Duk Karfin Izzata Book 1 Complete


 *💫STAR LADY💫*

https://chat.whatsapp.com/Cx1u7E8LUUX1XY8pJeHfMO


*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 1*
            

💖الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر💖




London United Kingdom


  Wasu haɗaɗun samari ne zaune  awani katafaren palo mai girman gaske,Mai ɗauke da manya manya sofa set 2,launin Brown da ratsin milk, gawasu triple staircase ɗaya ta bangaren hagu ɗaya bangaren dama ɗayan kuma a tsakiya daga gefe kuma wani haɗaɗen table ɗin chin abin chine, ga wata makekiyar Tv a gefe guda,palon yaji komai da ake buƙata dan in nache zan tsaya zayyana muku ha'ɗuwar palon nan tofa sae mukare littafin nan a palo kawae, kae dakaga wajen kasan baƙara min dukiya aka narka awajen ba,"zaune suke,shiru ba mai magana " kowa da abin dayake fuskar nan tasu kuwa tamkar an aiko musu da sakon mutuwa " gasu kyawawa sosai kamar larabawa

Farare ne sosai  dukkan su kamannin su ɗaya kallo ɗaya zaka musu kagane yan uwan juna ne amma biyu dake zaune a saman sofa mai zaman mutun 2 nan,sunfi kama da juna sosai dan kuwa kamar an tsaga kara, haka suke suna da dogon hanchi sosai, ga manya manyan ido sai dai abun mamakin kowa dakalar idansa biyu daga chikinsu dake zaune saman sofa guda kwayar idansu ash colour ne biyun dake gefe kuma idan nasu light green ne shikuma ɗayan idan sa baki ne, ga idon nasu manya manya " ga ɗan karamin red lips, ga lallausan bakin saje kwanche a guskar su, sai dai uku daga chikin su gemun su bai da tsawo sosai san nan kuma suna da gashin kai mai tsawo har baya kamar mace.

 "wani haɗaɗen saurayi ne ya sauko daga staircase ɗin tsakiya yana faɗin haba DON yabaku'shiryaba Aryan Aiman yusuf Ahmad me kuke jira

 (nikoh nache daman wayannan turawan sunajin hausane)  

ɗago ido DON yayi  "wadda shi idansa ya kasanche light green ne,yana faɗin "shirin zuwa in kuma Khalid,Akule khalid yace "shirin zuwa Nageria mana ko kun manta gobe za'a ɗaura auren hisham,mike DON yayi yana faɗin "bazanje ba nikam san nan yanufi saman stair ɗin  ban garen hagu,da sauri khalid yajuya daniyar yasha gabansa,Yusuf yamike yarike sa, a'fusache khalid Yajuyo yana faɗin "yusuf kasakeni " Yusuf ya ɗago ido shima dai idan nasa light green gasu manya manya masu kyan gaske yache "aa khalid bazan sakekaba kafasan kokabishi ba chanza magana zaiba saidaima kubata,yakamata ache idan dasabo kasaba ɗan kasan, yaya prince fa idan yayi magana to yayine baya chan zawa, shiyasa muka chanza masa suna daga prince Safras muka maidashi DON, dan in yayi maganafa  it's done angama baya chanza wa "pls yusuf ka kyaleni wlh yau kam dole DON, ya chanza magana haba dan allah ai kobazaije bikin kowaba dole yaje na hisham, saboda tare muka taso gaba ɗayan mu, dukkan mu abu ɗaya'ne chewar khalid "ɗaya daga chikin matasan dake zaune saman sofan ne yamike yache "to ni ma dai ba zuwa zanyi ba, yana gama fadin haka yajuya yanufi stair ɗin  ban garen hagu "a fusache yusuf yajuyo yana binsa da kallo yace what wae Aryan meyake damun kune "ɗaya daga chikin su'ma yasake mikewa yana faɗin to dai kunsan tsakanina da Aryan,  babu ban ban chi, idan yayi abu, nima zanyi idankuma bai yi'ba nima bazan yiba, dan tare aka haife mu kuma tare muke komai, yana kaiwa nan ya juya shima yanufi stair ɗin bangaren dama " kwashe wa da dariya Ahmad yayi, yana fadin amma Aryan da Aiman yan iska'ne wlh anafaman kashe wutar da DON yake kokari kunna'wa su kuma zasu kunna nasu. "akule yusuf yache kaikuma Ahmad menene hakan to ae wan nan ba abun dariya bane,ae ko zakuyi'wa, kowa irin wan nan rashin mutunchin tofa banda hisham, kar'kamanta fa tare muka taso, tare mukeyi duk wani abun daza muyi komai namu iri'ɗaya duk da iyayen mu ba ɗaya ba, katashi muje mushawo kan DON  tukunnan muje musamu yaya Aryan, dan shine matsalar idan yache zaije tofa Aiman mai sau'kine, dan shi duk abun da Aryan ya aika'ta shima ae'katawa zai yi "  kama hanyar tafiya khalid yayi yana faɗin wlh yau DON ya batamin rai haba dan allah " da sauri  Ahmad ya rufe'masa baki da hannun sa yache ya isa yanzu dai muje mushawo kansu dan sulhu muke nema dasu ba faɗa ba "faɗa masa dai chewar yusuf " haurawa saman stair sukayi wani  katafaren  hadadde palo suka shiga "  palan ya tsaru iya tsaruwa komai na chikinsa farine tas harta labulayen suma farare ne tas ga manya manya sofa set ɗaya gawani makekiyar plasma TV dake gefe,babu kowa a palon sae karan AC dake tayi, kai tsaye suka nufi chikin betroom ɗin,"subhanallah tsarki ya tabbata ga ubangiji jama'a ninaga aljannar duniya,manya manya sofa set ne,set 1 ga wani ɗan karamin table a tsakiya,gefe guda kuwa wani katafaren gado wadda ko mutun 10 zasu iya kwan chiya a kae, daga ɓan garen hagu kuwa kofar dressing room ne,sae kofar toilet kusa da dressing room ɗin, betroom ɗin ya tsaru'ne sosai idan nache zan tsaya zayya no muku tsaru war batroom ɗin nan to zamu kwana mu wuni bamu gama ba"kwanche DON yake akan katafaren gadon'sa dake shin fiɗe da white bet shit,kwan che yake ya miƙe kafar'sa har tawuche gadon tsawo,ya chire rigar sa faffaɗar kirjin nan nasa abuɗe ga wani gashi dark black mai tsantsi kwan che a kan faffadar kirjin nasa, damtsen hannun nan nashi kuwa tamkar zasu fashe,saboda karfi, kamar wani sa'daukin yaƙi,"yana'jin shigon war su Khalid amma ko kallan inda suke baiyi ba
 yusuf ya wuche wajen courting ɗin yasa hannu ya yaye,wata kofar glass ne ya bayyana awajen daga chikin daki kana kallan me a wajen,wajen shaƙa'tawane mai dauke da runfa da kugeru awajen da wata table a tsaki yar kugerun, agefen kuwa wani dan karamin pool ne mai kama da baf ɗin wanka, yana ɗauke ta sky blue ruwa 

"DON pls katashi muna'san magana, da kai ne chewar Yusuf" shiru DON yayi  kamar baiji su ba "hayewa gadon Khalid yayi,yana faɗin  pls prince katashi mana, ko kallan inda suke DON bai yi'ba bare su sa ran zai amsa musu, "haba big bro dan allah to imma bazaka tashi ba,pls kaba mu amsa dan awan nan karan ba shiru muke san kayiba, kanaji koh chewar yusuf " DON dae bai tanka su ba "a fusace Ahmad yace look DON dan Allah kar ka che bazakaje bikin hisham ba wlh idan kayi haka baka kyauta ba,kasani hisham fa jinin mune " dogon tsaki DON yaja atakai che yace in kungama zanchen naku saiku fita kubar'min ɗaki, dan kuna damuna wlh " afusa'che Khalid yafara magana wlh bazamufita mu zakawa iskan'chi to barikaji dole kaje bikin hisham, in bahakaba sai dai kazaba ko,mu kokuma ka kasanche kai kadai "a'takaiche DON yace ae daman ni ka ɗae nafijin daɗin rayuwa  "haka kache koh, baisake che musu ko uppan ba haka sukayita surutun su har suka gaji sukamike suka fita suna fita " DON ya daukoh wata remot ya saita'ta saitin kofar dakin  ya danna remot din jikake lok lok kofar tana kulle kanta,ajiye remot ɗin yayi yajuya yana fiskantar wajen shaka tawan,  

 Su yusuf kuwa suna fita dakin, DON ɗakin, Aryan suka nufa wani ɗan corridor suka bi ɗan tafiya kaɗan sukayi suka shiga palo Aryan, komai na palan iri ɗaya ne dana DON sai dai na Aryan ash colour ne babu kowa a palo kai tsaye betroom ɗin sa suka nufa,da sallama a bakinsu suka shiga, Aryan yana zaune yana aiki a laptop shikuma Aiman na kwanche yana latsa waya " chikin ladabi da neman sulhu yusuf yafara magana wai me hakane bro,baikamata muyiwa hisham haka'ba,pls kar kuche baza kuje ba " daga Aryan har Aiman ɗin ba wan da ya tanka yusuf " akule yusuf yakuma chewa pls wai meyasa ku keyin hakane dan Allah " yusuf idan fa yaya Aryan ya yarda zaije nima wlh zan je, amma in bazai jeba takin takalmi babu inda zanje nima chewar Aiman " juyo Yusuf yayi yana kallan Aryan da ko kallan in da suke su bai'yiba  bro dan allah kar kache bazakaje ba' dan wlh ko bazakaje bikin kowa ba ya'zama dole kaje na hisham dan kuwa hisham yazama tam kar jinin mu ya'zama tamkar ɗan uwan mu,a'fusache Aryan yajuyo' yana faɗin  "kasan dai bani da yayan daya wuche DON koh to ko bikin shi ake bazan jeba " a'fusache khalid yache wai meyasa bakuda hali mai kyau ne dan allah, daurin aurefa kawai zakuje,"shiri Aryan yayi bai sake tan kasu ba yachi gaba da aikin sa " yusuf kuwa kallan Aiman yayi yace bro zo muje waje muyi magana

 palon suka fita, yusuf yayita lallaɓa Aiman har ya yarda zai bisu "kowa ya nufi ɗakin sa dan shirin tafiyar, 

shir'yawa sosai sukayi suka fito suka haɗu a babban palo,"to bari na tambayo mana Aryan sae muyi using jet nashi koh chewar yusuf ya karisa maganar yana hayewa stair ɗin yanufi dakin Aryan, a kwanche ya same sa yana latsa waya, harara Yusuf ya wunga masa kafin yache zamuyi anfani da jet naka "batare da ya kalle'sa ba yache adawo lfy "  juyawa yusuf yayi yafito, yasa mu su Khalid a palo suka jera zuwa waje motochi 4 suka ɗauke su zuwa Airport, Khalid Yusuf, suka shiga mota ɗaya Aiman Ahmad suma motar su ɗaya, saura moto chi 2 kuma sojoji yaran Yusuf ne a chiki, a jere motochin suka chera da matsakai chin gudu suka miƙi hanyar fita daga gd, da sauri security dake bakin gate suka wan gale  katafaren gate ɗin, a hankali suƙa danna han chin moto chin waje,suna fita su ka karawa motochin gudu, sosai suke sharara gudu chikin kan kanin lokachi suka isa Airport, suna isa suka tarar an gama shirya komai su ka ɗai ake jira su tashi, basu wani ɓata lokachi ba suka fito daga motochin,suka nufi jet ɗin Aryan suka shiga suka zauna ba wan da yache da ɗan uwan sa kala kamar an musu zuwa dole karfe 7 na safe jirgin nasu ya ɗaga suka lula a sararin, sama'niya sai babban birnin tarayya Abuja Nigeria

Jirgin su na sauka a Airport na Babban burnin ta'rayya, dan kara dan karan motochi masu numfashi ne sukazo ɗau kan su, wan ɗa a'kallah yawan motochin zasu kai 8 ga kuma motochin 5 na sojoji abaya " wasu jib ga jib gan sojoji guda 4 ne suka diro kasa daga samar motar su fiskar sun nan babu annuri ko kaɗan riƙe suke da manya manya Gun a hannun su, su na takawa irin takun jaruman maza,suka nufi su Yusuf, da sauri biyu suka tare bayan su biyu kuma suka tare gaba, Yusuf kuwa sae taku yake kamar wani sa dauki,har suka karisa wajen motochin,da sauri sojojin dasu gaban su suka fara buɗe musu kofar motochin, Khalid da Yusuf suka shiga mota ɗaya Aiman da Ahmad kuma suka shiga mota ɗaya,hannu sojojin suka ɗaga suka sara wa Yusuf san nan suka rufe kofar motochin,da gudu suka juya suka nufi nasu motar, sauri sauri suka motochin key, da matsakai chin gudu suka bar Airport ɗin,suka miki shin fi ɗadɗiyar titi gudu suke shararawa sosai har suka kusa chikin anguwar wuse 2 bakin wani katafaren gida na alfarman kae kaga ganin gidan kasan ya tsaru,suna karisawa bakin gate ɗin suka rage gudun motochin nasu, wani soja dake zaune kan plastic chair ne ya taso da sauri ya wan gale musu katafaren gate ɗin, kusa motochin chikin gida sukayi kai tsaye parking space suka nufa suna kashe motochin sojojin suka fito da sauri suka buɗewa su Yusuf kofar motar, a nitse suka fito,jingina da jikin motar Yusuf yayi yana bin gidan da kallo,gidan part 4 

wani saurayi ne yafito daga ɗaya daga chikin part na gidan ya nufo su Yusuf yana ɗan murnushi, da sauri ya karisa wajen yayi hugging na Yusuf yana faɗin Wellcome,my brother's bai jira amsar Yusuf ba yasake sa yabi su Khalid ma ɗaya bayan ɗaya yana hugging nasu, bayan yagama hugging nasu ne ya dawo da kallan sa kan Yusuf yana faɗin,"Yusuf DON da Aryan basu zo bakoh "sorry hisham Yusuf ya faɗa yana ɗan sosa kai, murmushi hisham ya ɗanyi yana faɗin bismillah muje chiki,gaba yayi suka bishi a baya,part nashi suka nufa,a haɗaɗ'ɗiyar palon sa suka zaune, shiru sukayi ba mai magana dan duk kansu ba masu yawan surutu bane almost 15 mnt Yusuf ya katse musu shirun da chewa, " Hisham ana gama daurin aure nanfa, zamu wuche kano,da sauri Hisham ya ɗago yana faɗin "haba yusuf sai kace ko rin ku ake dan Allah kun fa San ni bani da wani friends Sai ku taya kuke san naje wajen dinner ba friends, "aa Hisham tun dana che maka ana ɗaura aure zamu wuche tofa sai mun tafi,dan kuwa mu iya ɗau rin aure kawai mu kazo "nasani Yusuf amma pls ku bari sae gobe ku wuche,mikewa Aiman yayi yana faɗin "yau zamu tafi ba sae gobe ba kuma karfe 4 dai dai zamu bar garin man ko an daura auren ko ba a daura ba yana gama faɗin hakan yanufi waje, girgiza kae kawai Khalid yake, shiru Hisham yayi dan kuwa yasan ko me zai che musu bazasu tsaya ba tunda su kache yau zasu wuche tofa ba abun da zai hana su tafiya,dan duk chikin su ba mai magana ya sauya in sun yi magana sun yi ne ba chan'ji,shiri suka zauna palon ba wan da yasake chewa ko uppan

 Aiman kuwa yana fitowa waje kai tsaye inda sukayi parkin na motochin su yanufa, da gudu ɗaya daga chikin sojojin dasuka zo dasu ya nufo shi buɗe masa mota yayi,Aiman yashiga ya zauna,ya zuro kafar sa waje ya chiro wayar sa yana latsawa, gefe sojan yakoma ya tsaya yana jiran permission su tafi almost 20 mnt yana zaune yana latsa wayar sa, ɗago kai yayi zai yiwa sojan magana sai wayar sa tafara ringing,bin screen ɗin wayar yayi da kallon ganin sunan Aunty Mardiya che ya sashi  jan dogon tsaki,har wayar ta katse bai ɗaga ba kira na 2 yasake shigowa, tsaki yakuma ja kafin yayi picking call ɗin ya kara wayar a kunne yana faɗin hello, daga ɗayan ɓangaren "Aunty mardiya tace hello Aiman ykk " daure fuska yayi kamar yana gaban ta yace lfy ykk " ina lfy wai da gaskene kun shigo naija "eh mun shigo sai akayi yaya "to dan Allah za kuzo gida na,tsaki yaja kafin yace "wai meyasa kekam Aunty mardiya baki da wata matsala ne arayuwan ki kedai burin ki kawai a zo gidan ki, kin dai san baza mu zoba "dan Allah Aiman ka daina faɗin hakan kaji pls kuzo mana koda 5 mnt mu gai sane  kawai,ni kasan da za abar ni nazo na gan ku wlh da zanzo,duk da niche babba " Aunty mardiya sai anjima kuma baza mu zoba yana gama faɗin haka ya katse kiran, ɗago ido yayi zai yiwa sojan magana idan sa ya sauka kan wata budurwa dake tsaye a kusa da mur fin motar kawar da kan sa yayi kamar bai ganta ba, chikin ran gwaɗa ta karaso gaban sa ta kashe murya tana faɗin "aslm ykk, tam kar bai san da mutun awajen ba, sake matsowa tayi kusa dashi sosai har kamar zata taka masa kafa "tace sunana Zubee,kuma ni babban kawar amarya che nasan kaima kana ɗaya daga chikin friend ɗin ango Ko,shiru Aiman bai ko kalli inda take ba bare tasa ran zai amsa mata, sake kashe murya tayi tana faɗin haba ƙyaƙkyawan saurayi inama magana kana share ni me yayi zafi kodai ban maka bane, "wani tsawa ya mata leave this place, jin hakan yasa sojan ya karaso wajen da gudu ita kuma zubee  tsabar tsorata sai da jakar hannun ta ya faɗin jiki na rawa ta duƙa kasa ta ɗauki jakar da gudu tabar wajen,a fusache yabawa sojan umarni daya shiga motar yaka sutafi, da sauri ya shiga ma zaunin driver shi kuma Aiman ya mai da kafar sa chikin motar ya rufe marfin motar da sauri sojan yama motar key yaja suka nufi gate security suka gan gale masa gate ɗin ya danna han chin motar waje gudu yake shararawa sosai"oga ina muka nufa sojan ya tambaya yana kallan face ɗin Aiman ta chikin miro " hotel Aiman ya bashi amsa a takai che gudu sosai sojan ke shararawa da motar chikin kan kanin lokachi suka isa wani katafaren hotel, horn yayi a bakin gate ɗin mai gadi ya wan gale masu gate ɗin, a hankali ya kusa motar chikin hotel ɗin parking space nasu yanufa yana kashe motar yafito ya buɗewa Aiman kofar, a nitse ya zuro kafar sa waje kafin yafito gaba ɗaya, chiki reception yanufa sojan na biye da shi ɗaki ya kama ya karɓi key yawuche, shiga chikin ɗakin yayi shikuma sojan ya tsaya a bakin kofar ɗakin, a gurguje yanufi toilet yayi wanka yafito ɗaure da towel yanufi waje, sojan na tsaye a bakin kofa Aiman ya fito"Abbas kaje ka ɗauko min trolley na a mota, da sauri Abbas ya wuche ya koma mita within 2 mnt sai ga Abba ya dawo rike da trolley, Aiman na tsaye a bakin kofa,Abba yazo ya miƙa masa trolley ɗin,ansa yayi ya koma chikin ɗakin Abbas kuma ya gyara tsayuwar sa a bakin kofar, jallabiya baka Aiman ya fitar yasa,da sauri sauri ya haye gado ya kwanta ba jimawa barchi yayi awan gaba dashi

Around 1:20 su Hisham sungama shirin zuwa wajen ɗaurin aure Hisham na sanye chikin dakakkiyar shadda fara tas,ya sanya kula baki da takalmi baki, Yusuf kuwa sanye yake chikin wandon jeans baki da t-shirt ash ya gyara gashin kan san nan kamar wani balarabe, Khalid na sanye chikin blue jeans da white t-shirt Ahmad ma na sanye chikin blue jeans da black t-shirt dukkan su sunyi kyau sosai "wae ina Aiman ne Hisham ya tambaya yana kallan Yusuf " guntun tsaki Yusuf yaja yana faɗin oh bari dai na kirasa awaya muji chiro wayar sa yayi daga aljihu yanufi waje yana kiran layin Aiman ɗin 

Hotel 

Aiman na chikin barchi yaji wayar sa  na ringing wani dogon tsaki yaja, batare daya buɗe ido ba yasa hannu yana lalubar wayar da kyar ya isa ɗauko wayar dan har kiran ta kusa yan kewa da kyar ya iya ware idon sa dan barchin daya masa yawa picking call ɗin yayi yana faɗin wae dan Allah Yusuf me namaka ne da kake ta'kurawa rayuwata "Yusuf yace amma gaskiya Aiman baka kyauta ba dan Allah menene hakan wato ma barchi kaje kake koh to kazo mutafi ɗau'rin auren lokachi yayi chewar Yusuf, a fusache Aiman yace "bazan jeba yana yana kai karshen maganar batare daya jira amsar yusuf ba ya katse kiran yayi wurgi gefe da wayar ya chigaba da barchin sa

