanda gashi suka kwanta lub lub ajikinta kafin ya saukar da idanunshi kan fuskarta yanda take baccinta innocently kaman ka kirata tai magana, cikin wani irin cool free voice yace "Jewel" shiru yayi yana kallon fuskarta kafin ya lumshe ido yana kara holding hand nata tight, yadan fuzar da iska yana ganin d first time he saw her face daya shiga cikin ruwan, how he felt dakuma yanda yaga fuskarta tamai wani irin haske sosai acikin ruwan, motsin dayaji a hanunta dake cikin hanunshi yasa yabude idanunshi dahar sun soma chanxa kala sun kankance ya daurasu akanta, motsi yaga tanayi sosai tana yatsine fuska kadan kadan idanunta alumshe tana motsi da hannayenta da kafafunta, da sauri yatashi daga kan kujeran dayake yakai fuskarshi gab da fuskarta yana wani irin kallonta, cikin wani irin murya mai cike da natsuwa da dadin ji yakirata. "Jewel" dan shiru yayi yana kallon yanda idanunta ke rawa tana kokarin budesu, ahankali ya hura mata iska asaman idon kafin ahankali kaman mai whispering yay magana asaitin kunenta yace "open your eyes Jewel" bude idanunta tayi gabaki daya a lokaci daya dasuka mata wani iri sabida ruwan dasuka shiga cikinsu ta daurasu akanshi, dishi dishi take gani danjin idanun tayi kaman an zuba mata oil acikinsu, ahankali murya chan kasa yace "Jewel can you see me" hanunta ta daga dakeda lafiya ahankali ta daura kan idanunta ta shiga sosawa non stop dan murmushi yayi yakai hanunshi yakama hanunta datake sosa idanun nata dashi ya janye hanun daga idanun nata yana kallon kwayar idanunta, ware idanunta tayi da kyau tana kallon mutumin datagani akanta cike da mamaki yana mata wani irin cool smile yana bata wani irin warm look, da sauri ta runtse idanunta cike da tsoro kirjinta na bugawa sosai dan d last abu data tuna was lokacin data bude ido ta ganta acikin ruwa, where is she yanzu and who's this man dayake mata murmus.... Bata karasa maganan zucin ba taji sauka iska akan idanunta ba shiri tabude idanun a mugun rude tana kallonshi, shima kallonta yake ahankali yadan matsa hanunta dayake rike dashi har lokacin yana kallon kwayar idanunta yace "how are you feeling now Jewel?" zaro ido tayi arude tana wani irin kallon shi kafin tafashe dawani irin kuka ta fizge hanunta daga nashi da sauri arude ta yunkuro zata tashi kanta da nashi suka gware, wani irin ihu tasaki da saida ya mike tsaye da sauri yana shafa gaban goshinshi yana kallonta yanda take kuka tarike gaban goshinta tana shafa inda ta bugen yasa da sauri ta dira daga gadon batare data lura da drip din hanunta ba dudda batajin karfi sosai saida tai gaba zata gudu tai wurin kofa, wani irin jiri ne ya debeta tai baya zata fadi da sauri yatareta hakan yasa tafado jikinshi, wani irin ajiyan zuciya yayi yana kallon fuskarta yariketa gam gam, zaro ido tayi hawaye na zuba daga idanunta tana kallonshi bakinta na rawa sosai shima kallonta yake calmly da lumtsatsun idanunshi, saukar da idanunta tayi tana kokarin fizge jikinta daga nashi amma takasa sabida yanda yariketa, sake dago ido tayi dasuka cika da hawaye sosai ta kalleshi koina na jikinta rawa tama kasa magana, ahankali yadan sauke ajiyan zuciya kafin ya dagata ya zaunar da ita akan gadon da sauri ta dau filo tana kare fuskarta dashi jikinta na rawa sosai, dan matsowa yayi kusa da gadon ganin yanda ta rude saukar da muryanshi yayi sosai yace "Hey Jewel calm down, am not gonna hurt you, you are safe okay" kare fuskarta tai da filon sosai hannayenta na rawa daidai lokacin nurse  tabude kofan ta shigo sabida ihun dataji, arude Hamida tasaki wani irin kuka tana kara rufe fuskarta da filon tana neman inda zata shige bakinta har rawa yake ta damke filon sosai tace "Ma...ma, Mama, wayyo Allah na Mama!" ta kwalama Maman su kira, ahankali nurse din takaraso gaban gadon ta kalli Aabid dayay folding hannu yana kallonta tace "Sir your patient ta tashi, hello Jewel stop crying, am your nurse, nurse Kuburat, how are you feeling now, meke miki ciwo?" tai maganan tana fizge filon hanunta cikin dabara, fashewa tayi da kuka sosai tana komawa karshen gadon tasa hannu ta daura akan fuskarta tana kuka sosai tana kakkare fuskarta arude tace "pls Mama, ina Mama na?" cikin rarrashi nurse din tace "don't worry Mama zatazo yanzun nan, but for now ga maganin ki kisha, inhar kinsha kinji sauki gobe da safe zamu sallameki, saikije kiga Mama, you drown a ruwa and Sir brought you here" tai maganan tana nuna mata Aabid, ahankali tana hawaye sosai tadan juyoda kai ta kalleshi hada ido sukayi da sauri ta sake dukar dakai tana kakkare fuskarta da hannu daya tana share hawayen datakeyi da bayan dayan hanun, maganin nurse din tazuba a marfi 5ml takai saitin bakinta tana murmushi tace "yauwa to open your mouth kisha ba daci" ahankali tadan juyo dakanta jikinta na rawa har lokacin tadan bude bakinta da sauri nurse din ta zuba mata maganin, hadiye maganin tayi hawaye na gangarowa, murmushi nurse din tace "good" ta kalleshi tace "Sir taci abinci please, I will come back anjima nai checking vitals dinta" tajuya tafita daga dakin, saukar da kanta tayi kasa tana kuka sosai tana gogewa da bayan hannu, kara jan kujeran yayi ya zauna tareda daukan takeaway dayayo mata yabude fried rice din yasa spoon aciki ya mika mata yana kallon fuskarta, kawad dakai tayi chan gefe tana kare fuskarta da kyau, dan murmushi yayi yace "take d food and eat kona duramiki, kinsan menene force feed?" yay maganan yana dage mata gira daya, adan rude tafashe dawani kukan tadan juyo ta kalleshi, hada ido suka sakeyi da sauri takara juyar dakan tana goge fuskarta da hannu, dan matsar da kujeran baya yayi zai tashi hakan yasa tadanyi ihu ta yar da filon ta mikamai hannunta dake bari da sauri, bata abincin yayi yana murmushi takarba da sauri tana goge fuskarta da bayan hannu, murmushi yasakeyi dan hakanan yaji yarinyar na burgeshi, abincin ya kalla ya kalli yanda takeyi da hannu taki diba taci, murya chan kasa yace "nabaki dakaina?" da sauri ta girgiza mai kai batare da ta kalleshi ba tadebo kadan takai bakinta taci, hanunta dake rawa sosai yabi da kallo yace "what's your name Jewel?" dan dago kai tayi ta kalleshi da sauri ta janye idonta dan kasa jure kallonshi tayi saima kirjinta data fara bugawa danji tayi zata kware abincin ya tsaya mata a kirji da sauri yadau bottle water ya bude marfin yamika mata, karba tayi da sauri tasha kadan hakan yasa ya mika hannu ya karba yana kallon fuskarta tareda karban takeaway from her ahankali yace "ya sunanki" yay maganan yana debo fried rice din a spoon yakai bakinta.

_🌹IN BANI🌹_ 




 _M. Shakur_


8....


Kara zaro idanunta tayi duka tana kallonshi tana wani irin kallon abincin daya kawo bakinta yanajira tabude yasamata aciki, dan lumshe ido yayi yabudesu ahankali ya sake daurasu akan white oily eyes dinta, cikin wani irin dense voice yace "open your mouth Jewel" ja baya tafarayi akan gadon arude yana binta rike da spoon din harsaida takai bangon gadon tafashe da kuka tana kare fuskarta da hannu, ahankali ya zauna kusa da ita ya mika hanunshi yakama hanun datake kare fuskan dashi yakai spoon din mouth dinta yana wani irin kallonta batare dayay magana ba, da sauri ta bude bakin yasaka mata rice din ta karba zata fizge hanunta yakara rikewa gam gam, ahaka yacigaba da bata abincin hartaci kusan 5 spoons sanan ta kauda kai tace "na..na koshi" rufe abincin yayi ya ijiye a inda yake yadau bottle water yabata, ahankali ta karba tasha kadan tabashi ya karba ya ijiye yana kallon yanda gefen bakinta ya baci da oil din food din, hanunshi ya zira a aljihu yaciro clean white handkerchief dinshi mai taushi da kamshi yakai saitin bakinta yana wani irin kallonta, arude ta yunkura zata koma baya da sauri yasa hanunshi yakama waist dinta yana wani irin kallonta, kwalalo ido tayi tana wani irin kallonshi adaburce kaman wacce ke shirin suma, ahankali batare daya yanke eye contact dinsu ba ya daura handkerchief din gefen bakinta yana share mata ahankali harya gama yana kallon kwayar idanunta, zare handkerchief din yayi batare daya saketa ba yana rike da ita har lokacin yace "what's your name Jewel?" kulle idanuwanta tayi da sauri dan bazata iya jure kallon dayake mataba, ita tunda take bata taba ganin namiji mai eyes irin nashiba, yatsarshi yadaura kan nose dinta yana kallon long eyelash dinta yace "what's your name Jewel?" wani irin nishi tayi dan sosai yatsarshi ke mata wani irin sanyi a hanci hakan yasa tasaki wani irin ajiyan zuciya tace "Amatullah" murmushi yayi sosai dayawani irin karamai kyau maidan sauti hakan yasa ta bude idanunta, kallonta yasakeyi yace "your name is very cute just like you Ama" sake ware idanunta tayi ta kalleshi adan tsorace, gyadamata kai yayi yace "yes, you're beautiful Jewel" saukar da idanunta tayi kasa da sauri hakan yasa ya sanya hannu yakama habarta ya daga fuskarta ta fuskance shi, sosai zuciyarta ke neman dena aiki sabida yanda yake kallonta, da sauri ta sanya hanunta tana tura nashi daya rike mata habanta dashi muryanta na rawa sosai tace "s...stop touching me" da sauri yace "why?" tabe baki yayi yace "ba kyau ko? In UK is a normal thing" shiru yayi yana kallon yanda har lokacin hawaye ke fita daga idanunta and he could feel yanda jikinta ko'ina yake rawa sabida riketan dayayi ahankali yace "kinaso na sakeki?" da sauri ta dagamai kai batare data kalleshi ba, dan murmushi yayi yace "okay to stop crying and listen to me, I wanna talk to you, inba hakaba I will hold and touch you again" da sauri ta sanya hannu ta share hawayen nata tass tadan kalleshi irin kallon nan na antursasani ne, ahankali yajanye hanunshi daga waist dinta ya saki habarta yadan koma baya da ita kadan dan yasan inhar yana kusa da ita he will touch her again and yanaso he wants her to be comfortable, gyara zama yayi  ya kalleta murya chan kasa yace "Amatullah" da sauri ta dago kai ta kalleshi dan sosai yanda ta kira sunan ya daki ranta danko kadan a gida ba'a saba kiranta da Amatullah a gidaba dan sunan Kaka ne, babu wanda ya isa yakirata da sunan. "where are you coming from, tayaya kikai drowning? Kinje Beach ne?" shiru tayi tana kallonshi kafin cikin siriruwar muryanta tace "bikin Anty Ayush" da sauri yace "who's Anty Ayush?" ahankali batare data kalleshi tace "My sister" "aruwa kuke bikin?" gyadamai kai tayi tace "yes d husband is navy a jirgin ruwa suke party" da sauri yace "to tayaya kika fada ruwa basu ciroki ba?" cikin wani irin muryan kuka tace "jiri" da sauri yace "jiri kika dinga gani?" gyadamai kai tayi batare datai magana ba, shima shiru yayi yana kallonta, dan dago kai tayi ta kalleshi suka hada ido da sauri ta saukar da kanta tana share hawayen daya zubomata tace "I thought na mutu ma" murmushi yayi yace "no, I was the hero, I saved u Jewel, am your superman Jewel" batare data kalleshi ba tace "my name is not Jewel stop calling me  that" murmushi yayi maidan sauri yakamo hanunta yace "you're my Jewel, I found you a water, and bazan barki ba Jewel, I just li..." hawayen dayaga tana sharewa yasa yadanyi shiru yana kallonta, dago kai tayi ta kalleshi adan tsorace ahankali tace "zan kira Mama na" dan yatsine fuska yayi kaman wani karamin yaro yace "I don't want them to come and carry you now Jewel" duka hannayenta tadaura kan fuskarta tana share hawayen dake zubo mata sosai wanan wani irin mutum ne haka, wani asibiti ne wanan, tasan su Anty Lami da Ayush kowama ana chan ana neman ta, tasan hala yanzu ma har an kira su Baba da Mama harma Kaka duk an sanar dasu ta bace, hanunta taji yakamo ya matsa. "Jewel stop crying pls, zakiyi magana da Mum dinki?" gyadamai kai tayi hakan yasa yaciro wayarshi daga aljihu ya mika mata dan dago kai tayi suka sake hada ido, karban wayan tayi tasaka number Mama tai dailing, harya katse mama bata dauka ba, ana biyu ne ta dauka muryanta yadan shake alamun taci kuka tace "Assalamu Alaykum, waye?" jin muryan Mama yasa taji hawaye yazubo mata da sauri tace "Mamaa" tashi Mama tayi daga kan gado datake kusa da Abba dake lallashinta, dafe kirjinta tace "Hamida, Hamida kene?" gyadamata kai tayi ahankali tace "uhm nine Mama" kaman Mama zatai kuka tace "Hamida ina kike? Ina kikaje su Ayush hankalin su dukya tashi anata neman ki, Hamida I promise bazan kara turaki kije wani waje idan bazakije ba kinji, fadamin inda kikaje, inkika boye? Anbicika jirgin kakap ba'a gankiba, ina kika boye Hamidana nakira su Ayush nafada musu suzo su daukeki ki koma gida gobe sudawo min dake nan kano tunda bakison chan, kina ina Baby na? and wanan wani number ne kika kirani dashi naga banaki bane, da number wa kika kirani, ina kika boye eh Hamida na fadamin?" Mama tai maganan muryanta narawa sosai hankalin ta atashe, dama ance yaro mai matsala yafi shiga rai, bala'in son Hamida take bana wasaba, ko Ihsan auta tabiyo bayan son datake ma Hamida, ahankali Hamida tace "ruwa nafada Mama" "innalillahi wa innailaihi raji'un ruwa Hamida? Wanan babban rafi da manya manyan jirgin chaina kebi kika fada? Ru kika fada Hamida? Are you fine? Kina ina yanzu?" ganin yanda tabi ta rude ko'ina najikinta na rawa yasa Abba karban wayan daga hanunta yakara a kunne yace "Mamana kinajina" gyadamai kai tayi tana kuka murya chan kasa tace "eh" anatse yace "yanzu kina ina?" ahankali tajuya ta kakkali dakin cikin kuka tana lankwashe kai kaman tana gabansu tace "asibiti" da sauri yace "subhannallah asibiti? Garin yaya? Waya kawoki asibiti?" fashewa tai da kuka tace "nima ban sanshiba Abba" da sauri Abba yace "da wayanshi kika kiramu to" gyadamai kai tasake yi cikin kuka tace "eh shiya bani wayan" da sauri Abba yace "bashi wayan nai magana dashi" ahankali ta dago idanunta dake cike da hawaye ta kalleshi hada ido sukayi ya rungume hanunshi yamata kuri da ido yana kallonta kaman zai cinyeta, mikamai wayan tayi tace "Abba na zaima magana" kallonta yayi kafin ya kalli wayan yasake kallonta, sanan ya karbi wayan yakara a kunne a natse yay sallama kaman bashiba sanan yajuya yafita daga dakin tabi bayanshi da kallo, yakai kusan 10min awaje sanan yadawo dakin, gyangyadi yaga tanayi a zaune, kujera yaja ya zauna hakan yasa tabude ido da sauri ta kalleshi da idanunta dasuka dan kankance sabida bacci tace "za'azo a daukeni?" gyadamata kai yayi yace "amma saida safe za'azo nafada musu sunan asibitin" wani irin bakin ciki taji ya tsaya mata a wuya dan bataso kara koda minti daya da wanan mai shegen kallon ba, ahankali ta kwanta kaman marainiya ta juyar da kanta dayan side din tana danne kukan daya wani irin taushe mata makoshi.

_🌹 IN BANI 🌹_ 





 _M. Shakur_


9....


Magana zai mata wayarshi ya shiga ringing da sauri ya kalli wayar ganin number dazune Dil❤ yasa yay wani irin cute smile yay picking call din cikeda murmushi yace "I know you're missing me Dil just admit" daga tachan bangaren cikin wani irin cool voice dayamafi na Aabid din dadi gata yar karama yace "when are you coming back Bid?" dariya Aabid yadanyi yace "me nawani cin magani? Saikace kayi missing dina sanan zan fadama ranan dazan dawo Dil" shiru wanda aka kira da Dil yayi baice komiba hakan yasa da sauri Aabid yace "kaifa kacika zuciya matsalana dakai kenan Dil" cikin fushi sosai ya daga murya cikeda fada yace "I said when are you coming back?" dariya sosai Aabid yasakeyi yace "say u miss me first" katse wayar yayi dip hakan yasa Aabid ya kalli fuskar wayan da sauri ganin ya katse yasa ya ware manyan idanunshi, dailing number yayi back da sauri wayar yay ringing harya gama ba'a daukaba hakan yasa yasake dailing number akaro nabiyu.


Da sauri fine dattijuwan matar data shiga babban hadadden kitchen dinsu hadamai hotchocholate tafito daga kitchen din, hadadden dining din takaraso tadau wayar tai picking, murmushi tayi cikin muryanta mai dadi  tace "hello Son" wani irin murmushi Aabid yayi yace "Mami na, I miss you so much, ina Dil Mami?" dan murmushi matar tayi mai sauti tana kallon tilin brunch dake kan dining tace "mekama dan uwanka Son? Yay fushi yabar phone din da abincin duka a dining, dama kasan da kyar na lallabashi yazo yaci dan rabonshi da abinci tun jiya" dan murmushi yayi yana karajin son dan uwan nashi aranshi yace "Mami I told him yazo muje tare yaki zuwa wai bazai iya zaman flight ba he's scared, and Nigeria weather is harsh sabida nataba cemai garin dazafi, sai yanzu dana zo shine zai wani dameni nadawo yanamin fushi to baza'a dawon ba" yay maganan yana daure fuska shima alamun ranshi yabaci, hadadden kujeran dining matar taja tazauna tana saukar da ajiyan zuciya kafin ahankali takira sunanshi. "Aabid" da wuya Mami ke kiran sunan su hakan yasa yasake natsuwa yace "na'am Mami na" dan ajiyan zuciya ta saukar tace "you know your brother's condition, you know how your twin brother is so attach to you, kasan baida lafiya sosai, please kadawo kaji and be with him am sure yanzu yanadaki he's crying" sosai maganan Mami yatabamai zuciya hakan yasa yaji hawaye sun taru a idanunshi da sauri ya hadiye su murya chan kasa yana kallon Hamida data dade dayin bacci yace "please Mami kaimai wayan lemme speak to him" tashi Mami tayi daga dining tai sama, wani babban hadadden daki ta shiga da akai komi blue, gadaje biyune adakin hadaddun gaske komi iri daya, hangoshi tayi akan gadon yana kwance yaja bargo yarufe jikinshi yajuyama kofa baya, shiga ciki tayi ta maida kofar ta rufe takarasa jikin gadon, ahankali ta zauna abakin gadon ta daura hannu akanshi tana shafawa cike da lallashi ta mikamai wayan tace "gashi Aadil dina, Aabid zaima magana" ture hanunta yayi cikin fushi yana juyo da kanshi dan bayason ya karbi wayan. Hadadden saurayi ne kyaykyawan gaske ebony, kamanninshi daya da Aabid banbancin shine kana ganin wanan kasan baida cikakaken lafiya, dan sosai bakinshi ke dilalar da miyau kanshi na wani irin rawa kaman kan karamin jariri, yana sanye da plain white t-shirt na givency, yasanya 3quater black iya guwiwa, bakaramin kyau yakeda shiba saidai shi yafi Aabid jan lebe, dakuma sleepy eyes. 

Cikin wata irin raunanniyar murya Aabid yace "yaki karban wayan ko Mami?" ahankali tace "eh yaki Son" dan murmushi yayi yana share hawayen daya zubomai da sauri yace "sani a speaker Mami and keep the phone close to him" saka wayan Mami tayi a speaker ta ajiye wurin kanshi ta tashi tafita daga dakin ta rufo mai kofa, karan rufe kofan Mami dayaji yasa yace "I know you can hear me u dis rascal, rascal boy meyimin wayau in muna buga kwallo kawai, little rascal me boyemin car keys idan zan fita, u better talk ko I will come out through that phone and pinch your cheeks so hard kasan u hate that ko? Now say something to your twin brother please my Aadil, kaji D...il" yay maganan bakinshi narawa sosai hakan yasa yatashi da sauri yafita daga dakin yarufo mata kofa, waje yafita ya shiga cikin mota ya rufo yana gyara zama yace "kamin magana please" ahankali yamika hannu yaja wayan kanshi narawa sosai ya kara wayan a kunenshi yatashi ya zauna bakinshi na zubar da miyau kaman karamin yaro yafashe da kuka sosai yana shesheka yana murza ido, arude muryan Aabid narawa sosai yakira shi da karfi arude "Aadil! Aadil! please stop crying, tell me yaushe kakeson nadawo koma yaushe ne i will come back I promise you, stop crying dan Allah kaji" sosai yake kukan miyau na zuba daga bakinshi yana wani irin nishi kaman wanda aka zane yace "now, kadawo yanzu, I want to see you now" runtse ido Aabid yay ahankali ya sassauta muryanshi yace "Aadil" cikin kuka sosai yana turo mai baki yace "uhm" murya chan kasa yace "kasan I don't lie ko, banama karya, am sorry Dil but I can't come back right now, Please stop crying I promise you I will come back soon okay" turomai baki yayi yana share hawayen kaman small yaro yace "w...wat..wat is keeping you there then?" dan lumshe ido yayi yabude ahankali dan muryanshi ayanda yakejinshi yanzu is really breaking his heart, yasan he's brother is missing him, murya chan kasa yace "she" da sauri cikin kuka yace "she??" gyadamai kai yayi yace "yes twin I saw my Jewel yau, and is love at first sight" da sauri yace "love? Bid we found our Jewel, I love her too, love at first sight ko" gyadamai kai yayi yana share hawayen dayake yi yace "yes, love at first sight my Dil" da sauri yana share kukan dayake yi yace "to when are we going to get married to her?" murmushi yayi sosai jin yasoma dawowa daidai yace "I don't know Dil, she don't like me" da sauri yace "give her roses, plenty plenty rose like kaman a movie" murmushi yayi yace "okay Dil, yanzu kaci abincin da Mami tabaka, go and eat your food and take your drugs okay, anjima your Dr will come" gyadamai kai yayi kaman karamin yaro yace "okay, tell her I love her" dariya yayi sosai yace "rascal okay" dariya shima yayi yatashi yana tsalle akan gado yace "I will tell Mami na kacemin rascal again batahanaka ba yaro kawai" da sauri yana murmushi yace "wayace ma ni yarone zan haihu innai aure dankaji" da sauri shima yana share miyan daya zubanmai awuya yace "me to, nima zan haihu dan kaji, plenty plenty babies" dariya yayi sosai yace "okay naji go and eat your food to" turomai baki yayi yace "the food is peprish Bid" shima turo baki yayi kaman yanda yayi yace "eat small okay and be taking water d pepper will go" dariya yayi yace "Bid I've gotten two friends on my messenger, Anty Hamida and Ihsan, can I be their friend Bid?" yay maganan yana lankwasa kai yana turamai baki, dan dariya Aabid yayi yace "yes chat with them but don't tell them who you are okay" da sauri yace "okay I will not, and...and..and" da sauri Aabid yace "and wat" da sauri yace "my Skype is not working kuma" dan shiru yayi kaman mai tunani yace "I will check it for you inna dawo" da sauri yace "okay, tell her I love her, bye am hungry" da sauri yace "okay I will, oya run, run jekaci abincin ka, finish everything okay" da sauri ya gyadamai kai yana katse wayan, yay tsalle ya dira daga gadon yafita daga dakin yana tsalle sosai yana sauka daga stairs din, da sauri Mami ta tashi daga kan kujera tace "stop jumping Son karka fadi" washe mata baki yayi yataho dawani irin shegen gudu yafada jikinta yace "oyoyo Mami na" yamata kiss a kumatu kafin yatashi da gudu daga jikinta yay dining yaje ya zauna ya bude abincin ya cillar da marfin kasa yadau spoon yafara ci rabi na zuba cikin plate din da dining rabi na shiga bakinshi, sosai Mum ta kafeshi da ido taji hawaye zai zubo mata da sauri ta hadiye kukan ta taso ahankali tazo inda yake taja dayan kujeran kusa dashi ta zauna ta karbi spoon din daga bakinshi, dago idanunshi yayi saikuma ya turo mata baki yace "feed me Mami" debo rice din tayi yabude mata clean mouth dinshi tazuba mai tana murmushi tace "very Good Son" hadiye abincin yayi da sauri yana mata fari da ido kaman wata mace yace "kuma I will not tell you something da Bid yafadamin taaaa" yamata gwalo, murmushi tayi takara kaimai abincin baki tace "fadamin mana Son, haba my one and only Aadil" washe mata baki yayi shinkafan bakin na zubowa waje tana sharemai yace "no I will tell you when Bid is back, but Mami" yakira sunanta yana zare manyan fine lulu eyes dinshi yace "I love her too Mami yeeee" yay maganan yana lumlumshe idanunshi kafin yay luuu zai kwanta akan plate din abincin da sauri ta janye plate din abincin ya daura kanshi kan table yay bacci, shiru tayi tana kallonshi kafin ahankali ta ijiye plate din a gefe ta daura hanunta akanshi tana shafa soft gashin kanshi dayasha gyara dayan hannu ta kuma tana cire rice din daya bata kumatun shi tana sharemai oil din, ahankali tama forehead dinshi kiss kafin takira sunanshi tana bubbuga bayanshi. "Aadil, Son, Son get up muje ka kwanta adakin ka" cikin bacci ya make mata kafada yana turo baki yana tsotsan bakin, kyaleshi tayi tana kallon agogo dan nan da 15min Dr shi zaizo ya duba shi as usual idan yazo yatashi dole.

_🌹IN BANI 🌹_ 





 _M. Shakur_



10....


 Gyara zaman kujeran motan yayi yadan kwantar da kujeran ya rungume wayan sosai a kirjinshi yana tunanin dan uwanshi, shi karan kanshi he's missing him, he miss his twin Brother so much, tunane tunane yadinga yi harwani irin bacci mai dadi yay gaba dashi acikin motan.

Kiran Sallan asubahi dayaji yatayar dashi daga baccin dayay awon gaba dashi, ahankali ya bude ido gabaki jiyayi duka jikinshi namai ciwo, yana kallon inda yake yatuna acikin mota ya kwana, dan gajeren tsaki yayi yabude motar yafito ya rufe ya fita daga asibitin ya sallaka titi dan masallacin yana ta dayan side of d road ne.


 Saida yajira rana tafito yasakeyin raka'a biyu sanan yafito daga masallacin, wani dan mini supermarket dake gefen mosque din ya shiga yasai brush da tooth paste yafito ya tsallako yadawo cikin asibitin yana tafiya ahankali yay wani irin kyau yana lumlumshe ido alamun bacci bai isheshi ba, shigowa cikin asibitin yayi yy hanyar dakin da aka kwantar da ita, da sallama ciki ciki yabude kofar dakin datake, babu kowa adakin saima gadonta da aka gyara, anyi mopping tiles din kasa sun bushr sai sheki suke, karasawa ciki yayi yana karabin ko'ina da kallo yaja kujeran ya zauna yana kallon TV dakin dayaga an kunna yana tashar CNN, karan bude kofan bathroom yasa yadago kai da sauri wata nurse ce daban tafara fitowa tana kallon cikin bayin, shima kofar bayin ya tsare da ido ya kosa ya ganta, ahankali tafito kanta akasa tana wasa da kumbunan hanunta dasukai wani irin haske, kana ganinta kasan wanka tayi an bata doguwan riganta da aka wanke mata a laundry tasaka yamata kyau sosai, fuskarta babu komi looking natural, kanta babu dan kwali dan nata tun aruwa yabata, kafafunta na cikin wani white slippers dasuka bata tasa, tai wani irin kyau cikin sea blue gown din kaman wata amarya, tunda tafito idanunshi ke kanta bayako kyafta ido harta karaso wajen gadon kafafunta na harhardewa, jitake kaman zata fadi, nurse dince ta kalleshi tace "good morning Sir" gyadamata kai kawai yayi batare dayace komiba, ta kalleta yanda ta tsaya bakin gadon tana wasa da kumbunan har lokacin tace "ki zauna magani zan baki" ahankali ta zauna kaman wacce ke tsoron zama akan gadon, daukan  magungunan tayi nurse din tabata tasha da kyar sanan tadau coffee da asibitin suka hada ma patient dinsu dayake arufe yanada zafi sosai ta bata tace "finish it okay" gyadamata kai tayi hakan yasa tai murmushi ta kalli Aabid dake kallonta kaman zai cinyeta tace "Sir your wife is very beautiful" wani irin murmushi yayi yana kallon fuskar nata harda dan kada kafa yace "oh yeah she is, right Jewel?" da sauri tasa hannu tana sosa idonta ko kadan batajin dadin yanda suketa kallonta batada dan kwali batada hijabi jitake kaman ta nutse akasa sabida kunya, murmushi nurse din tayi dake kallonta tace "shy, shy" ta kalli Aabid tace "Dr is coming, he will examine her first before discharging her, dama you've cleared all d bill babu abinda zaka biya kuma kawai sallaman ki zaiyi" gyadamata kai yasakeyi batare dayace mata komiba tajuya tafita daga dakin ta rufo musu kofan.

Juyo dakai yayi ya kalleta yanda har lokacin take rike da cup din coffee sai sunnar dakai takeyi, ahankali yatashi daga kan kujeran ya matsar da kujeran baya yay kneeling akasa agabanta har kafafunta na gogan kirjinshi da sauri ta daga kanta ta zaro ido cike da tsoro, murmushi yamata ya zare cup din coffee daga hanunta ya ijiye akan side drawer yana kallon fuskarta, hanunta yakama ahankali kaman yana kama kwai da sauri zata fisge hanunta yarike gam da sauri yana girgiza mata kai yace "no please" yay maganan yana kama dayan hanun yana kallon fuskarta itama shi take kallo kirjinta nawani irin bugawa idanunta sun cicciko da kwalla, murya chan kasa yakirata. "Amatullah" marmar tai da idanunta dake shirin fitar da ruwa, ahankali yace "your brother is on his way to come and pick you, and I don't want you to go batare dana bayyana miki sirrin dake rainaba" shiru yayi yana kallonta itama shitake ta kallo he could feel yanda kirjinta ke bugawa daga veins din hanunta, kara kwantar da murya yayi yace "I love you Amatullah" wani irin bugawa da kirjinta yayi yasa tafashe da kuka sosai dan ko kadan ta tsani soyayya ita babuma abinda ta tsana irin aure, tsoron maganan aure ma take barinma soyayya, ko wanan ma daya ganta haka sa'a yaci batada lpy kuma batasan ina takeba da tuni tasan yanda tayi ta sabe, hanunta yadan matsa yana kallon yanda take kuka da muryanshi datai rauni sosai yace "I just saw you jiya and am completely blown away, I love every single thing about you Amatullah tunkafin ma ki bude ido, the way am connected to sunrise tun ina yaro I've always said maybe akwai wani abu da Allah ya tanadan mini a irin lokacin ne, wen I was small nasha mafarki na tsinci my Jewel acikin ruwa, ashe hakane, the first time I saw you was d yamma, the first I saw you acikin ruwane, your face was glittering yana wani irin haske as bright as the moon acikin ruwan nan, and right there, just right there nasan you are mine, nasan you are the one, deep down I felt this force of attraction dat keep pulling me towards you, I fell for you the very  first time I set my eyes on you, please Jewel I know you are not married cus u don't look married, will you give me that honor to become your life partner? Zaki aureni my Ama?"  a tsorace tana kuka sosai ta shiga girgizamai kai, shiru yadanyi yana kallon yanda take kuka tana girgiza kai, ahankali kaman wanda ke tsoron ta yace "I have ur Mum's number, inkina tsoron fadamusu ne nakira nafada mata ina sonki?" da sauri ta girgiza mai kai hakan yasa yace "please be my wife kinji Jewel nakamu da tsananin sonki, will you be mine forever?!" da sauri ta girgiza mai kai kanta akasa, dan lumshe ido yayi yabude su kadan ya daurasu akanta yace "an miki mijine, are you engage?" da sauri ta gyadamai kai dan kawai yarabu da ita, tsayawa yayi chak yana kallonta sosai yaji zuciyarshi tamai wani irin zafi kaman an watsamai rushin wuta, ahankali yace "saisa bazaki aureni ba because u are engage?" gyadamai kai tasake yi da sauri, da sauri ya lumshe ido yana kokarin saita bugun heart dinshi kafin ahankali yabude su  ya daurasu kanta idanun sun kada sunyi ja, cikin wani irin harsh voice yace "bazaki aure shi ba, and if you do saina kashe shi, koma wakika aura I will kill him!" da sauri ta kallai yanda taga idanunshi sun chanza kala yasa ta saukar da idanunta kasa  tafara karanto addu'a, wanan wani irin mutum ne Allah yahada ta dashi, ahankali yasaki hannayenta yace "you are my wife Amatullah kifadama kowa haka, and zaki gani saina aurek..." ringing da wayarshi yayi yasa yay shiru ya ciro wayar daga ajihun shi yana kallo ganin bakuwar number ce yasa ya dauka batare dayay magana ba yakara wayan a kunne, daga ta chan bangaren akace. "Umar Faruk Abdullahi mai kaji ke magana, am at d hospital reception daka turamana address din" ahankali ya mike tsaye yana kallon yanda take hawaye yace "okay, am coming" katse wayar yayi ya kalleta ahankali yakarasa jikin gadon yawani irin fizgota tsaye saida tai kara. "wayyo Mama" sata yay ajikinshi yay cupping face dinta yana wani irin kallon fuskarta, itama kallonshi take dan ayanda yarike fuskarta dole ta kalleshi, ahankali ya daura forehead dinshi kan nata yana breathing fast fast kaman yanda takeyi itama kaman zata suma, cikin wani irin voice mai taushi da zafi yace "you are Mrs Aabid Amatullah" dan sassauta rikon daya mata yayi kafin ahankali yay hugging dinta so tight yasa kanta a kirjinshi yay hugging nata well ya lumshe ido, salati kawai take tunda take bata taba hugging namiji in her life ba, gidansu ma gabaki dayan yaran babanta mata ne sai Ya Faruk dayake dan kanin Abba and maganan kirki ma baitaba hadata dashiba, bayanta ya shafa kafin yama soft virgin gashinta kiss ahankali ya chusa hancinshi a gashin cikin wani irin murya data kasa gane ko kuka yake komeyake oho yace "I love you Amatullah My Jewel" shiru yayi ya chusa hancinshi cikin gashin yana shakan kamshin ruwa dayake idanunshi sunyi ja sosai, yakai kusan 2min sanan yasaketa dan sosai yakejin yanda hawayenta suke jikamai gaban riga, kallon idanunta yayi dayaga harsun kumbura sun baci da hawaye,  yakai yatsarshi ya sharce mata hawayen datake yace "I'm sorry for hugging you, I couldn't control my emotions, and I feel better danai hakan" kasa sakinta yayi shi kanshi yarasa wani irin so yake mata he just don't wanna let her go, wani irin bakin ciki yakeji idan yatuna anzo tafiya da ita, he just don't want this moment to end, betaba sani haka akeji wen you are in love ba, sake hugging dinta yay akaro nabiyu dudda yanda take kokarin ta kwace kin bata chance din yayi da muryanshi datai rauni sosai yace "please stop crying Jewel, your Dad told me a kano kuke I will come, keep yourself for me for me and you" sakinta yay ahankali yaciro handkerchief daga aljihun shi ya share mata hawayen daya gama wanke mata fuska kafin ahankali yya bending over yama forehead dinta light kiss yay shiru batare daya janye bakinshi daga kan forehead dinba yana sauraran yanda take kuka, cikin wani irin cool calm voice dakenan chan ciki yace "I love you so much Amatullah, your brother is here bari na shigo dashi" janye bakinshi yay ahankali idanunshi sunyi jajir shi kanshi baimasan sonta ya shigeshi hakaba baitaba sanin kana iyason mutum jiya yau son yakaru ba ahankali yajuya yafita daga dakin tareda rufo mata kofa. Fashewa tai dawani irin shegen kuka idanunta sunyi jajir.



A reception yaga Faruk tsaye yana danna waya yana sanye da complete kayan sojoji daya karamai kyau da kwarjini, hanunshi rikeda waya yana dannawa, dailing number daya kiranshi dashi back yayi yana kallon sojan dayaji aranshi shine, ringing wayan Faruk yayi hakan yasa ya dago kai neman me kiranshi, hada ido sukayi sukama junansu kallon kallo kafin Aabid ya daga wayarshi dayay dailing number shi ya nunamai, shima daga wayan yayi ya nunamai hakan yasa sukadanyi murmushi Faruk ya karaso wajen yana jan jakan ya mikamai hannu yace "thanks, we appreciate your hospitality" murmushi kawai Aabid yayi yace "let's go" yay gaba Faruk biye dashi abaya bude kofan da akayi yasa ta dago kai da sauri Ya Faruk ne ya shigo dakin sanye da kayan sojojin s

dasuka mai kyau sosai yawani irin kafeta da idanu yana kallonta, itama kallonshi take ahankali kafin ta dauke kai, ahankali yatako yazo gaban gadon shikuma Aabid ya tsaya jikin kofa yana kallonsu, tsayawa yay agabanta ya sauke baban bag din hanunshi a gefe yana kallonta, murya chan kasa yace "ya jikin?" gyadamai kai tayi batare datai magana ba hakan yasa yay shiru yana sake kallonta yana nazarin idanunta dasuka kumbura sosai, ahankali yace "why are you crying? Meke miki ciwo" hanunta da aka sama ta drip da aka cire ta nunamai tace "zafi yakemin" hanunshi ya mika ya karbi hanun yana kallon wajen dayadan kumbura daidai lokacin aka bude kofar dakin aka shigo nurse ne da Dr, sunnar da kanta tayi Dr yakaraso jikin gadon yace "My patient takosa ta tafi gida" yay maganan yana gyara stethoscope din jikinshi ya dubata sanan yacire yana murmushi yace "good to go" ya karbi file dinta daga hanun nurse yay yan rubuce rubucen shi na discharge summary sanan yamata prescribe maganin da za'a siya mata, karba Faruk yayi sanan Dr yamusu sallama yafita daga dakin nurse biye dashi, jakar hanunshi Aliyu ya bude yaciro mata dogon hijabin ta baby pink ya mika mata da sauri ta karba tasaka hijabin a zaune bakaramin kyau yamata ba hijabin mai hula dakuma hannu, glasses dinta yamika mata ta karba tasaka ahankali, yabata wani flat shoe na cikin jakan ta saka, sosai Aabid ke wani irin kallonta dan tamai wani irin mugun kyau, hada jakan Faruk yayi yarike yamika mata hannu kallonshi tadanyi kafin ta saukar da kanta kasa ta mika hanun hanunta dake rawa ta rikeshi sanan ta sauko daga gadon ahankali kaman me tsoron saukowa, juyowa Faruk yayi da murmushi kan fuskarshi ya mika ma Aabid hannu yace "thank you so much, Abba yace amika gaisuwar shi, Allah yabada lada, mungode da dawainiya" murmushi yamai yabashi hanun yace "bakomi, ina zaku yanzu?" dan shiru Faruk yayi kafin yace "we are going home, Abba yace nadawo da ita gida straight bazata koma gidan bikin ba, airport zamu yanzu" da sauri yace "I can drop you guys" dan murmushi yayi yace "no you don't have to worry, taxi na jirana awaje, thank you so much" gyadamai kai yayi ahankali yanadan Satan kallon Hamida da kanta ke kasa har lokacin, hannu Faruk yasa yabude kofan yasakai yafice yana rike da ita sosai yaji zuciyarshi nawani irin breaking yana kallonta hoping ko zata dago kanta su hada ido, ya zuba hannayenshi a aljihu amma har suka fice daga dakin bata dago kantaba wani irin jingina yay da bango ya lumshe ido zuciyarshi yamai so having wani iri yakeji da baitabaji ba in his life, kasa daurewa yayi yabude idanunshi dawani irin sauri yaja kofar yabude yafita daga dakin harda dan gudunshi he wanna see her one last time, yafita bude kofar reception din yayi ya tsaya akan stairs din wajen daidai lokacin Faruk yabude mata bayan motan zata shiga da sauri ya kwala mata kira. "Amatullah!" da sauri daga ita har Faruk suka waigo, hada ido yayi da ita kirjinshi nawani irin suya ahankali yasakin mata wani irin murmushi mai ciwo ya daga mata hannu alamun bye, da sauri ta dauke kak ta shiga cikin mota tana watsa da bakin hijabin ta Faruk yarufe kofan ya juyo yamai murmushi ya dagamai hannu ya shiga gaban motar mai taxi din yaja motar suka tafi sukabar haraban asibitin, motar yabi da ido zuciyarshi namai wani irin rawa rawa har saida yadena hango motar ya lumshe ido, ahankali yabude idon ya sauka daga  ya wuce ya shiga motarshi ya kifa jikin kujera yakai kusan 3min kafin yadago yatada motar yaja yabar asibitin da kyar.


Ihun daya cika gidan dashi yasa Mami ta farka daga baccin datake firgigit da salati. "innalillahi wa innailaihi raji'un, Abie, Abie" firgigit magidancin da akalla zaiyi shekaru 60 shima ya farka yana kallonta yanda Mami ta firgice tana kokarin zira slippers yasa shima sauka daga kan gadon kafin ma yasa nashi bathroom slippers din har Mami tafice daga dakin da sauri tafita tai dakin tabude dake facing nasu, wutan dakin akashe sai ihu yake yana kuka, da sauri Mami ta kunna wutar dakin tai kan gadon, yana kwance sai ihu yake yana juye juye yana kuka idanunshi a rufe, da sauri takarasa jikin gadon ta zauna tana bubbugashi. "Son, Son, Aadil, Aadil" da sauri baban nasu ya karaso ya zauna ta wuraren kanshi  yasa hannu yadagoshi ahankali yana kiran sunanshi shima. "Aadil" ganin bai bude idoba har lokacin wani irin kuka yake yasa yanuna ma Mami bottle water shi da ake ajiyemai a gefen bed dan yana tashi yasha ruwa cikin dare, da sauri Mami ta dauka tabude, hanunshi ya mika mata ta xubamai ruwan kadan yashafamai a fuska yana kiran sunanshi. "Aadil, Aadil" bude idanunshi yayi yana kallon ko ina nadakin yana jujjuya idanunshi, da sauri Mami ta matso kusa dashi  takama hanunshi tace "am here Son, menene? Mekake so eh? Mekema ciwo tell me" tashi yayi daga jikin Abie yafada jikin Mami yasaki kuka ya rirriketa kanshi narawa yana kuka sosai, shafamai kanshi dataji yay zafi ta shiga yi tama kasa magana sabida yanda gabanta ke faduwa, tsugunnawa Abie yayi agabansu bayan ya sauka daga gadon ya shafa kanshi yana kallon fuskarshi yanda yake kuka ashagwabe, cikin lallashi yace "is okay, are you missing Aabid, zance yadawo gobe okay" fashewa yay da kuka sosai harda shesheka yarike Mami gamgam yana girgiza kai, shafa kanshi Mami tayi ta dagoshi handkerchief dinshi Abie yamika mata ta karba ta sharemai wuyanshi da fuskarshi tace "menene? Mafarki kayi? Why are you crying like this, tell me menene" cikin kuka sosai kanshi na rawa yace "s...she..she" da sauri Mami tace "she? Wace she? Menene kuma she Aadil?" fashewa yasakeyi da kuka yace "Mami I want to see her take me to her, Abie" ya kalli baban su yana kuka sosai yace "Abie take me to her" da sauri Mami tace "wane Aadil? Wazamu kaika wurinta? Who are you talking about" fashewa yayi dawani irin kuka yana jan rigan Mami cikin kuka sosai yace "shee" hawaye Mami ta share tana gogemai nashi tace "kaga Aadil dan Allah kadena kukan nan is not good for you, u had a dream I guess, bamusan waye she ba, but zamuyi addu'a ko my Son" make mata kafada yayi yana kuka sosai yana wani irin nishi yana make mata kafada yana tura Mami yana komawa baya  ganin haka yasa Abie yahau gadon yana kamashi ganin yana neman buga kanshi yace "Aadil come, a ina she din take to mukaita wurinta? Why are you looking for her, dena fushi zamu kaika wurinta, fadamin who is she eh my Boy?" cikin wani irin kuka yana kallon Abie da idanunshi dasukai ja yana lumlumshe ido yace "she, Abie She, she, Abie I want to see her" da sauri Abie yace "to dena kukan zaka ganta, zamuje but saikasha magani sai muje wurin she, zakasha ai ko?" da sauri ya gyadama Abie kai yana dafe kanshi dakemai wani irin ciwo yana lumlumshe ido kanshi na kokarin tunano mafarkin daya gamayi yanzun nan,  fuskar Hamida yagani tazo dakinsu ta tsaya abayan labule shikuma yana kan gado yana buga game din race awaya, dan bude labulen tai kadan ta kwalamai kira tana dariya sosai. "Aadil" da sauri yadago kanshi amma saita koma bayan labulen baiga fuskarta ba, make mata kafada yasakeyi yaki tasowa yacigaba sake lekowa tayi tana dariya sosai takirashi. "Aadil" da sauri yadago kai da gudu takara buya abayan labule, ahankali ya ijiye wayan yatashi daga gadon kanshi na rawa yana sanye da clean white t-shirt danshi mayen white ne baya yadda yasa wani kaya ko Mami tabashi inba white rigaba, da wani fine common flag 3quater daya tsayamai agaban gwuiwa kadan, kafanshi sanye da slippers white yataho kanshi na rawa bakinshi na zubar da miyau yanadan lankwasa kai yana leken labulen yana turo baki kaman mai shirin yin fada yana hararan labulen kaman dan yaro yace "who...who are you?" makemai kafada tayi tacikin labulen tace "oh'oh find me and know me Aadil" cigaba da tafiya yayi harya karaso jikin labulen yana hararan labulen yasa hannu yaja labulen da karfi da gudu tana dariya sosai tajuya zata gudu ya damko hanunta dan juyowa tayi kadan ta kalleshi one side din fuskarta yagani tana sanye da glasses fari, zaiyi magana yaga ta fizge hanunta ta gudu da gudu shima yabita amma koda yafito harya sauko kasa bai ganta ba hakan yasa yadinga kuka cikin mafarkin yana nemanta.


 _Wanan littafin is a pure, clean, sweet, mesmerizing, warm, twisted love story dabaku taba ganiba, trust maman Shakur kullum sabon Salo nake kawoma makaranta littatafai na_ .




Alhamdulillah anan nakawo karshen free pages din littafin _IN BANI_

In kinason cigaba da karanta littafin nan mai suna _IN BANI_ danjin yanda zata kaya Zaki tura 300 ta account number na 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na sainai adding dinki a group din danake posting. 

Zaki iya turo katin MTN ta watsapp number na kaman haka 07012181461, for any enquiry you can contact me through my watsapp number 07012181461. Thank you lovelies. I love you and I appreciate your support.

_🌹IN BANI 🌹_ 





 _M. Shakur_


11...


Suna kaiwa airport yabiya musu kudin komi suka jira kafin suyi boarding flight dinsu, tana rike da hanun nun Faruk gam tana bobboye fuska, ahaka harsuka iso kano saukowa sukayi suka shiga taxi dazai kaisu gida.


Sosai taji hankalinta yawani irin kwanta data gansu a anguwan su sai murmushi take tana kallon anguwan su, ta mirror Faruk ke kallon fuskarta yanda take murmushi tana kallon hanya, suna parking a kofar gidansu da sauri tabude kofan motar tafita, Mama ce kadai a tsakar gida da matan dake zuwa musu wankau, wani irin murmushi tayi ta kwala mata kira. "Mama" da sauri Mama ta juyo jin muryan Hamida, wani irin gudu Hamida tayi taje tafada jikinta tana dariya ahankali yanda takeyi, cikin jin dadi da tsananin farin ciki Mama tawani irin rungumeta tace "kedawa yene Hamida?" tai maganan tana cirota daga jikinta dan taji tsoro ganinta kaman an jehota, ko kadan batasan Abba yacema Faruk yaje yadaukota ba jiya da daddare ba, tana jikinta rungume da ita tace "Yaya Faruk yazo yadauko ni fa Maman mu" daidai lokacin Faruk ya shigo gidan rike da jakanta, murmushi Mama tayi tace "to aisai kije ki gaishe da Kakan ku kizo" tasaketa tana kallon Faruk dake karasowa wajen rike da jakanta tace "sannu soja shine ta barka da jakan ko" ahankali ya ijiye jakan agaban Mama kanshi akasa yace "ina kwana Mama" sakin Mama Hamida tayi tai hanyar sasan Kaka, ahankali ta turo kofan ta shiga tana kallon ko'ina tai sallama cikin daga murya Kaka tace "Hamida, Hamida, aini tun ranan dazaki tafi nace saikinsan mekika yi, sai kinsan me kikayi, me kika shirya, saikinsan kirsa da kisisina dazaki hada ki dawo garin nan, Hamida anya bazan kiramiki malamai azo amiki rukiyya ba inaga aljanu gareki fa" dan turo baki tayi tasami waje ta zauna nesa da ita tana wasa da bakin hijabin ta kaman bada ita ake magana ba, zaro ido Kaka tayi tace "nikika maida mahaukaciya ina magana kinmini banza" daidai lokacin Faruk ya shigo dakin, watsa mata harara yayi yace "ke tsohuwar nan kin cika ihu, please inada ciwon kai yau kiyi shiru pls" yay maganan yana karasawa wajen fridge din dake falon, binshi da kallo Kaka tayi baki abude hakan yasa Hamida tarufe bakinta da hijab tana dariya chan kasa kasa, juyowa Kaka tayi ta kalleta ranta abace tace "dan gidanku dariya kike mini" da sauri ta girgiza kai still tana dariya chan ciki gudun karta ji tana kare bakinta da hijabi daidai lokacin shima Faruk yadawo rike da bottle water ya zauna a gefen Kaka zai bude bottle water, duka ta dakamai abaya da sauri ya kalleta cikin fushi yace "auch waike old lady nan me haka kike dukana agaban yara" kaman Kaka zatai kuka ta nuna kanta tace "kafara kirana da wanan yaren yahudancin ko Faruku, to wlh bari ubanku yadawo saina fadamai cin mutunci dakuke shigowa har Sasa na kukemin, ku tashi kufita, kutashi kufita nace, kuma bani ruwan gorana saurayin Zainaba ya kawomin su kusan katan biyar, bani" tafada bacin rai tana mika hannu zata karbi ruwan, tsaki yayi yadaura kafa daya kan daya yanashan ruwan shi ahankali Kaka tasaki baki tana kallonshi tace "ai shikenan kasha wuta shege dan buhun uba" fashewa da dariya Hamida tayi dayasa Faruk saukar da ruwan daga bakinshi ya watsa mata wani mugun kallo da sauri ta tashi tafita daga dakin da gudunta yabita da kallo, hararan kofan Kaka tayi tace "ja'irar yarinya, ai wlh Faruk banso kaje ka daukota ba, so nayi jiya da Sama'ila nama maganan kace aiki zaka, baga tanan ba rass bataima kama da wacce tafada ruwaba" juyowa Kaka tayi ta kalleshi daidai ya ijiye ruwan akasa tace "kaje wurin Maman kane yau?" girgiza mata kai yayi yana yatsine fuska, yace "sai anjima da yamma yanzu aiki zan tafi" washemai baki tayi tana kara matsowa kusa dashi tana murmushi tace "Faruku na wai har yanzu ba'ayi albashin bane, kamin alkawarin dubu ashirin fa" hararanta yayi yace "jiya agabana Abba yabaki dubu talatin wai mekike yi da kudi ne haka?" sake matsowa kusada shi tayi kaman zatai gulma tace "na rantse maka Faruku adashi nakeyi, tara kudin bikin Hamida nake" wani irin kallo yamata yace "wace Hamidan?" baki tabude tace "kagamin iskanci munada wata Hamida agidan nanne  bayan wanan hamidan data fita daga dakina yanzu?" cikin daure fuska yace "yaushe tai saurayi?" sake matsowa tayi kusa dashi kaman wacce ke shirin yin gulma tace "a'a kaima dai kasan ko mashinshini Hamida batadashi ko, amma so nake kabani kudin dukna hada naita zubin adashi ina tari, inama bikin ta tari, kasan Hamida yar wajena ce, itace mai sunana fa, kaga shegen fadan nan danake mata wlh sonake ta chanza ne dan batayi gadon halina ba, bataci sunana da aka bataba, amma dazaran ta chanza zamu zo mu fara shiri sosai, nama tuna bari naje sasan su hado kayanta zatayi tadawo shashin nan ma yau dinan" shiru tayi tana nazarin yanayin fuskanshi yanda yay kini kini darai, tace "kaikuma lafiyan ka naga kai wani iri" yatsine fuska yayi yace "am fine" ya mike tsaye yana gyara kayan jikinshi yace "natafi aiki" tashi tayi tace "muje na rakaka, kadan tahomin dayar bakan leda kaji inzaka dawo, tunda su Zainaba da Ayush sukabar gidan da yunwa nake kwana Faruku" hararanta yayi yanaji kaman ya bugeta kiri Kiri sai Kaka tabude ido tana karya, dariya tayi sosai ganin yanda yake kallonta tace "bawai yunwan abinci ba na kayan kwadayi, idan kadawo kaza bani kudin aiko? Bazanyi barci ba zan jiraka" hararanta yayi yajuya zai fita hanunshi da damke tace "dan ubanka saika bani danma ina lallabaka" kaman zaiyi kuka ya kalli yanda ta damke well ironed uniform dinshi yace "naji inna dawo zanbaki, ki saken to" sakinshi tayi tana dariya ta dungure mai kai tace "ja'iri barima ubanku yadawo yau zan mishi maganan aurenka ne, wlh koka fito da mata kona je kauye nahadaka dayar aminiyata Iyami" tsaki yayi tsabagen takaici baima tsaya yabata amsaba yawuce yafita daga sasan da sauri tabi bayanshi amma har yay wajen gate hakan yasa tai tsaki ta wuce part din su Hamida. 


Da sallama ta shiga falon su Hamida tagani zaune a falon tanacin indomie data dafa da boiled egg tana kallon zee world tana ganin Kaka tai murmushi tana sunnar dakai, hararanta Kaka tayi tace "aikin kenan ki zauna ke kadai awuri babu kowa shine burinki a duniya miskilan banza, ni ina mamarki?" daidai lokacin Mama tafito daga kitchen rike da tray data debo wake dan gyarawa zatayi tana ganin Kaka tai murmushi tace "yau Umma a shashin mu" da sauri Kaka tace "eh nazo ne, kihada ma yarki kaya sasana zata dawo" turo baki Hamida tayi tana tauna abincin dake bakinta ahankali Kaka ta kalleta tace "ahap ai saidai ki mutu ingayamiki yarinya, yaushe zasu koma ma makarantan yama sunan hutun da sukaje?" murmushi Mama tayi tana karasa shigowa cikin falon tace "mid semester break" da sauri Kaka tace "yauwa shi yaushe zaku koma ke?" tai maganan tana kallon Hamidan dakecin abincinta, dan turo baki tayi tace "ranan Monday" kwafa Kaka tayi tace "saura wanan karan ma ki kwaso zero zero a makarantan kaman na wanchan karan, wlh cema Sama'ila zanyi bazai kara kashemiki koda sule biyar a makarantan ba, aure zamu miki, inyaki kuma nida kaina zan aurar dake" da sauri ta kalli Kaka, gyada mata kai tayi tace "eh kinjini da kyau, wlh aure zansa amiki inhar wanan karan ma kin fadi kaman wanchan tunda kedai bazaki saki ranki ki jona mutane kikoyi abuba, ba nannan zainaba ke zuwa makaranta karatu ba banda ke, malami na koya muku abu kina kakkare fuska kikasa kallon allo, yoto menene amfani Sama'ila yay ta bata kudi akanki har shekara hudu? Kema kinsan naso keda Zainab da Ayush dakuna gama sakandire a aurar daku amma kuma sainazo na hakura da Sama'ila ya nunamin yanaso kuyi karatu amma kam wanan karan bala'i zanyi dashi dan wlh bazan bari dan kudin dayake samu a saida kaji, saida kajifa jama'a yazo yana batasu akanki ba, dan asarace, da'ace nine yabama uban kudaden danasan menayi dashi kuma Allah kaimu mondan, ni nan dakaina zan kaiki har Bayeron incema malamin ku wlh yazane min ke tunda dai kinki maida hankali kiyi karatu" tai shiru tana kallon Hamidan data daura hannu a fuska tana share hawaye, tsaki tayi ta kalli Mama data zauna kan kujera tafara gyaran wakenta ita yanzu bala'in Kaka baya damunta dan tsufa ce yamata yawa, cikin masifa tace "ai cewa nayi kibar gyaran waken nan kitasa keyanta taje dakinsu ta ciro kayanta daga sip dinsu, na Zainab da Ihsan kawai zaku bari a sip din ta tattaro tadawo Sasa na, nariga na share dakin dazan bata tastas, Allah kuma yakaimu Monday zakiga nizan kaiki makarantan na rantse miki saina sa malamin ajinku yamiki bulala goma hala hakan zaisa kifara karatu, kici jarabawa da kyau, kigafa tunda sukai hutun nan banga tabude littafiba fa, kullum tana nanike adakin su daga taci saita bacci sai shegen bacci kaman kaza, ki ajiye kwanon wanan tsutsan kampanin duksu kesaki bakida kyan gani, yarinya taci tuwon dawa da miyan kalkashi abinci mai Gina jiki bazata ciba sai tsutsan kampani" murmushi Mama tayi tace "Kaka indomie ce ba tsutsan kampani ba" cikin daga murya kaman zata fasa gidan tace "injiwa Haleematu" ta nuna plate din tace "ke bakiga yanda abin take a lankwashe ba, wani irin ziza ziza da ita, tsutsa ce saisu busar saisu barbadeta da fulawa fa asaka a leda a sayar" ta kalli Hamida dake share kwalla tana tauna indomie bakinta ahankali tace "ba dake nakeba dan gidanku, tashi kije mamar ki ta tayaki hada tulin kayan ki, dama gobe su Zainaba zasu dawo sa sami sarari adakin suma" tashi tayi ahankali tai hanyar corridor inda dakinsu yake, ajiye waken Mama tayi ta tashi tabita tana murmushi kasa kasa Kaka tabisu da harara kafin takarasa tadau plate din indomie tafice dashi tana hararan abincin takarasa wajen bolansu zubar da indomie tayi sanan ta wuce chan pampo ta ijiye kwanon ta wuce Sasan ta.

_🌹IN BANI 🌹_ 





 _Maman Abd Shakur_ 


12....


Tashi Abie yayi yadauko maganin shi da yawancin inya fara surutai haka shi ake bashi ya dauko da sauri yadawo kan gadon ya dagoshi yana mikama Mami maganin yace "tashi kasha to saimuje wajen She" gyadama Abie kai yayi yana kuka ahankali yana yatsine fuska, zuba maganin Mami tayi ta mikamai ahankali yabude baki ya shanye maganin  da kyar kullum yake yarda yasha amma yau yasha da kanshi, yanasha ko two minutes baiyiba bacci yay gaba dashi, gyaramai kwanciya Abie yay da kyar yaja bargo ya lullubeshi ya tofamai addu'a yajuyo ya kalli Mami dake share kwallan dake xubo mata, tasowa yayi ahankali yadawo bakin gadon kusada ita hanunshi yasa ya rungumota batare dayay magana ba, ahankali ta saukar da kanta kan kafadarshi wasu sababbin hawayen na gangaro mata kumatu tace "Abie why this? Why we? Why our Son? Shekaru talatin da biyu kenan muke fama, Abie please kafadamin what else dazanyi da yaronmu zai sami lafiya, banda burin daya wuce nabude idanuna naga Aadil kaman kowani namiji aduniyan nan, kaman dan uwanshi, Abieee" taja sunanshi cikin kuka, kiss yama forehead dinta yanadan shafa bayanta shima idanunshi sunyi ja, zaiyi magana wayarshi dake aljihun jallabiyar shi ta shiga ringing, riketa yay da hannu daya yasa hannunshi a aljihu ya ciro wayar yana kallon screen din, dan juyowa yayi ya kalleta yace "Baba ne" da sauri ta share hawayen datake yi tana mishi alamu daya dauka, daukan wayar yayi cikeda girmamawa harda dan dukar dakai yace "barka da safiya Baba" daga tachan bangaren tsohon da akalla xaikai shekara 80 yace "da Abdullahi nake magana ko?" yay maganan a natse kuma dadaddaya kaman yanda tsofaffi ke magana, cikeda girmamawa yace "eh Baba nine" a natse yace "to, to, to Masha Allah, ya kuke? Ya sana'ar taka tachan?" murmushi yayi yace "Alhamdulillah Baba, sana'ar munakan yi kuma ana samun riba daidai gwargwado" ahankali yace "masha Allah, Allah ya taimaka, Maryama fa?" murmushi yayi yace "gatanan Baba bari nabata wayan" ahankali yace "tsaya tukunna" cikeda girmamawa yace "to Baba" dan shiru yayi kafin ahankali yace "ina Hassan da Hussain?" kallon Mami yayi suka hada ido sanan ya maida hankalinshi kan wayan yace "Alhamdulillah suna lpy, Hussain na Nigeria yanzu haka yana Lagos ya...." cike da fada yace "Hussain na Nigeria shine baizo gidaba? Abdullahi dagakai har Maryama inda kusan bazaku iya bama jikokina yan biyuna tarbiya mai kyau ba dakun banisu na rainesu sun girma sun taso anan wurina, amma yaro ace yana kasar iyayenshi munan bamamu da labari yana gari, kenan inda ban kirakaba da bazaka fadi mini ba" cikin kwantar da murya yace "kayakuri Bab..." da sauri yace "bannemi wanan daga gareku ba, yau kwanan shi nawa?" ahankali yace "kwanan shi tara Baba, wani assignment yajeyi a Lagos amma dama..." katseshi yayi ta hanyar kiran sunanshi. "Abdullahi" da sauri cikeda girmamawa yace "na'am Babana" ahankali yace "kafadama Hussain yakamo hanya yazo kano yauyau dinan gidan kakanin shi banason naji wata magana, sai magana nabiyu dayasa na kira" yadanyi shiru yana hutawa, a natse yace "ina Hassan, yaya jikin nashi?" dan juyawa yayi ya kalli Aadil dake bacci har lokacin yace "Alhamdulillah Baba, jikin nashi da sauki" cikin dan kakkausar murya tsohon yakira sunanshi. "Abdullahi" ahankali yace "na'am Baba" shiru yayi nawurin minti biyu kafin yace "kaima kasan nabaku lokaci mai tsawo, na tsaya sanan na zuba muku ido ina kallon ku dakai da Maryama, nasan ku nasan halinku na yaran zamani, sanan bankuma tauye muku hakkin ku ba a matsayin ku na iyayen yaraba, na barku babu kasashen duniyan nan dabaku zaga da Hassan ba tun yana dan mininin shi neman mishi magani, to kanajina?" da sauri yace" eh Baba ina jinka" cikin yar shakakkiyar muryanshi ta tsofaffi yace "masha Allah, abinda nakeso daku shine, ka tattaro yinaku yinaku ka kawomin jikana nan kano, ku kawomin shi nan kano afara mishi maganin gargajiya, zamu jaraba mugani abinda Allah zaiyi, bazan zuba muku ido ku karar min da rayuwan jikana a hanyar asibiti ba, burina shine ya warke namai aure naga tattaba kunnena kafin mai afkuwa ta afku wato mutuwa, ku kawomin jikokina Kano zan nema mishi magani da kaina, ku kawomin su, ku zaku iya komawa indanta Hassan ne zan daukomai babban nurse ko Nani dazai dinga kulanmin dashi" yay dan shiru yana Tari da sauri yace "sannu Baba" saida tarin ya lafa sanan yace "kuyi shirye shiryen dazakuyi, ku kwasan mai duk wani abu dayake so gudun karya muku kuka a jirgi inya gaji da zama, ku hada komi kutaho Nigeria gobe, kufadima Hussain ina jiranshi shikuma yauyau dinan" ahankali yace "to Baba" "yauwa ka gaidamin da Maryama" "to Baba zataji" ahankali yace "Allah yamuku albarka dukan ku, Allah yabama Hassan lafiya, Allah ya kiyaye hanya yakawoku lafiya" da sauri yace "Ameen Baba" "yauwa to, nabarku lafiya" ya katse wayan. Ahankali ya zare wayan daga kunenshi ya juyo ya kalli Mami data gamajin komi, ahankali yace "anjima kihada mai kayanshi komi da komi, I will sort out d booking" gyadamai kai tayi tace "to Alhaji Allah yabada sa'a" juyowa sukayi dukansu suna kallon Aadil din dake bacci ahankali Mum tasa hannu tana shafamai kai kafin tadan kwanta a gefenshi tana shafamai kai tana kallon fuskarshi, Allah kadai yasan yanda takeson Aadil dinan, zata iya bada duka abinda ta mallaka a duniya inhar zai warke, shafa fuskarshi tayi tana kallonshi hawaye ya gangaro mata daga ido ahaka bacci yay gaba da ita hanunta akan fuskarshi, kafesu da ido Abie yayi feeling guilty, babu irin tunane tunanen da baiyi ba, blanket din gadon yaja ya lullubesu dashi yatashi yafita daga dakin yarufo musu kofa yafita, dakinshi ya shiga ya zauna gaban study dinshi ya kunna laptop dinshi yaje sight din emirate airlines, booking yamusu yay making payment aka turamai booking reference din ta email dinshi sanan ya rufe laptop din yay shiru yana kallon wani babban zoben dake kan yatsarshi yakai kusan 10min yana kallon zoben sanan yasake daukan wayarshi, dailing number Aadil yayi amma baishiga ba hakan yasa yatashi ya kwanta akan gado.




***

Shafashi dayaji anayi yasa yabude ido daga wani irin nauyayyan bacci daya samu ya kwasheshi around 4 nadare tunda jiya dayadawo daga asibitin da aka kwantar da Hamida yakejin wani irin kunci, sosai zazzabi yarufe shi jiyan nan, ahankali ya daura idanun akan fuskar Vanessa dataci gayu sosai tai makeup a fuskar tana daure dadan white towel, kwanciya tayi akan kirjinshi tanama kirjinshi kiss murya chan kasa tace "handsome baccin ya isa haka okay, your temperature is normal yanzu, am so lonely Aabid how are you feeling now?" lumshe ido yayi yanadan cije lips yakira sunanta achan kasan makoshi yace "Vanes...sa" dago kanta tayi tace "yes Handsome menene? something seems off about you tun jiya dakadawo, kodai yarinyar nan is a witch ne dama she's too fine" bude idanunshi yayi duka yadaura akanta yana mata wani irin kallo da idanunshi dasuke cike da bacci a gajiye yace "watch your tongue" yay maganan yana kara lumshe idonshi danko kadan baison hayaniya ko motsi zaiyi sai Hamida tafado mai arai, anytime daya kulle idanunshi ita yake gani, ta tsayamai arai, ta tsayamai a thought, ta tsayamai akomi ma, baitabajin yanda yakejin nanba akan any girl, pink lips dinshi Vanessa takafe da ido kafin ahankali ta daura fuskarta kan nashi tana kallon lips din tana breathing heavenly takira sunanshi dawani irin low sweet voice. "Aabid, talk to me handsome, what's the matter uhm?" tai shiru tana kallon fuskarshi amma baiyi magana ba, kiss tamai akan fine soft lips dinshi light one, bude ido yayi kadan ya kalleta batare daya cemata komiba, murmushi tayi tai cupping face dinshi tace "lemme make you feel better" zaiyi magana ta daura yatsar ta akan lips dinshi tana wani irin mai sexy kallo tasanya dayan hanunta ta warware towel din jikinta tai flinging dinshi, lumshe ido yayi da sauri dan she's so tempting, yasan dayana school he and Vanessa dated for a very long time, but yanzu ya girma he really wants to change, baya sonta but she's just a girl a d tun yana school ta makale mai dudda ba same course suka karantawa ba, kuma ba same school sukayi ba, lokacin dasuka haduma masters yakeyi ita tana degree dinta a New York film academy, another thing dayasa yake kara kulata is because bata kula any guy bandashi dan yanada mugun kishi, yarinyar na sonshi sosai bana wasaba, they had sex couple of time dan akwai wasu abubuwa datake mai da koyaya yaso karyayi saiyayi but yanzu he really wants to change, yasan a Islam abin is a sin haramun ne saisa yaketa son yay aure but baitaba ganin wacce yakeso ba, wacce tamai ta kwantamai arai baitaba ganiba, yaje kano sau da dama all his cousins, duk yanmatan garin dayake gani ko sha'awa basu bashi balle yamaji yana sonsu, sai akan Hamida dayaji he loves every single thing akan yarinyar, yaji his whole world is revolving akanta. 


Grabbing dinshi dayaji tayi down there yasa ya saukar dawani irin ajiyan zuciya ya ware Ido ya kalleta, da kyar ya iya yay fighting yanda yakeji dan he so want it shima bana wasaba, hanunta yarike cikin rashin karfi ya girgiza mata kai yace "stop it" fashemai tai da kuka ahankali tace "please Aabid, I want you badly handsome, nakasa saurayi Aabid, nobody can f*ck as good as you, please my love, okay I understand you said  having sex without marriage in your religion is a sin right" tai maganan tana share fuskarta da bayan hannu ta kalleshi, gyadamata kai yayi yana mika mata bargo danta rufe kirjinta dake dancing a face dinshi, karban bargon tayi tarike tareda hanunshi tace "okay let's get married handsome" lumshe ido yayi ya girgiza mata kai yace "I cannot get married to you" da sauri tace "why?" bude idanunshi yayi ya kalleta ahankali yace "because I don't have feelings for you" fashemai tayi da kuka tafada jikinshi tana girgiza mai kai tace "please love dont say that kaji My Aabid, am begging you" zaiyi magana wayarshi tai kara alamun shigowan message ahankali yamika hannu yadau wayar da sauri yabude sakon ganin daga Abie ne, yana gama karantawa ya ijiye wayan wani irin murmushi yayi yace "Kano!" tashi yayi daga kan gadon, drawer gefen gadon yajawo, bundle din kudi yaciro nayan dubu daidai guda biyar ya ijiye mata yana kallon yanda take goge idanunta da hannu yace "get ready and leave, am going to my grandparents house, my parents are coming to Nigeria tomorrow, take care okay will call you" juyawa yayi ya shiga bayi tabi bayanshi da kallo kafin ta kalli kudin daya ajiyemata tafashe da wani kukan sanan ta tashi ta kwashi kudin ta wuce tafita ta shiga next room ta shirya tsaf tsabagen yanda takeji haushin shi ko jiranshi tamai bye batayiba tadau jakanta tafita tana kumbura kumbure.


Yana fitowa shafe shafenshi yayi yana murmushi, yasan halin kakan shi hakan yasa ya shirya cikin wani white soft yard da akamai dinki jumper, bakaramin kyau kayan sukamai ba, kallon wardrobe din yayi yana kallon kayanshi he's so lazy, baida karfin dazai wani hada kayanshi a akwati banda hakama yanada kaya achan kano, hakan yasa yaje gaban madubi turaruruka ya fesa yana kallon kanshi a gaban mirror yanda farin kayan yawani irin haska shi ya shiga kayan dam yay wani irin shegen kyau, ahankali yana murmushi yace "am coming Jewel saina nemoki koma a ina kike agarin kano, ur husband is coming Mrs Aabid" murmushi yasakeyi ya zira takalmin shi na Gucci yadau wrist watch dinshi ya daura, wayarshi ya dauka yafita daga dakin yafara sauka kasa yana danna waya yana order Uber, ya sauka kasa yana wani irin kamshi dukya cika gidan da kamshin turaren shi, kitchen ya shiga yahada coffee a mug yafito zama yayi kan kujera yanashan coffee kafin Uber yazo yana cikin sha mai Uber yazo, tashi yayi yaje ya ijiye mug din a kitchen yafito ya kulle gidan, mai gadin yabama key yamai sallama tareda mai kyauta sanan yawuce yafita gate ya shiga motar Uber yajashi har airport yana zuwa yay komi Azman airline zaibi to Kano, ya karbi boarding pass dinshi yawuce upstairs ya shiga departure lounge bai wani dadeba akai announcing boarding dinsu, tashi yayi yawuce yaje yay boarding jirginsu yadaga, 1: 25 jirgin su ya sauka a Airport din kano, wani irin murmushi yayi yafito yana kallon ko ina rabonshi da kano almost a year kenan, yasan inda yafadama grandpa yana hanya da yanzu airport dinan yacika da motoci anzo daukan shi, he's so eager yaga Aadil gobe, karasawa yayi yashiga taxi yacema mai taxi din "New GRA zaka kaini".

_🌹IN BANI 🌹_ 



Maman Abd Shakur



13....