Yusuf kuwa Aiman na katse kiran ya juya jiki ba kwari ya koma chikin palon a zuchiyar sa yana faɗin wlh yau Aiman da nine yayan ka da sai nayi maganin ka, wan nan wani irin wulakanchine kan chine sae kace ba tare suka taso da Hisham ba a sanyaye ya shiga chikin palon, Hisham na ganin sa yace"Aiman ɗin yace bazai zo bako,shiru Yusuf yayi dan ban san amsar da zai bawa Hisham ba kunyar haɗa ido da Hisham ɗin yake ji, dafa kafaɗarsa Hisham yazo yayi yana faɗin karka damu yusuf nasan halin ku gaba ɗaya SO duk wani abun daya da suke gudun zuwa aure nawa nasa,ni ban ma taba tunani daman zaku so aure naba,kadai na damuwa ngd sosai da zuwan da kukayi, kasani DON da Aryan Bawai basu sona bane yasa suka ki zuwa jiya da daddare DON ya turomin 1m a matsayin gift haka Aryan ma 1m ya turamin to kaga bawai basa sona bane kawai sudai a nasu ganin dakuma tunanin su duk wan da ya raɓi mace to yaza mai rauni sukuma kasan basa san mauni sunfi san kullun su ji su zam zam,"murnushi kaɗan yusuf yayi zai yi magana Hisham yace "No badai yanzuba, yanzu kam muje lokachi yayi ana jiran mu, jerawa sukayi gaba ɗayan su suka fito harabar gidan, 
su yusuf suka shiga motochin da suka zo dasu Hisham kuwa yashiga nashi motar,suka yiwa motochin key, security ya wangale masu gate da gudu suka danna hanchin motochin waje sosai suke gudu dan sunyi latti kai tsaye babban masallachin jummaa suka nufa a harabar masallachi sukayi parking dub bannin jamaa ne suka halak chi ɗaurin auren kama daga minister's governors members har shugaban kasa muhammadu buhari yazo ɗau rin auren dashi da Shugaban kasa mai jiran gado tinibu, misalin karfe 2 dai dai na rana dubbanni jama'a suka she'da ɗau rin auren Hisham Nasir  alkali tare da matar sa ilham Abdussalam, ana gama ɗau rin aure Yusuf ya dawo chikin mota da sauri dan yaji jama'a nata faɗin ina yayan Abubakar saraki ma sunzo bikin, yana zaune chikin mota yana jin jama'a na ta neman family Abubakar saraki,amma yayi kamar bar ji ba, buɗe kofar motar da Yusuf ke chiki ango Hisham yayi yashiga ya zauna yana faɗin "yanzu Yusuf abun da kayi ka kyauta eh " ɗaure fuska Yusuf yayi yace to me kuma nayi "ka fini sanin me kayi ae ka dubi yan da jama'a ke naman ku kuzo kuyi hoto kowa Burin sa yayi hoto da family Abubakar saraki, amma ka watsa musu kasa a ido koh "kaga Hisham idan kagama dana ka jama'a mutafi dan ni yanzuma zan wuche kano, Hisham zaiyi magana Khalid ya buɗe kofar motar yashigo yana faɗin "Hisham me kuma ka zauna kake a nan baza kaje kutafi walimar bane "yanzu Khalid kuna nufin da gaske baza kuje walimar nawa ba Hisham yayi tambayar yana kallan fuskar Khalid, Khalid zai yi magana Yusuf ya riga shi da chewa "gaskiya ba zamuje ba ae nafaɗama iya ɗau rin aure kawai mukazo dan haka yanzu zamu wuche tun da angama abun daya kawo mu, shiru Hisham yayi yana tunani, ganin yanayin da Hisham ya shi gane yasa Khalid chewa, " No Hisham dole zamuje walimar taso muje ga jamaa na chan na jiran mu,jiki ba kwari Hisham ya fito daga motar Khalid na rike da hannun sa suka bar Yusuf a chikin motar,

Fito Yusuf yayi ya kira sojojin sa tare da basu umarnin akan su wuche Airport dashi, da sauri suka shiga mota suka wa motochin key suka bar masallachi sae tsaye Airport suka nufa, jirgin kasuwa Yusuf yabi yabar wa su Khalid jet ɗin Aryan a Airport ɗin tare da sojoji 2 ya tafa ya nar biyu su taho dasu Khalid, 

Karfe 3:45 jirgin su ba yusuf ya sauka a malam Aminu Kano international Airport,bai sanar da kowa zu'wan nasa ba ba wan dayazo ɗaukan sa motar haya suka hau shida sojojin nasa suka nufi gd, a bakin gani gidan sarki mai motar ha'yan ya ajiye su sauƙa Yusuf yayi ya biya sa kuɗin sa yanufi chikin gd sojojin na biye dashi, ɓangaren sa yanufa natare daya shiga chikin gd ba a bakin ɗan karamin gate na shiga ban garen nasa sojojin suka tsaya shi kuma ya wuche chiki, wanka yayi a gur guje ya zura jallabiya ya kwanta ba jimawa barchi yayi awan gaba dashi

Aban garen su Khalid kuwa ansha walima duk chikin su Khalid ne kaɗai ya halak chi walimar karfe 4 dai dai a ka tashi taron, wajen holl ɗin Khalid yafito da sauri yana kiran layin Yusuf, wayar tayi ta ringing sai da ta kusa katsewa Yusuf ya ɗaga chikin muryan barchi yace,"hello "ina kake ne  Yusuf lokachin tayi fa yayi "ina kano mana " kano kuma Khalid ya tambaya yana riƙe haɓa "wani dogon tsaki Yusuf yaja yana faɗin kaga Khalid dan Allah ka kyale ni wlh bar chi nake kata dani " to yanzu Yusuf mota kake so mubi zuwa kano ne kokuma me menene dazaka dafi kabar mu "oh my god nima Khalid bada jet na zaba jirgin kasuwa nabi jet ɗin na Airport na bar muku, yana gama faɗin hakan ba tare daya jira amsar Khalid ba ya katse kiran, bin wayar da kallo Khalid yayi yana faɗin ya Allah ka shirya min yaran bappa ba mutane ne sai kache wasu aljanu bazaka taba gane kan suba in sun juya ba mai iya juyo su, layin Aiman yafara kira again har ta katse Aiman bai ɗaga ba, tsaki Khalid yaja yasake kira, wayar nata ringing har ta kusa katsewa Aiman yayi picking, "ina kake Aiman Khalid ya tambaya a fusace, chikin muryan barchi Aiman yace " wai dan Allah menene naha bazaku bar mutun yayi bar chin sa ba "au barchi ma kake ke nan to wlh sai dai ka kwana a Abuja dan tafiya ta,zanyi, wani dogon tsaki Aiman yaja yana faɗin to a sauka lfy san nan ya katse kiran, Khalid kamar yayi wurgi da wayar dan haushi haka yasake hakura yafara neman layin Ahmad kira ɗaya Ahmad yayi picking " ina kake chewar Khalid "haba Khalid ni karamin yaro ne da zaka min irin wan nan tambayar, a fusace Khalid yace to wlh idan ba kazo Airport nan da 20 mnt ba tafiya ta zanyi na bar ku " to yaya Khalid a Allah ya sare hanya yana kai kar shen maganar ya katse kiran, a fusache Khalid ya juya yanufi motar su yana faɗin wlh ku kam idan mutun ya biye muku zaku kashe sa da bakin chiki, chikin mota yashiga driver ya ja motar da gudu suka nufi Airport, abun ma maki ko da yaje Airport ɗin zaune yasamu Aiman da Ahmad chikin jirgin suna jiran sa dan bakin chiki ko sannu bai che musu ba ya shiga jet ɗin shima ya zauna suma ko sannu basu che masa ba har jirgin su ya ɗaga 
 
Karfe 6 na yamma dai dai jirgin su yayi landing a malam Aminu Kano international Airport kano basu wani ɓata lokachi ba suka fito shiri suka tsaya sai yanzu suka tuna basu sanar da zu wan su ba wan daya zo ɗaukan su wuche Aiman yayi ya fita Airport ɗin ya tari motar haya yashiga abunsa, ganin Aiman shiga motar haya ne yasa suma suka fito suka tari motochi biyu na haya suka hau suna nufi gd a bakin gate sukache da mai motan ya tsaya suka sauka,suka Biya shi suka nufi chikin gd,kowa ya nufi ɓangaren sa Khalid kuwa yanufi babban gate ɗin ya shiga chikin gd a dai dai bakin gate ɗin ya haɗu da Umar da haidar sosai suma suke kama da su yusuf ko ba'a faɗa ma ba kasan kannen sune "kai haidar ina yusuf Khalid ya tambaya yana kallan fiskar haidar "haidar yache nima ban sani ba yaya Khalid daman yaya yusuf na gidan nan na,juyo da kallan sa Khalid yayi kan Umar dake tsaye yana mur tuƙe  fiska "kai Umar awani ban gare Aunty farida take,kara ɗaure fuska yayi yace "kai yaya Khalid dan Allah ka shiga chiki ka duba mana mu ka daina tambayar, mu tana gama faɗin haka yaja hannun Haidar suka nufi waje, baki buɗe Khalid ke kallan ikon Allah a zuchiyar sa yake faɗin, gaba ɗayan su ƴa'ƴan bappa halin su ɗaya ba yaran ba ba man yan ba, juyawa yayi shige chikin gida, 

Wani katafaren Falo na Al'farma Khalid ya doka sallama,haɗuwar falon ya zarce tunanin me tunani yaji komai na furniture,wasu hadaddun Sofa set ne,Launin Milk colour,masu numfashi,a tsakiya kuma akwai Sofa tabls,daga gefen Hagu,Tv stand ne,baka jin sautin komai sai Sanyin A.c dake ratsa sassan jiki, yan matane 3 ke tsaye a tsakiyar palon suna goge goge da alama kuyangu ne,har kasa suka duƙa suka gaida Khalid fuska ba yabo ba fallasa ya amsa yana tambayar su "ina Ammi, "tana chikin ɗaki suka amsa masa, bai jira sun kai karshen maganar ba ya haura stair case ɗin,wani ɗan karamin haɗaɗɗen palo ne a saman mai ɗauke da sofa set 1 ash colour atsakiya kuma a kwai sofa table gefen dama kuwa wani makekiyar Tv awajen,palon ɗauke yake da ko'fofin betroom's 4 a chikin sa,babu kowa a palo sai sanyin A.c dake tashi bakin kofar betroom ɗin Khalid yanufa sallama yayi ya gyara tsayuwar sa yana jiran a masa izinin shigowa almost 7 mnt kafin a amsa masa sallamar tasa tare da izinin shigowa, tura kofar yayi ya shiga

Wata kyakkyawa mata che sosai, kamannin ta ɗaya da DON,fuskarta ɗauke da murmushi,a zaune take saman tulu irin na gidan sarauta,babbar macace A ƙalla tayi 45 years,irin hajiyoyin nan ne wanda naira ta zauna masu,jikinta na sanye da tsadadden cord lace,wanda akayi mata bubu gown dashi,duka hannayenta da wuyanta,Kayan adone na Zallar zinayi, karisawa chiki Khalid yayi ya zauna a kasa a gaban ta,chikin ladabi da girmama,yace "barka da hutawa Ammi,shafa kansa Ammi tayi yace "baba saukar yau she "yanzu nan muka zo Ammi "to zuwa babu sallama,ina sauran yan uwan naka, "prince da Aryan basu zo ba suna London "ni basu nake tambaya ba ina ruwa na dasu,murmushi Khalid yayi daman da gangan ya kawo wa Ammi zan chen DON "baba ba kache komai ba ko dai kai kaɗai kazo ne "aa Ammi ni da su Yusuf ne amma ae kin san halin su ni ko in da suke ma ban sani ba "to ka sanar da Salma kun zone "aa Ammi kamar yadda bamu sanar ɗa ku ba haka ba wan da muka faɗawa "to yaka mata ku sanar da ita dan kaga kuka ɗai gare ta ku rinka tau saya mata "to shike nan Ammi zanyi yadda kika che amma ina Aunty farida "inajin tana bangaren Ummi,mikewa yayi yana faɗin to Ammi bari na dubo ta, "ok kawai Ammi tace, yana kokarin fita daga ɗakin wata kyakkyawar budurwa tashigo wadda a shekaru bazata wuche 16 ba kyakkyawa che sosai duk kaman nin su ɗaya dasu DON da gudu tatafi ta faɗa kirjin Khalid tana faɗin "oyoyo yaya Khalid, rungume Khalid yayi shima yana faɗin "oyoyo Auta oyoyo, ina kika fito hakan nan sai kam shi kike " turo baki Zahra tayi tace daga wajen Aunty farida nake "ina take Aunty farida yayi maganar yana raba jikin sa da nata " tana ɓangaren Ummi "ok to muje ki rakani "aa yaya Khalid ni tun danaga ka nasan ba kai kaɗai kazo ba, nasan su yaya prince ma sun zo ni bazan fita ba ina tsoran su "murmushi Khalid yayi yana faɗin"kai Auta tsoran me kuma ai dani zamuje "Allah yaya Khalid shiyasa nafi son ka dan duk gidan nan kai kaɗai ne mai sona " aa Auta kowa na gidan nan na son ki "aa yaya Khalid badai kowa ba Aunty Maryam da yaya prince da yaya Aryan da yaya Aiman, "girgiza kai kawai Khalid yayi ya ja hannun ta suka nufi waje yana faɗin,Ammi mun tafi, Ammi dai murmushi kawai take tana binsu da ido..✍️



Pls more like comments and share 

*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*

💖The talent troupe writer's 💖


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 2*
       

Khalid rike da hannu zahra suka fito daga part ɗin,Ammi suka nufi part ɗin Ummi suna tafiya suna hira kamar wasu friend, a dai dai kofar da zata sada su da part ɗin Ummi, su kayi karo da yusuf  fiskar nan a daure kamar bai ma san menene dariyaba, nan take jikin zahra ya hau kerma, murya na rawa tache "inawuni yaya yusuf,bai bai amsa ba ya ra ɓa ta gefen su zai wuche, da sauri Khalid ya damki dam tsen hannun sa, juyowa Yusuf yayi yana kallan chikin idon Khalid ɗin "me kuma kake kallo na eh idan bazaka amsa gai suwar Zahra ba ni ba yayan ka bane dazaka raɓa gefe'na ka wuche " a kule Yusuf yace sorry ykk "ban sani ba Khalid ya faɗa  yana sakin hannun Yusuf ɗin,aiko kamar jira yake Khalid yasake sa da sauri ya wuche ya barsu tsaye, dawo da kallan sa Khalid yayi kan Zahra dake tsaye kamar zatayi fitsari a wando saboda tsoro"menene Auta,chikin rawar murya Zahra tace,"yaya Khalid shiyasa fa nache maka kai da Aunty farida da Aunty mardiya ne kawai kuke sona sai Aunty salma, kana ganin yaya Yusuf ko gaisuwa ta bai amsa ba bare ma ya tambayeni ko ina lfy,ta karisa maganar kamar zatayi kuka, kakalo murmushin dole Khalid yayi dan ko shi kansa Yusuf ya ɓata masa Rae "karki damu Auta muje mutafi hai ki rabu dasu tun da ni ina son ki kinji yayi maganar yana shafa kanta "to shike nan yaya Khalid muje, chiki suka nufa a kofar balon Ummi sukayi sallama kafin su shiga komai na chikin palon Ummi irin na Ammi ne har colour komai iri ɗaya 


Wata kyakkyawar mata che zaune saman sofa mai zaman mutun 2 a gaban ta kuwa sofa table ne dake ɗauke da kwan dan fruit mai kyan gaske a hankali take gatsar Apple ɗin take hannun ta fara che itama tas kaman nin ta ɗaya da yusuf a kallan zata kai 36 years, da gudu Zahra ta tafi ta faɗa jikin ta tana faɗin Aunty "farida na dawo "kai Auta zaki balla ni ai, dari Zahra tayi tana faɗin to Aunty na tashi, karisa shigowa chikin palon Khalid yayi ya zauna saman sofa mai ma zaunin mutun 3 yana faɗin "Aunty babba barka da hutawa,murmushi Aunty farida tayi kafin tace ai kune manya yanzu na bar muku girman, da sauri Zahra ta miƙe zaune tana faɗin "Aunty farida harda ni, ki kabawa girman "eh Auta har dake mana,tsalle Zahra tayi, tana faɗin nima na zama babba yan zukam, murmushi kawai Khalid da Aunty farida keyi suna kallan irin farin chikin da kanwar tasu ke chiki

  Wayar Aunty farida dake zaune kusa da Zahra yafara kara alamar shigowar kira,da sauri Zahra ta ɗau wayar tana faɗin ni zanyi picking call ɗin ni zanyi picking call ɗin," to Auta yimana chewar Aunty farida tayi maganar tana kokarin ajiye Apple dake hannun ta a chikin kwandan fruit ɗin, takawo wayar Zahra tayi dai dai sai tin fuskar ta zatayi picking call ɗin, a sukwane tamiƙawa Aunty farida wayar ta hannun ta har kema yake, ansar wayar Aunty farida tayi tana kallan Zahra da mamaKi, dariya Khalid yayi kafin yace Auta lfy irin wan nan riki chewa haka DON ko Aryan ne suka kira wayar ko, Zahra dai shiru tayi bata che komai ba, zai faman zazzare ido take
Picking call ɗin Aunty farida tayi takara wayar a kunen'ta "hello Aryan ykk, daga ɗayan ɓangaren Aryan yace lfy lau Aunty babba ykk "ina lfy y prince, bai bata amsa ba sai dai yace "kinyi magana da Abba ne "aa bamuyi ba lfy dai koh ta tambaya a ɗan ruɗe "eh to lfy kedai in kinyi waya dashi sai muyi magana " aa Aryan wlh ban yar daba za kasa nashiga tunani pls kafa ɗa min da wata matsala ne "aa Aunty farida babu komai ke dai ki kula mana da kanki kinji, bai jira amsar taba ya katse kiran, dagowa Aunty farida tayi tana kallan Zahra"Auta lfy kika nitsu haka "turo baki Zahra tayi tace ba komai, Khalid kuwa sai dariya yake musu dan yasan dalilin nisuwar Zahra, dawo da kallanta Aunty farida tayi tana faɗin lfy, bro kake kallan mu haka," lfy lau kawai ina mamakin irin son damuke miki ne, duk zafin ran DON da Aryan in zasuyi magana dake sas sauta murya suke, idan ran DON ya ɓachi gaba ɗaya gd kai bama gd kawai ba gaba ɗaya family mu ba mai iya tin karar sa sai ke komai ɓachin ran da yake chiki inya ganki sai ya sas'sauta zuchiyar sa kike ɗai kike sashi ya chan za magana inyayi abun yana bani mamaki, murmushi Aunty farida tayi kafin tace kasan meyasa gaba ɗayan ku kuke kau nata "aa ban sani ba "saboda nima ina matikar kaunar ne, duk da ba iyayen mu ɗaya ba narike ku da zuchiya ɗaya "da sauri Zahra tace Aunty farida daman ba Abba bane ya haifi su yaya Khalid "eh Auta ba Abba bane marigayi bappa usman ne baban su yaya Khalid yaya Ahmad dakuma Aunty Salma, "kai Aunty farida to ya akayi haka ni ban san bappa usman ɗin bama chewar Zahra tafaɗa da mamaki a fuskar'ta "kai Auta kiche dai tarihi kike son sani to matso nabaki tarihin a gurguje dan zanje wajen Abba,kara matso kusa da Aunty farida Zahra tayi ta kasa kunne, Aunty farida ta gyara zama tafara magana kamar haka

*Abba su uku ne awajen baban su sarki khalid awan chan lokachin, Abba shine babba sai bappa usman sai bappa Aliyu ne ƙarami kakan mu shi ya haɗa auren Abba da Ummi na alokachin, baban Ummi shine sarkin katsina ansha biki sosai, bayan auren ummi na da Abba da shekara ɗaya Allah ya albarka che da samun Aihuwa ɗiya mace kuma bakowa bace face ni, ina da shakata biyu a duniya Ummi na ta haifi Mardiya, an haifi Mardiya da wata uku Abba yace zai kara Aure da farko Ummi na taki yar da amma daga baya sai ta aminche Abba ya auro yar sarkin gombe kuma itace Aunty amarya, bayan auren su da wata 10 Aunty Maryam ta haifi ɗiya mace Abba yasa mata suna maryam,alokachin ne kuma bappa usman yayi Aure ya Auri umma'n su Khalid itama data zo ya mace ta haifa, Abba ya shiga tunani da damuwa dan yana son ɗa namiji gashi shiru shiru daga Ummi har Aunty amarya ba wan da yasake Aihuwa, wani taro dasu Abba sukaje da kakan mu garin yola a chan yaga Ammi ya dage sai ita Ammi ba fulatanan ruga che iyayen ta sunki bawa Abba auren ta amma Abba yana che haka suka hakura suka bashi Auren Ammi a kasha biki auren Ammi da wata uku tasamu chiki a tare suka samu chiki da Umma'n su Khalid chikin Ammi na da wata 3 Aunty Amarya ma tasamu chiki chikin Aunty Amarya na da wata 4 Ummi na ma tana mu chiki kamar abun haɗin baki rana ɗaya Ammi da Umma'n Khalid su aihu Ammi ta haifi ɗa namiji Umma'n su Khalid ta haifi yan biyu namiji da mace, bappa Usman yayiwa kakan mu takwara yawa ɗan sa na mijin suna Khalid,macen kuma salma, Abba kuma ya sawa prince Safras musha murna sosai a satin da a ka haifi khalid da prince a satin kakan mu mace ta rasu musha kuka da bakin chiki sosai, kakan mu tana da wata uku da rasuwa Aunty Amarya ta haifi yan biyu Abba yasa musu suna Aryan da Aiman, Aryan suna da wata uku Ummi na ta haifi yusuf daga nanne basu sake hai huwaba, Khalid da salma na da shakara biyu Umma'n su ta haifi Ahmad, shiyasa kikaga da yaya prince yaya khalid yaya Aryan yaya Aiman yaya Yusuf dakuma yaya Ahmad sun taso kamar wasu ta gwaye dan dukkan su banda Ahmad ba wan da yabawa ɗan uwan da full 1 year, shiru shiru su Safras na da shakara uku Ammi ta haifi Fahad, Fahad na da shekara uku Ammi da Aunty Amarya suha aihu a tare kuma dukka ƴaƴa maza suka haifa, Abba yasa musu suna Umar da Haidar Umar na koyan zama kakan mu da bappa Usman sukayi haɗari a kan hanyar su na dawowa daga wani taro dasuka je maiduguri munji mutuwar bappa usman wan da har gobe ma inajin mutuwar bazan taba daina jin mutuwar bappa usman ba har nakoma ga Allah, tun lokachin da aka sanar da Umma bappa Usman ya rasu ta faɗi bata sake lfy ba har itama takoma ga Allah, Ammi ta ɗauki su Khalid ta haɗa su dasu prince tariƙe, Abba ne ya karɓi sarauta bayan mutuwar kakan mu sarki Khalid Abba ya karɓi sarauta wajen da shekara 5 Ammi ta haife ki tun daga kanki ba wanda yasake Aihuwa har yanzu to kinji ta kai chan chen tarihi idan idan kina san jin komai kine kisamu Ummi taba ki lbr Aunty farida ta karisa maganar tana sauke ajiyar zuchiya*

Ji su kayi daga bayan su ana faɗin ae basai tazo waje naba wan nan lbr dakika batama ya isa, murmushi sukayi gaba ɗayan su Khalid yace "ina wuni ummi "lfy lau baba saukar yau she Ummi tayi maganar tana kokarin zama saman sofa mai zaman mutun 1 "ɗazun mu kazo Ummi "to ina sauran ko kai ka ɗai kazo "Aunty farida tace aa Yusuf ya shigo kina bar chi ai daman shida yusuf ɗin da Aiman da Ahmad ne sukazo ƴa'ƴan basu zo ba,Aunty farida ta karisa maganar tana dariya, murmushi nasu irin na manya Ummi tayi tana faɗin " kawai Ummi tayi batare datayi magana ba "Aunty tashi kije ki kiramin Haidar da Umar kinji chewar Aunty farida, miƙewa Zahra tayi jiki ba kwari ta fice daga palo, fita tayi daga ɓangaren Ummi gaba ɗaya, ta ɗan yi tafiya kafun tashiga ɓangaren su Haidar, da sallama a bakin ta ta shiga palon, babu kowa, shiru ta tsaya tana waswasin taje betroom na su ne,  kokuma tajuya taje tachewa Aunty farida bata gansuba kamar daga sama taji anche "what are you doing here ɗago ido,tayi tana kallan sa yana sanye chikin 3cuter wando ruwan kasa da farar riga mara nauyi, saurayi ne dan shekarun sa zasu fi 25 ba kyakkyawar gaske ne kaman nin sa ɗaya da DON ban ban chin sa da DON shi idan sa fari ne DON kuma light green, murya na rawa Zahra tafara magana "Aunty farida che tache nakira mata yaya Haidar da Yaya Umar "daman Aunty farida ta zone ya tambaya yana chiro waya daga aljihun sa  "eh tazo tana part ɗin Ummi, shiru yayi bai sake chewa komai ba, itama Zahra shiru ta tsaya almost 10 mnt a hankali ta ɗago kai dan taga wai ya tafine ko yana nan, yana tsaye a jikin stair case ɗin yana latsa wayar sa chikin tsoro da fargaban amsan da zai bata tace "yaya Fahad ina su yaya Haidar ɗin, shiri yayi bai tanka ba kamar ma bai san akoi mutun awajen ba ko sai latsa wayar sa yake, chikin tsoro Zahra ta sake mai mai ta tambayar "tayi yaya Fahad ina su yaya Haidar, wani dogon tsaki Fahad yaja chikin tsawa yake faɗin "wai kin bani ajiyar sune abeg get out, tun bai kai karshen maganar ba Zahra ta fita da gudu dan daman kamar a kan kaya take

Da gudu tashiga palon Ummi kan chin yar Aunty farida ta faɗa tana Kuka "subhanallah Auta meyafaru wa ya taɓaki chewar Aunty farida Zahra dai kukan ta take batayi magana ba "ai kema Aunty farida kinsan halin su banso kika aiki Zahra wajen suba, yanzu kilama ta haɗu da Yusuf ne a hanya ya daka mata tsawa, chewar Khalid Aunty farida tasa hannu tana shafa kan Zahra tana faɗin "sorry my lovely Auta kyalesu duk abun da suke miki kitara saiki rama akan ƴa'ƴansu in sunyi aure sun aihu  kinji koh share hawayen ki, 
dariya khalid yayi sosai san nan yace wai wa yaga yara, tab waƴan'nan akoi zan chen aure ma a'lamarin sune, ai wlh ko zan chen mace ban taɓaji sun yiba, mutane kamar dutse basu da shauki ƴanzu haka maganar danake miki friend mu hisham zai yi aure bakin san Hisham ba Aunty farida ta gyaɗa kai alamar eh "to Hisham dan yayi Aure Aryan da DON suka raba gari dashi "what? Kana nufin saboda Hisham yayi aure ne DON da Aryan  zasu raba gari dashi, abotar kufa tun yarinta kai ina hakan ba zai yuba " to gashima yayuwu kuwa dan ba yadda bamuyi dasu ba akan suzo bikin sunki zuwa,shima Aiman damuka samu muka lallaɓashi yazo yaki halaktar daurin auren, shi kuma Yusuf ɗaurin aure kawai yaje yaki zuwa wajen walimar " tab to wlh basu isaba dolene su zauna tare da Hisham kilama sanadiyar zaman nasu suma sufara sha'awar auren yanzufa kusan 30 years kuke dashi kun zauna ba abunda kuka iya daga mai rike bin diga sai mai rike sirin jin Allura sai mai fama da laptop wai da sunan zane, Khalid ya dukar da kai kasa dan anzo kansa shima dan shine mai fama da laptop, aunty farida tachi gaba da chewa "sai mai fama da rigar lauyoyi gamasu tasowa nan yanzu duk kun lalata musu tunani dan suma ba mai wani maganar aure chikin su,  duk kun chika mana gida,  to mun gaji da ganin ku ƴaƴa muke san gani, su Ammi suna bukatar jikoki gashi ni tunda nayi aure ɗa 1 Allah yabani karamin Safras har yanzu shiru kakeji ban samu kariba to gwaranima, mardiya ko ɗayan bata samuba dan haka muna bukatar ƴaƴa agidan nan,  yanzu haka Fahad shekarun sa inban mantaba zasukai 25 ga Haidar da Umar suma sun kai 23 ga Zahra Auta an zama yan mata yanzu haka Zahra nada 16 years to mekuke bukata dayawuche aure Allah ya hore muku komai,to yazama dole kuyi aure yan zu kam  takarisa maganar da alamar ɓachin rai a face ɗinta, Ummi dai ido ta zuba musu tana kallon su dan ita ba mai yawan magana ba che " laaa ni Aunty farida kin tunamin ma inasan muyi wata magana, chewar khalid ɗin "ok to inzo muje waje ke nan, Khalid ya ɗan sachi kallan inda Zahra da Ummi suke san nan yace eh to muje palan Abba zai fi tunda nasan yanzu baya nan yana fada "to muje amma kafin nan bari nayi waya da yan uwan kan nan dan inasan gabaɗayan mu muhadu a palan Abba bayan sallar issha "to kawai Khalid yace tare da mikewa yanufi hanyar fita "Ummi tache adawo lfy Baba tunda abun sirri ne "murmushi yayi yana shafa kansa batare da yache komai ba yafiche daga palon 


To 


(Garin  yola ✈️🛬



 kyakkyawar yarinya che fara tas ga  dogon hanchi har baka doguwa che amma ba sosai ba bata da kiba duk da tana sanye chikin hijabi, hakan bai hana gashin dake kwanche a gaban goshin ta fito waba dark black ne gashin very smooth gata da manya manyan blue eyes, laɓɓan'ta ɗan karami pink colour bazata wuche 14 years ba sanye take chiki wata ko ɗadɗiyar  atamfa ta koɗe tayi fari ga wata je mam miyar hijabi baki ne amma saboda koɗewa sai da ya dawo ash colour tsaye take tana riƙe da bokiti irin na penti almost 5mnt tana tsaye chikin fushi tafara magana da harchen fullanchi "hiyana idan bazaki fitoba wlh tafiyata zanyi na barki, tayi maganar tana kallan kofar wani gida 
Gida ne ɗan ma dai dai chi kofar gidan ansa masa buhu an rufe a matsayin labule,irin gidan fulanin nanne masu kiwon shanu ke waye gidan yake da zana, daga chikin gidan hiyana ta da wata murya mai daɗin gaske tana faɗin adin kai diyana ina zuwa ina dubawa amrat hijabi ne "to wai waya chemaki amrat zata bi mu ne,  zamuɗebo har da rabonta dan haka ta zauna a gida taƙarisa  maganar tana yamutsa fuska "  yaye labulen buhun hiyana tai tafito, subhanallah sarki ya tabbata ga ubangiji da yayi wan nan halittar hiyana tafi diyana  kyau sosai ta ɗan fita fita tsawo, kuma da alama zata ɗan fita shekaru dan hiyana zata kai 16 years farache sosai tafi diyana haske idon tama yafi na diyana girma da shiga colour idon ta yayi blue sosai kyakkyawa che ajin farko, rike take da hannun wata yarinya wadda bazata wuche 11 years ba yarinyar tana kama da diyana sosai sai dai ita idon ta baki ne manya manya, karaso'wa wajen da diyana ke tsaye su kayi hiyana na faɗin kiyi hakuri diyana kinji "haba hiyana ke che babba amma keche ke ja'mana duka kullun "to shike nan diyana kiyi hakuri zan gyara kinji muje to "aa bazamu tafi da amrat bafa ki mai data gida "diyana kibari mutafi da ita mana babu kowa fa a gidan bappa kuma yayi barchi kin sani bansan mu barta a gd ita kaɗai "nikuma Allah hiyana bansan amrat tabi'mu rafin nan akoi wahala Allah "to yanzu kam tun da mun fito muje kawai mu daina ɓata lokachi, juyawa diyana tana tura ɗan karamin bakin tan nan suka jera su kasa amrat a tsakiya 

Wani dan siririn hanya suka nufa mai chike da dogayen chi yayi tsakiyar chi yayin suka kutsa tafiya sukayi mai nisan sosai kafin su isa wani rafi mai girma gefe gefen rafin chike yake da gona'ki da shuke shuke, ruwa suka ɗiba a buket ɗin dasuka riƙe hiyana ta ɗora'wa diyana nata buket ɗin chike da ruwa san nan da kyar itama ta ɗora nata ta kamo hannun amrat suka fito daga rafin suka kama hanyar gd, tafiya suke ba wan da yace da ɗan uwan sa ko kala, a dai dai wata katuwar bishiyar mangoro wani saurayin da bazai wuchi 24 years wani ɗan dotti dashi pusu pusu kamar an kwato shi daga bakin Kura  ba yasha gaban hiyana birki suka ja suka tsaya suna kallan sa, ɗaure fuska diyana tayi tana faɗin "buba me haka dan Allah kabamu hanya mu wuche, wani kallan uku 10 buba ya watsawa diyana kafin yace "ke ba take nake ba tukun nan kibari nagama da hiyana zan dawo kanki "chikin sanyin murya hiyana tafara Magana buba kayi hakuri kaji kabar mu,mutafi wlh ruwan nan akoi nauyi kabari in  muka dawo ɗiban na biyu sai mu tsaya muji me zakache "ke ni sa'ankine dazaki che na jira ku to baku isa ba yanzu nake san yin maganata idan ruwan yamuku nauyi,sai ku sauke kasa ku ajiye idan nagama maganan da zanyi sai ku ɗauki ruwan kutafi, diyana sarkin rashin hakuri a kule ta juye'wa buba ruwan dake kanta ajikin sa tun daga kansa har kafa yamike shar'kaf ta watsa a guje tanufi hanyar gida, dafe kai hiyana tayi tana faɗin "kayi hakuri buba..bata kai karshen maganar ba buba ya buge ruwan dake kanta ya faɗi kasa ya zube ɗaukar boket ɗin buba yayi yafara bugawa da katsa yana kokarin fasawa, hiyana kuwa ganin hankalin buba ya koma kan yana san fasa musu boket ne yasa ta kama hannun Amrat suka kwasa aguje sukayi hanyar gd, sai buba ya gama fashe musu bo'kitan gaba ɗaya san nan yabi bayan su a guje
 
Da gudu diyana ta faɗa gd wani ɗakin buk'ka tashiga,sai haki take tana numfashi da kyar, wani bawan Allah dake zaune chikin ɗakin, a kan  gadon chiyawa, daka gan shi kaga ka mannin hiyana duk da tsufa da wahala dake tattare dashi ba zai hana ka gane kyan sa ba "diyana lfy kika shigo kina haki haka meyasaki gudu wani kika tso kana ko "bappa wlh buba ne shine zai bugeni na gudu kuma ba abun dana masa, bappa zaiyi magana sai ga hiyana tashigo rike da amrat dukkan su sai haki suke suna numfashi sama saman "hiyana har dake yau kuma bappa ya tambaya yana kallan hiyana, chikin sar'kewar murya hiyana tace "aa bappa laifin diyana che ta shafe ni, "ya Allah ya kawo muku mafita ƴa'ƴana, har suna haɗa baki wajen chewa ameen bappa, basu gama rufe baki ba aka ba paɗo ɗakin babu ko sallama wata mata che baka mai ƙaton hanchi, damkoh wuyar hiyana ta jata zuwa tsakar gd ta hau bugu matar nan tsaka nin ta da Allah take bugun hiyana, ta ko ina ihu hiyana keyi tana faɗin "dan Allah inna kiyi hakuri, "au kinsan da hakuri ke nan koh har buba zaku jiƙa da ruwa kuma ku zage'shi koh to wlh yau sai kun yabawa aya zakin ta, komawa ɗakin tayi ta damkoh diyana da gudu Amrat tayi bayan bappa ta buye, inna kuwa jan diyana tayi har tsakar gd ta ɗaukoh wani itache ta hau bugun hiyana da diyana dashi bugun su take sosai duk inda ta samu take sauke musu itachen, tun kukan su na iya fita har sautin kukan ya daina fita,duka sosai inna tamusu sai da ta faffashe musu jiki, san nan ta kyalesu takoma gefe kan wani dutse ta zauna tana mai da numfashi, su kuma suka dun kule waje ɗaya suna kuka, sai da inna ta gama hutawa san nan ta ɗago ta dube su tafara magana, "ke hiyana ko kina so ko baki so buba zaki aura dan kin samu ma zai rufa miki asiri, kuma kutashi tun da kun fusata buba ya fasa buket ɗin ɗiban ruwan to da kofi zaku koma ɗiban, wlh kutashi ku ɗauki kofi kutafi kufara ɗiba min ruwa yanzun nan, ku chika komai na gd san nan ku chika durum na dabbobin nan,kutashi tun ban zo na karai'raya kuba ta karisa maganar chikin tsawa, da kyar suka miƙe har suna tangal tangal suka sufi wani ɗan  ki chin suka ɗaukoh kofi kowache ta ɗauki cup 1 suka fito suna kuka suka nufi waje

Bappa na zaune chikin ɗaki yana hawaye Amrat ta fito daga buyan datayi a bayan sa tafara goge masa hawayen tana faɗin bappa ka daina kuka kaji, rungume ta bappa yayi yachigaba ga kwalla 

Su hiyana kuwa han yan rafin suka nufa suna rike da kofin suna kuka, "chikin kuka hiyana tace yanzu diyana bakin ga irin abun danake faɗamiki ba, kullun ina faɗamiki komai buba zai mana muyi hakuri dan in mu kache zamu biye masa wlh mu zamu sha wahala komai kan mu zai dawo amma ke bakiji,bansan wani irin kai ne dake ba "share kwallan fiskar ta diyana tayi tana faɗin yanzu hiyana haka zamu chigaba da rayuwa ni gaskiya bazan iya jure wa ba, yazamuyi mu ɗebo ruwa da kofi kuma a che mu chika abuba dake gida da ruwa har dana dabbobi nidai bazan iyaba "to duk bake kika jaba da zaki che bazaki iyaba kin nafa sane da kyar bappa yasamu yaje chikin birni ya sawo mana buket ɗin nan, yanzu gashi kinsa buba ya fasa bappa kuma ba takawa yake ba yanzu bare ya sawo mana wani ai dole ma mu ɗebo ruwa da kofin tun da dai kin san inna in tayi magana ba wan da ya isa yasa ta chanza, shiru diyana tayi bata sake chewa komai ba harsuka kai bakin rafin suka ɗebo ruwa a kofin suka juyo suka kama hanyar gd
*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Mrs BMB*


            💫New team 💫
                         ⬇️
 💖The talent troupe writer's 💖


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 3*
          


Kwan che DON yake chikin ɗan karamin pool nashi dake wajen sha'katawar sa na chikin ɗaki kwan che yake chikin ruwan gaba ɗaya jikin sa na chiki iya kansa kawai yabari a waje idon sa a lunshe kamar mai barchi, Aryan dake zaune saman ɗaya daga chikin kujerun wajen, yace "DON da alama fa maganar Yusuf zai zama gaskiya, batare daya buɗe ido ba yace "haba Aryan kayi magana da Yusuf ɗin ne "aa bamuyi ba amma dai da alama zan chen nashi zai iya zama gaskiya "hmm da kuwa sun gama dani sun kashe idan haka ne "to yanzu wani mataki zaka dauka Aryan ya tambaya yana kallan face ɗin shi, sai lokachin ya buɗe green eyes nashi ya sauke su akan Aryan, yayi da Aryan ɗin ma shi yake kallo " Slowly ya furta banyi tunani a kai ba amma anjima zanyi magana da aunty farida Jinjina kai Aryan yayi yana faɗin "why baza kayiwa, Ammi maganar ba "hmmmm kai ma dai Aryan da wani magana kake,kafasan halin Ammi ni ko kallo ma ban ishetaba bare tasa baki a lamari na,  shiru Aryan ya ɗanyi  kafin yace "bari nizan gwada, yimata magana, guntun tsaki DON yaja yana faɗin "dama ka kyaleta dan ba sauraran mu zatayi ba nasani "eh to hakane kam  amma dai yakamata tasa baki, mikewa yayi yana kokarin fita daga chikin pool ɗin,wayarsa dake ɗaki tafara kara, daukan towel dake jere awajen yayi yana goge jikin sa, yana faɗin "nifa inaganin kai tsaye zan yiwa Abba magana dan gaskiya a yadda nakeji yanzun nan bazan iyaba "to kana ganin hakan shine mafita " kwarai kuwa, yayi maganar yana kokarin shiga ɗaki " 

Katafaren gadon sa yanufa yasa hannu ya ɗauki wayar, dake kan gadon kafin ya ɗauki wayar kiran ta katse,dubawa yayi dan yaga waya kirasa ganin Khalid ne,yasa yabi kira ringing ɗaya Khalid yayi picking, sa wayar a H-free DON yayi ya ajiye saman mirrow, yana gyara lallausan haɗaɗɗen gashin kansa sai kyalli gashin ke yi kwanche har bayan sa, 

daga ɗayan ɓangaren Khalid yace 'wai yanzu DON  da gaske bakuyi kewar mu ba ko?,ko neme mu bakuyi ba, guntun tsaki DON yaja yana faɗin abun da ka ƙira ka tambaya ke nan, "kwarai kuwa shi nakira na tambaya "DON zai sake magana, Aryan yasa hannu ya ɗauki wayar yana faɗin " dan Allah ku zauna a naija pls kar ku dawo dan da kuka tafi rayuwar tafi daɗi ma,dariya Khalid yayi kafin yache hakan ya tabbatar min da kunyi kewar mu ke nan, tun da kache mu zauna a naija hakan na nufin muyi sauri mudawo ke nan tsaki Aryan yaja kana ya jefar da wayar a kan gado ya juya yanufi hanyar fita ɗakin  yana faɗin  in kagama shiri kakirani awaya san nan ya fiche daga dakin, DON kuwa yana jin Khalid nata magana achikin wayar amma yayi banza, har yagama gyara gashin sa yatara ya ɗaure a baya san nan ya shafa mai mai kamshi da tsada ya fesa Dubai perfume mai kamshi sosai yanufi dressing room almost 30mnt san nan yafito, sanye chikin black jeans da blue t-shirt kayan sun kara bayyanar da Asalin kyan sa chi'kakkiyar surar sa irin na jaruman maza yakara bayyana, faffaɗar kirjin san nan a tsaye dam dam ga dam'tsen hannun sannan kamar zasu fashe a chike suke sosai laɓɓansan yayi ret sosai kamar yasa jan baki, sake fisa turare yayi a jikin sa yasa booth baki akafara sa sai wata dan ƙareriyar agogon daimon mai matikar kyau da tsada ya daura a hannun sa ba karamin kyau yayiba tamkar shiyayi kansa, a hankali ya tako kamar bai san taka kasan yanufi gaban, katafaren gadon sa hannu yasa ya ɗauki wayar sa yana bin screen ɗin da kallo a hankali ya buɗe baki kamar bayasan magana yace Khalid wai har yanzu baka gama surutun naka bane "a fusache Khalid yace gaskiya DON kai dan rai'nin hankaline "oh baka gama surutun ba kenan to pls in kagama ka katse kiran dan zan fitane,rai a ɓache khalid yake faɗin "zaka sanine wlh zamu haɗune,  DON dai bai sake chewa komai ba, Khalid dayaji shiru sai ya  katse kiran girgiza kai DON yayi yana faɗin na sani bani da masoya kamar ku nima kuma ina kaunar ku  
dau kan wayar sa yayi a nitse yanufi waje yana ko karin kiran layin Aryan kirayayi har takatase Aryan bai ɗagaba, waje gaba ɗaya yanufa, a dai dai baƙin kofar babban palo sukayi karo da Aiman da Ahmad, ko kallan inda suke  bai yiba yabi gefen su zai wuche "wato DON bakayi murna da dawowar mu bakoh? chewar Ahmad 


Aiman kuwa wuche warsa yayi shima ko kallan DON ɗin bai yiba ya haura stair ɗin tsakiya yanufi ɗakin'sa DON  kuwa chigaba yayi da tafiyarsa batare daya tankawa  Ahmad ba, sai daya kai tsakar gidan batare daya juyoba yafara magana to daman wayache kudawo  "rai a bache Ahmad yace ae daman badan kai muka dawoba dan kuwa inda dan kai nema wlh ko kallan kasar nan bazamuyi ba, DON dai bai sake chewa komaiba hasalima tsayuwa yaje yayi a bakin katafaren pool nasu na tsakar gidan, tsayuwa yayi ya juyawa chikin gd baya ya zura hannu a aljihu