_This novel is for sale karki karanta in baki biyaba_


_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_

_you can also send MTN card ta watsapp number na sainai adding dinki a group din danake posting_






Agaban wani babban gida yasa akai parking, gidan babban gaske ne dan yay girman wani anguwan, fitowa yayi daga mota yabama mai taxi kudi, masu gadin gidan dake sanye da kayan security ne suna ganinshi suka washe baki. "laaaa jikokin Alhaji ne, barka da zuwa oga" murmushi yamusu ya gyadamusu kai dan baijin yin magana suka budemai gate ya shiga, babban gidane dakeda fadi sosai gawani hadadden water treatment plant a tsakiyan compound din dayay kaman round about ta gefe kuma wajejen parking cars ne inda cars sunfi kala goma apake awurin, gawasu irin hadaddun design din flower dayabi ko ina na tsakar gidan babu kowa atsakar gidan kasancewa babu kananun yara a gidan inbadai jikoki sun zo kokuma anyi hutun school shine zakaga yara cike a gidan, da saurin shi yakarasa shiga ciki yay shashin kakanshi bude kofan part dinshi yayi babban falone dayasha hadaddun manyan kujeru sai carpet mai bala'in kyau da taushi dake shimfide akasa, wani tsohone azaune yasha manyan kaya dadan rawani akanshi idanunshi sanye da glasses nakara karfin ido, yana zaune akan wata lumstatsiyan kujera hanunshi rike da jarida yana dubawa gefen kujeran dayake zaune kuma yar sanda ce ajingine awajen wanda daga gani kasa ita ke taimakamai ya tsaya yay tafiya, manyan mazane guda uku a falon zaune akasa wanda suke yaranshi Uncle Suleman, Uncle Muhammad, sai last namijin shi Uncle Mustapha, sai mace guda daya wacce take yayar Mami tana sanye da hadadun kayan kamansu daya da Mami mai suna Asma'u, sunfi kiranta da Big Mum, itama tana zaune a falon suna hira suna shan slice fruits dake wadace agaban su, ahankali yay sallama ya shiga falon yana dan sosa keya dan yasan shima laifine, dukansu dagokai sukayi suna kallonshi cikeda mamaki Uncle Suleman wanda yake babban yayan su yace "kaga daman zuwa yanzu Hussain aika kyauta" kaman zaiyi kuka yakaraso cikin dakin yace "sorry Uncle" cikeda masifa Uncle Muhammad yace "bazaai sorry ba, shine baka fada ka shigo hanya ba kadauko taxi daga Airport kataho wat if something happen akai kidnapping dinka ahanya eh?" sake dan turo baki yayi yana kallon Baffan daya janye jaridan daga fuskarshi yana kallonshi yanamai wani irin calm love look irin na kakanni da jikoki, a sanyaye yay murmushi yanadan sosa keya ya ware hanunshi yatafi wajen tsohon. "oyoyo Grandfather oyoyo Oldman dina" karasawa yayi zai rungumeshi tsohon yadau sandar gefenshi yana nunashi dashi cikeda masifa yace "ka zonan kaga yanda zan kwaleka da sandar nan" da sauri yakoma baya ya zauna kusa da Anty Asma'u dasuke kira da big Mum kaman zaiyi kuka yace "Big Mum kinga grandfather zai bugamin wanchan ugly sandan nashi ko" dariya duka yaran sukayi tsohon yanunamai sandar cikin jin haushinshi yace "kana Nigeria kusan sati biyu saiyau zakazo dan baka da mutunci bakasam mahimmmancin yan uwanka bako, kullum da tunanin ku nake kwana nake tashi aika kyau" kallon Uncles dinshi yayi dake kallonshi cike da so yace "Uncles am sorry kunji, Big Mum am sorry wani assignment fa nazo yi dama nace saina gama zanzo, kema kinsan bazan iya zuwa Nigeria banzo wajenki ba, please Uncles kucema grandfather am sorry" duk dariya sukayi gabadayan su, Big Mum ta shafa kanshi tana kallon mahaifin nata tace "amai afuwa Baba bazai karaba" baban yayansu Suleman yace "Baba amai afuwa ai gashinan yazo, muma madan huta da maganan yan biyun ka dakake ta mana" kallonshi tsohon yayi yanajin wani irin sonshi aranshi tun yana saurayi yaso yan biyu yakeson yan biyu amma Allah baitaba bashi ba sai akan jikokin shi akuma kansu saisa yake mugun sonsu, ahankali yamai alamu da hannu. "yaka" da sauri yatashi yaje yana murmushi rungumeshi yayi ahankali yana dariya yace "My old grandfather kajika fadafa duk randa kabugamin sandar nan ai shikenan sai mutuwa" da sauri yadan zaro mai ido yace "kul denamini maganan mutuwa, sainaga yaranka, naga yaran Hassan dinka ma in sha Allah" dariya duka yan dakin sukayi, murmushi shima tsohon yayi ya nunamai gefenshi yace "zauna anan" ya kalli Asma'u yace "Asama akira masu aiki su kawomai abinci, kice suzo sufarajin meyake so tukunna abinda yakeso shi za'a dafa" da sauri tace "to Baba bari na turosu"  tashi tayi tafita, ya kalli Suleman babban danshi yace "Sulemanu akiramin duka jikokina duk suzo gida ayi liyafa na kwana uku tunda Hassan da iyayensu gobe zasu shigo suma" murmushi duk sukayi sukace to Baba, yasake kallon Aabid din dake kallonshi kaman zai cinyeshi dan dudda tsufanshi badai kyauba yace "kaikuma tunanin me kake" shafa kanshi yayi ya kwanta akan kujeran yadaura kanshi kan cinyar Baffan yace "nothing old man" gashin kanshi ya shafa yace "wanan karan bazaka bar garin nanba saida mata namaka alkwari kodai kafito da ita kokuma na nema maka dakaina" sosai gabanshi yaji yawani irin fadi hakan yasa yadan lumshe ido yakai hanunshi yadaura kan kirjin yana ganin Hamida a idanunshi. Hanunshi Baffa daya gani akan kirji yakama yana kallon yar karaman yatsarshi yanda yabar kunba a yatsar yace "kumban nan fa Hussaini zama cikin yaran yahudawa ne yasa zaka fara abu kaman su" dan murmushi yayi yace "ina jirane fa jumma'a nayi na yanke ta" daga kanshi yayi daga kan cinyarshi dan ya tsani ganin mutum da doguwan kumba yace "tashi ka daukomin kayan yanke kumba adakina kazo nan na yanke maka ita" tashi yayi yana dariya dan grandfather is just d best ne, he's so caring akansu, ga masifa, ga kirki ga korafi ga naci shidai Baffa babu abinda bai hadaba. Dakinshi ya shiga da komi yake a gyare dakin sai kamshi yake yadauko abin yanke kumban yafito yadawo kusa dashi a shagwabe ya zauna kaman wani yaro yabashi yace "please Grandfather karka ciremin kaji" hararanshi yayi yakama hanunshi yana gyara glasses din idanunshi yashiga yanke mai kumban tass har sauran da basukai wanan fitowa ba saida ya yanke, daidai lokacin masu aiki sun shigo dakin sanye da uniform cikeda girmamawa suka gaishe shi suka tambayi mezasu dafamai ahankali yace "just something light" dan bama yunwa yakeji ba yasan idan yace yakoshi ne bala'i zasuyi da Baffa dan dole saiya sashi aci wani abu zaima iya yabashi da kanshi.

Haka ranan yawuni da grandfather banda masallaci babu inda yabari yafita yaje dudda yaso yabi bigmum yaje gidanta hanawa grandfather yayi, koda daddare kin bari yaje part dinshi yayi yace anan part dinshi zai kwana wani hadadden daki dake kusa da nashi ya shiga yana kumbure kumbure hakanan yay bacci awurin. 





Biyar saura daidai yafito daga dakinshi yana bugan kamshi yasa kananun kaya, Baffa yasamu zaune akan dadduma a falon yana jan charba, komawa daki yayi yadauko daya daga cikin tulin keys din motar Baffa yafito yadawo falon yazo inda yake yace "am going Oldman" shafa addu'a yayi ya kalleshi yace "kaje da driver karka tafi har airport da asuban nan kai kadai, bari ma tsaya nakira Sulemanu da Muhammad subika" kwankwaso yarike yace "waini yarone Baffa, ni gaskiya bawanda zaka kira, airport dinne ban saniba ko banda karfin kare kainane" yanda yake maganan cikin jin haushi yasa Baffa cikeda lallashi yace "a'a maida wukar, idan wani abu yasaman min ku mutuwa fa zanyi, naji kaje to amma kai tuki ahankali kaji, kadanje da driban kaji yaron kirki" to yace yafita daga dakin da sauri dan he's so eager yaga dan uwanshi, wajen motoci yayi yashiga motar yay warming sanan yay horn aka budemai gate yaja motar yafita daga gidan, minti kusan 20 ya dauke shi yakai airport din ya tsaya agaban arrivals yana jiran yaga fitowa su yana duba wristwatch din hanunshi no rolex.

Kaman daga sama yahango Mami cikin shiga ta alfarma tasa doguwan riga irinta larabawa tana rike da handbag sai Abie dake rike da hanun Aadil dake tafiya ahankali idanunshi sunyi jajir sun kumbura alamun yaci kuka yakoshi acikin jirgi gefensu kuma wani mutumi ne dake tayasu tura laugage dinsu a cart da sauri ya juya ya boye dan bayaso su ganshi, bayan motoci yadinga bi harya kai karshe sanan yaje ya kutsa ta cikin mutane ya zagayo ta bayansu suna cikin tafiya yazo ta daidai saitin Aadil dake tsakiyan su yasa hanunshi yarufema Aadil ido tabaya, ihu Aadil yayi yana turo baki dan dama acike yake daga Mami har Abie da sauri suka juya suka wanda yarufema dansu ido, ganin Aabid ne yasa duk sukayi murmushi duk sukai shiru. Cikeda masifa dakuma shagwaba Aadil yay ihu yana buga kafa akasa yace "open my eyes, leave me eyes alone" yay maganan ya daura hanunshi akan hanun Aabid din yanaja ihu yasakeyi yace "Mami My eyes" da karfi ya fizge hanun ya juyo cikeda fushi dan yaga waye ya kullemai ido Aabid yay wani irin ihu cike da tsantsan murna ya rungumeshi yace "oyoyo you this fight fight yaro" cikin wani irin murna Aadil yasakeshi yana murmushi dake lobar da two sided dimple dinshi yana ware manyan fine lulu eyes dinshi yace "Bid" wani irin tsalle yayi kaman yaro karami kanshi na rawa sosai yanajan riganshi yace "Bid, Bid, Bid, Aa...Bid" shima tsalle Aabid din yayi cikin tsananin farin ciki da mugun son dan uwanshi yanajan white long sleeve high neck Givenchy shirt da Mami tabashi yasa sabida sanyin jirgi yace "yes..yes, my one and only twin Bro, rascal, yes is me, hug me" cikin wani irin bala'in murna da rabon shi da irin murna haka tun Aabid nanan yawani irin fada jikinshi ya kankameshi sosai yana gogamai fuskanshi awuya yana murmushi sosai yana tsalle da kafa, rungumeshi back Aabid yayi yana shafamai baya Mami data gaji da tsayuwa ta ballamai harara tace "tunda bakuda ranan gama oyoyo oyoyon Abie mutafi mudai sa samemu a parking lot" da sauri Aabid yasakeshi yana dariya handkerchief dinshi yaciro daga aljihu yakai fuskarshi yana sharemai fuska da wuya yace "su Mami are jealous banyi hugging dinsu ba saikai My Dil" washemai baki Aadil yayi yana kallonshi, gama gogemai yayi shima ya goge wuyan nashi sanan yarike mai hannu yace "let's go kaga grandfather, kagaji ko" gyadamai kai yayi batare dayay magana ba dan sosai yaji yawani irin gaji gabanshi sai faduwa yake, hanunshi yakama sukai wajen Mami da Abie dake hiransu saida yafara bude motar yakai Aadil gaba ya zaunar dashi sanan yadawo ya saka akwatinan su a bot yarufe yadawo gaba ya shiga yana waigen su Mami da Abie yace "welcome Abie and Mami hope you all had a smooth flight" yakarshe maganan yana kallon Aadil dayay shiru yanata kallon waje, kunna motar yayi yaja saida suka fara tsayawa a wani masallaci sukai sallan asuba sanan suka dawo motar sukaja sai gida, horn yayi aka bude gate din yaja motar ciki gidan su, Yayin Mami ne da bigMum Dakuma Baffa dayafito daga daki rike da sandarshi kashe motar yayi Mami tafita da sauri ta karasa ta rungume yar uwarta Abie ma fita yayi, juyo dakai Aadil yayi ya kalli Aabid yana daddure fuska yace "who are all this people?" dan shiru Aabid yayi yana kallonshi dan wani zubin idan Aadil yay magana kaman wani Boss wani zubin kuma kaga kaman yaro dan shekara 3, ahankali ganin rigima yakeji kaman bashi yagama murna dazuba yace "gidan su Mami da Abie ne anan suka girma, and ko last year big eid ba anan mukayi ba kaman tane?" yatsine fuska yayi yace "take me back to our house I don't like here" hanunshi yakamo da sauri yace "iskancin naka yatashi ne rascal? Okay let's do this look" dan juyo dakai yayi ya kalli Aabid din idanunshi suncika da hawaye sosai suna shirin xubowa, ahankali Aabid yace "how about we just stay here sabida we want to be good children muma su Mami biyayya but kullum kullum am gonna be taking you out kana ganin cool places muna zuwa yawonmu how did you see d idea? Idea yamaka?" shiru yayi kafin ya daura hanunshi akanshi yana yatsine fuska, da sauri Aabid ya matso yataba kan nashi yace "menene ciwo yakema?" gyadamai kai yayi hawaye na xubowa da sauri yace "sorry sorry, tashi muje kaga Baffa sai muje daki kayi wanka kai bacci" fitowa yayi yazagayo ta side dinshi ya budemai kofa, fitowa yayi ahankali yana kallon Baffan su dayagani yana dogara sanda yana karasowa inda suke shima kakan nasu wani irin kallon Aadil din yake wani abu ya tsayamai awuya yaro har yaro amma ba lafiyan kwakwalwa, da sauri Aabid yaja hanunshi kafin kakan nasu yakaraso yace "Dil zokaga old man mai gilas" dariya kakan nasu yayi yadaga sandarshi zai bugama Aabid cike da wasa yadan matsa gefe yana dariyan isgilanci, ahankali ya daga hanunshi yana wani irin kallon Aadil dake kallonshi yana kokarin tunashi ya shafa kumatun shi har zuwa sajenshi yace "Hassan barka da zuwa, menene idanunka sukai ja haka kagaji ko?" gyadamai kai yayi ahankali, murmushi Baffa yayi yace "muje kahuta" ahankali yake tafiya Aabid a gefenshi sukai babban falo inda har ancika ko'ina da abinci, kin gaida kowa Aadil saima kuka daya saki shizai koma gidansu sai lallabashi ake yakiyin shiru, Baffa yacema Aabid yawuce yakaishi dakinsu yay wanka abiyosu da abincin.

_🌹IN BANI 🌹_ 



_This novel is for sale karki karanta in baki biyaba_


_in kinaso novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_

_you can also send MTN card ta watsapp number na sainai adding dinki a group din danake posting_




 _Maman Abd Shakur_



14.....

 

Fadawa yayi kan katon gadon dakin ya rungume filon, ahankali Aabid yamaida kofar yana kallonshi dan idan lafiya yake yanda yaganshi dinan murna zaitayi yana tsalle yanajin dadi, takawa yayi yakarasa gaban gadon ya tsugunna yana shafa gashin kanshi ahankali ya juyo da kanshi ya kalli Aabid dake kallonshi  idanunshi sun cika da kwalla sosai hakanan yaji baida sukuni gabanshi na faduwa sosai, ahankali Aabid yace "menene, are you sick Aadil talk to me" fashewa yayi da kuka again yatashi yafada jikin Aabid din, gyara zama Aabid yay a kasan shima ya rungumeshi back yanajin wani irin kunci sabida yanda dukyay wani suku suku, ahankali yace "shiiiiii, menene tell me meke damunka? your stomach?" girgiza mai kai yayi yarike hanunshi yana kallonshi yana turo baki, handkerchief yakara sawa ya gogemai bakinshi yace "kanka ke ciwo?" girgiza mai kai yayi, ahankali yana kallon idanunshi cikeda damuwa shima kaman zaiyi kuka yace "in kirama Mami to?" makemai kafada yayi yana kuka still, ahankali yace "tome kakeso kanaso kasani kuka ne nima?" gyadamai kai yayi da sauri yana Kuka ahankali, murmushi Aabid yayi ya dungure mai kai yace "zaka fara ko, tashi muje kayi wanka" ahankali murya chan kasa yanadan lumlumshe ido yace "she" da sauri Aabid ya kalleshi yanadan ware ido yace "she?" gyadamai kai yayi yace "uhm she" shiru Aabid yayi yana kallonshi ahankali yashafa kanshi yadanyi murmushi dan no one understands Aadil kaman shi, their emotions are so connected da at time he feels wat Aadil is feeling, ahankali yace "alright tashi muje kayi wanka to" dagashi yayi ahankali yamike tsaye, wani irin faduwa gabanshi yayi hakan yasa yay baya zai fadi da sauri Aabid yarike shi yace "Aadil!" rikeshi yayi gam suka kalli juna da sauri yawani irin dagoshi ya rungumeshi yace "are you okay Aadil? Come" ya kaishi kan gado, zaunar dashi yayi yaciremai hadadden takalmin kafarshi da safa ya ciremai rigan jikinshi ya barshi da singlet daya bayyanar da fadaddan kirjinshi dakeda wasu irin kwantattun gashi, kwantar dashi yayi yace "anjima kayi wanka rest, are you hungry?" girgiza mai kai yayi yana runtse ido da karfi, hanunshi Aabid yarike yana kallon fuskarshi dukya damu, ahankali Aadil yamika dayan hanunshi yakamo dayan hanun Aabid din yashiga wasa dasu yana kirga yatsunshi bakinshi na motsi yana murmushin dake karamai wani irin bala'in kyau shikadai, dan ajiyan zuciya Aabid yayi yacigaba da kallonshi yana kallon yanda yake maganganu chan kasa yana wasa da hannayen yana lumlumshe ido har bacci yay gaba dashi ahaka shiru Aabid yayi yana kallonshi batare daya karbe hanunshi daga nashi ba, bude kofan da akayi yasa yadan waigo Mami ce da big Mum suka shigo, maida kofar sukayi big Mum ta kalli Aabid tace "lafiya dan gidana?" dan ajiyan zuciya yayi yace "I don't know big mum but Mami wat is wrong with Aadil? Baida lafiya ne" zama Mami tayi abakin gadon tana kallonshi tace "lafiyan shi lau oho nidai banmasan yazance ma ba, yanata cemana she she tun jiya fa, wai mukaishi wurin shi, I don't know waye she din" kallon Mami yayi sanan ya kalleshi yanda yake baccin shi a natse ga dogon black eyelash dinshi kaman na mace yace "Mami kunfita dashi daga gidane bayan nai tafiya? Could it be yaga wata ne" da sauri Bigmum tace "dayake so ko Aabid? Hala saisa yake ta damun ku yanaso yaganta" dan murmushi Mami tayi tace "kai Anty tayaya yaro da baida lafiya ace yaga wata yanaso ai is impossible, IQ yarafa Aadil kedashi tayaya ma zaiso wata? Maybe kawai mafarki ne, mafarkin dayayi ne" da sauri Aabid yace "no Mami bahaka bane, look at it like this, yes IQ yara Aadil kedashi and yara tun suna kanana zakiga wasu yaran sunada ability to love, mutane nawa sukayi aure da sun fara soyayya ne tun basusan kansu ba tun suna wasan kasa? Is very possible, inhar Dil was able to connect with me, Mami, Abie, and kome nacemai yayi zaiyi, ya soni yay understanding dina, inhar bananan he will be crying and he feel my absence then I think ya..." da sauri bigmum tace "yafara son wata ba, tunda ai lafiyan shi kalau da baya zazzabi, amma dukya duburce, shi kanshi yarasa gane kan meyakeji, yarasa sukuni, yanata cemutu ku kaishi wurinta, wlh Maryam son wata yake" shiru duk Mami tayi tana kallon su daga ita har Aabid din maganganun suma dariya yabata tadan murmusa tace "boko ce tamuku yawa wlh inba hakaba tayaya Aadil ku kalli fa Aadil, look at Aadil fa me bambancin shi da yaro dan shekara 4-5, saidai ya nunamai iya magana da gane magana, dakuma iya karanta abu, tayaya ma Aadil zaiso wata ne jama'a, dan Allah kubar maganan nan is totally impossible" da sauri Big Mum tace "kajiki fa Maryama wani irin abar magana, so fa dakike gani rahama ce inbaki saniba, sanan so magani ne, kikasan ko ta sanadin sonta ya warke?" dan tabe baki Mami tayi ta buga tagumi tana kallon Aadil din tace "ba irin cutarnan so ke warkarwa ba Anty, so bata warkan da cutan datafi shekara talatin da, inhar asibitocin kasashen duniyar nan basu iya sunsa ya warke ba banjin so yanada wani tasiri ba, am sure hala yaga yarinyar dawani abu dayake so musaimai ne nawasa kokuma wani abun dayake so yananu mana saisa ta tsayamai arai" ahankali Aabid yana kallonshi yace "Mami nidai yanzu yaushe zamu koma na nemomai she din dayake so yagani, am sure he saw her somewhere a UK ne" Mami tace "ai Allah kadai yasan ranan komawan mu Son, Baba yace nemama Aadil maganin gargajiya za'ayi sanan kaikuma aure zakayi kafin kabar garin nan" dan murmushi yayi ya juyar da kanshi ya kalli Aadil, dariya bigmum tayi tace "wanan murmushi haka Aabid daga gani kanada budurwa ko" shiru yayi yana murmushi, Mami ta harareshi tace "miskilin banza kadai fito da ita inba hakaba in Baffa yasamo ma mata baruwana wlh dole ka aura" ta tashi daga kan gadon tace "Yaya mutafi".





*******

 Tana zaune afalonsu suna kallon wani hausa film tareda Zainab da Ihsan da dazu da safe suka dawo daga Lagos, Mama kuma na daki Kaka ta rafka uban sallama daga bakin kofa batare data shigo ba ta kwalama Hamida kira. "Hamida, Hamida ai kinajina kikai shiru ko, oya fito mutafi kulle kofata zanyi na mikar da hakarkari" kaman zatai kuka ta kalli Zainab dake kusa da ita, hararanta Zainab tayi sanan tamata gwalo murya chan kasa gudun jar Kaka taji tace "wuce kitafi dakin Kaka dake warin daddawawiya" tafashe da dariya Ihsan ma natayata tace "Anty Zainab harda warin busashen kubebbewiya" suka kwashe da dariya dukansu Zainab harda sauka daga kan kujera tsabagen dariya Ihsan kuma taboye fuskarta a cinya tana dariya, wasu hawaye ne suka cika mata ido ta tashi, wayar ta dake kan kujeran ta dauka cikin fushi sanan tajuya zata fita daga dakin saikuma ta juyo ta kalli yanda suke mata dariya tadau filon kujera ta jefa musu da sauri Zainab ta chabe filon tana dariya harda hawaye tace "byebye daddawee" wani irin fashewa tai da kuka sosai da sauri Kaka dake bakin kofa tatura kofan ta shigo tana kallonta tace "ga aljana tazo ko takiraki kizo ki kwanta dole kiyi kuka" cikin kuka ta nuna Zainab tace "Kaka sunefa sukemin dariya wai dakinki na warin daddawa" da sauri Kaka ta kalli Zainab dahar lokacin ke dariya takama habanta tana shigowa dakin da kyau tace "rubabbiya haka kikace, dakina ne me warin daddawa?" da gudu Zainab ta tashi tai hanyar corridor dan tasan bakaramin aikin Kaka bane ta durma mata dundu, bin bayanta Kaka tai da kallo tace "aida kin tsaya nagadai ubanki ma anan yake karin safe bai taba cewa dakin uwarshi yana wariba" ta kalli Ihsan data kife kanta a cinya tana dariya tace "kekuma uban me kikeyi kanki akan cinyan ki wari kikeyine kike shinshinawa?" dariya Hamida itama dake kuka tafita daga dakin da sauri tana dariya tai hanyar sasan Kaka da gudu karo taci da mutum hakan yasa tai baya da sauri ganin Ya Faruk ne yadaure fuska kaman bai taba dariya ba yana sanye da da shirt da jeans ya watsa mata harara da sauri ta sunnar da kanta kasa tana wasa da yatsun ta ahankali tace "sorry bangan kaba" dan kallonta yayi na kusan 1min sanan yafara tafiya yazo zai wuce saikuma ya tsaya ta daidai inda take ahankali yace "gobe zakuyi resuming school get ready I will drop u off" gyadamai kai tayi da sauri kirjinta na bugawa da sauri ta wuce ta shiga cikin gidan tabude dakin Kakan ta shiga, dakinta da Kaka ta gyara mata tabude kofa ta shiga dan gadone guda daya sai sip irin normal sip dinan data tayata jera kayanta aciki kwanciya tayi kan gadon tana kallon wayanta dake hanunta rabon data danna wayan tun suna Lagos, gyara kwanciya tayi ta lulluba da bargo ta kunna datan wayan nan yan few messages suka shigo saikuma message na massenger, zaro ido tayi kafin ahankali kaman mai tsoron wani abu ta shiga messenger taga new messege from Aadil Abdullahi, sosai taji gabanta yawani irin fadi takai kusan 2min tana kallon sunan dakuma profile picture account din dayake na rubutu an rubuta Unique ajiki ahankali tai sliding in tabude message din.


 _Hello Anty Hamida_

_Hello Ihsan_

_I want to be your friend too_

_Anty Hamida pls don't beat Ihsan okay, Mami said beating is not gud_

_Me too I don't have friends and my brother said i can be your friends yayy_

_bye Anty Hamidaaaaa_


Murmushi tayi tana kallon chat din ahankali tace "wanan daga gani da kadan zai girmi Ihsan" shiru tayi tana kallon chat din saikuma takara murmushi ta shiga typing.


_I did not beat her, she was just scared_

_take care bye_

Tafita daga messenger ta shiga watsapp ganin batada any message yasa ta sauka ta shiga pinterest tana duba styles and latest arab collection na abayas, messege ne ya shigo da sauri ta sake zaro ido ganin is from Aadil, sosai gabanta yafadi ahankali kaman wata matsoraciya ta danna tabude.


_Anty Hamida where is she?_

_you see Mami and Bid don't want to take me to she, am seeing she anytime I close my eyes_

_I'm sick_

Shiru tayi tana kallon last maganan dan bataga ne da sauran maganun shiba, hakanan taji she felt somehow sabida yanda yace baida lpy, ahankali ta rubuta

_sorry, get well soon_ da sauri ta kashe datan ta kafin takara ganin wani chat din ta kwanta ta ijiye wayan nesa da ita tana kallon wayan maganan sick din ya tsayamata arai sosai ahaka bacci yay awon gaba da ita.


Da asuban farko Kaka ta shigo ta tadata kaman zata mutu da haushi ta shiga bayi ta wanko baki tai alwala tafito tazo tai nawafir sanan ta zauna tafara karatun saida aka kira sallan asuba sanan ta tashi tayi bayan ta idar tai azkarus subhi, ahaka tafara bacci, hararanta Kaka tayi tacigaba da jan katoton charbin hanunta, takwas saura Kaka ta daka mata duka a baya hakan yasa tabude ido da sauri tana kwalalo ido cikin bacci ta kalli Kakan, dakuwa Kaka tamata tace "ba zakije makaranta bane wai? Yi sauri ki shirya nina shirya d'an har wanka nayi, jekiyo wanka kiyi Kari na kaiki da kaina na fadi ma malamin ku abinda kikeyi" zaro ido tayi tana kallonta kafin tace "ni bazaki bini school ba".

_🌹IN BANI 🌹_ 





_Maman Abd Shakur_




15.....



_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba_


_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number 07012181461_


_you can also send MTN card 300 ta watsapp number na 07012181461_



Wuce ta Kaka tayi tai dakinta tace "aikuma sai mugani danko ubanki bai isa yahanani kaiki makarantan nan yauba" tai kwafa ta shige dakinta, tashi tayi ahankali tanaji kaman tai kuka ko kadan bataso taje makarantar nan ta tsani zuwa makarantan, mutanen ajinsu sukai dari da hamsin, batason zuwa, dakinta tawuce ta shiga ta shiga bayi dan Kaka tace takaimata ruwan zafi, sirka ruwan tayi sanan tayo wankan bayan tabata kusan 10min a bayin dukdan kartaje school, saida Kaka tazo ta buga kofan tace "jama'a wai bazata fito daga bayin bane, ke kinsan karfe nawa kuwan? Zainaba fa harta tafi abinta, Ihsan ma ta tafi tata makarantan, ke kina nan bayi kina kwainane, wlh koki fito kona fado cikin bayin nan yanzu kuw..."  bude kofan tayi tafito Kaka ta matsa gefe tana kallonta, turo baki tayi tawani kumbura taje gaban sip tabude sip din kaman zata balle kofan tsabagen masifa Kaka dake tsaye a inda take tana kallonta tace "wlh kika ballamin sip sai ubanki yabiyani atoh" dogon bakin hijabinta taciro da wani doguwan rigan atampa ja ta ijiye tadau mai ta shafa sanan ta dago ta kalli Kakan dake binta da kallo, akule tace "ni kifita zansa kaya" tsaki Kaka taja tafice tana cewa "kidaiyi sauri ga kokon ki nan afalo, shima kokon dan Allah zanbaki" shiryawa tayi cikin doguwan rigan dayay looking so simple yet elegant a jikinta ta zauna kan gadon tana bude eyeliner dinta tadau madubi taja asaman idonta as usual, bakaramin kyau tayiba ta maida ta rufe ta ijiye, lipgloss tasa abaki tafesa dan simple bodyspray dinta da Abba ke siyoma dukansu duk karshen wata body fantasy na vanilla sanan ta maida kayan kwalliyan tadau channel sandals dinta baki ta saka ta daure igiyan takalmin, bakaramin kyau yama yar farar kafarta ba kaman wata kafar jaririya sanan tadawo tadau jakarta da littatafan ta ke ciki ta rataya jakan akafada kanta ba dan kwali gashin ta daya tsufa sosai sai lilo suke tadau hijabinta tarike a hannu tafita daga dakin, falon ta shigo inda Kaka ke zauna a kasa tanacin dumaman tuwonta acikin tukunyan kasa tai hanyar fita daga dakin Kaka tace "dawo nan kici abincin ki mutafi" makemata kafada tayi da sauri Kaka tacire hanunta daga tuwon ta tashi hakan yasa tawani irin kwasa da gudu tafita daga dakin, cin karo tayi da Ya Faruk yana sanye da white jallabiya tai baya luuu zata fadi da sauri ya tarota tafada jikinshi arude daidai lokacin Kaka tafito da sauri ta kalli Kakan ta tashi daga jikinshi takoma bayanshi ta labe jikinta narawa ahankali tace "Ya Faruk please karka bari Kaka takaini school wai lecturer dinmu zata fadamawa ya dakeni" daga bakin kofa Kaka ke kallonsu tace "ina jinki muna fika, haka nace eh sainasa malamin ku ya dakanmin ke bar ganin Farukun soja ubanme zai iyamin" juyawa yayi ya kalleta fuskarshi adan daure yace "put on your hijab" da sauri tasaka hijabin dayay mata kyau sosai yafito da hasken fatarta, hulan hijabin har goshinta yace "let's go" ficewa sukayi Kaka tai kwafa tace "wlh zaku gamu danine dukanku munafukan banza" takoma daki, waje sukayi bahalin tacemai zataje ta gaida Mama da Baba yabi yadaure fuska motarshi yabude ya shiga itama ta shiga dayan side din lokacin kusan karfe tara yaja motar har BUK, sosai gabanta keta faduwa tana kallon ko'ina har gaban department dinta ya kaita na Islamic studies sanan yay parking dan dagokai tayi ta kalleshi suka hada ido, ahankali tace "thank you" 3k yaciro daga wallet dinshi yabata yana kallonta yace "make sure you eat" gyadamai kai tayi ta karbi kudin murmushi tayi tace "thank you" ta bude marfin motan tafita, binta yayi da kallo yanda take tafiya a mugun natse kaman tana tausayin kasa kanta akasa as usual tana kakkare fuskarta da hijabi, hijabin nan har kasa dan ko kayan datasa aciki ba'a hangowa, saida ta kule mai sanan yadan fuzar da iska wayarshi dake ringing ya kalla ganin Ammi ne yasa yadau wayan yakai kunenshi. Daga tachan bangaren cike da masifa matar tace "where are you Son, kacemin you're having headache bazakaje aiki yauba ina kaje this early morning eh Umar Faruk?" shiru yadanyi batare dayace komiba dan ya tsani karya, kuma baya karya, dan ya tsani anamai ihu aka, ahankali yace "sorry Ammi na" cikin fada tace "Faruk kullum kullum saika nunamin ban isa dakai bako son? Am sure kaje gidan wan Baban kane, am sure kaje kai wanan mai aljanun makaranta ne sabida kai hired driver dinta ne ko, Faruk wats wrong with you? Narabaka dasu kakiji, tun baban ka nada rai wanan mayyar wicked Kakan taka tasa aka sakeni dan haka nafa and am going to say it again, jinina bazai kara hada wani abu da wanan family ba, tun wuri kacire yarinyar nan aranka inba hakaba wlh fushin dazanyi dakai wanan karan saiyafi na wanda nai dakai ranan dakaje Lagos ka daukota stubborn boy, and come back home rightaway Dr na jiranka" tai tsaki ta katse wayan, ahankali ya zare wayan daga kunenshi kirjinshi namai wani irin zafi, he don't know where all this hate is coming from but one thing is for sure yasan idan har abinda Ammi ke fada gaskiya ne, Kaka tasa aka saketa dan Kaka batai laifi ba dan ko kadan Ammi batada kirki yana ganin yanda takema yan aiki wani zubin ma shiyake hanata, yasan mahaifiyarshi sosaisosai. Yakai kusan 5min a wurin yana tunane tunane sanan yaja mota yabar wajen yadau hanyar gidansu.


Faruk yaron kanin mahaifin su Hamida ne, shika dai suka Haifa shikadai ne kuma jikan Kaka namiji, inda Baban su Hamida yahaifi yara bakwai dukansu mata, baban Faruk ya rasu a plane crash ne, his Mum is from a rich wealthy family, bayan rasuwan baban Faruk Faruk yadawo hanun Abba da Kaka, rashin mutunci Ammi tazo tai dasu Kaka akan abata danta, in other to maintain peace yasa Abba yacema Faruk yakoma wurinta but dudda haka kullum yana gidansu, weekend yana yawan zuwa gidan kajin Abba yana tayashi aiki dan sana'ar baban su Hamida kenan saida kaji da Kwai and he's making it Alhamdulillah Allah ya sanya mai albarka a sana'ar.


**

Dan lekowa tayi daga inda ta labe ganin yatafi babu yasa tafito ahankali tana tafiya da sauri da sauri wani kantin taje dayake safiya ne ba mutane sosai, take away abinci merai da lafiya tayi guda biyu tabiya kudi ta karba tafito tafita daga school din gabanta na faduwa sosai, kasa samin Keke tayi hakan yasa tafara tafiya akasa tana kakkare fuskarta, saida tai nisa sosai tamugun gaji da tafiya takai junction din wani layi keke napep ta tare ta shiga tace "old railway" "hajiya dari uku" ahankali kanta akasa tace "muje" tada keke napep  yayi suka shiga hanya, sukayi tafiyan kusan 15 minute yakaisu wurin, ahankali ta sauko taciro dari uku tabashi batare data kalli fuskarshi shi tajuya ta shiga wajen tana kallon kan kujeran da Baba yake zama yanajin yar radio shi ganin bashi yasa ta karasa wajen,  takeaways din ta ijiyemai ta ta wuce ciki hango wasu samari tayi kusan biyar ko shida zaune a inda ta saba zama suna kokarin kunna wiwi da sauri ta juya kafinma su lura da ita, cin karo tai dawani abayanta idanunshi jajir da alamun yasha yai tatil yace "ke waya kiraki nan?" kwalama sauran dabama su lura da ita kira yayi yace "babaa jimana, tawaye ne tazo? Ba munce babu wacce zai kira tashi nanba yau" da sauri amugun rude tai gefenshi zata wuce yatareta yace "ki tsaya mana baby nakira miki su, hala wajen Sani kikazo dan nasan mayen da shegen iya zabo zafafan mata" arude tana dan waigen bayanta jin sahun mutane suna zuwa ta kwalama tsohon dake gadin wajen kira. "Baba, Baba" daidai lokacin sauran sun iso wajen fashewa sukai da dariya dayan yace "Baba wai me gadi kike kira? Ke yarshi ce?" daya daga cikin su yace "kaima jibeka dawata magana ina Baba mai gadi yakeda kyan haifan irin wanan lu'u lu'un?" daya daga cikinsu yace "kodai me zuwa bashi kayane?" kulle bakinsu sukayi suna zaro ido irin na isgilanci atare sukace "tsoho yaji chakwai" fashewa tai da kuka ta duka a tsakiyan su tana kwalama Baba kira. "Babaa" daya daga cikinsu yace "ankai Baba kauyen su Baba ba lafiya muma fanshi Baba yau, kingan mu mushida kici har ki koshi ko yan mata" yay maganan zai kama mata hannu boye hanunta tayi ajikinta tafashe da kuka, hijabinta ya fizgo ya mikar da ita tsaye fasa wani irin ihu tayi a mugun tsorace ta bugamai kafarta hakan yasa yay baya yasaketa yana tsaki dan yaji zafi da sauri sauran sukayo kanta tawani irin kwasa da gudu tana kuka wanda ta hambaran yawani irin tadiyota tafadi akasa hancinta ya shiga cikin dan kasan yashin dake wurin.

_🌹IN BANI 🌹_ 





Maman Abd Shakur



16....




_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba_


_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_


_you can also send MTN card 300 ta watsapp number na 07012181461_






Kafafunta yajawo tafasa ihu sosai tana kuka ta dibi kasan wajen da hannuwanta biyu ta juyo da kanta cikin kuka, watsa musu kasan tayi a idanu hakan yasa ya saketa da sauri yay ihu shida sauran suna sosa ido suna kokarin budewa sun kasa, dawani irin sauri ta tashi tadau jakanta taruga aguje suka biyota, fitowa tayi tana gudu sosai tana kuka, black hijabin ta gabaki daya ya baci da kasa tana gudu suna binta.... 



Anatse Mami ke tuki taci gayu sosai tasa wani hadadden exclusive atampa brown da yellow dayay mata kyau tayafa wani babban mayafi brown tana tuki, gefenta kuma Aadil ne yana zaune agaba yana wasa da fingers dinshi yana counting dinsu one, two, three, yana sanye cikin wani Fendi white t-shirt daya kama jikinshi sosai, hanun rigan are dark brown, yana sanye da dogon brown pant yasanya white sneaker na Fendi, wrist dinshi daure da agogo na rolex gashin kanshi a kwance yana kara bubbude manyan idanunshi yana magana kasa kasa yana counting yatsunshi sai wani hadadden kamshi dake tashi ajikinshi, murmushi Mami tayi tadan kalleshi ta maida hankalinta kan tukin datake yi tana tunani Aadil kenan, Ball fa suke bugawa a compound shida Aabid Baffa kuma na zaune acikin bukkan dake compound din yana kallonsu yana murmushi, yana ganin Mami tafito rike da car key gidan BigMum zata yafashe da kuka ya yarda kallon zai bita shine ta taho dashi.

Ahankali takira sunanshi. "Son" dan juyowa yayi ya kalleta da manya manyan idanunshi yadan daga cikakken gyararren giranshi sama kaman na tamace yana kallonta, itama dan kallonshi tayi ta maida hankalinta kan tuki tace "wat are you counting Son" turo mata baki yayi kafin ya maida kanshi kan hanya yana lankwasa kan yana cizan wet lips dinshi batare dayace mata komiba yafara counting motocin gabansu. Dawani irin mugun gudu Hamida tafado kan titin tana waigen baya saura kiris Mami ta bigeta ta gitta, dan batakai ga taka birki ba ta buga salati. "subhannallahi wanan lafiyanta kuwa" wani irin ganin gittawan ta yayi kaman flash of light, dasauri yakara ware ido yabi bayanta da kallo harta karasa tsallake titin da gudu tana waigen baya tana kuka tana share fuskarta da hijabi dan gani tayi kaman suna binta, da sauri cikin wani irin rudewa kirjinshi nawani irin bugawa kaman zai tsage yasaki lips dinshi daya rike da hakori tun dazu dayake wasa yana waigenta ta baya dan sunriga sun mata dan nisa, arude yay pointing saitin Hamida yana kyafkyfata ido kaman mai stammering yace "s...s...she Mami" wani irin juyawa yayi batare daya damu tafiya suke akan titi ba ya tuge sitbelt din jikinshi yawani irin bude kofan motan iska yaja kofan, kofan ya bude gaba daya ya daki wani mai machine dake tafiya, salati Mami tayi arude dan bama ta lura dazai bude motar ba saida taji wani irin iska, kafin kyaftawan ido yafita daga motan kanshi na rawa sosai yawani irin fadi akasa sosai dan da wuya in baiji ciwo ba, ihu Mami tayi tawani irin taka brake din motarta duka tana kallonshi kar wani abin hawa ko babban mota yatakeshi before you know it motar dake bayan Mami dat was on speed tazo da gudu ta bugi boot din motan Mami danta taka burki ne unexpectedly ta tsaya, motar Mami tai gaba kan Mami dayake ta lekone tana kallon Aadil arude kanta yawani irin bugu da starring, cikin ikon Allah mota bata bugeshi ba, da sauri batare daya lura da Mami bama yatashi yana waige waige kanshi na rawa sosai yana yarfe hannu danya bugu sosai akafa baima damu da mutanen dake salati ba ana kallonshi ana kallon mai machine dayay hatsari da two cars ya shiga gudu yana hango Hamida datamai nisa sosai yana yarfa hannu yafashe da kuka yace "she noo, don't go" yacigaba da gudu, gajiya yayi sosai kaman zai suma yafashe da kuka yana kallon titin dan baitaba gudu hakaba a rayuwan shiba, wani mai machine ne dayazo wucewa ya tsaya yana kallonshi cikeda mamaki yace "malam amma mutuwa ne kake kuka haka miyau na zuba" cikin kuka sosai yamai pointing Hamida dake shirin yin kwana tai nisa sosai yace "she" kallon inda yake nunamai yayi sanan ya kalleshi ganin yanda yake kaman mara lafiya sanan wanda yake nunamai itama gudu take yasa yakawo aranshi halama mai gudun shi take nema itama, tausayi yabashi hakan yasa yace "hauna kaikah wurinta to" tsayawa yayi yana kallon machine din yana kuka hannu mai machine din yamika mai da sauri yarike shi ya dafa shi sanan ya iya hawa kan machine din, mai machine din ya kunna yaja machine din, rikeshi yayi a tsorace yana kuka, adaidai bakin layin lokacin harta shiga layin mai machine din ya tsaya yace "sauko ka bita bazan shiga layin nanba, machine dinan daga wajen wanki na karbota yanzu haka, layin nan duk chabalbali" lekoshi yayi da kai yana kallon fuskanshi dan baicika gane manyan hausaba, ahankali mai machine din yace "come down" saukowa yayi yana kallonta yana kuka da karfi ya kwala mata kira. "sheeee" arude Hamida dake gudu har lokacin tana kuka sosai tafada wani uncompleted building ta tsugunna tana kuka sosai tana addu'a Allah yasa basu ganta ba, tabude jakanta arude ta shiga neman wayanta tanaso takira Ya Faruk amma bataga wayanba hala tafadi awurin, tafashe da wani sabon kuka tana kare fuskarta ta hijabi ta.


Da gudu yay cikin layin clean white sneaker dinshi na shiga cikin chabali, bai damuba burunshi yakai gidan data shiga yaganta, wani irin mugun faduwa yayi cikin ruwan chabalin white rigan shi da wandonshi suka baci sosai, tashi yayi ahankali yana kuka sosai yana kallon hanunshi da jikinshi danko kadan ya tsani datti yacigaba da gudu yakai gaban gidan, da gudu shima ya shiga haryana neman faduwa sabida block dake wajen ya buge kafanshi ya kwala mata kira yana kalle kalle. "shee" amugun tsorace Hamida ta dagokai ta mike tsaye da mugun sauri tana kuka tana komawa baya, tsabagen yanda tai gudu tana haki, ga heart dinta dake beating way to fast yasa har dishi dishi take gani, zaro idanun dabata gani sosai tayi ta kalleshi kaman yanda yake kuka sosai yake wani irin kallonta cikin wani irin low and calm voice yace "uhmm is me" yay maganan yana takowa gabanta kanshi na rawa yanadan dingishi danya buge kafanshi sosai, zaro ido Hamida tayi tana komawa da baya tana ganin dishi dishi tana ganin mutum na tahowa amma bata ganin fuskarshi da kyau tsabagen dishi dishin dayake gani, ahankali take komawa baya yana tafiya ahankali shima yana goge kukan dayake yi yakeyi yana tafiya ahankali yana kallonta yana biyota hartakai jikin bango ta tsaya, karasawa yayi shima har inda take yana breathing fast sosai yana wani irin kallonta numfashin duka na sauka akan fuskarta, wani irin kallonshi take da idanunta that went completely blind tsabagen yanda zuciyata ke bugu shima kallonta yake zuciyarshi nawani irin bugawan da tunda yake baitaba jin yamai irin bugun ba, wani irin nishi yayi yana kara matso ta har kafafunshi na gogan nata, dawata irin murya chan kasa yar karama chan ciki yasakin mata wani irin kuka dako su Aabid baitaba sakin musu irinshi ba yabude hannayenshi ahankali yafada jikinta yana kuka yay cuddling nata so tight not knowing what exactly yakeyi and yake feeling but he just wanna cuddle and cuddle and cuddle her, dip wuta ya daukemata tai wani irin passing out instantly kafafunta suka lankwashe zatai kasa, ahankali yadaga kanshi daga wuyanta yana kuka sosai yana kallonta dukya jika mata wuyan hijabi da hawaye da miyau, binta yay da kallo ta yanda arms dinshi ne are d only things dake rike da ita danda tuni tazube akasa asume, jijjigata yayi ahankali ya fashe da kuka kaman karamin yaro yace "wake up, are you sleeping?".

_🌹IN BANI 🌹_ 




_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan_



_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_


_you can also send MTN card 300 ta watsapp number na sainai adding a group din danake posting_




Maman Abd Shakur



17....


Goga fuskarshi yayi anata yana kuka sosai yace "wake up pls" yay maganan yana turo baki cikin kuka yana kallonta ganin shiru yasa ahankali ya kwantar da ita a kasan wajen, kwanciya yayi shima gefenta yana kallonta shi kanshi baisan meke damubshi ba, fashewa yasakeyi da kuka yarike hanunta dan wani iri heart dinshi kemai, he's feeling something all over his body, stomach dinshi kaman an watsa ice a ciki sabida wani irin sanyin dayake mai dayake kaiwa kowani nerve najikinshi, ahankali ya daura kanshi a wuyanta yana kuka sosai bana wasaba ahaka shima baccin wahala da ciwo sukai gaba dashi jikinshi yadau wani irin zafi sabida ciwukan dayaji a kafa gakuma zazzabi.



Ahankali Mami ke bude ido, dishi dishi take gani sosai maganar bigmum taji dakuma matse hanunta da akayi. "Maryam kin tashi" dan juyo dakai tayi da kyar ta kalli gefenta Big Mum tagani zaune akan kujera idanunta sunyi ja sosai ta rike hanunta gam, baki Mami tabude zatai magana takasa sabida yanda bakinta yamata wani irin nauyi sai kallon ko ina datake yi dakuma kanta daya mata wani irin nauyi da zafi, shiru tayi tana lumshe ido tana kokarin tunano abinda yafaru. "Maryam" Bigmum tasake kiranta hakan yasa tabude idanunta da kyau tanadan lumlumshe ido sabida yanda kanta ke mata ciwo zatai magana aka bude dakin aka shigo yayyinta Mazane su uku da Abie dakuma Aabid da taga idanunshi sunyi jajir, da sauri Aabid yama rigasu zuwa wajen Mamin, cupping fuskarta yayi kaman zaiyi kuka yace "Mami na ina..ina Aadil?" sunan Aadil daya kira yasa ta lumshe ido da sauri, ahankali komi yafara dawo mata har lokacin daya bude kofar motan yafadi akasan tsakiyan titi, dawani irin sauri tabude ido tai wani irin ihu tana mika hannu kaman zata kamoshi. "Aadilll" arude ta shiga kalle kallen dakin ganin dakin asibiti take babu Aadil a wurin saima ruwa da ake samata fashewa da wani irin kuka tayi numfashin ta na sama sama arude tarike Aabid tace "where's Aadil Aabid? Tell me what happen to Aadil?" da sauri tasaki Aabid tana kallon sauran yan dakin tana nunasa da yatsa tana magana kaman wacce ta zare. "kufadamin gaskiya ina yarona yake? Ina d'ana? Abie where is Aadil eh" da sauri Abie yakaraso wajen Big Mum ma tariketa ahankali yace "calm down wife, calm down, muma bamusan meya sami Aadil ba, wani bawan Allah dai yakira ta wayarki Big Mum ma aka kira dan anga itace last contact din dakikai waya da ita a phone dinki ance you had an accident u were unconcious" "noooo" ta fizge kanta daga jikin big mum tace "karya kuke yimin kufadamin gaskiya mota ya takeshi ko? Aadil dina yamutu?" kaman wacce tasami tabin brain ta kalli yatsunta kaman yanda Aadil keyi tafara kirgawa cikin sambatu tace "Aadil was counting his fingers playing while I was driving, all of a sudden ya cire sitbelt yabude kofan mota yafice, yabuge yafadi sosai a kasa, matching brake nayi arude na kalleshi daganan bansan meya faruba, tell me!" tai wani irin ihu tana kama rigan Abie dake kanta tace "Abie meya sami d'ana wlh inkamin karya zanyi fushi da dukanku kafadamin" alamu yama Aabid dake zaune yana kallon Mami yamatsa, zama yayi ya bata one side hug yadan jijjigata yace "in sha Allah nothing will happen to Aadil, zamu nemeshi zamu bada cigiyarshi, and we will get d police involve inma d accident was a well careful plan accident dan ayi kidnapping nashi we will know, calm down okay karwani ciwon yakama ki, I swear, I swear to you zan nemo mana danmu" cikin wani irin kuka mara kara tace "promise me Abie u will find my Aadil for me" shima idanunshi sunyi jajir jijiyoyin kanshi duksun fito yace "I promise you Mum Aadil" tashi yayi da sauri yay hanyar kofa su Suleman zasu bishi yay murmushi irin na tashin hankali yace "karku damu am coming, in baku ganni dawuri ba get d police involve" da sauri Suleman yace "ina zaka Abdullahi?" Juyawa kawai yayi yana kokarin hana kanshi hawayen dazasu zobomai yace "ina zuwa kawai Yaya" ficewa yayi da sauri Mami ta fashe da kuka tai hugging Aabid tace "Son where is your brother? Idan ban ganshi ba mutuwa zanyi wlh, you and Aadil are my entire life, please So.." tafashe da kuka sosai, ahankali yadago kanta daga jikinshi yasa hannu ya share mata hawayen, da muryanshi data dishe sosai yace "stop crying Mami, I will find my Bro okay" gyadamai kai tayi tana kuka, Big Mum ta kwantar da ita tace "kwanta ki huta ruwan ya shiga jikin ki da kyau" tashi Aabid yayi yafita shida Yayin mamanshi.




Sosai Abie ke zuba wani irin uban gudu akan hanya, bini bini yake share yan hawayen dake zubomai, sosai yay tafiya kaman zaibar garin kano sanan ya yanki cikin wata yar karamin kauye yadinga kutsawa cikin kauyen nan da jeep dinshi haryakai wani babban farm house, a kofar gidan yay parking yafito rike dawata yar jaka yarufe motar, yaciro wasu key yabude gate din ya shiga, gidan ciyayi sunma soma girma kota ina, ya karasa har gaban wani flat dake compound din ya shiga yar barandan dazai sadashi da daki rike da makullin da wayarshi, ciro key yayi yabude kofan ya shiga ciki, babban falone dayay dan kura da alamu an dade ba'a shiga gidan ba, wani dan corridor yayi hanunshi har rawa yake yabude wani katoton makulli dake makale jikin kofan ya bude sanan ya zare ya ijiye key yabude kofan amugun hankali ya shiga dakin, dakine da komi nacikinshi ja, kaman dajan kyalle aka zagaye bangon dakin, kasanma wani irin jan carpet ne ja sosai a shimfide kota ina, ahankali ya shiga dakin da yay dan kura ya maida kofar ya rufe yasaka sakatan sama data kasa sanan ya shigo ciki ya ijiye jakan daya dauko akasa duk da sauri sauri yake komi ya zage jakan ya bude wasu jajayen kayane suka bayyana da sauri ya kwabe manyan kayan jikinshi ya ijiye kasa sanan yadau jajayen kayan yasaka babban bubun rigane dake jamai har kasa da sauri ya tsugunna ya kwashi kayan daya cire ya maida cikin jakan yaciro ashana daga jakan ya daga jakan ya jinginata da bango yatashi yaje gaban dakin inda wani manyan gumaka suke da aka musu zane a fuska kaman da chalk, kafafunsu daure dawasu irin bangles sai kuma jajayen candles guda shidda suma, kneeling yayi ahankali agaban gumakan sanan ya kyasta ashana ya kunna  duka candles din sanan ya hura tsinken ashanar ta mutu ya yar a gefe, shiru yayi yana tunani yana kallon gumakan kafin ahankali ya dukar da kanshi yahade hannayenshi biyu agaban gumakan yace "Ozo the tittle holder, Ozo the tittle holder, Ozo the tittle holder, macukubelebele kaino kaino, macukubelebele kaino kanooo" shiru yadanyi zuciyarshi namai wani irin azababben zafi, ahankali cikin wani irin dishashiyar murya yace "Ozo ka bayyana agareni inada bukatar ka, I summon you Ozooo" bai karasa kiran sunan ba wasu mutane guda uku suka bayyana a dakin a tsaye da ba'a ganin fuskokin su suna sanye da jajayen dogayen riguna daya rufe har kafarsu sai babban su dake sanye cikin black doguwan riga shima kanshi akasa yana rike dawani karfe dakeda Kwai kaman kwan jimina asaman karfen, cikin wani irin magana mai echo sukace. "mesa kake neman Ozo" kaman jira yake ya rarrafa da gudu yaje gaban me bakaken kayan yay kneeling yana hada hannayenshi yace "great one Ozo, Ozo nakiyaye kowace irin dokan ka, wanan zoben" yanuna babban zoben yatsarshi arude yace "kaman yanda kace bantaba cireta daga yatsata ba, Ozo nasan ni mai laifine tun kafin na shigo kungiya aka fadamin sharuddan kungiya wacce shine d'a namiji dazan fara haihuwa a duniya nakune shine sacrifice dazan...." yay shiru hawaye na zuba daga idanunshi sosai da kyar cikin wani irin asalin tashin hankali yace "great Ozo bantaba sanin haka abin yakeda mugun wuya and tough ba saida na haifo yan biyuna mazaje kyawawa" yadanyi shiru yana goge hawaye sanan yace "great one Ozo da gudu nabarosu a asibiti nadawo gida na shiga boyayyen daki namaka kira ka amsani, ka bayyanan min, naroki afuwa da alfarma akan karku daukemini Hassan wanda yake na farkon, karku kashemin shi, great one Ozo nasan kamin adalcin da baka taba yima wani a kungiyan nan ba, kabani zabi biyu masu sharudda sabida yanda ka tausayamin kakuma Soni, zabin shine ko kukashe shi kusha jini, koku shanye min shi, da ranshi amma shida yaro basuda bambamci, da gudu na yarda tsabagen yanda nakeson Yan biyuna, gakuma wani irin special son Hassan din da Allah ya dauramin danshi nafara dauka a hannuna a tsumma kafin na dauki dan uwanshi Hussain, na yarda da Hassan mutu gwara kunsaka ranshi a kwalban kunyi duk yanda kukaga dama dashi daku kashemin shi na yarda dari bisa dari ku maidashi yaron kusa ranshi a kwalban bakomi, sai kuka fara koromin sharuddan zabin danayi na karya mutu, kace duk wani ciki da Maryama zatayi tun cikin na wata biyar zaku shanye cikin,  haka na yarda cikin da Maryam ke dauka dai, dai, dai, har sau uku Maryama nayi duk kuna shanye wa tana bari duk sabida karku kashemin abin kaunata Hassan ban damuba har mahaifanta ya sami matsala tsabagen wankin ciki da ake mata tadena samin cikin, bayan haka kuka bani sharadin cewa ko bayan shanyayyen dan nawa yay girma bazai sake yay aureba shima na yarda to tayaya ma mara lafiya yaro mai kwakwalwan yara zaiga mace yace yanaso duk na yarda, kun hanani cin naman rago duk banaci, kun hanani cin dabino shan zuma duka banyiba dukdan karku kashemini Hassan, mesa yanzu zaku chanza komi ki daukemin farin cikina eh bayan na kiyaye kowace doka da sharuddan ku eh Ozo the great one?".

_🌹IN BANI🌹_ 




Maman Abd Shakur



18....


_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan_


_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_


_you can also send MTN card 300 ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_


_masu fitarmin da novel waje, please kindly stop_





Sosai Abie yafashe dawani irin kuka ya kife kanshi akasa yana kuka sosai yana hawaye, shi karan kanshi baisan wani irin so yakema Aadil ba, Allah yaga abinda yagani ne ya jarabce shi da mugun son yaron, Aadil nada wani irin shiga rai fiye da tunanin kowa saika zauna dashi zaka gane hakan, son Aadil yake bana wasaba, idan har Ozo ne ya daukeshi hala mutuwa zaiyi dan baijin zai iya rayuwa babu yaronba. "Tursoso!" yaji an kiranshi dan bayan ya jona kungiya sunan da Ozo the great one yasamai kenan, da sauri ya dago kanshi yana goge hawayen daya gama wanke mai fuska idanunshi sunyi ja sosai, cikin wani irin murya dake echo adakin mai bakaken yace "bayan kasan ka kiyaye sharudda, me a tunanin ka zaisa mu daukema d'a? Bama dauka saidai mu tsotsa agabanka, bama dauka saidai mu tsotsa kaman yanda muka tsotse cikin matarka agabanka haka zamu tsotsemai jini agaban ka ya mutu babu jini ko digo a jikinshi" yaydan shiru sai chan cikin wani irin murya mai firgita zuciya yace "babu hanun mu abatan danka saidai zamu gargadeka akan abu daya" yasakeyi yin shiru yace "ba danka ba aure Tursoso, ba danka ba aure Tursoso, ba danka ba aure Tursoso" gyadamai kai yayi hankalinshi yawani irin kwanta kaman an yayemai wata irin bakin tsoka daga kirjinshi yay murmushi yace "nagode, nagode Ozo the great one" wani irin nishi Ozo yayi irin na matsafa yace "shikenan matsalan ka ko akwai wata?" murmushi yayi cikin jin dadi yanda Ozo keji dashi yace "dama Ozo naga jiya yakamata zobena yamin aman kudi, jiya lahadi amma baiyiba, shine nace maisa baimin ba? Ko wata laifin nayi?" dariya Ozo yayi irin dariyan matsafan nan. "ha ha ha hmmm, Tursoso anchanza ranan aman kudin ne, gobe ne zaimaka aman kudin" da sauri yay murmushi yace "to Ozo nagode" batcewa sukayi bat da sauri ya hure candles din duka ya tashi yaje ya chanza kayan ya maida asalin wanda yasa yamabar akwatin a wurin sanan yacire sakatan kofan yabude kofan yafita daga dakin yarufe kofan da katoton key dinshi sanan yawuce yay tsakar gidan yafice ya shiga mota yaja yabar wajen.




***

Kiran sallan magriba dakuma wani irin zafi dataji sosai ajikinta yasa ahankali ta bude ido, da sauri takara bude idon ganin inda take iskan magrib na kadawa gari yadan soma duhu kadan dudda da haske, dan nauyin dataji dakuma hanun mutum dataji akan cikinta an rike mata ciki gam, gakuma wani irin hadadden kamshin turare datakeji yana shiga hancinta yasa ta mugun zabura tadan dago, arude tace "you" dan wlh ta manta sunanshi amma dai ta tuna fuskar mutumin nan daya kaita asibiti ranan datana Lagos tagani yana bacci kanshi awuyanta jikinshi da kafafunshi akasa close to her own danhar gogan juna suke, jikinshi zafi sosai bana wasaba yana numfashi ahankali ahankali datake jin saukarshi harta cikin wuyanta, long gashin idanunshi duksun tattare waje daya tsabagen kukan dayasha, ihu tayi ganin takasa janye kafadarta. "wayyo Allah na" ta ture kanshi daga jikinta kaman zatai kuka, bude idanunshi yayi ahankali cikin bacci dasukai ja sosai sabida zazzabi ya daurasu akanta kirjinshi nawani irin bugawa da sauri da sauri, zaro idanun tayi danji tayi idanunshi sunmata wani iri ajiki da sauri ta ture kanshi daga kafadarta ta matsa baya da sauri tamakale a jikin bango, saura kadan kanshi dake rawa sosai ya buga kasa yatashi ya zauna zuciyarshi namai wani iri sosai yana kallonta ko kyafta ido bayayi, ahankali kaman dan yaro yace "you are awake" samin kanta tayi da gyadamai kai  gabanta na faduwa sosai dan yanda yay maganan saida tajishi har kasan zuciyarta, kallonshi takeyi kaman yanda shima kemata wani irin calm cool look da lumstatsun idanunshi, ganin yanda yake yine kanshi narawa sosai kirjinta na bugawa sosai fiyeda na ranan farko ma data fara ganinshi tace "how did you follow me here?" wani irin kallonta yayi da shanyayyun eyes dinshi dayake budesu sosai, da sauri ta kawad da kanta tana murza hanunta danji tayi she's so nervous, ahankali dawata irin murya chan kasa kaman ba na normal Aadil ba yace "am hungry" da sauri ta kalleshi danjin maganan tayi har zuciyarta, tashi tayi da sauri dan wani irin tsoronshi ne taji ya dirar mata arai da sauri tazo zata wuce shi hakan yasa yasaki kuka sosai yana binta da kallo yarike mata hijabi miyau na zuba daga bakinshi yana cizan lips dinshi dat were looking so pinkish and tender, adan tsorace ta kalleshi ganin yanda yake kuka yana kallon fuskarta kaman zai cinyeta yana taune lips dinshi yana girgiza mata kai alamun karta tafi yasa ta sake kawad dakai cike da mamaki aranta, meya sameshi? Ya akayi ya zama haka? ganin yanda yacigaba da kukan yana goge fuskarshi akafarta yasa tadan juyo ta kalleshi shima ita yake kallo, Ahankali yasa bayan hannu yana goge idanunshi dasukai jajir sundan kumbura ga rigar jikinshi da wandon duksun baci da chabali dahar ya bushe, sake dagowa yayi ya kalleta yana kara rike kafarta hawaye yasake gangarowa daga idanunshi sosai taji zuciyarta yay wani iri dan tsugunnawa tayi agabanshi zatai magana yafada jikinta da sauri ya kankameta yana kuka ahankali babu abinda bayamai ciwo, kanshi ciwo, kafafunshi ciwo, hanunshi ciwo, ga zuciyarshi bayajinta kaman yanda normally yake jinta, yanda yafada jikinta yasa batasan lokacin data zauna dabas a kasan wurin ba ko'ina na jikinta na rawa, fashewa yayi da kuka sosai a wuyanta ya kulle hanunshi abayanta kaman yanda yake rungume Mami, kokarin tura shi take amma takasa ga jikinshi zafi sosai kaman wuta, adan rude tace "to ka sakeni kaga" makemata kafada yayi batare daya gane metake cemai ba, cikin wani irin kuka yace "u want to run and leave me again, that's how you use to do even in my dreams u will come but once I raised d curtain you will run and ask me to find u, I've found you now and I will never let you go" Wani irin tsorone ya shiga jikinta yanda babban namiji yabi ya rungumeta haka ahankali muryanta na rawa sosai tace "please ka sakeni" jin muryanta kaman tana kuka yasa ya saketa ya kalli fuskarta hawayen daya gani yasa ya make mata kafada yakai hanunshi ya share mata hawayen yana turo baki yana wani irin kallon eyes dinta, kallonshi tadanyi kafin murya chan kasa tace "what happen to you why are you like this?" shiru yayi yana wani irin kallonta dayasa taji wani iri da sauri ta dauke kai tace "you are not feeling fine, ur body is hot, stand up and go home" turo baki yayi yanadan lumlumshe ido yace "okay let's go together, you will see Mami, Abie and my Bid, zaki gansu?" yay maganan yana ware mata manyan idanunshi alamun tambaya da sauri ta kalleshi jin yanda yay maganan dan he don't really sound okay to wai meya dawo dashi hakane kodai ba mutumin nan da ya tsinceta a ruwa ya kaita asibiti bane? Kodai idanunta ne, but ha'a bagashi nanba, wanan ai shine but yaushe yasami tabin kwakwalwa haka yadawo zararre ahankali muryanta na breaking sosai tace "please katashi katafi gidanku you are sick" make mata kafada yayi yana neman fadawa jikinta cikin wani irin yanayi yace "pls don't leave me again" matsawa tayi gefe da sauri ta mike tsaye, shima da sauri yamike tsaye ya dafa bango da sauri jin kanshi kaman zai fadi yasaki kuka sosai yana cizan lips dinshi, da sauri tadan matso kusada shi wani irin mugun tausayi taji yabata ahankali tace "are you fine?" turo mata baki yayi yanaso yakara fadawa jikinta da sauri ta matsa baya kirjinta na bugawa, ahankali cikin kuka yace "am sick".



Ji tayi kaman itama zatai kukan sabida yanda yake kukan yana kallonta har yanzu bai dena kallonta ba, da sauri tai hanyar fita tace "stand up and go home kasha magani is magrib" dan juyowa tayi ta kalleshi ganin har lokacin kuka yake yana binta da kallo, sosai taji zuciyarta yay wani iri, lekawa waje tayi amma bataga kowaba hakan yasa kawai tafice abinta da sauri dan taje gida kafin a fara neman ta amma still taji duktabi tadamu da sauri take tafiya dan takusa gida, tafiya tayi nakusan minti goma sanan ta shigo anguwan su, hannu tasa zata bude gate din gidansu taji an rikemata hijabi amugun tsorace ta juyo ganin shine idanunshi sunyi jajir bamaya iya bude idon sosai da kyau yasa ta juya ta kakkali anguwan su ganin ba mutane awaje yasa arude ta kalleshi tace "na bani, you followed me why?" make mata kafada yayi yace "I will never let you go again" da sauri takara kallon ko'ina tace "na shiga uku, wai menene to zakajamin fitina, sakenmin hijabi" ta fizge hijabin ta kaman zatai kuka dukta rude dan tasan ware haka Abba ke shigowa gida, dan sassautar da murya tayi dan wlh mugun tausayi taji yabata ayanda taganshi sha bakwai dinan gashi zazzabi yake sosai kuma koba komi yataimaka mata shima, gashi ya kafe ta da ido idanunshi cike fal da hawaye har wani irin shining suke, sosai taji wani iri hakan yasa ta kwantar da muryanta kasa sosai kaman meson lallashin yaro tace "you are sick, you are very sick, touch your body" ta daura hanunta akan wuyanta tanamai demonstrating yana kallonta kaman yasami wani irin TV, tace "your body is very hot, u are running temperature, go home kaji" takarashe maganan tana kallonshi kaman yanda yake kallonta bayako kyaftawa ahankali ya lumshe ido kafin yabudesu ahankali yadaurasu akanta, da sauri ta janye nata idon danya mugun cika mata ido sosai, batare data kalleshi ba tace "what do you want?" murya chan kasa yana kallonta yace "water" dan juyowa tayi ta kalleshi sanan tace "okay wait here bari naje na daukoma ruwa kaji sai kasha katafi, lemme bring water for you okay" gyadamata kai yayi yana binta da kallo, da sauri tabude gate dinsu ta shiga gidan, babu kowa a tsakar gidan, gidan shiru kaman ba mutane ciki kasancewar babu wuta da taji hayaniyan su Zainab suna kallo a falon Mama, hanyar sassan Kaka tayi da mugun saurinta ta shiga falon, Kaka bata falon hakan yasa tai hanyar dakinta ta hango hasken fitila a dakin Kaka, murmushi tayi aranta tace hala salla take saisa bata kira sunana ba dan data kirani, dakinta ta shiga ta tumbuke takalmin kafarta ta yarda jakan akan gadon takarasa da sauri inda jakan pure water daya da Kaka ta ijiye mata adakin ta dau guda daya ta juyo danta koma waje ta bashi da saurinta, wani irin cin karo taida mutum abayanta tai wani irin ihu tai baya zata fadi da sauri ya rikemata hannu shima afirgice dan yana tsoron ihu sosai, azabure Kaka data sallame salla tadau fitila tace "innalillahi Hamida incedai lafiya daga shigowan ki kin kurma uban ihu haka" arude Hamida ta kalli kofan dake abude na dakin da sauri ta fizge hanunta tai wurin kofan kafin Kaka ta iso tarufe tasaka sakata, mutum taji yafado ta bayanta dan shima ya tsorata sosai ya riketa, zatai magana Kaka ta karaso wajen ta buga wani irin uban salati. "innalillahi Ke Hamida!" a mugun firgice ya juyo da Hamidan data kife da kofa ya ya rungumeta jikinshi na rawa sosai ya kalli Hamidan zaiyi magana, arude Hamida da jikinta ke wani irin masifar rawa ta daura yatsarta akan pink lips dinshi ta girgiza mai kai, ya ware manyan idanunshi yana kallonta, arude Kaka ta buga kofan. "ke Hamida menene? Meya sameki? Budemin kofan nagani? Ko cinnaka ne? Dan dazu na sharo shazumama adakin nan sunfi guda dari uku, ashe kinyi barin sugar kafin kitafi makaranta kinsan kuma duk inda shazumama yake cinnaka na wurin, mugani idan itace ta cijeki nasiyo cacatin a kasuwa dazu na mulka miki a wurin" arude Hamida da jikinta ke wani irin rawa ta runtse ido tana kokarin saita bugun zuciyarta tace "uhn...uhn lafiya lau, bugewa nayi na kofa fa Kaka" tai maganan har lokacin yatsarta nakan soft lips din Aadil dake rungume da ita yana wani irin kallonta da dan ragowan hasken dakin, cikin fushi Kaka ta buga kofan tace "karya kike ja'ira, irin wanan uban ihun dakikayi bude kofan nagani" wasu irin hawayen tsorone suka zubomata, idan Kaka ta shigo dakin nan taga namiji aciki aiyau kasheta za'ayi a gidan nan, Yayyinta biyar duka mata babu wacce ta taba kawo namiji gidan nan bada sanin Baba ba, kumama Maza ne da aka sansu akasan asalin su wayanda zasu aura, ita har cikin dakin kwananta ma kuma kome zatace baza'a yarda ba, wani irin kallonta Aadil yakeyi yanda hawaye ke zuba daga idanunta harwani irin zufa ta shiga yi a goshi tsabagen tsoro da rudewa, numfashin ta na sauka akan fuskarshi dayasa yaji wasu irin abu namai yawo akai, ahankali yasa hanunshi na dama ya janye yatsarta daga bakinshi yarike hanun da sauri ta bude idanunta ta daura akanshi, daga waje Kaka tace "wai bazaki bude kofan nanba Hamida kosai na kira Faruku ya ballata?" matsa hanunta yayi yadan lumshe mata ido yana matso da kanshi saitin fuskarta ahankali kaman wani irin abu na janshi towards her, kokarin matsar da kanta tayi ya make mata kafada cikeda shagwaba yasake matsowa zatai magana takasa sabida kar Kaka dake bakin kofan taji gashi yawani irin cika mata gaba, sakin kuka tayi hakan yasa shima yasaki kuka yana lumlumshe mata ido kafin ahankali yay landing forehead dinshi akan nata yana breathing way too fast, he has never ever experience irin wat he's feeling right now da baimasan ko menene ba, lumshe ido tayi da sauri tana kara shegewa jikin kofan kaman zata fasa ta shige lips dinta nawani irin rawa suna vibrating tana kokarin hanasu fitar da sound din kukan datake yi kar Kaka taji ta taro mata jama' a asirinta ya tonu danyau Abba da Ya Faruk sai sun kasheta, ahankali ya kafe lips din da ido, lumshe ido yayi yakara rike hanunta gam gam kanshi narawa, dawani irin sauri kaman wanda aka bashi naman dawisu for d first time akace yaci yay placing lips dinshi akan nata yana numfashi sosai kirjinshi na bugawa danko ita tanajin yanda heart dinshi ke beating kaman zai fashe yafito, dawani irin sauri ya shiga kissing dinta batare dayamasan meyake yiba yana wani irin nishi da sauri da sauri yajawota yasata ajikinshi sosai.



_Assalamu Alaykum Fanmily, am really sorry bakusamun frequent update, am not that strong, Kano people 😎 you guys have to explain this for me daga zuwa garinku sai zazzabi nake, gaskiya I think air din Kano is foul😜 Just joking. But pray for me okay, I love you all_.

_🌹IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur


19....




_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan ko pay achan_


_in kinason novel dinan zaki turo just 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment to my watsapp number 07012181461_



_you can also send MTN card zuwa watsapp number na 07012181461, sainai adding dinki a group din danake posting_






Ya wrapping his left hand around her waist yana shesheka kuka sosai yana kissing dinta, da sauri Kaka daharta kai kofar dakinta tasake juyowa tadawo bakin kofarta ta buga kofan cike da masifa tace "wai lafiyan ki Hamida rukuku rukukun menake ji kaman bera na barna?" da sauri ya kabar da hanunta dake kirjinshi tana tureshi cikin hawaye yasake fadawa jikinta yay lamo kirjinshi na bugawa sosai while kissing har lokacin batare daya denaba, runtse ido tayi da kyar ta daddage ta fizge bakinta daga nashi zata tureshi ya riketa sosai yana make mata kafada yana kallonta yana kuka ahankali mara kara, da kyar ta iya saita muryanta gudun kar Kaka ta zargi wani abu tace "Kaka bacci, kidena tashi na" tsaki Kaka tayi tace "kyaji dashi ja'ira kawai, abincin ki na falo dai koda yunwa ta farkar dake cikin dare kije ki dauka" tana maganan tai hanyar dakinta ta shige ta rufo kofa dan itama tagaji yautai aiki da rana, jin karan rufo kofar dakin Kaka yasa ta tureshi daga jikinta da karfi, komawa baya yayi yana turo baki yana share hawayen da yakeyi da bayan hannu, share hawayen daya kasa dena zubo mata tayi ta kalleshi kaman ta zubamai mari dan takaici, yanda yake kallonta ya tsaya a inda ta turashi yana goge idanunshi da bayan hannu kayan jikinshi sunyi daka daka yasa taji yasake bata tausayi dan wanan asibiti yake bukata, ahankali ta saita muryanta ta kalleshi tace "inane gidanku?" dan matsowa yayi kusa da ita da sauri dan kaman jira yake dama tamai magana, da sauri ta matsa takoma kan gado ta zauna, juyowa yasakeyi ya kalleta daga inda yake a tsayen a tsakiyan daki yace "gidan mu?" da sauri ta kallai jin yay mata magana ta gyadamai kai tace "eh gidan ku" kallon yatsunshi yayi yana turo baki yace "gidan mu na chan chan, there's basketball field in our house, Bid and I use to play basket ball" yay maganan yana mata murmushi yana juya mata manyan idanunshi looking super cute, da sauri ta janye idanunta daga kanshi ganin ayanda yake magana ma baisan inda gidansu yakeba yasa ta shiga damuwa sosai. Innalillahi, ita yanzu yazatayi dashi tabani, tayaya ma zatayi ta fitar dashi daga gidan nan yanda ya shigo dinan batare dawani ya gansu tareba?, cikin tsaka da tunani taji mutum ya zauna kusada ita da sauri ta dagokai ta kalleshi kafin ma tai wani yunkuri ya daura kanshi akan kafadarta yana turo baki yace "am hungry" yay maganan yana lumlumshe ido, tsabagen tsorata yasa ta tura kanshi daga kafadarta ta tashi daga kan gadon da sauri tana nishi tace "bari na daukoma abinci" tai hanyar kofa tashi yayi da sauri ya biyota salati tayi a tsorace tace "innalillahi dan Allah ka zauna abinci zan daukoma" make mata kafada yayi hawaye na sake taruwa a idanunshi, sake rudewa tayi dan dazaran yafara kuka zai tona mata asiri jarumta tayi ta daura hanunta akan bakinshi ta rufemai baki da sauri ya ware manyan idanunshi ya kalleta, murmushi tamai tace "yauwa yayama sunanka?" tai maganan tana jan hanunta daga bakinshi da sauri shima yay mata murmushi daya wani irin karama fuskarshi kyau yamata fari da ido a shagwabe yace "Aadil, but Bid use to call me Dil" yanda yay maganan was damn mesmerizing da sauri ta kawad dakai tace "okay muje ka zauna I will bring food and paracetamol for you ok" tai maganan tana nunamai saman gado, zama yay akan gadon yana rike hijabinta ya turo mata baki tareda mikamata kafarshi ya lankwasar dakai a shagwabe yace "remove this shoe from my leg am tired" kallonshi tadanyi kafin ahankali ta tsugunna ta warware igiyan ta ciremai takalmin ta ijiye, ya miko mata dayan kafan ta ciremai shima ta ijiye duk yana kallonta, yace "will you come back?"




Yi tayi kaman batajishi ba ta shareshi ta mike tsaye zata wuce, fizgota yayi da karfi atsorace tajuyo saura kiris tafada kanshi ta cije da kyar ta ta kallai, marmar yay da ido kaman zaiyi kuka yace "will you come back? Don't leave me again pls"  gyadamai kai tayi da sauri ta dauke kai ahankali ya saketa ya washe mata baki yay tafi yace "yay am happy" juyawa tayi tai wajen drawer dakin tajawo dan taga Kaka na yawan zuba makulli a drawowin wajen duk yana binta da kallo kaman zai cinye ta da idanu, wani makkulin kwado ta dauka taboye ta hanyar rufe hanunta ta maida drawer tai hanyar kofan dakin ta cire sakata tadan waigo hada ido sukayi har lokacin kallonta yake ya washe mata baki white teeth dinshi suka fito da sauri tafita daga dakin ta tsaya ta ta rufo kofar dakin ahankali gudun karta tashi Kaka tadau key tasaka sanan tai hanyar falon tadau kulan tuwonta da miya sanan tai hanyar doguwan kujeran Kaka tadau kwalin paracetamol din Kaka dake ajiye awajen tabude taciro sachet guda daya tamaida tarufe ya ijiye takwashi kulan tai ciki, agaban dakinta ta tsaya ta ajiye kulolin akasa sanan tasa key tabude kwado ta bude kofan ta kwashi kulan ta shiga ciki tana kallon fuskar Aadil ganin yanda yake kwance kan gadonta ya lumshe ido, ajiye kulan tayi tarufe kofar tasaka sakata sanan ta dau kulan tai wajen gadon ta ijiye akasa tana kallonshi yanda yake numfashi ahankali ahankali yana bacci, yay wani irin kyau kaman ba shine mara lafiya ba, da sauri tadena kallonshi dan sosai fuskarshi yacika mata ido, ahankali takai hanunta dake rawa sosai ta buga katifar muryanta nadan rawa tace "A..Aadil" ko motsi baiyiba bacci yay gaba dashi sosai, kallonshi tayi ta kafeshi da idanu hakanan taji tanajin wani irin tausayinshi, ahankali ta mike tsaye ganin yay bacci yasa tai wajen sip ta bude sip din tana kallon jerin nikakkun kayan ta dake ciki, wani simple free doguwan rigan atampa ta dauka ta maida sip din tarufe tai hanyar bayi, sake juyawa tayi ta kallai ganin har lokacin baccinshi yake yasa tabude bayin ta shiga ta garkama sakata, ahankali tacire hijabinta dayay duku duku ta saka cikin wani empty bucket, tazare kayan jikinta ma duk tasa a botukin sanan tafara wanka, wankan tayi sanan ta tsane jikinta tadau doguwan rigan data shigo dashi ta saka tai alwala sanan tabude kofan ahankali tafito har lokacin bacci yake sip tabude taciro wani hijabin tahau kan dadduma tafara biyan sallolin da ake binta, saida tagama sanan tacire hijabin sabida zafin datake ji sosai ta ijiye hijabin akan dadduma ta juya ta kalli Aadil dahar lokacin ke bacci sosai, ahankali ta matsar da hijabin saman dadduman ta kwanta ta daura kanta kan hijabin datai filo dashi tana kallonshi zuciyarta na tambayarta yazatayi dashi? Ta ina zata fara neman gidansu? Tayaya zata fitar dashi daga gidansu batare da anganshi ba? Idan aka ganshi mezata cema Abba, Mama, Kaka, da Ya Faruk? Yayama zatayi da wanan babban mutun din? Kodai to takaishi asibiti ne adubashi? To ta ina zata sami kudin? Yaya zatayi ta nemo gidansu yanzu? Takai kusan 10min tana kallonshi tana tunane tunane kafin ahankali tajuya mai baya cikin maganin bacci ta kwanta ta hannun damanta wani wahalallen bacci yay gaba da ita.


Kaman amafarki taji ana mata kuka awuya ana bubbuga mata ciki ana shurinta da kafa ahankali, da kyar ta iya bude idanunta cikin bacci tadan juyo Aadil tagani ya kwanta agefen ta yachusa kanshi awuyanta yana mata kuka sosai gabaki daya hawayen shi nabin wuyanta some nabi har cleavage dinta, hanunshi nakan cikinta yana bubbuga matashi yana kuka, sosai tawani irin tsorata tafara ture kanshi daga wuyanta bakinta har rawa yakeyi tace "d...dagani, menene mekake so? Please dagani, katashi daga jikina I can't breath" make mata kafada yayi batare daya tashiba cikin kuka sosai yace "a...am hungry, my stomach hurts"

_🌹IN BANI 🌹_ 





Maman Abd Shakur



20....


_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan ko acahn_


_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment to my watsapp number 07012181461_


_you can also send MTN card to watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_





Tureshi tayi da karfi tace "na shiga uku dan Allah ka dagani, ga abincin ka chan" sake make mata kafada yayi cikinshi na murdawa dan har kukan cikin tanaji, dan kwantar da murya tayi tace "look at your food there, pls dagani" ahankali ya dagata ya kalli fuskarta jin yanda tai maganan muryanta na rawa sosai kaman tana kuka, hawaye yaga tana shareware, ware ido yayi sosai kaman dan yaro saikuma yafashe da kuka maidan kara yace "you are crying whyyy?" da sauri ta tashi daga kwancen gudun kar Kaka tajishi ta share fuskarta da bayan hannu ta kakalo murmushi tamai tace "kagani niba kuka nakeyi ba" hadiye kukan yayi ya kalleta irim kallon da gaske mugani, murmushi ta sakar mai hakan yasa shima yasakin mata murmushi mai kyau sosai yana kara kama cikinshi dayaji ya murdamai da sauri ta tashi ta dauko mai abincin ganin yanda yayi takawo gabanshi ta bude kulan tuwon shinkafa ne da miyan dry kubewa ta kalleshi yanda yake binta da kallo ta nunamai kulan tace "eat" kallon abincin yayi yasake kallo sanan ya yatsine fuska kaman yanda yara keyi yace "wat is this? I want rice with meat balls, i want yam fritata, i want smoked prawns" zaro ido tayi ta kalleshi dan wlh wasu abincin ma daya kira batasan suba hakan yasa tabuga uban tagumi ta lankwashe kafa tana kallonshi inda ace za'a gwada jinin ta yanzu sai anga yahau dan wlh fargaban gobe take, kukan shi ne yasa ta dago kai da sauri ta kalleshi sosai yabata tausayi dan ayanda yayi gaskiya baisan abincin bane, da sauri tace "zakaci biscuit to?" gyadamata kai yayi yana neman fadowa jikinta da sauri ta tashi tabude sip dinta, chan saman kayan ta taboye biscuit din sabida kar Ihsan tagani ko Zainab ta dauko guda biyu ne short bread biscuit tadawo ta zauna agabanshi ta mikamai, karba yayi da sauri yana murmushi yana kallonta sanan yabude daya ya ijiye daya agefe yasa hannu yaciro biscuit daya ya dago kai da sauri ya kalleta kaimata dayan bakinta yayi da sauri ta kalleshi, murmushi yamata yana wani irin kallonta kaman wani mai lafiya ya ware manta manyan idanunshi dake cike da bacci gashin idon duk sun tattare sabida lema leman ruwan hawaye yace "eat my wife yay" zaro ido tayi ta kallai, fari yamata da ido yana goga mata biscuit din a lips kaman yana shafa mata jan baki yace "eat, haaa, haaa, hamm" yay maganan yana bude mata baki kaman yanda akema small baby yaci abinci, dan murmushi tayi ganin yanda yake bude mata baki bama tasan lokacin data saki murmushin ba sabida yanda yay maganan dan har yasa ta manta da fargaban datake ciki na gobe, ahankali tasa hanunta ta karbi biscuit din daga hanunshi takai bakinshi tai murmushi tace "kaika ci kaine kejin yunwa, eat" bude bakin yayi da sauri kaman jira yake ya balli kadan yanaci yana kallonta lumshe ido yayi yana taunawa saikuma yabude idon ya kalleta suka hada ido yace "is very sweet" ya fizge rogowan daya rage daga hanunta yakai bakinta yace "eat my wife" dan kallonshi tayi dan duk idan yace my wife"sai gabanta yafadi tadan balli kadan da sauri yatura sauran bakinshi yataso yadawo kusada  ita kaman an jehoshi ya kwanta ya daura kanshi kan cinyarta yanacin biscuit din yana kallonta yana mata murmushi sosai wani irin farin ciki yakeji idan ya kalleta fiye da misali dan ko damuwa dasu Mami ma baiyiba shi kawai bayason ta barshi konan da chan, tagumi tabuga itama tana kallonshi tana tunani sosai, maganan shine yadawo da ita daga duniyar tunani yace "water" pure water daya ta dauko ta mikamai, tashi yayi ya zauna ya karba yana kallon ruwan yana juyawa dan bai taba shan irin wanan ba, ganin haka yasa ta karbi ruwan tabude mai takai bakinshi da sauri ya kafa baki tareda daura hannayenshi kan nata yakara rike ruwan da kyau yanasha, wani irin sanyi taji har brain dinta da sauri ta lumshe ido saida yakusa shanye ruwan sanan ya janye kai yana murmushi yana kallonta, dan murmushi tayi itama ta dauke kai tadau marfin kulolin abincin tana rudewa tace "jeka kwanta akan gado" make mata kafada yayi ya nuna mata kan dadduman data kwanta akai dazu yana turo mata baki yace "lets sleep there" kallonshi tayi saikuma ta chusa kanta kan kafarta tai shiru abin duniya yay mata yawa, wanan wani irin kaddara ne tahadu dashi, shima shiru yana kallonta duk sai yaji wani iri kaman baida lafiya sabida yanda ta kifa kai taki kallonshi, ahankali ya share hawayen daya zubomai kaman maraya ya kwanta akasa a gefenta ya jefar da ragowan biscuit din dake hanunshi yana kallonta yana lumshe ido yana goge hawaye, ahankali kaman matsoraci ya dafa kafadarta yakira sunanta "my wife" ture hanunshi tayi cikeda masifa data dade batai irinshi ba dan tagaji da yanda yake tabata yace"leave me alone" ta turemai hanun tasake maida kanta kan guwiwa, matsawa baya yayi atsorace yana kallonta yasaki kuka ahankali yana share ido da bayan hannu, ahankali ya kwanta akasa awurin yana kuka sosai yana kallonta so kawai yake tadago kai ta kalleshi, haka bacci yasake daukan shi kaman zaiyi ihu ya dukunkune gwanin ban tausayi.

🌹IN BANI 🌹




Maman Abd Shakur



21...




_this novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binka bashi, pay anan or pay achan_



_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_you can also send MTN card ta watsapp number na 07012181461, sainai adding dinki a group din danake posting_





Saida tajishi shiru sanan ta dago kai idanunta sunyi jajir ta kalleshi, sosai taji wani irin tausayinshi yanda ya dukunkune kaman wani maraya, zanin lullubanta tajawo ta lullubeshi dashi sanan ta tashi tahau kan gadon ko minti biyu baya karaba wani bacci mai nauyin gaske yay awon gaba da ita.

Wuraren karfe biyar na asuba Kaka tazo tabuga kofarta. "Hamida, Hamida wai bazaki tashi kiyi salla ba iyye yarnan?" da kyar ta iya bude ido cikin bacci ta kalli inda take kafin ta kalleshi ganin har lokacin yana kasa bacci yakeyi sosai ya dukunkune kaman maijin sanyi yasa ahankali tace "natashi inakan dadduma ne Kaka" kwafa Kaka tayi ta wuce dakinta tana masifa tace "yau bazaki zo dakin nawa muyi tareba, kyaji dashi mai bakin hali" tahau kan dadduma takabbarta salla, yunkurin tashi tayi daga kan gadon takasa takara komawa ta kwanta wani banzan bacci ne yakara tafiya da ita dan tamugun gaji gashi batai baccin kirki da daddare ba sabida Aadil dinan.


Wuraren bakwai ta iya farkawa daga baccin da kyar, ahankali ta karanto addu'an tashi daga bacci tabude idanunta ahankali tana kallon window dakin yanda rana ya hasko har zuwa tsakar dakin ta tashi zaune tana dafa zanin katifar gadon abune taji ya soke mata hannu hakan yasa ta kalli gefenta da sauri ledan biscuit din data bashi jiyane tagani ya ninnike ya maida shi suffar flower da sauri tadau ledan biscuit din tana juyawa tana kallo tadanyi murmushi ta mika hannu zata ijiye idanunta suka sauka akan yar takarda akan gadon da sauri ta dauka tajuyo da paper, zanen fuskan mutum ne yana kuka saiya rubuta sorry my wife a gefe, dan murmushi tayi saikuma ta tabe baki ta juyo dakai da sauri danta kalli inda yake taga bashi awurin, da sauri ta mike tsaye tana kalle kallen dakin ganin bashi yasa tai kofar bayin ta tsaya tai knocking har sau biyu, jin ba'a amsaba yasa tabude kofan da sauri ta leka amma babu kowa cikin bayin, dawani irin sauri tai hanyar kofan ta tana karanto addu'a aranta ta kalli sakatan data saka ganin babu sakata ko daya yasa gabanta yawani irin mugun faduwa, juyowa tayi ta kalli tsakar dakin ganin har lokacin akwai sneakers dinshi akasa yasa taji cikinta yawani irin yamutse ya kulle sosai tsabagen tsoro, kaman daga sama taji Kaka taja wani dogon ihu tabuga uban salati. "innalillahi wa innailaihi raji'un jama'a, Sama'ila, Sama'ila" ta kwalama Abban su kira, arude ta dafa kirjinta dake neman tarwatsewa yadena aiki koina na jikinta na rawa "jama'a gardi a sasa na kufito, Sama'ila" karan bude kofan sasan Kaka taji saikuma taji muryan Abban su yace "lafiy..." bai karasa ba taji yay shiru, muryan Mama taji itama bayan ta turo kofan sasan Kaka arude tace "Umma lafi..." jitayi gabaki daya jijiyoyin jikinta sun dena aiki tsabagen wani irin shegen tsoro da fargaba dasuka dirar ma zuciyarta, ahankali take matsawa tana jan kafarta dasuka mata wani irin nauyi sosai tana komawa baya, maganganun dataji afalo da tsabagen tsoro yasa tama kasa gane me'ake cewa yasa ta sanya hanunta akan bakinta tana kokarin taushe wani irin kukan dake shirin kufce mata, tura kofar dakinta akayi da karfi suka hada ido da Aadil, da gudu Aadil dake sanye da dogon wandonshi da farin singlet ya shigo dakin hanunshi duk ruwa kaman yay wasan ruwa, da gudu yayo wurinta kafin ma tai yunkurin matsawa ganin kanta yayo ya shige bayanta ya riketa gam gam  ya sakin mata kuka awuya kirjinshi na bugawa sosai, daidai lokacin su Abba suka bude kofan dakin suka shigo, da sauri ya daga hanunshi yana rikiketa yanuna mata su Kaka yace "my wife see this people they're scary, sunata kallona am sacred, hide me" yay maganan yana kara komawa bayanta hanunshi duka biyu akan cikinta ya riketa gam cikin tsananin tashin hankali ta fara kokarin turashi daga bayanta da kafadarta take amma ya riketa gam ta bayanta yana make mata kafada yasakin mata kuka ahankali yana kara kankameta, daga idanunta tayi dasukai jajir tahada ido dasu Kaka, Abba, Mama, dasu Zainab daduk sun kasa magana sunyi suman tsaye sun kasa gasgata abinda idanunsu ke gane musu, sai Ya Faruk dake sanye da kayan sojoji shigowanshi gidan kenan ganin yanda su Abba suka shigo dakin Kaka da gudu yasa yabiyo bayansu shima ya tsaya a gefen Zainab ya zubama Hamidan ido kirjinshi nawani irin tafarfasa, fashewa Hamida tayi dawani irin kuka ganin yanda yan gidansu ke kallonta ta fizge hanunshi daga kan cikinta da karfi tawani irin tureshi cikin tsananin fushi har yana buga bango tace "let go off me" da sauri tai wajen Abba ta kalli Abba cikin tsananin faduwan gaba tana kuka bakinta har rawa yake tace "A..bba wl..." cikin wani irin zuciya Abba ya dauketa dawani irin hadadden mari da baitaba mata shiba tunda ya haifeta jikake "pau!" tai wani irin tangal tangal tai baya zata fadi tsabagen yanda marin ya shigeta zaro ido Aadil yayi yazo wajen da mugun sauri yatare ta tafado jikinshi luuu kaman wacce ta suma, fashewa da kuka sosai Aadil yayi ya kalleta yanda take kokarin ta bude ido ma takasa, cikin wani irin tsananin fushi da zuciya yawani irin kalli Abba, fizge ta Abba yayi daga hannunshi cikin fushi yakara daga hannu zai sharara mata mari Aadil yawani irin fizgota da karfi ya rungumeta ajikinshi ya kankameta sosai kanshi na girgiza wa sosai jijiyoyin gaban goshinshi sun fito idanunshi sunyi jajir ya kalli Abba da jajayen idanunshi yay wani irin ihu ya nunamai hannu yace "stop beating her mugu".






Yay maganan yana kara kankameta ajikinshi sosai da kyau yana kuka shima kaman yanda take kukan tana neman fizge jikinta daga nashi dan wani bala'in yake kara jefata, a zuciye Faruk yazo zai wuce Abba ya damko Aadil Abba yarike mai hannu cikin tsananin bacin rai batare dayace komiba, daidai lokacin Hamida ta fizge jikinta daga na Aadil dake kuka sosai da karfi ta tureshi tana kuka tace "stop touching me" tajuyo cikin tsananin tashin hankali da sauri ta tsugunna tasa guwiwanta akasa ta hada hannayenta, cikin kuka bakinta har rawa yake tace "Ab...ba dan Allah, Mama" takira sunan Mama da jikinta yay wani irin mugun sanyi idanunta sunyi jajir tana kallon Hamidan tace "Mama p..pl.." tama kasa magana tsabagen yanda zuciyar ta ke bugawa tajuya ta kalli Kaka dage mata wani irin mugun kallo tace "Kaka dan Allah kiyakuri wlh, wlh bansan yabiyo ni...." cikin tsananin fushi Mama ta fizgota tsaye tawani irin watsa mata mari, zatakai mata na biyun Aadil yajawota da karfi har Mama ne neman faduwa,  yaboyeta abayanshi dudda yanda take fada dashi akan yasaketa yaki ya rike mata hannu gam yana make mata kafada Mama ta saki baki tana kallon ikon Allah yanda yarike Hamidan dayafi karfinta yana boye ta abayanshi kaman wani mijinta, cikin tsananin fushi Faruk yay kan Aadil Abba yawani irin dakamai tsawa yace "karka sake kataba dan mutane Umar karkai kisa agidana, yarmu itata nunamai gidan nan, ita ta shigo dashi, ita ta..."  cikin fushi da kunan rai Kaka da tuntuni batai magana ba ta nuna Hamida dake kuka sosai a tsugunne Aadil shima a tsugunne a gefenta yana kuka yana leka fuskarta kaman wani yaro dan yaye tace "Hamida wlh kincuci kanki bamu kika cutaba, inda kinsan aure kikeso dakin fada anhada bikin ki dana Ayush tuni, kullum sai munafinci kina sussunar dakai ke adole mai tsoron mutane, ke adole ustaziya, hijabin nan biya biya har kasa yake sharewa ashe iskanci kikeyi, Sama'ila" takira sunan Abba cikin wata irin kakkausar murya tana share hawaye da bayan zanin ta tace "wlh Sama'il, kaji na rantse maka da Allah, tun jiya da Hamida tadawo bata bari nasata a idanunaba, bayan magriba yarinyar nan ta shigo gidan nan Sama'ila, yarinyar da kullum kofarta a bude yake kwana wlh tana shigowa jiya ta garkame kofan da sakata bam, ni dama nadinga jin motsi a dakinta harda ihu dasu barambarama kaman ana kaukawa.." tasake goge hawaye tana kallon Hamidan dake kuka sosai tace "babu yanda banyi da itaba tabude na dubata taki wai bacci zatayi, nai nai tafito to tazo taci abinci tadau tuwonta dake falo nan ma taki ashe tanada babban abinci ne acikin dakin, koda asuban nan danazo kin budemin tayi dudda mun saba sallan azuba tare a dakina ashe da kwarto tazo, yanzu Hamida har gida, har Sasa na, har gidan mahaifin ki zaki taho da namiji ki kawoshi shashina dankin rika, kin balaga, kinajin kanki sa'ar uwarki gaki kema kin tasako abinda uwarki kedashi kema kinada shi, to wlh bari kuji nafada muku dukan ku" tai maganan tana gyara tsayuwa tadawo gaban Abba ta tsaya ta nunamai Hamida da yatsa tace "nice uwarka daiko Sama'ila, nice kuma uwar mai gidan nan, sanan nidai bantaba iskanci ba dana auri ubanka ba, ubanka ma baitaba iskanci ba, sanan kaima baka taba iskanci ba dan haka bazan taba yarda dawata yar iska a matsayin jikata ba wlh, ni dama batun yauba nasha cewa Hamida ba jini na bace dan komi nata daban ne agidan nan bakaga kyan ta ba" tunda tafara maganan Mama ta kafeta da ido, hararanta Kaka tayi tace "kinsan menake fadi ai, dan haka Sama'il wlh dole ka zaba koni ko yarka, Hamida ta tattara tabar min gidana ga uwarta nan tafadi mata waye mahaifinta taje chan tasame shi, dagayau itaba yarka bace dan bama tayo komi nakaba, da uwarta take kama kaman tai kaki kanajina ko"  wani irin runtse ido Faruk yayi zuciyarshi na tafarfasa dan sosai yaga haukan Kaka yatashi yau tafara maganganun banza, ahankali Abba cikin kwantar da murya yace "Umma kibari an...." "kamin shiru nace mara mutunci rubabben yaro kawai to wlh bazan bari kazama zanin daurawan mace ba" Kaka ta dakamai tsawa tace "tunda bazaka iya koranta ba nizan koreta kuma wlh inga wanda ya isa yadawo da ita gidan nan, na rantse da Allah saina tsine masa" ta kalli Hamida dake kuka sosai  a tsugunnen tace "dau kwarton ki gashinan ya tasaki agaba yana kallo yana kuka kaman sabon maye, ki tashi kibar gidan nan yar iska, wato har cemai kikayi yadinga abu kaman dolo ko makira mai kama da uwarta, dau kwarton nan kibar gidan nan kafin nabar Faruku ya kaishi lahiran"





Kaka  ta daka mata tsawa. "tashi kibar gidan nan nace" cikin fushi Faruk yace "wai ina zatane Kaka? Ga wanda yabiyota bazaku ce komiba kuna cewa tabar gidan mahaifinta ina kikeso taje eh, kunki tsayawa ku saurari yarinya, ina kukeso taje?" "gidan uwarka zata"  Kaka tabashi amsa cikin tsananin bacin rai tace "nace gidan uwarka zata, wlh ka kara magana anan wajen saina maka shegen duka na rantse da Allah, Sama'il kama Faruku magana ya maidani sa'arshi yauzan nunamai na isa da kowa a gidan nan dan ubanshi" ta kalli Hamida tace "tashi kibar gidan nan, wlh inhar batabar gidan nanba saina fada rijiyar sasan ku na rantse da Allah" kin tashi Hamida tayi sai kuka take tama kasa magana, kanta Kaka tayo hakan yasa ta tashi da gudu tafada jikin Mama tana kuka tana haki da kyar tace "Mama wlh shiya biyoni, mahaukaci ne, shine shine ya taimakeni a..." wani irin ingizata Kaka tayi har saida tabuge su Zainab tafita daga dakin tafadi akasa timm, da sauri Aadil yatashi yana kuka sosai ya bangaje Kaka da saura kiris ta fadi ta rike kofa yafita  yadago Hamidan da sauri yana kuka sosai yasa hannu ya share mata hawayen yace "stop crying i will call police to come and arrest them, they're beating u, they're very wicked people" hanunta ya kalla data gurje yana dan jini yarike hanun da sauri yana zaro manyan eyes dinshi yakai hanun bakinshi da sauri yana lashe jinin yana kuka sosai, sosai take kuka tana kallonshi yanda duk hankalin shi yatashi dukya rude, ya cire hanun daga bakinshi yakai hannun bakinshi yana hurawa yana kuka. "fo, fo, fo" Cikin tsananin fushi Kaka tace "kagani ko Sama'ila Hamida tadawo karuwa, kutashi ku fitarmin daga gida" tadau tsintsiyar kwakwa dake gaban dakin Hamida tayo kansu, da sauri Aadil yasaki hanunta yaja Hamidan yasata ajikinshi yamata rumfa yana kuka sosai cikin turenshi dayafi kwarewa akai yace "stop beating my wife, stop, stop, mugu, mugu" rufeshi da duka sosai Kaka tayi da tsintsiyar tana haki yana ihu, tako ina take kaimai dukan yaki sakin Hamidan, Hamidan itama tana kuka dan yanda Kaka ke dukanshi yana kuka har cikin zuciyarta takeji, cikin fushi sosai Kaka tasaki dan ragowan tsintsinyan daya rage a hanunta dan dukya katse a jikinshi tace "kubarmin gidana, kutashi kubarmin gidana, kubarmin gidana"  Kaka ta hankadashi, da kyar ya mike tsaye yana rike da Hamidan har lokacin yana kuka ba'a taba dukanshi haka a duniyan nan ba, Kaka tawani irin tura keyanshi tana dukan bayanshi tarakasu da duka har wajen gate suka fita daga gidan.





Binsu da kallo yan mutanen anguwan dake waje sukayi sabida yanda Kaka ke dukansu sanan tajuya takoma cikin gida ta rufe gate taciro wani karamin makulli daga lalitar ta ta kulle gate din tana masifa tana haki tace "inga mai fita daga gidan nan yau" taja kujera ta zauna anan gaban gate din tana karkada kafa tana kokarin ballan namijin goron data ciro daga lalita saikuma tafashe da kuka tana nuna kanta tace "Hamida, Hamida" tai kwafa tace "kinma kanki, uwarki kika cima mutunci bani ba".




Ahankali tazare jikinta daga nashi cikin kuka sosai tawarware dan kwalin kanta dakeda girma sosai ta yafa ajikinta, hanunta yakara rikewa yana kallo yasa dayan hanunshi yagoge hawayen dayake yi dayaki dena tsiyaya yace "you are hurt, u are bleeding, those people are wicked" ahankali ta share idonta ta kallai yanda yake kuka sosai gashi sai kallonsu ake, ahankali cikeda jarumta tace "stop crying, am fine" kallonta yayi da jajayen idanunshi itama shitake kallo asanyaye, lumshe ido yayi wasu hawayen suka sake xubowa yace "i will tell Mami and Bid saisun rama miki" yasake kai hanunshi kan idanunshi yana kuka sosai, murmushi tamai taji wani irin tausayinshi tace "stop crying people are looking at u, let's go" gyada mata kai yayi ahankali miyau na xubowa, sosai yawani irin bata tausayi ga wuyanshi da kafadarshi duk shatin tsintsiya, ahankali tasa bakin gyalenta takai saitin bakinshi ta share mai miyan bakin, lumshe ido yayi hawaye suka zubomai, asanyaye tazare dan kwalin daga wuyanshi tace "i said you should stop crying" gyada mata kai yayi yabude idanun dake cike da kwalla ya daurasu akanta  da sauri ta dauke kai sabida yanda taji idanunshi sunsa gabanta yafadi sosai ta daga kafa zatai gaba yariko hanunta gam da sauri ta juyo ta kallai suka sake hada ido yasakin mata wani irin kuka mai tsuma rai, da sauri tace "menene why are you crying?" kallonta yayi cikin kuka sosai kanshi da kirjinshi namai zafi sosai baimasan meyake jiba yakasa magana, dan matso wa tai kusadashi tace "menene? Tell me" kafeta da ido yayi yana kuka batare dayah magana ba, cike da damuwa idanunta sun ciko sosai da kwalla tace "tell me Aadil menene?" ahankali yana kallonta da idanunshi dasukai ja suna kyallin hawaye yace "I love you Hamida my wife".

_🌹IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur



22....


_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi pay anan ko pay achan_



_in kinaso novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_Zaki iya turo MTN card 300 ta watsapp number 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_



Ko motsi kasawa tayi jin abinda yafadin mata saima wani irin kallon idanunshi datakeyi, ahankali yakamo hanunta yana kuka yana lumlumshe mata ido gwanin ban sha'awa yace "i love you Hamida, and we will marry just like Mami and Abie right?" shiru tayi takasa magana jikinta yay wani irin shegen sanyi tundaga yatsar kafarta, lumshe ido yayi yasake budesu ya kalleta araunane kafin yasakin mata wani irin kuka, ta tsani taga yana mata kuka, sosai kukan shi ketaba mata rai, da sauri ta gyadamai kai tace "yes" wani irin ware mata manyan eyes dinshi yayi yace "yes Hamida my wife, she  will marry me like Abie and Mami na yay" yay maganan yana mata fari da ido yana juyawa, tsayawa tayi tana kallonshi sosai taji tana wani irin tausayin shi to wai mutunmin dayake da lafiyan shi meya dawo dashi hakane? Meya maidashi haka? Hanunta taji ya fizgo yace "lets go, bazamu koma dat mugu house bako" ahankali ta karbe hanunta daga rikon dayamata suka cigaba da tafiya, batamasan inda zasuba gashi ko naira daya batadashi tafiya kawai suke yana mata surutu yana kirga hanunshi yana nuna mata yana murmushi, sosai yake wani irin farin ciki yana murna sabida tacemai yes sai tsalle tsalle yake akan hanya yana kallon fuskarta, duk in sukazo wuce bishiyan fulawa saiya katso yabata, karba kawai take tana murmushi amma matsalan datake ciki yawuce tunaninshi. 



Gidan data  boye jiya sukaje, atare suka shiga yana tsalle tsalle, pure water data gani awurin tadauka da sauri ta bude tai alwala, Aadil dake tsalle tsalle shima yazo da sauri ya tsugunna yana kallonta sai leken fuskarta yake, turo mata baki yayi yace "me too zanyi alwalan" zaro ido tayi ganin saura dan kadan ruwan, mikamishi tayi da sauri ya karba yana murmushi yace "thank you my wife" yafada yana nuna kanshi yana wani irin fikifiki da idanunshi dimples dinshi na lotsawa, tashi tayi da sauri batason tana kallonshi inyana mata irin abubuwan nan dan wlh wani irin kyau da kwarjini yake mata bana wasaba, karasawa dan filin dakin tayi ta gyara kasan wajen da hanunta sanan ta yafa dan kwalin kanta da kyau ajikinta ta kabbarta salla sai alokacin taji zuciyarta yarage mata nauyin dayake mata na kunci da azaba sosai, yay wani fayau kaman an kawad da damuwanta, salla tayi tai addu'a Allah ya bayyanar da yanuwanshi burinta kawai bai wuce yaga yan uwanshi yatafi gidaba ita saita tafi gidan Anty Lami yayar Mama, zuwa yayi shima ya tsaya a gefen ta yafara sallan murmushi kawai tayi tacigaba da addu'oin datakeyi.


Jinginar da bayanta tayi da bango ta daura kanta akan guiwowinta tai shiru idanunta sun cika da kwalla sosai, alamun mutun dataji akanta yasa tabude ido ahankali, hada ido tayi da Aadil daya leko da kanshi yana wani irin kallonta, ganin yanda hawaye yacika idanunta yasa duk yabi ya damu, zama yay a gefenta ya daura hanunshi akan kadadarta  yawani irin dago kanta daga jikin kafafunta da karfi, kallonshi tayi shima kallonta yake ya daure fuska sosai, akumbure yace "why do you want to cry?" dan lumshe ido tayi da sauri tana kokarin ture hanunshi daga kafadarta takasa sabida yanda yarike ta gam, jiyayi kanshi yadau zafi da sauri ya fada jikinta yakai fuskarshi saitin nata, arude tabude idanunta dake gab da zubar da kwalla tace "Aadil kadena stop, kasakeni" makemata kafada yayi yakai hanunshi ya daura akan saman idanunta yana leka idanun kaman maison gano wani abu, murya chan kasa yace "you want to cry" girgiza mai kai tayi zuciyarta namata rawa sosa tace "n...no Aadil am not cr..crying, kaga....ni" saikuma tasaki kukan da karfi sosai sabida yanda zuciyarta kemata zafi, bamatasan tasaki kukan ba kawai kukan ne yazo uncontrollably, Kaka ta koreta daga gida batada gida ina zata, rudewa Aadil yayi sosai dan yatsani yaga ana kuka barinma na Hamida dayakeji har kasan zuciyan shi, wani irin rungume yayi yasata ajikinshi yana jijigata muryanshi shima narawa sosai yace "d...on't cry, i will call police for them, they will arrest them, they beat you and injury you i will go with police and beat all of them, stop crying Hamida" yanda yake maganganu dabama ta ganewa dan dukya rude muryanshi narawa sosai yana breaking kaman shima yana shirin kukan yasa  tai shiru tana tureshi tana kokarin tashi daga jikinshi, make mata kafada yayi yana kallon idanunta dasukai jajir sun kumbura sosai, hanunshi dake rawa sosai yakai kan fuskarta yay cupping face dinta yana share mata hawayen dake kan fuskar yana yana turo baki kaman zai fashe da kuka yace "i will beat them for beating you, stop crying, don't cry again kinji" gyadamai kai tayi ta hadiye duka kukan datakeji tamai murmushi tace "am fine" ahankali yana kallon idanunta batare dayasaki fuskarta ba yace "are you sure?" gyadamai kai tayi tama kasa magana kirjinta na bugawa sabida wani irin kallo dayake mata daya bambanta dana koda yaushe da sauri ta runtse idanunta gam tafara kokarin fita daga jikinshi, make mata kafada yayi yasata a kirjinshi ya kankameta yay shiru kirjinshi nawani irin bugawa, shikanshi baisan meyakejiba kawai yanaso yacire mata damuwan datake cikine, ganin ko motsin kirki takasa yasa dan bebata daman ba yasa tai shiru gabanta na faduwa tana sauraron yanda jikinshi kewani irin daukan zafi heart dinshi na beating da karfi and fast fast...




***

"Mami, Mami na" da kyar ta iya bude idanunta dasuka mata nauyi sosai tsabagen kukan datake sha ta kalli Aabid daya rame shima duk yay wani iri hanunshi rike da mug din hot tea yana kallon mahaifiyar nashi dake kwance kan gado ta lulluba da bargo, kaman zaiyi kuka yace "Mami please tashi kisha tea kinji Mami na, please sweet Mum" girgiza mai kai tayi muryanta narawa sosai tace "bazan iya shaba, bansan ina Aadil dina yakeba, bansan ko yasamu abinci yaci ba, am sure my baby is hungry yanzu haka, bansan wani hali Aadil dina yakeba, tayaya zan iyacin abinci bansan wani hali my poor innocent boy yake cikiba" hanunta Aabid yakamo yarike zaiyi magana Baffa da shigowan shi dakin kenan kusan shi yamafi kowa damuwa ya nunata da Sanda cike da masifa yace "tashi ki karbi shayin nan kisha, kashe kanki zakiyi tunda yaro yabata babu abinda kika sama bakin salati, tashi ki karbi shayin nan kisha Maryama kona mugun saba miki wlh" cikin kwantar da murya Suleman yace "ya isa Baba muje kahuta kaima bakajin dadin, yanzu nida Abdullahi zamu koma police station din da Hussain" wayar Aabid ne yay ringing da sauri yaciro wayar daga aljihu ya kalli screen din, da sauri yadaga kai ya kalli Abie dake kusa dasu Baffa yace "Inspecta ne" da sauri Mami ta yunkura ta tashi zaune tanajin wani irin masifaffen ciwon kai tace "dauka hala anga Aadil dina ne" da sauri yay picking call din yakai wayar kunenshi daga tachan bangaren inspecta yace "yallabai..." da sauri Mami da jikinta har bari yake tace "sa, saka a speaker Son" zare wayan yayi daga kunenshi yasa a speaker yace "i can hear you inspecta kace mene?" "yallabai jami'an tsaro damuka baza a kowani anguwa ne muka sami wani information da safen nan dayasa muke bukatar kuzo kuyi comfarming ko shine" da sauri Mami ta fizge wayar daga hannun Aabid tsabagen yanda jikinta ke bari tace "inspecta anga d'ana?" anatse inspecta yace "abinda yasa nake neman ku kenan anga wani amma shi gaskiya ga dukkan alamu ba kidnapping dinshi akayiba kaman yanda muke zargi ba, dawata mace muka ganshi yanzu haka suna under our watch suna wani uncompleted building da ba'a gamaba awata sabuwar unguwa, na zuba jami'an tsaro da yawa a anguwan tayanda bazasu fitaba harsai kunzo kun tattance idan shine na hoton dakuka  bamu, dan gaskiya wanan yay datti sosai yay budu budu kaman mahaukaci ko takalmi babu akafarshi kawai nadai ga dan kamaninsa da wanan saurayin daya kawo case din offis ne saisa mukace bari mukira" da sauri Mami ta share hawayen dake zubo mata tace "i...ina...inane wurin?" "zan tura muku address din yanzu" ya katse wayar saukowa Mami tai daga gadon tai baya luuu zata fadi sabida rashin karfi babu abinci acikinta tun jiya da sauri Aabid ya riketa, Baffa ne yace "ki zauna agida bari mu muje" fashewa tayi da kuka tace "Baba dan Allah zanje" share mata hawayen Aabid yayi yadau mayafinta ya yafa mata yace "muje grandfather muje da ita" fita dukan su sukayi harda big mum, Kafin ma su shiga mota har inspecta ya tura musu address din location din suka shiga manya manyan jeep dinsu kusan guda uku sukaja suka sukabar gidan.


Tafiyan wurin 25min yakaisu anguwan, parking sukayi agaban junction din anguwan nan inspecta da sauran yaranshi suka fito daga inda suka boye, fiffitowa daga mota sukayi inspecta yakarso wajen yace "muje"..... 





Yanda yake wani irin shishigewa jikinta yana numfashi da sauri da sauri yasa ta tureshi tace "stop" make mata kafada yayi da idanunshi dasukai ja sundan kankance kaman zaiyi kuka yace "am sleepy" matsawa gefenshi tayi da sauri tace "to sleep ga fili nan" make mata kafada yasakeyi hawaye ya cicciko a idanunshi yace "i want to sleep on your body" yay maganan yana matsowa kusada ita gabaki daya idanunshi sun chanza kala, da sauri ta mike tsaye adan tsorace ganin yanda ya chanza, kadangare tagani abango da sauri ta matsa baya tace "wayyo lizard" kallon bangon yayi kafin ya fizgo riganta tabaya juyowa tayi da sauri ta kallai tamai pointing lizard din tace "come let's play with lizard, kadangaren babba ne sosai ko" tashi tsaye yayi shima batare daya saki riganta ba ya kalli lizard din sanan ya kalleta yanda yaga tana kallon kadangaren tana komawa baya alamun tsoron kadangaren take yasa yaturata da karfi yace "lizard catch her" ihu tayi sosai takoma bayanshi da gudu ya kyalkyace dawani irin dariya yana clapping hands dinshi yace "Hamida my wife is afraid of lizard" kaman daga sama idanunshi suka sarke dana Mami data fara kunno kai dakin.

_🌹 IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur



23 & 24


_This novel is for sale karki karanta in baki biyaba_


_in kinason this novel, xaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_you can also send MTN card ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_






Ware manyan fararen eyes dinshi yayi yana wani irin cute smile yace "Mami" daidai lokacin sauran mutanen duk suka iso sukai turus ganinshi tsaye yana kallon Mami dasu dasuka karaso wajen, dan duhun data gani dan sunyi blocking ray din rana dayake shigowa ta kofan yasa ahankali tadan leko da kanta daga bayanshi, mutanen data gani yasa da sauri ta komar da kanta bayanshi ta labe.


Sake zaro ido Aadil yayi sosai ya kalli Aabid dayay shiru yana kallonshi kaman yanda kowa na dakin ke kallonshi yanda yay mugun butu butu, wandon jikinshi kaman an kwaba kasa akai, kafarnan da babu ko takalmi ajiki tai busu busu, shimin jikinshi ma tai datti idanunshi sunyi suntum sunyi wani iri alamun yaci kuka, fashewa dawani irin Kuka Mami tayi ta shigo dakin da sauri tayo kanshi tace "Aadil, my baby" budema Mami hannu yayi yana wani irin jumping yana murna kaman dan yaro. "oyoyo Mami, oyoyo Mami, oyoyo Mami na" tana karasowa gabanshi yawani irin fadajikinta ya kankameta yana tsalle da kafa hakan ya bayyanar da Hamida dake labe abayanshi ta sunnar dakai kasa tama rasa ma me zatayi har wani soshe soshe take, kallon ta Mami da duka kowa na dakin suke yi barin ma Aabid dayaji gabaki daya numfashin shi ya tsaya chak, Cikin wata irin murya yace "Amatullah" da sauri ta dago kanta ta kalli direction din da aka kira sunanta daidai lokacin Aadil yasaki Mami shima yajuyo cike da murna yace "Mami look at Hamida, my wife" kallon Aabid Hamida tayi saikuma ta kalli Aadil dayay magana yanzun nan wani irin faduwa gabanta yayi bana wasa ba dan bambamcin da ayanzu tagani ajikinsu shine daya tsaf tsaf yake yaci shadda gizna kanshi sanye da hula tangaran, shaddar jikinshi har wani irin kyalli yake yana walkiya sai dayan kuma wanda yake daka daka yana sanye da singlet da dogon wando amma kamaninsu daya tsaf, kasa kallon sauran manyan mazan dakin tayi da tsohon dake sanye da glsass yana rike dayar Sanda tasake sunnar dakai tahade hannayenta dake wani irin bari tana murzawa da sauri da sauri tana numfashi sama sama. Sakin Mami Aadil yayi yaje dawani irin gudu yafada jikin Aabid  batare daya lura da yanayin dayake ciki ba yaja hanunshi yace "come, come and talk to My Hamida Bid" yaja hanunshi yakawo shi gaban Hamida da kanta ke kasa har lokacin tana murza hannuwanta yace "Bid see my Hamida" yasaki Bid yajuya da sauri ya kalli Mami daketa binshi da kallo kaman zata hadiyeshi da so yace "Mami see Hamida my wife" da gudu yay wurin Baffa yafada jikinshi wani irin murmushi tsohon yayi ya shafa kanshi yace "Hassan" da sauri ya dago kanshi yana turamai baki a shagwabe yace "Am Aadil grandfather not Hassan" sake bubbude manyan idanunshi yayi yakama hanun Baffan yace "zokaga My Hamida Baffa" da sauri yakawo grandfather wajen, sanan yakoma yana wani irin tsalle yana kallon Abie da idanunshi sukai jajir yanamai wani irin murmushi kaman ya cinyeshi da so yace "Abie come and see my Hamidaaa" yaja hanun Abie yakaishi wurin kafin yakoma ya kwaso duka Uncles dinshi yakaisu gaban Hamida sanan ya tsaya shima kusa da Aabid yana kallon Hamidan da duk suka tsaya suna kallonta babu wanda yay magana cikinsu yana murmushi yace "Bid u see my Hamida, she's my Hamida" wani irin murza hanunwanta Hamida take jikinta nawani rawa, murmushi Mami tayi tace "baiwar Allah a ina kikaga Aadil?" ahankali tadago kanta ta kallesu, wani irin jiri tafara gani yanda duk suke kallonta bakinta har rawa yake tana nishi sama sama tace "i...ina...na...w...wun..."  batakarasa gaisuwan ba tai wani irin baya a sume dan kwalin ta data lulluba dashi tai daurin ta wuya ya xame yay kasa arude Aabid ya mika hannu zai tarota yace "Amatullah! " arude Aadil yamika hanunshi zai tarota shima yace "my Hamida" da sauri Aabid yatarota Aadil ya tsugunna ya dafa kafadar Aabid yana kallonta yasaki kuka yana kallon fuskarta yace "wat happen to her Bid?" dagokai Aabid yayi yace "mutafi da ita gida Mami" da sauri Abie yace "munsan tane da zamu kwasheta mutafi da ita gida?" makemai kafada Aadil yayi yana goge kwallan dayake hakan yasa Baffa yace "muje akira likita yadubata koba komi ga Aadil nan yasaba da ita, daga gani ita ta taimake shi, kumuje, yaka Aadil" zuwa wurinshi Aadil yayi yana waigen Hamida da Aabid yadaga, Baffa yarike mai hannu duk suka dunguma suka fita daga wajen, saida suka salami su inspecta sanan suka shiga mota sai gida.




Wani hadadden daki Aabid ya shimfidar da ita kan makeken gadon dake dakin yana kallon fuskarta, tsugunnawa Aadil yayi gefen gadon yana kallonta shima idanunshi yay jajir, ahankali Aabid yajuyo da kanshi yana kallon yanda Aadil ke kallonta yana leka fuskarta, runtse idanunshi yayi da karfi yanajin ciwo aranshi sosai, daidai lokacin Mami ta shigo dakin karasawa tayi gaban gadon ta zauna ata saitin kafafun Hamidan tana kallon fuskarta tace "ga Dr nan zuwa ya dubata Baba yakira shi, Aabid stay with her karta tashi bakowa" ta kalli Aadil dake wani irin kallonta tamikamai hannu tana murmushi tace "come Aadil, muje kai wanka and change this cloth, kaima Dr zai dubaka inyazo duba friend dinka" make mata kafada yayi yana hararanta a shagwabe yace "she's my wife" shiru Mami tayi tana kallonshi saikuma tai murmushi tace "naji, muje kayi wankan to kafin kafito nahada maka abinci" tashi yayi ahankali kanshi narawa yana kallon Hamidan tashi itama Mami tayi taja bargo ta lullubeta dashi tarike hanun Aadil suka fice suka rufo kofan, wani irin runtse ido Aabid yayi yafuzar da iska kafin yadaura hanunshi kan zuciyarshi yana dukan zuciyarshi yay hakan kusan na 2min sanan yadawo daidai, zama yayi agefen gadon yay shiru yana wani irin kallon fuskarta, dawani irin murya mai rauni sosai yace "tayaya kika hadu da brother na Jewel? I'm the one for you Amatullah" yay shiru yana kallon fuskarta, knocking da akayi yasa yatashi yay wurin kofan bude kofan yayi Dr ne da Baffa suka shigo dakin, Baffa yace "yauwa gatachan likita adubata" karasawa Dr yayi bakin gado yaduba ta sanan yaciro drip daga katon jakan hanunshi yamata fixing yay allura aciki wurin 15 minutes yabata akanta sanan yajuyo ya kalli Baffa yace "fever ne kawai, i guess tsoron kune yasta ta suma, yanzu dai komi lpy dazaran drip dinan ya kare aciremata and yanzu dai bacci take zuwa anjima chan haka zata farka" murmushi Baffa yayi yace "masha Allah itace taga jikana ta taimaka mai, muje kadubamin jika" wucewa sukayi suka fita daga dakin Aabid yadawo ya zauna.


Duba Aadil Dr yayi yarubuta magungunan daza asayomai sanan yamai allura da kyar ya yarda akamai, yaci abinci nan wani baccin gajiya da wahala yay gaba dashi shima.




 Saida yay bacci sanan Mami tarufa mai bargo takashe wutan dakin nasu tarage karfin Ac tafito, dakin da Hamida take tawuce ahankali tabude kofan har lokacin Aabid na zaune agefen gadon yazuba mata ido, budewan kofan dayaji yasa yadago kai, murmushi Mami ta sakinmai takaraso ta zauna kusada shi, ahankali yadaura kanshi kan kafadarta ya sauke ajiyar zuciya, shafa kanshi Mami tayi tace "menene Son?" dan murmushin yake ya kakalo mata yace "babu komi Mami na" dagashi tai daga kafadarta ta kalli fuskarshi jin yanda yay maganan danta tabbatar da abinda ke damun shi, lumshe ido yayi da sauri dan yasan tsaf Mami zata gano da damuwa a idanunshi, ahankali kira sunanshi. "Aabid" bude idanunshi yayi ya kalleta, nunamai Hamida tayi da ido tace "you called her Amatullah dazu kasanta ne daman?" shiru yayi yana kallon fuskar Mami kaman bazaice komiba saikuma yace "eh nasanta a Lagos nataba ganinta tafada ruwa nacirota nakaita asibiti daganan bankara ganinta ba saiyau" murmushi Mami tayi tace "Allah sarki, hala saisa itama ta taimaki Aadil maybe tazaci kaine" murmushi tasakeyi tasake jan kumatun shi tace "tashi muje kaci abinci idan ta farka sai a gaggaisa da kyau amata godiya saimu maidata gidansu ko" gyadama Mami kai yayi yatashi suka fita daga dakin, dining ta kaishi tazubamai abincin kadan ya iyaci sanan yakoma ya zauna a falon yana kallon CNN amma gabaki daya hankalinshi nakan dakin da Hamida keciki.




Kiran sallan azahar dayaji yasa yatashi yafita masallaci hakanan yakejinshi wani iri yarasa mesa kalman da Aadil yafada saimai yawo yake a kunne. "Hamida my wife" runtse ido yayi da karfi da kyar ya lallaba ya shiga masallaci yaje yay salla sanan yadawo ya bude kofar dakin datake har lokacin bacci take, maida kofar yayi yarufe yakoma kan kujera ya zauna har akai la'asar yasake dawowa ya lekata har lokacin bacci take yakoma kan dogon kujera yasake zama yana chanza tasha zuwa tashan kwallo.


Bude kofan da akayi yasa yadago kai Aadil ne ke saukowa yana sanye da plain white t-shirt dakuma wani black 3quater sai uban kamshi yake yay wani irin kyau da inka kallai saika kara, hanunshi rike da manya manyan chocolate guda biyu acikin ledan su, Aabid daya gani azaune yasa ya washe baki yataho da sauri yana tsalle tsalle, shiru Aabid yayi yana kallonshi shi kanshi baisan meka damun shi ba hakanan yaji yanajin haushin shi bana wasaba yakasa manta kalman Hamida my wife dayafada aranshi, inda dane all this tsalle tsallen dayake yi idan yaganshi yanajin dadi amma yau sosai yakejin haushin shi, fadowa jikinshi da Aadil din yayi yasa yadan fuzar da iska yatureshi kadan, dago kai Aadil yayi yaleka fuskarshi yana murmushi, dan murmushin yake Aabid ya sakan mishi ya lumshe ido batare dayacemai komiba, hakan yasa da sauri Aadil ya kalli chocolate din hanunshi dudda ya daukoma kanshi ne da Hamida amma saiya mikamai daya da sauri yace "Bid" dan bude ido Aabid yayi ya kalleshi ya kalli chocolate din dayake mikamai, girgizamai kai yayi yatureshi murya chan kasan makoshi yace "stand up from my body" kin tashi yayi yay shiru yana kara leka fuskanshi kaman maiso gano abinda ke damun shi wani irin tsawa Aabid ya dakamai tareda tureshi da karfi daga jikinshi yace "nace katashi daga kan jikina ko" yay maganan yana tureshi dawani irin fushi yafadi akasa, atsorace Aadil ya kallai dan idan da abinda ya tsana a duniya yakuma kejin tsoro bai wuce tsawa ba, tsaki Aabid yayi cikin fushi yatashi yana kakkabe shaddar jikinshi da Aadil ya yatsine yawuce yafita daga dakin, binshi da kallo Aadil yayi idanunshi nataruwa da kwalla sosai, ahankali ya lankwashe kafa anan kasan falon ya shiga kuka yana share ido yana kallon kofan, kukan shi da Abie yaji yasa ya shigo dakin da sauri dan shigowan shi kenan gidan, karasowa yayi inda yake zaune akasa arude dan kowa nagidan nan ya tsani yaga abu nadamun Aadil yace "menene? Why are you crying" kasa bama Abie amsa yayi sabida yanda Aabid yaturashi kemai ciwo baitaba mai hakaba, da sauri Abie yaciro handkerchief daga aljihun shi ya sharemai bakinshi da fuskarshi yace "wai menene? Why are you crying haka?" kasa magana yayi sai kukan dayake yi sosai, sallama Baffa yayi ya shigo shashin da sauri daidai lokacin itama Mami tafito dan dama wanka take, da sauri Baffa yakaraso yana dogara sanda ya kalli Abie yace "me kuka mishi wai? Yaufa yadawo harkun fara sakashi kuka, dan Allah kome yakeso kudinga mai gobe za'a faramai maganin, daga sokoto mai maganinshi dana kira zaizo" ya zauna akan kujeran dake saitin Aadil din dake kuka sosai yake yadafa kanshi yace "menene? Waya tabamin Hassan iyye?" makemai kafada Aadil yayi cikin kuka yana turomai baki yace "my name is Aadil right Mami" dariya dukansu sukayi harda Baffan yace "dan tselen uwa gadai ubanka nan katambaye shi da aka haifeka Hassan aka yanka rago aka sakama, yanzu dai dena kuka kaji, zomuje mu baga basket ball" yay maganan yana zazzago glass din idanunshi cike da tsokana, Mami murmushi tayi ta tashi ta wuce kitchen dan kawomai fruits din data yankamai ta sakamai a fridge. Makema Baffan kafada yayi yana turo baki yana goge hawaye da bayan hanunshi dayake rike da chocolate da sauri Abie ya karbi chocolate din yace "kawo nan karka tsole idanunka dasu" turoma Abie baki yayi sanan ya kalli Baffan dake kallonshi yana murmushi ya makemai kafada yace "you don't know how to play basket ball bazan buga dakai ba, i will only play with Bid ko Abie" ya kalli Abie dayay shiru yana kallon d'an nashi feeling wani irin guilt, murmushi Abie yayi ya mikamai chocolate din yace "hakane, nabude ma chocolate din?" gyadamai kai yayi ahankali hakan yasa Abie yabude mai daya ya mikamai, karba yayi yakai bakinshi ya gutsura yanaci kallonshi Abie yayi kafin yatashi ya shafa kanshi yawuce yafita dan yanda yakeji yasa bazaima iya shiga gidan ba yawuce ya shiga motarshi yafita daga gidan, binshi Baffa yay da kallo ganin damuwa akan fuskarshi amma bai kawo komiba dan yasan damuwan bazai wuce ta Aadil bace, taba keyan Aadil yayi hakan yasa Aadil yajuyo ya kalleshi, gefenshi Baffa ya nunamai hakan yasa ya murgudamai baki sanan yatashi ahankali ya zauna a kusa dashi, hannu Baffa yamika mai yace "bazaka sammin ba" wanda yakeci ya mikamai hakan yasa Baffa ya makemai kafada kaman yanda yakema mutane yace "ni kabani wanchan sabon shi nakeso" makemai kafada Aadil yayi sosai yace "this one is for Hamida my wife" zaro ido Baffa yayi cikeda wasa yace "wife kuma Hassan" gyadamai kai yayi da sauri yana washe baki yace "yes i will marry her, she will be my wifeee, just like Abie and Mami" yakarashe maganan awani irin sangarce yana murmushi yana fari da ido sosai, shiru Baffa yayi yana kallonshi yama kasa magana tashi Aadil yayi daga kan kujeran yasa chocolate din a bakinshi ya ballomai yakamo hanunshi yasaka mai aciki yace "bye bye Oldman, lemme go and see My Hamida, Mami" ya kwalama Mami kira kaman zaiyi kuka yace "my fruits" fitowa Mami tayi daga kitchen tamikamai bowl dake cike da sliced fruits dasukai sanyi sosai da fork ya karba da gudu yana tsalle tsalle yay hanyar dakin Hamida Baffa yabishi da kallo har lokacin maganan da Aadil din yayi na ringing akanshi saikuma yay murmushi yaciro wayarshi daga aljihu yatashi yana dogara sandarshi yafice daga dakin yaje rumfan da akamai musamman ta zama ya zauna yay dailing wata number.



Tura kofan yayi ya shiga dakin yana rike da chocolate din gam da bowl din fruits din, hada ido yayi da Hamida da bude idanunta kenan, da sauri yatura kofan yarufe yazo wajen gadon yana tsalle ya ijiye fruits din agefe, wani irin farin ciki yakeji idan yaga fuskarta bana wasaba, ahankali ta dafe kanta ta tashi ta zauna da kyar tana kallon karin ruwan dake hanunta wanda kadan kadan yake shiga jikinta, wani irin tsalle yayi yafado kan gadon yana leka fuskarta yanda ta runtse ido, dawani irin murya chan kasa yace "My Hamida" ahankali tabude idanunta ta daura akanshi tai shiru tana kallonshi yanda yay wani irin kyau sai kamshi yakeyi farin t-shirt din jikinshi yakamashi daidaishi, murmushi yamata yamika mata sabon chocolate din hanunshi da sauri yace "take" sake lumshe ido tayi tana kara tuna irinshi biyu tagani fa dazu, ganin tai shiru taki karba ta shareshi kuma taki bude ido yasa yafada jikinta kaman zaiyi kuka yace "Hamida my wife wat is it? Are you sick?" da sauri ta bude idanunta ta shiga tureshi da hanunta daya mai lafiya cikin yar siririyan muryanta tace "kadagani" daidai lokacin aka bude kofa aka shigo, da sauri ta dago kanta tana tureshi sukai ido biyu da Aabid da shima ya chanza kaya zuwa black 3quater da white long-sleeve t-shirt dan hakanan yaji yanadan jin sanyi sanyi kaman zaiyi zazzabi wani irin kallo ya watsa musu yana tsaye a wurin yay folding hand dinshi akirji hakan yasa gabanta yawani irin fadi da hannu tasake tureshi tace "ka dagani Aadil" make mata kafada yayi ahankali yana turo baki yace "u are angry with me Hamida my wife" da sauri bakinta har rawa yake tace "a'a am not nika dagani" da sauri yadago kanshi ya kalli fuskarta yana wani irin murmushi yana kallonta yace "yay am happy my wife, take my chocolate" yay maganan yana ciro chocolate din dake bakinshi yakai saitin bakinta yana ware manyan eyes dinshi dawani irin excitement yace "d chocolate is very sweet Hamida my wife" yakai bakinta, kin bude bakin tayi ta kawad da hanunshi, kaman zaiyi kuka ya make mata kafada. "oh'oh" yasake kaiwa bakinta da sauri, kin karba tayi hakan yasa yasaki kuka yafada jikinta zai kankameta, wani irin fizgoshi akayi a zuciye da sauri ya juyo da kanshi hada ido yayi da Aabid da idanunshi sukai ja, kafin ma yace wani abu Aabid yawani irin fizgoshi kaman zai karyashi ita kanta Hamidan saida ta tsorota yawani irin jashi yafitar dashi daga dakin yabugo mata kofa yay dakinsu dashi, bude kofar dakinsu yay azuciye yawani irin turashi da duka karfinshi saura kadan ya buge kanshi a gado yadafa bangon yana haki, da sauri yadago kai ya kalli Aabid din daya mayar da kofa ya rufe yanamai wani irin mugun kallo, yayo kanshi a zuciye yana tattare hanun riganshi sama hakan yasa Aadil yakoma jikin bango a tsorace idanunshi yataru da hawaye sosai yana kallon Aabid din da mugun mamaki dudda baida Ishashen hankali hakanan saiyake ganin Aabid kaman bashiba yau, dan koda wasa ko amafarki Aabid baitaba koda dauremai fuska ba balle ya hankadashi haka cikeda tsana.




Wani irin tsayawa Aabid yayi agabanshi yay folding hanunshi akirji yana wani irin kallonshi, ahankali Aadil ya saukar da kanshi dake rawa sosai kasa hakanan yaji yana wani irin shakkan Aabid din for the first time in his life, ahankali kanshi na rawa sosai ya matsa ta gefenshi batare dayace komiba yazo zai wuce shi da sauri, wani irin fizgo hanunshi Aabid yayi azuciye yadawo dashi inda yake har saida yabuge bayanshi da bango cikin tsawa yace "where do you think you are going?" sosai idanunshi suka cicciko da hawaye kaman maison kara tantance anya Aabid ne wanan yadan dago kai ya kalleshi ganin shine dai yanamai wani irin mugun kallo yasa ya saukar da kanshi dake rawa sosai kasa cike da tsoro dawata irin murya chan kasa yace "i want to go to Hamida My wife's place" wani irin fizgoshi Aabid yayi yarikemai wuyan riga yace "karka kara cemata your wife" makemai kafada yayi ahankali atsorace hawaye na gangarowa daga idanunshi yace "i don't want to stay here, i want to go to Hamida my wife's place" cikin wani irin bakin zuciya Aabid ya sakeshi yadaura hanunshi kan belt din jikinshi yana kwancewa yana zarowa yana kallonshi yace "karka kara cemata your wife" makemai kafada Aadil yayi hawaye na fita daga idanunshi sosai yace "she's my wife i will marry her just like Abie and Mam..." wani irin zaulamai belt din Aabid yayi da duka karfinshi cikin fushi sosai yace "karka sake cemata your wife" makemai kafada Aadil yayi yafashe da kuka sosai yana sosa kirjinshi da cinyarshi da belt din yasama sabida azaba da zafi dayaji yace "Hamida is my wife" zaulamai belt din yayi da shegen zafi hakan yasa yay ihu cikin kuka sosai yana sosa wajen yace "stop beating me Bid" shima Aabid cikin ihu yace "kaima stop calling her your wife and  karka kara rungumeta, she's my Jewel" Make mai kafada Aadil yayi cikin kuka sosai yace "Hamida is my wife" wani irin mari Aabid ya daukeshi dashi da saida yaga wuta da jiri cikin wani irin layi idanunshi najuyawa sosai yace "she's my wife" bugashi da bango Aabid yayi ya shiga dukanshi sosai yace "kai mahaukaci ne, Aadil kai mahaukaci ne bazaka taba aure ba danba abinda kasani kanajina, u are mentally unstable, kai pagal ne stay away from my Jewel kanajina mahaukaci" makemai kafada Aadil yayi  yana fitar da numfashin da kyar yana kuka sosai yace "she's my wife" belt din daya yar yakara dauka ya shiga dukanshi sosai kaman uba da d'a yace "kai mahaukaci ne Aadil bakada lafiya bazaka taba auren ta ba, bakada any use a dis life, stop touching and hugging my Jewel, stop calling my Jewel your wife inba hakaba sainai ma shegen duka" make mai kafada yayi wanan karan yakasa magana tsabagen kirban shi da Aabid keyi, hakan yasa Aabid yajawo belt ya shiga dukanshi sosai Aadil na ihu yana kuka sosai yana rirrikemai riga yanaso ya rungumeshi. "stop beating me Bid, stop beating me please" bude kofan akayi Mami ta shigo ganin yanda Aabid ke dukan Aadil da belt yasa tazo wajen da mugun gudu. "Aabid, subhanallahi, innalillahi wa innailaihi raji'un, Aabid zaka kashe dan uwanka ne" tarike mai kafada tana kokarin rike belt din hanunshi tureta yayi ta hanyar fizge kafadarshi yacigaba da dukanshi Aadil dake ihu daidai lokacin Abie da Baffa sun shigo sabida hayaniya da salatin Mami dasukaji, wani irin fizgoshi Abie yayi yace "Aabid kana hauka ne?" fizge kanshi yayi daga hannun Abie yacillar da belt din yafara dukanshi da hannu Abie najanshi amma dukanshi yake yana neman gagaran Abie tsabagen karfi, wani irin tsawa Baffa yadakamai ganin numfashi na neman gagaran Aadil din, da gudu Mami ta daga Aadil din ta rungume tace "ka dakemu tare kaji Aabid" hannu Aabid yadaga zaikara kaima Aadil din duka dudda Abie na rikeshi Baffa ya daga sandarshi ya rafkamai akafa.




_Slm Fanmily_

_Daga yanzu typing system dina will change, zan dinga skipping a day but duk ranan posting zan dinga yin 2pages in sha Allah_.


 _Thank you_

_🌹IN BANI 🌹_ 





Maman Abd Shakur


25.....


_this novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan, your choice_



_masu fitarmin da novel waje kuda Allah_


_in kinason this novel zaki turo 300 ta 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_you can also send MTN card ta watsapp na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_





Har Aabid yajashi yafitar dashi daga dakin wani irin faduwa gabanta yakeyi takasa daina kallon kofan kirjinta nawani irin bugawa tanajin wani irin tsoro, ihun dataji na Aadil yasa ta dafe chest dinta danjin ihun tayi har karkashin zuciyan ta, sakejin ihun tayi tareda kuka hakan yasa tawani irin zabura ta sauka daga kan gadon tai hanyar kofa dagudu. "auchhhh" tai wani irin kara sabida yanda taji allauran dake jikinta yawani irin chakanta, ita gabaki dayama ta manta dashi, komawa da baya tayi ahankali jikinta na rawa sosai tasa hannu ta cizge kanulan dudda hanunta na jini amma ko damuwa batayiba, tai hanyar kofa tabude ahankali kaman wacce tazo sata tana kallon ko'ina, tunda take bata taba ganin hadadden palo hakaba, hanyar inda taji kukan Aadil sosai tayi zuciyar ta namata wani irin rawa babu kowa a shashin daidai gaban kofan datakejin kukan sosai ta tsaya takasa budewa. "kai mahaukaci ne, Aadil kai mahaukaci ne bazaka taba aure ba danba abinda kasani kanajina, u are mentally unstable, kai pagal ne stay away from my Jewel kanajina mahaukaci" da sauri ta runtse idanunta ta dafe bangon da sauri harcikin zuciyarta taji zagin. "she's my wife, Hamida is my wife" taji muryan Aadil saikuma taji wani irin karan saukan belt ne ko bulala oho, ihu da kukan Aadil taji sosai yafashe da kuka itama kukan tasaki batare data saniba ta daura hanunta akan kofan tanajin wani irin radadi da ciwo aranta, kwas, kwas, karan takalmi da alamun gudu dataji yasa arude tafara waige waige tana kuka sosai jikinta na rawa tana neman inda zata buya, wani babban hadadden flower verse silver data gani gefen kofar su ga hadaddun flowers aciki yasa tai sauri taje bayan verse din ta tsugunna talabe ta daga kanta ta flowers tana kallon kofan dantaga wazaizo ya wuce, Mami ce tazo da gudu hartana neman faduwa ta bude kofar dakin ta shiga da gudu taji Mami ta kwala kara. "Aabid, innalillahi wa innailaihi raji'un, Aabid zaka kashe dan uwanka ne" wani irin taushe bakinta tayi da hannayenta duka biyun dan bataso kukan datakeji yafito, karan bude kofan datasake ji yasa tasake dagakai ta leka ta tsakakanan flowers wani tsoho tagani da dan magidanci sun shiga dakin cike da tashin hankali, taji muryan namiji yace "Aabid kana hauka ne?" kukan Aadil tacigaba da ji dake fita da kyar kanajin sautin kukan zakasan ya galabaita bana wasaba, muryan Mami taji tace "ka dakemu tare kaji Aabid".... 





Rafkamai sandar Baffa yayi akafa da karfi, hakan yasa Aabid da idanunshi sunyi jazur ya dago kai ya kalli Baffan dan yaji zafin bugun, wani irin mari Baffan yadauke shi dashi kafinma ya farga. "pa, pa, pau" yamai guda uku, dafe kucinshi Aabid yayi ranshi a mugun bace kanshi akasa, Baffa ya nunashi da sandarshi yace "kasheshi zakayi Hussain? Nace kashe shi zakayi? Koma meyamaka bazaka iya hakura ba sanin halin dayake cikiba, jibi irin dukan dakamai saikace ubanshi ne kai, bai girmeka ba?!" Baffa ya dakamai tsawa yace "Hassan yarigaka shan iskan duniya sanan saigaka kaima kafito, kai wani iri ne, bakada imanine Hussain? Uban wa yataba dukanka haka aduniyan nan tunda aka haifeka? Hassan dake bala'in sonka kama mahaukacin duka haka Hussain?" Baffa yay maganan yana nunamai Aadil dake kuka sosai jini nabin gefen pink lips dinshi bama ya iya kuka tsabagen kukan dayaci sai ajiyan zuciyan kuka yake ajikin Mami, Abie kuma yadauko first-aid box yana kokarin budewa dan sharemai jinin dakenbin lips dinshi, shatin jini-jinin da Mami tagani ta jikin white shirt din dake jikinshi yasa ta daga Aadil din daga jikinta da saura taja riganshi sama shatin belt dahar dan jini jini ke fita daga fatanshi, daga ita har Abie dagokai sukayi suka kalli Aabid din da kanshi ke kasa, hawaye Mami ta share ta kira sunanshi cikin wani irin raunanniyar murya. "Aabid" dago kanshi Aabid yay ya kalli Mamin da jajayen idanunshi, hawaye ta kara sharewa tasake rungume Aadil din dake nishi da ajiyan zuciyan kuka ko motsin kirki baya iyawa idanunshi a kulle yay lamo a kirjinta yarike mata hannu gam yana nishi, ahankali tace "Aabid d...dan uwanka kama dukan mu...g..." kasa magana tayi sabida wani irin kuka dayazo mata sosai bakaramin tausayi Aadil din yabata ba jitayi da ita Aabid yama dukan nan dayafi mata sau dubu akan  Aadil mara lafiya wanda baimasan zafin kanshi ba, yaron da kullun suna hanyar asibiti dashine yama wanan dukan rashin imanin, share mata hawayen daya kasa daina zuba Abie yayi tsabagen bakin ciki da kuncin datakeji, kana Abie shima kasan ranshi abace yake, janye hanunshi yayi daga fuskar Mami bayan yagama share mata hawayen yace "is okay, barshi" ya dago kai yama Aabid din wani irin mugun kallo yace "wuce katafi abunka" kasa daga kafa Aabid yayi yafita daga dakin ko motsi yakasa saima kanshi dayakai kasa, cikin wani irin ihu Mami taja belt dinshi dake gefenta ta wurgamai belt din yafada kanshi tace "ance ka wuce kafita daga dakin  nan, kozaka hada damune kadaka eh zalim?" dan dago kai yayi ya kalli Mami zuciyarshi namai wani iri da sauri yajuya yafita daga dakin kaman zai tashi sama yay tsakar gida ya shiga mota yaja motar yabar gidan da shegen gudu.





Ahankali tafito daga bayan verse din tana kuka sosai ta tsaya abakin kofan so kawai take taga Aadil din da zuciyarta ke mugun kwadayin ganinshi. 

Gogemishi jinin gefen bakin Abie yayi yadan bude ido kadan yana kuka ahankali ya rirrike Mami, kiss Mami tamai a goshi jin yanda jikinshi yadau wani irin zafi sosai kaman an sakashi a oven, tsugunnawa Baffa yayi shima yana kallonshi yamika mai hannu alamun yazo kaman yanda akema yaro yana kallonshi, ahankali Mami tadaga kanshi daga jikinta tace "zakaje wajen grandfather, oya go" wasu irin hawaye ne suka bulbulo ta gefen idanunshi yana wani irin nishin kuka da karfi kaman mai asma dan abun nawani irin sosa mai rai, cikin muryan kuka sosai yace "Bid beat me Mami" yay maganan wasu sababbin ruwan hawaye na zubomai daga ido, dasauri Mami tawani irin rungumeshi tsam tsam tana jijjigashi sosai Aadil weak point dinta ne sosai, batason abunda zai taba innocent boy dinan, tunda tahaifi Aabid baitaba bata mata raiba irin nayau, sosai take jijjiga kanshi a kirjinta tana bubbuga bayanshi jin yanda yake wani irin kuka tace "is okay, ya isa kaji, mekamai yadake ka? Karka sake kashi" cikin kuka sosai yanayi kaman zai suma yace "Bid hate me Mami" da sauri Mami ta girgiza maikai tana neman yin kuka dan daurewa kawai take tasa hannun riganta ta sharemai fuska tace "no, no no, dont say that, Aabid bai tsanake ba, yana sonka sosai ko Baba" ta tambayi Baffa dake kallon Aadil din, gyadamata kai Baffa yayi yace "Aabid na sonka sosai kaji dan kirki" girgiza musu kai yayi zaiyi magana saikuma yafashe da kuka sosai tafada jikin Mami, tashi Baffa yayi da sauri dan wani irin zafin dukan da Aabid yamai  yakeji yajuya yay hanyar kofa yana dogara sandarshi, ko kadan bataji alamun tafiyan mutum ba sabida kukan datake sosai tana sharewa da bayan hannu, yanda Aadil keta maganganu yanatasa zuciyarta nawani irin karaya jitake kaman ta daukemai ciwon dukan, bude kofan Baffa yayi arude tai baya tana kuka sosai ta saukar da kanta kasa tana kokarin tsayar da kukan datake data kasa, binta da kallon mamaki Baffa yayi wearing a smile akan fuskarshi kafin ahankali yace "bakuwa kin tashi ya karfin jikin?" gyadamai kai tayi tadan dago kanta ta leka Aadil ta gefen Baffa dake tsaya abakin kofan, hangoshi tayi jikin Mami dake kallonta asanyaye da Abie daidai lokacin Aadil din yabude idanunshi dake buduwa da kyar sun kumbura sunyi jajir ya kalleta innocently, lumshe ido yayi ya budesu ya miko mata hannu daga inda yake da kyar tsabagen zazzabin dake cinshi, dawata irin murya dabata da kara sosai yakira sunanta yana mika mata hannu yace "My H..Hamida" fashewa tai da kuka sosai tana share idanunta da bayan hannu tana kallonshi yanda taga fuskarshi ya kumbura da lips, takasa koda motsi daga inda take ta daura hannayenta akan bakinta tana kuka, wani irin tausayin shi takeji bana wasaba,  sosai Baffa ke kallonta yana karanta wasu abubuwa tattare da ita kafin ahankali ya juyar da kanshi ya kalli Aadil din dake kuka ahankali yana kiran sunanta agalabaice yana mika mata hannu yana lumlumshe ido kaman mai shirin yin bacci, ahankali Baffa yasake juyowa ya kalleta yace "ki shiga ciki mana yarinya kin tsaya anan" gyadamai kai tayi tana share hawayen datakey, Mami ma murmushi tayi tana kallonta tama kasa magana, ahankali tafara tafiya Baffa ya matsa mata ta shigo dakin Abie yay shiru yana kallonta harta karaso tsakiyan dakin ta tsugunna ata gefe tana kallon Aadil din tana kuka, wani irin tashi Aadil din yayi daga jikin Mami ya rarrafo da kyar yakaraso inda take ya tsaya gab da ita yana kallonta, fashewa tai da kuka sosai tana kallon fuskanshi, fadawa yayi jikinta yasaki kuka sosai itama kuka tasaki tana girgiza mai kai, ahankali ta ciro kanshi daga jikinta tai cupping face dinshi tana kallonshi, lumshe mata ido yayi hawaye suka zubo, murya chan kasa ta kuka yace "Bid beat me" yasake sakin mata wani kukan, girgiza mai kai tayi takai hanunta ahankali ta sharemai hawayen dake zubowa tace "stop crying okay" make mata kafada yayi yawani narke mata hakanan yaji yanajin wani iri farinciki sosai, ahankali tana kuka sosai dan kawai tasashi murna tace "where is my chocolate?" ware manyan kumburarrun idanunshi yayi yace "i don't know, I've lost it wen Bid was beating me" gabaki daya tama manta dasu Mami na wurin burinta kawai yay shiru yadena kuka yadawo normal Aadil daya iya damunta, hararanshi tayi ta murguda mai baki tace "find it" wani irin bude ido da baki yayi yana kallonta saikuma ya leka nose dinta kaman ba shine yaci duka yanzun nanba yace "ur nose is a robotic nose" murmushi tayi sosai daya bayyana dimple dinta da sauri ya daura hanunshi kan hancinta yaja yana dariya yace "do it again, saikin kara yimin" dariya tayi ta fizge hancinta shima yay dariyan yana clapping hands dinshi, Mami, Abie da Baffa duk sukai shiru suna kallonsu kowa da abinda yake kawowa aranshi daidai lokacin Suleman yazo wajen, hanunshi Baffa yaja batare daya bari ya shiga dakin ba suka bar wajen yace "Baba har yarinyar ta tashi ne" gyadamai kai Baffa yayi suka karasa falon Baffan, zama Baffa yayi akan kujeran zaman yi yay dan shiru nayan sakanni, shiru Suleman yayi dan yasan inhar Baba na tunani bayason anamai magana, dan ajiyan zuciya ya sauke ya kalli Suleman yace "Sulemanu" da sauri yace "na'am Baba" gyara zaman shi yayi yace "inaso kamin binciken yarinyar nan, wanan bakuwan data taimaki Aadil, inaso nasan wacece ita, sanan inaso nasan iyayenta dakomi nata daga nan zuwa gobe" gyadamai kai Suleman yayi yace "shikenan Baba angama, amma Baba mezakayi da information dinta haka?" shiru yayi saikuma yay murmushi yace "time will tell, kaidai kamin abinda nace".

_🌹IN BANI 🌹_ 



Maman Abd Shakur



26....



Agaban wani babban club Aabid yay parking yabude mota yafito kanshi harwani irin zafi yakemai kaman zai tarwatse tsabagen bacin ran dayake ciki ya juya ya shiga ciki, gaban counter yaje ya zauna ya kalli waiter dake aiki a wurin yana kokarin serving wasu samari dake kallonshi yace "meza akawo ma Sir?" dan bude ido yayi kadan ya kalleshi kafin ahankali yace "rum" da sauri guy din yadauko wani kwalba yabude yazuba awani dan karamin kofi zai mikomai, hararanshi Aabid yayi da jajayen idanunshi kaman wuta yace "give me the whole bottle" mikamai bottle din yayi ya fizge da sauri ya kafa abaki ya kurba yana yatsine fuska yacigaba dasha saida yay kusan rabin goran sanan ya janye daga bakinshi yana zaro manya manyan idanunshi kanshi kaman zai fashe tsabagen chajin daya dauka, da kyar yay relaxing bayanshi ajikin kujeran ya lumshe ido yakafa goran rum din abaki yana tunane tunane.



 _Asalin su_ 


Alhaji Muhammadu Gambo Sawaba (Baffa) shararren business man ne mai kirki bana wasaba, ga taimakon mutane, talaka, marayu da mabukata, babu inda zaka shiga afadin garin  kano ka ambaci sunanshi daba'a sanshi ba, matanshi biyu a duniya Rukayya da Maimuna, Rukayya itace ta haifi yaranshi maza guda uku, sai Maimuna wacce itace ta haifi Mami da Big Mum, yarane dasuka taso cikin gata da kulawa kome sukeso shi mahaifinsu ke musu kansu ahade. Kullum akwai direban dake kaisu school yaje yadauko su, lokacin islamiyya ma yakaisu yadauko su.


Kafin mahaifiyarshi ta rasu, akwai lokaci ta tattaro yinata yinata ta dawo birni gidanshi da zama tareda wani marayan yaron makwabcinta a kauye mai suna Abdullahi (Abie), Abdallahi yarone mai natsuwa da hankali wanda akalla zai girmi babban dan Baffa Suleman da shekara daya ko biyu. Tunda tadawo gidan da zama da Abdullahi ta damkama Baffa shi tacemai tanaso yarikeshi amatsayin danshi, gashinan amana, iyayen shi sun rasu, karya bambamtashi dasu Sulemanu, tabashi shine sabida koda tafadi ta mutu tasan yana hanunshi da zama, Baffa baimata musu ko jayayya ba ya karbi yaron dan yaron badai natsuwaba, nan Suleman da Abdullahi suka shaku suka zama abokan juna suna zuwa makaranta tare both boko da islamiyya dudda sun fishi aji.