Rai a ɓache Ahmad ya juya ya nufi chikin gida a tsakiyar babban palo yachikaro da Aryan shima yana sanye da black jeans da white t-shirt yana daure da agogon daimon irin na DON, ya tara gashin kansa waje ɗaya ya ɗaure yazuba jelar abaya kamar wata mace ga gashin da tsawo, har bayan sa yayi kyau sosai kamar shiyayi kansa, ko kallon in da Ahmad  yake  bai yiba ya wuce yanufi waje,  a kule Ahmad yafara magana "kudai bakuji daɗin halinkuba mutane ne kamar wasu aljannu yanzu haka kafin mu iso sai danayi tayiwa Aiman faɗa amma ko kallona bai yiba haba dan Allah yakamata ku chanza hali, Aryan dai wuchewar'sa waje yayi batare da yace komai ba, haurawa san benen Ahmad yayi yana surutai


Waje Aryan ya nufa kai tsaye inda DON ke tsaye yanufa irin tsayuwar da DON yayi shima yayi ya zura hannu a aljihu suna fiskantar babban gate ɗin gd, gaba ɗayan su fiska kaman an aiko musu da sakon mutuwa, Almost 30mnt suna tsaye a haka babu wanda yache da ɗan uwan sa kala kuma ko motsi basuyiba a tsayuwar tasu 
 jim kaɗan saiga Aiman yafito shima ya shirya chikin blue jeans da t-shirt ash yayi kyau sosai kuwa duk kansu agogon hannun su iri daya ne, gefen Aryan yazo ya tsaya   
 juyawa DON yayi  yafara tafiya ta ɓan garen dama, ganin DON yajuya yafa tafi yasa Aryan juyawa shima yabi bangaren hagu,Aiman kuma ya miƙi hanyar tsakiya yanufi bakin gate 

wani gate dake chikin gidan ta ban garen daman DON yashiga, wasu haɗadɗun motochi ne masu tsadar gaske awajen da alama nanne parking space na gd zubawa motochin ido  yayi na ɗan wasu mnt, wasu jibga jibgan sojoji ne suka nufo inda yake tsayen a kalla zasu kai 10, kusa dashi suka ja suka tsaya hannu suka ɗaga suna sara masa, jinjina kai kawai yayi,batare dayayi magana ba kana yasa hannu ya musu nuni da motar da zai hau wata dan karekiyar motache kirar Marcedes Benz, black colour, wani matashin sojane mai jini jiki kato mai ji da karfi fari tas yanufi motar da DON yanuna ya shiga yawa motar key har,inda DON ke tsaye ya jawo mota,  wani bakin soja kato dashi kak karfan gaske yazo da sauri ya buɗe wa DON kofar motar
takawa yake sannu a hankali yashiga motar ya zauna, sara masa sojan yayi san nan ya rufe kofar motar, sojan yaja motar da ma tsakai chin gudu suka fita ta ɗayan gate ɗin

A gaban Aryan da Aiman motar DON tayi parking, sauƙe glass din motar DON yayi, yasa hannu ya karbi bindigar da Aryan ke mika masa juyawa Aryan yayi yanufi nashi motar   
Aiman kuwa yana tsaye,suma kuma suna tsaye basu tada motochin nasu ba Almost 5 mnt suna tsaye shiru a nitse DON ya ɗago green eyes nashi yana kallan Aiman calmly yafara magana "kai inbazaka shiga bane muyi tafiyar mu, tsaki Aiman yaja yana faɗin "au ashe dai bazaku iya tafiya ku barni ba, na zachi nima wulakanchi zakumin DON dai bai sake magana ba sai ma mai da glass ɗin motar yayi ya rufe  Aiman kuwa sai da ya sake tsai dasu for Almost 5mnt tukun nan yabude motar DON yashiga, ko kallan in dayake DON bai yiba yayiwa Abdol umarnin akan suwuche a nitse Abdol ya taɗa motar da matsakai chin gudu suka nufi gate, tun basu karisa security suka wangale musu katafaren gate ɗin a jere suka dan na hanchin motochin nasu waje, motar DON ne a gaba sai na Aryan ke bi masa sai wasu motochi 3 chike da sojoji, shinfi ɗadɗiyar titi suka miƙa 

kira ne yashigo wayar DON saida wayar takusa katsewa yachirota daga aljihu, Yusuf shine sunan daya bayyana a kan screen ɗin wayar, picking call ɗin yayi ya kara a kunnensa yana faɗin hello daga ɗayan ɓangaren Yusuf yace "bro ykk "a hankali ya furta normal kai fa "Yusuf yace nima normal, inaganin gobe zan shigo abun dayasa ban shigo yau ba kaga Abba yana da zama damu, Aiman da Ahmad sun gudu sunki jiran meeting ɗin , SO kaga bai kamata nima naki tsayawa ba jinjina kai DON yayi yana faɗin "eh hakane amma kayi amfani da lokachin ka dan lokachi bata jira sai dai ajirata "kai DON tun munayara kake yawan faɗa mana haka inshaa allah zamuyi amfani da lokachin mu, "  good  kawai yace san nan ya katse wayar
 Aiman dake zaune Age'fensane yace akoi matsala fa DON  " batare da ya kalla inda Aiman yakeba yafara magana matsala batada wajen zama a family Abubakar saraki, tsaki Aiman yaja kafin yace "ta kanka kuwa zatama fara "koh? DON ya tambaya yana kokarin mai da wayar sa aljihu Aiman dan haushi bai ma sake maganaba 


Yola Nigeria

Da kyar da kyar suke tafiya suna rike da kofi a hannun su kamar bazasu kai lbr ba tun safe yaran nan suke debo ruwa da cups amma har yanzu karfe 6 na yamma basu gama ba subhanallah 

da kyar diyana ta bude baki tafara magana hiyana bazan iya chigaba da ɗeban ruwan nan ba wlh yinwa nakeji numfashi na zai iya ɗaukewa   "ki kara hakuri diyana Allah natare kinji, kiyi addua kawai adun halin dakika tsinchi kanki kuma ki kasan che mai godewa Allah sai Allah yakawo miki sauki "alhamdulillah alhamdulillah alhamdulillah Allah ngd, Allah mai kyauta mai kari ya ubangiji kadube mu da idon Rahma Allah ka kawo mana sauki " 
 ameen ameen diyana haka zaki rinkayi a kowanihali kika tsinchi kanki, diyana batare da ta sake magana ba tanemi waje kasan wata bishiya ta zauna, a'razane hiyana ke faɗin "aa diyana kitashi dan Allah mutafi inbahakaba kinfasan inna "wlh hiyana sai dai yau inna takashe ni, haba da wani kafa kikesan intafi nagaji nagaji yinwa nakeji ko ran dunan dake chikin gidan nan fa bamugama chikawaba barema har musa na dabbobi ta karisa maganar kamar zatayi kuka, hiyana zatayi magana sai sukaji magana ta bayan su da sauri suka juya gaba ɗayan su har suna haɗa baki wajen chewa "inawuni yaya bello "lfy me kukeyi anan da man'gariban nan " ruwa muke ɗiba wa inna diyana tabashi amsa, "to ya kamata kutashi kutafi gida tunda kunga man'gariba ta kawo kai ga dajin nan da machizai, ina ruwan naku in taya ku ɗauka zuwa chikin gari, hiyana ta nuna masa kofin dake hannun ta tache gashi nan "to yau kuma da kofi kuka koma debo ruwan ne ina boket na ɗiban ruwan naku, da sauri diyana tace buba ne ya fasa mana boket, inna kuma tache mukoma debowa da kofi, girgiza kai bello yayi yana faɗin  kuchigaba da hakuri kuna addua inshaa Allah, Allah zai kawo muku mafita amma dai yanzu kutashi kutafi gida 
"da kyar diyana tamike daga zaman datayi yaya bello yayi gaba su kabi bayan sa tafiya suke kamar babu jini ajikin s,Juyowa bello yayi yana faɗin "ga gyada ku karba kuchi yanzu na chiro a gona yayi maganar yana mika musu ledar gyaɗan dake hannun sa chikin ladabi hiyana ta ansan musu gyadar tana faɗin mun gode murmushi kawai bello yamata batare daya amsaba ya juya ya chigaba da tafiya,suma suka chigaba da tafiya da kyar da kyar har suka fito chikin gari, bello ya nufi gidan sukuma suka tsaya a kasar bishiya mangoron kofar gidan nasu, suka fara chin gyaɗar da yaya bello yabasu

kinsan me hiyana naso ache gyadar nan dafaffache "au yanzu diyana hakanma baki godewa Allah ba karki manta fa tun safe fa ba abun da mukachi, kuma babu wanda ya tausaya mana yabamu wani abu dan kin'samu yanzu yaya bello yabamu gyada shine zaki waniche da dafaffache koh, to kije kidafaɗin, in bazaki iyachi hakaba sai kibari dan bawanda yamiki dole "aa hiyana abun ae bafaɗa bane kawai daga faɗin  ra'ayi na "wan nan ba ra'ayi bane diyana rashin godiyar Allah ne kawai, kuma kullun ina faɗa miki kirinka godewa Allah a duk yadda kika samu kanki "to kiyi hakuri hiyana nayi kuskure alhadulillah Allah nagodema dakaba mu abun da za mu sa abakin mu "to kokefa yanzu naji magana "la hiyana kingafa kamar lamrat che ke zuwa diyana tafaɗa tana ɗan murmushi " da sauri hiyana ta juyo tana kallan inda diyana ke nunawa "itache wlh mujirata ta karaso sai mushiga gd tare koh  

Gyara tsayuwar su sukayi har lamrat ta kariso, sanye take da kayan fulani farache tas itama mai dogon hanchi kamannin'ta ɗaya da hiyana sai dai idon su ba iri ɗaya bane idon lamrat baki ne idon hiyana kuma blue ne lamrat bazata wuce 13 years ba " lamrat kindawo chikin harchen fullanchi diyana tayi maganar " lamrat tace eh Aunty diyana nadawo  "Allah yasa kin sayar da nonon chewar hiyana "eh aunty hiyana nasayar dukka "murmushi diyana tayi tana faɗin  alhamdulillah nagodewa Allah dayasa kika sayar yanzu kinga inna bazata bugekiba " nifa aunty diyana duk dukar da inna takemin bai dameni'ba nidai kawai bansan naga tana bugun ku,in nika'ɗai zata yita bugu bazan damuba "to aimuma hakanne bamusan inna ta bugeki ya'fimana tabuge'ni nida diyana tabar ku ke da amrat "hmmm hiyana yakamata mushiga gd kunji anfara kirar sallar mangariba koh chewar diyana " hiyana tace gaskiya kam mutafi tayi maganar tana mikawa lamrat ledar gyadar dake hannunta "aa Aunty hiyana nasan tun safe baku chi komai'ba, ni kuma kinga bintu tabani abinchi awajen talla kuchi kawai "  hannu hiyana tasa aledar ta debo gyadar ta mikawa lamrat tana faɗin abinchi daban gyada ma daban " lamrat tasa hannu ta amsa gyadar kana tayi godiya haka suka jera har chikin gida 

da sallama suka shiga innar tasu na tsakar gida tana zaune ga amrat zaune a gefen ta, tana tuka mata tuwo, wuchewa kichin hiyana da diyana sukayi dan juye ruwan dasuka ɗebo lamrat kuma tazo ta sugunna a gaban inna ta chiro kudi tamika mata 
inna ta karba ta irga kudin san nan tace "yau Allah ya rufa miki asiri kitashi kije ki daukoh wanke wanke kimani,murya na rawa lamrat ta fara magana "inna dan Allah kibari nayi sallah dan wlh ko a'zahar da la'asar banyiba ga kuma mangarib..  bata karasa maganarba ta'farajin saukar duka, da karfi tafara ihu tana faɗin dan Allah inna kiyi hakuri, da gudu diyana da hiyana suka fito daga kichin ɗin sukayo wajen inna suka duka kasa suka kama kafarta suna faɗin inna dan Allah ki kyale ta mu ki dakemu a madadin ta dan Allah inna kiyi hakuri, kafa inna tasa ta shuresu ta ɗau koh itachen a chikin wuta a murhun da amrat ke tuka tuwo tafara bugun su dashi, suna ihu kamar ran su zai fita, amrat na tuƙa tuwo tana kuka, haɗesu inna tayi tamusu duka mai isar duk ta gun bura musu jiki, zama tayi a saman dutse tsakar gidan tana mai da numfashi, "ke diyana ke da hiyana kutashi kutafi ɗiban ruwan ku wlh tun ban tashi na ɓaɓɓala ku ba chikin tsawa inna tayi maganar ke kuma lamrat kitashi ki kama aikin dana saki, ba kun che bakuji ba to wlh zan gyara muku zama a gd nan

da kya hiyana da diyana suka mike ga yinwa ga gajiya ga wahala ga duka gashi ko sallar azahar basuyiba ga mangariba tayi ga dattin da jikin su yayi haka suka mike suka dauki cups ɗin suka nufi waje  suna hawaye lamart kuma tamike tanufi kichin ta tattara wanke wanke ta fito ta ɗebo ruwa ta fara wanke wa tana kuka mara sauti

Misalin karfe 9 na dare,tafiya suke achikin duhu suna kuka suka shiga chikin dabbobin su, suka juye musu ruwan suka fito, diyana ta tsaya akusa da bishiyar mangoro kofar gidan su A gala baice hiyana tace "diyana muje saura mana sahu biyu ne ae "wlh hiyana ba zanjeba Allah sai dai inna ta kasheni yau tayi maganar tana kokarin zama awajen "to shike nan kizauna a nan kihuta bani kofin naki naje nadebo har da rabon ki, amma dan Allah karki koma gida dan in kika koma nasan inna zata buge ki, ki zauna har nagama, ɗebowa sai mushiga gida tare, diyana dai ko magana takasa jin hiyana kawai take,
juyawa hiyana tai chikin duhu tanufi hanyar rafin, diyana kuwa kwanchiya tai a kasar itachen ba jimawa barchi ya dauketa, hiyana tana tafiya chikin kun gurmin dajin nan tanata surutu ita kaɗai," ya Allah kaba mu ikon chin wan nan jaraba wan Allah ka mikarma na da bappan mu yafara takawa da kafarsa ya Allah kajikan innan mu ya allah kakaremin yan uwana Allah mungode mungode alhadulillah alhadulillah, Allah karkabari a ɗaura aure na da buba ba'nason sa ko kaɗan, wayyo Allah na wai meyasa bappa ya Auri inna habiba ne meyasa bai yi zaman sa haka nanba tunda dai shi da kansa kullun yake chemana baya santa to meyasa ba zai che tatafi gidan suba, wayyo ni hiyana ya zanyi Allah kadubi mu da idan rahma, hakadai hiyana tayi ta addu'oe da surutanta, harta karisa ɗebo sauran sahu biyun dasuka rage,

 tadawo wajen da diyana ke kwanche kasan itachen, tafara kiran sunan ta, wajen duhu ne bata kallon komai,"diyana kitashi mutafi gida nagama ɗiban ruwan, shiru diyana bata amsa ba kara kiran su nanta hiyana tayi nanma tasake jin shiru, da saurin hiyana ta duƙa kasa tana laluɓe kozata tabota amma shiru bataji diyana awajen ba, Arude tamike zubur tayi chikin gida da gudu, ɗakin su ta faɗa ko sallama babu, amrat da lamrat tasamu zaune suna fiskantar ɗan fitillar kwan dake ɗakin sunyi jugum jugum "lamrat ina diyana,hiyana ta tambaya tana zaro blue eyes nata waje  "chikin rau'nanniyar murya lamrat tace ban ganta ba, hiyana zata sake magana amrat tamiƙe ta riƙe hannun tana hawaye chikin muryan kuka tace "Aunty hiyana yinwa nakeji chikina chiwo yakemin sosai, dan Allah kine momin abunda zanchi ko kaɗanne hiyana batasan lokachin da hawaye zuba wani na bin wani yafara zuba a kuma'tun taba, da wanne zata ji gaji'yar ɗebo ruwa ko kuma yinwa, ko ɓa'tar diyana, gasu amrat na kukan yinwa, riko hannun amrat ɗin tayi chikin dashe war murya tace "jeki zauna kinji yanzu zannemo miki abinchi duk inda yake "to kawai Amrat tace san nan takoma wajen zamanta ta zauna, da sauri  hiyana ta juya tafito daga ɗakin tana tunanin mugunta irin na inna watarana su suke girka abinchin gidan nan amma inna bata basu sai ran da taga dama ko bappan suma babashi take ba, kai Allah wadaran zuchiya irin na inna

Da wan nan tunanin tanufi ɗakin inna bakinta ɗauke da sallama, kwanche ta isko ta a kan figaggiyar gadan chiyawar'ta " bata amsa sallamar ba kuma idanta biyu Murya na rawa hiyana tafara Magana "inna banga diyana  bafa "to idan bakiga diyana ba sai me ina ruwana dawata diyana zaki'tashi kifita min a ɗaki'ne ko sai na tashi na babballaki, mikewa hiyana tai tafita tana tunanin tafaɗawa bappa ne kuma intafada masa ma hankalin sa ba karamin tashi zai'yi ba, gashi ba lfy ne da shiba, kai gwara dai naje tanemo ta da kaina basai na faɗawa bappa ba, da wan nan tunanin nufi waje.

KANO 

Aunty farida Ammi Ummi da Aunty amarya sai  Khalid da Zahra  zaune suke awani katafaren palo mai girman gaske, mai ɗauke da manya manyan Sofa masu matikar kyau da tsada ga laushi set biyu launin milk colour, ga wata makekiyar Tv daga gefe, sai table ɗin chin abinchi mai ɗauke da gujeru 12, idan nace zan tsaya zayyana muku kyan palon nan tofa zamu kwana a nan, zaune suke shiru,sallama Fahad yayi ya shigo palon zama yayi a saman 1str yana gaidasu Ummi, da sallama haidar da Umar ma suka shigo da alamadai family meeting zasuyi  Almost 20 mnt suna zaune ba wanda yake magana  kowa da abun da yake daga masu latsa waya sai mai daddan na laptop "wayar Aunty farida che yayi kara alamar shigowar kira, ɗaukar wayar tayi tana bin screen ɗin da kallo,ganin sunan my prince, yana tamiƙe da sauri tayi waje,daga gefen bakin kofar ta waje ta tsaya san man tayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnenta tace "hello prince daga ɗayan bangaren DON yace "kun gama meeting ɗin ne "aa yanzu dai zamu zamu fara Abba muke jira yafito "to amma kina ganin zamuyi nasara kuwa "kai prince kabari dai idan mungama mayi magana, naji muryan Abba yafito bata jira amsar'saba da sauri ta katse kirar, ta koma chikin palan, wajen zamanta takoma ta zauna 
Abba kyakkyawar  dattijo ne mai chike da kalama, kallo ɗaya zaka masa ka gane duk yaran gd ka'maninsa suka yo farine tas mai dogon hanchi ga manya manya ash eyes yana da dogon gemu da lallausan saje, gashin kansan nan a kwanche kamar na larabawa zama yayi  saman sofa mai ma zaunin mutun1 bin yayan sa yake ɗaya bayan ɗaya da ido yana kallan su shiru palon yayi Almost 5mnt san nan Abba yayi gyaran murya, yafara magana ina Aliyu yake,yayi tambayar bai kai ga rufe baku ba uncle Aliyu yashigo da sallama sanye yake chikin wata dakakkiyar shedda fara tas mai kyau da tsada,  kaman'nin sa ɗaya da Abba, gaba ɗaya palon har suna haɗa baki wajen amsa masa sallamar da gudu Zahra tamike ta nufe sa tana faɗin "oyoyo uncle Aliyu oyoyo ta faɗa jikin sa, rungumeta yayi shima tana faɗin "oyoyo autar'mu oyoyo autar'mu san nan ya zare daga jikinsa ya rike hannunta suka nufi wajen Abba saman sofan dake kusa da Abba uncle Aliyu ya zauna tare da zaunar da Zahra a gefen sa, a nitse uncle Aliyu yace ina kwana yaya da fara'a Abba ya "amsa lfy, juyowa yayi ya gaida su Ammi, suma da fara'a suka amsa masa san nan matasan gidan suka fara gai dashi yana amsa musu ɗaya bayan ɗaya da murmushi a face nashi 
A nitse Abba yafara magana to ku bani hankalin ku nan,duk suka nitsu suka zubawa Abba ido suna saura ren sa chigaba da magana Abba yayi "nataraku a nanne dan inasan magana daku gaba ɗayan ku amma baku gama haduwa'ba dan haka farida ki kiramin sauran yan uwan naki awaya kifada musu duk Abun da suke subari nan da rana ita yau ina bukatar kowa a nan,"
Aunty farida zatayi magana Abba yaɗaga mata hannu aa farida umarni'ne kuma banasan ɗaya daga chikin ku yamin wata magana kutashi kuje zamu sake magana rana ita yau 
sai yanzu nagane aina su DON suka ɗau koh idan sunyi magana basa chan zawa ashe awajen Abba ne tab aiko akoi kallo wayyo



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*

💖 The talent troupe writer's💖


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 4*
          

 YOLA


 Almost 11 na dare hiyana na waje tana neman diyana amma shiru shiru ba diyana ba lbrn'ta hiyana tayi kuka har ta godewa Allah kamar zatayi hauka, ta juyo ta dawo gida jiki a sake ba kwari,  yanzu tama daina jin yinwar da takeji burin ta kawai taga ƴar uwar'ta 
tana shiga gida ɗakin su tanufa kwanche tasamu lamrat da amrat manne da juna sunyi barchi, ga hawaye nan abushe a fuskar su da'alama sunyi kukan yinwa har sun gajine  barchi ya dauke su 
zama tayi akasa kusa dasu su,ta zuba musu blue eyes nata, wasu siraran hawayen takai'ci nabin kunchinta duniyar tunanin inda diyana take tafaɗa,  kamar daga sama taji an bude kofar zanan ɗakin nasu an shigo, zubur tamike tana kallan sa ɗauke yake da wani abu a'kafadarsa kamar mutun hasken fitilar baya haska su sosai shiyasa bata gane me yake ɗauke dashi ba, murya na rawa "tace yaya bello kaine, kasa kasa bello yafa magana "eh nine kana ya raɓa ta gefen su lamrat ya kwantar da diyana, a ruɗe hiyana tace "yaya bello me yasame'ta'? aina kagan'ta? Ta mutune'? Naga bata numfashi 
"hiyana kinitsu mana bata mutu ba suma tayi, kinga yanzu dare yayi zanje gida da safe in kunzo ɗeban ruwa saimuyi magana,in bahaka ba kinsan idan inna ta ganni to nashiga uku, dan haka kiyi shiru karma taji wani motsi, yana gama faɗin haka yajuya ya fiche daga ɗakin 
itakuwa hiyana ta gyara zaman ta, tana kallan fuskar diyana tana kuka, haka ta kwana kamar yadda taga rana haka taga dare 

washe gari tun asuba inna ta shigo ɗakin nasu hannu ta riƙe da tulu mai ɗauke da ruwa da karfi ta zubawa diyana nan take diyana ta farfaɗo tana ihu, inna bata bi ta kanta ba ta juya ta zubawa amrat da lamrat a razane suma suka farka, juyawa inna tayi ta zuba sauran ruwan a awajen Kwan chiyar hiyana a tunanin ta hiyana na ɗakin,Amma sai taga akasin haka ba hiyana a wajen a fusache ta juyo gun su diyana zatayi magana taji diyana na sambatu, tana faɗin "dan girman allah buba ka kyale ni kayi kahuri, wayyo allah hiyana ta ina kike kizo ki chech..bata karisa maganar ba taji saukar duka ta ko ina ajikin ta, ihu diyana ta fasa wayyo Allah na shiga uku hiyana kizo ki tai makeni buba zai kashe ni, wani bugu inna ta kai mata a baki sai da bakin nata ya fashe, ihu a zaba diyana ta saki, shake mata wuya inna tayi tana faɗin "me buba na yamiki da za kiche ya kyale ki, ko kinga buba a nan ne eh, kodai wani mugun abun kuke shirya masa, jin maganar inna yasa diyana ta dawo chikin hayyachin ta, da kyar ta iya faɗin "inna kiyi hakuri zan mutu dan Allah ki sake min wuya, naushi inna ta sake kai mata a baki tana faɗin "ki mutu mana ina ruwana daman uban me kuke tsinanamin a gd ba gara ku mutu kowa ya huta ba, kara shake diyana inna tayi sosai sai dataga blue eyes nata sun fir fito waje sosai tana kokarin mutuwa da gaske,da sauri ta sake ta tana mai da numfashi, juyawa tayi tana kallon amrat da lamrat in da suka takure waje guda suna hawaye chikin tsawa tace "ke lamrat kitashi kije ki ɗoramin girki idan kin gama kizo kitafi talla, ke kuma amrat ki wuche kije kimin wankin kayana kiyi shara da wanke wanke, itakuma wan nan shai ɗaniyar ni zata sa na zubar da ruwa a kasa koh to wlh gaba ɗaya ruwan gidan nan sai na zubar dashi ku ɗebo wani, ke diyana ki tashi ki ɗauki kofin ki nemo wan nan shai ɗaniyar kufara ɗebomin ruwa kuma wlh daga nan zuwa karfe 10 ku chika komai na gd nan, dan dole yau ku jemin tallah ba zanyi asara ba,  tana gama faɗin hakan,
 ta juya tayi nufi hanyar fita har ta kai bakin kofa sai kuma tace wlh idan kuka bari na kai tsakar gd baku fito ba na lahira sai yafi ku jin daɗi, jiki ba kwari lamrat da amrat suka mike suka fice suka bar diyana kwanche baki na jini sai kuka mara sauti dake


Inna na fitowa tayi karo da hiyana a tsakar gida hannun ta rike da cup guda biyu da alama ruwa take ɗebowa "ke ni zakiwa iskanchi to wlh barikiji duk ruwan dake gidan nan saina zubar dashi a kasa kun ɗebo wani, san nan kuma ke kafin kifara zubawa a randu nan nan, sai kinyi sahu 10 kina ɗebowa kina zubar wa a kasa har sau 10 tukun nan, kifara zubawa a tulu, ni zakisa nayi a sara ruwa ba nashiga ɗaki zan tashe ki ashe ba kinan ki kasani na zubar da ruwa a kasa koh, ke gaki mai wayau tun asuba kintafi ɗebo ruwa,  kuma barikiji duk yadda zakuyi kuyi nan da karfe 10 dole kuchika ko ina na gidan, nan san nan ku jemin talla dan yau bazanyi asaraba, tana kaiwa nan ta wuche tanufi kichen, tafara zubar da ruwan dake chikin randu nan da kuma tulu nan,sai da ta tabbatar babu wani tulun daya yage da ruwa a chikin sa san nan tafito tawuche ɗakin ta ta haye gado, babusallar asuba
 Dur kushewa kasa hiyana tayi ta rushe da matsanan chin kuka, mai tsuma zuchiyar mai sauraro, kuka take kamar ranta zai fita sai datayi kukan, mai isar ta san nan ta ɗago kai tana kallan su amra dake tsaye a bakin kofar dakin su,  alama ta musu da hannu aka sutafi sufara aikin su kar inna tafito ta gansu, ganin babu diyana a wajen ne na yasa ta mike da kyar tanufi ɗaki dan tadubo ta 

Kwanche ta samu diyana sai kuka take "ita chikin muryan kuma tace diyana kitashi mutafi mu fara aikin mu tafaɗi hakan chikin shasshakar kuka "wlh hiyana bazan iya tashiba jinake kamar zan mutu chikina murdamin yake saboda yinwa "to diyana ya zamuyi kinsan dai in kika zauna inna ta dazo ta sameki duka zata kara Miki,  kitashi muje saiki zauna a gonar yaya bello ni kuma  na ɗebo ruwan "to zoki rikeni natashi, matsowa hiyana tayi ta kama kafaɗarata, ta tai maka mata tamike har tangal tangal take kamar zata faɗi da kyar ta tsaya a kan kafafunta aruɗe hiyana tace "diyana yanaga jini a jikin zanin ki wai ma ina ki kaje jiya
"a tsorache diyana tafara magana hiyana bansan ya akayi naga jininba nima, daga gabana ya fito 
shiru hiyana ta ɗanyi kafin tace to chanza kaya muje, zamuyi magana a hanya dan in muka tsaya magana a nan inna zatazo ta same mu, da sauri ta ɗauko wa diyana wani tsunmar zanin atampa yasha ruwa duk ya koɗe ta ɗaura mata, tariko hannun ta 
da kyar diyana ke ɗaga kafa da kyar take ɗin gisa kafar tana tafiya suka fito tsakar gida, suka samu su amrat kowache takama aikin ta, amma kallo ɗaya zaka musu kasan suna chikin tashin hankali ga yinwa duk sun galabaita, girgiza kai kawai hiyana tayi, ta duƙa ta ɗauki cups ɗin data ajiye suka nufi waje 

Suna futa hiyana tafara tambayar diyana "ina kikaje jiya diyana "jiya na kwantane awajen da kika barni sai barchi ya ɗauke ni ina chikin barchi kawai sainaji a'na kokarin chiremin zani, nabuɗe idona a razane sainaga bubane,  da nayi kokarin guduwa shine yakamani ya wanka min mari, kuma yasa kafa ya takamin wuya ya chiremin zani, inata rokansa da ya kyaleni amma yaki da kyar na samu na laluɓi wani karfe nabuga masa a kafa, shine yachire kafarsa a wuyata yafaɗi kasa ni kuma natashi da kyar zan gudu kawai naji ya bugamin wani abu a kai daga nan kuma ban sake sanin komai ba saida inna ta zuba mana ruwa ɗazun ta kare maganar chikin shesshekar kuka "to ae na ki kasamu jinin jikin kin nan kuma "nifa hiyana nache miki ban'saniba kawai ganinsa nayi " jinjina kai hiyana tayi tana faɗin yazama wajibi muneman wa kammu mafita wlh " to yanzu ya zamuyi ke nan tayi maganar dai dai lokachin dasuka isa bakin rafin"hiyana tace ki bari inmun samu lokachi iri idan inna bata nan sai muje muyi magana da bappa, yanzu dai  ki ɗebo ruwa ki wanke jinin jikin ki nan, san nan muyi al'wala kinsan jiyama bamuyi sallar azhar laasar mangariba da kuma issha ba, gashi yan zu kuma ana sallar asuba sai muhaɗa dukka,muje kasar itachen chan mubiya bashin sallolin kafin mufara ɗiban ruwa "to kawai diyana tace san nan tanufi bakin rafin ta ɗebo ruwa ta koma gefe  ta wanke jikinta tas san nan sukayi al'wala suka nufi kar'kashi bishiyar mangoron suka shinfiɗa ɗan kwalin su suka ta da sallah,
 sai da suka biyan bashin sallar da akebin su, najiya san nan sukayi sallah asuba 


addua hiyana tai sosai" ya allah kayafewasu amra ba laifin su bane innache kehanasu yin sallah Allah mun'tuba haɗa sallah da muke Allah kayafe mana 
diyana kuwa adduar Allah yakawo musu mafita take hakadai suka gama adduar san nan su kamike " hiyana tanufi bakin rafi tana faɗin diyana kishiga gonar yaya bello ki zauna ki huta, ruwa ta ɗeba a cups ɗin ta kama hanyar gd, ta kuma diyana tashiga chikin gonar yaya bello ta zauna da yake gonar a bakin rafin yake daga chikin gonar kana iya kallan chikin rafin

 har  karfe 8  na safe diyana na zaune a chikin gonar bello, hiyana kuwa saifaman jidan ruwa take ammafa da cups yan zuma taɗebo ruwan takama hanyar gida tanajan kafarta da kyar da kyar har takai kusa da gida zata shiga ke nan, buba ya tare mata gaba ɗaure fuska hiyana tayi sosai" babu kabani hanya 
 hannu buba yasa ya buge cups ɗin dake hannunta yafaɗi kasa ruwan yazube, hiyana kamar zatayi kuka ta duka kasa ta ɗauki cups din har kwallah yafara zuba a idan ta batachewa buba ko kalaba takama hanya tajuya tanufi hanyar komawa rafin, tana tafiya wasu siraran hawayene masu dumin gaske ke zuba mata a'kan kunchin ta.

haka takoma rafin tasake debo ruwan tajuyo ta zata tafi ke nan taga diyana a tsaya a bayan ta "hiyana kawo in karɓa miki kekuma kije ki huta tunda tun asuba kike deban ruwan nan "aa diyana kingafa ke baki da lfy dan haka kije ki zauna kibari zanyi "diyana tace aa to kawo nayi ko sahu 10 ne sai ki karba " sahu 10 yayi yawa diyana ki daiyi 3 "to bani cups din,  mikama ta cups ɗin hiyana tayi, tawuche tanufi chikin gonar yaya bello 
diyana kuma tanufi hanyar gida kodataje itama zata shiga gida buba tagani tsaye a bakin kofar gidan su batache masa ko sannuba tazo taraba gefen'sa zata wuche, buba ba tsoran Allah yasa hannun sa yasake buge cups din ruwan da diyana take da shi suka faɗi kasa ruwan ya zuɓe "a fusache diyana ta ɗago zatayi magana kome ta tuna kuma sai tafasa ta duƙa ta ɗauki cups din tajuya takama hanyar komawa rafin, buba kuwa yana ganin ta tafi yayi murmushi mugun ta cheke da izza da iya shege yafara magana,"ai kunshiga uku dani wlh bazan taba bari ku zauna lfy ba, narinka kuntata muku san nan kuma in na Auri hiyana in maida ta baiwar kowa na kauyen nan,dariya yayi sosai san nan ya chigaba da chewa kai amma goggo habiba ma yar aljanna che wlh ta iya horaku ɗeban ruwa da kofi ai shine maganin ku, a hakanma nikuma ba barin ku zanyiba, narinƙa addaban rayuwar ku kenan ina kifar da ruwan, yau sai kafarku ta daina takawa yasake kwashe wa da dariya kamar mahaukachi

diyana kuwa juyawa tai komawa rafin ta taɗebo wani ruwan tanufo gida, ko datazo kofar gida ba'tasami buba'ba ba'karamin daɗi tajiba alhllh ta furta san nan tanufi gidan zata shiga,  kamar daga sama taji an buge cups ɗin hannunta sun faɗi kasa ruwan yazube 
a fusache ta ɗago ganin bubane a gabanta hakan yasa tarufe ido ta zabga masa mari a kumatu
 diyana daman bata da hakurin jure wulakanchi 

buba kuwa bai'yi wata wata ba ya kwashe kafafunta tafaɗi kasa kanta ya bugu da jikin wani dutse dake bakin kofar gidan, wani ihu azaba ta sake, buba kuwa bai tau saya mata ba ya hau bugunta kamar ai aikoshi
 diyana sai ihu take ganin zai mata illa babu wanda yakawo mata agaji yasa tamike da kyar tana kokarin guduwa
damkoh hijabinta  yayi tabaya ya shake mata wuya ya bugata da kasa wani azaba taji gashi yaki sakin hijabin nata ga wuyan'ta a shake da gyar take numfashi ,tagama sad'dakkarwa mutuwa zatayi sae kuma taji buba yayi ihu kuma ya saketa "da kyar ta iya buɗe ido ta sauke su a kan yaya bello dake tsaye rike da sandar kiwo,sai huchi yake kamar wani zaki, ga buba kuma sume a kasa
hannu yaya bello yasa ya ɗauke ta chak ya saɓata a kafaɗarsa yanufi hanyar rafin da ita,   nan sukabar buba kwanche,  bello irin mazan nanne masu karfi gashi dogo sosai kakkarfa 

kai tsaye gonarsa yanufa da ita hiyana na zaune taga yaya bello ɗauke da diyana a kafadarsa 
da sauri tamike tanufi'sa tana faɗin hande miboni yaya bello me kuma yasame'ta  bello bai yi magana ba  sai da ya isa wajen dayake zama inyazo gonar, wajen shinfiɗe yake da katifar chiyawa, akai ya kwantar da diyana  da sauri hiyana ta karisa wajen ta zauna a kusa da diyana, tana fadin "diyana me yasame'ki waya bugeki waya pasa maki baki "hiyana kiyi shiru mana ki kyale'ta ta ɗan huta tun da kika gammu tare ai koma me yafaru zakiji chewar bello" hiyana dai hankalin ta bai kwantaba mikewa bello yayi yana faɗin ina zuwa san nan yakama hanyar fita daga gonar  


hiyana na ganin yaya bello ya tafi, ta matso kusa da diyana ta rike hannun'ta murya na rawa tafara magana "diyana meyasame'ki, chikin sarƙewar murya diyana tache "buba ne ya bugeni, dafe kai hiyana tayi tana faɗin  "diyana banache duk abun da buba zai miki kirinka hakuriba, ae'nafaɗa miki koma me kika masa a kan mu abun zai sake dawowa tun da mudai bamu da gata, bamu da mai tare mana fada ki dubafa kigani gaba ɗaya kauyen nan gudun'mu suke saboda kalar idon'mu, kinsa ni wasuma har mayu suke chemana, wai idon'mu ba irin na mutane bane irin na mayune bawanda yake kusantar mu kowa wai tsoro muke bashi, duk kauyen nan yaya bello ne kawai mai tausaya mana sai bappa, su biyu suka rage mana amma duk da kinsan da haka sai kije kirinka biyewa buba kina jawa kanki wata masifar koh
hiyana zata sake magana kenan idanta ya sauka a kan jinin dake jikin zanin diyana,a ɗan razane tace "diyana wai wan nan jinin kam na menene haka, chikin dashe war murya diyana tache "nima wlh ban saniba tunfa dana tashi yau da safe naketa ganin jinin yana fitowa yaki dai nawa, girgiza kai hiyana tayi tana faɗin "kuma kin duba bakiji chiwo'ba "ni banji wani chiwo'ba, shiru hiyana  tayi tana tunanin a dai iya karatun da bappa ya koyamu'su tabbas yataɓa faɗa musu idan mace tafara girma to zata fara jinin haila, to ke nan wan nan shine, to idan koh hakane ae no yakamata nafara jinin ba diyana ba, tun da ni che babba amma yau zanje na tambayi bappa gaskiya dan muji wan nan jinin na lfy  tayi nisa chikin tu naninta 
sae' taji muryan yaya bello yana faɗin tashi kuchi abinchi, dawo da kallanta kan'sa hiyana tai yana rike da samira rufe da pai pai, a dayan hannun'sa kuwa kwaryar nono ne, ajiye musu yayi yana faɗin "kutashi kuchi dawuri "yaya bello bazan'mu iya chin abinchin nan,mu barsu amrat ba, basu chi komai bafa tun jiya da safe hiyana tayi maganar kamar zatayi kuka,yaya bello yace "hiyana karki damu  kuchi kinji zanje in sayo muku rogo a dan dali sae' ku ɓoye ku kai musu yana gama faɗin hakan ya ɗau fatan yar'sa yanufi wajen da yake shuki, hiyana ta miƙe,ta kama hannun diyana ta tai maka mata ta miƙe zaune, san nan ta jawo musu samiran Abinchin gaban su ta buɗeq, ɗumamen duwon dawane mai kyau da miyar kuɓewa yaji man shanu gashi sai tiriri, yake kuma da yawa dan yakusa chika samiran nan fa sukafara chi, hannu baka hannu kwarya, saida suka chinye tas san nan suka jawo kwaryar nonon ma suka shanye, hiyana tamike ta ɗauki samiran da kwaryar nono ta nufi rafin ta wanke'su san nan ta debi ruwa a chikin kwaryar tash takuma kawowa diyana 

wai shin wanene bello?

Bello dai dashi da buba babansu daya mamane daban daban baban su buba kuwa yaya inna habibache inna habiba kishiyar mamansu diyana bello yana da mata yayi aure kuma a chikin gidansu yake zaune da matar tasa shiyasa duk taimakon da zaiyiwa su diyana yakeyi a boye dan indai yabari inna habiba tasani to wlh sharri zata masa tache yana nemansune ta haddasa masa masifa tsakaninsa da matarsa shikuma yana matikar tau saya musune shiyasa yake tallafa musu wan nan takai checchen wanene bello ke nan

hiyana ta kawowa diyana ruwan ansa diyana tayi tasha san nan hiyana ta dubi diyana tache to barinaje na chigaba da ɗeban ruwan "aa mutafi tare dai dan yanzukam nasamu karfi ae "to muje jerawa sukayi har inda bello ke noma sukaje, suka masa godiya tare da sallama, to bello yace san nan yaɗora da chewa "an jima zan kawo muku rogon bari na gama noma naje dan dali ya sawo muku koh sai kubawa su amrat ɗin "to yaya bello mun gode sosai hiyana tafaɗa tana kamo hannun diyana har sun juya zasu tafi hiyana takuma juyo tache yaya bello wai dan allah me buba yayiwa diyana jiyane naga jikin'ta sai jini yake


Shiru bello ya ɗanyi kamar mai tunanin wani abu, a nitse yafara magana babu abun da yama'ta dayaso yama'ta fyaɗe'ne sai kuma Allah ya tsare najiyo ihun'ta shine naje na kwache'ta, amma lokachin dana shiga ɗakin buban, dai dai lokachin yabuga mata sandar'sa a kai shiyasa kikaga tasuma,  batun jini kuma ina ganin girmane yazo mata amma kuje gida zansan abunyi a kai hiyana tace "yaya bello menene kuma fyaɗe "shikenan ku daije gida ba sai anmiki dalla dalla ba, chewar bello 
Jiki ba kwari  suka'nufi rafin suka ɗebi ruwa a kofu nan suka wuche gida  da sallama suka shiga gida inna na tsakar gida tana ƙirgawa lamrat robobin nonon dazata tafi talla dasu a tsiyache innar ta ɗago tana kallan'su " kuzo ku ajiye kofin, ku ɗauki tallar nan kuje ku sayarmin idan kun dawo ko da dad darene kwa karasa ɗiban ruwan "da sauri sukaje suka ajiye cups ɗin a kichin, suka fito suka dawo gaban ta suka tsugun na 

Kirga musu nonon inna tayi tana gamawa ta fara musu kashe di, "wlh ko kwana zakuyi a chan ku kwana amma karku dawo baku sayar da nonon nanba 
to kawai suka che mata san nan suka ɗauki tallar kowa da nata kwaryar suka nufi hanyar fita daga gidan suna masu tau'sayawa amrat dan kuwa yanzu duk aikin gidan nan ita kaɗai zatayi innalillahi wa inna ilaihir rajiun suna fita "diyana ta dubi hiyana tafara Magana wai yanzu yazamuyi ne kinfasan mu ba'a sayan faran'mu, dan chemana suke mayu ajiyar zuchiya hiyana ta sauƙe kafin tace "Allah na tare damu ai, muje kekam muyi addua,
 kai tsaye dandali suka nufa dukkan'su uku diyana hiyana lamrat sukabar amrat a gida daman ita amrat ba'a ɗora mata talla sai dai aikin gida kawai inna ke kasheta dashi 
suna zuwa kowa ta ajiye kwaryar nonon ta nan take mutanen wajen suka fara matsawa nesa dasu, sudai ko ajikin su dan in da sabo sun saba zaman'su sukayi shiru bawanda yache dawani kala a chikin'su 
wani  