Bayan wasu yan shekaru sun gama makaranta alokacin Baffa kuma yanso yay retire saiya daura Suleman baban daddanshi shugaban kampanin shi duka ukun, yasa sauran yaranshi maza biyu da Abdullahi duk a kampanin yabasu office suna aiki ana biyan su duk karshen wata makudan kudi, abin bakaramin ciwo yama Abdullahi ba yaso ace shine zai Baffa yabama shugaban kampanin dan yafi Suleman kai a business, banda haka yanada mugun sha'awan yaganshi yazama shugaban kampani, hakanan ya tattara ya watsar da zancen amma abin na nan ranshi ras duk idan yatuna har kuka yakeyi a boye yace wato sabida shi ba danshi bane saisa baibashi shugaban kampanin shiba ko bakomi shima zaiyi kudi wataran, ana haka wani irin soyayya ya kullu tsakanin Abdullahi da Mami bana wasaba, Allah ya dauramai wani irin soyayyan Mami bana wasaba.


Akwai ranan da Baffa yay order wasu hadaddun motoci toyota camry alokacin ana yayyin su yabama duka yaran nashi daidai as end of the year prayer gift amma banda Abdullahi yacemai shi tashi bata isoba, kuma harga Allah bata iso bane dan Baffa yaso yay surprising dinshi ne yatabaji yana hira da Suleman yacema Suleman shi yanason babban mota arayuwan shi jeep na burgeshi  hakan yasa Baffa yaso yay surprising nashi kodan jarumtar shi a kampani yabashi shi jeep amma sai tashi bata isoba dan ba'a gama yima motar custom duty ba harsai next week, nan fa bayan komi yadan lafa Abdallahi yasaci hanya yafita daga gidan yatafi kampanin su yadinga kuka yanajin bakin ciki sosai yana zagin rashin kudi da zama a karkashin wasu, dafashi yaji anyi da sauri yadago kanshi wani inyamurin gateman dinsu ne yagani yana sanye da hadadden suit baki, murmushi yamai yace "kasoma gane basu sonka ko Sir? Kawai amfani suke da talent dinka suna making money a kampanin nan" da sauri ya kalleshi yace "ya akayi ka sani?" murmushi yayi ya kalli ko ina na wurin kafin yaciro wata yar Kati daga aljihun wandonshi ya mikamai yace "inhar kanaso yau yau dinan rayuwarka ta chanza from this poor man dakekeci a gindin wasu kana musu boyi boyi kaima kai kudin bala'i, kudin da sunema zasu rokeka, inhar kanason money and fame, kanason dukiya, kanaso kafada aji kahana ahanu, kanaso kadawo yaro mai gari a hannu to ka kira number nan da kagani ajikin katin nan, Ozo zai biyama bukataun ka, zakai kudin ban mamaki, kudin dasu kansu saisun koma suna rokon ka kudi.



_Manage this guys, nai typing duka ya goge, da kyar na iya nai wanan yanzun nan, gobe kuna bina bashin daya in sha Allah_.

_🌹IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur



27....


 _Cigaban labari_



 Baki yasaki yana kallon gateman cikeda mamaki yama kasa cewa uppan, murmushi gateman yayi yace "kaga tafiyata dama resignation letter na nazo nabasu kai baka ganni ba level don change, nima wani yamin hanya wanan harkan, dazaran ka shirya kaima kawai kiran number kadai zakayi, nina gayama har gidana zakazo kamin godiya sabida gatan danama, sai anjima" yawuce yay gaba yana wani irin tafiya irin na masu kudi dinan Abie yabishi da kallo kasa tashi yay daga wurin sai kallon katin yake yana jujjuyawa har aka kira sallan magrib yatashi yaje yayi yajira har akai isha'i yayi daganan yakoma gida ranan kasa baccin dare yayi sai tunane tunane yakeyi yakira ko kar yakira, shidai harga Allah yanason yyi kudin nan kodan yanuna Baffa baidamu da kudin suba hasalima saidai su sudinga begging nashi, har gari yawaye yatafi masallaci baibar tunane tunane va, arana na uku ne ya yanke shawara zai kiradai kodan yaga me gateman kecewa idan ma karyane yagano, Motar gida daya sabaja yadauka yafita daga gidan ya gangara chan wajen gari yay parking motarshi ya kashe sanan yaciro wayarshi yadau katin ya kwafe number jiki yay dailing number, ringing daya wayan yayi kawai saiyaga wani irin duhu a idanunshi daganan kuma bai karasanin inda kanshi yakeba yadai farka yaganshi a wani jan daki yana sanye da jan riga akwance akasa, saiga wasu mutane sun zagayeshi daga cikinsu harda gateman suna rike da jajayen candle dake ci da wuta suna wasu irin wake wake suna zagayeshi, kasa koda motsin kirki yayi tsabagen yanda jikinshi yahau rawa yamugun tsorata kaman daga sama yaji ankira sunanshi. "Abdullahi yakira Ozo, Ozo ya amsa mishi saki jikinka kafada ma Ozo mekake so" tashi yayi zaune daga kwanciyan ya kankame jikinshi ko ina na jikinshi narawa sosai yama kasa daga kai ya kalli kowa hanunshi nawani irin rawa jikinshi na kakkaurwa yace "dan Allah kuyakuri dama inaso nayi kudine amma yanzu nafasa, banison kudin tsafi dan Allah kumaidani gida" wani irin dariya akayi kaman zai fasa dakin saikuma akai wani irin nishi kaman na zaki. "ba'a kira mana Allah anan ka kiyaye, dazaran mutum yakirani babu gudu babu komawa baya ka shiga ka shiga ne baka isa kafita ba, inda kasan bakaso da tun aranan ka yarda katin baka kiramu ba" hanunshi yakai baki jikinshi narawa sosai yace "natuba, natuba, ayakuri, amin afuwa, wlh banison kudin tsafi" wani irin dariya akayi dake kama da tsawa akace "nine Ozo duk wanda yakira ni yanemi sanan yace yafasa to motar nan dakasan ka kirani aciki, anan yan uwanka suzo su dauki gawanka tsotse jinin ka zamuyi tsaf dama ga jininka nan mai karni ne jinin virgin, daman irin wanda nake nema kenan jinin musulmi virgin" abun dayaji yana zuba daga ka sanshi yasa yabude ido da kyau yaga ashe fitsari yake, "Abdullahi" a firgice yadago kanshi yace "na...na'am" dawata irin murya kaman nayar jaririya yaji ance "step forward" gabaki daya organ din jikinshi karkadawa suke yay nadaman dailing number dayayi ahankali yamike tsaye kafarshi bankarewa sukeyi tsabagen tsoron dayake ciki yana tafiya kaman wani kwashoko yay gaban dakin yakasa daga kanshi haryakai gaban dakin da candles kenan dayawa da gumaka kanshi akasa. "ka daga kanka" yaji anfadi cikin wani irin kakkausar murya da sauri yadaga kanshi wani kwarangwal yagani agabanshi yamikomai wata yar karaman kwarya da abu keciki ja kaman jini, ihu yayi zaikoma baya yaji kafafunshi sunkasa motsi kaman yataka gum, yafashe da kuka cikin wata irin murya mai echo yaji ance "karba kasha" kasa mika hanunshi yayi tsabagen tsoron kwarangwal din mai jajayen idanu, hanunshi yaji ana kaiwa saitin karyan yadaiga ya karbi kwaryan amma baisan tayaya ba yadaiga hanunshi ya amshi kwaryan yakai bakinshi wani irin yatsine fuska yayi yanajin wani iri amai natasomai haka yaga abun kaman ana controlling dinshi yabude baki da kyar yafara shan jinin hawaye nafita daga idanunshi, ahaka ya shanye na kwaryan tass, wani irin sanyi yaji cikin jikinshi tundaga yatsarshi har cikin kwakwalwanshi kafin idanunshi suyi wani irin ja yazaro su saikuma sukadawo farare, dariya dakin yadauka sauran mutanen sukace "welcome to the family, money and fame duka nakane ayanzu" shiru sukayi sabida wani hadadden zobe da kwarangwal din yadauko yakawo saitin hanunshi, ahankali yamikamai hanunshi yanajin wani irin farin ciki yasakamai ring din jikinshi yay wani irin kara saikuma yadawo daidai, daga sama yaji magana. "welcome to the family Tursoso, kudi saidai idan kaine kace sun isheka, Ga zoban kanan koda yaushe ka bukata zai maka aman kudi, wanan cult din mai adalci ne babu bukatan wani abu babba kuma bamu tsanan tawa kasani cewa duk randa ka haifi d'a namiji, danka nafarko namune, namune, namune " nan yace ya yarda haka yakoma gida ya shiga dakinshi ya kulle ya xauna akan gado yanaso ya gwada ya kalli zoben yatsar tashi yace" kudi", ko gama ambata baiyiba zoben yafaramai aman kudi dahar saida yaji tsoro ya tsugunna yana tumurmusan kudin yana ihu yana murna yana mamaki yanzu wanan duka kudin shine, nan ya tatatra kudin yazuba a ghana masgo kusan biyu ya cika yafara tunanin karyan dazai shigo yafadi cewa ya sami wani aiki ne, wani paper ne yaga an wurgo akanshi da sauri ya chabe yaga job offer letter ne nawani kampanin sport cars ihu yay najin dadi yace thank you Ozo the great one, washe gari ya nunama Baffa sosai duka yan gidan sukaji dadi nan Baffa yace tunda hakanr za'aska ranan bikin shi da Mami kafin yatafi haka aka saka wata biyu yatafi UK abinshi yana fanchakala da kudi yabude wani durmemen kampanin motoci inda har kira motoci akeyi aikuwa fame yasamu dan kusan kowa na UK din saida ya sanshi lokacin bikin shi yakoma ya auro Mami yadawo suna zama na soyayya dan sosai Yakesan Mami yanadai ta addu'a kartasami ciki, bayan shekara daya.




Kwatsam Mami tasami ciki sosai cikin ke bata wahala bana wasaba haka suka cigaba da rainon cikin, cikin nawani irin girma, ko kadan baida kwanciyan hankali dan tun kafin yaga mezata haifamai Allah ya dauramai son cikin bana wasaba sai fargaba yake har bayason ranan haihuwan tazo haka wani Friday night Mami ta tashi da serious nakuda ya kwashe ta sai wani babban asibiti, takai kusan awa biyar da kyar ta sullubo yaranta maza, biyu Hassan akafara shiryawa aka fitomai dashi nannade a towel sosai gabanshi yawani irin fadi yana addu'a Allah yasa mace ce banamiji ba, karban yaron yayi ahankali jikinshi a mugun sanyaye ya kalli yaron ganin namiji ne, yaron gwanin kyau jajur dashi bulbul ahankali ya sumbaci goshinshi kafin ma yazare bakinshi daga kan goshinshi yaji wani irin sanyi duk idan Ozo zai bayyanar mishi haka yakejin irin sanyin nan, da sauri yadaga kai hada ido yay da Ozo daya tsaya a jikin bango, shi kadai ke iya ganinshi duk sauran mutanen dake waje da fice basu ganinshi, wani irin hawaye ne suka gangaromai yana kallon Ozo, ahankali Ozo yay pointing babban yatsarshi ajikin Aadil wani irin farin hayaki ne yafito daga jikin Aadil din yataho wajen Ozo, Ozo ya bude wani kwalba hayakin ya shiga ciki duk Abie na kallo hawaye na zuba daga idanunshi, Ozo yarufe gwangwanin yabace bat daga bangon, wani irin nishi Aadil yayi dake kan hanun Abie  wani kumfa yafara fitowa ta bakinshi da hancinshi ihu Abie yayi arude. "nurse, Dr my son is dying, somebody help" dagudu  Dr na nurses suka fito daga labour' room din suka karbi Aadil Dr na jijjiga yaron adan rude, dawani irin gudu Abba yajuya kaman mahaukaci yafita daga asibitin yana sumbatu i don't want my baby boy to die, gida yakoma ya shiga wani underground secret room dinshi dako Mami batasan dashiba yay kiran Ozo wanda da kyar ya bayyanar mishi, da kyar ya shawo kan Ozo akan karya kashemai Aadil nan Ozo yace yaji ya yarda amma ga yanda zai komar da yaron gakuma sharudda yace duk yaji kuma ya yarda ya kuma amince.


Da kyar likitoci suka ceto Aadil, Mami kuka harta godewa Allah, ta rungume Aabid tsam tsam a jikinta, tundaga ra nan ake fama da Aadil yau lafiya gobe ciwo, yaron Allah yasamai wani irin shiga ran mutum tun yana yaro, duk likitocin shi bakaramin sonshi sukeba, haryazo ya girma yana abin yara bama sutaba zatan zaiyi girma yakai hakaba, babu asibitin mahaukata duniya dabasu jeba. Allah yadaura musu wani irin son yaron bana wasaba daga Abie har Mamin. 


Koda wasa Abie baitaba yin abin dazaisa Mami ko wani nashi ya zarge shiba, asibitoci kuwan shida kanshi yakekai Aadil din.  Wanan kenan.



 _Cigaban labari_

_🌹IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur



28 - 29


_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta keda Allah_


_in kinason this book zaki turo 300 ta 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_



_you can also send MTN card 300 ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_


_masu fitar min da novel waje kuda Allah, kunma kanku_





Sosai Aadil yake clapping hands dinshi yana murmushi yana dariya kaman bashine yagama kuka yanzun nan ba, wani irin murmushi Hamidan tayi tana kallonshi dan jitayi dariyan dayake mata means everything to her, looking at the way he's doing yanzu yana smiling da swollen eyes dinshi yasa taji ta manta da duk wani bakin ciki da tsoron datake ciki all she sees is Aadil yana mata murmushin dake sanyaya mata rai tama manta dasu Mami da Abie dake wurin, hanunta ya karba da sauri yana kallo, zaro ido tayi tana kallonshi asanyaye, yatsun ta yafara kirgawa yana murmushi sosai yace "your fingers are fine, and they're so fair" dan murmushi tayi tanajin wani irin tausayinshi ta mikomai dayan hanun ahankali, da sauri yahadasu yana kirgawa yana dariya sosai, shiru Mami tayi  takama habanta tana kallon Aadil din da kyaykyawan yarinyan dayake wasa da yatsunta suna magana kasa kasa  dan kosu basujin mesuke fada Aadil sai dariya yake kyalkyacewa kaman ba gobe. Dan lumshe ido yafara yakai hanunshi yana sosa saman idanunshi hakan yasa tace "you are sleepy" gyadamata kai yayi ahankali yanajin wani iri sanyi da sauri ta nunamai kan gadon tace "zoka kwanta" make mata kafada yyi yace "you will run away" da sauri ta girgiza mai kai tanajin wani iri kaman tamai kuka tace "bazan gudu ba i will be here, zoka kwanta" tashi yayi ahankali kanshi narawa jikinshi namai mugun ciwo ya kwanta akan gadon yasaka kanshi ta wajen saitin kanta yana kallonta, ahankali yamiko mata hannu yace "promise u will not go away" yatsarshi dayake miko mata ta kalla tace "yes" murmushi yayi dayama fuskarshi wani irin kyau dawata irin murya kaman na dan karamin yaro yace "thank you Hamida my wife" yay maganan yana kamo hanunta yarike gam ya lumshe ido yana hamma wani irin wahalallen bacci yay gaba dashi, Sai alokacin ta sauke wani irin ajiyan zuciya, "sannu da fama" Mami tafada ahankali, da sauri ta dagokai ta kalli Mami wani irin kunyan matan taji tanaji hakan yasa ta sunnar da kanta kasa da sauri tanajin wani irin kunya dakuma nauyinta, ahankali tace "ina yini" murmushi Mami tayi tace "lpy lau, mungode sosai kinji Allah yabaki lada a ina kika ganshi?" kanta akasa batare data dago ba tace "awanan anguwan na ganshi yanata bina na tambaye shi inane gidan su baifadamin ba tun jiya nasoma yadawo gida" ahankali Abie yace "angode yakamata kizo kitafi gida kar'a nemeki" dan kallonshi Mami tayi gyadamata kai yayi yatashi Mami ma ta tashi tana kallonta tace "zauna bari na kawo miki abinci da mayafi idan kikaci saimu tafiko" gyadamata kai tayi ahankali a kunyace, Mami tajuya tareda Abie suka wuce suka fita daga dakin.




Ahankali ta waigo ta kalli fuskarshi bacci yake sosai yana sauke ajiyan zuciyan kuka dake wani irin taba ranta yay wani irin kyau gashin idonshi dogaye bakake sosai sunyi lub lub dasu, hancinshi dogo dan siriri ya tsaya a fuskanshi das, sai lips dinshi pink sosai gasu sunyi moist, shiru tayi tana kallonshi kirjinta nawani irin bugawa, ahaka idan ka ganshi bazaka taba cewa baida lafiya ba, yanada wani irin kwarjini a fuska bana wasaba dabaka iya jure kallonshi for long unless idan yana haukanshi, janye idanunta tayi daga kan fuskarshi jin yanda gabanta kefadi tajuya tana kallon dakin, dakin hadadde ne bana wasaba gadon makeke ne sosai guda daya an shimfida white bedsheet ajiki, juyawa tayi tana kallon bangon dakin ta saukar da idanunta kan katoton hoton bangon dake makale a bangon dakin, inda Aadil din da Aabid suke a tsaye sunsa fararen shadda iri daya kaman ma ranan salla ne dan Aabid na rike da dadduma, shiru tayi tana kallonsu ta iya gane bambamcin sune sabida chocolate da Aadil yake rike dashi a hannu kafe Aabid tayi da ido wanda ke rike da dadduma tana tuna ranan dasuka hadu dashi a lagos, ahankali ta lumshe ido kafin ta bude tasake kallon fuskar Aadil ajikin hoton tana jin wani irin sanyi na shiganta. "baki taba sanin yan biyu bane bako?" taji magana akanta da sauri ta dagokai Mami ce ta shigo dakin wayansu masu aikin gidan biye da ita guda biyu suna dauke da tray a hannu, nuna masu gabanta Mami tayi tace "ku ajiye anan" ajiyewa sukayi suka wuce suka fita daga dakin sukamaida kofa suka rufe, ahankali Mami ta zauna a gefenta taidan murmushi ta kalli fuskar nata tace "twins ne wanan ne babba shine Hassan" ta nuna Aadil dake bacci tadan shafa kanshi tai shiru jin jikinshi da zafi, ahankali ta janye hanun tace "dayan kuma shine Aabid, dukansu haka sukeda zuciya barin ma wanan" ta nuna Aadil tace "yauma bansan meya faruba, dan Aabid dawuya kiga fushin shi, inata miki surutu ko baki fadamin ba ya sunanki?" ahankali kanta akasa tana wasa da yatsun ta dan hakanan taji tanajin kunyan matan tace "Hamida" ahankali Mami tace "suna mai dadi amma asalin sunanki kenan?" girgiza mata kai tayi tace "sunana Amatullah" "masha Allah wat a nice name, wani mataki kike a karatu?" wasa ta shigayi da yatsunta tace "100 level Islamic studies" "masha Allah, oya ci abinci karya huce kinji daughter na" gyada mata kai tayi ta kalli uban tilin abincin tarasa mema zataci da kyar ta mika hannu tadau spoon ta dau plate hanunta na rawa takasa diba, ganin haka yasa Mami ta karba tace "kawo nai serving dinki tunda kunyana kikeji" zuba mata white rice din Mami tayi a plate tazuba pepper soup din asama ta mika mata ahankali ta karba tace "Allah amfana" murmushi Mami tayi dan taji dadin addu'an tace "Ameen Amatullahi" diban abincin tayi tai Bismillah takai baki duk Mami na kallonta tana yaba natsuwan yarinyar da kyar ta iya tai 5 spoon sanan ta ijiye ta dau ruwa tasha batare data taba juice din wurinba tace "nakoshi nagode zan tafi" "kai dan Allah daughter bakici dayawa ba" girgiza mata kai tayi tace "nakoshi" gyadamata kai Mami tayi tace "Tom ina zuwa bari nazo saimuje mu saukeki daganan mayima iyaynki godiya" gyadamata kai tayi gabanta na faduwa, fita Mami tayi daga dakin ba jimawa yan aiki suka shigo suka kwashe kayan abincin, juyawa tayi tasake kallon Aadil dake bacci hakanan taji bataso ta tafi ta barshi tasan idan yatashi saiya nemeta, kafeshi tayi da ido tana kallonshi daidai lokacin Mami tabude dakin da sallama ta shigo kallon Mami tayi, Mami takarso ta mika mata wani hadadden black gyale tace "gashi ki yafa" karba tayi kanta akasa tace "nagode Mum" murmushi Mami tayi batare datace komiba, ahankali tamike tsaye ta yafa gyalen kaman yanda taga su Zainab nayi sosai gyalen yamata kyau Mami tace "masha Allah yako miki kyau, muje" gyadama Mami kai tayi Mami tai gaba tana binta abaya harsunkai bakin kofa takasa daurewa saida tajuyo ta kalli Aadil din dake bacci sosai da sauri ta goge hawayen dake neman zubo mata  tasakai tafice tarufo kofan ahankali suka fito tsakar gida sai sunnar dakai take Mami ta bude mata bayan mota ta shiga ta zauna Mami ta zauna agaba Abie yatada motar yaja sukabar gidan, sosai gabanta ke faduwa itato ina zata kaisu yanke shawara tayi gidan Anty Lami haka tadinga nuna musu hanya har zuwa gidan Anty Lami dake ta wuraren gwamna road har zuwa kofar gidansu suka sauko daidai lokacin ana kiran sallan magrib fitowa sukayi daga motan Abie yarufe motan ya kalli Mami yace "ku shiga ciki bari in shiga masallaci" ya mikama Mami key dan akwai abubuwa acikin boot din, yanda ta tsaya gefen Mami kanta akasa tana wasa da yatsunta yasa Mami tace "muje daughter" gyada mata kai tayi tabude kofar gate din ahankali ta shiga Mami biye da ita.






Babu kowa a hadadden tsakar gidan sai tulin textbooks dake kan wani table da alamu yaran homework suke sun tafi masallaci, sallama tayi ahankali tabude falon ta shiga babu kowa ciki ta kalli Mami dake tsaye tana kallonta tace "ki shigo Mum" gyadamata kai Mum tayi tai sallama ta shiga ta zauna akan kujera hakan yasa tai ciki da sauri sallama tayi agaban dakin Anty Lami daidai lokacin anty Lami na sallame salla ta juyo da sauri ta ware ido tana kallonta daga sama har kasa takama haba cikeda mamaki tace "Hamida!" kasa amsawa Hamida tayi saima kasa datai da kanta tana wasa da yatsunta, cikin mugun takaici Anty Lami ta tashi daga kan dadduman tana gyara daurin zanin jikinta tace "ba magana nake mikiba kinyi shiru tun safe mahaifiyar ki ke kirana taji kokinzo nan bakizo ba Hamida, ina kikaje kodai mazan kika farabi da gaske? Ina kikaje Hamida" girgiza matakai tayi ahankali tasa bakin gyalenta ta share hawayen dasuka zubomata, tsayawa kallonta Anty Lami tayi ta rungume hanunta akan ciki cike da mamakinta tace "hala namiki wani abune dakike min kuka?" girgiza mata kai tayi ahankali. "to menene?" cikin muryan kuka tana goge ido tace "ana nemanki a falo" zaro ido Anty Lami tayi tace "wakika kawomin gida?" tai maganan tana zuwa hanyar falo da sauri ta yaye curtain ganin kamilalliyar mace cikin shiga ta alfarma zaune akan kujera tana fira da yaranta maza guda uku su Ra'is dasuka dawo daga masallaci tana murmushi yasa tasaki labule da sauri ta kalli Hamidan dake gefen ta tace "ke wacece wanan ni yatsu? A ina kika samo wanan hajiyan Hamida?" ahankali tace "nima bansan suba, maman yaron ne" da sauri Anty Lami tace "yaro? Au wai wanda aka ganku tare?" gyadamata mata kai tayi ahankali da sauri Anty Lami ta yaye curtain tafita fuskarta cikeda murmushi tace "barka da zuwa" dagokai Mami tayi da sauri ta mike tsaye, da sauri Anty Lami ta nuna mata kujeran tace "please sit, ki zauna dan Allah" zama Mami tayi ahankali tace "ina yini ina gajiya" cikeda fara'a Anty Lami tace "Alhamdulillah, maraba, sannu dazuwa, Hamida" ta kwalama Hamida kira ta kalli yaran nata dake kallon cartoon tace "kutashi kutafi dakinku, ku kiramin Hamida daga nan" tashi sukayi sukai ciki ba'a jimaba Hamida tafito kanta akasa Anty Lami tace "je kawo drinks da snacks mubama bakuwar mu ko" da sauri Mami tace "haba haba wlh bakomi dama har gida nazo namuku godiya akan  karamcin da Amatullah daku kukama d'ana mara lafiya nagode, nagode, ubangiji Allah saka da alkhairi" daidai lokacin mijin Anty Lami ya shigo tareda Abie aka zazzauna ana gaggaisawa Hamida da kanta ke kasa ta kawo drinks ta ijiye da snack takoma ciki, ruwa kawai Mami tasha Abie kuma sai hira yake da mijin Anty Lami kaman sunsan juna nan Mami tabama Anty Lami labarin yanda Aadil din yafita daga mota haryasa tai hatsari, sosai Anty Lami ta tausayama yaron dudda bata ganshi ba sai bayan sallan Isha sanan sukai sallama Anty Lami ta kwalama Hamida kira. "Hamida" fitowa tayi kanta akasa Anty Lami tace "zasu tafi" dan dagokai Hamidan tayi ta kalli Mami a kunyace tace "Allah ya kiyaye hanya Mum" murmushi daga Mami har Abie sukayi sukace "mungode Hamida" suka wuce suka tafi har gate suka rakasu sanan suka dawo ciki ko minti daya basuyi da zama afalo ba wasu yara suka fara shigo da kaya niki niki wasu manyan ledoji ne guda uku na hadaddun turare da gyaluluwa, saikuma na atampopi guda uku da lace guda uku, dayan kuma na su chocolate da lot of cookies da sauri Anty Lami tace "inaa gaskiya bazamu karbaba haka akeyi" binsu akayi da kayan amma har sun tafi haka aka dawo da kayan.


Wanka tayi adakin Anty Lami takawo mata wani free doguwan riga blue tace "gashi nan kisa inkin gama kizo dakin Abban su yana nemanki" tajuya tafita, ahankali takarasa gaban madubin dakin tadau man Anty Lami ta lakato da hannu ta kalli Madubin zata shafa fuskar Aadil tagani ajiki yana turo mata baki yace "why did you leave me?" da sauri ta juyo ganin babu kowa a wurin yasa taji wani irin sanyi ajikin ta, jikinta yay wani irin sanyi taji jikinta dukya mutu, ahankali ta juyar da kanta tafara shafa man ajikinta kaman ance ta kalli madubin, Aadil tagani ta madubin yana mata kuka ahankali yana mata alamu da hannu datazo cikin kuka sosai yace "please come back Hamida my wife, I need you in my life, u promise you will not leave me" da sauri tasake waigawa ta kalli bayanta babu kowa a wurin wani irin fadawa kan kujeran gaban madubin tayi ta kifa kanta akan slap din madubin jikinta yay wani irin sanyi, kwala mata kira da akayi yasa ta dago kanta da sauri tace "gani nan zuwa" man dabata shafa ba kenan ta tashi ta dau doguwar rigan ta zira tafita.




Sallama tai agaban dakin mijin Anty Lami suka bata izinin shiga dakin ta shiga kanta akasa tace "ina wuni Abba" murmushi yayi yace "Hamida kenan tawaje na, zauna kinji abinki" yanuna mata kan kujera, tabe baki Anty Lami tayi tace "wlh bakai zabi me kyau ba indai Hamida ce ta wajen ka Alhaji, wanan miskilan yarinyar kayan haushi kenan, yarinyar nan saita sama ciwon zuciya" "baruwan ki tsakanin uba da ya sai Allah, ya kike kinji y'ata" dan murmushi tayi Anty ta harareta tace "ja'irar banza kawai" sunnar dakai tayi da sauri tace "lpy lau Abba" gyadakai yayi yace "masha Allah, ashe abinda yafaru kenan Allah ya kyauta ya kiyaye gaba amma ke mesa bakima iyayenki explaining ba, tsaya ma menene asalin abinda yafaru ya akayi kika hadu dashi yaron mara lafiyan?" ahankali kanta akasa tace "da ina dawowa daga makaranta yaboyoni, nina tsayama naji tausayinshi ne sabida naga shine yataba taimakana a Lagos dana fada ruwa" da sauri Anty Lami tace "au shine daman?" girgiza kai tayi tace "bashi bane yan biyu ne amma kaman ninsu daya nadauka shine, shi kaman baida hankali ne nace yatafi yaki tafiya yadunga bina yana kuka harnakai gida akofar gida yace min zaisha ruwa na shiga gida na daukomai ina dauka najuyo kawai naganshi abayana ashe yabiyoni ciki, shine na kulle kofa dankar Kaka taganshi tasa Abba koya Faruk yadaken" hararanta Anty Lami tayi tace "kaji wawancin natako Alhaji inda ace tafadi ko Kaka saita bashi wajen kwana inyaso washe gari a nemi gidansu amma tai shiru, waye zaiga kato daga dakin yarshi baiyi tunanin wani abuba incedai bai miki komiba ko?" gyadamata kai yayi ahankali, Anty Lami zata cigaba da mata masifa yadaga mata hannu yace "ya isa haka" , ya kalli Hamidan yace "tun dazu dasafe da mahaifiyar ki takira tafada na shirya naje gidan naku amma lokacin mahaifinki yatafi gidan kaji haka nabishi wajen nan yafara koromin laifuffukan ki, Hamida kema baki kyautawa fisabilillahi ace baki attending lectures, saida aka tura zainab taje department dinki nan yan ajinku sukace rabon dasu ganki harsun manta, Hamida karatun nanfa kanki kikemawa, ina ruwanki da mutane mezasu miki iye?" da sauri Anty Lami tace "su dena kashe kudinsu wlh akanta nafada ma mamanta ai, aure yarinyar nan take bukata bawani abuba, duk wani abinda zai fitar da Hamida waje batason shi itad..." shiru tayi sabida mugun kallon da Alhaji ya mata saanan ya kalli Hamida da kanta ke kasa yace "tashi kije ki kwanta in Allah ya yarda gobe da safe zamu maidake inyaso sai atattauna mu lallaba Kaka tahakura, tashi kije ki kwanta Allah bamu alkahiri" tashi tayi ahankali tace "nagode Abba" tajuya tafita yabita da kallo yana girgiza kai sanan ya kalli Anty Lami data rakata da hararan takaici, yace "ku dena abinda kukeyi yarinyar nan ba itatai kanta ba, Kune iyayenta dole ku nuna mata so ayanda take, sanan kununa mata taso kanta ayanda take, kune zaku bata confidence amma wanan abun dakuke mata saisa kuma batason rabanku zakiga saidai ta gwammace ta zauna ita kadai kokuma ki ganta da Ihsan, kokuma ta nemi wani irinta wanda halin su yaso yazama daya, addu'a zaku mata wata rana sai labari" ahankali Anty Lami tace "hakane nagode Alhaji" murmushi yamata yace "bakomi Hamida y'ata ce kaman su Ra'is da Ra'yyan" murmushi tayi nan suka cigaba da hira.


Koda takoma daki dadduma tahau tai salla sanan tai shafa'i da wuturi tajawo AL Qur'ani ta karanta danyau bata karantaba sai wuraren sha daya sanan ta rufe ta ijiye ta kwanta akan dadduman tai shiru tana kallon yatsunta tanajin wani irin sosai, ahankali tafara kirga yatsun kaman yanda Aadil yakeyi kafin takai hanun saman kan idanunta tafashe da kuka sosai da ita kanta batasan kona menene ba but deep down jitake tanaso ta ganshi koda sau dayane, tasan hala yanzu yatashi yana nemanta yana kuka, sosai tafashe kukan tawani irin lankwashe har bacci ya kwashe ta ahaka.




 Bubbugamai kafada da akeyi yasa yabude idanunshi ahankali kanshi namai wani irin masifaffen ciwo ya kalli waiterncikin muryan maye da bacci yace "wat?" ahankali yace "sorry Sir natadaka, we've closed this is 1 nadare, you have to go zamu rufe" wani irin dogon tsaki yaja yana bude idanunshi da kyar dake neman rufewa yace "nawane bill dina" "56,000 naira Sir, 3 bottle of rum kasha" da kyar ya sauka dagakan kujeran dayake kai zaune yatura hanunshi a aljihu yaciro wallet dinshi yazaro ATM card dinshi ya jefamai a fuska yakara kife kanshi saka katin a pos yayi ya mikomai yace "your pin sir" saka pin dinshi yayi kanshi na juyawa mutumin ya cire kudin shi sanna ya mikamai atm card din da slip ya karbi ATM card din yafara tafiya yana layi da kyar yakai parking space ya zube a wurin yana amai saida yayi yagama sanan yatashi yana tangadi yatashi ya xaga wajen mazaunin driver yabude ya shiga ya kunna motar.





Yaja yana bubbuge ido da kyar da kyar yakai gida yay horn aka budemai gate ya shiga yay parking yakai kusan minti biyar zaune sanan yafito ya rufe motar yay wurin tap din dake wajen yabude ya wanke fuskarshi sanan ya kuskure bakinshi yarufe tap din yazaro handkerchief daga aljihun shi yana goge fuskarshi tass sanan yawuce cikin gida yana tafiya ahankali yabude palonsu ya shiga, hayaniya yaji sosai. "kuka yaketamin kan ina Hamida, daga nafadi mai gaskiya nace tatafi gida shine yafara convulsing" taku yaji daidai lokacin Abie da Suleman dake sanye da jallabiya sun fito rike da Aadil dake wani irin convulsing sosai kumfa nafita daga bakinshi idanunshi suna kakkafewa kaman wanda ke shirin mutuwa, Abie nafadin. "innalillahi wa innailaihi raji'un, innalillahi wa innailaihi raji'un, Hassan, Hassan" Mami na kuka sosai, duk wani mayen dayake ciki wartsakewa yayi ya kalli Mami data fito da gudu tana kokarin saka hijabin data riko a hannu harta na neman fadi kasa, arude Abie yace "Sulemanu tsaya kaga kar yaron nan yafadi daga hanunmu ya karye, tsaya mu kwantar da shi nan akan kujera tukunna he's running serious temperature jikinshi kaman wuta" kwantar dashi sukai akan kujera amma tsabagen yanda jikinshi kewani irin jijjiga uncomfortably yana bankarewa yasa yayo kasa da sauri suka tareshi suka kwantar dashi akasa, Suleman yaciremai riga suka taru sunamai fifita arude, fashewa sosai Mami tayi takama fuskarshi tana jijigashi tace "Aadil, Aadil haka zakamin? Eh, haba Aadil dan Allah kamin adalci, Aadil, Aadil dina tashi, dan girman Allah katashi har gidan damuka kai yarinyar zan kaika kaji Aadil din Mami, Aadil" Mami takirashi a mugun raunane tana wani irin kuka, jiyayi kafafunshi sun kasa daukanshi wani irin fadi zaune yayi yadafa hanun kujera yana kallon Aadil dake convulsing jikinshi duk shatin belt din dukan  dayamai dazu.

_🌹IN BANI 🌹_ 






Maman Abd Shakur



30 - 31




_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba_



_3107021073 first bank aisha Muhammad pay 300 access fee in kinason this novel sai kituro evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_you can also send MTN card ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_



_masu fitarmin da novel waje kunma kanku_


Da sauri Abie yatashi yana kallon Aabid dayay wani irin zaman kalan tausayi yabi ta gefen Mami dake kuka sosai yawuce kitchen dinsu, bawani jimaba yafito dauke dawani bowl da towel aciki karami yakaraso wajen inda Suleman yake rike dashi ya ijiye bowl din akasa ya matso towel din yakai kan goshinshi yana kiran sunanshi ahankali "Aadil, Aadil, open your eyes" kara maida towel din yayi cikin ruwa ganin jikinshi ya soma rage kakkarwan yasake maida towel wuyanshi yana gogamai da sauri Mami ta tashi tarike hanunshi tace "sannu Aadil dina, wake up my baby please, tashi kaji ga Mamin ka anan kusa dakai" tai maganan tana sharemai fuskanshi da lema leman ruwan towel kekai ta manna mai kiss ahankali a kumatu, ahankali tamai whispering. "Aadil wake up" slowly jikinshi yay relaxing sosai yadena convulsion din da sauri Mami ta karbi towel din daga hannun Abie takai cikin ruwan taciro ta sharemai gefen bakinshi tanamai magana. "wake up Aadil, tashi tashi yaron Mami" ahankali yabude idanunshi dasuka kumbura sukai jajir ya daura kan Mami yay shiru yana kallonta batare dayace komiba, yay wani irin kalan tausayi kaman kamai kuka, da sauri Mami ta rungume fuskarshi a kirjinta tace "am sorry Aadil kaji, my babyboy tell me mekake so?" tai maganan tadago kanshi tana kallonshi tanamai murmushin da uwa kema yaro na tsantsan so, hawaye ne ya gangaro ta gefen idanunshi suna shiga kunenshi wani irin bakin ciki yakeji sabida rashin ganin Hamida kaman zai mutu, zuciyarshi sosai takemai zafi kaman ana soyawa amma bazai iya bayanin mekemai ciwoba, da sauri Mami tasa hannu ta gogemai hawayen muryanta narawa sosai tace "talk to me Aadil dan Allah kamin magana kaji" shiru yayi yana kallonta batare dayace komiba hakan yasa Abie ya karbe shi daga hanunta, ahankali ya kalli Abie hawaye na gangarowa daga idanunshi yay wani irin shiru kaman bashiba, murya chan Abie yace "menene Aadil mekema ciwo? Mutafi asibiti? Me kakeso" shiru yayi yana kallon Abie hawaye yasake gangarowa daga gefen idanunshi yakasa magana, dan ajiyan zuciya Suleman ya sauke yace "kodai natado Baba ne?" da sauri Abie yace "a'a kasan Baba nada hawan jini in gari yawaye yasani, mubarshi yay bacci yana bukatar bacci" kallon Aadil yayi ahankali ya sharemai hawaye yace "ga Hamida nan zuwa kaji, be fine kaga Mamin ka dukta damu" gyadamai kai yayi yafashe da kuka ahankali mara kara dake fita da kyar, zuciyarshi namai wani irin zafi sosai jiyake kaman zai mutu, kirjin Abie wani irin bugawa yake sabida abinda ke shirin faruwa, da kyar ya tattaro duka kuzarinshi ya kalli Sulemanu yace "mutafi dashi asibitin" tashi sukayi ahankali suka dago Aadil din dake kuka sosai mara kara  Mami na sharemai hawayen sukai hanyar fita daga dakin, Suleman ne ya kalli Aabid dayay wani irin zama akasa kanshi akasa kaman wanda akama mutuwa hakan yasa yace "lafiyan ka Aabid kokaima ba lafiyar ne" ahankali ya dago kai ya kalli Mami da sauri Mami cikin fushi ta wuce tafita daga dakin Abie yace "muje Suleman" sukawuce suka fita daga dakin suka saka Aadil din a mota Suleman yaja motar sai asibiti, wani irin tari Aadik din yafarayi yana kuka agalabaice yana dukan kirjinshi dakemai zafi sosai, bottle water Mami ta bude ta mikamai da sauri tace "ungo kasha" ture ruwan yayi da hannu yana tari sosai jinin da Mami tagani jikin goran ruwan datake mikamai ta sanadin tarin dayayi mai karfi yafito yasa tasaki salati tasaki ruwan akasa. "innalillahi wa innailaihi raji'un, Abie Aadil, Ab..." baya Aadil yay luuu kaman ya sume jini duk a lips dinshi da gefen bakinshi, da sauri Mami ta kamoshi ta rungume shi sosai tama rasa mezakayi, chan kasan makoshi idanunshi a kulle yana wani irin nishi yace "Mami Hamida my wife, call her for me" yafara wani tarin jini na fitowa sosai, fashewa da kuka Mami tayi tace "Abie, Abie d'ana, Yaya Suleman ka kara gudu, Abie Aad...." denajin numfashin shi da tayi a wuyanta yasa gabanta yay wani irin mummunar fadi tawani irin sakeshi yay baya luuu daidai lokacin suka iso asibitin.....



Aabid yakai kusan minti arba'in a zaune kanshi yadau wani irin zafin daya dade baimai ba, da kyar ya iya tashi ya ja kafa yay hanyar dakinsu, ahankali ya bude kofar dakin yay shiru yana kallon dakin ya sauke idanunshi akan belt dinshi da Mami ta jefomai dazu akwance akasa wanda ya daki Aadil dashi, shiru yayi yana kallon ko ina yanda ya bugi Aadil na dawo mishi sabo a ido yana kallon fuskar Aadil yana kuka yana sosa inda ya dakai yana cemai. "stop beating me Bid" shigowa dakin yay ahankali yana jan kafa, idanunshi ya sauka akan aman da yasan Aadil dinne yayi sosai zuciyarshi tamai daci, miyan bakinshi ma yamai daci yakasa hadiyewa, fita yayi yakoma yadauko mop da bucket ya gyara kasan dakin tass ko ina ya dauki kamshi sanan ya shiga bathroom yayo wanka yafito sanye da bathrobe yarasa meyake mai dadi, zama yayi abakin gadon su ya kurama hotonshi dayay tareda Aadil din ranan salla ido yana kallon Aadil din, yay mugun nadaman dukanshi dayayi bana wasaba, har tsoron kulle ido yake dan ganin fuskar Aadil yake yana kuka yana cemai "stop beating me Bid" wani irin fadawa gado yayi ya daura hanunshi akan heart dinshi dake beating fast, kafin yatashi da kyar yabude wardrobe dinsu ya zaro white jallabiya yasaka, ya shimfida dadduma yay sallolin da ake binshi sanan yadau car key yafita yabisu asibitin.








**

Da asuban fari ta tashi daga baccin daya dauketa kan daddumar, jinginar da bayanta tai jikin gado tana karanto addu'an tashi daga bacci, ko kadan batajin dadi jikinta saima wani irin kanta dataji yana mata ciwo, bude kofar dakin da akayi yasa ta dago kai ahankali, Anty Lami ne ta shigo sanye da dogon hijabi tace "au harkin tashi" gyadamata kai tayi tana sosa ido hakan yasa yace "to tashi kije ki dauro alwala" gyadamata kai tayi ahankali ta mike tsaye Anty Lami tabita da kallo harta shiga bayi, yarinya kyau har kyau ga diri amma haryau bata da saurayi ko daya, shiru tayi tadan tabe baki dam bataso tasaka lamarin Hamida arranta da sassafen nan dan zata tashi da ciwon kaine abanza ta maida kofar ta rufe tai dakin yaranta maza danta tasosu subi Abban su masallaci. 


Baki kawai ta wanke tafito daga bayin ahankali danji tayi cikinta namata ciwo sosai, drawer Anty Lami taja nanko taci karo da pad, guda daya ta dauka takoma bayi wanka tayo ta shirya tsaf sanan ta dauro alwala tafito daga bayin, adaddafe ta shafa mai tasa riga tahau gado ta kwanta dan sosai taji zazzabi na neman kadata, wajejen 7 Anty Lami takara shigowa dakin ganinta dukunkune kan gado yasa ta maida kofar ta rufe takaraso ciki da sauri dantasan Hamida bata komawa baccin asuba saitai karatun Al Qur'ani, ahankali ta yaye bargo data rufa dashi hakan yasa Hamida tabude jajayen idanunta ta kalli Anty Lami dake wani irin kallonta, ahankali tace "ina kwana Anty" dasauri Anty Lami takai hanunta kan wuyanta ganin yanda take maganan arude ta janye hanunta daga kan wuyanta tace "bakida lafiya Hamida,  meke miki ciwo?" dan yamutse fuska tayi tace "cikina ke ciwo" da sauri Anty tace "kin fara kenan kinga pad a drawer na?" gyada mata kai tayi tana goge hawayen dasuka zubomata na wahala, maida bargon tayi ta lullubeta tace "sannu kinji bari nakarasa breakfast nakawo miki kici kisha magani anjima idan ya lafa saimu je gida" gyada mata kai tayi hakan yasa  Anty lami ta shafa fuskarta tawuce tafita daga dakin. Fashewa tayi da kuka sosai tarasa meke damunta deep down jitaje kawai so take taga Aadil, she miss his innocence dakomi ma nashi, ko hanunta ta daga saita dingajin kamshin shi, hakanan ma saita dingajin kamshin shi kaman yana wurin, gashi batada waya balle yadan rage mata kewa kokuma wani abun, kasa dena kukan tayi har Anty Lami tadawo dakin da sauri ta share hawayen fuskarta gudun karta gani tafara mata masifa, karasowa ciki tayi rike da tray tana kallon fuskarta tace "kuka kike ko? Kodai muje asibiti ne" girgiza mata kai tayi ahankali, ajiyen abincin tayi akan rug tayaye bargon jikinta ta miko hannu ta dagata ta sauko da ita tace "ga kunun nan kisha da chips kisha magani saiki kwanta wuraren shadaya zamu je gidan, yanzun nan ma muka gama waya da maman ki" kallonta tayi ahankali tace "Mama" "eh maman ki tace nagaishe ki" murmushi tayi tadau kopin kunun takai baki hakan yasa Anty Lami tai murmushi tawuce tafita ta shiga kitchen ta kwaso lunch box din yaranta ta mimmika musu tace "kuje ku gaishe da Antyn ku saiku tafi driver na jiranku" da sauri sukai dakin Hamidan fadawa jikinta sukayi ta washe baki sosai dan tanason yara ta shafa kansu tace "byee ayi karatu da kyau" da gudu suka fita ta cigaba da shan kokon taci chips din kadan sanan ta tatatara ta kwashe tafita daga dakin ta shiga kitchen ta wanke duka kwanukan data gani a wurin ta share kitchen din tsaf konina na kyalli. kwala mata kira akayi. "Hamida jeki shirya Abban ku zai tafi aiki yanzu" ahankali tace "to" ta dauraye hanunta a sink tawuce tafita daga dakin ta shiga dakin Anty Lami kayan data gani anty Lami ta ijiye mata akan gado ta shirya acikin su bakin gown ne mai kyau tadau hijabin tasaka daidai nan Anty Lami tashigo dakin tace "iyye mai kama da mamanta kinyi kyau, mutafi to" murmushi tayi ta sunnar dakai tana wasa da yatsunta ta, tabi bayan Anty Lami suka fita tsakar gida motan Abban ta shiga bayan sun gaisa yatada motar suka shiga hanya dashi da Anty Lami sai hira suke gwanin ban sha'awa har jan bulo, ganin kofar gidansu yasa gabanta yawani irin fadi, akofar gidansu Abba yay parking suka fiffito daga motar, Anty Lami takama hanunta ganin takasa shiga jikinta sai wani rawa yake suka shiga cikin gidan, Abban su Ra'is biye dasu, agaban falon su Anty Lami ta kwada sallama ta shiga Abba da Mama dake zaune kan kujera ne suka amsa su Zainab da Ihsan kuma nakan dining suna gyaran wake a tray, Tashi Mama tayi tai murmushi jin muryan Anty Lami tace "shigo Yaya" shigowa Anty Lami tayi Hamida biye da ita abaya kanta akasa, ta kalli Abba dayawani irin kafe Hamidan da manyan idanu tace "ina kwana Abban su Ayush" dan murmushi yayi yace "barka da zuwa ga wuri" kokarin zama tayi tana mikama Mama jakarta tace "tareda Abban su Ra'is muke yana tsakar gida" da sauri Abba yamike tsaye yace "la shine kika barshi waje" yafita dan shigo dashi, wani irin kallonta Mama tayi yanda kanta ke kasa takasa dago kai sai wasa take da yatsunta yasa Mama buga uban tagumi, da gudu Ihsan ta sauko daga dining tazo tafada jikinta tace "oyoyo Anty Hamida naaa" Zainab kuma ta balla mata harara tacigaba da gyaran wakenta dan lamarin Hamida yanzu haushi yake bata, Sallaman su Abba yasa Ihsan tasaketa tai dining Anty Lami ta nuna mata gefen ta hakan yasa taje ahankali ta zauna akasa kusada kafarta, Abba kuma ya shigo tareda Abban Ra'is Mama kuma tadawo gefen yar uwan ta ta zauna, su Ihsan suka taso suka gaishesu ya amsa cikin fara'a Zainab tawuce kitchen tafito da tray da drinks ke ciki da snacks takawo ta ijiye sanan tadau tray din tawuce itada Ihsan suka wuce dakinsu.


Ruwa kawai Abban su Ra'is ya dauka yasha sanan ya ijiye ya fuskanci Abba da kyau zaiyi magana saikuma yajuyo ya kalli Hamida dake zaune akasa kusada matarshi kanta akasa gabanta sai wani irin faduwa yake yace "tashi kiwuce ciki Hamida, tafi dakinku" ahankali ta gyada kai tana goge kwalla tawuce ciki Abba yabita dawani irin kallo harta shige  corridor, sake kallon Abba yayi sanan ya kalli Mama dake dan murmushi cikin tattausan murya yace "haba, haba, haba dan Allah, a gaskiya raina yay matukar baci saisa nazo har gida namuku fada sanan nadawo da Hamida, ko kadan bakuma yarku adalci ba wlh, kuma nan gaba karku kara yankema yara mata irin hukuncin nan dan irinshi ne ke jafa yaro ga halaka, karuwai da sauran su dakuke gani duddaga haka aka fara daga koransu daga gida ne, to ina amfanin wanan? kome yaro yayi afara bashi damar bayani tukunna kafin a yanke hukunci, sanan adena yankema yaro hukunci cikin fushi, hanunka ai baya rubewa ka yanke ka yar, kai yanzu idan ka kalli Hamida fisabillahi bata baka tausayi?" yay maganan yana karkada kafa yana kallon Abba dake kallonshi asanyaye sanan ya cigaba."yarinyar nan ta shiga duk bala'in data shigane daga taimako, taimako fa jama'a, taimakon da annabin mu shiyace muyita, jiya har gida iyayen yaron nan sukazo suka mana godiya wlh idan kaji labarin yaron ma saika zubda mai da hawaye abin tausayi......" nan yafara bama Abba labarin da Hamida ta bayar na yanda ta taimakai dana Mami data bayar na Aadil din, dakuma labarin rashin lafiyan shi, sanan yace "yanxu abinda kukayi kun mata adalci?" dan ajiyan zuciya Abba ya sauke yace "nima nasan bamu kyauta ba kuma tun jiyan hankalina yaki kwanciya, naba Kaka hakuri, nabata hakuri harna gaji da bata hakurin amma taki fahimta ta tsaya akan bakanta, abinda yakara batamin rai shine yanda bata attending lectures ko kadan inda tasan bazatai makarantan ba dabatasa nai asaran kudina ba jiya result dinsu na first semester yafito Zainab ta dauko hoton takawomin wlh carry over bakwai gareta acikin courses tara dasukeyi last semester ina amfanin haka fisabillahi? Hamida bayar gidan nan bane? Hamida yarinya ce? Ba nannan ta taso taga yan uwa ta ba? Narasa yanda zanyi da ita, isilamiyan ma inda ba har gida na dauko musu malamin ba shima na tabbatar maka da bazata jeba, yaya zan mata? Saisa na yanke shawara da zaran miji yafito wlh aure kawai zan mata hala ta chanza muma ma huta dan lamarinta sai godiya...." sallaman da Kaka ta rafka yasa duk sukai shiru sai Anty Lami data amsa Kaka ta shigo tana kallonsu daidai, Anty Lami ce tadan zamo daga kujera tana murmushi tace "ina kwana Kaka" wani irin mugun kallo Kaka tamata kafin ta kalli Abba dayay shiru yana kallonta asanyaye tace "Sama'ila me wayan nan sukazo yi gidan nan da sassafen nan? Ince ba yarinyar nan suka kawoba" ahankali Abba yace "itace Umma tanama ciki amma duk ba abinda muke tunani bane, ashe taimakon yaron tayi, yaron kuma baima da lafiyan kwakwalwa, kinsan komu munga haka mun zaci pretending yake ashe da gaske ne baida lafiyan kai ne, jiyama saida iyayen yaron sukazo suka yima su Alhaji Ibrahim godiya, yanzu komi yawuce Umma" wani matsiyacin kallo Kaka tamai tace "idan kai yaro ne sunzo sun wanke ma kwakwalwa bayan Hamida taje ta shirga musu karya ka yarda niba yarinya bace, sanan abinda babba ya hango yaro ko yahau bishiyar kwakwa bazai hango ba, na kori Hamida daga gidan nan kuma ta koru ne, billahillazi la'ilaha illahuwa duk wanda yace zai nunamin ban isaba sainaje naci abincin gidan kajinka na mutun maka a wuya Sama'ila kana jina" tai maganan tana gyara kullin zaninta ta kwalama Hamida kira daga nan inda take tsaye. "Hamida! Hamida, dan uwaki kifito daga dakin nan kafin nazo dan wlh idan kika bari na shigo dakin nan sainai miki ruwan zabori aka, kifito nace" tagumi Mama tayi kawai tana kallon Kakan cikeda mugun takaici, Anty Lami ne ta tashi tace "Haba Kaka ki mata afuwa ki yafe mata mana idan kika korata daga gidan uban ta to ina kikeso taje? Tanada wani ubanne?" nunata Kaka tai da yatsa tace "kinga Lami lamiso kinga ina ganin mutuncun kiko karki kara kiran Hamida diyar Sama'ila, nariga nacireta daga yaranshi karki kara, Hamida!" ta kwalama Hamida kira da mugun karfi daidai lokacin wasu yara suka shigo guda biyu. "salama alaykum wai ana neman megidan awaje, ance ana sallama damai gidan" tashi Abba yayi ya kalli baban Ra'is yace "ina zuwa dan Allah" yawuce yafita, hakan yasa Abban Ra'is yace "Kaka kima Allah ki yakuri ki zauna ki saurareni haba Kaka ta" shiru tayi ganin yadan cika mata ido ta zauna akan kujera ta daure fuska tace "ina jinka yimaganan tun ina ganinka da gashi" sake kwantar dakai yayi yace "yauwa Kakana, wlh yarinyar nan ba iskanci tayiba taimakon mutumin nan tayi na rantse miki bari nabaki labarin yaron kiji...." nan yafara koro mata labarin har karshe zai cigaba da magana Abba yay sallama ya shigo ya kallesu dukansu yace "tareda baki nake ku gyara, iyayen yaron nanne sukazo" tashi Baban Ra'is yayi yace "masha Allah gasunan Kaka kyaji gaskiyan zancen daga bakinsu ai" fita Abba yayi tareda Baban Ra'is ko minti biyu basu dauka ba suka shigo da manya manyan baki sunci manyan kaya, Baffa, Suleman da Abie da idanunshi yay mugun jajir yau yana cikin tashin hankalin da rabonshi daya shiga irinshi tun ranan da aka haifi Aadil, gefe daya Aadil ne rai ahannun Allah yana sambatu yana kiran Hamida yana asibiti ansaka mai oxygen, gefe daya kuma Ozo ne dayace mai karya sake yabari Aadil yay aure, kanshi yadau zafi bana wasaba binsu Baffa kawai yake amma hankalin shi baya jikinshi baimasan me akeyiba, sai Mami da itama idanunta har kumbura sunyi tsabagen kuka saikuma big Mum dake biye da Mami, dawani babban Abokin Baffa wanda yake limamin jumma'a na masallacin dan ja, malam Kabir duk suka shigo dakin aka zazzauna, Mami daurewa kawai take tama kasa zama akan kujeran da kyau Kaka dai saibin manyan mutanen take da kallo danji tayi falon yadau wani irin sabon kamshi, Anty Lami ne ta tashi taje kitchen da kanta ta kwaso lemukan kwali tafito dasu a ijiye a tsakar falon sanan tadawo gefen Mama ta zauna tana kallon yanda su Abba ke gaisawa da mazan ana gaishe gaishe. 



Gyaran murya Baffa yayi zai fara magana, Mami takasa daurewa ahankali ta zamo daga kan kujera ta saukar da gwuiwanta kasa ta hade hannayenta biyu alamun roko tana kallon matar da kamanin ta da Hamida yasa tagane itace mahaifiyar Hamidan tace "dan Allah, dan Allah ba danniba, ku dauki Aadil a matsayin danku kunsan duk abinda zaisa yaron nan farin ciki ya taimaki rayuwan shi, kome yakeso zaku iyayimai koma menene abin dan samun lafiyan shi" da sauri ta share hawayen daya zubo mata, zatai magana saikuma wani irin kuka yazo mata tafashe da kuka sosai tsabagen yanda zuciyarta kemata wani irin rawa, da sauri Mama da Anty Lami sukace "subhanallahi, hajiya dan Allah kidena kuka" cikin wani irin kuka Mami ta girgiza musu kai ta kalli Abban Ra'is da Abba ta kalli Kaka data kafeta da ido sanan tasake kallon Mama har lokacin hannayenta ahade tace "dan girman Allah badanni ba bakuma dan halina ba, alfarma nake nema dudda nasan mai girma ne, mai kuma wuya babu wanda zai dauki yarshi yabama mai kwakwalwan yara, amma dudda haka da Allah nake hadaku Maman Hamida da baban Hamida, ku dubi girman Allah, ku taimakama d'ana kubama d'ana Aadil auren Hamida karya rasa ranshi dan darajan All...Allah" tafashe da kuka sosai kowa na dakin saida kukanta yataba ranshi har Kaka, da sauri Mama ta dagata tama kasa magana Baffa yace "ku shiga ciki mu maza zamuyi maganan mu anan" tashi Big Mum tayi da Anty Lami da Mama suka wuce da Mami dake wani irin kuka sosai ciki tana sambatu bama tasan metake cewaba.

_🌹 IN BANI 🌹_ 




Maman Abd Shakur



33...



_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi pay anan or pay achan_



_in kinason novel dinan, zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_



_you can also send MTN card 300 for those da basu da account ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_





Tsaki tayi tana kokarin warware daurin zaninta tace "wa kuwa, Hamida mana" wani irin taka birkin dayayi saida ta tsorata tasaki namijin goron hanunta tadafa kirji tana kallon ko ina tana zare ido tace "innahu min sulaymana, wa innahu Bismillah rahmani rahim, kai meya faru haka? Kasheni zakayi?" da kyar ya iya gangarawa gefen hanya yay parking yajuyo ya kalleta yace "wace Hamidan?" hararanshi tayi har lokacin kirjinta nawani irin masifaffen bugawa batadawo daidai ba tace "dan ubanka kana neman kasheni a hanya sanan kuma kana tambayata wace Hamida, tunda munada wata Hamida ne bayan wanda kasani ai shikenan nidai tada mutafi ka kaini gida akwai shirye shirye agabana" Kasa koda kunna motar yayi yajuyo yana kallon Kakan, hararanshi tayi tace "nidai yanda nake cikin farin cikin nan bazan bari bakin cikin ka yabata mini raiba, kaga tafiyata ka jika motarka da ruwan bunu ka tsoma tayoyin motar aciki kasha ka cinye shege mai kama da ifiritu tsabagen bakar mugunta" tabude motan tafita tana surutu ta tare keke napep ta shige tana ballama motar Faruk harara kaman idanunta zasu zazzago kasa.




Akofar gidansu aka sauketa tafito tana soka hannu a lalita tace "nawane kudin ka Malam?" "dari biyu ne Hajiya" hararanshi tayi tazaro dari dakuma naira hamsin tace "dari da hamsin zan baka yaro tsadarka tai waya nagadai ba wuyan fetur akeyiba" ta mikomai kudin karba yayi ganin tsohuwa ce yace "to shikenan Allah sa musu albarka" Ameen tace tajuya tabude gate ta shiga cikin gidan, Mama tagani a tsakar gidan da Baba dabasu dade da dawowa daga rakiyan Anty Lami da mijinta ba, dauke kai tayi tai kaman bata gansu ba tai hanyar sasanta, da sauri Abba yabita yace "daga ina kike Umma?" "inda ka aikeni" tafada atakaice tana kokarin bude kofar sasanta, zai biyota ta juyo fuska adaure tace "karka sake ka shigomin sasa ka wuce kacema Haleema a shirya gobe zanyi baki, manya manyan baki kuwa, sanan kabata kudi tai cefane, sanan katuromin Hamida yanzun nan ina jiranta" tana maganan ta rufo kofarta ta wuce ciki abinta, shiru Abba yayi yanabin kofar da kallo kafin ahankali ya saukar da ijiyan zuciya ya juya ya shiga dakinsu dan Mama tabar tsakar gidan, labulen falon ya yaye yaga Mama na kokarin shiga corridor yace "kirama Kaka Hamida zan tafi gidan kaji ni" ahankali takaraso inda yake tsaye tana kallonshi ganin damuwa karara sosai akan fuskarshi, hanunshi takama ahankali takai kan bakinta ta sumbaci hanun kadan tace "karka damu Umma zata sauko okay" gyadamata kai yayi yakai hanun nata kirjinshi ya rungume yana kallonta nayan sakanni kaman yanda itama take kallonshi asanyaye cikeda tausayin shi, saida yadanji dama dama sanan yasaki hanunta ahankali yace "thank you best wife, natafi" murmushi tayi tace "Allah kaika lafiya yakawo kasuwa best husband" kiss yama forehead dinta sanan yawuce yatafi itakuma takoma ciki, dakinsu tabude ahankali suka hada ido da Hamidan da har lokacin bata cire hijabi ba tana zaune kan gado kirjinta bai dena dukan uku uku ba, sai harba ido take kaman wacce tai kisan kai, Ihsan na gefen ta tana homework sai Zainab data gama gyara waken ta turesu gefe ta bude wani littafi tana dubawa, duk dagokai sukayi suna kallon Maman banda ita data saukar da kanta da sauri kasa tana wasa da yatsunta ahankali, da sauri Ihsan ta ajiye byron ta sauko daga kan gadon tace "Mama biscuit din dakikace zaki bani" hanun Ihsan tarike tace "muje yana dakina" sanan ta kalli Hamidan dataki dago kai tace "inkinga dama kije Kaka na kiranki" tana fadin haka tai gaba abinta, Zainab ta gimtse dariyan dake cinta saida taga Mama ta wuce sanan tasaki dariyan da sauri Hamidan ta kalleta da idanunta dasuka cicciko da kwalla, hararanta Zainab tayi tace "Allah ya tsagamin baki sainaki dariya ni" sauka tai daga gadon da sauri Zainab ta tashi itama daga kasa tana kallonta tace "wai ba cewa Mama tayi Kaka na kiranki ba eh hajjaju" harara ta watsama zainab din da manya idanunta tawuce tafita daga dakin ahankali tai sasan Kaka.



Ahankali ta shiga falon da sallama tana kallon ko'ina komi nadawo mata kaman wata matsoraciya, daidai Kaka tafito daga uwar dakan ta rike da wani turmi da tabarya na karfe, shigowa falon tayi ta ijiye turmin a tsakar dakin ta kalli Hamidan tace "kin wani tsaya hala nadawo aljana ce ko kike kallona da katun katun idanun ki kaman kwan lantarki, bazaki shigoba" shigowa tayi dakin Kaka kuma tadau ledojin data fito dasu tana budewa tana dubawa tace "yauwa saiwar ce" ta dago kai ta kalli Hamidan data zauna achan gefe tace "tashi ki cire hijabin nan kije fridge ki daukomin nono da kofi da chokali kizo nan" tashi tayi ta cire hijabin ta ijiye akan kujera taje fridge ta dauko nonon dakeda sanyi ta maida fridge din ta rufe ta kawo ta ijiye kusada ita sanan taje ta dauko kofi ta chokali takawo da sauri Kaka ta ijiye dakan ta karba ta zuba nonon a kofi ta zuba wasu magunguna aciki ta juya sosai sanan ta mika mata tace "yauwa shanye wanan kafin gobe suzo su kawomin kudaden saina dauko miki yar buzu tazo ta fara miki gyaran jiki dan wanan fatar taki fatar manya ce dole kiji gyara, ungo" ahankali ta karba tana kallonta dan ko kadan bamata gane metake cewaba ganin bata mata fadaba yasa taji zuciyata tai sanyi tai maza ta shanye batare data damu da dacin maganin ba.


Haka Kaka tarike ta a Sasan batare data bari tafita ba, tabata wanan tabata wanchan har bayan magrib sanan tasata taje tayo wanka, wanka tayi ta shirya cikin doguwan riganta na atampa sanan tasaka hijab tafito tai sasan su.


Falonsu ta shiga, babu kowa sai kamshin turaren wuta dayake yi, ahankali tawuce ciki ta tsaya agaban dakin Mama, sallama tayi chan kasa tanajin wani irin tsoro aranta, daga taciki Mama tace "waye, shigo" bude kofan tayi kaman wata matsoraciya ta shiga tana zare ido hada ido sukayi da Mama dake tsaye gaban wardrobe tana maida wasu kaya dake kan gadonta ciki, kallonta tayi kafin ta dauke kai tace "rufemin kofana sauro, meya kawoki kuma?" mayar da kofan tayi ahankali tarufe sanan tajuyo ta kalli Maman data mayarda hankalin ta kan abinda takeyi kaman batasan da ita a wurinba, jitayi jikinta yadau rawa wani irin kuka yazo mata ta tsani taga Mama na shashareta kotana fushi da ita, abin na mugun damunta arai bana wasaba, batasan lokacin dataje da gudu tawani irin rungume Mama ta baya ba tafashe da kuka sosai tace "Mama kiyakuri dan Allah  kiyafemin kinji bazan karaba, wlh, wlh, biyoni yayi, tsoro naji nayi ihu Kaka tazo ta dakeni tahadani da Abba koya Faruk saisa naki fadi, am sorry kinji Maman mu" tasaki wani irin kuka dayasa Mama sakin kayan hanunta kasa ahankali ta lumshe ido tanajin kukan nata akowani jijiya na jikinta, kasa daurewa tayi ta juyo ahankali, hakan yakara bata dama tafada jikinta sosai tasaki wani irin kuka dayake cinta kwana da kwanaki tana shesheka tace "dan Allah ki yafemin bazan karaba, am sorry" ganin yanda take kukan yasa ahankali Mama ta dago kanta daga jikinta ahankali takai hanunta ta share mata idon tana girgiza mata kai tace "ya isa haka kukan" gyadama Maman kai tayi wasu hawayen na sake xubowa, hanunta Mama takama takaita gefen gado ta zaunar da ita sanan ta zauna itama a gefen ta, ahankali tai cupping fuskarta da duka hannayenta takira sunanta chan kasa. "Amatullahi" ahankali akuma natse ta amsa da "na'am" dan Mama bata taba kiran asalin sunan ta hakaba, murya chan kasa Mama tace "wacece mahaifiyar ki?" ahankali tace "kece Mama" zama Mama ta gyara tace "maisa baki bani matsayin ba? Kinada wata kamata ne aduniyan nan?" girgiza mata kai tayi, "kinada wacce zata soki regardless, wacce zatai understanding naki kaman nine a duniyan nan?" sake girgiza mata kai tayi ahankali hakan yasa Mama tace "to mesa baki fadamin matsalar ki? Mesa baki gayamin kowani hali kike ciki? Inaso kifadamin yau mecece matsalar ki tell me everything, tell me anything, tell me the whole thing Amatullahi and your mother will listen to you, mesa bakison mutane? Mesa baki attending lecture mesa? Mesa u are not free da kowa, eh? Talk to me Hamida ina jinki, i want to know your problem" hawaye ta share ahankali sanan ta girgiza kai tace "nima i don't know Mama, kunya nakeji idan naga mutane dayawa sun taru sai naga anata kallona saina dingajin kunya saikuma nafara jin tsoro idan banvar wajenba sai nafarajin kirjina na bugawa sosai, kaina yafaramin wani iri, kafufuna sufara rawa, nafara ganin jiri, inji kaman kallonsu na shakemin wuya, numfashi na nafita da kyar, banson zuwa lectures sabida yan ajinmu kullum nunani suke yi wai nice maicin 3 da 5 a CA, duk in naje class kallona suke saisa bana zuwa ajin" ahankali Mama na kallonta asanyaye tace "to ina kike zuwa in baki shiga lecture ba?" murya chan kasa tasake share hawayen daya zubo mata tace "old railway station chan nake zuwa?" cikin wani irin yanayi na mamaki Mami tace "old railway Hamida? Bakisan irin wajajen nan matattaran yan shaye shaye bane?" gyadamata kai tayi ahankali tana kokarin fashewa da kuka tace "sunma biyoni ranan nagudu shine harna hadu da mara lafiyan nan shima yadinga bina har gida" ahankali Mama tai salati "innalillahi wa innailaihi raji'un, Hamida all this suka faru baki fadamin ni mahaifiyar ki ba anya kinmin adalci kuwa?" girgiza mata kai tayi tana kuka tace "am sorry Mama bazan karaba Allah kuwan" shiru Mama tayi tana kallonta kafin tace "dena kukan share hawayen ki" share hawayen tayi wasu na zuba, Mama tace "daga yau kome yasame ki any problem at all, ko wani abu dakikeji lemme be the first person to know kina jina" gyadamata kai tayi ahankali kafin ta rungume Maman da sauri tace "am sorry Mama, kiyafemin" kanta ta shafa tace "nayafe miki ya isa kinci abinci" gyadamata kai tayi ta tashi tace "bari na gyara miki kayan" hijabin jikinta ta cire ta gyara kayan ta jerasu a wardrobe din tass Mama nabinta da kallo tana mata addu'a aranta Allah ya shiryata, yakuma chanzata sanan yabata miji nagari, mayarda kofan tayi tarufe sanan tadawo ta zauna kusada Mama suna hira su biyu ahaka bacci ya kwashe ta gyara mata kwanciya Mama tayi taja bargo tarufe ta tana kallon fuskarta, duk cikin yaranta tafijin tausayin ta kodan sabida itace shiru shiru bata saniba amma hakanan takejin wani irin tausayinta da sonta bana wasaba, Hamida daban takejinta aranta tun ranan data haifota duniyan nan, all children are special but deep down tanaji Hamida zata dawo wani abu nan gaba, inka kalli Hamida innocent dinta zaisa ko cizonta bazaka iyayiba.

Sallaman Abba dataji yasa ta kalli agogo goman dare lokacin dawowan shine tashi tayi takara fesa kanta da turare tabude kofan tafita daga dakin dan zuwa tarban mijinta.



Ranan Kaka batai baccin dareba wani hadadden kwaleman dakinta tayi tana masifa ita kadai. "ja'irar yarinya tatafi bata dawoba sun barni nikadai naketa aiki, ai wlh duk kudin dazasu kawo gobe sisi bazasu ciba nikadai nasha wahalata nizan mori kudina, Hamida tasami gidan hutu miji pagal kaman ita chan su karata sa warkar da juna" tai maganan tana tura kujeran falon ta jikin bango ta tsaya tana kallo yanda dakin yay kyau sosai tace "masha Allah komi yay tsaf tsaf, sun gogu kujerun jibi yanda suke kyalli gobe dazaran sunzo shashina zan kawosu darat ayi magana in yanke musu sadaki, sati hudu zan saka biki, babu kyau jan biki yay tsawo ga yaro ma ba lafiya, yar buzuwa ma kudin ta rabi zan bata sai bayan biki zan cika mata rabin, wayyo Allah na bayana" tai ihu tana kokarin zama akan kujera dan tagaji iya gajiya, ko minti biyu batayi da zama ba bacci yay awon gaba da ita.

_🌹IN BANI 🌹_ 





Maman Abd Shakur



34 - 35



_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi pay anan or pay achan_



_in kinason novel dinan zaki turo 300 acess fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_



_you can also send MTN card ta watsapp number na 07012181461 for those da basu da account sainai adding dinki a group din danake posting kullum_





 Da asuban fari Kaka ta tashi tana mitsike ido tana salatin annabi ta wuce bandaki tayo abunda zatayi tafito daure da alwala tadau charbin ta tasaka hijabi tahau kan sallaya ta kabbarta salla, saida gari yay haske sanan ta sallame ta ijiye hijabin kan kujera tafito tabude kofar sasan ta tafita tai dayan sasan indata tarar da Hamida da Zainab suna sharan compound din, Hamida ce tafara gaisheta tana murmushi tana sunnar dakai. "ina kwana Kaka" ballamata harara Kaka tayi tace "rike gaisuwar ki munafika" dariya Zainab tayi itama tace "ina kwana Kaka" kallon Zainab din Kaka tayi yanda takema Hamida dariya tana washe baki tace "ke dalla chan rufe mana wanan bakin mai kama da rubabben shadda" wani irin ware manyan idanunta Hamida tayi kaman ba itaba tawani irin fashe da dariya tana kallon Zainab din tana yatsine hanci tace "hmmm saisa naji wari" wani irin gudu Zainab din tayi tabita, da gudu Hamida ta saki tsintsiyar akasa tana ihu tana dariya tana kwalama Mama kira Kaka tace "Allah ya wurgo ubanku gidan yaga abinda kukemai kulllum agida inya tafi masallaci" tasakai ta shige falon tana Kwalama Mama kira, fitowa Mama tayi daga dakinta rike da charbi tace "ina kwana Umma" daure fuska Kaka tayi ita a dole fushi take tace "lau, ba gaisuwar ki nazo najiba nazone nafada miki ki kira Lami tazo ita da mijinta, sanan kuyi hadadden girki, baki zanyi da sassafen nan, girki mai rai da lafiya fa" ahankali tace "to Umma" juyawa tayi zata fita saikuma tajuyo tace "ina Ihsan banganta ba?" "tana daki ne, tari take da mura shine nace kartai sharan" "maganin shan ruwan sanyi, babu randa bana wakar subar shan ruwan sanyi amma saisu nuna nai kadan, anjima tazo ta amshi zuma da tafarnuwa awajena tasha zatasami sauki, tarin zai lafa" ahankali Mama tace "to Umma angode" yaye labulen tayi tafice daidai Baba na bude gate yana shigowa sanye da farin jallabiya da hula akanshi da sauri su Hamida suka gaidashi amsasu yayi da sauri ganin Kaka yasa yataho dadan saurin shi yasamu ya lallabata, shan mur Kaka tayi ta dauke kai kaman bata ganshi ba tai hanyar Sasan ta, da sauri ya cin mata yasha gabanta cikeda damuwa kaman zai mata kuka yace "haba Umma inata gaidake kinki amsani wai har yanzu baki huce ba eh?" hararanshi tayi tace "gafara kabani sasana zan shiga ko" matsawa yayi hakan yasa tabude kofa ta shiga yabi bayanta da sauri ta shiga falo ta zauna akan kujera da sauri ya zauna kusa da ita ya daura kanshi akan kafarta ko kadan ya tsani yaga Kaka na bata rai dudda yasan ba'a mata komai kawai itake kirkiro rigima da kanta amma baya taba barinta ta dinga fushi for long, ta riga ta tsufa d fact dat she's very strong bai zama guarantee na cewa wani ciwon bazai kamata ba saisa yake lallabata dan yawan fushi zai iya jawo mata hawan jini ko ciwon zuciya, ahankali yace "kiyakuri Umma na bazan kara ja dakome zaki ceba, kowani hukunci zaki yanke kinyi daidai bazan kara cewa wani abuba Umma kinji" sosai zuciyarta yay sanyi amma saita daure tace "kai alkawari bazaka kara ja da hukunci naba?" da sauri ya daga kanshi jintamai magana yace "eh Umma kome kikafada daga yanzu hakan take kuma haka za'a bita bazan kara cewa wani abuba" kallonshi tayi saikuma ta kece da kuka taja bakin zaninta ta daura akan fuskanta tana share hawaye, arude yace "dan girman Allah Umma kidena kuka, wlh, wlh, wlh Umma kinji na rantse miki bazan kara, bazan kara ja da maganan kiba ke zaki dinga yanke hukuncin komi daga yanxu" cikin kuka sosai tace "baka sona ka tsaneni Sama'ila gani kake takurama nakeyi dankaga kai kadan karagemin aduniya baban Faruku mai sona maijin maganata ya rasu, wayyo Allah na, kaduba fa da baki daya nacemai yasaki shegiyar matar nan nashi Maman Faruku ya saketa amma kaiko kullum nunamin kake ban isa dakaiba, banjin dadinka ko kadan, agaban matarka, yayanka, kai agaban duk duniya ma kake nunawa niba komi bace agareka ba, nasan inda ace kasan guban dazaka sakamin a abinci naci namutu da tuni kasamin naci na mutu danka gaji da wahalata da matsalata so kake ka huta" "innalillahi wa innailaihi raji'un Umma, Umma dan yarasullullahi kiyakuri wlh bazan taba iya kashe uwata ba uwardata haifeni ba" tadan hujin yatsun data daura akan fuskarta take kallonshi yanda taga yay kaman zaiyi kuka dukya tsure yasa tai wani irin murmushi jin dadi aranta dan tasan ko yaji abinda ta aikata anjima bazaice kalaba sabida fargaban karta sake irin abin nan, share hawayen tayi tass tass tai tagumi tai shiru tana kallon sama kaman wacce akama rasuwa, ahankali yace "Umma, Ummana dan Allah ki kalleni" kallonshi tayi sai shar saiga hawaye, rudewa yayi gwanin ban tausayi yatashi tsaye daga kan kujeran yasa hannu a aljihu yaciro yan bandir din dari biyar biyar da wani makocinshi yanzun nan bayan sallan asuba yabiyashi kudin kaji guda dari daya saya, yadaura mata kudin acinya yace "gashi Umma sukenan gareni yau, nabaki kome zakiyi dasu kiyi amma dan Allah kiyakuri kinji" washe baki tayi kaman ba itace tagama kukan ba tadaga kudin tana kallo tace "kai Sama'ila wayan nan sababbin kudaden fa nawane?" "dubu dari da hamsin ne" murmushi tayi sosai tace "a'a baza ai hakaba, bandai dubu hamsin din saman kaika rike darin ko, Allah ampana" tai maganan tana kwance robalin ta kirgo dubu hamsin ta cire ta tura a lalita sanan ta mikamai sauran tana murmushi tace "Allah shi maka albarka, Allah karo kasuwa agidan kaji, Allah ya tsaremin kai yakaremin kai daga shairin mahassada kaji Sama'ila Sama'iloli yaci kafan bunsuru yahana Kaka bacci" murmushi yayi sosai aranshi yace Umma da son kudi yarasa uban me zatai da kudi haka hatta lipton shiyake kawomata ko tsinke bata siyafa amma sai masifar son kudi, "kanajina" da sauri ya kalleta tace "yau bazaka fita gidan kaji da wuri ba zamuyi manya manyan baki ne" da sauri yace "su waye Umma?" dariya tayi tana ballan goro tace "in sukazo zaka gansu, ka kira Mijin Lami yazo dakuma limamin unguwa, sanan kayoma Haleematu cefane nace ta girka haddden abinci wanda zamu tarbi bakin dashi, ka siyo lemukan kwali kaji" ahankali yana kallonta yace "to Umma shikenan" murmushi tayi sosai tana washe baki tace "yauwa dan albarka na, tashi katafi tun jiya banga Faruku ba baizo yasha furan shiba shegen goran" dariya yadanyi yace "kina kewan abokin fadan nakine kenan anjiman nan nasan zaizo wurinki" dariya Kaka tayi tace "wanan shegen goran ne zanyi wani kewan shi Allah kyauta, nidai yi sauri kaje kayi abubuwan dana saka" to yace yafice yanama kiran Abban Ra'is sukace suna hanya dan Mama takira, anty Lami na zuwa itada Mama da yaran su Hamida da Zainab suka fara girkin bakin Kakan, sukuma su Abba suna falo suna hira, wuraren tara da rabi suka gama komi Kaka dataci gayu cikin wani lashin hadari lace best lace dinta kenan tunna aurenta ne, bata saka lace dinan sai occasionally, tashigo kitchen din sai albarka take samusu, bakaramin Mamaki sukayi ba ganin kaka da kayan dan sunsan sai akwai babban abu take sawa, Zainab data gimtse dariyan ta tace "Kaka wlh hadari lace dinan baya miki kyau" dudda ta mata abaya Hamida ta sunnar dakai tana murmushi, Kaka tace "dan ubanki lashin nan ya girmi ubanki, tunna akwatina shegiya yar baka rubabbiyan yarinya kawai" turo baki Zainab tayi tawuce ciki Hamida tabi bayanta sum sum Kaka tabita da kallo.