Wani katon mutunne mummuna baki yazo wajen dasu diyana ke zaune ko sallama bai yiba ya dubi diyana yace ke ki dama min fura da nono na naira 100 ki kawo min masauki na, ya karisa maganar yana nuna mata hanya da masaukin nashi yake "nifa bansan wajen masaukin naka ba diyana tabashi amsa "dakin fita daga dan dalin nan  kika ɗan yi kwanar hagu zakiga wata bukka to nanne wajen nawa "to zan kawo ma chewar diyana, juyawa yayi yabar tafi,
Hiyana ta dubi diyana dake kokarin dama nono a kwarya dan ta damawa mutumin tache "aa diyana wlh bazaki kai masaba' nifa tunda nake zuwa dan dalin nan ban taɓaganin mutumin nan ba kai ni ko sau ɗaya ma ba a dan dalin kawaiba koma aina ban taba ganin'saba
Girgiza kai diyana tayi tana faɗin aa hiyana kibari nakai masa in bahakaba Kinsan dai bamai sayan fura da nono mu ko "to shike nan diyana kije,ki kai masa amma kiyi addua dan wlh in tsoran, karya sacheki kinga ba sanin sa mukayiba a diyana ta amsa da "to tafara dama furan 

bajimawa tagama dama furan ta ɗauka tanufi inda mutumin ya nuna mata, a bakin kofar bukkan nasa ta tsaya ta masa sallama, yana daga chikin dakin ya amsa sallamar tare da faɗin  "ki shigo mana, diyana ba musu ta shiga a zaune ta'sameshi a tsakiyar ɗakin, gabansa taje ta ɗuka ta ajiye masa damammi yar furan a gaban sa, tana faɗin a ban kuɗin murmushi yayi ya ɗago jajayen idon'sa yana kallan ta "yarinya mai kyau kinasan kuɗi koh, diyana zatayi magana sai taji ya riko hannun'ta yachi gaba da faɗin "ni zan baki kuɗi dayawa in kinaso ya kai karshen maganar, yana kokarin rungumar'ta
Da karfi diyana ta ture'sa  tamike da gudu ta nufi waje, tana waige waige ko mutumin yana binta, a dai dai bakin kofar ta waje tayi karo da bello, baya tayi zata faɗi da sauri bello ya riko kafaɗar ta yana kallon chikin idon tana yana faɗin lfy diyana ita kuwa sai waige waige take, murya na rawa tache "yaya bello wlh shine ya kamamin hannu wai zai bani kuɗi
A'fusache bello yache "ae daman bayan'ki nabiyo,  yanzu zuwa'na dan dali na tambayi hiyana ina kike shine  fadamin kinzo kawo wa wani nono, yanzu dai ki koma dan dali ina zuwa yayi maganar tare da sakin kafaɗar ta
Da gudu diyana tawuche tanufi dandali, shi kuma bello yanufi chikin ɗakin mutumin zaune ya samesa yana shan furan da diyana ta kawo wani kallan banza bello ya bishi dashi daga sama har kasa kafin yache malam wanene kai " mutumin yaɗago kai daniyar yayiwa bello rashin mutunchi sai kuma yaga bello chikakken namiji'ne mai ji da karfi dan ko faɗa zasuyi bello zai masa dukan mutu, dan haka sae yanitsu chikin girmama'wa yace "ni bakoh ne rai a ɓache bello yafara magana "eh ae nasan kai bako ne tun da ban taɓa ganinka a nan ba chewa nai daga ina kake, kuma meyakawo ka garin nan shiru ya ɗanyi kafin yache "daga kauyen tongo nake kuma hanyache tabi dani tanan na tsayane dan na hutane, idan na huta sai nachigaba da tafiya "shine zaka lalata mana yara bello yayi tambayar chikin tsawa,  shiru mutumin yayi
Yaya Bello ya chigaba da chewa aradun Allah idan kasake yiwa ɗaya daga chikin kannena magana wlh sae dai a ɗau gawarka murya na rawa mutumin yace "kayi hakuri bazan sakeba, bello bai sake magana ba yasa kai yafeche daga dakin a fusache, 

 wajen su diyana yanufa,suna zaune suna yar hirar'su bello yazo kusa dasu kamar mai sayan nono kasa kasa yafara magana "duk wanda ba zai sayi nono a nan ba sai dai abari, karku kuskura ku sake  kai ma wani sai dai ya hakura san nan kuma  ki damamin fura da nono na 100, da sauri hiyana ta bude kwaryar nono ta ɗauko roba biyu ta juyesu a chikin wani dan karamin kwarya tasa fura biyu ta dau ludayi tafa damawa, tagama ta juye masa a leda ta mika masa,hannu yasa ya ansa, yasa ɗayan hannun sa a aljihun ya chiro kuɗi naira 500 ya juya gabas da yamma dan yaga akoi mai kallan sane ko babu, dan bai san inna tasani, mikawa hiyana kuɗin yayi, Kin ansa tayi, tana girgiza masa kai alamar ya bar kuɗin kawai, kan pai pan dasuka rufe kwaryan nono ya ajiye musu kuɗin kasa kasa yache kichere 100 na nono kibawa inna, sauran 400 kisaya muku rogon 100 ki ajiye 300 kuma zai muku am fani gobe, bai jira amsar suba yajuya da sauri, dan ya lura hankalin mutane yafara dawowa kansu kar wata matsalar tazo tafaru

wuni zumbur su hiyana sukayi awajen ban da bello daya saya nonon bawan da yasake saya, shima mutumin da diyana ta kai wa nono bai basu kuɗin ba, haka sukayita zama da nono har karfe 6 na yamma, san nan hiyana ta miƙe tana faɗin kutashi mutafi gida, mikewa diyana da lamrat sukayi  suka ɗauki kwaryar nono suka ɗora akansu suka kama hanyar gida
Suna tafiya ne diyana tache "wai lamrat waya saye furan ki  na jiyane lamrat tace "ae dayake kinga jiya kasuwane akoi baki,ni kuma kinga ai idona ba irin naku bane ba wanda yake chemin mayya shiyasa bakin suka rinka sayan nonon
Hiyana ta girgiza kai tana faɗin "ae kema da idon ki yayi irin namu babu wan da zai saya koda bakin nema, suma chewa zasuyi ke mayya che
Diyana tache "yanzu ya zamuyi da inna, ɗaure fuska hiyana tayi tana faɗin "ya zamuyi kuwa dukane dai kamar yadda muka saba shi zamusha "Allah kakawo mana mafita chewar diyana, dukkan su suka amsa da ameen

Da sallama suka shiga gidan sai faman rakuɓe rakuɓe suke, muryan inna che ta daki dodon kunnen su daga ɗaki, tana faɗin "ae shiyasa nakesan hiyana ta Auri buban kinga ita hanyar mutuwar ta mai sauki ne, sukuma sauran zamusan yadda zamuyi dasu
 amma bazamuyi kisa a chikin gidan nan ba dan kinsan al adar kauyen nan, amma na chi al'washin duk dabbobin nan nine zan gajesu wlh dukkan'su nizan zama sanadiyar mutuwar su , wata murya mara daɗin ji sukajiyo daga chikin ɗakin inna tana faɗin "ae wahalar da kike ba suma habiba am zata iya zama ajalin su, Wani dariya inna tayi san nan tace ae yanzu ma kara nin'ka musu wahalar zanyi, kuma sati nan mai zuwa za'a ɗaura Auren buba da shigiyar nan .

Baya baya sukayi suka fita daga gidan suna fita suka rushe da kuka,suna kuka suna tafiya har suka isa kasan itachen mangoro dake ɗan bayan gidan su  zama sukayi awajen,suka sauke kwaryan nono dake kansu suka chi gaba da kukan su, sai da sukayi kukan mai isarsu san nan sukayi shiru dan kan su, dan duk chikin su ba mai rarrashin dan uwansa

Suna zaune awajen har aka kira sallar mangariba, tukun nan suka mike, suka ɗauki kwaryar nono jiki ba kwari suka nufi gida ko da suka shiga, a tsakar gidan suka samu inna jiki a sanyaye suka karasa chiki gaban ta sukaje suka tsugun na, suka sauke kwaryar,sukayi jugum jugum gwanin ban tausayi suna jiran hukunchi, inna naganin haka tagane basu sayar ba miƙewa tayi tanufi ɗaki ta dauko wani katan bulala tafito, tafara bugun su dashi
Diyana da hiyana suka hadu suka rufe lamrat bulala na sauka ajikin su, bugun su inna take baji ba gani abun tun suna iya kuka ma har kukan nasu ya daina fita duk sai da tamusu ruɗu ruɗu da jiki, ta kyale su ta kuma fiche daga gidan tana ta mai da numfashi, Amrat na ganin inna ta fita, itama tafito daga ɗakin bappa tayo wajen su da gudu tana kuka haka suka haɗu a tsakar gida suka rungumi juna sunata kuka, sai da sukayi kuka mai isar su 
San nan su kamike jikin dukkan su jikin su sai karman yinwa da wahala yake, suka nufi dakin bappa  da sallama suka shiga amma bai amsa musu ba, akusa dashi suka zauna yana kwanche idon sa Abuɗe yana kallan sama
   chikin shesshekar kuka hiyana tace "bappa ina wuni shiru bai amsa ba "  bappa bakada lfy ne diyana ta tambaya a ruɗe, nan ma shiru bai amsa ba Hiyana tasa hannu ta taɓa shi ko motsi bai yiba a firgiche tafara jijjigasa tana ihu tana kiran sunansa Amma shiru
Chikin kiɗima hiyana tafito daga ɗakin tayi waje tana ihu



London United Kingdom

Tsaye yake a tsakiyar babban palon su hannun'sa ɗaya na rike da trolley ɗayan hannun kuma  yana rike da wayarsa yana latsawa, sanye yake chikin black jeans da blue t-shirt ya rage tsawon gashin kansa, yanzu gashin bata wuche zuwa iya wuyar'sa ba, yana sanye da booth black colour a kafarsa dakuma p-cap shima baki hannun sa na ɗaure da wani haɗadɗen agogon daimon mai kyau da tsada fiskar nan kuwa babu alamar annuri akanta a taure take tam kamar an aiko masa da sakon mutuwa amma yayi kyau sosai laɓɓansan nan kuwa kamar yasa jan baki jaa sosai ga sajen sa a kwanche yasha gyara bakaramin kyau yayiba, faffaɗar kirjin san nan kuwa a tsaye dam dam kamar zai fashe ga damtsen hannun sa a chike kamar zasu yaga hannun rikar, almost 10mnt yana tsaye

A hankali  Aryan ke sauko daga saman stair ɗin  shima shigarsa iri ɗaya dana DON abun mamaki shima ya yanke gashin kansa ya rage mata tsawo, rike da trolley shima yana ja sauko wa yayi yazo dai dai inda DON ke tsaye, da wan nan sexy voice nashin ya furta sorry bro,DON bai tanka saba yaja trolley sa yanufi kofar fita, da sauri Aryan yabi bayan sa sukayi waje tare, da gudu rundunar jibga jibgan sojojin masu ji da lfy da karfi sunsha trenin  suka nufosu, da sauri abdol ya karɓi trolley hannun DON, Shahram kuma  ya karɓi trolley  hannun Aryan, suka samu su a chikin haɗaɗɗun motachin, da akajera musu dan tafiyar 

Aryan yadubi  DON yace "muje a mota ɗaya koh,DON batare daya amsa ba yace "wai ina Aiman da Ahmad ne "ae tunjiya suka wuche naija Aryan yabashi amsa yana kallan fuskar sa kama hanya kawai DON yayi batare daya sake magana ba yanufi motar, da sauri abdol yabuɗe masa kofar motar, slowly ya shiga ya zauna, ɗaga hannu Abdol yayi ya sara masa san nan ya rufe kofar motar,  zagayowa ta ɗayan kofar motan Aryan yayi, da sauri Shahram ya buɗe masa kofar a nitse ya shiga ya zauna Shahram ya sara masa san nan yarufe kofar motar
Da gudu sojojin suka hau nasu motochin su suka tadasu, da matsakai chin gudu suka nufi gate ɗin tun basu kariso ba security suka wangale masu gate ɗin,  da gudu suka danna hanchin motochin waje,motar sojoji 2 a gaba sai motar su DON a tsakiya sai motochi 2 na sojoji a baya gudu suke shararawa a kan mikakkiyar titin

Aryan ya dubi  DON yace sai dai fa mutafi da jet ɗinka dan kuwa nawa yana naija dashi su Ahmad suka tafi "Ok kawai DON yache, chikin kankanin lokachi suka isa Airport Already angama shirya komai su kawai a ke jira, batare da ɓata lokachi ba suka fito daga chikin moton su suka nufi kyakkyawa kuma haɗaɗɗen privet jet ɗin DON mai ɗauke da tambarin sunan'sa PRINCE SAFRAS suna shiga batare da ɓata lokachi ba jirgin yaɗaga sai malam Aminu Kano international Airport Kano Nigeria



More comments and share pls 


*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*



💖 The talent troupe writer's 💖

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 5*
          

DON

Misalin karfe 5 na yamma jirginsu yayi landing a malam Aminu information Airport kano, wasu dan kare dan karan motochi 5 sukazo ɗaukansu ga motochi 3 chike da sojoji, basu wani ɓata lokachi a chikin jirgin ba suka fito tare suka jera, sai wani kara ɗaure fuska suƙe da ka gansu kaga wayan da akawa zuwa dole, musamman DON nashi daban ne,  Abdol da Shahram suna biye dasu a baya,rike musu da trolley sojojin nan na ganin fitowar su suka jinro daga nasu motochin suka nufe su, Fahad na ganin fitowar su ya nufesu da sauri, yana ɗan murnushi hugging na DON yaje yayi yana faɗin "Wellcome back bro, hannu DON yasa yayi taying ɗin yana faɗin "missed U my blood "missed U too yayi maganar yana zare jikin sa daga jikin DON, yajuya yayi rungume Aryan ma, yana faɗin yaya Aryan nayi kewar ku sosai, rungume sa sosai Aryan yayi yace "nima nayi kewar ka sosai my blood, ganin DON yayi gaba ya barsu ne yasa Fahad ya saki Aryan da sauri sukabi bayan DON wajen motochin nasu suka nufa,nan take su Haidar suka fara musu sannu da dawowa ko kallan in da suƙe DON bai yiba bare su saran zai amsa musu, ya shige motar ya zauna yana yamutsa fuska, Aryan ma shiga mota yayi riƙe da hannun Fahad sai da suka zauna san nan ya dubi kannen nasu yace "yauwa to ku shiga mota muje gd koh sai mu gaisa a chan zaifi, da sauri suka koma chikin mota, drivers su kama motochin key da gudun gaske suka bar Airport ɗin gudu suƙe shararawa sosai a kan mikakkiyar titi, sai da suka kusa da bakin gate ɗin gida suka rage gudun motochin, batare da ɓata lokachi ba security daƙe tsaron gate ɗin su wangale musu gate ɗin a nitse suka kutsa chikin gd, kai tsaye parking space suka nufa suna kashe motochin, Shahram da Abdol suka fito daga nasu motar da gudu su kazo suka buɗewa DON da Aryan kofar motar, a nitse DON ya zuro kafafun'sa waje kafin ya fito gaba ɗaya bai bi ta kan kowa ba yanufi ɓangaren sa, Aryan ma ɓangaren sa yanufa riƙe da hannun Fahad suna tafiya suna hira,  Yusuf ya karɓi trolley DON daga hannun Abdol yabi bayansa da shi  Ahmad ma ya karɓi na Aryan daga hannun Shahram ya nufi ɓangaren Aryan ɗin, su Haidar kuwa kowa yakama kansa yayi part nasa 

Ammi na zaune akan kujera a palan'ta tasha kwalliya chikin wata ɗankarekiyar lace baki da ratsin ja mai shegen kyau ga wasu gwala gwalan data zuba a wuya da hannu ta,ba karamin kyau tayiba inka ganta  kace bata,wuce 25 years ba, Aunty farida tashigo da sallama ɗauke a'bakinta, da fara'a Ammi ta amsa mata sallamar, shigo chiki palon tayi ta zauna saman sofa mai zaman mutun 2,tana fuskantar Ammi "feeda dayake haka Ammi ke kiran Aunty farida feeda,ina junior yake "Junior yana wajen mardiya chewar Aunty farida " ok kawai Ammi tace tana kallan face ɗin Aunty farida "Ammi magana nakesan muyi dan Allah "ae feeda tun shigowar'ki Na fahimchi hakan, badamuwa ina jinki "Ammi daman, magana che a kan price, tun!bata kai karshen maganar ba Ammi ta ɗaga mata hannu, tana faɗin a'a feeda, kinsan dai bazan saka bakina a maganar bako,babu ruwana, dan kuwa kinsan mai martaba idan yayi magana baya chan'zawa "Ammi mun san Abba idan yayi magana baya sau'yawa, amma ae ke ki nasashi ya sauya magana koh, dan Allah Ammi, ki samana baki pls takarisa maganar kamar zatayi kuka "aa feeda babu ruwa'na wai ni ina ruwa da wani prince, ae wan nan ɗan Ummi ne ba ɗa naba  kije kisamu Ummi ita tashiga masa amma ban dani "dan Allah Ammi kinfasan Abba yafi sauraren maganarki fiye da kowa a gidan nan" Feeda kin dai san in nache bazanyi abuba tofa bazanyin bane koh dan haka kibar maganar kawai,"to shike nan Ammi na barta barinaje namusu sannu da zuwa "baki Ammi ta taɓe tana faɗin eh lallai feeda ɗaure wa karya gindi,su da suke kannenki basu zasuzo su gaida kiba ke zakije ki gaida su lallai yaran nan suna abun dasu ka gadama
Aunty farida tamike tana faɗin kai Ammi kedai babu ruwan ki tsakanina da yan uwana ko inche yayyuna dan yanzu nabasu girma takai karshen maganar tana kokarin fita daga pallan bata tsaya ta jira amsar Ammi ba ta wuche abunta tana fita tayi part ɗin DON 

Da sallama tashiga palan nasa babu kowa, kai tsaye betroom ɗin sa tanufa, yana tsaye gaban mirrow yana gyara gashin kansa,sanye yake da bakar jallabiya, da alama wanka yayi, jin sallaman ta yasa yaɗago green eyes nashi ta chikin miron yana kallan'ta, batare da ya juyo ba "yace Aunty babba yanzu nake tunanin inje in ganki, kafin  inyi barchi
Harara wasa Aunty farida ta wurga masa tana fadin "daka ganniba dole kafaɗi haka nasan da banzoba ba zuwa zakayi ka nemeni'ba, slowly ya juyo ya zuba mata green eyes nashi nan kafin yace "a'a Aunty farida ae kema kinsan dole na nemeki


Karisa shigowa chikin ɗakin tayi tai, a bakin katafaren gadansa dake shinfiɗe da White bet shit ta zauna tana faɗin,"to ya hanya "Tafiyar da bada san ranmu mukayotaba Tafiyar dole,ya kae karshen maganar yana ɗaure fuska , guntun murmushi Aunty farida tayi kafin tace, "hmmm yanzuma nagama magana da Ammi kafin nazo nan, kara ɗaure fuska yayi yana faɗin "ai dama baki mata magana ba, da baki ɓata bakin ki bama dan nasan baza ta saurare mu ba jinjina kai Aunty farida tayi kafin tache,mudaiyi addua karkadamu inshaa allah komai zaitafi yadda kakeso,tana kae karshen maganar tamike,bari na dubo Aryan, batare da ta jira amsar saba tayi waje dan tasan ba amsa war zai yiba,"juyawa yayi yachi gaba da abun daya'keyi


 Tana fita ɓangaren DON tanufi ɓangaren Aryan bakin ta ɗauke da sallama tashi palon babu kowa a palon sai sanyi A.c dake ratsa jikin  betroom nashi tanufa, sallama tayi a bakin kofar kafin ta tura kofar tashiga kwanche ta same sa akan katafaren gadansa,idon sa a lumshe da alama barchi,yafara ɗaukan, jin an taba kofar ne yasa ya buɗe idon'sa da kyar, yana ganin ta ya dan saki fuska yana da kyar ya buɗe baki da murya irin na mai barchi yace "Allah ya barmana ke aunty mu wlh naso nazo,na dubaki amma barchi ya hanani, murmushi tayi tana faɗin "an dawo lfy my tagar "lfy lau lovely Aunty "to bari na kyale kayi barchin ka daman dai ina san inzo inji an iso lfy ne tun da lfy ba wata matsala ayi barchi lfy sai mun haɗu awajen chin abinchin dare ahuta gajiya,tana kae karshen maganar ta juya tanufi waje juyawa yayi shima yana fuskantar gefen dama yachigaba da barchin daya fara" 

Misalin karfe 8 nadare gaba ɗaya family Abba sun haɗu  a palon, dan chin abinchin dare, banda Aryan DON da kuma Fahad, sun zauna shiru suna jiran fitowar Abba, Ammi che ta katse musu shirun da chewa "nikoh meyasa mairo da salma basu zo bane kodai basu da lbr meeting martaba ya shirya
   A tsiyache Aunty amarya tace ke Aisha kidaina ɓatamin su nan yarinya, kuma ina ruwanki da zuwar ta inba muna furchiba
"haba Aunty amarya daga tambaya chewar Ummi "ke Ummi baa kasa dake ba idan kemaɗin muna furchinne sai naji akule Aunty mardiya tache "a'a wlh ya isheki haka gaskiya bazaki zauna kina zagin iyayen mu, a gaban mu'ba tayi maganar tana nuna Aunty amarya ta hannu, hannu Aunty farida tasa ta ɗan buge bakin Aunty mardiya, tana faɗin to ke ina ruwanki ae dukkan'su iyayen'mune wan nan fadar'sune tsakanin'su
Umar ya ɗago rai a ɓache yana faɗin "to ae gashi muma Aunty mardiya rashin kunya kike neman kiyiwa mahaifiyar tamu, A'kule haidar yache "haba Umar kai bakaji abun da Aunty amaryan ke faɗe bane, dafe kai Khalid yayi yana faɗin, to ya isa haka ae kuyi shiru, amma ina ba wan da ya saurari Khalid sunki yin shiru wan nan ya faɗa wan nan ya faɗa abun hat'tafara zama kamar faɗa
Dafe kai kawai Ammi da Ummi sukayi suna kallan ikon Allah kowa kokari yake yakare ma haifiyar'sa wan nan abu dame yayi kama" sai faman kache na che suke abu har ta fara zama kamar faɗa

Kamar daga sama sukaji gyaran murya daga bayan su nan take, sukayi tsit dan kuwa ko basu juya ba sunsan mai wan nan voice ɗin tsaye yake a bakin kofar shigowa palon, yazura hannu a aljihun wandan,sa' yana kallon su fuskar nan tamkar batasan menene dariya'ba a daure take tam, a nitse yafara takowa izu chikin palon,wajen table ɗin yanufa,da sauri Haidar yamike, yaɗan jamasa kujeran zaman, baya tayadda zaiji daɗin zama gaba ɗaya matasan suka mike,ban da Khalid da Aiman da Yusuf jiki na kerma sukafara "faɗin sannu da fitowa yaya Aryan  zama yayi batare daya amsaba yana binsu da ido jiki ba kwari suma suka koma suka zauna, murya na rawa Zahra tache "sannu da dawowa yaya Aryan
ko kallan in da take bai yi ba bai kuma amsa sannu nata ba ita ma,nan take kowa a chikin su yasha jinin jikin sa kallon fiskokin su yake sosai kamar mai karantar wani abu a tattare dasu

"me za'a zubamaka ne Aryan Ammi ta tambaya tana kallan fiskar sa, sai lokachin yadawo da kallansa kan Ammi kana yaɗan saki fuska calmly yace "abun daya dache kawai  "ok to bintu kuzuba masa ferfesu kayan chiki da fraid rice Ammi tabawa masu aikin umarni, da sauri suka fara zaran plate dan su zuba masa,hannun su har rawa yake dan tsoran sa da sukeji suna kokarin zuba masa abin chin'ne 
Aunty amarya ta daƙa musu tsawa "bashi zaku zuba masaba dan babu wanda ya isa ya zabawa ɗa na abun, da zai chi sai ni dana haife'sa kowa a gidan nan yana da nashi ɗan ae to kowa ya kula da nashi ba ruwan shi dana wani,dan haka tuwon shinkafa zaku zuba masa
Shiru yan aikin sukayi sun rasa umarnin wa zasu bi "kamar daga sukaji Aryan yana faɗin ku bar'shima kawai am ok, Aunty amarya zatayi magana sukaji takun tafiya ta bayan su dukkan su suka juya ban da Aryan,  tafiya suke chikin kwanchiyar, hankali sun jero kamar ,sanye suke chikin jallabiya dukkansu Fahad bakin DON kuma fari tas, fiskar sun nan dukkansu babu wasa a ɗaure taku suƙe irin na chikakkun maza, kamar wasu yan biyu haka suka jero dan dai kawai DON yafi Fahad tsawo dakuma chika sai kuma kalar kwayar ido daya ban ban tasu Fahad kwayar idon sa baki ne DON kuma green amma ban da haka kaman'nin su ɗaya
 
A take palon yayi tsit suka kara nitsu wa dan duk gidan idan ka chire Abba Ammi da Ummi Aunty farida sai Aryan to kowa na gidan tsoran DON yake, har Aunty amarya tsoran sa take kamar me dan tasan DON ba wasa ba'a kawo masa wargi yanzu zai sumar da mutun, bakaramin tsoransa Aunty amarya ke jiba, da sauri Haidar yamike ya gyara musu kujerar da zasu zauna, a nitse suka zauna slowly DON ya ɗago yafara gai da iyayen nasu, da fara'a suka amsa masa, da sauri kannen nasu suka fara ɗaga masa gaisuwa, bai amsa gaisuwar kowa daga chikin su ba sai ma wayar sa daya chiro daga aljihun sa yafara latsawa 
 "prince me Za'a zubama,Ummi ta tambaya tana kallan face nashi, shiru ya ɗanyi kamar mai tunani sai kuma ya dawo da kallan sa kan Aunty farida,batare dayayi magana ba, Aunty farida ta gane me yake nufi da sauri tace,da masu aikin "ku zubawa kowa ferfesun kaji da chips kawai
Chikin sauri, suka fara zaran plate suna zubawa suna mika musu

A hankali Aryan ya ɗau spoon yafara shan ferfesu, wani kululun bakin chikine ya tokare wa Aunty amarya makoshi tana san tayi magana tana tsoran DON a zuchiyar ta take faɗin wai komai farida tace a gidan nan ko, basaso sai sun yarda, gashi dai ni tana haifi yaran nan amma bani da wani iko da su, maganar farida tafi nawa muhim manchi dole nayi maganin abun wlh bazayyiwu'ba 

Da Sallama Abba yashigo palon yana sanye chikin jallabiya fara tas kai tsaye table ɗin yanufa,tun bai karisa zama ba suka fara gaishesa,Sai da duk suka gama gai'dashine ya haɗesu yabasu amsa ɗaya  da sauri bintu mai aiki ta rari plate ta zuba masa abinchin zaɓin Aunty farida wato ferfesun kaji da chips
Tunda Abba yaga irin abinchin'ne a plate ɗin kowa dake wajen yagane zaɓin Aunty farida ne dan haka shima karba kawai yayi yafara chi

(sai yanzu nasan a inda yan gidan suka gado rashin magana dan kuwa shima Abba baya magana shiru shirune)

Shiru kake jin palan ba mai magana sai karan spoon kawai zakaji,da sautin A.c dake tashi 

Bayan sungama chin abinchin ne DON ya mikewa ya nufi hanyar fita daga palon, harya kai bakin kofar sai kuma ya juyo yana faɗin "dukkan ku mazan nan kusameni a ɗaki,ke kuma Zahra karfe 10 dai dai ina bukatar ganin ki bai jira amsar su ba yayi waje, da sauri suma suka muke sukabi bayan'sa
Suna fita Abba ya dubi su Ammi yana faɗin "sun aikata wani abun da ba dai dai bake nan,Ammi dai shiru tai bata bashi amsaba hakama Ummi
aunty amarya che tache "zagina mana sukayi, Shiru Abba yayi dan yasan halinta sarai yanzu haka ita ta takalo faɗan "ranka shidade inasan magana dakai chewar Ammi, Abba zaiyi magana
 Aunty amarya tarigashi dache'wa "to ae yau ba ranar ki bane bake kike dashi ba sai ki bari sai yadawo dakin ki,  shiru Ammi tai dukkansu ba wanda yasake magana

DON na shiga dakin sa ya zaune a gefen katafaren gadon sa  yana jiran kannen nasu
Da sallama suka shigo gaba dayan su
Aryan ya wuche ya zauna a kusa da DON a bakin gadan, shi kuma Fahad hayewa yayi kan gadon abunsa ya kwanta ya dauko wayarsa yafara latsawa,domin kuwa yariga da yasan dalilin kirannasu to shi baya chiki maganar

Dukkan su zama sukayi a saman sofan dake  ɗakin Khalid ma agefen gadon yazauna suka sa DON a tsakiya shida Aryan ryan
 Almost 10mnt DON bai che dasu komai ba kamar ma baisan da zaman su a ɗakin ba, shiru sukayi suna tunanin me yasa ya kira'su kodai yaji abun daya faru a palo ne  calmly yafara magana "daga yau sai yau duk wanda ya sake,idan iyayen mu suna magana a tsakanin'su yasa baki kunsan me zai biyo baya ina ruwan ku da faɗan su 
Shiru sukayi bawanda yache kala
DON yachi gaba dace wa "last warning nake muku idan kuka bari nasake kama'ku da irin wan nan dabiar bama sai nayi magana ba, kai Haidar da kai da Umar kuje wajen kwallo bayan nan kufara frog jump ina zuwa ya kai karshen maganar yana kallansu Haidar da Umar ɗin 

 mikewa sukayi suka fita jiki ba kwari suna fitowa Umar ya dubi hadar yafara magana "mun shiga uku wlh, yau zamu gane kuren'mu wayyo sheidan baka mana adalchi ba daga dawowar big bro muzai fara yiwa hukunchi ke nan wayyo Allah,
Chikin nar kewar murya Haidar yache "waima daman meyakai'mu shiga fadar matane yanzu gashi zamu karbi hukunchi,wlh ni nasan yau sai munkasa mikewa da kafafun'mu
Haka'dai sukayi ta surutai suna tafiya har suka isa wajen kwallan dukawa sukayi suka fara frog jump ɗin.


Miƙewa Yusuf Aiman Ahmad sukayi suka musu sai da safe suka fito nuka kowa yanufi part nashi ɗakin yarage daga DON Aryan Khalid Fahad, shiru suka zauna kowa na latse latse a wayar sa almost 10mnt Khalid ma yamiƙe ya musu sai da safe yayi waje, Khalid na fita Aryan ya ajiye wayarsa ya dawo da kallon sa da kuma hankalin sa kan DON yafara magana "zanje nayi magan da Aunty amarya batare da DON ya ɗago ba yace "a kan me fa "akan abun daya faru dazun a palo mana kasan komai kaji komai da kunnen ka,kasan wayafara taɗa rikichin to yakamata mu dakatar da abun tun bai yi nisa ba sai lokachin DON ya ɗago green eyes nashi yana kallan Aryan ɗin kafin yache "a'a ka kyaleta to idan ma kaje me zakache mata itafa ta haifemu bamu muka haifetaba dan haka kabar abun zamu'san abunyi a kai "a'a DON duk da ita ta haife mu amma ai idan tana kuskure addini ya halakta mana mu mata gyara,amma tun da kache in bari to shike nan zanjira matakin dazaka ɗauka
DON bai sake magana ba shiru suka zauna na dan lokachi kafin Aryan yamike ya musu sai dasafe yanufi waje
 juyowa DON yayi yana kalli Fahad dake kwanche yana latsa waya "kai wai a nan zaka kwana ne, da sauri Fahad yace "a'a yanzu zan tafi ya kai karshe maganar yana miƙewa, "sai da safe yache da DON batare daya jira amsar DON ba ya sauko yanufi waje


Karfe 11 nadare

Sau kowa yake a nitse yana sanye da kayan barchi dogon wando da riga mai dogon hannu yan shara shara marasa nauyi white colour jikinsa sai kamshi yake, ya tara gashin kansa ya ɗaure a baya sosai kayan suka fito masa da surarsa na chikakke kuma jarumin namiji mai ji da lfy da karfi,taku yake irin na jaruman maza masu jini ajiki, kofar baya ya buɗe ya fito waje kai tsaye wajen kwallo yanufa

Frog jump yasamu sukeyi da kyar da kyar suƙe iya ɗaga kafa duk sun galabai ta sama sama suke numfashi sun jiƙe sharkaf da zufa
da kak'kausar murya yache "kutashi ku tafi ɗaki a gala bai che Umar yace "sorry bro wlh bazan iya miƙewa ba   da kyar Haidar ya iya buɗe baki shima yace "wlh yaya prince nima bazan iya tashiba
Chikin tsawa DON yafara magana "zaku kwana a nan ke nan, zaku tashi kutafi ɗakine ko sai nayi kwallo daku ai tun bai kai karshen maganar ba suka tattara sauran karfinsu gaba daya suka miƙe, har jiri suke gani rungume juna sukayi suna ɗungisa kafa da kyar da kyar suka nufi hanyar part nasu, shi kuma DON ya juya ya koma ta in da ya fito


jimeta yola 


Jama'a ne zaune a kofar gidan su diyana suna karɓan kai suwar rasuwar bappa chikin gida kuma matane zaune suna yan koke koken su, hiyana diyana Amrat lamrat kuma suna zaune a kusa da rafe kasan wani bishiyar mangoro suna kuka, duk fuskar su ta kunbura kuka suke sosai kamar ransu zai fita chikin kuka da dashewar murya diyana ke faɗin "shike nan bappa ya mutu ya bar mu munshiga uku ina zamusa ranmu wayyo allah "da kyar hiyana ta iya buɗe baki muryan ta duk ya dashe saboda kukan data sha tafara magana "a'a diyana ki daina chewa munshiga uku gaskiya bamu shiga uku ba tun da mun rike Allah inshaa Allah, Allah bazai kyalemu muchigaba da wulakantaba chikin shessheka lamrat tace "eh hakane Aunty hiyana addua kawai bappa ke bukata,  duk kansu suka haɗa baki su kache Allah yajikansa da rahma
Diyana tache "hmmm jiya fa Bappa yarasu amma baza abar'mu mu dan huta ba muji da rasuwar bappa ba inna tace, dan Allah yanzu muji da wanne muji da rasuwar Bappa ne ko kuma muji da ɗebo ruwa
Mikewa hiyana tayi tana faɗin "kutashi ma mukarasa ɗeban ruwan nan kar inna ta buge'mu da kyar suka mike suka nufi rafin suna rike da cups a hannunsu
Sun ɗebo ruwan zasu wuche ke nan sai sukaji muryan yaya bello na kiran'su daga chikin gona, chikin gonar suka nufa, a zaune a inda yasaba zama suka same sa ga tulu sababbi guda 4 a gabansa
A gaban sa suka duka suka gaidashi ya amsa chikin faraa san nan yamusu taziyar mutuwar bappa tare da adduar Allah ya jikansa suka amsa da ameen, kana yache ku ɗauki tulu nan nan dasu zaku rinka deban ruwa dan ku nasaya, duk da kukan rasuwar bappa dasuke hakan bai hana'su yin murna da ganin tulun ba ɗauka sukayi suna murna sai godiya suke masa suka fito gonar suka nufi rafi, ruwa suka ɗeba a sabon tulun su sai murna suke,suka nufi hanyar gida

 One day later 

 yau Bappa yachika kwana uku da rasuwa, jama'a sun watse babu kowa a kofar gidan kowa kama kansa


diyana  hiyana da lamrat sunbar amra a gida tana tikar aiki duk kansu suna dauke da tulun da yaya bello yasa musu suka nufi rafi suna tafiya suna yar hirarsu
Diyana tache "wai ya akayi inna batayi magana akan tulun nan bane Girgiza kak hiyana tayi tana faɗin "hmmm ai bata lura bane inda ta lura ai da saita tambayi waya bamu ko kuma ma ta fasasu 
Lamrat tache "to yanzu idan inna ta tambayi waya bamu tulun me zamu'che mata,dogon tsaki diyana taja kafin tace "sai muche muma ba mu san mutumin daya bamu'ba,yaga muna ɗeban ruwa da kofine sai yabamu "yauwa diyana gaskiya kin kawo shawara daman sai tunani nake idan inna ta tambaye mu me zamu'che chewar hiyana,tayi maganar dai dai lokachin da suka iso bakin rafin ruwa suka debo,a tulun suka juya suka nufi hanyar gd, 

"hiyana wai yan zu haka zaki Auri buba diyana ta tambaya, buɗe baki hiyana tayi zatayi magana sai taji an ture tukun dake kanta ta baya ya faɗi ya tar watse, asukwa'ne buba tagani tsaye yana mur mushin mugunta diyana naganin buba ta kwasa a guje tayi hanyar gida, gudu take iya karfinta har ta iso dai dai zata shiga ke nan tayi tun tube da dutsen kofar gidan ta faɗi kasa  tulun ya faɗi kasa ya tar watse, wani kukan bakin chiki ta sake kuka take kamar ranta zai fita
 a wan nan yanayi Hiyana da lamrat suka zo suka sameta tai maka mata Hiyana tai tamike tsaye ga goshin ta sai jini yake, dukkanbsu sai hawaye suke haka suka shiga gida

 inna dake zaune a tsakar gd tache ina ruwan, kuma tun dazun na zauna a nan nake jiranku zan dora ruwan shayi
Chikin shesshekar kuka lamrat tace "wlh inna buba'ne ya kifar da ruwan
Da sauri inna tamike tana faɗin buba na zakuwa sharriko ai nama buba ya ganku bare ya kifar da ruwan to wlh yau zaku yabawa aya zakin'ta, suna tsaye awajen suna matsar kwalla, har inna tashiga ɗaki ta daukoh wasu manya manya bulalin bishiyar dalbejiya 

Ta nufosu gadan gadan baji ba gani tafara sauke musu zabga zabgan bulalun nan ajiki babu ko imani bare tausayi, ihu suƙe hiyana da diyana suka haɗu suka kare lamrat, duka inna ta musu sosai sai da ta kutun suna iya kuka har kukan nasu ya daina fita sosai, sai da ta bugesu iya san ranta san nan ta kyalesu tana faɗin kutashi tun kafin na rufe ido na buɗe ku ɗauki kofi ku tafi ku ɗebo min ruwa,yanzun nan kugama kuzo ku jemin tallah tana kai karshen maganar ta nufi ɗakin ta, da kyar suka mike suka nufi Kichin suka ɗauki cups suka fice daga gidan, Amrat dake duƙe a wajen wanke wanke tana wanke kayan inna sai kuka take kamar ranta zai fita ba abun da take tunawa sai mahaifiyar su a zuchiyar ta take faɗin yanzu da umman mu bata rasu'ba da tana nan inna bazata musu haka ba wayyo Allah ka jikan umma da bappa haka dai Amrat wunin ranan ta wuni tana kuka su diyana kuwa suna jidan ruwa da kofi ga yinwa ga nisan rafi ga zafin rasuwar Bappa.


Misalin karfe 11 nadare zaune suke a dakin'su dukkan'su ba wan da yayi barchi saboda yinwar dasuke ji ta hanasu barchi diyana che ta dubi hiyana tafara Magana "hiyana yaufa tun safe jinin nan yasake dawowa na chanza zani har nagaji duk kayana sun kare jinin kuma bai daina fitowaba
A ɗan tsorache Hiyana tache "bari na lallaɓa  naje na tambayo innar yaya bello sai muji kodai akoi wani abun da zakisha sai ya daina zuwa a razane lamrat tace "Aunty diyana wani jini kuma, diyana zatayi magana hiyana ta rigata da chewa ina ruwan'ki  dake ake magana ne, shiru lamrat tayi taba sake magana ba
Amrat dai takasa magana jimamin mutuwar bappa har yanzu bai saketa ba, dan kuwa duk tafisu shakuwa da Bappa su basu yawan zama dashi sosai saboda aikin ɗeban ruwa da tallah, wani lokachima sai sufi kwana uku basu samu damar ganin saba saboda balai inna,shiya ita amrat tafisu shiga damu dan kuwa ita kullum tana gida idan tagama wa inna aikin gida sai tatafi ɗakin bappa, ta kwanta ajikinsa suyita hira.

Mikewa hiyana tai tana faɗin, bari dai na lallaba naje wajen innar yaya bello dan nasan itama batayi barchiba,tana kai karshen maganar ta fiche daga ɗakin, lallaɓawa take kamar wata ɓarau'niya ta fiche daga gd tana fita ta kwasa da gudu dan tsoro dare yayi ga duhu, sai data shiga gidan su yaya bello san nan ta ta tsaya tafara tafiya a hankali hankali dan kar wani yaji ya ganta ya faɗawa inna

Da sallah ta shiga ɗakin innar yaya bello sai wani sanɗa take innar bello na zaune a tsakiyar ɗaki ta tasa dakkere a gaba tana chi ganin Hiyana yasa tamike tana tambayar ta "lfy hiyana me yafito dake chikin daren nan "lfy inna daman nazo tambayar ki wani abune "to menen faɗi, hiyana tasanar da ita komai abun da yafaru da diyana har fyaden da buba yaso yayi mata san nan taɗora da chewa kuma inna jinin fa kwana binyu da suka wuche ya dai na zuba sai yau kuma ya dawo 
Shiru inna ta ɗanyi kafin tace "kai buba Allah dai yashirya mana shi batun jini kuma al'adane bari nabaki pant da tsunmma guda 2 kibata tasa summa daya yanzu dasafe sai tachire ta wanke ta shaya, sai ta dauki dayan tasa, ba'a ajiye summar jinin kinaji na da an chire za'a awanke, to wakai hiyana tace, inna tanufi kwallar kayan sawar'ta ta buɗe ta dauko pant da tsunmma guda biyu  ta mikawa Hiyana,  amsa tayi tana fadin "to inna tayaya zatasa, inna tasake amsar summar  tasa a chikin pant ɗin ta nuna mata yadda zatasa, san nan ta miƙa mata,  Hiyana ta ansa tana faɗin mungoɗe inna,tanufi hanyar fita har takai bakin kofa sai kuma ta juyo tache inna "menene al'ada kuma
Inna tache "idan mace ta girmane yake zuwa mata kuma alokachin da mace tafara al'ada to karta yarda wani namiji ya sake tabata idan kuma tabari ya taɓata tofa zata samu chiki
Zaro ido waje hiyana tai jin an ambachi su nan chiki murya har rawa yake tache inna to meyasa ni banyi al'adan ba kuma ai niche babba, dafe kai inna tayi tana faɗin "kai hiyana sarkin tambaya to ai kowa da irin halittarsa ne shiyasa wata zakiga shekara 13 take farawa wata kuma sai takai shekara 16 to kowa da irin tasa halittar "to inna kullun yake zuwane dan naga na diyana fa yanzu kusan sati 1 ke nan kuma diyana tache kwana biyu dasuka wuche ya daina zuwa yau ne kuma yasake dawowa, shiru inna ta ɗanyi kafin tace "ina gani diyana na da sanyi'ne shiyasa al adan ke mata rikichi, yanzu dai dare yayi kije gd inkin samu lokachi idan azzalumar innan kun nan bata nan sai kizo in baki maganin sanyi kibawa diyana, yanzu kinga dare yayi kuma ban haɗa maganin bama tukun nan Hiyana tache "to inna mungoɗe sai da safe ta nufi waje  tana fitowa kofar gdsu yaya bello, da gudu tayi gidan su chikin duhu dan dare yayi tana tsoro
In da ta barsu diyana a nan tadawo ta samesu zama tayi gefen Amrat tafara yiwa diyana bayanin da inna tamata
Diyana kam tunda akafara bayani take sauraro anazuwa wajen da akache intabari namiji yataɓata to zata samu chiki a tsorache tache
Hiyana yanzu ko yaya bello tab nashiga uku na wlh yanzu ke nan zan samu chiki tun da kunga ko jiyama na kama hannun yaya bello,wayyo Bappa na dan Allah meyasa katafi kabar mu yanzu ni ya zanyi da raina ni diyana da chiki 
Girgiza kai hiyana take tana faɗin "ki dai na kuka diyana kinji kibari dasafe sai muje mu tambayi inna muji kina da chikin ne ko babu, da kyar hiyana tasamu diyana tayi shiru, san nan to koyawa diyana yadda zata yi amfani da tsumma da pant ɗin kamar dai yadda innar yaya bello ta koya mata, mikewa diyana tayi hiyana ta taimaka mata tasa pant ɗin san nan tasa tsunmar, suka kwanta shiri babu wan da yasake magana da haka har barchi ya ɗauke su 
 


3 days later

Zaune take a tsakar gida ita kadai diyana ta tafi tallah amrat tatafi wanki kayan inna a rafi lamrat kuma tana debo ruwa ita kuwa inna ta bartane tamata girki
Shigowa gidan inna tayi babu koh sallama tache "ke hiyana ko ki shirya ko karki shirya gobe  za'a ɗaura auren ki da buba 
Hiyana dai bata che da inna ko mai ba amma a chikin zuchiyarta tana tunanin yadda zata gudun wa Auren, wunin ranar kuka hiyana ta wuni yi dan yau rasuwar bappa ya dawo mata sabo fill tasha kuka har blue eyes nata suka kumbura suka kankan che.