Kujera taja ta zauna a tsakar gidan, Allah Allah take suzo so kawai take dazaran taji sallama ta shigo dasu, wani almajiri karami ne yabude gate ya shigo da sauri ta tashi tace "kai baki suka aiko ka?" da sauri yace "a'a Hajiya sadakan biyar ko goma nasai omon wanki" wani irin dogon tsaki taja takoma ta zauna sanan ta chusa hannu a lalita tace "zo ungo" tamikamai naira hamsin karba yayi yanata mata addu'a sanan yajuya yafita daga gidan, ba'a wani jimaba wani yaro ya shigo shiru tayi tabuga tagumi batason tasa ranta awanan karan. "Salama Alaykum wai ance ana sallama da masu gidan" da sauri Kaka ta mike tana murmushi sosai ta kwalama Abba kira. "Sama'ila, Sama'ila kufito ku shigomin dasu" fitowa Abba da Abban Ra'is sukayi da sauri Kaka ta nuna musu gate tace "kuna bata musu lokaci tun dazufa sukazo, shashina zaku kawosu" tawuce shashinta sukuma su Abba sukai gate wondering who could bakin Kaka be, bakaramin mamaki sukayiba dasukaga mutanen jiyaba amma duk suka boye mamakin nasu suka gaisa sosai cikin mutunci sanan sukai musu iso. Baffa ne da yaranshi maza uku su sulaiman sai kuma limam dawani amininshi duk sunci manyan fararen kaya suja shigo, ta window Zainab da Hamida da Ihsan suke lekawa sukace su waye wayan nan ita Hamida bama ta ganesu ba wlh hakan yasa suka dinga lekensu har suka shige sasan Kaka.


Zama akayi dayake falon Kaka da girma fes ya daukesu harda wani enough space dazai dau kusan mutane goma ma, gaisuwa akai ta mutunci suka gaishe da Kaka sosai ana raha ana dariya kaman ansan juna nan Anty Lami da Zainab suka gabatar da aban sha da kulolin abinci, ba laifi sunci abincin sosai suka sha lemu sanan aka tattara komi Baffa yabude taro da addu'a ya kalli su Abba yana wani irin murmushi mai nuna tsantsan farin ciki yace "bazan taba mantawa da karamcin ku da alkahirin ku aduniyan nanba, kun taimake ku kun share mana hawaye, ba kowani musulmi zai iya abinda kukayi ba saimai karfin imani da taqwa, kuma inamai tabbatar muku bazamu taba wulakantar muku da yarku ba da izinin Allah, xamu riketa amana sanan ina mai shaida muku da in sha Allah Hassan dinma yakusa samin lafiya yanzu haka zamu faramai na gargajiya ne dazaran yasami lafiya an sallameshi daga asibiti kuma munasa ran za'a dace in sha Allahu, yanda kuka taimake mu kuka sharemana hawaye ubangiji Allah ubangiji ya share muku hawaye kuma ranan gobe kiyama, shi aure dakuke gani yana tattare da dunbin rahma da ni'ima damu bazamu taba sanin mai Allah ke nufi da auren nan nasuba sai nan gaba domin kuwa komi dakaka yafaru aduniyan nan kaddara ce kuma da dalilin faruwanta, fatan mu shine ubangiji Allah ya basu zaman lapiya Allah yakuna albarkaci abinda muke kokarin hadawa ayanzu" atare duk akace Ameen dudda dai Abba bai gama gane kan zancen ba he's a lil bit confuse, gyara zama Kaka tayi tana murmushi tace "yauwa to Alhamdulillah komi daka gani kaddara ne, mun hadu ta alkhairi insha Allahu mun daura kenan yanzu sai afara gabatar da kayayyakin dana fada muku jiyako, kudin kun gani kunaso, kudin gaisuwan iyaye, kayan sarana dakuma kudin sadaki" wani irin kallonta Abba yayi zuciyarshi na neman bugawa, dauke kai tayi kaman bata ganshiba Abban Ra'is kuma yadanyi tapping cinyar Abban ahankali alamun karyay wani abu dazaisa suji kunya hakan yasa yay relaxing wearing a smile, murmushi Baffa yayi yace "to Hajiya" ya kalli su Suleman da Muhammad yace "Bismillah"  tashi sukayi suka fita daga dakin basu jimaba suka fara shigowa da kaya niki niki tareda wasu yara yan anguwan akwati set biyu suka kawo guda shida shida na Louis Vuitton, sai manya manyan tabarma guda biyar, dasu goro jaka goma, su dabino sai wasu kwalayen hadaddun sweet da chocolate katon goma, sai su kwalin biscuit saikuma kudi yan dubu wrappers na dubu daidai  da bama tasan na nawa bane sai harba ido take shiko Abba da Abban Ra'is shiru sukayi suna kallon ikon Allah, aminin Baffa ne yasake bude taron akaro nabiyu da addu'a yace "ga kayan nagani ina so dinan, gakuma kayan sa ranan, munaso ayanke mana sadaki sanan asaka ranan ko to Bismillah Alhaji" yay maganan yana kallon Abba da miyan bakinshi gabaki daya ya kafe ya bushe, hadiye miyau yayi ahankali ya kalli Kaka data zuba mai idanu irin kallon nan na kace bazaka karamin jayayyaba, dan gyara zama Abba yayi Anatse yana kallon kayan yace "wanan kaya haka Alhaji kaman muna sayar da yarinya agaskiya sunyi yawa, banda haka wanan akwatin ai babu bukatar su awajen sa rana ko? Kawai abarmata su amatasayin akwati kar akawo wan..." "kaga yaron nan nawa bai iya komiba haryau" Kaka tafada tana dariya ganin Abba na neman mata bukulu tace "ko yayyin Hamida gabaki dayansu nina aurar dasu saisa baisan kan abubuwan al'adun mu na hausawa ba, yanzu dai maganan sadaki muke ko?" tai maganan tana hararan Abba ta kasan ido ahankali ya saukar dakai, tace "yauwa sadaki" tace "yauwa sadaki kubada dubu dari, kudin kun gani kuna so dubu dari, sanan kudin gaisuwan iyaye dubu dari" innalillahi wa innailaihi raji'un Abba kawai yake fadi aranshi wace irin uwa gareshi dakeda shegen son kudi haka sabida taga masu kudi ne takeson siyar da yarshi haka dan anasu Ayush duk batai abinnan ba, patting cinyarshi Abban Ra'is yayi hakan yasa yasake murmushi, abokin Baffa yace "to Masha Allah" ya dauko wrap na yan dubu daidai guda uku duba dari uku kenan yamikama Abba cikeda ladabi, asanyaye Abba yamika hannu ya karba yana murmushi Kaka ta saki buda. "ayiriririi" Abba ya kalleta ganin yanda take murna yasa ya kalli Baffa yace "nabaku ubangiji Allah ya kaimu ranan yaja mana rai" Ameen duk akace Kaka tace "sati hudu, nan da sati hudu biki, asabar din dazata fado ana sati hudu ne biki da izinin Allah" takara sakin musu guda dayasa su Baffa dariya sosai nan aka kachame ana hira Abba yadan saki jiki yana basu amsa wuraren karfe daya suka tattara suka tafi bayan sunma Kaka kyautan ragowan kudin wai tarabama jikoki aiko Kaka harda rawa tarakasu har gate saida taga tafiyar su sanan suka shigo gida ta daure fuska rass dan karma Abba yakawo mata wata maganar ta kwalama Mama da Anty Lami kira tace "kuzo mu bude akwati muga abin ciki".



 Tai sasan ta Abba yabita da kallo zaiyi magana Abban Ra'is yace "kayakuri iyayen mune, babu yanda zamuyi dasu sai hakuri kawai, ko zaka mata ba yanzu ba, kabari anjima koda da daddare ne saika mata magana kaji" gyadamishi kai kawai yayi Abban Ra'is yace "muje gidan kaji kawai" fita kawai sukayi waje suka shiga mota suka tafi..


Zama Kaka tayi akan kujera tana kallon kayan daidai nan Mama da Anty Lami suka shigo, da mamaki suke kallon kayan Anty Lami tace "kayan waye wayan nan haka Kaka?" cikin tsananin murna Kaka tace "dukna Hamida ne wlh, mai sunana nada kashin arziki wlh, mutanen jiya nakirawo suka dawo dan sunban tausayi nabasu auren Hamidan ansa rana sati hudu, wanan akwatunan fa duk na sa rana ne, akwai na asalin aure na nan zuwa gab da biki" shiru daga Mama har Anty Lami sukayi dan maganan ta mugun basu mamaki bama tasan tayaya zasu amshi maganan ba. "dalla kuzo kuyatayani bude akwatin" ahankali suka shiga Mama ta kakalo murmushi Anty Lami tafara bude akwatunan suna dubawa kayane hadaddu bana wasaba, Kaka tabasu su sweet da dabino da goron tace "gashi nan a kulla a aikawa makota sati hudu, akwatin anan shashina za'a barsu ni yanzu fita zanyi akwai abinda zanje nayi" tai maganan tana Jan babban gyalenta dake kan kofa Lami tace "Allah kiyaye" ameen tace tafice, ahankali Mama ta share hawayen daya zubomata ta tashi fuuu da sauri Lami tarike mata hannu tace "zonan Maman Ayush ina zaki?" cikin fushi da Anty Lami ta dade bataga Mama cikiba tace "haba Anty, haba Anty dan sunga nai shiru komi ina kawaici na dauki Kaka a matsa yin mahaifiyata saisu nemi su takani, nice mahaifiyar Hamida inada right akanta haba Anty yarinyar da gata sai ahankali ne bamata da baki shine zasu dauka subama mahaukaci, wlh bazan yarda a cucen min Hamida ba, tausayin yarinyar nan nake bana wasaba, duka duka guda nawa take, shekaran ta ashirin fa, ki barni naje nakira mahaifinta Allah yau zaiga bacin raina bana wasaba" riketa gam Anty Lami tayi hakan yasa tafashe da kuka tafada jikinta, rungumeta Anty Lami tayi tace "calm down yanzu ranki abace yake don't take any decision a haste, am sure ko Abban Hamidan baiso hakan ba, Bakiga uwar tashi bane, jarababbiyar uwa taga kudi, kiyakuri kinji ki tsaya kiyi tunani kibari har anjima yadawo saikimai maganan kinji" Gyadama Anty nata kai tayi ahankali trying to calm herself down ta zauna kan kujera zama gefenta Anty Lami tayi tana shafa bayanta hartai shiru sanan Tace "bari na gyara kayan ko saimu kwashi goron da sweet din mutafi dashi karya zama wani abin maganan kuma" gyadamata kai tayi ahankali, hakan yasa Anty Lami ta tattara ta gyara kayan ta kawshi sweet din dazata kwasa da chocolate daidai ta kalli Mama dake kallonta asanyaye duktai wani iri sanan tace "muje" tashi Mama tayi ta tayata rike wasu suka fita daga dakin suka rufo kofan suka fice sukai sasan su Hamida suka samu daf Zainab dake wasa da filon kujera sai dariya suke Ihsan na tsalle, da sauri Hamida ta yarda filon ta kalli Mama da manyan eyes dinta da kitson kanta dasukai shegen tsufa tace "Mama kinga Anty Zainab na tsokanana ko" hararan su dukansu Mama tayi ta wuce tai ciki dan ranta abace yake duk sukabi Maman nasu da kallo, Anty Lami ta ijiye su sweet din tace "Zainab dagake har Ihsan kuzo kutaya Hamida tsefe shegen kitson nan yay tsufa dayawa" da sauri Zainab da Ihsan sukazo duk suna kallon su chocolate din hanunta batare dasun rokaba dan anhanasu roko tun suna yara, ajiyewa tayi ta bude ta debo dayawa ta basu suka karba suna murmushi sanan tawuce ciki wajen kanwarta sukuma sukai zamansu a falo suna kallo amma bini bini Aadil ke fado mata arai bana wasaba tarasa mesa takasa mantawa dashi.






Bayan la'asar Kaka ta shigo gidan tareda yara sun kwaso mata kaya a ledoji, kwalama Hamida kira tayi. "Hamida, Hamida" dakama Hamidan duka dake bacci zainab tayi hakan yasa tabude ido ahankali ta kalli Zainab din. "Kaka na kiranki" tashi tayi daga kan gadon ta sauko tafito daidai Kaka takaraso bakin kofar su ta kalleta tace "uwar bacci wuce kije kiyi wanka ki shirya kici gayu kifesa turare yanzun nan zanyi salla nafito, fita zamuyi" gyada matakai tayi ahankali tana murza ido sanan tawuce Kaka ma tabita da kallo kafin tasaki labulen tawuce sasan ta.


Wanka tayi duk jikinta ba karfi kaman ciwo nason kamata, wani material lace tasaka red sanan ta tsaya gaban madubi taja eyeliner saman idonta sanan tasaka man baki daya fito da pink lips dinta sosai saika rantse jan baki tasaka ta gyara gashin giranta tai carving dinshi da brush yay wani irin kyau har kyalli yake sanan taciro black hijabinta har kasa tasaka tafito da hannayenta tasaka flat sandals dinta na vintage sanan tadan fesa body spray dinta tafito, bakaramin kyau tayiba bakin hijabin yakara fito da hasken ta sosai kaman wata yar larabawa dama gashi anmata tsifa ta taje gashin tai parking sai hijabin da hulan sukai wani irin das ajikinta, fitowa tayi jin Kaka ta kwala mata kira ta shiga dakin Mama da sauri suna zaune suna magana da Anty Lami tace "Mama Kaka tace wai na shirya narakata wani wuri" tabe baki Mama tayi tace "saikun dawo" kallon Maman ta tsaya yi ganin kaman ranta abace yake jin Kaka ta kwala mata kira yasa tafita da sauri harara Kaka ta watsa mata tace "bazaka fitobane" ahankali tace "yakuri" Kaka tai gaba tana binta abaya tamika mata wani leda ta karba tace "hadaddiyar fura ce mai sanyi sosai mukaje sai kibashi" da sauri tace "wane Kaka?" bude gate Kaka tayi tasakai tafice tace "wanda zaki aura" da sauri tana wani irin kallon Kaka tace "wanda zan aura?" daidai Kaka ta tare napep ta shige ta kalleta tace "wai bazaki shigo ba kin isheni da shegiyar tambaya" ahankali ta shiga tace ma mai keken asibitin prestige suka yatada suka tafi, kusan tafiyan minti ishirin ya kaisu asibitin suka fito Kaka tabada kudi sukai ciki itadai bin Kaka kawai take dan batasan inda Kaka zatakai taba to wama takeda shi mara lafiya, har sukahau bene hakanan taji gabanta yasoma fadi, wani daki Kaka ta dosa tace "yauwa ga dakin chan" suka karasa sallama Kaka ta kwada tareda bude kofan, Baffa ne kawai da Mami adakin sai Aadil dayawani irin rame kwance akan gadon yana bacci dan tunda akamai allura wuraren shabiyun rana bai farkaba, kallo daya Hamida tamusa ta saukar da kanta kirjinta nawani irin bugawa, cikin tsananin murna Mami tazo da sauri tadan duka ta gaida Kaka. "sannu da zuwa Umma, kunsha hanya, ina yini" tai maganan tana kallon Hamida da kanta ke kasa, dan buge Hamida Kaka tayi cikin style hakan yasa tace "ina yininku" kamo hanunta Mami tayi ta shigo da ita dakin ta zaunar da ita kan kujera tace "welcome daughter na" Kaka ta shigo dakin tana kallon Aadil din tace "Allah sarki jibi yanda yarame Allah ubangiji yabashi lpy" Baffa yace "Ameen" cikin wasa Kaka tace "mudai kutashi mufita mubama yaranmu waje anjima ma dawo" murmushi Mami tayi, cikin fara'a Baffa yace "dama akwai wajen shan iska bari mu sauka, muje Maryama" yama Mami magana, fuskarta Mami ta shafa tace "feel free kinji bari muje mundawo" gyadama Mami kai tayi ahankali duk suka wuce suka fita aka rufo kofan dakin yarage daga ita saishi, ahankali ta dago kanta ta sauke manyan eyes dinta akanshi yanda yake kwance kaman wani maraya yay wani irin kyau a kwance yana sanye da white riga mai dogon hannu sabida sanyin ac dakin sai dogon wando da bakin safa akafanshi, gashin sajeshi sun wani irin kwanta lublub na idanunshi sunyi shar sun wani mike yana sauke ajiyan zuciya ahankali, wani irin taji tundaga kanta har dan yatsar kafarta ahankali ta ijiye ledan cup din furan hanunta akasa ta tashi dagakan kujeran ahankali ta zauna a danta bakin gadon tana kallon fuskarshi kirjinta nawani irin bugawa, dan runtse ido tayi dan sosai duk idan yana bacci ta kalleshi takejin wani irin shakkan shi saidai idan idanunshi biyu ne yanamata abin yaranshi takeji normal harta iya wasa dashi, bude idanun tayi ahankali ta saukesu akanshi asanyaye samin kanta tayi da kiran sunanshi cikin siriruwar muryanta batare data shiryaba dan sosai tai wani irin kewanshi gani take kaman yakai shekara daya rabon ta dashi. "Aadil" dan motsi yayi kaman yaji kiran sunanshi datayi zatai magana kenan taji anbude kofan dakin da sauri ta dago kanta ta kalli kofar ido da ido tayi da Aabid dake sanye da white riga mai dogon hannu irin na Aadil da dogon wando hanunshi rike da wayarshi iPhone 11, wani irin faduwa gabanta yayi sabida kallon dayake mata da sauri ta sauka daga kan gado zata wuce taji Aadil yarike wrist din hanunta gam hakan yasa arude ta kallai taga idanunshi a lumshe kasa koda motsi tayi saima kanta datamaida kasa kirjinta na dukan uku uku, ahankali Aabid yakaraso tsakiyar dakin ya tsaya agabanta kamshin turarenshi nawani irin shiga hancinta tana kokarin karban hanunta da Aadil yarike gam takasa, rungume hanunshi yay akirji yana kallonta tundaga tsakiyar kanta danyafita tsawo sosai har kafafunta cikin wani irin low voice yakira sunanta. "Amatullah".

_🌹IN BANI🌹_




Maman Abd Shakur



36....



Ahankali ta dago manyan idanunta ta kallai, wani irin kallon dayake mata yasa ta saukar da idanunta kasa ahankali, cikin wani irin cool voice yace "i have a request for you" yadanyi shiru yana kallonta kafin ya cije lips dinshi kadan sanan yasaki sabida wani irin zafi da zuciyarshi kemai kaman an zuba wuta aciki, cikin wani irin low voice mai rauni sosai yace "kece mace tafarko dana faraso Amatullah" yasake yin shiru kafin amugun hankali sama da muryan dazu yace "inhar bazaki aure niba please karki bari amiki auren nan da dan uwanshi" yay shiru sabida wani irin zafi da zuciyarshi kemai, cikin wani irin low voice mai rauni sosai yace "kece mace tafarko dana faraso Amatullah" yasake yi shiru kafin amugun hankali sama da muryan dazu yace "inhar bazaki aure niba please karki bari amiki auren nan da dan uwana, bansan tayaya zuciyata zata iya amsar ki amatsayin matar dan uwana ba amatsayin matata ba, i can't accept wacce nakeso amatsayin matar dan uwana, banson na tsani dan uwana sabida ke, inada mugun kishi seeing u as his wife zai iyasa nai abubuwan da daga baya zanzo nai nadamar aikatawa, karki auri dan uwana Amatullah bazan iya jurewa ba ko kadan, i...i....i love you dayawa Amatullah" yakarashe maganan amugun hankali muryanshi nadan rawa kaman zaiyi kuka yana kallonta, kasa koda dagokai ta kalleshi tayi saima ji tayi da hakanan ta tsani zuwa asibitin dasuka yi harta hadu dashi, meyake nufi da auren dan uwanshi? Kaka ma dazu tace zasuzo wajen mijinta duk mesuke nufi?  motsin dayaga Aadil yayi yasa yajuya ahankali zuciyarshi kaman zai tarwatse yafita daga dakin da sauri tareda rufo musu kofa, ahankali Aadil yabude jajayen idanunshi dasukai mugun ja sun wani irin yin yaushi alamun na wanda baida lafiya sosai, sunkuma mai nauyi, jikinshi komi ciwo yakemai, hanunshi ya kalla ganin yana rike da hanun mutun yasa ahankali cikin muryanshi dake fita da kyar tsabagen yanda zuciyarshi takemai wani irin zafi da nauyi yace "M...ma...mi" da sauri ta goge hawayen daya zubomata jin muryanshi dan samin kanta tayi da mugun daukin ganinshi tajuyo da sauri tana ware mai manyan idanunta murmushi kwance kan fuskarta ta kalleshi suka hada ido ta matso da sauri jikin gadon tadan rankwafo da kanta kadan tana kallonshi tanamai wani irin murmushin dake kunshe da tausayinshi dan kana ganinshi kasan ciwo nacinshi bana wasaba, da sauri tasake share hawayen dake neman zubomata ahankali tace "Aadil" cikin wani irin tsananin fushi da zuciya yature ta da duka ragowan karfin dayake dashi yajuya mata baya ya kalli dayan bangaren yaki kallonta, rike gadon tayi da sauri dan data fadi ta kalleshi asanyaye dan tasan fushi yake da ita dan ta tafi bai ganta ba, da sauri ta zaga ta dayan side din gadon ta kalli fuskarshi ya daure fuska tamau hawaye yataru a idanunshi ta tsugunna ta saitin fuskarshi takira sunanshi ahankali. "Aadil" da sauri yasake juyar da kanshi ta dayan bangaren dan bayaso ya ganta fushi yake da ita sosai, ahankali ta dafa gadon ta mike tsaye tana kallon bayanshi tace "fushi kake dani danna tafi, am sorry kaji" tai maganan tana zagayowa ta bangaren daya juya tana leken fuskarshi, a sanyaye ta tsugunna ta dafa gadon takai hanunta ahankali dake rawa sosai zata tabamai fuska murya chan kasa tace "am sorry kaji" ture hanunta yayi yasake juya mata baya ya kalli dayan bangaren batare daya kulataba, hawayen datake rikewa ne suka zubo da sauri tasa hannu ta share batasan dalilin hawayen ba amma ko kadan bataji dadin abinda yamata ba, tazaci idan yaganta zaiji dadi yayta murna yana tsalle tsalle ne amma sai baiyiba, rike kukan dayake zuwan mata tayi da karfin gaske ta mike tsaye ahankali tace "tunda bakason gani na shikenan, natafi" tadan tsaya ta kalleshi kozataga yajuyo amma saitaga ko motsi baiyiba balle tasaran zai juyo, sosai gwuiwanta yamata wani irin mugun sanyi ahankali tajuya tana share hawayen dayake zubomata da bayan hannu tafara tafiya, wani irin rungumota akayi tabaya dahar saida ta tsorata, wani irin juyoda ita yayi ta gaba ta kalleshi a tsorace danhar mamakin karfinshi take ya riketa sosai dan gabaki dayanta tana cikin jikinshi fuskarta ne kawai yadan koma baya datake kallonshi dashi, jikinshi zafi sosai kaman wuta, idanunshi sunyi jajir kaman gauta, gashi sun ciko da kwalla sosai amma basu zuboba sai wani irin sheki idanun sukayi yana kallonta dasu numfashin na fita da sauri da sauri yana sauka akan fuskarta, hawaye ne ya gangaro daga idanunta ahankali bakinta narawa sosai tace "am so sorry kaji Aad...." wani irin rungumo kanta yayi yasata ajikinshi ya matseta yafashe da mugun kuka danhar tanajin yanda kirjinshi ke bugawa kaman zai fito yana wani irin shesheka yana make mata kafada, rudewa tayi tana kokarin fizge kanta daga jikinshi amma yaki barinta sai makale mata kafada yake yana wani irin kuka dake tsuma mata zuciya, ahankali takira sunanshi itama kaman zatai kukan. "A...A..Adil" jin yanda muryanta ke breaking yasa yasaketa ahankali yadago kanshi yana kuka sosai ya kalleta da sauri kafin yakara rungumeta tai wajen gadon ta zauna kan gadon ta nunamai gefen gadon ta kalleshi tace "zoka ga, zoka zauna anan" sosai yake kuka kanshi na rawa yataho ahankali yana tafiya kaman zai fadi tsabagen rashin karfi yazo ya zauna kusada ita sosai yana kuka hannayenshi akan idanunshi yana kukan, kana ganinshi kasan abin yamai ciwo he just want to cry and cry and cry for her, kalle kalle tafara duk hankalinta atashe sabida yanda take kuka, white handkerchief dinshi data gani a gefen pillow dinshi ta dauka da sauri ta matsa dan kusadashi tana kallon fuskanshi, ahankali ta sanya hanunta dake rawa sosai ta janye hanun nashi daga kan fuskarshi, dago jajayen ice dinshi yayi ya kalleta handkerchief din takai kan fuskarshi ahankali tafara sharemai hawayen tana kallon kwayar idanunshi tanaji kaman taita mai kuka kawai kotaji dadi, cikin wani irin murya da ita kanta batasan kanta dashi ba tana sharemai fuskan tadan lankwasar dakai cikin sigan lallashi tace "am sorry bazan kara barinka natafi ba kaji" ta karashe maganan tana janye handkerchief din daga kan fuskarshi wani irin fadawa jikinta yayi yadaura fuskarshi akan wuyanta yanaji kawai kaman ya shige cikin jikinta yahuta da yanda yakeji, shi kanshi baimasan meyakeji ba kawai inya ganta jiyake kaman kanshi ya tarwatse tsabagen wani irin shauki dasonta dayake ji da baisan menene suba, kasa cemai kala tayi dan ayanda yay wani irin cuddling nata kaman za'a kwace mishi ita tana iyajin yanda heart dinshi ke beating kaman zuciyarshi na kokarin communicating da nata, dan lumshe ido tayi kafin ahankali tabude su murya chan kasa tace "Aadil kasakeni" make mata kafada yayi sai a lokacin yamata magana da shakakkiyar muryanshi yace "you will run away again" girgiza mai kai tayi tace "no i won't" ahankali yakara tura fuskarshi cikin wuyanta sosai yana shakan kamshin dayaji tanayi dakemai wani irin masifar dadi akai, yaji wani irin natsuwa na shikanshi hankalinshi na kwantawa sosai, ahankali ya mika mata karaman yatsarshi murya chan kasa yace "pinky promise" kallon fine black yatsar nashi tayi da kanshi ke kwance akai ta gyadamai kai batare data bashi nataba tace "yes" make mata kafada yayi a shagwabe yana kara miko mata karaman yatsar yace "ni kiyi" ahankali ta mikamai nata yatsar yakama da sauri ya sakalesu yay dan murmushi yana kara riketa dayasa taji she's feeling uncomfortable sosai kuma tasan kotace yasaketa bazai sakiba tunawa da furan Kaka yasa da sauri tace "tsaya kagani, i brought fura for you" tai maganan tana ture hanunshi daga gefen cikinta da kanshi dake wuyanta ta janye jikinta da sauri daga nashi ta sauka daga kan gadon ta zauna akan plastic chair da sauri tadau ledan taciro furanshi dakeda sanyi sosai har lokacin tadago kai ahankali ta kalleshi kallonta yake sosai kaman zai hadiyeta ko kadan baiji dadin yanda ta tashi ta zauna a wurinba, ahankali ta mikamai cup din tace "ka iya shan fura? Is very very sweet" kallonta yake da manya manyan idanunshi kaman yaune rana na farko daya fara ganinta har saida taji wani iri sosai hakan yasa ta maida furan ta ajiye akan drawer kusa da gadonshi ta saukar da kanta kasa tana wasa da bakin hijabinta, jin shiru ko tarinshi batajiba yasa tasake dagokai ta kallai hada ido suka sakeyi har lokacin ita yake kallo, washe mata baki yayi sosai yasakin mata wani irin cute smile da rabonshi dayay irinshi

tun ranan dasuke tare cikin muryanshi mai dadi sosai yace "you look beautiful sosai sosai Hamida my wife" yanda yay maganan yana mata wani irin fari da ido kaman wani dan karamin yaro yasa tai dariya ahankali itadai hakanan batasan menene Aadil kedashi ba but duk duniyan nan shine d only man datake nan very free with him, ko Faruk cousin dinta bata sakin jiki dashi haka har taita mai murmushi tana dariya sosai hakan nan, amma Aadil ko hakanan saita dinga jinshi kaman wani kaninta sabida yanda yake abu kaman yaro kodan batada kani namiji ne saisa takejin hakan oho, hanunshi ya miko mata yana hararanta yana lankwasar da wuya kaman bashine mara lafiyan nanba yace "give me my thing and stop smiling" da sauri ta kalleshi dan bamata gane my thing din dayake cewaba, furanshi ya nuna mata da baki da sauri ta dauka ta mikamai, make mata kafada yayi kaman zaiyi kuka yace "spoon" murmushi tasakeyi ganin yasoma komawa normal tafara dube duben neman spoon, drawer data gani tajawo nantaga spoon dauka tayi ta tashi tsaye yabita da kallo ta shiga bathroom din data gani ta daurayo tafito sai kallonta yake kaman wacce zata gudun mai takawo mai spoon din ya karba, da sauri ya debi furan yakai bakinshi, lumshe ido yayi yace "uhmmm Sweet, i will remain for Bid" yakara diban nabiyu zaikai baki tsayawa yayi baishaba ya make kafada yana turo baki tunawa dayayi Aabid ya dakai yace "i will not remain for him, Bid beat me" yakai bakinshi ya hadiye sanan ya debo wani ya matso yakawo saitin bakinta yana washe mata baki yace "haa Hamida my wife sha, sha, shaaaa" yanda yaja shaa din yasa tai murmushi sosai daya bayyanar da dimples dinta ahankali ta budemai bakinta tana kallonshi shima yana kallonta yasaka mata furan ta hadiye ahankali  dan da dadi sosai, dariya

yayi harda kyalkyacewa dan yanda ta hadiye tana lumshe ido ya mugun burgeshi da sauri yadebo another one yakai saitin bakinta yace "again" da sauri ta girgiza maikai tana dan hararanshi tace "no am okay, ya isheni kai kasha" make mata kafada yayi yadebo wani da sauri zaikai bakinta da sauri ta tashi daga kan kujeran zata gudu dan kunya taji tanaji, fizgota yayi tafado jikinshi kafadarta ya buge spoon din, spoon din yay tsalle yay sama yafadi akasa furan ya zuba a kumatun ta, a tsorace ta kallai wani irin kallo yamata shima yana kara janyota jikinshi dan abinda yake mugun so kenan yajita ajikinshi, da sauri yana ijiye cup din hanunshi agefenshi tai sauri tai baya zata gudu yasa hanun ya rike kafadarta yajawota jikinshi da karfi ahankali bakinta har rawa yake dan yanda taga idanunshi tace "Aa...dil saken, s...sakeni" sakata yay ajikinshi gabaki daya yasa hannunshi ya rike waist dinta gam dayan hanun kuma yakama habarta yana kallonta, bakinta har rawa yake tace "dan Allah kadena kaji babu kyau" make mata kafada yayi yana kallon furan daya zuba akan kumatunta kafin ahankali yakai bakinshi saitin fuskarta wani irin runtse idanunta tayi a mugun tsorace kirjinta na bugawa sosai kaman zai bullo, ahankali yana kallon long eyelash dinta yasa harshen shi ya lashi furan kan kumatun nata slowly, wani irin nishi tayi taji wani irin mugun shocking batasan lokacin data rike wuyan riganshi gam ba kaman her whole life depend on it, yanda tarikemai wuyan rigan da yanda some part of her hand yataba bare skin dinshi yasa yaji wani irin abu dabai tabashi ba shima tundaga yatsar kafanshi harkanshi, yasake fito da duka harshen shi ya lashe duka furan soft naman kumatun ta namai wani iri kaman yaci, yanda tarikemai wuyan riga gam tana nishin kuka sosai dake sauka akan wuyanshi yasa ahankali yaji duka tsigar jikinshi natashi hakan yasa yafara matsa kafarshi da sauri jin he's having erection abinda baitaba yiba through out his life saiyau, bakinshi har rawa yake muryanshi ta dishe sosai yana shirin yin kuka yace "am feeling something Hamida my wife".

[11/28, 9:55 AM] +234 701 218 1461: 37...



Bude idanunta dasukai wani kala sabida kankamesun datayi cikin tsoro tayi ta kalleshi jin maganan dayayi tana kokarin fizge kanta daga jikinshi, make mata kafada yayi danko kadan bayason ta tashi daga jikinshi wani irin dadi yakeji da shauki dawasu abubuwa dayake sashi yakejin he wants the moment to go on batare daya yankeba, yanda yake kallonta yana mamatse kafa sosai dan he could feel yanda yake dripping down there, sosai taji wani tsoro dudda bata lura da wat he's having ba dan hijabin ta yarufe mai cinya, ahankali tace "tokasakeni na zauna kaji" make mata kafada yayi hawaye suka zubo daga idanunshi a shagwabe yana karakai bakinshi kan kumatun ta da sauri ta runtse ido gam sabida yanda tsigan jikinta kewani irin tashi, ahankali yadaura bakinshi akan kumatun wani irin nishi tayi tasaki kara ahankali. "wayyo" tarike wuyan riganshi da kyau sabida yanda tafin hanunta kemata wani irin shocking, da sauri da sauri yake lasan soft kumatunta kafin ya birkito da fuskarta ahankali yana kallon fuskarta yanaji kaman kanshi zai tarwatse, lips dinta dake shining din man bakin data shafa ya kafe da ido baisan lokacin daya wani irin daura bakinshi akan bakin ba ya shiga kissing dinta da sauri har wani nishi yake yana sauke ajiyan zuciya shi kanshi baisan meyake yiba kanshi kawai ke directing dinshi yake abinda yakeyi, da duka karfinta tasa hannu ta ture kirjinshi ganin kaman zai cire mata baki hakan yasa yasake a tsorace, cikin fushi ta waska mai mari da karfi tana hararanshi sabida bakin cikin abinda yamata da sauri yadafa wajen yana kallonta, goge bakinta tayi tanaji kaman tai ihu hawaye na zuba daga idanunta kafin ta kalleshi shima ita yake kallo hanunshi dafe da kucinshi, harara tasake ballamai tama rasa mezatace mai tajuya da sauri zata fita daga dakin dan ko ina na jikinta rawa yakeyi, wani irin fashewa yayi da kuka yana girgiza mata kai cikin kuka sosai yace "don't go please" tsayawa tayi chak tajuyo ta kalleshi batare datama san meya hanata tafiyan ba, sakin mata wani irin kuka sosai yayi daya wani irin narkan da zuciyanta yana girgiza mata kai cikin kukan yace "please don't leave me again" karasawa ciki tayi asanyaye batare data sake kallon fuskarshi ba taja plastic chair ta zauna tareda daukan furan ta rufe ta ijiyemai akan saman drawer sai kallonta yake soyake ya shige jikinta kozaiji dadi but he's scared bayaso tamai fada kota sake marinshi, baiso yaga tana fushi, dan kallonshi tayi ganin yanda yay wani irin zuru zuru sai goge kwalla yake yasa tadan sakin mai murmushi da sauri ya sakin mata murmushi yana clapping hands da sauri hawaye na zuba daga idanunshi yace "Hamida my wife is smiling" murmushi tasake mai tai shiru tana kallonshi dan wani irin mugun tausayi yake bata zataso taji yanda yafara ciwon nan, zataso taji labarinshi, zataso taji ya akayi shi baida lafiya and dan uwanshi is fine, hakanan takeji zata iya komi dan kawai taga yadawo kaman kowani babban namiji, sosai takejin Aadil aranta kuma tarasa mesa hakan, bude kofan da akayi yasa duk suka dago kai, Baffa ne ya shigo tareda Kaka sai Mami da Abie da Aabid dake tareda Mami dan sun shirya yanzu duk yay wani iri, ahankali ta saukar da kanta kasa tana wasa da yatsun ta, Kaka ta kalli Aadil din dake kallon Mami yana mata alamu datazo tace "sannu da jiki, Allah sarki ya rame sosai, idanunshi sun kode alamun ciwo, ya jikin?" kallonta yayi saikuma yaturo mata baki tareda mata fari da ido yace "fine" sanan ya kalli Mami batare daya kalli Aabid daketa kallonshi ba cikin tsananin farin ciki yamata alamu datazo yana mata pointing Hamida yace "Mami come and see My Hamida, tazo" ya kalli Baffa daketa murmushi yana kallonshi ganin yanda yay kaman bashiba yace "come and see her grandfather" Mami ce takaraso kusa dashi yawani irin fada jikin Mami cikin tsananin murna yana nuna mata Hamidan da hannu yana wani irin cute smile dake karamai wani irin mugun kyau, murmushi Mami tayi tace "naganta amma yanzu Hamida zata tafi itada grandma dinta she will come tomorrow okay kaga yamma tayi" kallon Mami yayi da sauri kafin ya make mata kafada yace "no i don't want her to leave me again" ahankali Mami tace "please Aadil zata dawo kaga magrib tayi ko" make mata kafada yayi kafin yasaki kuka ahankali, Mami ta kalli Hamidan data kasa dago kanta tace "tashi kutafi daughter kinji" sakin Mami yayi yarikema Hamidan hannu da gudu yana kuka yana bubbuga kafa da sauri Kaka ta share hawayen dake neman zubo mata ta girgiza kai, kai wanan yaro na bata tausayi bana wasaba wlh, hakan yasa ta matso kusada Mami tace "kinga maman yan biyu barshi kinga sai kuka yake kar zazzabin yarufe shi kuma, anjima inyay bacci matafi" da sauri Baffa yace "a'a baza ai hakaba, magrib tayi Hajiya in aka biye tashi ba yanzu zaiyi baccin nan ba" yay maganan yana dogara sanda yana kallon fuskan Aadil din daya rirrike hanun Hamida yana kuka sosai yana bubbuga kafa, wani irin jin kukan nashi Hamida  take har akasan ranta amma takasa dago kai balle ta lallashe shi sabida kunyan su Mami gashi saijan hanun nata yake yana kuka, ahankali Baffa ya dafa kafadarshi yace "zokaji" magana yamai a kunne da sauri ya kalli Baffan cikin kuka sosai yace "are you sure?" gyadamai kai Baffa yayi cikin lallashi yana sharemai hawayen, ture hanunshi yayi ya tsugunna agaban Hamidan ya daura hannayenshi akan cinyarta ya leka fuskarta hawaye nafito daga idanunshi jiyake kaman zaiyi hauka, hada ido sukayi da Hamidan, ahankali cikin kuka yace "is it true zamuyi video call?" gyadamai kai tayi dudda bamata da waya, girgiza mata kai yayi yace "please don't go and leave me zan mutu" yanda yay maganan yana kuka saida yataba zuciyar kowa adakin da sauri Abie yafita daga dakin ya shiga restroom dayake hanyar dakin, ya shiga wani bayi da sauri yarufo kofa yaciro handkerchief daga aljihun shi ya daura akan idanunshi yahau kuka, kuka sosai bana wasaba. "wani irin kwadayin duniya yakaini na jefa d'ana wanan halin dayake ciki yau? Banrasa ci ba, ban rasa shaba, ban rasa sutura ba,  inada su Suleman dasuka daukeni a matsayin dan uwan su, inada mahaifin su daya daukeni a matsayin danshi, ina da aiki na, ana biyana daidai na level din karatuna a kamfanin Baffa what push me? Wani irin greed yakaini nafada wanan halakan? Aadil na cuceka, na cuce ka bana wasaba, nacuce ka my son, i can't forgive myself, i can't forgive my self, my son has been suffering yanzu for more than 30yrs all because of me ya zanyi? Tayaya zan bulloma wanan tsaka mai wuyan danake? Tayaya zan hana Aadil auren nan? Tayaya zan ciremai son yarinyar nan? Tayaya zan rabashi da yarinyar nan" yabata kusan rabin awa abayin yana kuka sanan ya wanke fuskarshi ya share tass sanan yafito.



Fitowa yayi daga bayin daidai lokacin Mami tafito daga dakin hada ido sukayi da sauri ya saukar da idanunshi kasa dan bayason tagane yay kuka, hakanan kawai yaji yana wani irin jin nauyin ta dan ya mugun yaudaranta, ya cuceta itada yayan su, hanunshi dayaji an kama yasa yadago kai suka hada ido da ita, tattausan murmushi ta sakin mai tasa hannu ta shafa sajenshi cikin muryan kwantar da hankalin miji down tace "kadena damuwa Abie, Aadil dinmu zai warke da izinin Allah, watarana duk wanan abin labari zai zama kaji" gyadamata kai yayi asanyaye hakan yasa tai murmushi tace "zomuje office din Dr, kaina fito na nema dama Aadil yay bacci, Dr yace muganshi, ni inaso a sallameshi ma gobe kawai dasafe mukoma gida mai maganin da Baffa yakiramai yazo afara gwada maganin gargajiyan kafin bikin nashi ko, let's see what Allah has install for us and banda hakama aure rahama ne let's just team up and be praying for our children ko Abie" gyadamata kai yayi yama kasa mata magana sabida yanda jikinshi yay mugun sanyi, yasha attempting yafadi mata gaskiya but bayataba iyawa he loves Mami so much da he's afraid of losing her, bayaso yafadi mata gaskiyan wayeshi ta tsaneshi taki zama dashi, his heart cannot bear that, ahaka suka bude office din Dr suka shiga shiga sai tunane tunane yake.



**

Gari yafara dan duhuma dan gab da isha'i suka isa gida, Mama kadaice a tsakar gidan tana nannade tabarma zata shiga daki, da sauri Hamida tai wurinta tafada jikinta tana murmushi tace "Mama mun dawo" dan murmushi Mama tayi dan sosai take fushi ta kalli Kaka data karaso wajen tace "sannu da zuwa Umma, ina yini" "yauwa Haleematu, lpy lau ina sauran yaran?" Kaka tafada tana daure fuska ta kalli Hamidan tace "ke wuce mutafi akwai gyaran dare dazan miki" tai maganan tanajan hanunta tai gaba da ita Hamida tajuyo da sauri tana kallon fuskar Mama data shige daki abinta, Kaka tawuce sasan ta da ita, akwatin falon ta nuna mata tace "ga akwatunan kayan sa ranan ki nan keda Aadil sati hudu baban ki yasaka, shi suka kawo dazu da safe shine ubanki yace na dauke ki nakaiki ki gaida yaron, ashe haka yaron ke sonki yarnan? Jibi yanda yadinga babbaka kuka dazaki tafi, Allah dai yakaimu bikin mu auramai ke yahuta da wahala wlh yaron na masifan bani tausayi" da sauri Hamidan ta kalleta dan bakaramin faduwa gabanta yayi da maganan ba ahankali bakinta har rawa yake tace "ni Kaka? Nace muku ina sonshi ne? Ninace zanyi aurene? Ba Anty Zainab za'a aurar ba kafin niba" mugun harara Kaka ta watsa mata tace "kisami ubanki kimai maganan ja'ira rasakunyan beran tanka, ai bani nabada auran nakiba, wuce kije kiyo alwala kiyi salla akwai abinda zan hadamiki kici, kuma wlh aure bafashi saisa daga yanzu andena ganin murmushi na balle wani shege ko shegiya takawomin maganan banza a gidan nan, bazan bude ido inaji ina gani kumin bukulun gidan hutuba, arziki inaji ina gani kumin bakin cikin samuba" taja tsaki tawuce tabude dakinta ta shige tana ihu tace "kuma wlh nabaki minti goma kiyi salla kizo nan wurin, gobe yar buzu zata zo tafara miki gyaran jiki" da gudu Hamida ta shige dakinta tafada kan gado wani irin kuka neyazo mata sai maimaita kalman aure take abakinta tama kasa yarda wai ita za'ama auren, to wani irin aure ma, Aadil, ita ta shirya aure ne yanzu? Tayaya zata auri Aadil ma? Haka taci kukanta takoshi saida Kaka ta kwala mata kira sanan ta tashi ta shiga bayi ta daura alwala tafito tahau kan dadduma tai salla sanan tawuce dakin Kakan tana goge kwalla.



Misalin 10 nadare Abba ya shigo gidan, abinci Mama takaimai, sai bayan yagama ci yay wanka sunyi shirin bacci sanan Mama ta gyara zama ta fuskance shi fuskanta adaure, ahankali tace "tundazu kadawo kai shiru ina kallonka nazuba ido inji kozakamin maganan amma kai shiru ko kala bakace min bako, ka dauki y'ata kabama mahaukaci baka fadanmin ba baka shawarceni ba saidai naji  abakin wasu sabida kaganni shiru shiru kome kakeso shinakeyi ina binka sau da kafa saika nemi ka takemin hakkina a matsayina na mahaifiyar Hamida gas...." da sauri Abba yatareta ta hahanyar cewa "Hamida ba yarki bace kadai ba nima y'ata ce, sanan yanda abin nan kemiki ciwo haka nima yakemin ciwo, yakike so nayi eh Haleematu? Umma ita taje tahado komi kawai nima ganin mutane nayi yau da kayan saka rana sun taho, so kike na nabada Umma agaban su? So kike amana kallon kananun mutane da basusan mesuke yiba? Yayama zanyi eh" da sauri Mama tace "gaskiya bazan yardaba, nibazan bari Hamida na ta auri mahaukaci ba nafadama bazan bari ba kacema Kaka anfasa, nibazan bama y'ata mara lafiya ba" shima Abba cikin tsananin bacin rai kyace "sokike ta tsinemini? Ke bakiga Umman bane? Yaya zanyi da ita mahaifiyata ce dole kome tace namata biyayya, yaya zanyi Haleematu fadamin" fashewa da kuka sosai Mama tayi takasa cewa komi hakan yasa ya dafe kanshi yay shiru yasan Mama da mugun hakuri kuma yasan da gaskiyan ta amma yaya zaiyi? Shi kanshi abin yafi karfinshi, ahankali ya janye hanunshi daga kan

goshinshi ya matsa kusa da Mama ya rungumota jikinshi yana shafa bayanta yana jijjigata harta rage kukan ahankali yace "kiyakuri Haleematu, i need your support more than anything ayanzu, kece karfi na, idan kika karaya haka ninai yaya eh? Nasan Umma bata kyautaba amma kiyakuri, bamu miki adalci ba amma kiyakuri uwata ce dole nabi abinda tace, addu'a zamubi yarmu dashi, babu wanda ya isa yahana kaddara faruwa, kuma rabo na kisa bamusan me Allah yagani yahada suba, kawai mubisu da addu'a kinsan Allah na karban addu'an uwa akan yaranta, mumata addu'a kinji muga me Allah zaiyi, am sorry for hurting you kinji best wife, stop crying" gyadamai kai Mama tayi ahankali hakan yasa ya sumbaci gaban goshinta yasake rungumeta da kyau yace "akwai wasu kudi danake expecting once anbiyani zan baki kije ki siyo mata duk abinda yadace kinji" gyadamai kai tayi nan yadinga bata kalamai masu ddi da sanyaya rai harta sauko sosai ta share ta barma Allah komi kawai ta tasa addu'a agaba.




***

Kwanaki nataja sosai gidaje biyun aketa shirye shiryen biki, gabaki daya Aadil baida lafiya magungunan hausan da Baffa yasa akemai da in yasha ma amai yakeyi gashinan gashinan ne kawai mugun so yake yaga Hamida bana wasaba, gashi kullum yana dakin Mami inyaga Aabid wani irin tsoranshi yakeji yayta tuna yanda yamai mugun duka yay lamo koya kulle ido, Aabid gabaki daya yadawo wani iri shima saiyahau ciwon abun yama Mami yawa ga Aadil ga Aabid Abba yay wani irin ramewa shima haka dai suka dinga lallabawa Dr na zuwa treating nasu a gida, Aadil harda drip yasha kusan hudu.


Kaka takawo yar buzuwa anata ma Hamida gyaran amare bana wasaba, gabaki daya Hamida duktai zuru zuru kullum saitaci kuka, ko kadan batason auren nan dudda kullum tunanin Aadil take bana wasaba takuma rasa mesa take tunanin shi, tasan yana chan yana nemanta yanzu yana kuka rabonta dashi tun yana asibiti.


Kuka, kukane aikinta gashi tai wani irin kyau tai haske bana wasaba, fatarta dama yanada taushi saiya kara wani extra ordinary taushi, ga sheki ga kamshi datake yi, ana saura sati daya biki family Aadil suka kawo akwati nagani nafada guda 12, Kaka harda rawa tama manta da Faruk da rabonta dashi yafi sati, dasuka tashi tafiya aka hadamusu shatara na arziki, Hamida kin duba kayan tayi Zainab da Ihsan sai rawa suke sunata murna Hamida zatai aure, Mami dai kullum bayan magrib takan koya mata yan dabaru na zaman gidan miji, ko kadan tarasa sukuni bama ta iyacin abinci hakan yasa wani irin ciwo yakamata tafara zazzabi bana wasaba, har aka fara sha'anin biki yayyinta duka harda su Ayush duk sunzo sai mamakin aurenta suke yaushe Hamida tai miji, yaushe tai saurayi kawai sunji bikin ne, ranan walima saida Abba yakira wata likita sabida yanda ta dinga kwara amai hankalin Mama duk yabi yatashi sai sannu kowa yake mata.


Ana gobe daurin auren Abie yakusa karamin hauka adakinshi, baisan me Ozo zaimai ko Aadil gobe idan an daura auren ba, baisan wani hukunci Ozo zai yankemai ba, dudda dai har yau baisan meye dalilin dayasa Ozo yace kar Aadil yasake yay aure ba amma yadamu, abinda haryau yake bashi mamaki shine Ozo yariga ya maidashi yaro ababba to menene dalilin shi nacewa karya sake yabari yay aure, kodai aure zaisa Aadil yadawo normal ne? Ajiyan zuciya ya fuzar yana fifita kanshi da hulan daya zare daga kanshi yacigaba da tunani, gashi yanzu Ozo bai bayyanar mishi ba koda warning ne yabashi ba, kawai yay shiru yasakamai ido kome yake planning oho. 



********

Hausawa sunce rana bata karya!

Yau asabar misalin karfe biyu na rana dubbanin jama'an dake cikin babban masallacin janbulo suka shaida dauren auren Hassan Abdullahi Aadil da Amatullah Isma'il akan sadaki dubu dari inda jama'a da dama suka hallarci auren suka shaida, Aadil dayaci gayu sosai ya rame kaman bashiba yana tareda su Baffa da Suleman dan tun safe yau ba'aga Aabid ba sai murna yake yana tsalle, yau yay wani irin kyau na musamman yawani irin cika yafito sak cikakken namiji dashi kodan yau auren shine oho amma dai yau akwai wata irin haiba da kwarjini daya kara na musamman dahar abin saida yabama Baffa mamaki yadai share yacigaba da attending to jama'a, Abba ma sai neman Faruk yake bai ganshi ba dan rabon shi da Faruk tun sati daya daya wuce. 


Misalin karfe nine nadare akazo tafiya da amarya Hamida kuka kaman zata shide harsaida tasa Mami kuka da kyar yayyinta da yan uwanta suka rakata gidan mijinta daya mugun hadu.

[11/28, 9:58 AM] +234 701 218 1461: 38..


Part din Baffa aka kaita dan nan ake taro, part din ya cika da su yan uwan su Mami da Big Mum, matan su Suleman da yan uwa da abokan arziki, da kawayen su Mum, wa'azi sosai akai mata sanan aka fara mata manni ana liki ana rawa kafin abama Maman ango wuri, Mami ta taso tai shiga na alfarma tana murmushi sosai danyau tana cikin tsananin farin ciki tazo ahankali ta yaye hulan alkyabban, fuskar Hamida yafito tana kuka kanta akasa, guda aka dauka su Zainab da Yayyinta nata murmushi sunajin dadi, ahankali Mami tabude wani dan box dake hanunta taciro wani sarkan gold babba nan aka fara guda dan al'adan sune hakan, ta sanyama Hamida sarkan awuya sanan takamo hanunta tasaka mata warwaro biyu takamo dayan hanun tasamata biyu sanan ahankali tai cupping fuskarta tana murmushi tace "welcome to the family daughter na" ta sumbaci gaban goshinta nan dakin yadau guda anata ihu da ayiriri, ta tashi takoma sit dinta nan haka kowace matan dakin ke tasowa one by one suna bata gift dinsu Hamida tagaji iya gajiya danhar ji take kaman zata sume sai wuraren sha daya sanan aka dunguma aka kaita bangarenta dakeda wani irin mugun kyau ana wake wake akasa tai alwala sanan aka bude dakin aka shiga da ita, dakin na wani irin hadadden kamshi turarukan wuta, babban falone da akai komi ash da black aka wuce da ita bedroom dinta dakenan off white da gold akazaunar da ita akan makeken gadonta, family Aadil bayan sun gama yan wake wake da wa'azi suka juya suka musu sallama suka fita yarage daga Hamida sai family ta, zama kusa da ita Anty Lami tayi ta rungumota tace "wai bazakiyi shiru ba haka kukan ya isa Hamida, kar zazzabi yataso miki kinga dama bakijin dadi" ta kalli Ayush dake kokarin cire sarkan wuyanta tace "Ayush zoki rakata tayo wanka sanan tazo taci abinci tasha magani" tashi Ayush tayi takama hanunta suka shiga hadadden bathroom din dakin sukuma su Zainab da Ihsan da yan uwanta sukai falo suna kallon hadadden gidan dayasha kayan more rayuwa.


Fitowa sukayi daga bayin tana wani irin kamshin turare ta daura wani farin towel daya tsaya mata acinya sai wani irin sheki take an mata gyaran gashi, gashin yay wani irin tsawo yay baki sosai yana sheki da kamshi, wani doguwan riga na bacci Anty Lami ta bata tana kallon yanda idanunta suka kumbura suntun tasaka sanan tasa hijabi tai nafila dantai isha'i tun agida tana idarwa Anty Lami tahada mata wani farfesun kaza dasuka taho dashi Kaka ta basu tace abata da daddaren dawani kunun aya, da kyar ta iya taci sanan tasha kunun ayan sosai tabata paracetamol tasha tana yatsine fuska daurewa kawai take amma sotake tai kuka sosai ko zuciyarta zatai mata sanyi, wai yanzu shikenan tai aure, saida abincin yadan kwanta sanan Anty Lami tace ta tashi taje ta kwanta ahankali ta tashi tana kallon durmemen lumtsatsen gadon tahau kai gudun kar Anty Lami tamata fada Anty Lami ta lulubeta da bargo sanan ta kashe mata wuya tace "kiyi bacci karkiyi ciwo, bari muje falo mu gyara jere anjima zan shigo kinji" gyadamata kai tayi ahankali Anty Lami tawuce tafita zuciyarta cike da tausayin yarinyar.


 Falo sukaje sunata hira suna ciye ciye suna zaga gidan.

Kasa koda rufe ido tayi sai kukan datakeyi bana wasaba ko kadan batason auren nan, yaya zatayi tai rayuwa da Aadil? Tayaya? Sosai take missing Mama so kawai take taje gidansu tai kwanciyar ta adakin Mama, kuka tai sosai har kanta yafara wani irin sarawa, daga bayane bacci ya awon gaba da ita.


Sallama Mami tayi Baffa yabata izinin shigowa bude kofar dakin tayi ta shiga tana kallon Aadil dake kwance kan gadon Baffa hanunshi rike da chocolate yana share hawaye Baffa kuma na zaune gefenshi da alamu magana yakemai, yana ganin Mami yatashi zaune da gudu yana kallonta yana turo baki yana shirin fashewa da kuka, ahankali ta zauna kusada shi kan gadon da saura yafada jikinta ya rungumeta muryanshi narawa sosai yace "where is my Hamida Mami?" murmushi Mami tayi ta daura hannu kan wuyanshi sabida zafin dataji sosai tace "don't worry zaka ganta gobe kaji" make mata jafada yayi a shagwabe hawaye na gangarowa daga idanunshi yace "i want to see her now" shiru Mami tayi tana kallonshi ganin ya chanza matayau saikuma tai murmushi tace "zaka ganta gobe kaji" fadawa yayi jikinta yafashe da kuka sosai, shafa bayanshi tayi ta kalli Baffa cikeda damuwa tace "banga Aabid ba Baba, numbershi baya shiga, baban suma bangan shiba kona tambayeshi koyay trying number shi, duk bangan suba Baba"  gyara zama Baffa yayi yace "Aabid yace yana Lagos yaje wani aiki dazu nakirashi da banganshiba" da sauri Mami tace "shine bai fadamin ba" tai maganan asanyaye ta kalli Aadil dake kuka ajikinta tace "tashi muje ka kwanta Aadil yauka dade bakai bacci ba" Dakinsu Mami tabude ya ta shiga yana biye da ita zama tayi abakin gadon su yazo ya kwanta ya daura kanshi kan cinyarta yana goge kwalla ahankali yace "Mami where is Bid" kallon fuskarshi tayi kafin ahankali tasa hanunta cikin soft gashin kanshi ta shafa ta kakalo murmushi tamai tace "don't worry he will be back tomorrow kaji" gyadamata kai yayi yace "Mami My Hamida" murmushi tamai tace "itama zaka ganta gobe kaji" gyadamata kai yayi ahankali ya chusa kanshi cikin cinyarta yana kuka sosai yace "i want to see her now, you said she's my wife ko?" anatse tace "yes she's your wife Aadil, zaka ganta gobe i promise" sakin kuka yayi sosai yana shure kafa, tagumi Mami tayi tana kallonshi tama kasa magana kukanshi nataba ranta amma dole yay hakuri har gobe yanzu da mutane awurin Hamida, ahaka bacci yay gaba dashi sai ajiyan zuciyan kuka yake cikin dabara ta zare kafar nata ahankali tana kallon agogon bangon dakinsu ganin sha biyun dare harda minti biyar to ina Abie? Abie baitaba dadewa haka baidawo gidaba, tagumi tayi tasake juyowa ta kalli Aadil dake bacci ta kalli wurin da Aabid yake kwanciya taji dukta damu tana wani irin mugun kewanshi, wayarta taciro tai dailing number Aabid din amma bai shigaba hakan yasa ta juyo ta tofama Aadil addu'a taja bargo tarufe shi sanan ta tashi tafita daga dakin harzata shiga dakinta saikuma tabude dakin Abie ahankali ta shiga babu kowa dakin sai kamshi da dakin yakeyi maida kofan tayi tarufe tana kallon ko'ina tadawo ta zauna akan gado tai dailing number Abie amma sai cemata switch off yake hakan yasa ta tashi tawuce ta shiga bathroom dan dama dakinta cike yake da mutane, kaya tacire tafara wanka saida tagama sanan ta daura towel tadau brush tafara  kara taji sosai kaman fadowan abu hakan yasa ta cire brush din daga bakinta da sauri magana taji. "wayyo Allah Ozo kayafemin, great ine Ozo forgive me, wayyo karka kasheni dan Allah banso namutu yanzu narasa yanda zanyi nahana auren ne, Ozo please don't purnish me, Oz..." da sauri Mami ta jefar da brush din ko dauraye baki bata tsaya yiba jin muryan Abie tabude bayin da sauri tafito wani irin kwalalo ido tayi tace "innalillahi wa innailaihi raji'un Abie".

38..


Part din Baffa aka kaita dan nan ake taro, part din ya cika da su yan uwan su Mami da Big Mum, matan su Suleman da yan uwa da abokan arziki, da kawayen su Mum, wa'azi sosai akai mata sanan aka fara mata manni ana liki ana rawa kafin abama Maman ango wuri, Mami ta taso tai shiga na alfarma tana murmushi sosai danyau tana cikin tsananin farin ciki tazo ahankali ta yaye hulan alkyabban, fuskar Hamida yafito tana kuka kanta akasa, guda aka dauka su Zainab da Yayyinta nata murmushi sunajin dadi, ahankali Mami tabude wani dan box dake hanunta taciro wani sarkan gold babba nan aka fara guda dan al'adan sune hakan, ta sanyama Hamida sarkan awuya sanan takamo hanunta tasaka mata warwaro biyu takamo dayan hanun tasamata biyu sanan ahankali tai cupping fuskarta tana murmushi tace "welcome to the family daughter na" ta sumbaci gaban goshinta nan dakin yadau guda anata ihu da ayiriri, ta tashi takoma sit dinta nan haka kowace matan dakin ke tasowa one by one suna bata gift dinsu Hamida tagaji iya gajiya danhar ji take kaman zata sume sai wuraren sha daya sanan aka dunguma aka kaita bangarenta dakeda wani irin mugun kyau ana wake wake akasa tai alwala sanan aka bude dakin aka shiga da ita, dakin na wani irin hadadden kamshi turarukan wuta, babban falone da akai komi ash da black aka wuce da ita bedroom dinta dakenan off white da gold akazaunar da ita akan makeken gadonta, family Aadil bayan sun gama yan wake wake da wa'azi suka juya suka musu sallama suka fita yarage daga Hamida sai family ta, zama kusa da ita Anty Lami tayi ta rungumota tace "wai bazakiyi shiru ba haka kukan ya isa Hamida, kar zazzabi yataso miki kinga dama bakijin dadi" ta kalli Ayush dake kokarin cire sarkan wuyanta tace "Ayush zoki rakata tayo wanka sanan tazo taci abinci tasha magani" tashi Ayush tayi takama hanunta suka shiga hadadden bathroom din dakin sukuma su Zainab da Ihsan da yan uwanta sukai falo suna kallon hadadden gidan dayasha kayan more rayuwa.


Fitowa sukayi daga bayin tana wani irin kamshin turare ta daura wani farin towel daya tsaya mata acinya sai wani irin sheki take an mata gyaran gashi, gashin yay wani irin tsawo yay baki sosai yana sheki da kamshi, wani doguwan riga na bacci Anty Lami ta bata tana kallon yanda idanunta suka kumbura suntun tasaka sanan tasa hijabi tai nafila dantai isha'i tun agida tana idarwa Anty Lami tahada mata wani farfesun kaza dasuka taho dashi Kaka ta basu tace abata da daddaren dawani kunun aya, da kyar ta iya taci sanan tasha kunun ayan sosai tabata paracetamol tasha tana yatsine fuska daurewa kawai take amma sotake tai kuka sosai ko zuciyarta zatai mata sanyi, wai yanzu shikenan tai aure, saida abincin yadan kwanta sanan Anty Lami tace ta tashi taje ta kwanta ahankali ta tashi tana kallon durmemen lumtsatsen gadon tahau kai gudun kar Anty Lami tamata fada Anty Lami ta lulubeta da bargo sanan ta kashe mata wuya tace "kiyi bacci karkiyi ciwo, bari muje falo mu gyara jere anjima zan shigo kinji" gyadamata kai tayi ahankali Anty Lami tawuce tafita zuciyarta cike da tausayin yarinyar.


 Falo sukaje sunata hira suna ciye ciye suna zaga gidan.

Kasa koda rufe ido tayi sai kukan datakeyi bana wasaba ko kadan batason auren nan, yaya zatayi tai rayuwa da Aadil? Tayaya? Sosai take missing Mama so kawai take taje gidansu tai kwanciyar ta adakin Mama, kuka tai sosai har kanta yafara wani irin sarawa, daga bayane bacci ya awon gaba da ita.


Sallama Mami tayi Baffa yabata izinin shigowa bude kofar dakin tayi ta shiga tana kallon Aadil dake kwance kan gadon Baffa hanunshi rike da chocolate yana share hawaye Baffa kuma na zaune gefenshi da alamu magana yakemai, yana ganin Mami yatashi zaune da gudu yana kallonta yana turo baki yana shirin fashewa da kuka, ahankali ta zauna kusada shi kan gadon da saura yafada jikinta ya rungumeta muryanshi narawa sosai yace "where is my Hamida Mami?" murmushi Mami tayi ta daura hannu kan wuyanshi sabida zafin dataji sosai tace "don't worry zaka ganta gobe kaji" make mata jafada yayi a shagwabe hawaye na gangarowa daga idanunshi yace "i want to see her now" shiru Mami tayi tana kallonshi ganin ya chanza matayau saikuma tai murmushi tace "zaka ganta gobe kaji" fadawa yayi jikinta yafashe da kuka sosai, shafa bayanshi tayi ta kalli Baffa cikeda damuwa tace "banga Aabid ba Baba, numbershi baya shiga, baban suma bangan shiba kona tambayeshi koyay trying number shi, duk bangan suba Baba"  gyara zama Baffa yayi yace "Aabid yace yana Lagos yaje wani aiki dazu nakirashi da banganshiba" da sauri Mami tace "shine bai fadamin ba" tai maganan asanyaye ta kalli Aadil dake kuka ajikinta tace "tashi muje ka kwanta Aadil yauka dade bakai bacci ba" Dakinsu Mami tabude ya ta shiga yana biye da ita zama tayi abakin gadon su yazo ya kwanta ya daura kanshi kan cinyarta yana goge kwalla ahankali yace "Mami where is Bid" kallon fuskarshi tayi kafin ahankali tasa hanunta cikin soft gashin kanshi ta shafa ta kakalo murmushi tamai tace "don't worry he will be back tomorrow kaji" gyadamata kai yayi yace "Mami My Hamida" murmushi tamai tace "itama zaka ganta gobe kaji" gyadamata kai yayi ahankali ya chusa kanshi cikin cinyarta yana kuka sosai yace "i want to see her now, you said she's my wife ko?" anatse tace "yes she's your wife Aadil, zaka ganta gobe i promise" sakin kuka yayi sosai yana shure kafa, tagumi Mami tayi tana kallonshi tama kasa magana kukanshi nataba ranta amma dole yay hakuri har gobe yanzu da mutane awurin Hamida, ahaka bacci yay gaba dashi sai ajiyan zuciyan kuka yake cikin dabara ta zare kafar nata ahankali tana kallon agogon bangon dakinsu ganin sha biyun dare harda minti biyar to ina Abie? Abie baitaba dadewa haka baidawo gidaba, tagumi tayi tasake juyowa ta kalli Aadil dake bacci ta kalli wurin da Aabid yake kwanciya taji dukta damu tana wani irin mugun kewanshi, wayarta taciro tai dailing number Aabid din amma bai shigaba hakan yasa ta juyo ta tofama Aadil addu'a taja bargo tarufe shi sanan ta tashi tafita daga dakin harzata shiga dakinta saikuma tabude dakin Abie ahankali ta shiga babu kowa dakin sai kamshi da dakin yakeyi maida kofan tayi tarufe tana kallon ko'ina tadawo ta zauna akan gado tai dailing number Abie amma sai cemata switch off yake hakan yasa ta tashi tawuce ta shiga bathroom dan dama dakinta cike yake da mutane, kaya tacire tafara wanka saida tagama sanan ta daura towel tadau brush tafara  kara taji sosai kaman fadowan abu hakan yasa ta cire brush din daga bakinta da sauri magana taji. "wayyo Allah Ozo kayafemin, great ine Ozo forgive me, wayyo karka kasheni dan Allah banso namutu yanzu narasa yanda zanyi nahana auren ne, Ozo please don't purnish me, Oz..." da sauri Mami ta jefar da brush din ko dauraye baki bata tsaya yiba jin muryan Abie tabude bayin da sauri tafito wani irin kwalalo ido tayi tace "innalillahi wa innailaihi raji'un Abie".

_🌹IN BANI 🌹_ 



39 - 40



Maman Abd Shakur




Da yatsa Ozo dake jikin bangon dakin yasake daga Abba yabugashi da kasa yafesomai wani abu dayake nan kaman hayaki daga bakinshi jikin Abie, wani irin ihu Abie yayi. "wayyo Ozo wlh, wlh, wlh natuba dan Allah azabar nan tamin yawa bazan iya daukar taba, narasa yanda zanyi nahana auren ne mariki nane yahada, saisa narasa yanda zanyi, wayyo Ozo" dawani irin gudu Mami tazo ta tsugunna daidai inda yake kwancen akasa dagashi saidan gajeren wando tarike mai hannu arude takirashi. "Abie" kojinta Abie bayayi sai kuka dayakeyi yana sosa jikinshi dayay rudu rudu kaman anzane shi da bulalan inji, da sauri Mami tasake jijigashi ta kwalamai kira ganin yanda yake abu kaman mahaukaci. "Abie, Abie" afirgice ya kalleta saikuma ya kalli bango dakin ganin Ozo yabace yasa yawani irin rungume Mami ya daura kanshi akan cikinta yana wani irin nishi kaman wanda ake shirin kashewa yagudo, ya ririketa gam yace "help me, Maryama ki taimakamin dan Allah kitaimaka min, Ozo zai kasheni na karya doka akaro nabiyu" sosai gaban Mami kewani irin faduwa all maganganun daya fadi na dawomata kaman yanzu yayisu da sauri tace "me kake nufi dakai kokarin hana auren kakasa marikin kane yahada auren Abie?" da sauri Abie yadago kai ya kalleta suka hada ido yana wani irin nishi yana sauke ajiyan zuciya "kai shiru bakace komiba, waye Ozo? Wani doka ka karya" Mami ta tambaya kaman mai tuhuman shi akan wani abu lumshe ido yayi da sauri dan baimasan lokacin daduk ya faffadi abubuwan nanba, bazai iya jure kallonta ba hakan yasa yatashi ahankali yanadan dingishi jikinshi yay rudu rudu yafada gado yaja bargo tundaga kai har kafa ya lulluba Mami tabishi da kallon tuhuma zaitai magana saikuma tai shiru ta buga tagumi ahankali tana kallon kowani bangare na dakin kaman yauta fara ganin dakin, takai kusan awa daya ahaka kafin ta tashi tai wajen wardrobe tabude wardrobe din ta zaro wani doguwan riga na bacci mai dogon hannu ta zura tadau hula tasaka sanan ta maida sip din tarufe tadau hijabinta tasaka tasa silipas ta fita daga dakin, dakin Aadil ta shiga tana kallonshi har lokacin bacci yake maida kofar tayi tarufe ta shigo abakin gadon ta zauna ta daura hanunta akan kunenshi tana shafa kunen ahankali tana kallonshi maganganun Abie nadawo mata dasuka mugun daure mata akai, abinda ma yafaru gabaki daya ya daure mata kai, ihun me Abie yake, daga ina yake dan ai data shigo daki baya daki bata ganshi ba, tanadai cikin wanka taji kaman an wurgo abu daga sama, menene wai meke faruwa? wani irin ajiyan zuciya ta sauke kafin ahankali takama hanun Aadil din tarike gam tana kallon fuskanshi da sauri ta share hawayen daya zubomata ahankali tace "Aadil, My Hassan, my boy, i want you to be fine, Aadil ka warke, be fine and help me understand everything kaji, yau is a happy day for you, my not so little Aadil, my not so little yaro, Aadil dina is now a grown-up yaro magidanci mai iyalinshi" lumshe ido tayi da sauri jin hawaye zasu zubo mata da kyar ta iya ta hadiye kukan dan she really wanna be strong for her kids takai kusan 2min ahaka kafin tabude idanun ahankali ta kalli sama ahankali tace "Ya Allah, banda abin dogaro saikai, Ya Allah namika dukkanin al'amurana gareka nasan komi dayake faruwa jarabawa ce agareni kuma inaso inci jarabawan ka agareni, Ya Allah kabama Aadil lafiya Ya Allah ka sanyama auren nan dayayi albarka, Ya Allah ka kulamin kakuma tsaremini yarana aduk inda suke, Ya Allah ka tsaremin Aabid kadawo min dashi lpy Ya Allah kabama dan uwanshi lpy" ahankali tace Ameen kafin ta mike tabude bayinsu ta shiga ta dauro alwala tafito ta shimfida dadduma tafara salloli, sai wuraren uku da rabi sanan bacci yay gaba da ita, hayaniyan jama'a ne ya farkan da ita da asuba kallon gadon tayi ganin Aadil na bacci yasa ta tashi ta shiga ta dauro alawala tazo wurin gadon ta bubbugamai kafa tana murmushi yanda yay kyau da bacci. "Aadil, Son" ahankali ya turo baki yace "uhm" murmushi tayi sosai dan Aadil ya iya shagwaban banza, kara saukar da murya tayi dan saiya iya cewa shiba yanzu zai tashiba. "tashi my son time for subhi prayer, tashi kabi Baffa kuje masallaci kaga yanzu you are a married man, Hamida is your wife you need to be praying a jam'i" da sauri yabude ido jin Mami takira sunan Hamida, tashi yayi zaune  yana mitsittsika ido agajiye yace "where's my Hamida Mami?" folding hannu Mami tayi akirji tana kallonshi batare data amsashiba, da sauri yakara bude idonshi yana turo mata bakin shagwaba yace "good morning Mami na, where's my Hamida" murmushi tayi tace "zaka ganta anjima, go brush ka dauro alwala kazo kai salla in the night zaka tafi chan part dinku" make mata kafada yayi yace "i want to shower first my body is itching" da sauri tace "to sarkin wanka, tashi to kaje kayi" tashi yayi ahankali cikin layin bacci yay hanyar bayin Mami tabishi da kallo, ya bude kofan ya shiga bathroom din yarufo sanan tai wajen wardrobe dinshi taciromai white jallabiya ta ijiyemai kan gado itakuma tahau kan dadduka tafara salla, yadan dade kafin yafito sanye da bathrobe blue hanunshi da dan karamin towel fari yana goge fuskarshi sai kamshi yakeyi, tsayawa yayi yana kallon kan gadon wurin Aabid sosai yake wani irin kewanshi, idar da sallan Mami tayi tace "get dress kazo katafi mosque bari naje naduba babanku" tabude kofa tafita ahankali yadau man yashafa sanan yacire bathrobe din ya shirya tsaf cikin jallabiyan dayamai kyau sosai ya cikashi dam yasa takalmin shi sai wani irin hadadden kamshi yake, zama yasake yi akan gadon yana kallon bangaren Aabid, ahankali yadau wayarshi daya gani kan side drawer yadanna yana turo baki yay dailing number Aabid din dayake fushi dashi sosai dan hakanan yaji yana missing dinshi ringing daya Aabid dake kwance akan gado Vanessa a gefenshi tana bacci, yana rike da wayarshi  yana kallo yana tunanin dan uwan nashi wayar tai ringing yaga sunan Aadil.


Picking call din yayi yakai wuyan kunenshi kirjinshi namai wani irin ciwo murya chan kasa yace "hello" jin muryanshi yasa Aadil yakasa daurewa yasakin mai kuka ahankali yana goge ido batare dayace komiba, da sauri Aabid yature hanun Vanessa dake jikinshi yatashi ya zauna shikan shi baisan irin son dayake ma Aadil ba saisa yakasa yafema kanshi akan mugun dukan dayamai saisa kuma yabar gidan dan inhar akai auren agabanshi baisan mezai aikata ba, lumshe ido yayi yanajin kukan har ranshi yace "rascal" yakira sunan asanyaye kaman bashiba, makemai kafada Aadil yayi yana kuka batare dayace komiba, ahankali Aabid yace "I've tried many times nacema sorry but kanata fushi dani inka ganni guduna kakeyi, kakimin magana, ka tsaneni, kanata zuciya dani why are you calling me now kanamin kuka kana tadamin da hankali so kake ciwon zuciya yakamani namutu?" yay maganan yana dafa kirjinshi dakemai zafi sosai, da sauri Aadil ya girgiza kai cikin kuka yace "sorry" lumshe ido Aabid yayi kaman zaiyi kuka yace "am sorry too twin Bro, I've hurt you, am such a bad brother, am sorry Aadil, am so so so soo sorry" yay maganan while his tone was breaking kaman zaiyi kuka, da sauri Aadil ya share idonshi yace "are you crying?" girgiza mai kai yayo ya share hawayen daya zubomai da sauri yace "a'a" duk sukai shiru Aadil yanajin wani iri kaman something is wrong with Aabid, ahankali yace "are you fine?" gyadamai kai yayi ya gyara muryanshi trying to sound fine and normal yace "yes, where is your wife?" kaman zaiyi kuka yace "i don't know" gyadakai Aabid yayi yanajin wani iri sosai, ahankali Aadil yace "i miss you, you are not a bad brother, you are very good and I love you so much Bid, yaushe zaka dawo?" murmushi yayi hawaye ya gangaro mai daga ido, murya chan kasa yace "soon, don't worry i will buy something for you kaji, promise one thing" da sauri yay murmushi yace "what?" murya chan kasa ya runtse ido yace "take care of yourself and Hamida sosai, don't make her cry okay" washe baki yayi yay fari da ido yace "okay, i promise i will take care of Hamida my wife" murmushi yayi mai ciwo yace "je dakin Baffa kutafi masallaci is time for salat nima zantafi ne" da sauri yace "ok bye" bye yace yakatse wayan yatashi da sauri ya shiga bayi yana goge hawaye ya sakin ma kanshi shower. 




Tashi Aadil yayi yana murmushi sosai yanajin dadin maganan dayayi da Aabid yafito daga dakin daidai Mami da Baffa sun fito Baffa yakama hanunshi suka tafi masallaci.

Already Big Mum nawajen masu girkin da aka dauko tana gayamusu mezasuyi Mami kuma ta wuce dakinta da sallama ta shiga dakin ganin babu Abie akan gado yasa tai shiru tai tunanin hala yana masallaci ne hakan yasa ta shimfida dadduma tai salla.



**

Shigowa Anty Lami tayi ta tadata da kyar ta iya ta bude idanunta dasuka kumbura dan bacci bai dade da kwasheta ba ahankali ta tashi ta zauna tana sosa ido Anty Lami tace "yi sauri jeki dauro alwala kizo" bayi ta shiga ahankali bata wani jimaba ta fito daure da alwala komi atsanake takeyi dan ko kadan batada karfi tadau hijabin tahau kan dadduma tafara salla itakuma Anty Lami ta shiga bayin tahada mata ruwan wanka da turarukan da ake samata mai zafi sanan tafito taje gaban wardrobe dan ciro mata kayan dazata saka wani hadadden lace pitch tadauko an mata dinki riga da skirt ta ijiye sanan taciro undies din dazatai amfani dasu dukta ijiye ta juyo ta kalleta jinta sallame tace "yauwa inkin gama azkar din kiwuce bayi kiyo wanka ga kayan dazaki saka inkin saka sai zainab tazo tamiki kwalliyan" gyadamata kai tayi ahankali hawaye na taruwa a idanunta Anty Lami tawuce tafita, tana gama azkar din ta linke dadduman ahankali tana kara kallon dakin yanda dakin keda kyau sosai ta share kwallan daya zubomata da sauri tawude ta shiga bayin ahankali, tajima dan taji dadin ruwan zafin sosai kafin tafito daure da towel duk jinta take wani iri she's not just happy, zama tayi ta shafa mai, sanan ta shirya cikin kayan tsaf dasuka mata kyau bana wasaba, sun kamata sun mata chass ajiki, shigowa dakin Ayush dasu Zainab sukayi suna ihu, Ayush tace "wo amaryan Aadil, amaryan malam Hassan, wanan glow haka aisai kisa angonki ya suma, zee yimata makeup" da sauri Zainab tace "to bari nadauko makeup bag din" Ihsan tazo da sauri tarike mata hannu tana murmushi tana kallonta tace "kinyi kyau sosai Anty Hamida" dan murmushi tamata hawaye na shirin zubowa Anty Ayush ta harareta. "wai kukan bai isabane" daidainan Zainab ta shigo dawata katuwar jaka tazo tafara tsara mata makeup, subhannallah tsarkiya tabbata ga ubangijin daya tsara wanan hallitan! bakaramin kyau Hamida tayiba kaman ka saceta kagudu, sai hotuna suke daukan ta ganin abin nasu bamai karewa bane suna neman su kara sata kuka yasa Anty Lami ta kadasu duk kowa yaje yay wanka dan yau zasu bar gidan nan sukai wanka aka cici gayu kafin Mami ta turo ma'akatan part dinta aka fara jera musu abinci kala kala sanan sukabar shashin da kyar suka tasata agaba tadansha tea da chips aka ccici abinci sanan suka sake gyara gidan ko ina na kamshin turaren yan maiduguri, haka suka wunin mata ranan har yamma jama'a sai shigowa suke suna dubata duk wanda yaga Hamidan saiyay mamakin kyawun matar Aadil din, yan gulma nayi suna cewa hala iyayenta kudi sukagani saisa suka yarda suka bama mahaukaci inba hakaba ina mahaukaci ina wanan shuwa arab din.


Bayan isha'i suka shirya tsaf zasu tafi bayan sunsa tasake wankan ruwan turare ansake mata hadadden gayu, kuka, kuka Hamida bana wasaba takeyi kaman ana yankata dan harda bubbuga kafa akasa hankalinta yawani irin tashi dansai yanzu ta yarda yes anmata auren dan gashi yan uwanta zasu tafi su barta bada ita zasuba, janta dakinta Anty Lami tayi tama yan uwanta da duk sukai wani iri sabida tausayin Hamidan alamu dasu tafi waje su shiga mota sanan ta zauna kusa da Hamidan dake kuka sosai takama hanunta tarike ahankali takira sunanta. "Amatullah" dago jajayen idanunta tayi ta kalli Anty Lami, ahankali Anty Lami tace "kindai tuna fadan da mahaifinki da mahaifiyar ki suka miki ko, still shi zan kara tunatar dake, karkice dankinga matsalan mijinki yasa kikimishi biyayya kokin bin umurninshi, a'a, koyaya yake aljannar ki na karkashin kafarshi, kome yakeso kimishi, komeye bayaso karkimai, ki rufama mijinki asiri sanan ki rike sirrin shi, matsalar mijinki matsalar kice, farin cikinshi farin cikin kine, kikuma dage damishi addu'a nasan koba yanzu ba, koba yauba watarana zai bude ido yay alfahari dake dan kin kasance mace data soshi takuma zauna dashi da lallurarshi, kidau auren ki amatsayin jahadin ki, ki rike Allah nasanki da karatun Alqurani da yawan azkar karki sakesu ki kara rikesu da kyau kinji, kina tare da yan uwan mijinki ne kidinga musu biyayya tsakanin ki da kowa should be mutunci, respect and peace kinji Hamida na" gyadamata kai tayi ahankali tawani irin fadawa jikinta tasaki kuka sosai mai tsumma rai bubbuga bayanta Anty Lami tayi tana murmushi danji tayi kaman zatai kuka itama kafin ahankali ta janyeta daga jikinta tana kallon yana take kuka take haki tace "ina zuwa bari naduba wani abu a kitchen dinki nai plugging abu" da sauri tafita daga dakin tai waje duksu Mami na tsakar gida suka sallama na mutunci sanan ta shiga mota bayan sun hada musu shatara na arziki suka tafi.





Ita kadai aka bari abangaren sai kuka take, kukan yaki tsayawa, sallama taji anyi a babban falon shiru tayi taki amsawa sai hawayen data cigaba da sharewa, shigowa Big Mum tayi da Baffa, sai Aadil dayaci gayu sosai cikin wata faran hadadden gizna yasaka hula tangaran dake mugun kyalli sai wani irin murmushi yake kaman anmai kyautan maka yana leka dakin kaman zaiga Hamidan da akace za'a kawoshi wurinta sai Suleman da Muhammad atare dashi dan tun safe ba'aga Abie ba, Suleman ya riko ledoji a hannu zama sukayi a falon Aadil sai murmushi yake yazauna kusada Baffa yace "grandfather where's my Hamida?" kallon Big Mum Baffa yayi yace "shiga ciki kifito da ita" tashi big Mum tayi tawuce tai wani corridor kafin ta tsaya gaban bedroom din tai sallama ahankali tabude kofan sake lulube fuska Hamida tayi da mayafi tana kuka mara kara, ahankali big Mum ta zauna kusada ita ta dafata tace "kukan ya isa haka daughter na, ke yarmu ce bazamu taba cutan kiba kinji, taso muje Baffa na nemanki" tai maganan tana rike mata hannu da taimakonta Hamida ta sauko daga kan gadon tasa takalmi Big Mum takara lullube mata fuska da gyalen sanan takama hanunta suka fita daga dakin tunda suka shigo falon Aadil kewani irin kallonta tundaga kafa harkai dudda baya iya ganin fuskarta sai uban murmushi yake, taba Baffa yayi batare daya janye idanunshi daga kallonta ba yace "grandfather is that my Hamida?" gyadamai kai Baffa yayi big Mum ta zaunar da Hamidan akan kujera, gyaran murya Baffa yayi yabude taro da addu'a sanan yamusu wa'azi sosai mai ratsa jiki kafin ya kalli Aadil yace "she is your wife Hassan take care of her, don't make her cry, always keep her happy be her companion, kudinga salla tare, kuci abinci tare and do everything tare, dis is your house and she is your wife keep her happy kaji" wani irin cute smile yayi dayawani irin karamai bala'in kyau ya gyadakai yace "I promise you grandfather i will keep my Hamida my wife happy, very very happy, but grandfather i want to see her face" kowa na dakin murmushi yayi Baffa dai saida yadan dara kafin ahankali yakai bakinshi saitin kunenshi yamai magana aciki wani irin murmushi Aadil yayi ya gyadama Baffan kai, Baffa ya kalli Big Mum yace "maida ita ciki saida safenku, Allah yamuku akbarka" dagata Big Mum tayi tamaidata daki tafito sanan su Baffa sukai hanyar kofa Aadil yadaga musu hannu yana murmushi sosai Big Mum sai dariya takemai suka fita wani irin tsalle yayi yadau ledojin da su Suleman suka tayashi dauka yay ciki dasu yana murmushi yana murna, ahankali yabude kofar bedroom din wani irin kamshi ne ya ziyarci hancinshi, shigowa yayi ahankali yana kallonta yanda har lokacin take lullube da gyale sai kuka take tana goge idanunta da gyalen maida kofar yayi yarufe yay wani irin raurau da ido ganin kuka take, ahankali yakarasa gabanta ya ijiye ledojin tsugunnawa yayi ta gabanta ya leka fuskarta yadaura hanunshi kan cinyoyinta yakira sunanta ahankali. "My Hamidah" cigaba da kukanta tayi tai kaman batajishiba dan wani irin haushin shi takeji bana wasaba, kaman zaiyi kuka yay wani irin rau rau da fuska kaman wani maraya yace "stop crying kinji" cigaba da kukan ta tayi kaman bada mutum yake magana ba hakan yasa ahankali ya mike tsaye yazauna gefenta yaja gyalenta yacire gabaki daya ya ijiye, hakan ya bayyanar da riga da skirt na wani material dake jikinta pink anmata hadadden dauri daya bayyanar da tukin gashinta ta tsakiya, wani irin kallo yabita kaman yaune rana tafarko daya fara ganinta gawani irin kamshi datakeyi kaman zai shide sabida dadi, jawota jikinshi da sauri.

41....



Mugun rudewa tayi jin hanunshi akan manyan perky boobs dinta, arude ta daura hanunta akan nashi tana kokarin ture hanun daga kan boobs din muryanta na mugun rawa tace "to ka...kasake..ni dan...dan Allah kaji" kin sakinta yayi yana makemata kafada yana squeezing boobs din da sauri da sauri yana lumshe ido yace "let's go and sleep" kafanta ne yafara rawa da sauri ta girgiza mai kai tana kokarin fizge ajikinta ta sakinmai kuka ahankali tana ture hanunshi daga kan boobs dinta dan yanda yake squeezing dinsu nasa duka jinin jikinta na freezing dan ba'a taba mata jiki haka arayuwanta ba, cikin tsananin tashin hankali tana kokarin fizge jikinta tai kasa tace "na shiga uku, dan Allah kasakeni Aadil kaji" fashe mata da kuka yayi yarasa inda zaisa kanshi ga erection dinshi sai dripping yake tacikin wando hakan yasa yafara manna erection din da soft warm bare buttock dinta ya matse gam jikinshi na rawa yadaura kanshi kan kafadarta ya cusa hancinshi cikin wuyanta yana shakan hadadden kamshin datake dan dafata akai da turare, kasa daurewa yayi hakan yasa ahankali yafito da harshen shi yafara lasan ruwan wuyanta dabata riga ta tsane da towel ba, yanda yake lashe ruwan wuyan nata yasa tasaki wani irin nishi daya fito daga edge of her throat ta lumshe ido jikinta na rawa dawata irin murya chan kasan makoshi tace "wa...was...shhhh" matsa boobs dinta yayi gabaki daya yana manna joystick dinshi ta bayanta wani irin mugun tsoro takeji bana wasaba jin something like rod yana zungurinta tabaya yana lashe mata wuya kaman wani sabon maye, sosai yakejin wani irin shauki dawani irin mugun sha'awa dabai tabajin arayuwanshi, janye bakinshi yayi daga wuyanta jin yanda take kuka sosai idanunshi sunyi jajajir, ahankali ya zare hanunshi daga kan boobs dinta yarike mata hannu yana leka fuskarta hawaye yamugun cika idanunshi yace "why are you crying?" ganin taki magana takasa daga idanu ta kalleshi yasa yasake rungumeta a kirjinshi yasaki kuka ahankali shima yana rungume da itan yabude kofar bathroom din zai fita da ita falo, cikin kuka ta tureshi tace "kasake ni zansa kayana" make mata kafada yayi yace "oh'oh" yadaura hanunshi kan switch din dake gefen kofar bathroom din, kashe wutan dakin yayi yana sheshekan kuka yace "let's sleep" yahau kan gadon rike da ita, fashewa tayi da kuka  sosai shima fashewa yayi da kukan yana share idanunshi da hannu daya yana kama erection dinshi dayaji yanamai zafi da ciwo da hannu daya yana kuka, ahankali yazare dayan hanun daga idanunshi yarike mata hannu yace "stop crying" da sauri taja bargon gadon ta lullube jikinta tana gyadamai kai dudda ma bata ganin fuskarshi sosai tace "to" kwaciya yayi gefenta sosai dan har sunajin numfashin juna yarike hanunta gam yana kuka sosai itakuma tana kokarin hana kanta kukan jin yanda nashi kukan yay tsanani, share idanunta tayi ganin tsoron datakeji yadan ragu ganin yadena tabata sai kukanshi datake ji har ranta, ahankali tace "why are you crying?" cikin kuka sosai dawani irin murya kaman na small baby so soft and calm yace "zafi" da sauri tace "stop crying, meke maka zafi?" da sauri yasaki hanunta yatashi ya kwance mazarin wandon shaddarshi yazame wandon tareda boxer din jikinshi ya cire ya wurga kasa, tadaiji motsi batasan meyake yiba hakan yasa tace "me kakeyi? Nace you should stop crying please kaga is late, meke ma ciwo?" hanunta yakamo ahankali yana turo baki yana kuka yadaura hanunta akan erected manhood dinshi da crowns din were wet sosai sabida yanda yaketa tsiyaya tun dazu, lumshe ido yayi da sauri yasaki wani irin numfashi mai karfi jin soft moist hand dinta akan babban penis dinshi, awani irin mugun rude ta fizge hanunta jikinta narawa sosai gashi tana karshen gadon balle ta gudu, sakin wani irin mugun kuka yayi da idan akwai any mutum a around part dinsu saiyaji karan kukan dayakeyi, sakin kuka itama tayi arude ta tashi zaune ta makale ajikin bangon gadon, tunda take bata taba shiga irin tashin hankalin yauba mehaka Aadil kemata yau, gawani shegen kuka dayake mata kaman tana yankashi da wukoki, arude tace "dan Allah stop crying kaji Aadil" make mata kafada yayi cikin kuka sosai yace "why did you stop touching it, come and hold it for me, ciwo sosai" yasaki kuka yana tashi zaune shima yana matsowa kusada ita, da sauri tai yunkurin matsawa daga wajen hanunta yarike ya fizgota yasakin mata wani irin kuka itama kukan tasaki tana kokarin kwace kanta tace "Aadil dan girman Allah kayakuri, wai menene haka, kaga dare yayi let's sleep please kaji my Aadil" tai maganan cikin wani irin murya lallashi da tsoro, gyada mata kai yayi hawaye na zuba shi kanshi dukya fita hayyacinshi sabida wahalan dayake sha, cikin muryanshi data fara dishashewa yakama hanunta da karfi yaja yadaura akan joystick dinshi yace "am sleepy but ciwo, it hurt alot hold it for me My Hamida, is very very big today why?" a rude tana dunkule hanunta dan sosai take tsoron rikewa tace "no babu kyau rike na babba, is not good" fashewa yayi dawani irin kuka duk hankalin shi yatashi dan this is really a new thing to him, yadaura kanshi awuyanta yana kuka hawayen na gangarawa cleavage dinta sai wani irin ajiyan zuciya yake saukewa yana kuka yana shakan kamshinta yana dukan joystick din data mike sambal bamata da alamun hakura duka, yana marinta shi adole saita kwanta yana jin zafin dukan sosai yana runtse ido da karfi.

42.....





Karki karanta in baki biyaba in kika karanta keda Allah, duk mai son novel dinan should chat me up 07012181461




Yanda yake kuka sosai yana dukan erection dinshi yanajin zafi yana ihu yakara sakata cikin tsananin tashin hankali itama hawayen idanunta sun kasa dena zuba cikin dishashiyar muryanta takirashi. "Aadil kadena kuka, so kake natafi ko?" girgiza mata kai yayi yace "don't go please my Hamida, ciwo" da sauri muryanta nawani irin rawa tace "okay sorry kadena kuka dan Allah" gyadamata kai yayi ahankali murya chan kasa kaman wani maraya yace "i want to sleep on your body" yay maganan yana kokarin  kwanciya ajikinta yarasa inda zaisa kanshi yaji dadi, da sauri taja bargon tana rufe jikinta har wuyanta, fizge bargon yayi yana gunjin kuka dawani irin gudu ta tashi tace "na shiga uku Aadil wai menene haka?" fizgota yayi yana kuka sosai kaman dan jariri ya kwantar da ita sanan ya kwanta shima yadaura kanshi a wuyanta yaja bargon ya lullubesu dashi, fashewa da kuka tayi ahankali kirjinta kaman zai tsage yafito tsabagen yanda yake bugu, yanda skin dinta yahadu da nashi yasa yaji wani irin shegen dadi yakara cusa kanshi a wuyanta yana matsa big erected joystick dinshi a cinyanta kaman zaici cinyan yana nishi da sauri da sauri hanunshi na yawo cikinta da sauri da sauri harya sauka kan boobs dinta, wani irin nishi yayi ya damko boobs din da karfi yana matsawa, wani irin dadi yakeji fiye da misali jiyake kaman kanshi zai fashe, wani irin kuka takeyi dan iya tsoro yauta tsorata, bata taba sanin joystick ba saiyau, bata taba sanin haka yake girma ba saiyau, ita tanama kula maza ne, sai wani irin matsa mata yake yana bubbugawa acinyanta yana nishi yana kuka yana matsa mata boobs gashi yarike ta gamgam ba daman tai kwakkwaran motsi balle ta gudu, kasa hakura yayi sabida yanda jikinshi kemai kaman zai haukaci yasaki boobs din yakai hanunshi yajuyo da fuskarta saitin nashi yana kuka dawani irin sauri ya fizgi bakinta yana kissing dinta kaman zai shide ya maida hanunshi kan boobs din yana matsawa yanajan nipples din yana matsasu yana matsa joystick dinshi da mugun karfi a cinyanta ko ina na jikinshi na rawa yana wani irin nishi da gurnani na wanda yamugun wahala dan yanda yake matsewa a cinyan nata yanajin dadi amma hakanan yakeji a jikinshi wanan bai isheshiba he needs more, sosai take wani irin kuka ga jikinta dayadau rawa ko ina yanda yake matsa mata boobs namata zafi bana wasaba hakama yanda yake kissing dinta, hawayenshi sai diddiga yake akan fuskarta, wani irin rawa hanunta ya shiga yi tanason kwace Tadaura hanunta dasukai zufa tsabagen chajin dayake saka mata akan kirjinshi zata tureshi, sakin bakinta yayi yay wani irin groaning da karfi yana kara matse joystick dinshi da mugun karfi a cinyanta cikin wani irin murya ta wanda yakai kololuwan bukata yace "My Hamida my stomach, My abdomen want to b..urst is..."  yay maganan muryanshi narawa sosai yakai bakinshi kan boob dinta trying to have comfort awajen sabida yanda jikinshi kemai wani irin rawa yanaji wani irin abu na zuwan mai mara yana karajin wani irin mugun dadi fiye da nada kaman zai zauce yarasa yanda zaiyi da rayuwanshi hakan yasaki boobs din na bakinshi yasaki wani kukan yana wani irin matsa dayan yana kara shigewa jikinta yanaji kaman ya tsagata ya shige cikin jikinta blood dinshi na pumping fast, fashewa tayi da kuka tasa hanunta akan kafadarshi tana tureshi nishi yayi yakama hanun yarike gam yana wani irin nishi jin wani abu namai yawo ajikinshi da sauri yasake maida bakinshi kan boobs dinta yay wani irin groaning dawani irin sharp kara yay wani irin uban releasing akan cinyanta da jikinta yana nishi da karfi baitaba yin hakama in his life ya rungumeta gam yana wani irin shan nonon ta yana nishi kaman wanda yaje filin yaki, hawaye kawai ke zuba ta gefen idanunta bata taba sanin haka auren yakeba saiyau sai cizan lebenta take sabida yanda yake zukan mata nono kaman zai zuko ruwa yana wani irin matse dayan yana ajiyan zuciya sosai tun yanayi da sauri da sauri harya somayi kadan kadan saikuma chan taji shiru taji kanshi yay nauyi a kirjinta alamu kaman yay bacci gabaki dayanta jitayi kamshin mayen turaren shi take sabida yanda yabi ya tumurmusata, sosai take kuka sabida yanda cikinta da cinyanta sukai pacha pacha, ga itama down dere she is still dripping, ahankali cike da dabara ta tureshi ahankali ta zare boob dinta daga bakinshi, kafin ta matsa gefe ahankali motsi taga yayi cikin bacci zai kara kamota yadanyi kara kaman na yara masu shagwaba. "aam" da sauri taja filo ta ijiye adan space din tsakanin su hanunshi yadaura akan filon hakan yasa yasake sauke ajiyan zuciya yay cigaba da bacci da sauri ta sauka daga kan gadon ta bude bathroom ta shiga tanabin jikinta da kallo, runtse idanunta tayi da sauri hawaye na zubomata ko ina jitayi yana mata ciwo bana wasaba wanka tayi tsaf da ruwan zafi sosai  ta tsane jikinta sanan tadauko rigan da tadauko dama dazu tasaka ta saka rigan yamata mugun kyau ajiki tai kaman wata barbie aciki, sanan tabude bayin tafito gatanan ne kawai bata jinta daidai daurewa kawai take, ahankali tabude kofa tafito tana addu'a Allah yasa bai tashiba ganin shiru dakin har lokacin da duhu yasai tai chan edge of bed ta kwanta ta tofama kanta addu'a kafin ta juya tadan kalleshi tofamai tayi shima dan tasan baiyi addu'a ba yay bacci tajuya ta rufa da bargo tana tunanin su Mama da Kaka dakuma abinda yafaru yanzun nan dabataso ta tuna, ahaka bacci yay awon gaba da ita.



"Ozo, Ozo kayakuri, azaban nan tamin bala'in yawa Ozo" hannu mutumin dake sanye da dogon jan riga na tsafi ya mika aka sakamai wani abu kaman fiffikin kaza amma bakinshi yana wuta sosai, wani irin ihu Abie dake makale ajikin bango yayi kaman an makala shi da gum yana girgiza kai yace "Ozo Ozo ba wanan abin ba haba Ozo kanafa sona kana tausayina ko amatsayina nadan arewa kadai dake wanan kungiyan yakamata kamin afuwa" cikin wata irin muryan tsawa daya girgiza dakin Ozo yace "sabida inason kane da mutuwa ce dakuma haukacewa kafin mutuwa makomar sabamini doka dakayi, tunda kashigo wanan kungiyan ka saba mana doka, kasan me kayi dakabari yay auren nan kuwa? Duk wani shiriri da tsafi da mukeyi da kwakwalwanshi muke samun kudi auren nan ya karyashi, duk kuma randa zai sadu da matar daya aura kwakwalwan damuka rike tun yana dan kankanu zai bi iska yakoma jikinshi yadawo lafiya lau, kakosan asaran dakasa nayi kuwa Tursoso" yay maganan yana chakama Abie abin a kirji wani irin ihu Abie yayi na tsananin azaba tunda safiya yau Ozo ya daukeshi yake ganamai azaba yay nadaman shiga kungiyan nan, yay nadama dudda dai shine one of the best kungiyan Nigeria dan kungiyar na baka kudi bila adadin dakuma fame suna zaka zama popular ko ina asan da zaman ka amma sharrudan su yay yawa, sunada tsanani, maganan Ozo ne yadawo dashi duniya yace "ba'a sabamin doka, kowa na wanan cult din saida mukasha jinin y'ayan farin su, kai naka baka bari munsha ba nakuma dagama kafa da sharadin karka sake kabari yay aure dan Aure sai karya komi dakuma amfani damuke dashi amma bakajiba, bakajiba Tursoso, i have one final last warning for you inba hakaba zamuma blood for blood dole ne musha jini da sauri Abie yace "eh eh na yarda koma menene wanan karan zan kiyaye Ozo kamin afuwa kafadamin nasan kamin adalci" shiru Ozo yayi kafin yace "karka sake karka sake karka yarda Tursoso dan farinka ya sadu da matarshi inhar yay haka aranan komi zai warware sanan bazan fadama wani hukunci zai biyo bayaba amma dai dole musha jini, karka yarda abinda ya maida danka namiji ya shiga cikin abunda ya maida mace mace" da sauri Abie yace "na yarda, wlh na yarda Ozo dan Allah ka saukeni" wani irin tsafi Ozo yayi yabugashi akasa sanan ya bace bat kowama nadakin yabace yarage Abie kadai adakin a kwance dagashi sai gajeren wando yafashe da kuka sosai yana wani irin shesheka, yagaji da rayuwan nan so yake yamutu yahuta, wanan shegiyar tagadiriyan yarinyar da tunda Aadil dinshi yaganta yahaukace akanta tabatamai komi, farin cikin dayagani a idanun Aadil bayan an daure auren was everything to him farincin cikin Aadil nasashi jin kwanciyan hankali dam yasan ya cuci yaron dayawa saidai wanan azaban da Ozo kemai kullum bazai iya jurewa ba gashi yanzu yau sati na biyu kenan zobenshi baimai aman kudi ba sabida Ozo na fushi dashi da wanan wahalan gwara koyaya zaiyi yasan yanda zaiyi yahana Aadil saduwa da Hamida dudda ma yasan Aadil bazai taba sanin yanda ake saduwa da mace ba dan yarone babu abinda ya iya saisa ya yarda d gudu dan yasan babu abinda Aadil zai iya, rawan sanyin daya fara yasa yatashi yabude kofar dakin yafita yashiga wani bedroom yadauko kaya yasaka ya kwanta sai bacci.

_🌹IN BANI 🌹_ 





Maman Abd Shakur


43...




Kiraye kirayen sallan asuba yatada ita daga nauyayyan baccin daya kwasheta, jinta tayi gabaki daya acikin jikin Aadil sun lulluba da bargon gadon mai shegen laushi yawani irin kwakumarta, dudda bataganin fuskarshi sabida duhun dakin amma tagane bacci yake sabida yanda yake saukar da ajiyan zuciya kadan kadan, ahankali ta janye jikinta daga nashi abunda yafaru jiya da daddare yana dawo mata sabo fil aranta, sauka tayi kasa ahankali tai hanyar kofar bathroom tadaura hanunta jikin bangon wurin tana neman switch din kunna wuta, kunna wutar dakin tayi hakan yasa dakin yay haske sosai dan juyawa tayi da kanta ta kalleshi yana lullube da bargo yana bacci kan gado abinshi, ganin yafara yatsine fuska a shagwabe ganin haske an kunna wutan dakin yasa da sauri tabude bathroom door din ta shiga, sakatan kofan tasaka kafin ta wuce tafarayin brush sanan tasakeyin wani sabon wankan ta daura towel sanan tai alwala ta tsaya gaban madubin bayin tana kallon kanta bakaramin kyau tayiba tai wani irin hasken amarci tai kyau fatarta nawani irin glow na gyara, gyaran gashin da aka mata yay wani irin mugun kyau gashin sun kwanta sosai barin ma nagaban goshinta dasukai kaman na sabuwar jaririya sun kwanta lub lub, ahankali tagoge jikinta da towel din sanan ta ijiye tana kokarin saka rigan taji ya kwala mata kira cikin muryan bacci chan kasa kaman zaiyi kuka. "My Hamidah, where are you" saida gabanta yafadi jin yanda yakira sunan nata, da sauri ta zira rigan hanun nata jin yafashe da kuka yana surutan nemanta, sake kwala mata kira yayi cikin kuka "My Hamida" jin yanda yake kuka yasa ta amsa shi cikin siriruwar tattausar muryanta. "n...na'am" da sauri ya yaye bargon ya sauko daga kan gadon jin muryanta a bathroom babu ko kaya ajikinshi yakaraso ya tsaya gaban kofan yakama handle din zai bude yace "are you in d bathroom?" jin kofan a kulle yasa ya jijjiga kofan arude yana neman sakin kuka yace "My Hamidah open the door" hanging towel din tayi da sauri tana karajan rigan jikin nata kasa yakai har wurin guwiwanta sanan tayo hanyar kofan kirjinta na dukan uku uku tana wasa da yatsunta, ahankali ta cire sakatan kofan jin yanda yake kuka tabude kofan kafin ma kofan yagama buduwa yaturo kofan tsabagen yanda yakosa ya ganta ya shigo bayin da sauri yana raurau da ido yana turo baki, tsayawa yayi chak ya kalleta ganinta tsaye daga ita saiyar jan riga daya tsaya mata a gwuiwa kanta babu dan kwali gashinta a gyare an mata parking sai lilo jelar gashin yake, gashin gaban goshinta sun kwanta sabida lema leman ruwan wanka, kafafunta farare tass tasanya white bathroom slippers akafarta daya mata yawa, wani irin kallonta yake yanajin wani iri mugun sonta kafin ya saukar da idanunshi kan boobs dinta da rigan yafito da shape dinsu da kyau sabida rigan bacci jikinta dayake cotton, yakafe boobs din da ido yana wani irin tuna jiya da daddare, washe mata baki yayi white set of fine teeth dinshi suka bayyana kafin yawani irin bata hug cikin so much excitement yace "My Hamidah, u are here, baki tafi ba, oyoyo" yay wani irin murmushi yana tura hancinshi a wuyanta, lumshe idanunta tayi jikinta sosai yadau rawa sabida yanda taganshi ba kaya ahankali muryanta har wani irin rawa yake batare data bude idanunta ba tace "uh...ana kiran salla a mosque jekai wanka katafi masallaci" da sauri ya saketa yana leka fuskarta yace "mosque?" gyadamai kai tayi da sauri yace "promise me you will not go and leave me" batare data kalleshi ba dan yanzu mugun jin nauyinshi take tace "i promise, jekai wankan" jin shiru yasa tadan dagokai ta kalleshi hada ido sukayi yana wani irin kallonta kaman yau yafara ganinta yana murmushi sosai, gabanta yafadi zata maida kan kanta kasa yarike fuskarta da sauri yay cupping face dinta yana washe mata baki yana mata fari da ido, dan murmushin yake tayi tadan juyar da idanunta ahankali tace "kaje kai wankan tsarki lokaci na tafiya" da sauri batare daya saketa ba yace "wankan tsarki?" gyadamai kai tayi batare data kalleshi ba, kara shigewa jikinta yayi yace "wats wankan tsarki?" dan shiru tayi kafin tai fighting kunya da kyar tamai bayani dalla dalla sanan ta janye hanunshi daga fuskarta tace "jekayi kazo kaje mosque" make mata kafada yayi yana kamo waist dinta yace "wait for me" batare data kalleshi ba tace "zan jiraka adaki hurry up kayi yanda nafada ma" sakinta yayi hakan yasa tafita da sauri dan tsoron kallonshi takeyi ahaka, gaban wardrobe din tayi tabude tana kallon uban tulin kayanta wani zanin atampa tajawo da hijabi samin kanta tayi da bude dayan bangaren wardrobe din taga kayanshi ne ajere jallabiya ta ciromai milk da singlet tana duba boxer bata ganiba hakan yasa tajawo drawer dake wajen taga tulin hadaddun boxers dinshi, daya tajawo mai wani baki ta ijiye akan bed din sanna ta tafi kan dadduma tahau ta tada, tana cikin salla yafito ya daura towel a kwankwaso yana goge ruwan kanshi da towel yana kallon Hamidan dake kan dadduman kasancewar Mami tariga ta koyamai ba kyau yima wanda ke salla magana yasa baiyiba yajuya yana kallon kan gadon ganin kayan data fitomai dasu yasa yasaka ya shirya tsaf yana kalle kalle yana neman turarenshi dan baison yaga baisa turare ba, wardrobe din yabubbude kafin yaga turarenshi a side dinshi feffesawa yayi sanan yawuce yafita yana yima Hamidan dake salla bye yatafi mosque. 





Tana idar da sallan azkar tafara tana lumshe ido saida tagama tass sanan ta shiga neman inda zata ga Al Qur'ani adakin ta karanta, ganin bata gani ba yasa tai isti'aza tafara karantawa da ka, tadan jima tana karatun harsaida gari yafara haske sanan ta dakatar tana kallon ko ina na dakin tana kara mamaki yanzu wai tai aure, ganin abunda Aadil yamata jiya yasoma komo mata yasa da sauri ta kawad da tunanin ta tashi ta linke dadduma ta zare hijabin jikinta ta linke ta ijiye su sanan ta tashi tsugunna ta kwashe kayanshi daya jejjefar akasa kayan sai uban kamshi suke kaman shine, bathroom tabude ta shiga ta sakasu a lundry basket sanan tadawo ta shinfida gadon fess dakin yay kyau sosai, wani irin mugun baccin ke damunta bana wasaba dan tasaba ko agida tana komawa baccin asuba yasa ta kwanta akan gadon tana sauke ijiyar zuciya taja bargo ta lulluba danta kasa gane kan yanda ake kashe AC dakin, sake tuna abinda Aadil yamata tayi hakan yasa da sauri ta runtse ido tana kokarin sa kanta baccin dole, muryan Aadil dataji daga falo yana cewa "bye bye grandfather" yasa ta runtse ido da sauri tai lamo akan gadon kaman tai bacci kirjinta na dukan uku uku.



Rufe kofan yayi yana tsalle yayo hanyar bedroom din, bude kofan bedroom din yayi wani kamshi ya daki hancinshi murmushi yayi sosai ji yake kaman an sakashi a aljanna tsabagen murna ganin Hamidan kan gado bata tafin ba dudda dai baya iya ganin fuskarta, da sauri ya maida kofan yarufe yana bude boturin jallabiyar jikinshi yace "My Hamidah are you sleeping?" shiru tayi kaman batajishiba tana kokarin hana jikinta rawa, zare jallabiyan yayi da singlet din jikinshi ya cire boxer dinma yana murmushi sosai jikinshi har rawa yake kanshi narawa dan so yake yakarayin irin na jiya da ita, barin kayan yayi akasa yahau gadon da sauri yana yaye bargon yana shigewa ya matsa tabayanta yawani irin rungumeta kaman zai hadiyeta yana murmushi. "oyoyo Hamida My wife" bakaramin faduwa gabanta yayi ba jinba riga ajikinshi sakeyin lamo tayi kaman tana bacci hakan yasa yaturo baki kaman zaiyi kuka yay shiru ya daura fuskarshi atawurin kunenta hakan yasa ya iya hango boobs dinta ta gaban wuyan riganta daya kwanta hakan ya bayyana white boobs din sosai, wani irin nishi yayi ya lumshe ido ahankali kafin yasake budesu yana kallo, jijjigata yayi yakira sunanta cikin crying tone. "My Hamida wake up" kin motsi tayi kaman tana bacci hakan yasa da sauri ya saketa ya tsallake ta yadawo ta gabanta ya kwanta ahankali kaman wani karamin yaro yazo wajen mum dinshi, sosai idanunshi suka taru da kwalla, ahankali ya daura hanunshi kan cikinta yay tapping cikin gently yana kallon fuskarta yakira sunanta. "My Hamida" shiru tayi tai lamo amma she's sure inda zai taba kirjinta dazai gane idanunta biyu sabida yanda kirjinta ke bugawa, hawaye ne ya gangaro daga idanunshi yasa bayan hanunshi ya share yana kara kallon fuskarta shiso kawai yake ta farka ta kalleshi, ganin taki tashi yasa ahankali ya shige jikinta ya matsar da kanshi kusada kirjinta ya kafe kirjin da ido yana tuna yanda yasha su jiya and yatuna yanda yaji dadi sosai bana wasaba, ahankali kaman wanda zaiyi sata yadan matsar da kanshi saman kirjin kadan ya matso da fuskarshi yasa yatsarshi yaja wuyan rigan ya sa kanshi ya leka boobs din tacikin riga yana kallon su, wani irin faduwa gabanta yayi takusan sakin fitsari a wando amma ta daure tasan once tai matso abinda yamata jiya zai sakeyi itakuma bataso ko kadan hakan yasa tai lamo ko numfashi ma kadan kadan take fitarwa tana sauraron shi.


Kara jan wuyan rigan yayi yana talewa sosai ya leka big perky boobs din nata da nipples din were still sleeping dan she wasn't arouse basu fitoba, wani irin murmushi yasaki daya bayyanar da dimples dinshi yana ware manyan eyes dinshi cikin wani irin karaman murya ta wanda ke magana da kanshi yace "nono, this is breast" yay maganan yana pointing dinsu da hannu, wani irin murmushi yayi daya karamai mugun kyau yakara lekawa kaman zaisa kanshi ta wuyan rigan nata yana kallon su yace "I want to drink My Hamida's breast" yanda yay maganan saida yasa tsigan jikinta yawani irin tashi haryasa nipples dinta suka tashi kadan, da sauri yasaki wuyan rigan ya dan yaye bargon yana binta da kallo yana tunanin ta yanda zai fito da boobs din waje yasha, hannu yasa ya juyar da ita, sosai gabanta ke faduwa, yasa hanunshi yaja rigan sama daga cinyanta saura kiris tasaki kuka tadai daure kirjinta na dukan uku uku, tattare rigan yayi duka har sama yanabin white pant din dake jikinta da kallo yanayi ahankali kaman wani barawo dayazo sata shi adole karya tasheta, a saman kirjinta yabar rigan yana kallon boobs din yay wani irin murmushi yace "oyoyo" yadaura kanshi kan nonon da gudu yana rungumeta yanajan bargon yana kara lullubesu, runtse ido tayi sabida yanda ya daura kanshi kan nonon bakaramin zafi tajiba, daga kanshi yayi ya kalli boobs din wani irin murnan dayakeyi yawuce misali jiyake kaman zai sume da dadi, ahankali ya daura bakinshi kan boobs din dagashi har Hamidan atare suka sauke wani irin ajiyan zuciya, wani irin zuko nipple din yayi yana murza dayan sosai yana kallonsu, ware idanunta tayi rass jin yana wani irin satajin wani iri bakinta har rawa yake takira sunanshi ahankali. "A...adil" dago kanshi yayi da idanunshi dasuka kankance ya kalleta batare daya saki boobs dinba yana zuka, hawaye ne yazubo daga idanunta ta girgiza mai kai tace "please kadena kaji My Aadil" make mata kafada yayi dan wani irin masifaffen jin dadi yake yana having wani irin strong erection at d same time, kasa daure yanda yakeshan boobs dinta tayi dan wani irin mugun dadi takeji sabida yanda yakesha mata kaman yasami sweet kuma da sauri sauri hakan yasa ta ture kanshi da karfi tana kokarin jan riganta kasa ta ballamai harara ganin abun nashi iskanci ne, rike rigan yayi ya shige jikinta a ashgwabe yana make mata kafada da muryanshi da bata fita sosai tsabagen sha'awa yace "don't close it please My Hamida, am drinking it" cikin masifa dakuma kuka tace "leave me alone" taja riganta kasa, fashewa yayi da kuka sosai yana murza kan joystick dinshi yana kallon fuskarta yana make mata kafada yace "open it for me, i want to do like yesterday" sosai taji yawani irin mugun bata haushi soyake ya kasheta gabaki daya boobs din ciwo suke mata ko dazu dataje wanka saida ta matsa da ruwan zafi mema haka yakeyi wanan ai iskanci ne inda tasan haka ya iya iskanci da batama taba sakinmai fuska ba, juyamai baya tayi ta kalli dayan side din, ahankali yawani irin fashe da mugun kuka yatashi ya zauna yana kallonta wani irin bakin ciki natasomai dan baiso ta hanashi abinda yakeyi ba dan wani irin dadi yakeji bana wasaba baitaba jin irin dadin ba saida ya aureta, dukan joystick dinshi yafara jin yafaramai zafi yana kuka sosai yana kallon bayanta. "My Hamida" kasa daurewa tayi jin yanda yake shegen iskancin kukan gashi gari yawaye kuma sosai kukan ketaba mata heart koba komi baisan meyakeyi ba, ahankali tajuyo ta kalleshi da sauri ta dauke kai dan yawani irin cika mata ido babba haka takesa kuka, no, no, don't take advantage of his condition kome yakeso kimai mijinkine akwai hakkinshi akanki, maganganun su Mama ne ke dawo mata akai hakan yasa ta tattaro duka jarumtar ta ta kalleshi yanda yake kukan hawaye mala mala akan fuskarshi yana kallonta gwanin ban tausayi, to ita wai yazatayi dashine batason abubuwan nan dayake mata yana sata jin wani iri kuma inta hanashi saiya dinga mata shegen kuka kaman ta dakeshi, jitayi tama tsani baccin datake so tayinma, ahankali ta tashi ta zauna ta jingina da gado tadan kalleshi cikin muryan lallashi tace "Am sorry stop crying kaji My Aadil, make mata kafada yayi cikin kukan yacigaba da kukan kaman bada shi takeba hakan yasa ta dake ta matso kusada shi ahankali, hanunta takai kan fuskarshi tana murmushi ta sharemai fuskan tass da hannu tace "stop crying baka kyau idan kana kuka kaji my Aadil" make mata kafada yayi yacigaba da kukan, murmushi tayi tana kallon fuskarshi dan bataso ta kalli kirjinshi dakeda fadin gaske, acike kuma ga wasu soft hair dakenan a kwance lub lub kaman na balarabe, kunenta takama duka biyun tana kallonshi kaman yanda yake kallonta yana kuka tace "am sorry kaji" sake make mata kafada yayi alamun bazai hakura ba dan so kawai yake yay wasa son ranshi ajikinta harsaiyaji dadin dayaji jiya, baki takama saikuma tai kaman zatai kuka tace "ka cika fushi My Aadil, to tell me yanzu wats making you cry eh?" cikin kuka ya yaye bargon jikinshi gabaki daya ya kama erection dinshi dake diddiga kadan kadan yanuna mata cikin kuka yace "its hurt badly" yasake fashewa da kukan, wani irin faduwa gabanta yayi da sauri ta koma baya ta runtse ido tana kawad dakai, dudda jiya ta jita but bata taba kawo haka yakeda girma ba, bakinta har rawa ya shiga yi tace "b..ba..bakasa wa..wando ba, ina wandon ka?" make mata kafada yayi ya taso yafado kanta sakin kuka tayi a tsorace tace "dan Allah karkamin komi kaji Aadil kaga am your friend ko" tsayar da kukan shi yayi yana kallon yanda take kuka jikinta na rawa tanamai magana, make mata kafada yayi a shagwabe yana share mata hawayen yace "not friend, you are my wife" yay wani murmushi yana kallon pink lips dinta kafinma ta farga gamai zaiyi yahada bakinsu yana kissing hanunshi jikin riganta yana shafa boobs dinta, sosai jikinta ke rawa hakan yasa tarike mai waist gam batare data hanashi tattabatan ba, ahankali ya kwantar da ita kan gadon ya kwanta akanta yana kissing dinta yana lumshe ido yana squeezing boobs dinta wani irin dadi yakeji bana wasaba, gabaki daya ta rude sai ajiyan zuciya take saki tana matse kafa sosai, hanunta yakama yakai kan joystick dinshi yasaki bakinta yafashe mata da kuka jin yanda takemai ciwo, har sheshekan kuka yake yace "zafi, My Hamida ciwo" yanda yasaki kukan yasa hanunta yafara bari sosai ahankali tai grabbing dinshi, da sauri yasaki wani irin moan yace "ahhhh, mmmm, hold it hard my Hamida is stopping" jin yace haka yasa tacire tsoro takama da karfi, wani irin kara yasaki yahada bakinshi da nata yana squeezing boobs dinta kanshi na tafarfasa so yake ya tsaga jikinta ya shige koyaji saukin abinda yakeji dashi kanshi bai saniba, danna joystick din da karfi yayi akan abdomen dinta jikinshi na rawa sosai kaman yanda nata yake rawa, ganin yaji dadin yanda hanunta kekai sanan kan joystick din nataba abdominal skin dinta yasa yaji wani irin dadi da sauri ya sauri ya dinga screwing abdomen din nata yana groaning in pleasure da karfi yana kuka har ya rirriketa da karfin bala'in yay squeezing boobs dinta hard dahar saida tai ihun zafi sanan yay wani irin explosion akan cikinta ya batamata jiki gabaki daya yana shesheka jikinshi narawa.



_Duk wacce ta karanta bata biyaba itada Allah, in kinason this book chat me up 07012181461_

44....


Riketa yayi gam yana nishi da karfi yanajin wani irin satisfaction din dabai taba jiba, runtse idanunta tayi gam hawaye nabin gefen idanunta suna fita wanan wani irin abune Aadil kemata haka, ahankali batare daya saki boobs din da bakinta ba yana sha yana matsa boobs din dayake mugun so bacci yay awon gaba dashi mai nauyin gaske, shirun dataji yadena kissing din nata yasa ta zare lips din nata dasuke mata zugi sosai daga bakinshi sun dan kumbura sunyi jajir, hannu tasa ta share hawayen dasuke zuban mata idanunta sunyi ja kafin ta ture hanun nashi daga kan boobs dinta dasuke mata zafi sanan tadan matsa gefe amugun hankali tai maza tasa pilo ganin yana yatsine fuska yana shirin kuka, daura hanunshi yayi akan filon hakan  yasa ta sauka daga kan gadon, ahankali tana goge kwalla ta shige bayi, wanka tayi tsaf sanan tafito daure da towel, wardrobe ta bude tafito da riga da skirt nawani english atampa dark green da black, tsayawa tai agaban mirror ta shafa manta mai kamshi, tadan shafa hoda tasa kwalli sanan tasa wani man baki ta gyara giranta dayay carve sanan ta shirya cikin kayan data ciro daga wardrobe tsaf, bakaramin kyau sukamataba tai kaman wata balarabiya, daukar  dan kwalin tayi ta daura da kyar dan bata iyaba aiko daurin yamata kyau sanan ta fesa turarurruka ta nan tafito amaryanta tsaf, sai amarci glow takeyi, kallon gadon tayi ganin yanda ya dukunkune yasa ta karaso taja bargon ta rufemai jiki batare data kalli fuskarshi ba sanan ta wuce tabude kofar dakin ahankali tafita tai hadadden falonta tana kallon ko ina, gaban TV taje ta kunna sanan takoma kan dogon kujera ta kwanta ta daura kanta akan filon kujera ta lumshe ido wani irin shegen bacci na dibanta, har baccin yafara dibanta taji anyi knocking da sauri tabude ido tareda tashi ta zauna, sake knocking akayi hakan yasa ta mike tai wurin kofan, ahankali ta bude kofan wasu maid ne guda biyu suka gaidata suna rike da warmers, akunyace ta gaishe su ta matsa musu suka shigo ciki sukai dining, abincin  suka jera akan dining sanan suka mata sallama suka fita dudda tanajin yunwa kasa hakura tayi da baccin dake mugun kwasan ta takoma kan kujeran ta kwanta sai bacci.






Bude idanunta tayi ahankali jin ana shafa mata wuya ana gangarawa down to her boobs ta wuyan riga, hada ido sukayi da Aadil dake sanye cikin farin t-shirt da 3quater kana ganinshi zaka gane yay wanka sabida wani irin hadadden kamshin dayake yi yay kyau sosai yay wani irin special haske yana mata murmushi ya zare hanun nashi daga cikin riganta kaman mara gaskiyan da aka kama yace "wake up my Hamida" hannu tasa zata goge idanunta dake mata kaikayi yay maza yasa nashi hannun ya goge mata idanun yana murmushi sanan ya janye hannun yana kallon fuskarta, bude idanun tayi ahankali ta kalleshi dan murmushi ta sakinmai ta tashi zaune ahankali, zama yayi gefenta da sauri kaman zai cinyeta, side hug yabata ya daura kanta akan kafadarshi yace "you look very very beautiful My Hamida, kinyi kyau" gyadamai kai tayi asanyaye, ahankali yana kallon gashinta dasuka kwanta lub yace "am hungry sosai, abinci" tashi tayi tace "ga abinci chan zomuje kaci" tashi tayi da sauri tai gaba kafin yariketa taja kujeran dining daya ta nunamai alamun ya zauna, karasowa yayi ya zauna akan kujeran yana kallonta, warmers din tabude tana kallon abubuwan ciki tana tunanin mezata zubamai, cikinshi yarike kaman zaiyi kuka yace "chips My Hamida, i want to eat chips" plate ta dauka ta zubamai chips da source din liver tasamai fork ta ajiyemai agabanshi sanan tabude fridge din dinning tadauko bottle water takawo ta tsaya ya mai a glass cup ta ijiyemai kusa dashi, kallon abincin yayi ganin baiga sign din any pepper ba dan baison pepper ko kadan yasa ya dagakai ya kalleta tana kokarin maida warmers din tarufe yafizgo hanunta harsaida ta firgita ta juyo zatai magana yajata ya daurata akan kafarshi yana dariya yace "i will feed u kaman yanda Mami use to feed me" yana maganan yana debo chips din da fork yakai bakinta yana mata murmushi yace "haa" lumshe ido tayi tadanyi murmushi ganin yanda yay maganan saiya tuna mata da Ihsan tace "ban wanke bakiba fa kaga natashi daga bacci" make mata kafada yayi kaman zaiyi kuka yace "oh'oh" yakai saitin bakinta, ganin yana neman yimata kuka yasa tabude bakin ahankali tana kallon fuskarshi kaman yanda shima yake kallonta yanaji kaman yahadiyeta a cikinshi sabida dadi da so da murna dayake ciki ganinta tareda shi, ahankali ta karba tana taunawa zai kara debo wani ta karbi spoon din ta debo tace "is your turn" takaimai mai baki, karba yayi da sauri yana murmushi yana ci sanan ya karbi fork din shima ya debo yabata karba tayi tana kallonshi sosai wani irin mugun tausayinshi taji tanaji hakanan kawai jitayi tanaso taganshi normal kaman kowani mutum aduniyan nan, hawayen daya gani a idanunta yasa ya tsayar da tauna chips din dake bakinshi dayakeci da murna, hanunshi ya daure akan fuskarta yana kallonta ahankali kaman zaiyi kuka yace "why are you crying?" share hawayen tayi da sauri tana girgiza mai kai tasake dauko fork di tadebi chips din zatakai mai baki tana kokarin danne kukan dake cinta da muryanta dake dan rawa tace "haaa, inasama abaki" rike fork din yayi yana kallon fuskarta ganin taki yarda su hada ido yasa cikeda damuwa yace "My Hamidah look at me" ahankali ta daura idanunta kanshi ta kalleshi yanda kanshi kedan rawa abincin dayake ci ya babbatamai wuraren baki idanunshi sun cika da kwalla yana kallonta, wani irin kuka ne yazomata  bata batasan lokacin data fada jikinshi ba ta kankameshi tafashe da kuka sosai ba tana shesheka tace "inaso ka warke Aadil, inaso ka warke, inaso ka warke My Aadil" tafashe da kuka sosai, rudewa yayi yana kokarin ciro fuskarta daga kirjinshi yace "stop crying My Hamidah, am sorry i will not do it again please" yama rasa yanda zaiyi hakan yasa yafara tattaba jikinshi wayarshi dayaji a aljihun wandonshi yaciro muryanshi narawa sosai ya danna yasa a front camera yace "Bid said anytime one is angry he should snap picture an automatic smile will appear on his face, let's take a selfie" yay maganan yana dagota daga jikinshi tasowa tayi tasa hanunta tai cuddling kanshi tana kuka sosai, sosai muryanshi ke rawa yana kokarin kuka yana kawo Cameran saitin su yace "look Hamida, selfieee" tana kukan tana rungume da kanshi ta juyo da kanta hawaye na zuba ta kalli wayan ya danna yay snapping yace "smile" dan murmushin kuka tayi tawani irin rungumeshi tana kallon fuskarshi tanajin wani irin mugun tausayin shi bana wasaba, dandanna hotunan ya shigayi harya saka a video batare dayama saniba juyowa yayi ya kalleta da murya chan kasa ya kalleta yana make mata kafada yace "i said you should stop crying kinji Hamida my wife" gyadamai kai tayi tana kara rungumeshi kaman wani zai kwace mata shi hakanan takeji tanaso kawai ta rungume shi sabida tausayin shi datake ji, murmushi yayi ganin tai murmushi yace "yeee she's smiling" dan murmushi tayi ta dago kanta ta kalli fuskarshi, ahankali takai hanunta ta sharemai bakinshi tass yana wani irin kallonta yana lumshe ido kafin ta maida kanta kirjinshi tai lamo tana shakan kamshin shi, da sauri ya  locking phone din ta hanyar danna side button ya ijiye yace "let's go to Mami's place" yay maganan yana dagata ganin duktai wani iri, makemai kafada tayi tace "ni a'a kunya nakeji, zauna ka karasa cin abincin" girgiza mata kai yayi ya rungumeta yana kallon kirjinta, murmushi tayi ta rikemai hannu tace "wait lemme clear d table first" sakinta yayi ahankali yay tsalle yatafi falo ya zauna akan dogon kujera itakuma ta gyara dining din tadau plate din dasukaci abincin dashi takai kitchen ta wanke sanan ta ajiye ta daurayo hanunta sanan tafito daidai anyi knocking kofan falo, tashi yayi daga kan kujeran yana tsalle  yabude kofan Mami ce taci gayu sosai tasa wani doguwan bakin riga fuskarta cike da murmushi tana kallon Aadil din datai wani irin kewanshi tsakanin jiya da yau bana wasaba, wani irin tsale Aadil din yayi yafada jikinta yace "oyoyo Mami na" saukar da kanta kasa Hamida tayi ta karaso falon, Mami ta shigo ciki tareda Aadil din tana murmushi tace "kai dalla chan sakeni karyani zakayi" tsugunnawa Hamida tayi tace "ina kwana Mum" karasawa Mami tayi ta dagota da sauri ta rungumeta kafin ta saketa ta zaunar da ita kan kujera sanan ta zauna agefenta da sauri Aadil shima yazo ya zauna kusa da Hamidan da kanta ke kasa ya kwanta ya daura kanshi akan cinyarta, kafafunshi kan hanun kujera ya daga hanunshi yana counting, sosai taji kunya yanda yadaura kanshi kan cinyarta gaban Mami, murmushi Mami tayi ta janye idanunta daga kan Aadil din dataga yana wani irin tsananin farin ciki bana wasaba tace "ya kuke daughter na nace bari nazo na dubaku da kaina, sai yanzu nasamu nakarasa sallaman ragowan bakin mu, hope kin kwana lafiya ko?" gyada ma Mami kan tayi kanta akasa tace "lpy lau Mum" murmushi Mami tayi tace "masha Allah, Allah yamuku albarka, ga wayanan nasan kina kewan yan uwanki ko" dan murmushi tayi akunyace, dadin yanda tai murmushi Mami taji tace "yauwa Amatullah" tai maganan tana samata ledan wayan ajiki, murmushi Hamidan tayi tarike wayan tace "nagode, Allah saka da alkhairi" "yauwa bari naje to ko, idan akwai any problem just call me kinji nasamiki number na a wayan" gayamata kai tayi Mami ta tashi ta kalli Aadil dake wasanshi tace "bye Son" waigowa yayi batare daya tashi daga jikin Hamidan ba yadaga mata hannu yace "bye bye Mami na" dariya sosai Mami tayi tana ganin tsantsan Son Hamida a idanunshi inda wani ne kome yakeyi once yaga zata tafi fashewa zaiyi da kuka yabiyota amma jibe yanzu kotashi baiyiba, cikin zolaya Mami tace "bazaka bini ba" make mata kafada yayi yawani tashi da sauri ya rungume Hamidan yadaura kanshi kan kirjinta yana makema Mami kafada yana murmushi sosai yace "i want to stay with my Hamida" Hamida takusa nitsewa akasa dan kunyan ta saukar da kanta kasa, murmushi Mami tayi tabude kofan tafita cikeda tausayin daga Aadil din har Hamidan datake ji kaman basu kyautama yarinyar ba.


Tafiya take tana tunanin Abie dan har yanzu bata ganshi ba, rabonta dashi tun shekaran jiya da daddare, sai mamaki take to ina yaje, ko tafiya yayi bai fadamata ba. 



Lamo yayi a kirjinta yana kallon dayan boobs din, ahankali ya mika hanunshi ya daura akan boobs din da sauri tabude ido ta kalleshi dago kai shima yayi ya kalleta yana turo mata baki yana taba hancinta yace "i want to do it again My Hamida" dan hararanshi tayi itama ta kabar da hanunshi daga kan boobs din  tace "kaga ana kiran salla jekayi" tashi yayi kaman zaiyi kuka yace "if i come back i will do like yesterday right?" gyadamai kai tayi tace "eh yi sauri karkai missing jam'i" murmushi yayi sosai kafin yafado jikinta harsaida tai kara ya matse fuskarta ya sakin mata peck akumatu sanan yatashi yana tsalle yafita daga dakin yace "lemme go and call grandfather" yarufe kofar binshi tayi da kallo kafin ahankali tasa hanunta tagoge kumatun nata daya bata mata da miyau tadau ledan da Mami tabata tabude taciro kwalin wayar iPhone X ce hakan yasa ta ware manyan idanunta ciro wayan tayi ta ganta a kunne ma ga sim aciki na mtn chaji cike, murmushi tayi tasaka number Mama da sauri takira amma harta katse ba'a daukaba hakan yasa tace hala tana wajen bakine, tai downloading watsapp sanan ya ijiye wayan tadau ledan ta shiga dashi ciki ta dauro alwala sanan tafito tahau kan dadduman tai salla tana idarwa tafito falon.

45.....


 Zama tayi tadau wayar tabude watsapp tama zainab da Anty Ayush da basa online sallama, tace musu itace daganan kuma tasake gyara kwanciya ta shiga games tana bugawa, sai chan ta dago kai ta kalli agogon bangon dakin ganin karfe har uku da minti biyar bai dawoba samun kanta tayi dajin wani irin kewanshi so kawai take ta ganshi, sake dailing number Mama tayi har wayan takusa katsewa Mama tai picking cikin tsananin murna tace "Mama nice, Hamida ce" shiru Mama tayi ta sauke ajiyan zuciya anatse dan tun bayan ankaita shekaran jiya bata kara bacci kirki ba kullum tunanin ta take da ita take kwana da ita take tashi. "Mama, Hello" dan murmushi Mama tayi mai sauti tace "na'am ammatan Maman ta, kina lpy?" murmushi tayi harda juya ido tace "lpy lau Mama, inasu Anty Zainab da Ihsan?" "duk sun tafi makaranta" "Baba fa, Ya Kakan mu?" "baban ki na nan lpy, Kaka kuma tana sasanta tana hadadda abubuwan dazata sa akawo miki" dariya tayi sosai tace "Mama yaushe zakizo inata kewanki sosai" "ba yanzu ba Hamida, amma karki damu watarana zanzo, Anty Lami zata dinga zuwa dubaki akai kai, ya Mijin naki?" cikin sassanyar murya tace "Alhamdulillah" gyada kai Mama tayi tace "gud, hope kina addu'a sanan kina azkar as usual ko, yau kinyi ko?" gyadamata kai tayi tace "eh inayi Mama" "to kidage dayi kinji, ki dinga ma mijinki shima sanan ki dingamai addu'a, inda halima ki dinga tashi tsakar dare kina gayama Allah bakutun ki kinji Hamidah na" gyadama Maman nata kai tayi tace "to Mama" murmushi Mama tayi tace "akwai abinda nakeyi yanzu, zan dinga kiranki kinji kowace matsala kike dashi nice mahaifiyar ki always consult me okay" ahankali tace "ok Mama" "Allah yamiki albarka, Allah yabaku zaman lafiya, Allah ya karemin ke aduk inda kike sanan Allah ya tsaremin ke kinji" ahankali muryanta narawa tace "Ameen" "don't cry kinji, my prayers are always with you haka aure yake nima haka Abban ku ya aureni yarabani da yan uwana yakaini chan wani gari nesa dasu bagashi yanzu yadawo labari ba and am very happy and so proud of your father ba" gyadakai tayi tace "uhm" "yauwa Hamida na, take care of your self ko, kidinga yima mijinki da yan uwanshi biyayya Allah ya karemin ke" ahankali tace "Ameen" Mama ta katse wayar, fashewa da kuka tayi danji tayi tanaso taje gidansu tana kewan kowa, ganin kukan yay yawa gashi Aadil yaki dawowa dan da yanzu yadameta yahanata sukuni, duksai taji wani iri kaman wacce ke zazzabi hakan yasa ta tashi tana kallon ko ina, tsintsiya ta dauko ta shiga share sharen da babu datti ko daya adakin amma haka tahauyi, saiyau taga amfanin kawaye batada kawa ko daya aduniyan nan balle azo taya amarya hira, inda aka jejjera mata hadadddun turarukan wutan maiduguri ta taje ta saka a burner ta kunna nan dakin yadau kamshi bana wasaba, ta wuce bathroom ta dauro alwala tazo tai salla sanan tafito da sauri jin ana knocking wasu maid ne guda biyu suka kawo abinci suka ajiye a a dining sanan suka kwashi na safe suka tafi dashi dudda tanajin yunwa kasa cin abincin tayi sai kallon kofa take tanaso kawai taga Aadil yabude kofan ya shigo, bowl ta dauka da zuba pepper soup kadai tasa spoon sanan tabaro dining din ta shigo falo akan center table ta ijiye bowl din sanan tai wurin window, bude labulen tayi tana leka tsakar gidan kozataga Aadil babu kowa a tsakar gida sai wani mai aiki dayake watering plant, an gyara tsakar gidan tsaf kaman ba'ayi biki a tsakar gidan ba, Leke leke tahau yi kozata ganshi ganin bataga Aadil ba yasa taji kaman tafashe da kuka, sakin labulen tayi asanyaye tadawo ta zauna kan kujera tadau bowl din pepper soup din tafara sha ahankali dama daidai cikinta ta debo bayan ta shanye ta tashi taje takai kwanon kitchen ta wanke plate din sanan tadawo ta zauna tana kallon Tv ahaka wani baccin yasake kwasheta.



Kiraye kirayen sallan magrib yatada ta kallon ko ina tayi da sauri ganin bashi yasa ta tashi tai hanyar daki, bathroom ta shiga ta dauro alwala sanan tafito tahau kan dadduman tai sallan magrib tai azkar na yamma sanan ta tashi ta linke dadduman ta cire kayan jikinta ta linke tass sanan tawuce bathroom tai wanka da ruwan zafi sosai tafito daure da towel tazo gaban madubi ta shafa mai ta feffesa turare kafin taje gaban wardrobe taciro wata yar rigan bacci iya guwiwa white mai spaghetti hand, rigan yay mata kyau sosai ya kamata daidai jikinta ganin ankira isha'i yasa tadaura zani tasa hijab tai isha'i tahada da shafa'i da wuturi sanan ta tashi ta linke dadduman ta mayar ta ajiye fesa turarukan ta tayi tadawo ta zauna kan gadon tabuga tagumi abin duniya yamata yawa. Jin karan bude kofa da muryanshi yana cewa bye bye grandfather yasa ta tashi da sauri tai hanyar kofa, bude kofan tayi daidai shima yazo zai bude ya shigo yana sanye da kayan dazu hanunshi rike da ledan super market, zubamata manyan idanunshi yayi cikeda kewan ta, dauke kai tai kaman bashi tazo ganiba tawani shamur tai gefenshi zata wuce ajiye ledan yayi awurin ya bude hannayenshi ya rungumeta da sauri yana murmushi sosai yana tsalle yace "oyoyo My Hamidah" yawani irin chusa kanshi a wuyanta yana shakan mayen kamshin datakeyi hanunshi na yawo abayanta, lamo itama tayi ajikinshi hakanan taji tanaso tarike shi, haka kawai wani irin natsuwa na shiga zuciyarta, sunkai kusan 6min ahaka dukansu sunyi shiru abakin kofa suna sauraran bugun zuciyan junan su, dan tureshi tayi hakan yasa yadago ya kalleta, hararanshi tayi kaman yanda yake mata kaman zatai kuka tace "ina kaje ka barni ni kadai?" washe baki yayi yace "grandfather took me out, and i even cried for him" yafada yana turo mata baki a shagwabe hakan yasa ta kama hanunshi tadau  ledan suka shiga daki ta zaunar dashi abakin gado tace "mesaka kai kuka?" raurau yayi da ido yace "i told him i want to go back to your place, i don't like that place i was scared i don't want you to leave again" dan murmushi tayi sabida yanda yay maganan was damn adorable and cute kumatun shi taja tace "I will wait for you don't be scared again okay" gyada mata kai yayi yafada jikinta yana murmushi yace "chocolate" da sauri ya dago yadau ledan ya zazzage duka abunda ke ledan akasan daki sanan yatashi ya kwaso duka chocolate din da sunmafi karfin hanunshi sabida yawansu ya mika mata yana murmushi yana kakkashe mata ido yace "your chocolate" karba tayi tana murmushi itama kaman shi tace "thank you My Aadil" da sauri yace "you are welcome My Hamida" "tashi kaje kai wanka kazo kaci abinci" girgiza matakai yayi yana kokarin cire rigan jikinshi yace "am not hungry" gyadamai kai tayi ta tashi tana tattare sauran chocolate din nakasa dan bakaramin aikinshi yacire kayan agabantaba, bayi yabude ya shiga hakan yasa tafita falo ta zauna akan kujera tana kallon game of love atashar Star life.



 Tayi nisa sosai acikin kallon taji ya kwala mata kira. "My Hamida" tashi tayi da sauri jin yanda yakiratan yana shirin barkewa da kuka, bude kofa tayi ta shiga, zaune taganshi akan gado kaman zaiyi kuka yay folding hannu akirji yana daure da towel a waist yace "where are my clothes?" dan murmushi tayi saikuma ta dauke kai tawuce gaban wardrobe din yana binta da kallo, pajamas ta ciromai milk color masu taushi ta ijiyemai kusada shi, make mata kafada yayi yace "i want boxer only" batare data kalleshi ba tajuya tajawo drawer taciromai wani boxer ta ijiye tadau pajamas din ta maida ciki tajuyo daidai yagama saka boxer yamika mata towel din daya daura a waist, karba tayi batare data kalleshi ba shikuma sai wani irin binta da kallo yake tabude bathroom ta shiga tai hanging towel din a hanger sanan ta kalli madubin bangon wurin, tai wani irin kyau da ita kanta batasan tanada irin kyan ba, hannayenta dasuka sha lalli tadaga ta nunama madubin hanun sunyi wani irin kyau kaman ba hanunta ba, bude kofan da akayi yasa tasaki hanun tajuyo da sauri ta kalli kofan, Aadil ne ya shigo yana kallonta yace "let's go, i want to do like yesterday, is very sweet" yay maganan yana kallon wuyanta zuwa kirjinta yana washe mata baki sosai, hararanshi tayi batare datace komiba tazo zata wuceshi ta fita hannu yasa zai kamota tabude kofan da gudu tafita tana dariya shima biyota yayi da gudu yana dariya sosai yace "i will catch you, ojuju calaba mai wasa da yara kamota" tuntsurewa tayi da dariya sosai, indai Aadil ne she's so free with him kaman ba itaba da bata iya kallon mutane ba. "ojuju kamota" dariya tasakeyi sosai dan duk idan yay hausa sai abin yaso yabaka dariya, hawa kan gado tayi shima yabiyota tai tsalle ta dirka kasa zata arce ya riko bayan riganta gam ya dirko shima yana murmushi yace "I catch you" yay maganan yana zama abakin gadon yanabin curved full hips dinta da kallo yawani irin fizgota tafado kan jikinshi tana nishi tadan harareshi tace "wat are you doing? Kaga kasa nai gudu am tired" make mata kafada yayi yana gyara zaman kafanta zuwa side side nashi kafafun a tsakiyan kafafun ta, zaunar da ita yay kyau yay wrapping hands dinshi around her back yana mata murmushi yana fari da ido yakai fuskarshi ahankali ya daura a gefen wuyanta yana shafa mata gashin sajenshi yana shakan kamshin dake fita daga jikinta, wani irin tashi tsigan jikinta yayi hakan yasa tarike mai kafada gam ta saki ajiyan zuciya murya chan kasa tace "stop it My Aadil" girgiza mata kai yayi yasa hannu yakama ass dinta yay squeezing sosai har saida tai kara. "mmmm, b...b..ari" ahankali batare daya denaba yadaura harshen shi kan wuyanta yawani irin laso slowly, kara rirrike shi tayi jikinta yafara rawa tace "washh, dan Allah kadena yanamin wani irin kaji my Aadil" make mata kafada yayi kaman zaiyi kuka ya daga hips dinta yaja riganta sama yatura hanunshi ciki yana shafa cikinta in circular form, kasa daurewa tayi ta kabar da hanunshi tana kokarin tashi yariketa gam cikeda tsoron karta tashi yasakin mata kuka ahankali yana kankame mata ciki yatura hanunshi sama yakama boobs dinta da sauri yana matsawa da karfi sosai yasa dayan hanunshi yajuyo da fuskarta yana kuka kaman wani jariri dake rigima ya chapke bakinta tareda sakin wani irin ajiyan zuciya kaman wanda yasami abinci yana jan nipples dinta tajikin riga sosai kaman zai ciro, runtse ido tayi tanajin wani iri dabata tabaji ba dan sosai takejin wani irin cool dadi kaman karya dena, ahankali yasaki bakinta yasakin mata kuka mai kara sosai yace "ciwo have start" yay maganan yana daga hips dinta daga kan cinyarshi shima yay bucking up kadan trying to free his erection dakemai ciwo sosai tacikin boxer, jan boxer yayi kasa yana kuka kadan kadan yabarshi ata wurin gwuiwa hakan ya bayyanar da huge erection dinshi, dawo da ita yayi arude ya zaunar da ita akai batare da yasan maiyakeyi ba jikinshi na rawa sosai, ihu tayi ta tashi da sauri dan dudda da pant dakuma riga ajikinta saida taji kaman ya daurata kan wani babban karfe, fashewa yayi da kuka sosai yana kama hips dinta yace "sit down" yay magana yana janta ya zaunar da ita akai daga ita harshi atare suka saki kara tana kokarin guduwa yana kara zaunar da ita akai yanajin wani irin jarababben dadi ya chapke bakinta yana squeezing boobs dinta sosai, kuka tasakin mai ahankali tana kara kama kafadarshi kaman her whole life depend on it.....



Horn Abie yayi masu gadin gidan suka budemai gate ya shigo baima tsaya ya paka motar da kyauba yafito yana gyara zaman babban rigan jikinshi ko rufe kofar motar baiyiba yadau hanyar part dinsu Hamida, kana ganinshi kasan baya cikin kwanciyan hankali fuskarshi harwata yar kumbura tayi sabida tsaban tashin hankali da azaban da Ozo ke ganamai kullu yaumin danna kwana talatin zaimai azaban na saba doka.

46....



Direct yadaura hanunshi kan handle din kofan batare dayay sallama ba ya murza ahankali ya shiga, maida kofan yayi yarufe yana kallon ko ina na falon da babu datti ko daya a dakin, dakin sai wani irin mayen kamshi yakeyi bana wasaba dake sanyaya rai, da sauri yay hanyar dining cover shoe takalmin kafarshi nabada sound pus pus pus kirjinshi na bugawa shikadai yasan the reason behind doing dis, corridor yabi ya tsaya agaban bedroom dinsu ya kafa kunenshi jikin kofan kirjinshi nawani irin bugawa kaman Ozo zai bayyana agareshi yamai punishment....


"uhnnnn" Hamida tai sound din atsorace ganin yau kaman yana neman tsinke mata nipple ne tana kokarin fizge bakinta, make mata kafada yayi yana karajan hips dinta yana daura dripping erection dinshi akai, rikeshi tayi gam tana girgiza mai kai da sauri tana kokarin fizge bakinta, wani irin loud groan yayi about to explode sabida yanda hips dinta ke gogamai erection dinshi yana hawaye yanajin dadi.....



Mugun rudewa Abie yayi jin yanda Aadil ke groaning yasaki wani irin salatin cikin tashin hankali, shikenan yamutu ya lalace, Aadil yayi, is Aadil having sex ko mene? Da kafa yadaki kofar dakin daga Aadil har Hamidan saida suka mugun tsorata suka dagokai atare suna kallon kofar dakin, dawani irin sauri Abie yashigo dakin kaman mahaukaci, arude Hamida ta ture hanun Aadil din daga saman riganta dayake kama boobs dinta tana kokarin tashi daga kan cinyarshi  tana kallon Abie da fuskarshi ya mugun tsoratata, kafin ta ankara Abie yawani irin fizgota cikin tsananin fushi ya tsayar da ita ya daga hannu yakifa mata wani irin hadadden wawan mari da batajin antaba mata irinshi a rayuwanta ba, wani irin wawan ihu tayi gabaki daya taga duhu dip bata gani, tashi Aadil yayi yanajan boxer dinshi sama yafashe da kuka yakaraso wajen yasa hannu yature Abie da karfinshi yaja Hamida ya rungumeta yanama Abie mugun kallon dabai tabamai ba, sake fizgota Abie yayi arude yace "dan uwarki abunda iyayenka suka koyamiki kenan? Eye? Tarbiyan da aka koyamiki kenan kinason ki lalatamin d'ana, me Aadil yasani dakike batamin shi, yaron da ko hanun mace bai iya tabawa ba, kina koyamai taba ki, kina koyama d'ana lalata Amatullah, raping yarona kikeso kiyi eh?" yafada yana jijjigata kaman zai katsa ta idanunshi sunyi jajir kaman bana Abie ba, tureshi Aadil yayi azuciye yace "stop beating My Hamida, you are a wicked Abie" turashi Abie yayi yadakamai tsawan dabai tabamai ba ya daga hannu zai kwasamai mari yakasa ya nunashi da yatsa yace "shut up, kamin shiru kafin kaja na bubbuge ka anan wurin Son, i will get back to you kaima so just zip your lips" yajuya kan Hamida dayake rike da ita yasa hannu awuyanta ya shaketa kaman zai kasheta yace "dan ubanki kifadamin gaskiya, did you sleep with my son? Kinmin raping d'ana ne? Inkikamin karya saina kaiki har lahira billahillazi" wani irin ihu Aadil yayi ganin yanda Hamida takeyi kaman zata mutu a hanun Abie ya rike Abie yana janshi yace "don't kill my Hamida, leave her, let go off her Abie" sakinta Abie yayi ganin yanda Aadil ke kuka yana jijigashi kaman zai shide, baya tayi tana shafa wuyanta tana tari sosai idanunta sunyi jajir sun fiffito, da sauri Aadil yay wurinta zai tareta yana kuka Abie ya fizgeshi yace "zonan dan uwaka, kaida ita har abada bazan zauna takoyama iskanci ku kaini kubaro ba, u are leaving this house yau yau dinan" yay maganan yana janshi yana fitar dashi daga dakin, fashewa da kuka sosai Aadil yayi yana dukan hanun Abie yana kokarin fizge hanunshi yana makemai kafada, fitar dashi Abie yayi daga dakin da karfi da yaji yay wajen motarshi dashi yace "muje, na tsaya nasaima kaya ahanya" fashewa da kuka sosai yana dukan hanun Abie yana kokarin cizonshi yana kuka sosai, ya kwala ihu yana kiran Mami da Baffa. "Mamiiii, Grandfather. "

47....




_masu fitarmin da novel waje suda Allah_


_Zaki tura 300 access fee ta 3107021073 first bank aisha Muhammad in kinason this book, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_


_you can also send MTN card na 300 for those da basu da account number ta watsapp number na 07012181461_


_karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi pay anan or pay achan_





"Mamiii" ya kwalama Mami kira da karfi sosai yana wani irin kuka yana kokarin fizge hanunshi daga na Abie, fitowa Mami tayi daga part dinsu adan rude tana waige waige batare datama lura da inda yay parking motar ba, cikin kuka sosai ya kwalama Mami kira. "Mamii" juyowa Mami tayi ta gansu , ganin Abie da rabonda tasashi a ido yau kwana uku kenan najan Aadil da babu kaya ajikinshi saidan gajeren boxer yana kokarin turashi a mota da karfi da yaji yasa da gudu tayo wajen tana salati. "innalillahi wa innailaihi raji'un, Abie lafiya, me Aadil yamaka? Ina zaka da shi ahaka, menene?" tun kafin takaraso wajen take jero uban tambayoyin nan, tana karasowa wajen Aadil ya daddage cikin kuka sosai ya fizge hanunshi tareda tura Abie yakoma bayan Mami da gudu ya rungumeta ya kulle hanunshi akan cikinta yana kuka sosai, yanda Mami taji kirjinshi na bugawa yana kuka yama kasa magana yasa ta dago kai ta kalli Abie dayake ma daga Mami har Aadil din mugun kallo, cikeda tashin hankali Mami tace "Abie mai Aadil yama haka kaji yanda kirjinshi ke bugawa kuwa ai wanan saiya iya fadi ya mutu, menene Abie ina zaku ina zaka kaishi ahaka babu kaya ajikinshi?" cikin kumfar baki sosai Abie ya nuna bangaren Aadil din yace "zan rabashi da shegiyar yar iskan yarinyar dakuka auramai ne, ni dama tun farko bantaba son auren nan ba aka nunamin iko da isa nida dan cikina amma aka nunamin banda ta cewa akan rayuwanshi, kamasu nayi fa yanzun nan tana koyama Aadil dinmu lalata ke kinga abubuwan datake mai kuwa saisa zan tafi da Aadil din kafin ta kaimu tabaro tana koyamai irin wayan nan abubuwan ai duk macen dayagani danneta zai dingayi yana duramata ciki kindaisan condition din danki kindaisan ba hankalin kirki gareshi ba, bazan zauna raye ba idanunna biyu, da karfina da lafiyata inga wata mace nakoyama d'ana lalata ba in kyale, dis innocent boy yaushe ya girma dazai fara irin wanan rayuwan" cikin kuka sosai Aadil dahar lokacin bai dawo daidaiba yace "he beat my Hamida Mami, he strangled her she almost faint" kallon Abie Mami tayi da idanunta dasuka kada tace "Abie da girmanka zaka fada dakin danka da matarshi at this hour of the night?" tai maganan ahankali saikuma cikin harsh tone tace "kace lalata? Wani irin lalata kuma da auren su, auren sunna da dumbanim jama'a sun shaida ne zakace haka? And inda ace Aadil yanada halin danne mata ai daba tun yau yafara ba dan naga batun yau yabalaga bako, shekaran Aadil talatin aduniya, uku da sifili Abie ba uku kadai ba dakake neman maidashi yaro dan shekara uku, daka fito dashi ahaka da daddaren nan karabashi da matarshi ina zaka kaishi? Wai anya lafiyan ka kalau kuwa Abie am worried about you fa, rabon dana saka a ido yau kwana uku daga shigowan ka kuma sai wanan, kaga nan tsakar gidane akwai yan aiki a part dinsu, kaga Baba ba ishashen lafiya gareshi ba karyaga muna hayaniya hawan jinin shi yatashi, Aadil wuce mutafi na rakaka part dinku" tai maganan tana zare hanun Aadil din daga kan cikinta ta rikeshi tana juyawa da zumar su tafi, wani irin unexpected fizgowa Abie yama Aadil da Mami tarike yace "na rantse miki da ubangiji yagama rayuwa da Hamida idan ke kwakwalwarki batasan miye lalata ba ni nasani because am a Man, and i can not risk karuwan yarinyar dakuka auromai tabatamin d'ana ba" yay maganan yana yin hanyar mota dashi Aadil na turjewa yana mikama Mami hannu, da sauri Mami tabisu tarike bayan rigan Abie tace "wai wat is wrong with you Abie? This is not you fa, bahaka kake ba, inma lalatan sukayi ba a dadin ka bane, at least zamusa ran watarana zamuga jikokin Aadil dinmu ko, to meme amfanin auren damuka mai mawai? Badan yasami natsuwa ajikin matarshi bane sanan su hayayyafa ko, so let go off this boy you know clearly Aadil can not live without me gakuma Hamida dayake so kasan idan karabashi damu u are just killing him ne completely" juyowa Abie yayi yana rike da Aadil din yama Mami wani mugun kallo cikin fushi da daga murya yace "sakeni, sakeni nace kodan kinga ina cikin gidan ubanki ne yasa kike feeling you have d right to grab my shirt like this" wani irin kallonshi Mami tayi dan as far as she knows Abie baita regarding Baffa as ubanta ba saida ubansu, mahaifinsu, baban su, amma yau jibi abinda kefitowa daga bakinshi, cikin wani irin mugun tsawa Abie yace "sakenmini raga kafin namiki abinda bantaba mikiba tsawon aurenmu shekara talatin da daya yanzu" rawa muryan Mami yafara ita tsoron Abie ma take hakan yasa takara rike rigan nashi da kyau tace "not until kasaken mini d'ana nima sanan zan sakeka" sakin Aadil Abie yayi cikin fushi daidai lokacin Baffa nafitowa daga shashinshi sabida hayaniya dakuma kukan Aadil daya cika ko ina na gidan, wani irin wawan Mari Abie ya dauke Mami dashi ya fizge hanunta daga riganshi ya murde hanun da karfi yana mata mugun kallo, wani irin kara Mami tayi cikin azaba Baffa yay salati yana karasowa wajen da sauri. "assha, assha, subhanallahi, Abdullahi me haka? A tsakar gida kuke irin abinnan" ture Mami yayi cikin tsananin tsana  tai baya tafadi akasa ya finciki Aadil dake mugun kuka yana dukanshi abaya sabida murdema Mami hannu dayayi yawani irin turashi abayan mota da karfi da yaji ya rufe motar yabude gaba ya shiga yay locking motar ya danna wani jarababben horn mai gadi daketa kallon drama tun dazu ta window dakinshi yafito danya bude gate, Baffa yakaraso wajen yana dogara sanda ya tsaya ta wajen window yana kiranshi. "Abdullahi, Abdullahi, Abdullahi bakaji nane, ina zaka da daddaren nan?" cikin fushi yaja glass din motar sama yay reverse batareda ya kalli Baffa ba yafita daga gidan Aadil na dukan glass din motar sosai yana kallon Mami da Baffa da Hamida daya hangota a labe chan gaban shashinsu tana wani irin kuka mai cin rai.




Juyowa Baffa yayi ya kalli Mami dake zaune dabas akasa tana kallon hanunta dahar ya kumbura nan da nan yace "me haka kukeyi a tsakar gida Maryama? Tarbiyan da mahaifiyar ki tabaki kenan kafin tarasu chachan baki da mai gidan ki har kina rikemai riga iyye Maryama" share hawaye tayi tamike tsaye da kyar tace "bahaka bane Baba" nan takoromai abinda yafaru daga A to Z, salati Baffa yayi yadaga kai ya kalli bangaren su Aadil din, hango Hamidan tsaye ta rabe ajikin bango tana kuka sosai yasa yace "tashi Maryama yi shiru, je, jeki lallaso ta, dubo mana diyar mutane, bari naje nakira Sulemanu karki damu komi zai wuce kinji" ahankali tace "to Baba" ta tashi tana kakkabe jikinta tai hanyar shashin su Hamidan, tsayawa tayi agaban Hamidan da bama tasan da zuwanta ba, ahankali ta daura hanunta mai lafiya kanta, dago jajayen idanunta tayi ganin Mami ne yasa tafada jikin Mami tasaki kuka sosai jikinta na bari tace "am sorry Mami, am sorry" rungumeta Mami tayi back tanajinta kaman yarta mace tace "shiii ya isa" tai maganan tana dagota daga jikinta ta tallabo kanta tana kallon shatin hanun Abie akan fuskarta da wuyanta dayay jajir, ahankali tace "innalillahi wa innailaihi raji'un, am sorry Hamida, am sorry for everything kinji, ke amanar mu ce daga zuwanki gidan nan look at what happen to you, yi shiru muje dakina na gasa miki wajen na shafa miki rub" tai maganan tana share mata hawaye ta rufo musu kofar part dinsu sanan tarike mata hannu suka tafi part dinsu, bedroom dinta Mami ta shigar da ita ta zaunar da ita akan gadon tawuce ta shiga bathroom bata wani jima aciki ba tafito dauke da bowl da karamin towel aciki tana kallon fuskar Hamidan tanajin wani irin bakinciki, tsoro duk yakamata tana addu'a Allah karya kawo yan uwanta gidan nan kwanan nan inba hakaba mezata ce musu, meya sami yarsu, zama tayi a gefenta jikinta duk rawa yake ta matso towel din daga ruwan zafin tadaura wuyanta da hanun Abie yafito sosai tana cewa "sannu kinji daughter dan Allah kiyakuri" saida tagama sanan tamata na fuskan takawo rub ta shafa mata sanan ta gyara wurin ta dawo rike da paracetamol da ruwa tabata tasha tasake rungumeta feeling guilty sosai akan abinda Abie yama yar mutane ahankali tace "nakawo miki wani abu? Nahada miki smoothie?" girgiza kai tayi ahankali hakan yasa Mami ta kwantar da ita taja bargo ta lullubeta dashi tace "get some rest kinji, don't worry Aadil zai dawo" gyadama Mami kai tayi tana hadiye kukan sabida Mami, Mami ta shafamata gaban goshi tana sauke ajiyan zuciya tana kallon yanda fuskarta da wuyanta sukai jajir har baccin dole yay gaba da Hamidan. Sai alokacin Mami tafarajin zugin hanun nata ta tashi ta shiga bayi tasaka hanun acikin ruwan zafi sanan tafito ta mitsike da rub tadau wayarta ta kashe wutan dakin tafita daga dakin ahankali ta wuce ta shiga dakin su Aadil ta zauna akan gadonsu tabuga uban tagumi.




She taught yanda suka aurama Aadil Hamidan nan dayake mugun so sunyi solving 90% of their problem sauran 10% din zai zama na yanda zasu nemamai magani ya warke ne, wanan problem din Abie daya kunno musu kai kumafa, yanzu ina yakai Aadil? Wai da gaske abinda yace suda Aadil har abada did he really mean it? Wat did he mean? Wat is Abie up to? Aadil bai isa yataba matarshi bane or wat? Ina yakai Aadil? Tasan yanzu ko ina Aadil yake kuka yakeyi bana wasaba yana kiranta, hakan yasa tafashe da kuka sosai bana wasaba takai kusan 20min tana kuka ganin kewan yaranta da tunanin Aadil din na neman mata illa danhar kirjinta yafara zafi yasa tadau wayarta ta kunna tai dailing number Aabid.

48....




_don't read my novel idan baki biyaba_

_masu son novel dinan can chat me up 07012181461_





_Lagos_

_Victoria garden city_


 Sosai Vanessa ke kuka tana begging Aabid ya barta dan tunda tasamu kwanan nan yafara sex da ita babu randa bazatai kukaba, gashi dai he is a good fucker dan duk duniyar nan babu wanda yake fucking dinta taji tai satisfy taji dadi kaman zata zauce kaman Aabid, he's so big duk inyana ciki cikata yake fam idan yafara trusting in har mahaifanta takeji yana tabo mata, abinda yafi damunta duk in yanayi yadinga kiranta jewel, jewel kenan ita kuma she's Vanessa kuma tasan Vanessa yake cemata baitaba kiranta jewel ba, sosai take kuka all her body rawa yake tai grabbing ass dinshi da karfi sosai tace "Handsome please spare me, am tired dont injure me" batare daya damuba yawani irin juyata danko kadan bata gamsar dashi kodako zaiyi awa darine akanta maneji kawai yakeyi dan bai iya biye biyen mataba ita kadaice dashi kuma yasan bata bin wasu mazan danda tuni ya rabu da ita saisa dole ita kadai zai juyema sha'awar tashi dan mugun mabukaci ne shi baisan ko gado yayiba, doggy style yafara yana ramming dinta da karfin gaske yace "you've been begging for this now am giving you my expensive billionaire penis as u use to say, so don't complain lemme have fun girl and ride you wella" yay maganan yana ramming da karfin bala'i yana squeezing boobs dinta da basu da wani girman kirki yana yatsine fuska dan yana mugun son big boobs arayuwan shi, fashewa da kuka tayi sosai tana nishi kaman zata mutu danyasa tai releasing yafi sau hudu shi har yanzu baiyi ko sau dayaba, dariya yayi cikin jin dadi dan yana mugun so yaga wanan penis din nashi nasa mace kuka abinna bashi joy bakadan ba yaja gashinta yace "beg me, beg me" cikin kuka sosai tace "please, please please handsome cum okay i have shoot tomorrow karkasa na kasa tafiya fa, please cum, your dick is monstrous and you f*ck wild handsome bazan taba barinka ba u are a God sent i love you" cikin jin dadi ya lumshe ido yana bugata hard yanaji kaman Hamida ce yace "you love me Jewel? Say that again" da sauri tace "yes, yes i love you Handsome" ihu yayi yana gantsarewa yace "I love you Jewel, i love you Jewel ahhhh is coming" da sauri kafin ya danneta Vanessa ta fizge kanta tawani irin daura bakinta akan joystick dinshi dayama bakinta kadan sabida tsawonshi tana shan kan, kama gashinta yayi yatura penis din ciki sosai yana groaning da karfi itama haka tana slapping buttuck dinshi yawani irin releasing abakinta yana shouting Jewellll, kafin yafada kan gadon warwas itama tabishi tana shan penis din kaman tasamu minti saida ta side tass sanan ta tashi da kyar ta kwanta ajikinshi tawani irin kankameshi kaman zata hadiye shi sabida so tace "i love you handsome thank you for f*cking me" taja hanunshi tana daurawa abayanta buge hanun yayi yana maida ajiyan zuciya dan yay kusan 3 hours yana abu daya, tashi tayi ta kwanta gefenshi takama nonon ta tana turamai abaki ture boobs din yayi yabude ido kadan akasalance ya kalleta murya chan kasa yace "if you got me arouse again i swear am gonna fuck your brains out, i will destroy your pussy" murmushi tayi cikin wani irin mugun sonshi tai cupping face dinshi ta sakinmai kiss abaki hakan yasa ya lumshe ido tace "I love you so much, i love everything about you, how you speak authoritatively, how you act like a boss, everything, am so crazy in luv with you" dan murmushi yayi hakan yasa ta shiga kissing dinshi kaman zata hadiyeshi ringing da wayarshi yafara yasa ta kalli face dinshi yanda ya lumshe ido kaman baya jinta, ahankali tace "handsome your phone is ringing, are you sleeping?" batare daya bude idonba yace "get me d phone" tashi tayi daga jikinshi tadauko wayar daga kan side drawer ta mikamai batare daya bude idoba yay picking wayar yakai kunenshi itakuma Vanessa ta kwanta a gefenshi tana kallon big penis dinshi dake sleeping tana murmushi.




 Murya chan kasa ta wanda yagaji sosai yace "hello" daga tachan bangaren muryan Mami narawa sosai tace "son" tashi yayi zaune da sauri jin muryan Mami, da sauri yace "Mami na menene are you okay? Why is your voice cracking?" dan lumshe ido Mami tayi dan Aabid yanada wanan baiwan duk lokacin datake cikin damuwa ko bata fadamai ba shizai gane. "is something wrong with My brother Mami? Meyasame Dil?" yafada cikin tashi hankali, cikin wani irin murya dake shirin kuka tace "Aabid Abban kune, i don't know wat is wrong with Abie, ya mari Hamida ya shaketa yakusa sumar da ita sanan yamare ni nima yakusa karyamin hannu, and yatafi da Aadil wai bazamu kara ganinshi ba Aabid ina Abie dinku yakaimin twin brother ka i can't live without you two, kubiyun nan are my life, Aabid help me where has your father taken Aadil" tai maganan tareda sakin ma Aabid kuka ahankali mai taba zuciyar d'a tashi tashi Aabid yayi daga kan gadon cikin tsananin tashin hankali yafita daga dakin Vanessa nabin bayanshi da kallo ya sauka downstairs zama yayi akan kujeran dake bayan piano cikin raunin murya yace "stop crying Mami please, kukan ki zai hargitsamin brain ne nakasa tunani da kyau, is okay Mami na kinji" gyadamai kai tayi, ahankali yace "ya hanun naki yanzu and ya Hamidan?" ahankali tana share ido tace "am fine, na bata paracetamol sanan na gasa mata wurin she's sleeping now" shiru yayi ya lumshe ido yanajin wani zafi aranshi ahankali yace "ina Lagos yanzu first flight zan biyo gobe nadawo, karki damu okay nasan Abie, he will never hurt Aadil koma ina zaikai Aadil inhar yana tareda shi i know Aadil is safe, they must be a good reason behind his act kiyakuri kinji Mami na, ki lallashi Hamida be her comfort, i will come gobe okay" gyadakai Mami tayi yauta kara tabbatarwa y'a ya' rahama ne, maganganun Aabid sun mugun saka mata natsuwa bana wasaba, ahankali yace "kwanta kiyi bacci just pray for him kinji Mami na i will come gobe and i will call d Abie zanje na sameshi da kaina zan dawo miki da Aadil din don't cry be strong kinsan kece our strength uhm Mami na, I love you" murmushi tayi sosai tana kokarin komar da hawayen dake shirin zubo mata tace "I love you too My Son, Allah dawo dakai lafiya be safe okay" "alright Mami, Aadil is fine don't think much" ahankali tace "tom saida safe Allah ya tsaremin ku" "Ameen sweet Mami, best Mami in the whole world" murmushi tayi tace "thank you the best Son bye" bye yace shima ta katse wayar ta kwanta ahankali tanajan bargo tanajin natsuwa sosai bana wasaba ta lumshe ido.

49...



Agaban wani katafaren mansion Abie ya tsaya ya dauko wani remote ya danna gate din yabude yaja motar ciki, babban gidane da yaci uwar na Baffanau kyau sama da sau miliyan gidan kaman a turai, murmushi yayi ya kashe motar yajuyo ya kalli Aadil din daya ke kuka sosai har lokacin yace "stop crying nakawo ka hadadden gidana wanda yafi na kakan ku kyau, akwai wurin buga basketball aciki, akwai wurin table teble tennis kaga har gym namaka aciki ga alot of teddies and all sort of chocolate you could think of dakasani su favorite dinka duk akwaisu aciki, yauwa Aadil dina come and have a look kagani inka gansu you will forget su Mami ma trust me pure enjoyment ne gidan nan" yafito daga motar ya zagayo ta baya yabude kofan bayan ya mikomai hannu yana murmushi yace "yauwa My Aadil, Abie big Boy, har fish pond akwai aciki ga lift ga stairs you take anyone your heart desires, akwai video games, i have alot of money sama dana kakan ku i will give you anything you want my boy i mean anything kome kakeso" makemai kafada Aadil yayi yana kuka sosai yace "My Hamidaaaa" harara Abie ya watsamai cikin takaici ya fizgoshi da karfi da yaji yafito dashi daga motar yay hanyar cikin gidan dashi da fingerprint yabude door din mini palor din kafin su shiga hadadden falon kaman ba'a Nigeria ba, murmushi yayi yana nunama Aadil dake kuka sosai yace "kaga falon ka, muhau lift muje ma sama kagani tukunna" shiga sukayi ya danna one yakaisu first floor transperent glass tiles ne akasan kana hango falo daga wurin, ganin yanda yakemai kuka jikinshi harya dau zafi yasa yabude wani daki ya shigar dashi ya subhanallah dakin yahadu to d core, zaunar dashi akan lumtsetsen gadon yayi yana murmushi da sauri yajuya yabude wardrobe ya ciro wasu sababbin kaya daga hanger yakawo ya ijiyemai yanamai murmushi yace "yauwa My Aadil tashi kasa kayan, bari kaga na kunnama video game kabuga" tv bangon dakin ya kunna yajuya yafita da sauri sai gashi ya shigo da basket of different expensive chocolate and sweets yakawomai yana murmushi yace "yauwa my Aadil sha kadena kuka, kaga dare yayi bacci yakamata kayi yanzu kaida kake bacci dawuri" kabar da sweet din Aadil yayi cikin kuka sosai duk suka zube akasa, dawani irin fushi ya makema Abie  kafada yana kuka, ajiyan zuciya Abie ya sauke kanshi na daukan mugun chaji dan baiso yaga abu yasami Aadil barinma in yana kuka, ahankali ya zare babban rigan jikinshi ya ijiye kan gadon ya ciro handkerchief daga aljihun shi ya share gumin dake keto mai yana kallon Aadil din dake wani irin kuka dake tsumamai rai har wani irin ajiyan zuciya yake saukewa cikin kuka idanunshi sunyi jajir jijiyoyin kanshi sun fito radau, tsaki yaja yana karajin wani irin tsanar Hamida aranshi duk haduwanta da dan shine ya zaman mai wani irin mugun matsala da kalubale arayuwa, ahankali yasa guiwanshi akasa yana kallon Aadil din yakama kunenshi kaman zaiyi kuka yace "dan Allah kayi shiru Aadil, i promise kome kakeso i will do it for you i promise, but dan Allah kai shiru kaji, kukan ka zai karasa kasheni, idan da kasan matsalolin danake ciki ayanzu haka daka tausayamin, kadena damuwa da wanan shegiyar yarinyar yar matsiyatan wanda ubanta ke saida kaji, kaji da kullum anacin sama da arba'in a gidanku gasunan him a frozen fridge, babanka nada kudi Son, kome kakeso zan makashi, kome kakeso daganan har zuwa bangon duniya inada kudin zansa akawo ma, barima kaga nakawo ma kudi kome zakayi dasu kayi" tashi yayi kaman mahaukaci yafita daga dakin baiwani jimaba yashigo dakin yana jan wani babban ganamasgo dake nan zin din a kulle yana kallon Aadil din dake kuka yanamai murmushi, zama yayi abakin gadon kusadashi yasa hannu ya zage zip din ganamasgon uban kudi dake nan dollars note suka bayyana cike a jakan, wani irin murmushin dadi Abie yayi yajuyo ya kalli Aadil din dake kuka yana kallonshi ya lashe baki kaman tsohon maye, yasa hanunshi da sauri ya ciro wraps din dollars note din guda hudu dake kyalli  yawani bubbuga kudin together agaban fuskar Aadil yace "kasan menene wanan My son?" yay maganan yana wani irin murmushin jin dadi yace "this is money Boy, manny, hausawa sukace milamila, kaga kudin nan na ganamasgon nan" yay maganan yana karkatamai ganamasgon da kyar sabida nauyinta dan acike take da kudi yace "duka kudin nan nakane kai yanda kakeso dasu nabaka, kai bacci akansu kayi bari dasu duk yanda zakai dasu, kaganni nan your Abie have money Aadil, plenty plenty money enough to buy all this kano kai Nigeria ma gabaki daya, kudin Abie ka basa karewa duk sati sati nake samin kudin da zan iya cika irin manyan ganamasgon nan guda goma sha biyar dasu, inhar you are a good boy kanajin magana na zan karoma irin ganamasgon kudin nan guda biyar kaji my son, my handsome boy kaji ko" makemai kafada Aadil yayi cikin fushi ya fizge kudin hanun Abie ya cillar dasu chan har suna tsalle suna fita daga dakin wasu kuma sukai wurin TV, cikin kuka sosai da muryanshi data dishashe yace "take me back to Mami, Mamiiiiiii, My Hamidaaaaaaa" yaja sunan Mami da Hamidan yana kuka kaman zai sume, tagumi Abie yayi yana tsinema Hamida aranshi yana tunanin wani dubara kuma zaimai ganin har wurin dayan dare Aadil kuka yake jikinshi yay zafi idanunshi kaman jan gauta yasa hankalinshi yatashi ainun, babu kallan dabaran dabai maiba amma sam Aadil Hamida yake kira hakan yasa Abie ya yanke sharawan kaishi wajen Ozo gobe dama gobe sunada meeting karfe taran dare, da kyar yasamu wani wahalallen bacci ya kwasheshi hakan yasa yadau bargo ya lullubeshi dashi ya zauna agefenshi yana tunane tunane, bayan kudi arayuwan nan d next abu dayake so da duka zuciyanshi is Aadil, maisa Allah yake testing dinshi da abu mafi soyuwa agareshi Aadil and Money?.





***

Wuraren shidda na safiya Mami ta bude ido, ganin yanda ta makara gari haryadan soma wayewa yasa tai bathroom agurguje, wanke baki tayi sanan tafito daga bayin daure da alwala, dadduma ta shinfida tai sallan bayan ta idar tai azkar sama sama ta mike da sauri dan zuwa tada Hamida, ahankali tabude kofar dakin bakinta dauke da sallama tana kallon yanda Hamidan ta kudundune kan dadduma tana bacci tana sanye da hijabin Mami, maida kofar Mami tayi tarufe takaraso cikin dakin tana kallon fuskar nata ganin yadan washe shaidan hanun Abie, tsugunnawa tayi agabanta takama hanunta tadan bubbuga tareda kiran sunanta. "Amatullah" saida takira sunan kusan sau uku sanan taji tabude kodaddun idanun nata dake cike da bacci, ahankali Mami ta mika hannu ta dagata zaune tana kallon fuskarta tace "kinyi sallan subhi?" girgiza kai tayi tana sosa ido, hakan yasa Mami tace "but naganki da hijabi akan daduma" cikin siriruwar muryanta dake cike da bacci tace "nakasa bacci ne shine natashi naita salloli" "sorry bansan kin kasa bacci ba ai danazo, tashi yanzu kije ki dauro alwala kiyi sallan kinji" gyadama Mami kai tayi Mami ta taimaka mata ta mikar da ita ta tashi ta shiga bayin itakuma Mami tawuce tafita daga dakin danzuwa fadinma masu aiki abinda za'a dafa, fitowa tayi tai wani irin mugun yaushi gabaki daya tunanin Aadil take jiya takasa bacci hakan yasa ta tashi ta dinga salloli tanamai addu'a ita kadan batasan lokacin data fara damuwa da Aadil hakaba, batasan lokacin daya shiga ranta hakaba, share hawayen dasuka zubomata tayi tasa hijabin Mami ta kabbarta salla, bayan ta idar tai azkar sanan tafara neman Al Qur'ani, akan drawer Mami taga wani hakan yasa ta dauko ta zauna tafara karatu har sai wuraren tara da rabi ta ijiye nan tasamu tadanji dama dama zuciyarta yadan yimata wasai. Tashi tayi ta linke dadduman ta cire hijabin ta ta linke ta ijiye sanan ta shiga gyara dakin gadon da baiwani yamutse ba ta gyara tsaf sanan ta zauna akan gado, shigowa Mami tayi tareda wata yar aikinta data riko tray ta nunamata idan zata ijiye tawuce tafita, ahankali tace "ina kwana Mum" murmushi Mami tayi tace "kintashi lpy daughter na, taso kiyi breakfast nabaki magani kisha kinji" gyadama Mami kai tayi ta sauko daga kan gadon kaman yanda Mami ta umurceta tahada tea tasha da su chips da egg da aka kawo mata tama kasa cinyewa dan sunmata yawa Mami takawo paracetamol takara bata tana murmushi dan sosai takeso ta danne damuwanta kotabama yarinyar strength but itama tunanin Aadil da Abie takeyi bana wasaba.

Sawa Mami tayi akazo aka fitar da tray din ta zauna kusada Hamidan tana janta da hira kadan kadan Hamida ke amsawa sallama akayi big Mum ta shigo dakin cikeda damuwa tace "meya faru sis? Ina Abban su yakai Aadil?" dan murmushi Mami tayi tana kokarin rike kukanta, ahankali Hamida tace "ina kwana Mummy" murmushi Big Mum tayi sosai tace "sannu daughter ya kk" tashi tayi ta kalli tace "lpy lau" ta kalli Mami tace "zanje nai wanka" gyadamata kai Mami tayi ganin yarinyar daurewa itama kawai take tace "dau hijabina kisa karki fita ahaka" hijabin ta dauka tasaka sanan tafita daga dakin tai shashinsu, ahankali tabude kofar shashinsu ta shiga tana kallon ko ina, kafin ta tadaga kafa kaman mai koyan tatata tai hanyar bathroom dinsu bude kofan tayi ta shiga idanunta suka sauka akan some few chocolate dake kasa wanda Aadil yakawo mata jiya, wani kuka ne yazo mata da sauri ta rufe fuskarta da hijabi tanayi kafin tafada kan gadon taja rigan Aadil din datagani akan gadon ta rungume sosai tanajin kamshin shi tana kuka ahankali tace "come back Aadil kaji, come back to me kaji My Aadil, inaso na kula dakai and watch you koda yaushe atare dani kanamin that ur cute smile and talk, i miss you so much" tafashe da kuka ahaka bacci yy gaba da ita sai wuraren azahar ta tashi gyara gadon tayi sanan ta shiga wanka.

50......


_Antyna! People like you are rare a duniyan nan, thank you so much, and i dedicate this page to you, thank you ones again for taking care of me_







Shiryawa tayi tsaf cikin wani free gown na atampa red and black, color yay mata kyau sosai ajiki, batasa ko kwalli ba danji tayi gabaki daya tagaji da komi, fita tayi taje kitchen ta dauko broom tadawo ajiye broom din tayi akasa ta gyara gadon tsaf dabai wani baciba sanan tadau tsintsiyar tafara sharan dakin just to while away time dan dakin ba datti, baban zoben silver color dakenan kaman na azurfa data gani a tsakar dakin yasa ta tsugunna tana kallon zoben, daukan zobe tayi da hannu da sauri ta kalli zoben jin zoben da shegen nauyi a hannu kaman tadaga wani babban abu, hakan yasa tace "me Aadil yakeyi da wanan zoben mai nauyi haka" ajiye zoben tayi agaban madubi tana tunani dan bata taba ganin zobe a hannun Aadil ba, kodai bata lura da kyau bane, no babu zobe a hanun Aadil ko daya.




Share batun zoben tayi daga ranta tadau broom din tacigaba da sharan ta share ko ina na gidan ta turare gidan da turare sanan tadauko wayarta tazauna akan kujera tai yan danne danne ganin duk batajin dadin maganan Aadil sai zuwanmata yake arai yasa takoma bedroom ta dauro alwala tasa hijabi ta zauna tafara karatun Al'qurani har lokacin la'asar tayi ta ijiye tai salla tana idarwa ta daura karatun danko kadan bamatajin yunwa har magrib ta tashi ta shiga bayi ta dauro alwala, sallaman Mami dataji yasa tafita tana zura hijabi, murmushi Mami da idanunta sukai wani iri tayi tace "jekiyi sallan ki mun shigo muduba kine dama" gyadakai tayi taredayin murmushi tajuya takoma ciki, Big Mum tace "yarinyar badai hakuri ba, ga dauriya dudda abin na damunta she's trying to hide it, muje muyi sallan muma" bude kofa sukayi suka fita daga dakin.

Sallan magrib tayi tacigaba da karatun har lokacin isha'i......






Wuraren takwas saura Abie yasake dawowa dakin ya kalli Aadil da tun safe yake kuka yaki shan daidai da ruwa agidan Abie hankalinshi duk yabi yatashi dan yasan yanajin yunwa kuma Aadil baison yunwa ko kadan nan da nan zakaga yanama kuka dazaran yaji yunwa, zama yayi gefenshi rike da bowl of fresh sliced fruits kaman zaiyi kuka yace "tashi to kasha saina kaika wurin Hamidan, idan bakasha ba bazan kaikaba" kallon Abie yayi da sauri yana tashi zaune yace "My Hamida?" gyadamai kai Abie yayi yay murmushi yace "yes but only if u have this fruits, you haven't eaten since when we get here" fizge bowl din yayi ya debo fruits din da fork yakai baki yasha yana murmushin kuka Abie na binshi da kallo yanajin son dannashi na ratsashi, sau uku yasha yamika ma Abie yace "am okay" tsabagen yanda ya kosa yaga Hamidan, kallon fruits din Abie yayi dudda baiwani ci wani abuba but at least is something, yasashi yasa wani abu a cikinshi tundama dabaran tai aiki haka zai dingamai kullum yanamai wayau yanasashi yaci abinci, kayan dayakawo mai ya nunamai yace "tashi to kasa mutafi" jumping yayi from bed yanajin wani irin mugun ciwon kai yasaka kayan yay tsalle tareda murmushi yace "let's go to My Hamida Abie" tashi Abie yayi yakama hanunshi suka fice daga dakin har zuwa compound yabude mota yasashi ciki sanan ya shiga gaba yaja motar suka fita daga gidan, tafiyan wurin minti talatin sukayi yay parking agaban gidan gonanshi dake wanan kyauyen, parking yayi yafito yabudema Aadil din fitowa Aadil yayi yana kallon gidan yace "My Hamida is here Abie?" yes Abie yace yakama hanunshi sukai ciki yaciro key yabude kofan ya shiga sitting room din dayay kura sosai kafin yayi hanyar dakin tsafinshi dashi, key yaciro yabude kofan yana rike da hanun Aadil suka shiga dakin dayay mugun duhu Abie yamaida kofan yarufe, rikeshi gam Aadil yayi yace "where's My Hamidah Abie this place da duhu" sakata Abie yasaka nasama dana kasa yace "don't worry u will see her now" yana rike da hanunshi yakarasa a duhun nan ya tsaya inda uniform dinshi suke yasaki hanun Aadil dake shirin yin kuka ya cire kayan jikinshi yasaka jan rigan tsaf sanan yana rike da hanun Aadil ya laluba yaciro ashana yay gaban dakin ya tsugunna ya kunna candles din wajen dake tare da gumaka da sunkai guda goma haske ya gauraye dakin, ihu Aadil yayi sosai ya rirrike Abie ganin mutane da sunkai guda goma shabiyar a tsaitsaye a dakin suna snye da jajayen kaya saikuma wani dake zaune gaban dakin fuskarshi kaman na biri idanunshi jajir dakaman jan wuta, runtse ido Aadil yayi gam ya rirrike Abie yace "Abie this is not My Hamida this is ojuju calaba, this is gorilla, am scared Abie" wani irin tsawa Ozo ya dakama Abie tareda buga karfen hanunshi akasa yace "kayi latti Tursoso sanan wayace kataho mana da wanan meeting iye" da sauri Abie yasa guwiwanshi akasa hakan yasa Aadil binshi, jikinshi narawa sosai yace "Great One Ozo tuba nake, tuba nake, inada dalilin kawoshi amma saika bani izini zan fadi" rike Abie Aadil yayi gam kanshi na juyawa idanunshi arufe, cikin murya mai kama data jarirai Ozo yace "fadi" ajiyan zuciya Abie yasauke yana addu'a Allah ya daurashi akan Ozo wanan karan kaman koda yaushe, ahankali cikin natsuwa yace "OZO na, Ozo mu, Ozo na kowa mai bamu kudade, Ozo mai bamu fame, Ozo the great one, zuciyata ta gaza natsuwa, zuciyata na cike da tsoron azaban ka dakuma hukuncinka, banzo koda da wasa nakara karyama doka ba dan banmanta abinda kaceba inhar na kara saba doka ban kiyaye sharadi ba bloodline must go dole saikunsha jini, saisa na shiryoshi takanas takano Ozo the great nazoma dashi, sonake ka shafemai gaba, sonake ka sideta ka shafeta tass ta yanda ko sha'awa bazaimaji ba balle harta mike yay kokarin saduwan, Ozo gashinan so nake ka shafeta dan kamashi nayi yana shirin saduwa da makirar yarinyar da aka auramai, Ozo inada matsalan jaraba kuma ina kyautata zaton yagado ni dan Aadil baisan komiba amma yana kebewa da mace gabanshi tafara mikewa, Ozo ka taimakamin nasan am asking too much nasan kuma you've always been granting my requests, Ozo kamin afuwa kataimaka min ka shafemin gabanshi ko hankalina ya kwanta nasan koshekara miliyan zaiyi da ita bazai taba karya dokaba dan baida gaban dazaiyi saduwan dashi, shikenan barata Ozo the the great" shiru dakin akayi kaman ba'ayi hallita awurin ba members duk kansu akasa ana jira aji abinda OZo zaiyi dan sosai sukejin haushin Abie, su Ozo baya daga musu kafa haka basu isa su karya dokaba sai Tursoso, babu dokan da Tursoso bai karyaba, duk ansha jinin yaransu na fari amma banda na Tursoso, wani irin tsawa Ozo yayi da saida dakin ya girgiza. "Tursoso!" zabura Abie yayi yamike tsaye Aadil kuma yasaki fitsari ya kankame Abie yana kuka. "Abie my Hamida" tureshi Abie yayi yana kallon Ozo, cikin fushi Ozo yace "Tursoso kan wanan yaron ne kaketa sabamin doka tun randa ka haifeshi ko, toyau zan zuke jininshi agabanka yamutu" ihu Abie yayi ya rungume Aadil tareda sakeyin kneeling cikin wani irin masifaffen tashin hankali yace "Ozo kayakuri natuba, natuba karka kashemin shi, to naji, naji basai ka shafe gaban nashiba, koda kashe yarinyar zanyi dandai nahanashi saduwa da ita zanyi Ozo the great kagafarceni karka tabamini Aadil dina Ozo" yanda yahaukace yana rokan Ozo yasa Ozo ya gyara zama yanamai wani irin kallon tsana yace "ina zobenka Tursoso?" da sauri Abie ya kalli yatsunshi ganin babu zoben dakemai aman kudi yasa yarude tsoro yamugun kamashi yace "Ozo, Ozo" yama rasa maizaice dan baisan inda ya jefar da zoben ba baitaba cire zoben daga yatsunshi ba koda da wasa cikin inda inda yace "Ozo hala nabarshi abayi danaje wanka ne amin afuwa" wani kallo Ozo yasake mai kafin cikin kakkausar murya yakira sunanshi azafafe. "Tursoso!" da sauri Abie yace "na'am Ozo da great one" "yarinyar nan tadamemu, tahanamu sukuni, tun jiya da daddare take konamu, kaje kafitar da ita daga gidan nan kanajina, kafitar da ita daga gidan nan da daddaren nan, i repeat kafitar da ita daga gidan nan inka sabamin zaka hadu da fushina dabaka taba ganin irinshi ba" cikin tsoro da fargaba Abie yace "to Ozo" wani jini Ozo ya mikomai a kwarya yace "ga sacrifice dinka jinin first born da ifufuwa" tashi yayi ya duka gaban Ozo ya karbi kwaryan yakafa abaki ya shanye jinin tass sanan ya ijiye kwaryan gaban wani gunki, Ozo yace "dau dandanka kuwuce kutafi kufitar da yarinyar nan daga gidan nan now, now, nowwwwww" yana fadin haka Ozo yabace daga dakin sauran yan dakinma haka, uniform din Abie ya chanza ya kashe candles din sanan yabude kofan yafita baima tsaya kulle kofan ba yanda Ozo yamai warning haka yasan abinda Hamidan tayi babba ne yafita da sauri yana rikeda Aadil da har lokacin idanunshi ke akulle mota yabude yasashi bude ido yayi sanan yasaki kuka sosai Abie baibi taka shi ba dan tashin hankalin dayake ciki yafi karfinshi ya shiga gaban mota yatada motar yaja dawani irin fitinannen gudu yabar wajen........






Sai bayan ta idar da isha sanan tai shafa'i da wuturi ta tashi daga kan dadduma ta linke ta tube kayan jikinta ta linkesu dan basuyi dattiba ta maida wardrobe taciro rigan baccin dazata saka ta ijiye akan gadon tana tunanin Aadil, bathroom tabude ta shiga ahankali tana share kwallan daya zubomata, brush tafarayi  sanan taja shower cap tasaka sanan tafara wanka da ruwan zafi sosau, tadan dade tana wankan sanan tafito tadau towel pink tadaura daya kusan kaimata guwiwa ta daura ta zare shower cap din daga kanta ta ijiye tana kallon fuskarta, share hawayen dasuka zubomata tayi danko kadan jitakeyi bataso tafita daga bathroom din batare dataga Aadil ba azaune kan gado yana washe mata baki ba, lallasan kanta tayi kafin tajuya tana tafiya kaman wacce kwai yafashewa aciki ta murda door handle tabude kofa tafito daga bathroom din tai gaban mirror ta tsaya tana tsane fuskarta da towel din, karan dataji na faduwan abu kwan yasa ta juya ta kalli kasa dan tasan bata taba komiba tome yafadi, zoben dazu tagani akasan dakin harzata dauke kai saitaga kaman zoben yakara girma fiye da dazu da sauri tasake kallon zoben tana ware manyan idanunta, gani tayi zoben yay girma kaman anhuramai iska da sauri ta dafe kirji tace "innalillahi wa innailaihi raji'un" kaman daga sama taga kwalliyan dake gaban zoben yakara girma saitaga ya dare yarabe biyu yabude baki yay katoo sosai, wani karamin paper tagani yafito daga bakin zoben yafadi akasan dakin saitaga paper yay wani irin girma shima taga yakoma kudi dubu daya sabuwa dal, wani irin faduwa gabanta yayi jikinta yafara rawa bakinta yafara rawa tana kokarin furta addu'a takasa, gani tayi bakin zoben yafara fiffito da kananun papers din dayawa suna zuba akasan dakin suna komawa yan 1, 1k note sababbi dal dal, wani irin ihu tabuga afirgice. "Mamaaaa!" tai wurin kofa da mugun gudu tabude kofan tafita kaman wacce ta zare tana ihu. "Mamaaa, Mamaa" ta kwalama Maman su kira ta kwasa da mugun gudu tai hanyar gate ta runtse idanunta gam dan zoben take gani a idanunta yana aman kudi zoben aljanu, bude gate tayi tafita dawani irin azababben gudu daidai kan wata mota Lexus ta danno yana shirin horn azo abudemai gate, ganin fuskar dabazai taba mantawa ba ko amafarki daure da towel kafafunta ba takalmi idanunta akulle dan gaban gidansu akwai manya manyan Street light bauuu sun haska ko ina yasa da sauri ya kashe motar yabude door yafito yana gyara zaman suit din jikinshi bude kofar gate dinsu yayi ganin babu kowa a compound yasa yawaiga da sauri ganin tana gudu yasa da sauri yabi bayanta, daidai tana shirin shiga titi yawani irin fizgo hanunta tadawo baya yariketa gam yana binta da kallo ganin idanunta a rufe ruf jikinta nawani irin rawa. "Mama Mama, Mamaaaaa! " tasake kwalama mamansu kira yasa ya jijjigata tareda kiran sunanta. "Amatullah" ko kadan kwanyanta baya aiki a lokacin sai kiran Mama Mama mama take ta datse idanunta gam, da hannu daya yarike ta yacire black jacket din jikinshi dake kamshi sosai ya daura mata akan kafadarta ya jijjigata tareda kiran sunanta. "Amatullah look, look, hey relax is me, open your eyes menene?" jin murya kaman ta Aadil sama sama yasa ahankali tabude idanunta dasuka kankance jikinta na rawa, Sanye yake da farin long-sleeve shirt wuyanshi daure da nicktie gashin kanshi a kwance yay wani irin mugun kyau yana rike da ita gam gam yana kallonta ganin ba lafiya tattare da ita, fashewa tayi da kuka sosai tafada jikinshi ta rungumeshi tace "My Aadil you are back" cirota yayi daga jikinshi da sauri fuskarshi adaure yace "where are you running off to daure da towel batakalmi ba hula are you okay" rikeshi tayi gam jikinta ya dauki ruwa tana kokarin sake shigewa jikinshi yahanata tace "som....something in...a..dakin" luuuu tayi baya zata sume da sauri yariketa ya dauketa yay hanyar gida da ita, bude gate yayi mai gadi yafito mugun kallo ya watsamai yace "bakasan aikin kabako how can be our security idan baka taking note of who goes in and out of this house eh? Anyway banda time dinka call Mami for me kace ta taho da Dr" yay hanyar shashin su Hamida dauke da Hamidan, bude kofar dakin yayi wani hadadden kamshin turaren wuta yadaki hancinshi kwantar da ita yayi akan kujera yatashi yay hanyar dining dan daukan bottle water dayagani daidai lokacin Mami da big Mum dasu Baffa da Suleman suka shigo dan duk suna tare ana maganan Abie inda yakai Aadil Mai gadi yace suzo Hamida ba lafiya, da sauri Mami takaraso ciki da gudu tana kallon fuskar Hamidan tace "maiya sameta Aabid? Kafafunta butu butu haka, wat happen son?" bude bottle water yayi yace "i don't know Mami dawowa na kenan naga tafito daga gate da gudu ahaka idanunta akulle i was trying to talk to her kuma saitai passing out" karban ruwan Mami tayi da sauri tana surutai. "na shiga uku wai meke faruwa ne ni Maryama" shafa ruwan tayi a fuskarta wani irin ajiyan zuciya Hamida tayi tabude ido tana kallon duka dakin, ahankali Mami tace "Hamida na kinajina?" kallon Mami tayi saikuma tajuya tana kallon duka yan dakin kafin idanunta ya sauka kan Aabid dayay folding hand akirji yana kallonta tashi tayi azubure tafashe da kuka tafada jikin Aabid tace "take me out of this place kaji My Aadil akwai wani abu adakin chan, akwai wani abu yanata girma am scared ka kaini wurin Mama dam Allah ku kaini wurim Maman mu da Kaka" takire Aabid gam, da sauri Suleman yace "to kodai tanada aljanu ne? " komawa bayan Aabid tayi tarikeshi gamgam jikinta narawa tace "abun na dakina chan bedroom pls take me out of here, zai fito yakamani i carried it dazu" tafashe da kuka sosai da sauri Mami ta tashi zatai magana Baffa yadaga mata hannu bayan yagama nazarin Hamidan yace "kubarta yarinya mai natsuwa haka dole akwai abinda ya firgitata bakuga bata hayyacinta ba, Sulemanu kumuje muduba dakin mugani" da sauri Suleman yace "to Baba" big Mum tace "ku dauko adduna incase maciji ne ko kunama" hararanta Baffa yayi yace "babu reptiles agidan nan ana fumigation ai" sukai hanyar dakin harda su Mami Aabid zai bisu tasake fashewa da kuka tana rikeshi tace "don't leave me kaji Aadil" juyowa yayi ya kalleta kafin ya dauke kai ganin she's not okay, ihun su Big Mum dayaji dakuma salatin su Baffa kowa nakiran sunayen Allah yasa da sauri yay hanyar bedroom din yana rike da hanun Hamidan gudun karta kara fita, kutasawa yayi ta tsakakanan su Big Mum dayaga jukunansu narawa duk suna kallon dakin ya kutsa kai ya shiga dakin, chak ya tsaya kyam jinin jikinshi ya tsaya kyam, ganin abinda tunda yake aduniya baitaba ganiba, wani katoton huge zobe yagani akasan dakin yana aman kudi yan dubu daidai sababbin kudi nafita daga bakin zoben, kudin sun cika kasan dakin har wasu sun soma hawa kan gadon sunyi himm, daidainan Abie ya buga kofan falo ya shigo dakin rai abace Aadil biye dashi.


_hello lovelies, due to high demand na next page am introducing VIP readers, in bakison suspense kinason kiji next page always koda yaushe all you need to do is subscribe for VIP and be my VIP readers, for those interested all you need to do is pay 1k, for more enquiry 07012181461, chat me up and know more. I love you 😘_

51.....






_karki karanta in baki biyaba in kika karanta ina binki bashi pay anan or pay achan_


_Zaki tura 300 kota card kota bank sai nai adding dinki a group din danake posting, 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461, you can also send MTN card to watsapp number na 07012181461_



_masu fitarmin da book kuda Allah_


 Hanyar bedroom Abie  yayi ganin babu kowa afalon straight cikin fushi yana daga murya yace "ina take zoki barmin gidana, mai bakin jini, mai kashin tsiya daga auroki kindawo mana bala'i" Hamida dake baki bakin kofar bedroom dinne tafara juyowa jin hayaniya da sahun tafiyan mutane, tana ganin Abie tareda Aadil daya fara tsalle zaiyo kanta gabanta yawani irin mummunan fadi sabida wani mugun kallo da Abie yake mata kaman zai chaka mata wuka, batasan lokacin data rike hanun mutum din dataji kusada itaba, hanun big Mum takama tarike gam da

sauri big Mum ta juyo jin anrike mata hannu ganin Abie da Aadil da yarike gama yasa tace "Baban yan biyu yauwa zokaga ikon Allah" daidai lokacin Baffa daya gama kiran liman din masallaci dan d whole scene looks spiritual da jinnish ya kalli Suleman da Muhammadu dasuke kafe a tsaye suna ganin abinda basu tabaganiba aduniya yace "kuje ku shigo da liman koma menene wanan abin ayar Allah yau zata kona manashi" da sauri suka jujjuya suka fita daga dakin ganin Abie a corridor rike da Aadil dayake kokarin fizge kanshi yana kuka yasa sukace "jeka gani kaima Abdullahi, abin mamaki" matsawa Mami databi Abie da kallo asanyaye tayi ganin yafara tafiya big Mum ma ta matsamai suka bashi wuri abakin kofan, sakin hanun Aadil yayi ganin yakaraso kuda da Mami da wani irin gudu Aadil yay wani irin tsalle ya rungume Hamida data makale ajikin big mum yace "oyoyo My Hamida" fashewa da kuka tayi sosai ajikinshi ta kankameshi tama kasa magana but she just miss him, jin muryan Aadil yasa Aabid yajuyo da sauri hada ido sukayi da Aadil daya rungume Hamida yana mata kuka ahankali itama tana kuka, ganin Aabid acikin daki yasa yasaki Hamida da sauri yawani irin ware manyan idanunshi yace "Bid" wani irin tsalle yayi ya shigo dakin batare daya lura da komiba yay wani irin jumping ya rungume Aabid kaman zai kadashi yace "oyoyo Bid" kyam idanunshi suka sauka akan ring din dake aman kudin har lokacin daidai lokacin Abie shima ya shigo cikin dakin, yanda gabanshi yafadi saida dan gajeren fitsari yazubomai daga wando yana tuna warning din OZo aranan da akabashi zoben kudin nan. "koda wasa karka bari zoben nan yay aman kudi agaban idanun wayanda basu taba shan jini ba, danka na zoben nan, karka bari zoben nan yay amai agaban mutanen daba yan gidaba, ka kiyaye, ka kiyaye idanu mashan jini ne kadai aka yarda su kalli zoben nan alokacin dayake baka kudi, idanun masu tsarki wanda suke gauraye da jini kadai sukeda ikon ganin lokacin aman kudin zoben nan, kariga kasan ranan dayake aman kudi sanan kariga kasan lokacin dazaima aman kudi ka kiyaye Tursoso, kakiyayeee".



Wani irin race da zuciyarshi Abie yafara yasa yaji saliva bakinshi ya bushe gabaki daya zaiyi magana, yana kokarin magana amma maganan taki fitowa sai iska yake fita. "ahhh, huuuu".... 



Ahankali Aadil yasaki Aabid yamike tsaye kanshi narawa sosai miyau nazuba daga bakinshi, kafe zoben Aadil yayi da ido yana kallon kullutun jikin zoben yaga yakawo wuta a jan wuta a idanunshi, kanshi yagani ajikin kullutun amma dan karamin shi, yana cikin keji an rufe, ganin Aadil karami yayi yarike karfen kejin yana girgizawa yana mai magana directly. "free me, free me kafin yagama aman nan, ninekai dasuka shanye, nine brain dinka dasuka shanye, free meee nowww, yakusa gamawa" wani irin juyawa idanun Aadil sukayi sama gabaki daya kafafunshi su lankwashe, duk dakin babu wanda ya lura dashi asandare yay baya ya zube akasa gabaki daya asume akan kudaden, ihu Hamida tayi ta shigo dakin da gudu kafin ta iso Aabid ya dagashi afirgice ya rungume kanshi a kirjinshi Mami ma ta shigo daidai nan su Muhammad suka shigo da limam dawasu malamai guda biyu alarammomi, dago kai Aabid yayi ya kalli Hamida data tsaya gefe takasa zuwa kusada shi tafashe da kuka sosai tana kallon Aadil datake so ta taba amma takasa sabida yanda Aabid yarikeshi, kallan Mami Aabid yayi yace "Mami take her to your room ta nemi hijabi tasaka please" tashi Mami tayi takama hanunta suka fita daga dakin Mami ta karbo mata hijabi

.





_karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan_



_this book is for sale, just 300 naira zaki turo ta 3107021073 first bank aisha Muhammad, idan baki da account u can send MTN card, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_





Shiga malaman sukayi suna kallon abinda ke faruwa da karfi liman din ganin yanda baban zobe ke fitar da kudi yafara karanto addu'a. "Bismillahil lazi la yadurru ma' ismihi shai'un fil-ardi wa-laa fil-samaa'i wa huwas Samee'ul Aleem" yakaranto addu'an yana tsugunnawa yakai hanunshi kan saman idanun Aadil dake hanun Aabid yabude idanun yana ganin yanda idanunshi suka juya sama baka ganin bakin ko kadan, jinin jikinshi yasha batare dayay magana ba ya kalli sauran malaman dake tareda shi, hakan yasa daya daga cikinsu yakalli baffa yace "muna bukatan ruwa a gora Alhaji danka kodai aljanu sun shafeshi kokuma da sihiri ajikinshi" gyara zama limam yayi yana kallon zoben dayake fitar da kudi har lokacin yafara karatun al Qur'ani, sauran malaman suka zauna kusa dashi suka jonashi suna karantowa atare da karfi sosai kaman zasu fasa dakin da zakin murya, wani irin girma zoben yakarayi kaman an huramai iska, Suleman Big Mum tarike gam dan wani irin tsoro taji tanaji kowani mutum na dakin tambayoyine fal aransu daga ina zoben nan yake? Daga ina tayaya yazo dakin nan?



Abie ko kyafta ido bayayi yay kokarin dazaiyi yay magana yakasa kaman wanda aka dinkemai baki yana kallon yanda zoben ke kumbura yana kumbura yana kumbura.

Ayoyi daban daban suke karantawa suna fuskantar zoben wani irin girgiza zoben yafara yana rawa rawa kaman abinda ke shirin fashewa kafin tuss yawani irin fashe ya tarwatse, kumfane yafara fita daga bakin Aadil jikinshi na girgiza kaman mai ciwon farfadiya yana mikewa yana bankarewa da sauri Aabid dake rike yana neman fizgemai yace "innalillah, Malam my brother meke faruwa dashi" cigaba da karatu malam yayi batare daya amsa Aadil ba, wani irin girgiza dakin yafara kaman saukan aradu hakan yasa malaman suka kara karfin karatu suna kiran Allah, rike Baffa Muhammad yayi gam yayi dakin na kara yana making sound kaman sound din guguwa, wutan dakinne sukai kara suka fashe tareda tarwatse wa dakin yay duhu dumdun abunku dadama darene kara karfi karatu malaman sukayi Aabid ya rungume Aadil da jikinshi ke rawa sosai har lokacin miyau nafita daga bakinshi yana zuba awuyanshi.




Wani irin bulluwo Ozo yayi da kwarangwal dinshi jikinsu na hayaki sosai ta bango, magana sukaji kaman daga sama maikama da murya irin ta abumai tsoratarwa. "Tursoso kanagani ana konamu kai shiru bakace komiba, Tursosooo!" yakira sunan Abie cikin wani irin fushi tone, tundaga silin gashin Abie nakai har zuwa karkashin tafin kafarshi rawa yake jin muryan Ozo, cikin wani irin yanayi na daburcewa da rashin sanin mai yake fadi yace "O...Ozo the g..great bansan cewa anan nabar zobena ba hala danazo inajan Aadil ne yana fada dani shine zoben yafita daga hannuna, Ozo dan Allah karafumin asiri kayakuri" Abie yakarashe maganan cikin tone din kuka, waya Baffa yaciro tsabagen son ya gasgasata me kunnuwanshi suka gama jiyemai ya kunna flash kaman dukansu sun hada bakine gabaki dayansu harda Aabid wayoyinsu atare suka ciro suka kunna flash light dakin yay haske bauu duk suna kallon Abie da idanunshi yay kuri alamun mara gaskiya sunyi jajir kirjinshi nawani irin bugawa gabaki daya yay wani iri yana kallon Ozo da kwarangwal dinshi dake jikin bangon dakin jikinsu na hayaki while malaman na karatun su har lokacin batare dasun yankeba, wani irin kara Ozo yayi ya buga karfen hanunshi sabida konewan dayakeyi yace "bazaka hanasu konamu ba Tursoso" da sauri Abie kaman mahaukaci ya tsugunna yanajan gwuiwa  ya zagayo tagaban malaman yace "kuwa Allah, kuwa Allah nace baniba kudena karatun nan zan fadi muku komi, kunga ran Ozo the great yariga yabaci, inhar kuka konashi kashe Aadil zaiyi, wlh, wlh, billahillazi la'ilaha illahuwa kuruwan Aadil na tareda shi, kai rayuwan Aadil gabaki dayanta ma yana wurinshi, shine ya shanye rayuwan Aadil ya shafemai kwakwalwa, shine ya zamad da Aadil abinan dakuke gani, inhar baku denaba mutuwa zaiyi, zuge jinin Aadil zaiyi tass" babu wanda bai girgiza ba dajin kalaman Abie ba, shiko Abie ko kadan bai damuda wanan ba yasan dukansu babu abinda suka isa sumai, yanada kudin da zai iya kullesu dukansu, yanada kudin dazai iya batar dasu aduniyan nan gabaki daya anemesu arasa, sanan yanada kudin da zaije daganan harbangon duniya inyanaso yaje just to free his self daga shame and talk of the town. Wani jarababben tsawa Ozo yadakamai karfen hanunshi yay haske yace "bazaka hanasu ba Tursoso" da sauri Abie yasa hannayenshi ya rufe bakin limam kaman zaiyi kuka yace  "kudena konamin Ozo, Ozo ne rayuwata, shine gatana, yabani abinda wanan mutumin marikina bai baniba dudda uwarshi tacemai yasoni sama da yaran daya haifa amma tana mutuwa ya manta da batun, Ozo ya soni ya fifitani akan duka members yan cult, shiko wanan tsohon yaranshi yafiso, suya sani baniba, dudda nafi yaranshi ilimi nafisu iya aiki, nafisu kaifin basira kullum ninake samamai customers da ciniki a kampani amma daya tashi raba motoci bai baniba yabama yaranshi, Ozo shiya bani kudi saisama har yarshi ta yarda zata aureni da bata aureniba ai, sanan Ozo ya zamaddani popular yabani fame akasanni globally aduka kasashen duniya, nazama babban mutum, kuduba fa duka abubuwan nan dayamin abu daya kawai ya nema awurina shine jinin dan farina, amma dana haifi Aadil nakasa badawa, nama Ozo daya sharemin hawaye butulci sabida yanda nake son Aadil, gadai yaron imbecile amma shine rayuwata duka, Allah ya jarabeni da masifaffen son Aadil, na roki alfarma Ozo yamin da sharadin duk cikin da Maryama zata kara samu tun kafin ahaifa zasu shanye duka, barin Maryama sau uku ba bari bane Ozo nabama yaran nawa tun suna cikin cikin uwarsu, dan Ozo ya chanchanci abinda yafi haka agareni ma, yamin komi a duniya, yaban duk abinda nabukata, inhar kundena konamin Ozo na zan baku ganamasgo manya manya na dollars guda dari uku na rantse da zatin Allah" yafada ahaukace, kabar da hanunshi limam yayi yacigaba da karatun da karfi dan maganganun Abie kara musu karfin guwiwa yin karatun more and more yayi, dole yau su babbaka matsafan nan da ayoyin Allah, su kawo karshen su sanan su kubutar da Aadil, wani irin haske karfen Ozo yafara ran Ozo amasifar bace, kwarangwal dinshi tafara rawa tana narkewa kafafunta sun narke suna diddiga kaman roba da akai melting da wuta, wani irin girgiza karfen Ozo yayi yana nishi yana kallon Aadil da Aabid da gudu Abie kaman zarare ya tube riga yay wani irin tsalle ya tare Aadil da Aabid ya karesu yace "dont kill my children Ozo, na rokeka idan akwai any atom of son dakake min aranka karka kashemin yaran nan, amma nabaka izini ka kashe kowane ne agidanan, kama kashesu gabaki daya banda asara, they're all bloodline but don't touch my children please Ozo, Ozo karka kashemin boys dina, Aadil baisan dadin asalin duniya ba, na tauyemai 30yrs of fresh life, kabarmin shi har lokacin da Allah ya kindayamai aduniya su cika karka kashemin Aadil Ozo na rokeka" wani irin hayaki ne ke fitowa daga bakin Ozo idanunshi na fitar da bakin ruwa, karfenshi na wuta sosai yana hayaki, ganin haka yasa Abie ya warware mazariyan wandonshi yace "Ozo kawa Allah karka kashemin yara, kai nace karka tabamin yarana fa, bakajina ne? Karka tabamin yara, Aadil zuciyata ne, karka tabamin yan biyuna, zanyi tsirara agaban duka duniya inhar bazaka kashemin yarana ba, karka tabamin yan biyuna Ozo" kana ganin Abie kasan ya haukace bil hakki dan maganganun dayakeyi basuda kan gado, daidai lokacin Hamida ta shigo dakin da gudu sanye da dogon hijabin Mami hankalinta atashe tana kallon fuskar Aadil dahar lokacin ke kulle bakinshi na fitar da yellowish kumfa tareda hancishi, mugun rudewa tayi batare data lura dasu Ozo ba tai wajen Aabid dake rungume da Aadil da mugun gudu tana kallon fuskar Aadil din ganin kaman yamutu daidai lokacin Ozo yasaki wutan tsafin karfenshi direct sai wutan tsafi yay saitin cikin Hamida ya shige, tsayawa Hamida tayi chak daidai ta karaso kusada Aabid ta mika hannu tana shirin taba kan Aadil dake kan kafadar Aabid ta zaro idanunta gabaki daya tareda daura hanunta akan cikinta tawani irin ja numfashi. "uhhh ahhhhh" sakin Aadil Aabid yayi yawani irin tashi da mugun sauri yatarota yakira sunanta cikin zafin rai. "Hamida!" lumshe ido tayi tabudesu ahankali ta kallai wasu irin hawaye masu dumi na fitowa ta gefen idanunta kafin ahankali wani irin jini with force yagangaro yana bulbulowa ta hancinta da gefen bakinta tai luuuuu hanunta na lilo akasa, riketa gam Aabid yayi zuciyarshi nawani irin bugawa dabai taba yiba in his life yace "ke Amatullah where do you think you are going? Stay with me, i said stay with me okay me and my brother, Aadil needs you, and...and...I..I need you too Amatullah" yay maganan yana jijiga fuskarta hakan yasa kanta yay luu ya kife akan kirjinshi ba alamun numfashi ko kadan atattare da ita wani irin ihu Aabid yayi da mugun karfi. "Nooooooooo! Jewel Noooo!" wani irin tsalle Abie yayi yana sosa kunne yatube boxer din jikinshi yace "yesssss, Ozona you spare my children once again Ozo" kara karfin karatu malaman sukayi trying to handle one situation at a time shine Ozo, hakan yasa jikin Ozo yakama da wuta sosai yana narkewa, ihu Abie yayi yace "noooo Ozo, na shiga uku" yarike kashiyarshi yasaki fitsari yana dariya yace "bari nakashe wutan da fitsari na Ozo na, yauwa kagani, kagani, kagani fitsarina dayawa karka damu saina rama maka zan dauresu, zanyi amfani da kudina na batar dasu a duniya, saimun sha jinin yaransu harda na jikokin su" kara karfin karatun sukayi hakan yasa sosai Ozo keci da wuta yana narkewa kaman dalma yana diddiga hakan yasa kudaden wurin ma suka shiga ci da wuta, alamu Malam yamusu dasu fice daga dakin, Suleman da Muhammad sukadau Aadil dake kwance flat akasa, Aabid narike da Hamida suka fice malaman kuma suka tsaya abakin kofa suna karatun sosai, Abie na ihu batare daya bar wurin wutanba yace "kubar konamin Ozo na, Ozo zan mutu taredakai yau zan mutu taredakai yau" dakin yakama da wuta sosai sukaji Abie yafara ihu kafin yafito daga dakin da sauri yana sossosa jiki yana zaro ido yana dariya, tashin hankali shine abinda idanuwansu yagane musu dis night, wanan abin shine definition of tashin hankali.




Jin yanda jikin Hamida yay sanyi ahanun Aabid yasa hawaye ya gangaro daga idanunshi da sauri yay hanyar fita da ita su Suleman da Muhammad dake rike da Aadil biye dasu, Baffa da Big Mum suka rike Big Mum dake wani irin kuka kaman zata shide dan gabaki daya taji bayanin Abie, har sunkai falo tasake fizge hanunta cikin kuka sosai daga na Big Mum takoma Corridor inda Abie ke tsaye yana kallon malaman dake karatu har lokacin yana sosa jikinshi, wani irin mari Mami ta daukeshi dashi cikin kuka tace "ka cuceni, ka cuceni, ka cuceni Abdullahi, ka cuci danmu, ka kashemin yara har uku,  yaran da Allah yabani akan son duniya, Allah ya isa tsakanina dakai, all dis while dakai muke wahalan Aadil kaishi asibitici gari gari, daban daban, ashe harda sa hanunka, kawai kallona kake kasan bazai taba warkewaba, Abdullahi, Abdullahi i will never forgive you, all pains din wankin ciki da azaban daduk nasha a wuraren barin yara ukun nan are still fresh a heart dina ashe u were behind it banyafema ba wlh, banyafema ba" tarufe Abie da duka sosai yana mata dariya. "hahahhahah, kekekekee, kyalkyalkyal kyal" fizgota Big Mum tayi tace "let it goo is too late gashinan Allah yafara nunamai ai tajata suka fita daga dakin, sukai tsakar gida, sosai wuta ya shiga ci adakin yana fitowa falo hakan yasa malaman suka fito shashin da sauri daidai Abie yafito  yana tsalle ginin part din yawani irin rushe sukayi ginin ya zubo kanshi agabansu kan Abie ya tarwatse Aabid ya runtse ido da karfi hawaye masu mugun zafi suna fitowa daga idanunshi.

...







Ahankali take bude idanunta dasuka mata nauyi sosai jikinta ko kadan ba karfi gabobin jikinta sun mata tsami sosai, bude idanun tayi gabaki daya ta daura shanyayyun idanunta akan makeken agogon bangon, tana fitar da numfashi ahankali ahankali da baki bata feeling jikinta ko kadan, motsin da kunnuwanta sukaji yasa tajuyo da kanta ahankali, sauka idanunta sukayi akan fuskar Aadil dake kwance agadon dake dayan bangaren dakin akwai dan gab a tsakanin su, motsi yake sosai batare daya bude idoba sai motsi dayakeyi idanunshi na rawa suna shirin su bude, lumshe idanunta tayi asanyaye takara budesu ahankali tasauke su akan fuskarshi, wani irin sanyi taji ajikinta bana wasaba, ahankali ta matsar da hanunta da kyar zuwa baki bakin gadon datake kai tai pointing Aadil din da hanunta tana lumshe ido batare datai koda kwakkwaran motsi ba, bude ido Aadil yayi gabaki daya yana kallon dakin yanabin ko ina da kallo, yakai kusan minti biyar ahaka kaman mai nazarin wani abu kafin ahankali yatashi ya zauna yana kallon drip din da ake karamai yadan yatsine fuska sabida ciwo da jikinshi kemai sosai yana shafa hanun nashi dan wurin karin ruwan namai zafi sosai, lumshe ido tasakeyi ahankali tanajin wani irin murna har cikin ranta ganinshi atare da ita dat means he's fine bai mutu ya barta ba, bude bakinta dayamata nauyi sosai tayi zatai magana wani atishawa mai karfi yazo mata tayi, da sauri ya waigo ya kalli bayanshi jin karan atishawa tsayawa yayi chak batare dayace komiba yakafeta da ido, wata yarinya yagani fara sosai kan gadon, tana sanye da wani pink rigan asibitin akwai bandeji biyu a jaws dinta tana kwance gashin kanta ya barbarzu kaman na yar buzuwa ta kafeshi da ido kaman mayyar dataga yaron dazata lashe, murmushi tasankin mai daya bayyanar da cute dimples dinta ganin ya ganta yajuyo yana kallonta, yatsine fuska yayi akasalance ya dauke kai ganin yarinyar tanamai murmushi tana wani irin kallonshi kaman zata hadiyeshi daidai lokacin aka bude kofar dakin za'a shigo, atare dukansu sukabi kofar da kallo, Big Mum ce ta shigo dakin tareda Baba Suleman suna hira batare da sunma lura dasuba. "eh saida na tabbatar tasha maganin Yaya sanan nafito, saida nahada da yimata alkawari zan kirata a video call taga fuskokin su sanan ta yard...." shiru tayi batare data karasa maganan ba ganin Aadil zaune abakin gado ya kafesu da ido yana kallonsu, dukansu kamewa sukayi tsaye suna kallon Aadil din daya kafesu da ido bayako kyaftawa, da wani irin sauri Big Mum tai wurin gadon ta zauna kusa dashi cikin murna tadaura hanunta akan fuskarshi tana shafawa tace "Aadil, Boy katashi, yaushe katashi ya jikin?" hanunshi ya daura akan nata dake kan fuskarshi yadan lumshe ido ya bude ahankali kafin cikin wani cool calm voice yace "Big Mum ina Mami na? Ina Bid?" chak daga Big Mum har Baba Suleman suka tsaya suna kallonshi ganin for the first time in life sunga Aadil yay magana batareda kanshi yay rawa ba batare da miyau ya zuba daga bakinshi ba and magana ba childish magana daya sabayi ba yana turo baki a shagwabe yana fari da ido yana lankwasa kai yana make kafada, tashi Big Mum tayi tafada kasa cikin so much happiness tai sujjada kafin ta tashi tafashe da kuka sosai tana kallon Aadil din dake binta da kallo, kawai takasa holding tears nata back ne, sake zama tayi ta matso kusada Aadil din sosai taima fuskarshi kyakkyawar cupping tace "Aadil, Aadil am I dreaming kaine Aadil, Aadil u are fine kaji sauki wayyo Allah na Yaya am so happy today, kalli Aadil dinmu fa, Alhamdulillah, ya rabb i can't wait to tell kanwata this good news dasu Baffa" tai maganan tana wani irin rungume Aadil dayay shiru yana kallonta kaman mai tunani yanason gano wani abu, karasowa cikin dakin Baba Suleman yayi ya zauna adayan gefen side din Aadil din yana kallon Aadil din today is such a good day hanun Aadil din yakama yarike, hakan yasa Big Mum tace "kagane shi Aadil?" juyodakai yayi ya saukar da manyan eyes dinshi akan fuskar Baba Suleman din ya kafeshi da manyan milky eyes dinshi yana kallo ahankali yace "Uncle" wani irin ihun dadi Big Mum tasakeyi tana goge hawayen datakeyi nonstop tana kokarin ciro wayarta daga jaka da sauri Baba Suleman ya fizge wayan yace "babu wanda zaki fadamawa saidai su ganmu mun da Aadil din kawai, lemme go an call Dr yazo yaduba shi" tashi yayi daga kan gadon  daidai zai juya yay wurin kofa idanunshi suka sauka akan Hamida dayagani idanunta biyu tana kallonsu hawaye nafita daga gefen idanunta tana kallonsu da sauri Baba Suleman yace "H...Hamida" yay maganan yana karasawa wurin gadon cikin tsananin farin ciki da sauri Big Mum ta mike tsaye jin sunan da Baba Suleman yakira, karawasa gaban gadon Baba Suleman yayi ya tsaya yana kallon Hamidan ahankali yace "Hamida kin farka?" kafin ma tabada amsa big mum takaraso wajen tana Share kwalla tace "daughter na, Hamida na kintashi" da kyar Hamida ta iya ta gyadamata kai sabida bones dinta dake mata ciwo sosai daidai lokacin Aadil yamike tsaye ahankali yana yatsine fuska ya cizge karin ruwan dake hanunshi ya yar, singlet da 3quater dayagani kan gadon ya dauka yadaga kafa ahankali yay hanyar kofar dakin dayagani wanda ya kyautata zaton na bathroom ne, yanda Hamida tabishi da kallo batare databa Big Mum amsar tambayanta ba yasa Big Mum da Baba Suleman suka juya atare dan suga metake kallo haka, ganin Aadil ne yatashi yana tafiya  yabude bathroom ya shiga yasa big Mum tace "Yaya akira mana Dr yakamata yasan sun farka beside Hamida doesn't look good, meke miki ciwo daughter?" fita Baba Suleman yayi dan zuwa kiran Dr, ahankali batare datai magana ba Hamida ta nuna mata fuskarta da jaws dinta alamun su kemata ciwo, a forehead big Mum tamata peck cikin tsananin son yarinyar tace "don't worry zakiji sauki kinji, Maman ki kullum saita kira taji yaya jikin ki, i know she will be very happy idan taji kin farka" shigowa Baba Suleman yayi tareda Dr da nurses guda biyu, kana ganin su kaga larabawa, da farin ciki gabaki dayansu suka shigo suna tambayan ina Aadil Baba Suleman yace "ya shiga bathroom wanka" Dr ya shiga duba Hamida daidai lokacin Aadil yafito daga bathroom din sanye da white single da 3quater ajikinshi yana tafiya ahankali, tafi duka Dr da nurses din suka fara suna kallonshi suna murna ganin patient dinsu yatashi strong and healthy, dan kallonsu yayi kafin ya dauke kai yakarasa yazauna akan wani plastic chair dan yagaji da kwanciya Hamida tabishi da kallo, so kawai take yamata magana koma ya kalleta amma yaki, saida aka gama dubata sanan Dr yaduba shi, babu wata matsala tattare da shi sai rashin kuzari wanda dazaran yaci abinci zai dawo normal, har Dr zai fita Baba Suleman yace "yaushe za'a sallame mu Dr? Munkosa mutafi gida dasu" dariya Dr yayi yace "i just want to run two scans for Amatullah once d result is clear and fine zanyi discharging naku yau, but before then amata wanka zan turo dietitian yazo yaduba su yafadi abinda zasu iyaci" murmushi Baba Suleman yayi looking satisfy da service dinsu yace "angode Dr" fita Dr yayi nurses biyedashi hakan yasa Big Mum yaye lullubin jikinta ta ijiye akan gadon da jakar hanunta tace "bari naje nahada miki ruwa mai zafi sosai ko kyaji dadin jikinki nazo muje muyi wankan, dan bude ido Aadil yayi kadan ya kallesu kafin yasake lumshe ido abinshi ya kishingida, shiga bathroom Big Mum tayi tahada ruwa sanan ta dawo dakin takama hanun Hamidan tace "yauwa tashi muje daughter na" ahankali Hamidan ta tashi tana yatsine fuska gashin kanta yakara barbajewa ta sauko da fararen kafafunta kasa ta zauna tana runtse ido sabida yanda jikinta ke ciwo bana wasaba kaman Big mum zatai kuka tace "sorry kinji" huta saimu tashi, kai ta gyadama Big Mum tadan saci kallon Aadil dahar lokacin idanushi ke lumshe kaman wanda yay bacci, hanunta da kafadarta bigmum takama tace "yauwa muje" saukowa tayi daga kan gadon ta mike tsaye da kyar jikinta na rawa kaman zata fadi hawaye ya gangaro daga idanunta sai sannu Big Mum take mata takaita gaban bathroom din tabude bathroom din suka shiga, yatsine fuska Aadil yayi dan surutun Mami na damun brain dinshi yabude ido kadan yana kallon kan gadon data tashi daga kai kafin yasake lumshe idon, basu jima da shiga bayin ba Big Mum tafito tabude wardrobe din dakin taciro free plain gown na cotton black mai kama da rigan da sauran abubuwan dasuke bukata da ribbon takoma bayin, sunbata almost 20min sanan suka fito yanzu tafiyarta yadanfi nada dan tanayi ahankali rigan jikinta yamata kyau yakara haskata, big Mum ta zaunar da ita akan gado zama tayi ahankali, daidai lokacin dietitian din ya shigo da abubuwan da zasuci bigmum ta karbi na Hamida Baba Suleman yakarbi na Aadil, sanan Dr yace "Hamida tagama da wuri za'a mata scanning" to Big Mum tace "ta shiga bama Hamida abincin" da kyar ta iya ta karbi abincin tanaci ko kadan batajin dadin komi ganin yanda ko kallonta Aadil bayayi bama ya magana ya lumshe ido kaman mai bacci, tana gamawa nurses suka shigo suka fita da ita dan zuwa scanning big Mum tabisu.





Sai wajen la'asar aka dawo d ita komi is fine babu wani complication, bakaramin dadi su big Mum sukaji ba nan aka basu sallama bayan Baba Suleman yagama clearing komi na bill, big Mum kuma ta shiga hada  kayayyakin su she can't wait to see Mami's face dana Aabid idan sukaga new Aadil not baby Aadil. 




Wuraren biyar da rabi suka gama komi tsaf suka fiffito har haraban asibitin Aadil da Baba Suleman suka shiga gaban mota itakuma da big Mum suna baya, Baba Suleman ya kunna motar yaja suka shiga hanya yace "i can't wait to see yanda su Mami da Aabid zasuyi idan suka ganmu" dan dagokai Hamida tayi ta side glass ta kalli fuskar Aadil taga idanunshi a lumshe suke kaman mai bacci, kuka ne sosai taji yazo mata, she's so longing for his talk, so kawai take yamata magana amma ya share ta, da kyar ta daure ta hana kanta kukan dan bamata da karfin yin kukan tanata kallon garin dasuke dan daga gani tasan ba Nigeria bane dan larabawa take ta gani tako ina, tafiyan kusan 20min sukayi taga Baba Suleman yay parking agaban wani babban gida yace "muna shiga da mota zasu gane kuzo muje" fitowa yayi hakan yasa Aadil yabude kofa shima yafito yakosa yaga  Mami da dan uwanshi, big Mum ma tafito ta taimakama Hamida itama tafito, Baba Suleman yabude gate suka shiga har gaban babban flat dinsu Baba, Suleman ne yajuyo yana zare ido hadaura yatsarahi akan lips dinshi ya kallesu, hanun Aadil yakama ya daura akan na Hamida da sauri Aadil ya yatsine fuska tareda janye hanunshi da sauri yana kallon Baba Suleman irin me haka, ahankali Hamida ta kallai yanda yake yatsine fuska, cikin rage murya batare da yalura damai yafaru ba Baba Suleman yace "kariketa karta fadi kaga batada karfi nida Aisha ne zamu fara shiga ciki kafin ku kubiyomu abaya" yay maganan yana kara daura hanun Aadil akan na Hamida ahankali Hamida ta saukar da kanta kasa dan tana gabda sakin kuka, Baba Suleman da Big Mum suka juya suka bude kofa suka shiga ciki atare, wani irin gajeren wahalallen tsaki Aadil yaja ya saki hanunta da sauri hakan yasa tai baya zata fadi atsorace taidan kara tadafe bango ahankali tana maida ajiyan zuciya, ko kallonta baiyiba yasa hannu yabude kofa ya shiga dakin idanunshi suka hadu dana Mami da Aabid yadebo rice a spoon yana kokarin kaimata baki danko kadan bata iyacin abinci sai an tursasata tarame sosai bana wasaba, Baba Suleman da Big

Mum tsaye agefe suna murmushi sosai suna kallonsu sunyi folding hand akirji, atare Mami da Aabid suka mike tsaye suna kallon Aadil din, wani irin cute adorable smile Aadil yayi yace "Mami na" ya kalli Aabid yace "rascal" sakin plate din abincin Aabid yayi akasa jikinshi yadau wani irin rawa bakinshi har rawa yake yana kallon Aadil din yace "d...Dil"

.. 








 Durkushewa Mami tayi tana kuka kuka kaman zata mutu ganin yanda gini ya ruguzo kan Abie, Baffa duk shine mai dan kwari a cikinsu ya kalli su Suleman da muryanshi data dishashe yace "ku wuce kukai yaran nan asibiti we will take care of the rest anan" juyawa duk sukayi Aabid da kyar ya iya daga kafarshi yay hanyar gate dan motarshi na waje har wani jiri jiri yake gani, bude motar yayi ya kwantar da ita abaya yamaida kofar yarufe ya shiga gaba ya tada motar, su suleman ma suka shiga tasu motar bayan sun kwantar da Aadil abaya sukaja motar sukabar anguwan sukai wani babban private hospital dasu inda da gudu Nurses and Dr suka karbesu sukai placing dinsu on admission, Baba Suleman ne yace "VIP room mukeso asasu" nan aka kwantar dasu awani hadadden daki mai gado biyu Dr suka taru akansu ana kokarin saving their lives, ahankali Aabid yatashi daga jikin kofan inda yake leka yanda Dr's ke battling suna kokarin cetosu ya zauna akan one of the kujera dake corridor da dakinsu yake ya saukar da kanshi kasa yadafe kanshi zuciyarshi na bugawa yanamai zafi, yanamai daci sanan yanamai yaji, for the first time a history din life dinshi yaji ya tsani life dinshi, ya tsani his life he hates who he is, yanzu dama cikin kudin jini Abie ya rainesu? Yasasu makaranta har ya karanci business administration, da blood money ya rayu daman? Thank God yanada aikin kanshi, yanada kampanin kanshi dayay establishing bayan yagama masters dinshi but dudda hakan d thought of yarasu yaci yasha yay karatu da blood money yakasa fita daga ranshi. "Astagafurullah" yafada sounding weak, he promised kanshi daidai da riga daya tak wanda Abie yasaimai shida Brother shi saiya cire ya kona ya zubar, komi na Abie daya saima shida Aadil saiya kona tass.




Dafashi da akayi yasa ya dago kanshi da kyar idanunshi sunyi jajir, Baba Suleman ne ya zauna kusa dashi yana kallonshi cikeda tausayawa yasan this is hard dole abin ya daki zuciyar Aabid da karfi. Murya chan kasa mai cike da calmness nason kwantar ma da yaro hankali yace "let it out Boy, let it out Hussain, Men cry too, am here for you, am here for you kaji" fadawa jikin Baba Suleman Aadil yayi yace "Uncle m...my....my father is is a ri...ritualist, he did all this thing to my brother, Uncle Abie, he feed us da bloodmoney, he cloth us da blood money, he did everything mana da kudin jini, Abie killed and ruin my brother's 30yrs of life, Abie yakashe mini kannai n...." zaiyi magana Baba Suleman ya taushemai baki yana sharemai hawayen daya dake zuba nonstop yace "is okay, is okay Aabid, kaddara ce haka Allah yariga ya tsara rayuwan dan uwanka Aadil, ahaka Allah yariga yarubuta zaiyi shekaru talatin a duniya batare da yasan waye shiba, koda Abie baiyi komiba one way or the other saikaga something happen dazaisa yay rayuwanshi ahaka, now lets all hope for the best, muyi creating new beginning and new memories and let's all forget d past okay, think of your Mum and think abinda take going through yanzu haka, wahala da dawainiyan Aadil tun yana jariri datasha kullum suna hanyan asibiti, sanan ga barin ciki har sau uku yaya kake tunanin takeji yanzu datasan dalilin? Ga kuma dan uwanka a asibiti shida matarshi yaya kake tunani takeji? Let's pray murokan ma Abie gafara daga Allah kaddara ce, dama annabi yafada aciki hadisi cewa kowace alumma nada fitinarta yace fitinar alumma ta itace dokiya, kaga arayuwan nan wasu mutane can do anything for money, inhar dai zasu sami kudi they can do anything, arayuwar nan tamu tayau mutum ya kasance mai godiyan Allah, d little da Allah yabaka ka godemai and be contented saikaga Allah will give you more masu albarka, one shouldn't be greedy da mugun son kudi, greediness dason banza can lead you to astray daga hakane zaka fara karban cin hanci which annabi yay hani akai yafadi ahadisi akan Allah ya tsinema mai bayar da cin hanci damai karba, yawan son kudi ma da mutane keso fitina ne, kudi kayane aka dan ranan gobe kiyama saikama Allah bayani akan each and every single kobo daka kashe, how? Tayaya ka kashe su ta hanya mai kyau ce kota hanyar sabon Allah ne sanan tayaya ka samesu ta hanyar halal ce, ta guminka ne kota hanyar haram, duksai kafadi ma Allah, saisa yakamata kowa kowani musulmi ya yawaita yin addu'a Ya Allah kabani dukiya ta halas, Ya Allah ka sanyama dukiyar Albarka sanan Ya Allah kasa na kashe su ta hanya mai kyau bata hanyar saboba, Allah yasa mudace kawai Aabid, Allah kuma yasa karshen mu tai kyau, Allah kuma ya kashemu muna musulmai sanan Allah ya ganar da dukkan musulmai dakeson kawai suyi kudi kota yayane kotahalin k'ak'a ne, sanan Ya Allah ya shiryi musulmai masu hali irin na Abie wayanda are willing to sacrifice koda mahaifiyar suce dandai kawai suyi kudi su sami abin duniya, wayanda zasu iya zuwa su sadu da gawa dan samin abin duniya, su sami kudi su sami na nunama jama'a ace wai wanan fa babba ne Alhaji ne motoci guda dari gareshi baya sati a nigeria yau yana dubai gobe yana china, Allah yarabamu da dukiyar dazata halaka mu, mu koma ga Allah kawai Aadil, is high time malamai sun tashi a tunatar sukuma tsawatar, kaga shi tunatarwa yana karkato da zuciyan mumini sanan yana kara samai tsoron Allah dakuma gujema kaba'ir, Allah yasa mudace, tashi muje masallaci muyi sallan asuba daganan saimu tafi gida dan akai Abdullahi gidan gaskiya, Allah ya jikanshi ya gafartamai yasa yahuta Allah kuma ya gafartamai kurakuran shi, May Allah forgive all his short comings" ahankali Aabid yace "Ameen" ya share hot hawayen daya zubomai deep down ko Allah yasani yanason mahaifinshi danshi shaida ne akan yanda mahaifinsu ke sonsu, sune komi na Abie amma wat can he do abu daya kawai zaimai shine ya rokamai gafara, yamai addu'a sanan yabude abubuwan sadakatun jariya wanda lada zai dinga kaimai kabari, saida Baba Suleman ya dagashi sanan ya iya tashi ko kadan baida karfi fita sukayi Baba Suleman da Muhammad suka rikeshi alwala sukayi sukai salla sanan suka fito suka shiga mota koda sukakai anguwan su mutane an cika fal tako ina, cikinsu harda baban Hamida da Abban su Ra'is dudda liman da Baffa sunriga sunce babu kyau fadin mummunan halin mamaci boyewa ake, addu'a kawai za'ama Abie saisa kosu baban Hamida ba'a fada musu gaskiyan abinda yafaru ba, banda limaman nan guda uku dasu babu wanda yasan zancen,  ancedai wuta ce takama shine ginin ya zubo yafado kan Abie, sanan sukace musu antafi da Hamida da Aadil asibiti sosai su Aban Hamida sukai addu'a sanan sukai musu jaje aka dauko motar daga gidi aka daga ginin aka  tattaro pieces din jikin Abie aka atattare awuri daya, rayuwan fa kenan! Saisa in this world d best thing to do shine kabi Allah koka samu kyakkyawan karshe, yau ina Abie dakeda kudi ghana masgo manya manya sama da dari na yan dollars? Ina Abie mai kampanin mota? Ina Abie maisa hadadden shadda dake kyalli yahau jeep yafita ina yake? Uban dukiyan daya tara yanzu sun hanashi mutuwa? Dukiyarshi ta taimakeshi? Ta amfane shi? Jama'ar musulmi mubi Allah mukoma ga Allah kar son kudi yarufe muku ido yasa kuyi sata, chacha, gambling, riba ta hanyar karban loan kabiya with interest and other ways, kisan kai, cuta, and many more, all kudin at d end of the day bazasu miki komiba bazasu tsinana miki komiba afarin kyalle za'a kaiki/ka, Allah ya gafarta mana kura kuran mu ameen yabamu ikon cin jarabawa dan no body is perfect, Allah saidai yasamu a aljanna dan rahaman sa badan aikin muba dan we are not doing enough.




Haka aka tattara Abie bayan an sallace shi aka kaishi makwancin shi duk dauriya da taurin zuciyan Aabid saida ya dinga kuka wata irin nadama ta shigeshi shima ya shiga tubanma Allah akan kurakuran shi, shan giya bin mata yay taubatan nasuha yama Allah alkawari bazai karaba, dawowa gida akayi ana amsan gaisuwa, Mama da Anty Lami da Kaka harda Zainab da Ihsan suma suka shiryo sukazo gidan gaisuwa ananta lallashin Mami da idanunta suka kumbura sosai babu wanda zai ganta dabazai tausaya mataba bayan sun gama aka kaisu hospital sukaje duba Hamida da Aadil danhar lokacin bacci suke bama asan ranan farfadowan suba.







***

_Bayan Wata Daya_


Yauwa yanzu labari zai fara dadi na zare Abie 😜😜😜




Ya Allah ya gafarta ma wayanda suka rigamu gidan gaskiya, Allah kasa mucika da imani.

..







Fita daga dakin Mami tayi tawuce dakinsu Aabid din dantai magana da Aadil, sallama tai tareda tura kofan dakin Aabid kadai tagani zaune kan kujeran dakin daure da towel a waist yadaura laptop akan cinyarshi yana aiki gefenshi kuma dan karamin cup ne na black coffee dayake sipping kadan kadan yana aiki, kan gado kuma Aadil ne kwance sanye da white bathrobe yana bacci peacefully dan daga fitowarshi daga wanka yahau kan gadon tsabagen baccin dake damunshi, jin anbude kofa yasa Aabid yadago kai suka hada ido da Mami, hakan yasa yay dan murmushi yace "Mami na" hararanshi tadanyi tace "keep that system katashi kasaka kaya kafin nabatama rai kasan jikin ka baisan sanyi ko" murmushi yadanyi saikuma ya ijiye system din yana kallonta a shagwabe yace "Mami nagaji ne wlh kiwiyan neman kayan nakeji" murmushi kawai tayi ta shigo dakin tai hanyar wardrobe dinsu tabude tana kokarin fitomai da kayan dazaisa tace "bakaki aure ba, bama kasan amaka maganan aure, get ready bakariga kaga komiba nan gaba har takalmin ka kasa dauka zakayi sabida kiwuya" dariya yayi ya janye cup din coffee daga bakinshi yace "Mami na ai u are here xaki nemamin ko" zaro hanger dawani riga da wandonshi ke jiki bakake tayi tadan waigo ta watsamai harara tace "eh sabida ancema banda aikin yi kullum sai nemama kayan dazaka saka ko zantayi, common taso kasaka kayan katada dan uwanka shima yasaka kuwuce kutafi masallaci is time for magrib" tashi yayi ahankali kaman zaiyi kuka yataho wurin gadon ta mikamai kayan ya karba taja kunenshi, dan kara yayi yace "wash Allah Mami kin katse kunen" "tukunna dai duk randa nakara kamaka kai wanka baka tashi ka shirya ba ranan ne kunen duka zan cisge nasa amaka pepper soup dashi" tasaki kunen tajuya tafita daga dakin, kaman zaiyi kuka ya shirya tsaf cikin kayan ya feffesa turaren ya shiga bathroom yaje yay hanging towel din a hanger sanan yadawo yana kallon Aadil dake baccin shi bilhakki yana fitar da numfashi ahankali ahankali, karasowa yayi yana kallon fuskarshi yanda lips dinshi sukai ja sosai kaman mai zazzabi hakan yasa yataba wuyanshi jin ba zafi yasa ya dakamai duka acinya. "hey rascal" bude ido kadan Aadil yayi dasuka dan chanza kala sabida bacci yace "stop it Bid, am sleepy" hanunshi Aabid yaja yana murmushi yace "baka isaba wlh, time for magrib tashi jor" lumshe ido yayi agajiye yanadan turamai baki, kara jan kafarshi Aabid yayi yace "kaifa miskili ne, common tashi mutafi mosque lazy ass dude" tashi yayi ahankali yana kallon Aabid din dakemai murmushin keta, tashi tsaye yayi da kyar yana dafa jikin gado Aabid yace "yauwa jekayo alwala to bari naciroma kayan dazaka saka" gyadamai kai yayi batare dayace wani abuba yajuya ya shiga bathroom yanajin ciwa ciwan ciki kadan kadan, alwala ya dauro yafito kayan da Aabid ya ciromai irin na jikinshi ya shirya tsaf cikinsu bakaramin kyau sukamai ba kamanin su daya yakara fitowa kawai dai Aadil looks cooler than Aabid, kana ganin nature Aadil from facial look zaka gane bamai yawan son magana bane, while Aabid kana ganinshi kaga mai raha ga murmushi, turare ya feffesa ya zira takalmi, 

Masallacin suka wuce, bayan magrib suka fito sukayo gida dakinsu suka wuce Aabid namai hira, Big Mum ce ta shigo dakin da sallama atare dukansu suka kalleta murmushi tamusu tace "yan biyun Mami kuzo yaya na kiranku" tashi sukayi suka biyota sukai wani wani babban falo da Baba Suleman ya sauka aciki, Baba Suleman ne zaune a hadadden falon sai Mami dake kan one sitter ta kafe Aadil din da ido kana ganinta kasan tana cikin damuwa, dayan kujeran Big Mum takaraso ta zauna akai kusada Mami hakan yasa Aadil da Aabid suka zauna akasa, ahankali cikin murya chan kasa irin na marason surutu dinan Aadil yace "gani Uncle" dan murmushi Baba Suleman yayi yace "masha Allah, magana nakeso nayi dakai Aadil, Baffa na Nigeria dole aduk inda Baffa bayanan nai representing dinshi, nasan inda Baffa nanan dole shine zaiyi maganan nan baniba, and banda haka dole nai discharging duties dina amatsayina na babba a family nan inaso na gyara komi kafin gobe, dan gobe nida Aisha mukeso mu koma Nigeria ku zaku zauna da mahaifiyar ku harsai tagama takaba saiku dawo gida, dama ciwon datayi bana wasabane yasa muka hadoku duka muka taho daku nan Egypt cikin yardan ubangiji ita tazo tafara samun lafiya kafin ku, Hassan!" yakira sunan Aadil da dan kakkausar murya alamun maganan dazaimai serious magana ce hakan yasa Aadil yadago kanshi yace "na'am uncle" gyara zama Baba Suleman yaya yace "naso ace gobe ne kafin mutafi da safe, alokacin kama kara samin lafiya da karfin jiki da kuzari da komima zanma maganan nan amma dole ce tasa dole nama maganan nan anan wurin akuma yanzu dan kaganmu dukan mu nan we cannot stand hatred dinka ma Amatullahi wato Hamida kodan yayane we can't stand it" Baba Suleman yafada adan zafafe, dan lumshe ido Aadil yayi yabude ya mayar da kanshi kasa jin ankira sunan yarinyar dazu dinan, gyara zama Baffa yayi yace "dukan mu nan we were shock to see yanda dukka sanmu kakuma ganemu i guess ikon Allah ne yasanya hakan ya karbi addu'an mahaifiyar ka kuma datasha yima, Aadil you've been sick tundaga ranan da aka haifeka ma'ana shekaru talatin dasuka wuce na baya dayan watan ni............" labari ya shiga bama Aadil natun lokacin da aka haifeshi dakomi da komi da Abie yayi da auren shi da Hamida da komi har zuwa yau daya warke yakarake da. "bazamu taba zaunawa and sit back mu kalleka ka wulakanta yarinyar da iyayenta suka mana halacci suka dubi condition dinka batare dasun kawo komiba suka baka auren taba dandai kasamu lafiya sabida tarin jini daka dinga yi alikacin, bari kaji nafada ma kaganni nan Hassan koni bazan zauna nabama mahaukaci y'ata ba inda ina dashi ba inaji inagani, iyayen Hamida sunma wanan family abinda har gobe har jibi bazamu taba mantawa ba and bazamu taba yarda ka wulakanta musu y'a ba ka wulakanta amanar muba da muka karba da hannu bibbiyu ba, nasan all this labari yataho maka wni iri wani iri it will take time kai assimilating everything a brain dinka and accept everything but bamu da lokacin nan,   this girl stay with you, ta kula dakai Aadil, sabida kai har koranta saida akayi daga gida daga baya baban Ra'is yakeban labarin bayan munje gidan su, mahaifinka yakusa kasheta ya shaketa ko anan kadai she had the chance tafadama iyayenta amma bata fadiba dudda marin da zagin datasha awurin shi but still ta zauna dakai, yanzu Aadil yarinya haka, yarinya tagari, mai natsuwa da hankali ga ilimin addini dakasamu amatsayin mata ce zaka ji sauki ka juyama baya babu ko kalmar godiya iyye?" Baba Suleman yay tambayan asanyaye yana karkada kafa yana kallon Aadil din babu alamun wasa akan fuskarshi yana jiran amsa, dan lumshe ido Aadil yayi zuciyarshi namai zafi sosai, yanajin wani irin sadness dabazai iya bayanin irinshi ba. "kanaji na kamin shiru Hassan kabani amsa" dan bude ido Aadil yayi idanunshi yay ja sosai ya kalli Baffa da muryanshi data dan shake yace "uncle bansont...." "karka fara kafadi kalmar nan Aadil karka kuskura" Baba Suleman yafada cikin zafi yana buga hanun kujera Mami ma ta watsama Aadil din mugun kallo hakan yasa  yay shiru ya saukar da kanshi kasa Baba Suleman ya nunashi da yatsa yace "kadena ganin muna sonka muna nan nan dakai inhar kan Hamida ne gabaki dayan mu nan wlh saimun juyama baya, baka sonta kakeso kafadi? Wlh kozaka kwana dari kana fadin haka bazamu yardaba, bazamu taba yardaba Hassan, dan kaso Hamida tun baka hayyacin tun bakasan kokai wayeba, tun kwakwalwarka nata yara, kasota tunkafin ma kafara ganinta so check ur self sonta nanan tattare dakai yana cikin zuciyarka ka bincikoshi aduk inda ya shiga, the love u have for Amatullah natural love ne da banjin zai taba mutuwa ba aranka, you don't expect us manya damu muzuba maka ido kai abinda zakayi ba at d end of d day mu maida musu da Hamida gida mucema iyayenta ka warkene shine kaga baka sonta karabu da ita, tayaya ma hakan zai faru iyye? Kamaida mu kananun yarane? Kagama musu da y'a ka cuceta yanzu katashi kace baka sonta Allah natuba wat if rabo yariga ya shiga tsakanin ku?" dago kai Aadil yayi ya kalli Baba Suleman dan sosai zuciyarshi ta tsinke da maganan Uncle, da yatsa Baba Suleman ya nunashi yace "katattara kawuce daganan zuwa dakinku chan, Mamarka ta riga ta kaita part dinku, chan dayan bangaren dazunan da muka tafi magrib dan masu aiki sun gama gyara part din, kabarma Aabid dakinshi dan kai ba gwauro bane kanada iyalinka, karka sake ka cutar da yarinyar nan, inka cutar da ita muka cutar Aadil, karike wanan aranka, Allah ya sanya muku albarka, Allah yabaku zaman lafiya, ya maganar mu kaikuma?" yay maganan yana kallon Aabid da kanshi ke kasa "dakainake" dago kai Aabid yayi yadan sosa kai ya kalli Mami harara Mami ta watsamai hakan yasa yace "very soon Uncle" gyadamai kai Baba Suleman yayi yace "nabaka nan da mamanku tagama Idda dazaran kun dawo Nigeria inbaka fito dashi ba zamu fitarma dashine gadai dan uwanka nan kwanan nan zamuzo suna" yay maganan yana dariya shiru Aadil yayi feeling sad sosai tashi Baffa yayi yace "ku wuce mutafi masallaci kana dawowa straight to part dinku dan matarka da mijinta zata kwana bazata kwana ita kadai ba" tashi sukayi duk suka fita daga dakin Aadil binsu kawai yake amma kanshi yay mugun zafi.



Hawaye Mami ta share hakan yasa Big Mum matsowa kusada ita tace "waiba kinmin alkawarin dena kukan nan ba eh Maryam" girgiza kai Mami tayi tace "na dauka matsalolina sun kau sai farin ciki yanzu da kowa yasami lafiya, jibi abinda Aadil yazo dashi kuma Yaya, Yaya yazanyi idan yadage baison Hamida? My heart can not take that, bansan yarabu da yarinyar nan idan yay haka ya cuceta sosai, mun cuceta sosai Yaya, wat if abu ya shiga tsakanin su Yaya? Bakiga yanda yake shishige mataba alokacin and is possible abu ya shiga tsakaninsu dudda yana abu kaman yara ai zai iya komi ko yaya, yanzu soyake ya maida yarinyar mutane bazawara? yazanyi da raina wlh nagaji da komi zuciyata namin zafi sosai zan...." hannu Big Mum ta daura mata akan baki tace "take it easy, dont think Much, auren Aadil da Hamida har jikokin su zaki gani trust me, ai real love baya taba mutuwa saidai yay bacci koya daskare, shi soyayya dakike gani kaman kakide ne wani zubin, time will heat d love kiga soyayyar ta tashi daga baccin datake yi, don't be weak bakiga yanda Yaya yamai zafi zafi ba bakiga yakasa cewa komiba, kema haka zaki bishi inkikamai sanyi ne zaiyi abinda yaga dama, hot hot zakibi Aadil, kome kika sani ki dinga saka Hamida nayi just tayanda zaki hadasu magana kuma suna tare koda yaushe, ki koyamata kissoshi na mata, zaki gani nan da yan kwanaki kadan zakiga wonders badai namiji bane dole zai shigo hannu ballema Hamida yarinya son kowa kin wanda yarasa" gyadamata kai Mami tayi tace "shikenan Yaya".

.... 






Yace "D...Dil" murmushi Aadil yamai asanyaye yace "Bid" Aabid couldn't believe wat he is seeing, ahankali yabude hanunshi alamun big hug dan d way he's feeling right now happiness din ganin twin brother shi, Aadil as normal person jiyake kaman zuciyarshi  zata fashe, da sauri Aadil ya shigo dakin yabude hannayenshi shima da sauri Aabid yataho sukai hugging juna so tight, Aabid sai hawaye yawani irin kankameshi yace "I love you Twin, I love you so much Hassan, I love y..." yakasa magana sai hawaye amma mara kara ta yanda Aadil dinne kadai zai iya jinshi, rungume dan uwan nashi yayi tsam ajikinshi yace "I love you more Twin, I love you so so much, I love you Hussain, am feeling somehow i don't know wats wrong with my head inajin wani iri, did anything happen to me? ina Abie?" jin kukan Mami yasa da sauri yasaki Aabid ya kalli Mami data zauna akan kujera tana wani irin kuka mai tsuma rai she can't believe Aadil yawarke bata taba sanin cewa zataga wanan rana aduniya ba dan tariga ta yanke tsammani, ahankali yakaraso yay kneeling agaban Mami yakamo hanunta yarike gam yana kallon fuskarta kaman zaiyi kuka yace "why are you crying Mami?" girgiza mai kai Mami tayi tadaura hannayenta akan fuskarshi tana tattabashi cikin kuka tace "Aa...dil" sashi tayi ajikinta ta rungumeshi a kirjinta tsam tsam tana kuka tadago kai ta mikama Aabid dake share hawaye shima hannu yana kallon su, da sauri yazo tahada su biyun ta rungume su ajikinta tana hawaye, big Mum ma kuka take takasa dena hawaye tana kallonsu, Baba Suleman ne kawai yayta maza bai zubda hawaye ba amma sun bashi tausayi da sauri big Mum ta share hawayen fuskarta tace "laaa Hamida, kai Aadil barinta kai awaje" sakin su Aadil Mami tayi jin an ambato Hamida da sauri ta tashi tsaye tace "dama tare kuke?" "eh harda ita aka sallama" da sauri Mami tai hanyar waje tabude kofa tafita, atsugunne taga Hamidan ta rabe abango ta tsugunna kaman wata marainiya dan tagaji da tsayuwa, da sauri Mami tace "Amatullah" dago fuskarta tayi ta kalli Mami asanyaye, da sauri Mami ta dagata ta rungumeta da sauri ajikinta, jin Hamida take har ranta bubbuga bayanta tayi tama kasa magana sabida yanda taji gabaki daya damuwarta sun kau matar danta da danta duksun warke, sakin Hamidan tayi tai cupping face dinta tace "muje ciki kihuta" shigowa sukayi tareda Hamidan Aabid yakafeta da ido dudda kanta nakasa bai samu yaga fuskarta ba but he's still very happy ganin ta tashi takuma ji sauki, tashi Aadil yayi daga kan kujeran ya kalli Aabid yace "am sleepy Bid, zanyi wanka, let's go to our room" hararanshi Aabid yayi cikin tsananin sonshi dawani irin kewanshi yace "dakina dai, kai dakin ka dana matarka daban danawa" kallonshi yayi kaman maison gane meyace hakan yasa ya maimaita maganan shi din yace "dakina dana matata?" sosai Aabid ya danne zuciyarshi dan yariga yay alkawari he's now a changed man, ya kalli Hamida dake zaune kusada Mami tana wasa da yatsunta Mami na duba jaws dinta da aka cirema bandeji yace "Mami bashi matarshi suje suyi wanka su kwanta duk sun gaji" wani irin juyawa Aadil yayi da kyau ya kalli Mami dakuma yarinyar da Aabid yake cema ace tazo tabi mijinta suje su kwanta sanan ya sake kallon Aadil yanuna kanshi da yatsa yace "matata?" kafin Aadil yay magana Mami ta janye hanunta daga jaws din Hamidan tace "eh matar ka, Hamidar ka baka ganeta bane Aadil?" nuna Hamida yayi da yatsa daga sama har kasa yace "wanan yarinyar ce Matata Mami?" tambayar shi bakaramin dukan zukatan yan dakin yayiba hakan yasa kowa ya kallai, ahankali Hamida ta dago idanunta dasuka cika da kwalla sosai ta kalleshi shima ita yake kallo tunda yamata kallon farko nadazu daya tashi a asibiti sai yanzu ne yasake mata kallo from head to toe saikuma yay dan dariya sama sama irin dariyan mamakin nan daya karama fuskarshi kyau sosai yace "no, no, no Mami this gurl can't be my wife, tayaya ma zan auri this kind of yarinya? Mami wai wat happen to me ne? Kodai are u guys joking? How can i be this thing husband?" yanuna Hamida kaman yana nuna kashi kanshi namai zafi yana kokarin tuno yaushe yama santa dahar ya aureta shidai yasan su Mami kowa adakin nan but ita wanan dake kama da aljanun ne zai aura zaiyi magana Mami ta dagamai hannu cikin kakkausar murya tace "enough Aadil" ta kalli Aabid da jikinshi yay wani irin masifaffen sanyi tace "wuce kutafi dakin naku tare" juyawa Aabid yayi Aadil yasake yatsine fuskarshi yabi bayan Aabid din yagaji sosai bacci kawai yakeso yayi, daga Baba Suleman har Big Mum jikinsu yay wani irin masifaffen sanyi Mami taidan murmushi tana kokarin danne zuciyarta ta kalli Hamidan da kanta ke kasa takama hanunta tace "tashi muje daki kinji daughter" kasa tashi Hamida tayi sabida yanda jikinta yay wani irin freezing saida Mami ta dagata, jikinta yay sanyi iya sanyi jin kanta take kaman ba itaba, Bin Mami kawai take har Mami ta shigar da ita wani hadadden daki ta zaunar da ita ta yaye hijabin jikinta tace "bari mucire hijabin kisha iska ko" gyadamata kai tayi tana kokarin maida hawayenta ciki Mami ta linke hijabin tace "bari naje nakawo miki abinci nazo nakira miki su Mama da Kaka ki gaisa dasu ko daughter na" sake gyadama Mami kai tayi ahankali, Mami tajuya tafita daga dakin tarufo kofan, jingina da bango Mami tayi ta lumshe ido tana dafe kirjinta, ko ita maganganun Aadil sunmata ciwo bare Hamida.... 



Mami na fita Hamida ta tashi da sauri tabude kofar bathroom ta shiga ta rufo ta kife fuskarta jikin kofar bayin tafashe dawani irin kuka mai tsuma rai, jikinta har wani irin rawa rawa yake, ita kanta batasan meke damunta ba but she just want Aadil, so kawai take ta rungumeshi, but ya tsaneta yanzu, saida taji sallaman Mami ta kwala mata kira yasa ta tashi ta kunna tap ta wanke fuskarta ta share fuskar da towel idanunta sunyi ja sosai, tajuya tabude kofa tafito kanta akasa taki bari suhada ido da Mami daketa kallonta tana observing yanayinta, zama tayi akasa Mami ta ijiye mata tiren abincin agabanta sanan ta zauna gefenta tasa hannu takama hanun Hamidan ta sauke ajiyan zuciya, ahankali takira sunanta. "Amatullah" "Na'am Mum" Hamida ta amsa da muryanta dayadan shake batare databari sun hada ido da Mami ba, ahankali Mami tace "everything will be fine, i promise you kinji" gyadama Mami kai tayi, Mami ta mika mata iPhone dinta tace "gashinan inkin gama ki kira kowa da kowa" gyadama Mami kai tayi ta karbi wayan, Mami tace "am coming".


... 






Sai wuraren tara da rabi suka shigo gidan da Uncle da Aabid ne kawai ke fira binsu kawai yake dan kanshi gabaki daya adagule yake, hanyar shashinsu Baba Suleman ya nunamai yace "wuce wajen matarka saida safen mu, ka kula da ita" kallon Bid yayi kaman zaiyi kuka shima jikin Aabid din saiyay wani irin sanyi zaimai magana yajuya da sauri yay shashin bude kofan yayi ya shiga falon, dakin kamshi sosai komi na dakin off white ko ina a gyare, zama yayi kan kujera ya kwanta yana lumshe ido sabida ciwan da cikinshi kemai saida ciwan yadan lafa sanan yabude idon yana kallon saman dakin yana tunani duka maganganun da Baba Suleman yafadi mai na abinda yafaru dashi abaya, wasu hot hawaye ne suka gangaro daga gefen idanunshi, iska ya fuzar mai bala'in zafi, lumshe ido yayi kafin ahankali yabude yace "Abie! Abie" sake lumshe ido yayi wasu sababbin hawayen suka kara fitowa ahankali yakai hannu ya share hawayen yana kokarin lallashin kanshi da yima kanshi wa'azi, yes I've wasted 30yrs of my life, I've lost those 30yrs, amman dudda haka he's grateful, Alhamdulillah da Allah yadawo dashi normal kaman kowani d'a namiji at this phase of life, komi kaddara ne, so yadauki wanan as kaddara and in sha Allah dagayau zai rufe chapter past dinshi yabude sabon life dagayau dan sabida ko Abie dayamai haka ina yake yau aduniya? Bashi yarasu, so is time to start afresh, sake share hawayen yayi tareda fuzar da iska daurewa kawai yake dauriya irin ta maza, ahankali ya dagakai ya kalli agogon bangon dakin da idanunshi dasukai lema lema, karfe kusan sha biyu saura yagani na dare, ahankali ya mike tsaye daga kujera ya daura hanunshi akan cikinshi jin cikin yasake murdawa , hanyar corridor yayi yana tunanin dole yaje yaga Dr gobe dan he don't feel okay at all, hanun ya daura kan handle din kofan ya bude kofar, ahankali yabude kofan yay sallama chan kasan makoshi, dakin na wani cool kamshi mai sanyaya rai sama dana falo ga sanyin AC wutan dakin a kunne, Hamida ya hango kan gado tana bacci ta kudundune blanket din jikinta data rufa dashi yadan zamo ya tsaya akan cikinta, pink spaghetti hand rigan baccin datasa ya bayyana ya kwanta ajikinta sosai, ta chusa gashin kanta cikin net, hulan net dinma yadan zamo baya gashin gaban goshinta sun kwanta, tai haske sosai tana baccinta fuskarta looks so innocent, shigowa yayi yamaida kofar ya rufe ya jingina da kofan tareda rungume hanunshi akan kirji yacigaba da kallonta bayako kyaftawa, ahankali yafara tafiya harya karaso jikin gadon yana kallonta, tsayawa yayi akanta yana kallonta kaman wanda aka aiko yazo ya kalleta yabada rahoto, Kaman taji ajikinta ana kallonta tabude ido ahankali dake cike da bacci, wani mugun kallo ya watsa mata batare dayace mata komiba, faduwa gabanta yayi sosai da sauri ta tashi tabar sosa idon datakeyi cikin bacci,  jingina tayi da bangon gadon tana kallonshi kirjinta na bugawa tana zaro manyan idanunta dan sosai taji tana shakkan wanan new Aadil din tunda ta kura baida mutunci baida kirki kuma, ahankali ta saukar da idanunta kasa dan kasa jure mugun kallon dayake mata tayi da manyan lulu eyes dinshi ta rike blanket din data rufa dashi gam gam kaman har whole life depend on it yatsunta na rawa, dan gyara muryanshi yayi kafin cikin cool voice dinshi yana kallonta batare daya janye idanunshi dagakan jikinta ba yace "ance ke matata ce?" yay maganan yana kallonta yana kallon yanda yatsunta ke rawa kaman wacce aka makalama electric shock, dan fuzar da iska yayi yace "i have a very sad past, anything daya danganci past dina i hate it, bazan taba iya rayuwan aure dakeba, karki sake ki kira kanki matata in as much as am concern banda mata, i give you dagayau zuwa gobe just tell me mezan miki inma biyanki zanyi i will do it, just anything koma menene zanyi just to get you out of my life, please tashi kifita daga dakin nan, i want to sleep" da sauri ta dagakai ta kalleshi hawaye sun taru a idanunta sosai dan maganar ta mugun dakanta, lumshe ido yayi ganin yanda eyes dinta ke shining murya chan kasa yace "if possible ma kifita daga shashin nan i don't want you to sleep around inda nake banson ganinki at al..." da gudu ta tashi tafita tabude kofar tafita tai hanyar dining kitchen tabude ta shiga ta maida kofar tarufe ta jingina da kofar tana kuka kafin ta sulale tazauna akasan wurin ta chusa kanta a cinyoyinta tana kuka sosai kaman zata mutu bata taba sanin rana haka zataso ba, jitayi tagaji da komi da komi so kawai take taganta gidansu wajen Mama da yan uwanta, so sai taci kuka idanunta sunyi bula bula ahaka bacci yay gaba da ita a wurin. 






Bin kofar data fita yayi da kallo idanunshi shima sunyi ja yakai almost 30min a tsaye kafin ya shiga bathroom ya dauro alwala ya shimfida dadduma yahau yafara salloli yana addu'a Allah yaragemai nauyin da zuciyarshi kemai da kuncin dayakeji, saida ya idar sanan ya cire kayan jikinshi yarage dagashi sao boxer ya kwanta kan gadon cikinshi namai ciwo da kyar bacci yay awon gaba sai juyi yake akan gadon.





 Kiraye kirayen assalatu yatada ta daga wahalallen baccin datakeyi, tashi tayi ahankali tana dafa jikin kofar sabida yanda kafafunta sukai tsami sosai tabude kofar kitchen din tai dining kafin takarasa falo tana kalle Kalle idanunta sun kumbura sosai sunyi ja sabida kukan datasha jiya, ganin babu bayi a falon gawani shegen fitsari datakeji yasa tai hanyar bedroom dinsu dudda ko kadan bataso ta shiga dakinba, ahankali tabude kofan dakin dakin duhu sai sako sakon gefen kofan bathroom dayake dan fito da rays din haske sabida wutan bathroom dayake nan a kunne, karasawa tayi tabude kofar bathroom din ahankali batare dayay making sound ba ta shiga, brush tayi bayan tai fitsarin sanan tai wanka agurguje da ruwan zafi sosai sabida jikinta dake mata ciwo bana wasaba, bayan tagama ta dauro towel dinta fari sanan tabudo kofa tafito ta maida kofan ta rufe dakin duhu sosai, so take ta kunna wuta ta nemi kayan dazata saka tadau hijab da dadduma tafita amma bata ganin komi adakin, tunawa tayi da wayanta akan bedside drawer hakan yasa tai wurin tana tafiyan ahankali kaman wacce tazo sata kirjinta na bugawa, karasowa tayi wurin gadon hakan yasa tafara mikar da hannu danta daura hanun akan side drawer ta laluba wayar ta dauka, tuntube tai da kafar mutum hakan yasa tai ihu tai baya zata fadi. "Mama!" hanunta yarike gam cikin duhun kafin ya fizgota da karfi sosai, fadowa tayi jikinshi yana zaune bakin gado bude bathroom datayi hasken yatadashi dan dama bacci bai dade da kamashi ba sabida ciwan da cikinshi ketamai, matseta yayi ajikinta gam yana shakan kamshin dake fita daga jikinta na sabulun ta dakuma kamshinta da dahuwar amarcin da aka mata na turarukan maiduguri dan yar buzu tace bayan shekara ne turaren zaiyi expire, sosai jikinta ya shiga rawa jin ya rirriketa hakan yasa da sauri tai yunkurin tashi maida ita yayi ya zaunar kan cinyarshi ya matse kafafunta gam a tsakiyar nashi harsaida taidan kara dan dama kafafun ciwo suke mata, ahankali ya daura habarshi akan kafadarta ya sanya hancinshi a wuyanta lema leman wurin ya sauka akan hancinshi, wani irin yarr taji ajikinta jin saukar hancinshi akan wuyanta da sauri ta zame wuyanta bakinta na dan rawa tace "w...way...wayana zan dauka please" soft hanunshi ya daura akan kafadarta ya dawo da ita cikin jikinshi sosai cikinshi nawani irin murdawa yace "how many times na sadu dake da banda lafiya? Kinji maganata kenan kinaso na sadu dakene tahakane zaki rabu dani, is that wat u want?" yay maganan da murya chan kasan makoshi batare dayamasan lokacin dayay maganan ba, rawa kafafunta suka shigayi tafara kokarin tashi dan dagashi sai gajeren wando, dan matse mata kafada yayi yace "eh?" bakinta har rawa yake tace "s..." tai shiru tama kasa fadar kalmar dazata fadi sabida yanda miyan bakinta ya bushe, ahankali yacusa  hanunshi cikin towel dinta ya daura hanun akan saman cikinta atare dukansu sukaji wani irin shock, cikin wicked edge of his voice yace "dama ance nai miki ciki da gaske u are pregnant for me?" hanunta tadura akan nashi arude ta shiga ture hanun tana girgiza maikai tace "a....a...a'a" dan murmushi yayi mai sauti kafin ahankali yace "dat means bazan iya rabuwa dake yanzu ba saikin haifamin babies dina kenan, don't worry am not gonna blame me for nemana okay, and for babies to grow sosai acikin mahaifiyar su they need lot of food daga jikin baban su, get this to your head gurl, i don't like you, bansan small girl like u can take me ba, anyway dole i must be sleeping with u everyday feeding my children" yay maganan cikinshi na kara murdawa wani irin Banzan sha'awa na sake addabanshi, fashewa tayi da kuka tana girgiza mai kai tana kokarin tashi daga jikinshi fizge towel din jikinta yayi ya yar yana rike da ita, ihu tayi sosai cike da tsoro tace "dan Allah my Aadil stop kaji" girgiza mata kai yayi shima yana lumshe ido yana kokarin kwantar da ita, kwantar da ita yayi ya kwanta akanta ya sakin mata nauyinshi cikeda mugunta ahankali yadaura hanunshi akan boobs dinta wani irin wawan ajiyan zuciya yayi cikin muryanshi dabata fita sosai yace "sha'awanki nakeji please keep quiet lemme have you in peace okay"







Girgiza mai kai tayi a tsorace tana fitar da numfashi da kyar sabida nauyin daya sakin mata  wasaba, kara tayi. "wayyo Allah na please kadagani" lumshe ido yayi sabida cool kamshin daya fito daga bakinta daya sauka akan fuskarshi ahankali yay placing forehead dinshi akan nata hancinshi da nata sukai kissing each other, sosai gabanta ke faduwa sabida yanda numfashin shi ke sauka akan fuskarta, cikin wani irin murya kaman ta jaririya tace "ka...kada..gan..." kasa daure cool breathtaking herbs scent din dake fita daga bakinta yayi ahankali ya daura bakinshi kan nata da sauri tai kokarin holding lips dinta tare ya fizge lips din da sauri, lumshe ido yayi jin wani irin feelings nabin jikinshi ya shiga kissing dinta passionately, sosai yakejin dadin bakinta kaman zai suma a zuciyarahi yace "I must admit her lips are so soft kaman nayar jarariya, kissing her da dadi sosai" hanunshi ne suka shiga yawo a fuskarta net din kanta ya cire ya yar ya shiga shafa gashin har zuwa wuyanta yanajin yanda take kuka tana kokarin fizge lips dinta amma yaki bata chance din, ahankali yadaura hanunshi kan kirjinta saida yaji wani irin shock hanunshi suka shiga rawa, da sauri ya matse da karfi yanajin wani irin dadi even though he wanted just to scare d girl off dan bayasonta ko kadan but kasa daurewa yayi kamshin datakeyi na tafiya dashi sosai, sakin lips dinta yayi yana kara sata ajikinshi sosai murya chan kasa yace "ur boobs are so full sabida babies dinane yasa suka ciko haka" girgiza mai kai tayi tasa hanunta ta tureshi da karfi ta tashi daga kwancen zata sauka daga gadon yasake fizgota a tsorace tace "dan Allah kasaneki, banso kadena" sata yayi ajikinshi kawai soyake ya manna warm jikinta danashi cikin kakkausar murya yace "sabida ina kokarin baki abinda kikazo nema ne shine zaki fara pretending, i told you bana sonki bakimin ba u are too small for me nima, me kike dashi? Wat can you offer me, banda haka kinyi kama da yarinyar aljanu haka suke farare bau kaman ke, am even this close to you sabida yarana da akace kina dauke dasu inda ba hakaba ko hannuna baki isa ki tababa" fashewa tayi da kuka sosai kaman zata shide maganganun shi sun mugun mata ciwo, fizge kanta tayi ta cikin fushi sosai ta sauka daga kan gadon tafice falo fadawa kan kujera tayi tafara kuka sosai kaman an ai kota jikinta ko ina na rawa, yakai kusan 10min azaune da kyar ya iya tashi yana yatsine fuska sallan kawai dayaji ana kira ne yasa yabarta inda bahaka ba she's too small to walk out of him yana cikin more ta, matsalan yara kenan, suma su Baffa me bazasu auramai babban mace ba wacce ta nuna, he's sure yarinyar nan can never gamsar dashi mikewa tsaye yayi 

yadan ja boxer dinshi kasa ya fito da huge erection dinshi dakemai ciwo sosai yana shafa kan dakemai ciwo, he really wanted ya soka mata shi koyayi releasing sperm din dakemai ciwo a ciki, ahankali ya cigaba da shafa kan yana lallashinta ya hada ruwa yay wanka sanan yafito agurguje ya shirya mosque ya sanya wani white jallabiya kanshi namai ciwo sosai, fitowa yayi daga dakin tundaga dining yakejin yanda take kuka shigowa falon yayi yana kallonta yanda take daure dawani dan karamin dan kwali tana kuka kanta akasa kana ganin yanda takeyi kamasan sanyi takeji, dauke kai yayi batare daya sake mata another look ba yafice mosque.


Da kyar ta lallaba ta tashi tawuce bayi wanka tasake yin wani wankan sanan tafito ta shafa mai agurgujr ta shirya cikin wani A-line gown na atampa yamata kyau sosau yabi jikinta sanan tadau hijabi tazura sanan tahaukan dadduma ta kabbarta salla tana idrwa  tai azkar ta karanta Al Qur'ani sosai taji zuciyarta yay mata sanyi sosai hakan yasa ta tashi ta linke dadduma batare data cire hijabi ba tabude kofa tafito danso take ta tafi wurin Mami kotaji dadi ahankali tabude kofar sitting room din tafito daidai Aadil ya sanyo kai matsawa gefe tayi da sauri kanta akasa tana wasa da yatsunta, hannayenshi ya zuba acikin aljihun jallabiyan yana kallonta yanda idanunta ke kasa haka ya bayyanar da zara zaran gashin idanunta dakenan ajike har lokacin sabida kukan datashi, gashin gaban goshinta sun kwanta lublub, jin shiru yasa ta dago kanta atsorace

....










Dago manyan idanunta tayi ta kallai, hada ido sukayi yawani tsareta da manyan idanunshi dakesa gabanta faduwa hanunshi zube cikin aljihun fararen rigarshi, mayarda kanta kasa tayi da sauri ta matsa gefenshi tana wasa da yatsunta bakinta har rawa yake tace "in...ina kwana" batare daya bata amsaba yabita da kallo, dawani irin murya kaman wanda akace dole saiyay mata magana yace "ina zaki this early morning?" batare data kalleshi ba kanta na kasa har lokacin cikin siruruwar muryanta na wacce ke shirin kuka tace "wurin Mami zani" harara ya watsa mata ganin tana neman ta haddasamai bala'i dawayan nan kumburarrun idanun nata ne zatace zata wajen Mami aisai yabani awurin Mami intaga idanunta haka, hanunta ya kama yashiga cikin falon da ita yamaida kofa ya rufe yace "am not done with you, let's go inside" girgiza mai kai tayi tana kokarin danne kukan datakeji dan bataso tanamai kuka tace "a'a ni anan zan zauna" tai maganan tana kokarin fizge hanunta daga nashi, fizgota yayi jikinshi batare daya saki hanun nataba ya sanyata ajikinshi ahankali yasaki ajiyan zuciya jinta dayay cikin jikinshi yasa hannu ya yaye hijabin jikinta ya wurgar da hijabin a kasa yabi jikinta da kallo yanda A-line gown din yamata kyau yakamata tsam ajiki, hanunshi ya daura kan zip din bayan rigan zaija kasa da sauri takoma baya tana girgiza mai kai hawaye na gangarowa daga idanunta, akasalance yamata alamu da hannu datazo yace "banson kuka, kimin shiru please, come here" akan kujera ta zauna tana girgiza kai dan ko kadan batason zuwa kusadashi ga shegen mayen turaren jikinshi dake sata jin kaman bacci bacci tsabagen dadinshi, wurin kujeran yayi da sauri ta tashi zata gudu daukarta yayi chak yay hanyar bedroom da ita fashewa tayi da kuka sosai tana wuntsila kafa tace "dan Allah kasakeni i don't want to go inside" wurgata yayi kan gado da karfi harsaida tai kara ya tsaya jikin kofa yana murza key yana kallon yanda ta tashi daga kan gadon da sauri tana kuka dukta rude, kulle kofan yayi yazare key yasaka a aljihun jallabiyan jikinshi, stool din gaban mirror yaja yana mata wani mugun kallo yace "come here" yanda ya watsa mata mugun kallo kaman zai kasheta yasa taji mugun tsoronshi ya dirar mata arai, ahankali ta sauko daga kan gadon tana goge hawayen datakeyi da bayan hannu takaraso gabanshi ta tsaya, kallonta yayi from head to toe hakanan tsayin yarinyar na burgeshi dudda yafita tsayi sosai but doguwa ce amma ba chanchan ba, rigan jikinta ya nunamata da yatsa yace "take it off and come here nabaki abinda kikeso" tsayawa tai tana kallonshi tama kasa magana sai numfashi take fitarwa da sauri da sauri, yanda ya zuba mata ido yasa taji hanjin cikinta sundau rawa zata iya rantsewa this is not her Aadil dake mata kuka yana mata shagwaba everyday every time saidai in bai gantaba, kasa koda motsi tayi sai share hawayen dasuka kasa dena zuba take, ahankali yatashi daga kan kujeran da sauri ta matsa baya sabida firgitan datayi karasawa gaban wardrobe yayi yabude wani dogon belt din wandonshi yaciro yajuyo yana kallonta, dan lumshe ido yayi kaman wanda baison yin maganan yace "will you take it off kosai kinji ajikin ki" girgiza mai kai tayi dan ko kadan batason duka gashi ya dauko wani sharbeben belt, ganin yataho yasa da sauri tafashe da kuka tace "zanyi please karka daken kaji" hanunta ta daura kan zip din rigan nata tajashi kasa tana kallonshi kaman yanda yake kallonta yana rike da belt din idanunshi sundan kankance, jan zip din tayi har kasa takasa saukar da rigan sai hawayen dake fitowa daga idanunta, saukar belt taji ajikinta hakan yasa tasaki ihu sosai dudda bai mata dawani karfi sosai ba amma saida tai uban ihu ta durkushe awurin tana sosa hanunta daya shaudamawa, tsugunnawa yayi agabanta da idanunshi dasuka chanza kala sosai ya daura hanunshi akan lips dinshi alamun tai shiru hadiye kukan tayi tana wani irin nishi tana kallonshi, alamu yamata da hannu akan ta tashi tsaye ta cire rigan tashi tayi ta cire rigan tana kuka sosai, bin santala santalan cinyoyinta tayi da kallo har zuwa white pant din dake jikinta da white bra, cikin muryanshi data dan dishashe yace "take off the bra" dago kanta tayi ta kalleshi nakusan 1min, hawayen daya zubo mata ta share tace "why are you doing this?" murya chan kasa shima yace "sabida ban sanki" sosai kalmar ta taba mata zuciya ya sosa mata rai, taji kunci sosai yataso mata, baki tabude zatai magana amma takasa sabida kukan dayaci karfinta dan lumshe ido yayi yabude su ya kalleta yace "my parents sunce dole saina zauna dake, auren da bana hayyacina aure ne? I want you to get tired kirabu dani da kanki ta yanda bazanyi laifi ba awurin su, anyway not that sha'awa nakeji sosai zo narage zafi dake cikina na ciwo" yay maganan yana ijiye belt din hanunshi yatashi ya zare jallabiyar jikinshi yarage dagashi saidan boxer.



Karasowa yayi yana kallon fuskanta yanda take kuka kanta akasa  ta bayanta ya tsaya yana kallon curved hips dinta ahankali yay hugging dinta ya daura kanshi a shoulder dinta ya placing hand akan soft butt dinta ya matse yanajin dadi sosai, jikinta ko ina taushi kaman na jaririya, shafa butt din yayi har zuwa sama kafin ya tusa hanunshi cikin pant din nata yay grabbing ass din nata da kyau, lumshe ido yayi cikin low yace "kinada soft ass i guess ninasa yay taushi haka ko" yay maganan yana dan cizan earlobe dinta, hanunshi ya zaro daga pant din ya daura hanun akan cikinta yay shiru yana sauraran yanda zuciyarta ke bugawa sabida kukan datakeyi, sosai yaji bayajin dadin kukan,, murya chan kasa yana shafa cikinta yace "stop crying yana damun babies dina dake cikin ki" tashi yayi daga bayanta yana bin bayan nata da kallo ahankali yay kissing keyanta yasa tip din finger dinshi yana running down her back, shocking takeji sosai dan every single touch of his har a brain dinta takeji, hanunshi yadaura kan Bra dinta ya kwance hook din bra tareda zame hanun daga hanunta ya yarda Bra din akasa yana saka kanshi akafadar ta yana leka boobs din nata dake nan a tsaitsaye, kwantar da wuyanta yay gently yana bata wani irin passionate vampire kiss hanunshi ahankali suna yawo a flat stomach dinta dakenan kaman bata tabacin abinci ba, hanunshi ta rike gam cikin wani irin tsanarshi dajin haushin shi fizge hanun nata yayi yajuyo da ita ya tallabe fuskarta yana murmushi kaman bashiba, hancinshi ya goga akan nata yace "dama kin iya fushi Miss innocent" yay maganan yana grabbing boobs dinta da karfi expectedly cike da mugunta yana kallon fuskarta, runtse ido tayi cike da azaba tace "wash, kadena please" make mata kafada yayi alamun a'a da sauri ta kalli fuskarshi ganin yay yanda Aadil dinta keyi, kallonta shima yake yace "i want to suck it" yay maganan yana shigewa jikinta sosai, harshen ya daura akan wuyanta yana lashewa, rawa kafafunta suka fara sosai danji taji kaman harshen na tickling nata ajiki, lashe wuyanta ya shiga yi kaman ta zuba zuma a wuyan  har zuwa cleavage dinta kafin cikin wani irin sauri ya chapke boobs dinta abakinshi, kasa daukarta kafafunta sukayi tai baya zata fadi, tareta yayi ya riketa ta hanyar cuddling nata sosai Yana sucking boobs din in a circular form tundaga arreola, runtse ido tayi da karfi sabida yanda yake sha kaman zai katsa mata haka Aadil dinta ke mata lokacin, kasa daurewa yayi ya dagata chak da sauri tai wrapping kafafunta around his waist jikinta ya mutu gabaki daya, kwantar da ita yay kan gado yana kallon fuskarta yanda ta lumshe ido hawaye na gangarowa daga gefen idanun, hanunshi ya daura akan fuskarta ya sharce hawayen murya chan kasa yace "stop crying malama" yay maganan yana kwanciya akan jikinta yana wasa da boobs dinta kaman danshi sukazo duniya, hanunshi yakai saman kan pant dinta ganin yanda ta jike yasa yay murmushi sosai ahankali yasa hanunshi zai zare pant din cike da tsoro ta harde kafafunta tace "no please dan Allah karkamin komi" murya chan kasa yace "no, i need you badly my penis needs to dive in there, bakiso najiki da lafiyata our last sex fa i wasn't myself, lemme have it pls" yafada cikin tsananin bukata, fashewa tayi da kuka sosai tana harharde kafafunta tana girgiza maikai da karfi yazare pant din yana binta da kallo, ahankali ya zare boxer dinshi kasa yay freeing huge manhood dinshi out dake dripping sosai, fashewa tayi da kuka tana girgiza mai tana kokarin sauka daga kan gadon arude mayarda ita yayi ya kwantar ya matseta sosai yana ware kafarta bakinshi ya daura akan kunenta murya chan kasa yace "kin saba dani why are u still afraid? am too big ko? baki iya containing dina, and kinsan wani abu so  nake na barbarkaki yau, yarinya akaiki asibiti" yakarashe maganan yana dan dariya cikeda tsokana kaman bashine yay maganan ba yakai manhood din zai shiga, ihu tayi ta rirrikeshi tana girgiza mai kai tana kallon fuskarshi cikin mugun tsorata tace "is me Aadil, nine fa your Hamida, dan Allah kadena min mugunta am so scared and afraid of you, look, kaga idan ka tsaneni baka sona i understand zaka iya rabuwa dani nakoma gidan mu, i will not be angry but please kayakuri karkamin mugunta tsoro nakeji sosai dan Allah, kaji My Aadil, kaji My Aadil, kaji My Aadil pls" yanda ta kikkira sunanshi idanunta a rufe tana mugun kuka yasa yaji zuciyarshi na amsa sunan, beating da zuciyarshi yafara fast fast yasa yay shiru yana kallon bakinta yanda take furta My Aadil dashi, lumshe ido yayi heart dinshi namai wani irii jiyayi kaman antaba kiranshi da sunan and someone so dear to him, sosai jikinshi yamai wani irin sanyi, rungumeta yayi ahankali batare daya iya mata komiba hakan yasa ta dago kai ta kalleshi, mayarda kanta yayi ya kwantar a kirjinshi hakanan yasami kanshi ya shafa bayanta yanadan patting, ahaka wani wahalallen bacci yay awon gaba da ita ajikinshi, saida yaji tai nauyi sosai ajikinshi sanan ya kwantar da ita akan gadon yay shiru yana kallonta yakasa dena kallonta yama rasa wat exactly yakeji aranshi sunan data kirashi dashi sai yawo yake aranshi "My Aadil, My Aadil" yakai kusan 20min ahaka kafin ya tashi daga kan gadon yaja bargo ya rufa mata yana kallon fuskarta, ahankali yatashi yabude kofar bathroom ya shiga yayo wanka cikinshi namai ciwo ciwo yafito yana yatsine fuska.



Shiryawa yayi cikin 3quater da wani black t-shirt dayamai kyau sosai ajiki ya matseshi yafito da cikan kirjinshi, fesa turaruka yayi jikinshi yay sanyi sosai yafita daga dakin, shashinsu yayi babu kowa a falo hakan yasa yay dakin Aabid bude kofar dakin yayi Aabid na zaune kan kujera rike da laptop yana daddanawa kallo daya yama Aadil din ya dauke kai ya maida hankalinshi kan system din dake kan jikinshi, karasowa cikin dakin Aadil yayi ya zauna a gefen Aabid din yadau daya daga cikin throw pillows din kan kujeran ya rungume tareda lumshe ido  yayi yay shiru sunan My Aadil namai yawo akai sosai, ahankali yafara ganin flash din mutum agabanshi dabaya iya ganin fuskar sosai sailuma yaji muryan mace tace "My Aadil! My Aadil stop crying" kama kanshi yayi sabida yanda kanshi yawani saramai kaman zai tarwatse ya yatsine fuska cike dajin azaban sarawan kan, da sauri Aabid ya ijiye system dinshi agefe ya matsa kusadashi tareda daura hanunshi akan kanshi yace "are you okay Aadil bakada lafiya ne? Kanka kema ciwo?" bude ido Aadil yayi ya kallai ya girgiza mai kai yace "am fine, kaina ke dan ciwo" yay maganan yana kwantar da kanshi kan kafadar Aabid yana sauke ajiyan zuciya ahankali yana tunanin flash din abu daya gani yanzun nan, shiru Aabid yayi kafin ahankali yace "wait lemme go and make coffee for you kasha, namaji u are trying to run temperature" daga kafadar Aabid din yayi, Aabid yatashi yafita daga dakin, yabi bayan Aabid din da kallo ganin ya ramemai sosai tsakanin jiya da yau kaman mai tunanin wani abu, sake lumshe ido yayi yana tunanin Hamida data dagulamai lissafi gabaki daya. Ko kadan baimaji shigowan Aabid ba saidai karan ajiye mug yaji akan table din gaban kujeran hakan yasa ya dago kai ya kalli Aabid din daya ijiye mug din yana nazarin shi, zama yayi kusada Aadil din yana mikamai wayar dayake hanunshi yace "are you sure you are okay Twin" gyadamai kai yayi ahankali batare daya iya furta wata kalma ba, dafamai kafada Aabid yayi yace "stop thinking about the past Aadil, karungumi kaddara duk yanda tazoma you have us and u have your beautiful wife, matarka yarinya ce tagari, kagode ma Allah kawai and move on okay we are all here to support you, this is a second chance Allah yabaka make use of it, ga wayanka nan Mami tabani nakawo ma" karban wayan yayi ya rungume a kirjinshi yana kallon Aabid din wasu siraran hawaye suka zubo ta gefen idanunshi da sauri Aabid yarikeshi cikeda damuwa sosai kaman zaiyi kuka yace "kaga tell me wats wrong with you, you are driving me crazy Dil, am so worried" girgiza mai kai Aadil yayi yace "i don't know Bid, bansan meke damuna ba, but deep down inaji ajikina kaman zan mutu anytime soon" chak Aabid ya tsaya yana kallonshi ko kyafta idanu bayayi maganganun shi ya mugun dakanmai zuciya bana wasaba, kallonshi Aadil yake ganin yanda yayi yasa yabude baki zaiyi magana asanyaye Aabid ya daura hanunshi kan bakin nashi yana kallonshi cikin daure fuska yace "are you mad eh Aadil?" yay maganan yana kaimai duka a kafada idanunshi natara hawaye, yace "are you mad eh? Mesa kakemin maganan mutuwa? And wayafadama yanzu zaka mutu Allah shine masanin gaibu, i just got you back karka karamin maganan mutuwan ka idan kasake bazan karama magana ba kaji ko" yay maganan hawaye na gangaromai daga ido gyadamai kai Aadil yayi yana kokarin tsayar da hawayen dake fitomai daga ido rungumeshi Aabid yayi yamai kiss a goshi yace "koma mekakeji u are not alone, we going to go through it together Aadil, kaine kadai dan uwan daya ragemin yanzu banson in rasaka" ahankali Aadil yace "me too Bid" "let's go out, zomuje muyi many many things outside and have fun zakaji dadin jikinka, tashi jeka shirya kazo" kallon fuskar Aabid din yayi ahankali yamika ma Aabid din hannu hakan yasa Aabid din yabi hanunshi da kallo kafin yasa nashi acikin hannun ya kalli Aadil din kaman yanda yake kallonshi, a natse Aadil din yace "meke damunka? Something has been bothering you i can feel it a zuciyata kana cikin matsala wat is it wat is the problem? Your problem is our problem ko Bid we are one, you've been thinking tun jiya banso kamin karya just tell me menene? Meke damunka? 



Lumshe ido yayi yay shiru sunan My Aadil namai yawo akai sosai, ahankali yafara ganin flash din mutum agabanshi dabaya iya ganin fuskar sosai sailuma yaji muryan mace tace "My Aadil! My Aadil stop crying" kama kanshi yayi sabida yanda kanshi yawani saramai kaman zai tarwatse ya yatsine fuska cike dajin azaban sarawan kan, da sauri Aabid ya ijiye system dinshi agefe ya matsa kusadashi tareda daura hanunshi akan kanshi yace "are you okay Aadil bakada lafiya ne? Kanka kema ciwo?" bude ido Aadil yayi ya kallai ya girgiza mai kai yace "am fine, kaina ke dan ciwo" yay maganan yana kwantar da kanshi kan kafadar Aabid yana sauke ajiyan zuciya ahankali yana tunanin flash din abu daya gani yanzun nan, shiru Aabid yayi kafin ahankali yace "wait lemme go and make coffee for you kasha, namaji u are trying to run temperature" daga kafadar Aabid din yayi, Aabid yatashi yafita daga dakin, yabi bayan Aabid din da kallo ganin ya ramemai sosai tsakanin jiya da yau kaman mai tunanin wani abu, sake lumshe ido yayi yana tunanin Hamida data dagulamai lissafi gabaki daya. Ko kadan baimaji shigowan Aabid ba saidai karan ajiye mug yaji akan table din gaban kujeran hakan yasa ya dago kai ya kalli Aabid din daya ijiye mug din yana nazarin shi, zama yayi kusada Aadil din yana mikamai wayar dayake hanunshi yace "are you sure you are okay Twin" gyadamai kai yayi ahankali batare daya iya furta wata kalma ba, dafamai kafada Aabid yayi yace "stop thinking about the past Aadil, karungumi kaddara duk yanda tazoma you have us and u have your beautiful wife, matarka yarinya ce tagari, kagode ma Allah kawai and move on okay we are all here to support you, this is a second chance Allah yabaka make use of it, ga wayanka nan Mami tabani nakawo ma" karban wayan yayi ya rungume a kirjinshi yana kallon Aabid din wasu siraran hawaye suka zubo ta gefen idanunshi da sauri Aabid yarikeshi cikeda damuwa sosai kaman zaiyi kuka yace "kaga tell me wats wrong with you, you are driving me crazy Dil, am so worried" girgiza mai kai Aadil yayi yace "i don't know Bid, bansan meke damuna ba, but deep down inaji ajikina kaman zan mutu anytime soon" chak Aabid ya tsaya yana kallonshi ko kyafta idanu bayayi maganganun shi ya mugun dakanmai zuciya bana wasaba, kallonshi Aadil yake ganin yanda yayi yasa yabude baki zaiyi magana asanyaye Aabid ya daura hanunshi kan bakin nashi yana kallonshi cikin daure fuska yace "are you mad eh Aadil?" yay maganan yana kaimai duka a kafada idanunshi natara hawaye, yace "are you mad eh? Mesa kakemin maganan mutuwa? And wayafadama yanzu zaka mutu Allah shine masanin gaibu, i just got you back karka karamin maganan mutuwan ka idan kasake bazan karama magana ba kaji ko" yay maganan hawaye na gangaromai daga ido gyadamai kai Aadil yayi yana kokarin tsayar da hawayen dake fitomai daga ido rungumeshi Aabid yayi yamai kiss a goshi yace "koma mekakeji u are not alone, we going to go through it together Aadil, kaine kadai dan uwan daya ragemin yanzu banson in rasaka" ahankali Aadil yace "me too Bid" "let's go out, zomuje muyi many many things outside and have fun zakaji dadin jikinka, tashi jeka shirya kazo" kallon fuskar Aabid din yayi ahankali yamika ma Aabid din hannu hakan yasa Aabid din yabi hanunshi da kallo kafin yasa nashi acikin hannun ya kalli Aadil din kaman yanda yake kallonshi, a natse Aadil din yace "meke damunka? Something has been bothering you i can feel it a zuciyata kana cikin matsala wat is it wat is the problem? Your problem is our problem ko Bid we are one, you've been thinking tun jiya banso kamin karya just tell me menene? Meke damunka?"







Girgizamai kai Aabid yayi yana danne zuciyarshi dankar ya fahimci komi game dashi, ahankali yace "bakomi kaina keta ciwo last night saisa nai wani iri" kafeshi da ido Aadil yayi dan bai yarda da maganan shi ba ko kadan hakanan zuciyarshi taki natsuwa taki aminta da maganganun, ganin yanda Aadil din ke kallonshi yasa yatashi da sauri yay bathroom yana tafiya ahankali yace "lemme shower kaje ka shirya kaima" yabude kofar bathroom din ya shiga yarufe, binshi da kallo Aadil yayi dan yanda yayi yanzu yakara tabbatar mai da wani abune ke damunshi ba ciwon kaiba da sauri yatashi sabida yanda yaji zuciyarshi taki natsuwa ya shiga duba dakin, pillows din gadon ya daddaga amma baiga komiba, side drawer ya bubbude nanma baiga komiba, wayar Aabid din daya gani akan gado ya dauka yana budewa yaga ba password hakan yasa ya shiga dube duben wayan amma baiga komiba harzai ajiye wayan yaga watsapp message ya shigo daga Dr Sham "get well soon" da sauri ya shiga watsapp din yabude Dr Sham din, maganan Aabid ya gani  kafin reply din Dr Sham " _na am fine now Dr i took d drugs"_ da sauri ganin baida lafiya ne da gaske yasa  yay scrolling sama dan yaga meke damunshi, idanunshi ne ya sauka akan maganan Dr yace _"you haven't told me the problem, Hussain u are too young to be suffering from heart disease!"_ wani irin faduwa gabanshi yayi ganin heart disease da sauri ya zauna kan gadon yana dafe kirjinshi dake bugamai way too fast, ya shiga reading chat din ahankali daya bayan daya.

_"i used to be a bad boy Dr, inabin mata, ina shan alcohol sometimes su kadaine abinda nakeyi idan rage tunanin dan uwana barin ma idan yana tsaka da ciwo, kullum kuka nake in rasa kwanciya hankali sainaje nasha giya sanan zan manta, my brother, my twin brother is not okay almost every every month saiya kwanta a asibiti, my brother is my life ina sonshi sama da komi aduniyan nan idan kacire iyayen mu, wata rana a Lagos nahadu da yarinyar da i fell for her at a glance, My Jewel! My Amatullah!"_ chak Aadil ya tsayar da karatun jin sunan Amatullah ahankali ya furta sunan Amatullah, dan yaji su Mum sun kira yarinyar nan na dazu Amatullah, cigaba da karatun yayi..

_"my Hamida!"_ tsayawa Aadil yay chak kanshi yawani irin sara yana ganin flash din fuskar Hamida a idanunshi tanamai murmushi tana kiranshi "My Aadil, stop crying to" dafe kanshi yayi ganin yasoma tuna da yacigaba da karanta message din da kyar.

_"I saved her lokacin datai drowning a ruwa, Dr Sham i love her, i just fell for her naturally, inasonta sosai with all the fiber in my body with all my soul, i love Hamida with all my mind, my heart and soul, and right then bayan nakaita asibiti i confess my love for her cus i understood she was d one for me, mine, dudda she was afraid of me i get to understand that she's a girl that hardly get comfortable around men lemme say mutane ma in general, bayan mun rabu, yan uwanta sunzo sun tafi da ita i was dreaming about her, babu randa zanyi barci na farka banyi mafarkin my Jewel ba, unfortunately my brother as well fell in love, he fell for her as well, funny right yanda twin brothers fell for mace daya, cikin ciwonshi bama tareda ya ganta ba tun amafarki yafara sonta"_ tsayar da karatun Aadil yayi kanshi na saramai komi na dawomai kadan kadan ya dafe kanshi dakemai zafi sosai kaman an kunna wuta.

_"maganan shi alokacin shine take me to she! She! Bid she! Ranan daya fara ganin Hamida was randa yafita shida Mami, dayaga Hamida saida yaja accident ahanya yafita yabita har gidansu har aka koresu ita da shi, atare mukazo muka gansu with the help of police dats d second time danake ganin Hamida, the way naga my brother hugged her touching her yana mata shagwaba playing with her saida yasa naji kaman an chakamin kibiya azuciyata, da kyar na iya na daure inata kallon Hamidan da at that instant nagane akwai strong connection and bond tsakanin ita da my twin dan she's always free with him, bazaka tabajin maganan Hamida ba sai tana tareda Aadil, her smile her teeth saitana tare da Aadil, bakajin maganan ta tana surutu saitana tare dashi, we took them both home kasan ranan danai worst mistake?"_ ya tambayi Dr yacigaba

_"ranan danaga yana kokarin sama Jewel chocolate abaki yana mata all sort of things tanamai murmushi tana lallashin shi sosai zuciyata tai baki i was madly jealous, i don't know Sanda nai raising hand dina on my brother inacemai yadena kiran Hamida his wife, banyi considering nashi ba banyi considering condition dinshiba namai duka sosai sabida kishi ina dukanshi yana kuka inajin zafin yanda nake dukanshi ajikina nima but i couldn't help it, ranan i cried my life out for beating him najamai ciwo har saida akai admitting nashi a hospital, daganan from how things were going saina fara lallaba kaina ina lallashin kaina  inason Hamida but my brother needs her more har akazo akasa ranan lallaba kaina nakeyi battling with depression dan i was seriously depressed ni kaina bansan lokacin danai ma Hamida wanan strong so dinba, banfadan ma kowa halin danake cikiba ranan daurin aure kasa daurewa nayi nabar garin straight to wurinka a hospital a Lagos sabida ciwon danakeyi harkai admitting dina bayan naji sauki na koma gidana a VGC nakira Vanessa nafara all sort of things just to stop thinking about Hamida, my brother's happiness is everything to me Dr Sham, Hamida is blessing to his life saisa na daure, karka damu ciwo baya kisa saidai idan lokacin ne yayi i will be fine zan cigaba da shan magungunan daka rubutamin"_ yanda gaban Aadil ke bugawa kanshi na vibrating abin yadawo kaman ana tariyo mishi lokacin dayay haukan  yana ganin komi daya faru yasa ya shiga dube duben dakin har ya jawo side drawer yaga wata yar box bude box din yayi nan yaga drugs din heart dayawa fashewa yayi da kuka sosai ya taushe baki komi nadawo mai yace "no no no, najama dan uwana ciwo" daidai lokacin Aabid yabude bayi yafito tsayawa yayi chak ganin Aadil idanunshi sunyi jajir yana rike da magungunan shi na ciwon zuciya yana kallonshi hawaye na zuba, da sauri yay wurin Aadil din yana rike da magungunan yanunamai magungunan cikin fushi yace "mesa kamin karya Bid why did you lie to me?" saukar da idanunshi Aabid yayi kasa yakasa magana chakumeshi Aadil yayi idanunshi sunyi jajir yace "you lie to me Bid, you are sick ka boyemin, you think i cannot take care of you? I can't give you wat you want and i will judge you ko? Aabid!" yakira sunanshi kaman zaiyi kuka hakan yasa Aabid ya dago kanshi ya kallai, ahankali Aadil yace "you love Hamida! Nasan komi, Kanason Hamida tun ranan daka fara ganinta, kanason Hamida sosai kazaci bazan iya barma Hamida ba? Now i remember everything, natuna komi, Aabid i remember yanda kake kula dani, I remember yanda kake rike dani kana tareda ni tun ranan da aka fara sakamu a nursery school a UK, i remember yanda kake kuka koda faduwa nayi akasa, i remember yanda idan banda lafiya bazaka ci abinci ba ni ciwo kaima ciwo sabida ni haryau kana suffering from ulcer, i remember yanda kake amfani da rigan jikinka ka sharemin miyau danake dilalar wa, i remember yanda nakeda saurin fushi i will not talk to you but u will stick around kanamin murmushi harsai nadawo normal, i remember yanda kake sona nida kai were inseparables, Hussain i remember each and every single memory of my past, duk abinda kakeso aduniyan nan sainama shi you are all i have, kaine jinina, kanina, dan uwana, abokina, abokina rayuwata and komi nawa, zan iya sadaukar ma da komi aduniyan nan, am leaving Hamida for you, zan saki Hamida!" yafada hawaye na rolling down his cheeks yana kallon Aabid din dake kallonshi.




Good morning readers, like i said ni makarantana nakema rubutu and am at your service after all you guys paid for it.

Please vote da Aabid da Aadil wanne yafi dacewa da Hamida, wanne kuke so? This book is love o, romantic love story, so feel free kufadamin, thank you. 

Aadil ☑

Aabid ♾






Wanan page din harda na  jibi nahada muku, jibi bazanyi typing ba, love you🥰 don't forget to vote and lemme hear reasons dinku.


No comments

Powered by Blogger.