Da daddare bayan su diyana sun dawone suna zaune a dakinsu kamar yadda suka saba
Hiyana ta dubi su diyana tafara magana "lokachi yayi da zamu bar gidan nan
A tsorache diyana tace "to muje ina muda bamu san kowaba bamusan ko inaba "ko bamu san ko inaba yazama dole mu bar gidan nan, dan gaskiya bazan Auri buba ba wlh na tsanesa bansan ganinsa mugune, gaskiya bazan tsaya a ɗaura mana Aure ba hiyana ta karisa maganar kamar zatayi kuka "to yanzu idan mun bar gidan nan ina zamuje diyana ta tambaya fiskarta chike da damuwa "kidai na damuwa diyana, zanyi tunani a kai dole na nemo mama inda zamuje chewar hiyana da sauri lamrat tace "to ko zamu nemo addan (yaya) bappa ne ba yataɓa faɗa mana yana da adda ba (yaya) 
Hiyana tache "to ai na zamuganta kenifa baruwana da kowa, yauwa birni zamu tafi muje munemi aiki har musamu kudi
Taɓe baki diyana tayi tana faɗin to yanzu muda bamu san hanyar birni ba ta ina zamu tafi, karfa mu bar gidan nan muje mu haɗu da masu yan kan kai suyan ke mana kai, da sauri Amrat tace "wlh bappa yataɓa faɗamin akoi masu yan kan kai a birni, kara zaro ido lamrat tayi, tana faɗin "tab nikam ba zanje ba wlh gara na zauna a nan ta karisa maganar kamar zatayi kuka, kallon hiyana diyana tayi tace "to yanzu ya zamuyi Shiru hiyana ta ɗan yi kafin tace  ke dai karki damu zansan yazamuyi, yanzu kan mu kwanta muyi barchi, da safe in munje ɗeban sai mukarasa maganar a rafi, har suna haɗa baji wajen chewa to

Suna kokarin kwanchiya kenan sukaga inna ta faɗo musu ɗakin kafin su ankara tafara sauƙe musu bulalun hannun ta ajiki, bugun su taƙe tana faɗin "buba ne bakiso ko to wlh koki mutu ko kiyi rai sai kin auri buba daga yau ba mai sake fita a gidan nan a chikin ku rufe ku zanyi a dakin nan ke hiyana gobe za'a kai ki gidan buba kukuma sauran yin'wache zata kashe'ku a chikin dakin nan dan kulle'ku zanyi ba inda zaku sake zuwa
Kuka suke sosai sun manne da juna diyana da hiyana sun haɗu sun karewa lamrat da Amrat ajikin su kawai bulalan ke sauka, inna kuwa  bugun su take baji ba gani da iya karfinta,sai da ta farfasa musu jiki tukun nan ta kyalesu ta fiche daga ɗakin, kankame juna sukayi suna kuka a haka barchi ya ɗauke su 


Kano ta dabo

Ammi na zaune a gefen katafaren gadan Abba shi kuma Abba yana kwanche a nitse da sanyayyiyar murya tace "ranka yadaɗe inasan muyi magana, mikewa Abba yayi daga kwanchiyar da yake ya zauna yana fiskantar ta "ina jinki Aishstu na manene yayi maganar yana kallan chikin idon ta, kasa da kai Ammi tayi chikin ladabi da girmamawa ta fara magana " daman inasan zuwa Yola ne wlh kwana biyun nan,bana jin daɗi ina ganin kamar akoi damuwa ina yawan mafarkin Ahmadu kasan shi ya ragemin kuma gashi na yaddashi, abun yana yawan damuna sosai, inajin a jikina kamar Ahmadu na chikin damuwa,tunaninsa har tafara yimin yawa, dogon numfashi Abba yaja kafin yace "ba'damuwa Aisha ae kin jima baki jeba kusan shekara 7 ke nanfa gaskiya yakamata kije, ki shirya sai kuje da su Safras su rakaki
"da murna Ammi ta juyo ta rungumi Abba tana faɗin ilove U ilove U
 rungumeta sosai Abba ma yayi yana faɗin "eyeeee yau kam ba fullanchi ke nan,kara shigewa jikinsa Ammi tayi tana murmushi


( Nikoh nache oh ka jimin tsofaffin nan gaskiya Abba da Ammi kuna shaaninku tsufa bata hana soyayya)


Misalin karfe 4 na yamma gaba ɗaya ilahirin family alhaji Abubakar saraki ne zaune a fada 
Abba na zaune a kugerar sarauta gasu, Ammi a gefensa gefe guda kuwa sarkin fada'ne dasu waziri ga uncle Aliyu ma a gefe DON da Aryan suna zaune saman sofa mai ma zaunin mutun 2 duk kansu fiskokin'su babu alamar wasa a ɗaure taƙe tam kamar basu san menene dariya ba kallo ɗaya zaka musu ka gane suna chikin baƙin chiki, Khalid da Yusuf suna zaune suma a saman sofa ɗaya mai ma'zaunin mutun 3 ko ajikin su sai ma murmushi mugunta da suƙe wa DON da Aryan 

 gyaran murya Abba yayi yafara magana a nitse gaba ɗayansu suka tattara hankalin'su suka maida kan Abba suna sau raron'sa 
" Dalilin dayasa na tara'ku inason sanar daku lokachi yayi da zan sauka a kan kujerar murki in mikawa ɗana Safras asukwa'ne DON ya ɗago kamar zai yi kuka nan take fuskar sa ta sauya sosai jiyake kamar yayi ihu shi gaskiya baya san mulki ai sojan shi kawai yake so, chigaba da magana Abba yayi "gaba ɗayan'ku ina mai baki umarni ku'nemi transfer a wajen aikin'ku kudawo kusa dani kuchiga da aiki a kasar ku Aryan Ahmad Aiman Khalid Yusuf a sukwane suka ɗago suna kallon Abba, Abba ko ajikinsa sai ma chigaba yayi da magana,"yau azumi saura wata 2 bayan Sallah da sati 1 zan sauka daga kan kujerar mulki na a naɗa sabon sarki Safras, buɗe baki DON yayi zai yi magana sai idon sa ya sauka a kan face ɗin Aunty farida, girgiza masa kai tayi alamar yayi shiru kar yayi magana shiru yayi, yafasa maganar ya mai da kansa yana kallon kasa, "akoi mai magana a chikin kune chewar Abba yayi maganar yana kallon fuskokinsu  shiru sukayi gaba ɗayansu Almost 10mnt ba wanda yayi magana "ok tunda bakuda magana kutashi kuje sai bayan Sallah da one week 

Da sauri DON ya mike ya fice daman kamar a kan kaya yake da sauri Aryan ma ya miƙe yabi bayan DON da ɗai da ɗai suka watse kowa yayi nasa ɓangaren 

Aunty amarya na fita tayi part nata sai huchi take,  tana shiga ɗaki  ta ɗau wayarta tafara neman hajiya sadeeya, bugu ɗaya hajj sadeeya ta ɗaga tana faɗin hello aunty amarya tache "hajjiya sadiya kina ina "ina nan kano mana meyafa "akoi matsala hajj ya sadiya ae bama abun da bai faruba, kinaji wai Safras za'a bawa mulki ba Aryan'ba "what? gaskiya bazai yiwuba dolene musan abunyi wlh dole Aryan ne zai karbi mulkin nan karki damu gobe zanzo mu tattauna chewar hajj sadiya  "to shike nan sai najiki amma dan Allah kiyi sauri dan jinake kamar zuchiyata zata buga "kar ki damu hajj Hajara ae damuwar ki damuwa tache inshaa Allah zan shigo da wurima,"to kawai Aunty amarya tace san nan ta katse kiran ta haye gado tanata kunkuni

Zaune yake a Katafaren palon sa saman sofa mai mazaunin mutun 3 yana fuskan tar sofar da Aunty farida ke kai a zaune ga Aryan zaune a gefensa sun zubawa Aunty farida ido, Khalid da Aiman suna zaune saman sofa mai mazaunin mutun 2 sai Ahmad da Yusuf suma a kujera ɗaya suke zaune dukkansu sunyi shiru sun zubawa Aunty farida ido suna jiran suje me zatache ita maɗin dai shiru ta zuba musu ido DON ne ya katse musu shirun da chewa "Aunty farida yanzu me mafita wlh bazan iya rike mulkin nan ba, mulki baya chikin tsarin rayuwata aikin sojana kawai nakeso bayan shi bana bukatar wani abukuma,dogon numfashi Aunty farida taja kafin tache "kar'kadamu nan da bayan sallah fa Abba yache kaga da ɗan sauran lokachi zamu shawo kansa a hankali, shiya dazun na hanaka magana domin kuwa kokayi magana ba sauraran'ka zai yiba amma zansan yadda zamuyi kafin lokachin inshaa Allah ka kwantar da hankalin'ka duk yadda zanyi naga ba'a baka mulkiba sai nayi, da sauri Aryan yache "dan Allah Aunty farida kada'fa kibari idan Abba ya yarda akan bazaa bawa DON mulkiba Ni kuma a dawo kaina, dan Allah kar'kibar hakan tafaru,wlh nima banaso mulkin nan a bawa Aiman ko Yusuf " da sauri Aiman yache "tab wlh banaso sai dai Yusuf, wani harara Yusuf ya wurgawa Aiman kafin yace kaima dakake likita kache bakaso to inaga ni soja kuma me soja zaiyi da wani mulki sai dai abawa yaya Khalid ko Ahmad, da sauri Khalid ya buɗe baki zai yi magana, Aunty farida ta dakatar dashi da chewa "a'a Me abun rigima bayan ga uncle Aliyu yana nan da ransa ae shi yadache ya karbi mulkin "good my lovely aunty ina sanki wlh akoi ki da basira chewar Aiman harara wasa Aunty farida tamasa zatayi magana sukaji sallama
Dukkan su suka juya da gudu Aunty mardiya tazo ta rungumi Aunty farida tana faɗin "nayi missing naku sosai  Aunty farida tache "sai yanzu kuka iso "eh yanzu shigowar mu Ammi ke sanar dani kuna nan Mikewa DON yayi shi da Aryan da Yusuf suka nufi hanyar betroom ɗin DON, jiki a sanyaye Aunty mardiya tache "bro kufa nazo gani ina kuma zakuje, tun bamu gai'saba tayi maganar kamar zatayi kuka,kuma dakaji muryan kasan a tsorache tayi maganar
Dukkan su ba wanda ya juyo bare ya tanka mata sukayi shige warsu chikin betroom ɗin, har ita kanta Aunty farida bataji daɗin abun da suka yima mardiya ba, a hankali ta dawo da kallanta kan Aunty Mardiya daniyar tabata hakuri, sai taga hawaye wani na bin wani a kan kumatun Aunty mardiya "kiyi hakuri Mardiya bai kamata kiyi kukaba duk da nasan basu kyau ta miki'ba amma kimu'su uzuri watarana sai lbr Chikin kuka mardiya tache "wai Aunty farida me namu'su ne dan Allah meyasa ni basa sona eh why? "suna sanki mana sudai haka halinsu yakene kawai amma suna sanki,wani dogon tsaki Aiman yaja kafin ya miƙe yanufi hanyar fita daga palon, chikin jin haushi Aunty farida tace "kai ina zaka kuma, a ta kaiche Aiman yace "ɗaki zanje batare daya jiya amsar Aunty farida ba yafiche da sauri, Aunty farida zatayi magana Ahmad ma yamiƙe da sauri yayi waje baki Aunty farida ta taɓe, girgiza kai kawai Khalid yayi ya mike ya dawo kusa da Aunty mardiya ya zauna yana bata hakuri, da kyar Khalid da Aunty farida suka shawo kanta tayi shiru, Aunty farida ta miƙe ta riko hannunta tana faɗin "muje ɗakin Ammi, koh, to kawai Aunty Mardiya tace san nan ta miƙe suka fice daga palon shikuma Khalid ya miƙe yabi bayan su DON ya shige chikin betroom ɗin shima, 


 Yola

 Jama'a sun chika gidansu hiyana sai faman shirye shirye ake ga maza a kofar gida suna zazzaune a kan tabarma,liman ya miƙe yana faɗin "kowa ya nitsu yanzu za'a ɗaura Auren ina wali amarya daya daga chikin dattijan dake zaune awajen yace gani nan liman yace to ina waliyin ango Baban buba yace gani na to kumatso kusa zama malam liman yayi kana yache "malam audu kayarda kabawa dan wajen malam sani auren yarka hiyana malam audu yache...✍️


more comments an share *💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*



Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawa




*Episode 6*
            


Malam Audu yace na..bai karisa ba sakamakon wasu If gudu Shahram da Abdol suka fito suka fara buɗe kofar motochin sai da suka bi kowani mota suka buɗe kofar san nan,suka dawo jikin motar su DON suka tsaya, a nitse Ammi ta sako kafarta waje kafin ta fito gaba ɗaya,sanye take chikin wata ɗankareriyar yace pink colour ɗinkin bubu wuyar ta da hannun ta sanye yake da  ta sanya musu wani ɗankareren gold mai matikar kyau da tsada wani bakin al'khabba, mai shegen kyau an masa kwalliya da duwasu fari masu kyalli ta sa a kanta a mai makon mayafi bakaramin kyau tayiba inka ganta kache bata wuche 25 years ba a hankali kamar bata son taka kasa tanufi hanyar gidan su hiyana tazo dai dai zata shiga gidan sai kuma ta tsaya ta juyo tana kallon su malam liman, chikin ladabi ta gaida malam liman san nan tace "malam taron me akene haka, murya na rawa malam liman yace aure zamu ɗaura, to Allah yaba da zaman lfy ta kai karshen maganar tana shigewa chikin gidan tana tunani a ranta yanzu Ahmad zai kara Aure ne ko yasanar dani, zan haɗu dashine wlh, da sallama a bakinta tashigo chikin gidan nanfa kallo yadawo kanta gaba ɗaya matan dake chikin gidan suka zuba mata ido "sannun ku dan Allah ina habiba Ammi ta tambaya tana kallon fuskokin'su 
 inna na daga gefe a ɗan tsorace tamike tana fadin "gani nan lfy wacece ke,gyra tsayuwa Ammi tayi tace "Aisha che yar Ahmadu, baki inna tabuɗe "laaaa indo keche a lallai kinzo a sa'a yau ake bikin ɗiyar taki hiyana,daure fuska Ammi tayi tafara magana "hiyana kuma Ahmadu hauka yakene da zai aurad da hiyana yanzu kwata kwata nawa au shine naga jama'a a kofar gida, to bazai yuba wlh baza'a aurad da yarinyar nan nan zuba ina Ahmadu yake yazo ya mai da musu da sadakinsu dan wlh baza'a ae wan nan Aure ba Hons ni tafiya ma nazoyi dasu gaba ɗaya yaran, chikin tsawa inna tace "ke Indo kishiga hankalinki wlh banga uban daya isa ya hana a ɗaura Aure'n nan ba, Ammi chikin ta kai chi maganganun da Inna tamata ta kalli Inna daga sama har kasa kafin tafara magana "ke habiba ko Ahmadu bazai tsaya yana faɗamin magana ba amma yanzu zan nuna miki na isa bama a kan ƴa'ƴan Ahmadu kawai na isaba har, a kan shi Ahmadu da kansa ke, bintu fita waje kiche da Safras wan nan umarni'ne su watsa jama'a nan su dakatar da ɗaurin Auren nan,ta karisa maganar chikin fushi tana kallon kuyangun daƙe gefenta, da gudu bintu ta juya tanufi waje dan ta isar da sakon Ammi, wani tsalle Inna tayi ta damko wuyar rigar Ammi tana faɗin "lallai Indo kin manta wacece ni ke nan wlh kibar ganin kinyi Aure a birni yanzun nan sai namiki mugun duka, chikin fushi Ammi tace "habiba ki sakarmin wuyar riga habiba "Indo bazan sakiba wlh yau sai namiki mugun duka a gidan nan dan kin shiga abun da bariwan'ki, da gudu kuyangar dake gefen Ammi tafita waje dan ganin abun da Inna ke kokarin yi, hannu Ammi tasa tana kokarin chire hannun Inna daga wuyar rigar ta, 

Kamar daga sama aka ɗauke Inna dawani gigitatcen mari wadda yasata faɗuwa kasa bashiri, da sauri Ammi ta ɗago tana kallonsa tsaye yake idon san nan ta sauya tayi jaa jijiyoyin kansa duk sun miƙe gaba ɗaya fuskar sa ta sauya sai wani huchi yake,kamar wani maƴinwachin zaki gadan gadan ya tin kari Inna dake baje a kasa tana ihu, da gudu matan dake gidan kowace ta kama kanta mace ɗaya che ya rage zaune bata gudu ba gudu ba, wani bugu ya kaiwa Inna a wuya nan taƙe numfashinta ya ɗauke hannu yasake ɗagawa a zuchiye zai kara kai mata wani bugun, da sauri Ammi tache "a'a Fahad ya isa tayi maganar tana karisa wajen da Fahad ke tsaye ganin Fahad na kokarin karawa inna bugune yasa Ammi tayi saurin shiga tsakanin su tana faɗin ya isa haka Fahad ka kyaleta, "Ammi pls ki kyaleni na bugu matar nan kina gani fa wuyar rigan ki ta riƙe wai ma wacece ita ? yayi maganar chikin matsanan chiyar ɓachin rai "aa Fahad ka kyaleta haka nan baka ganin ta sumane matar kawun ku che  "Ammi idan matar kawun mu che sae ta riƙe miki wuyar riga "ya isa Fahad jike ka kiramin su Safras kaji a zuchiye ya juya yafita sai huchiyake,
Juyowa Ammi tai tana kokarin taɓa  inna  karaf idon ta ya sauka kan su diyana dake tsai tsaye a bakin kofar dakinsu sunyi chirkoh chirkoh da sauri Ammi tafasa taɓa Inna tanufi wajensu tana faɗin "ina Ahmadu hiyana jin an amba chi ina Bappa yasa ta fashe da kuka, turus Ammi ta tsaya murya na rawa tache "hiyana me kikewa kuka  Ahmadu nache  kuka hiyana tache "Bappa yarasu satin daya wuche
Nan take Ammi tayanke jiki zata fadi da gudu hiyana tai kanta tana kokarin tareta dai dai lokachin su DON suka shigo da sauri DON ya karaso yasa hannu shima yana kokarin rikoh Ammi har karo sukai da hiyana bai ma bi ta kantaba ya rungumo Ammi ajikinsa yana kiran su nan ta da sauri su Fahad dukayi kansa suna kiran Ammi, Ammi
 ganin haka yasa hiyana tai baya 

Chikin tsawa Fahad ya ɗago ya kallo su hiyana yafara  "meyasa Ammi waya mata wani abun, yanzu nafita na barta lfy lau, 
murya na rawa Hiyana tache "ta tambayeni Bappa ne shine nafaɗa mata ya rasu shine zata faɗi..bata karasaba maganar ba, ya daka mata tsawa ya isheni haka shiru hiyana tayi jikinta sai kerma yake
DON  kuwa kwantar da Ammi yayi a kan tabarman dake wajen yaɗago ya dubi su Fahad dake tsaye a kansa "kai kubani ruwa kafin DON yakai karshen maganar ma, Fahad ya nufi waje chikin mota yashiga ya dauko ruwan faro da sauri yadawo chikin gidan ya mikawa DON  Aryan dake duƙe kusa da DON ya karbi ruwan ya bude ya tarfa a hannunsa ya shafawa Ammi a fuska, wani dogon numfashi taja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuchiya sai kuma tamike zubur kamar wadda akawa allura tana faɗin "ina bahaka bane kunne nane bai jimin dai dai ba DON  ya matso yarike ta a nitse yache "Ammi meke faruwane lfy "ba lfy ba dan naji kamar hiyana na faɗamin wai Ahmadu na yarasu "kiyi hakuri Ammi kinji ya karisa maganar tare da sakin ta,  juyowa Ammi tayi tana kallansu hiyana ta musu alama da hannu akan suzo, ba musu suka miƙe sukanufi inda take gaba ɗayan su suka zauna kusa da ita
Ganin Ammi ta dawo chikin hayya chinta sosai yasa Mikewa DON miƙe yanufi waje, Fahad da Aryan suka rufa masa baya 

Riko hannun hiyana Ammi tayi tafara Magana "yaushe Ahmadu ya rasu, chikin shesshekar kuka hiyana tache "juma'ar data wuce juma'ar data wuche Ammi ta mai mai ta da mamaki to amma "shine kuma ko sadakar 7 ba'ayiba za'ayi taran biki saboda me ? Hiyana zatayi magana Diyana tai saurin chewa "duk shirin inna che hakan ban gane duk shirin Inna ba che Ammi ta tambaya tana kallan fiskar diyana, sai yamzu matar dake zaune awajen tun dazun wadda kowa ya watse yabarta tafara magana, tashiga bawa Ammi lbr duk abun da yake faru,duk irin a'zabbatar da Inna ke wa su hiyana, Ammi sai hawaye take wani na bin wani chikin muryan kuka tafara magana "duk laifin Ahmadu ne ba yarda banyi da shiba akan yadawo kano kusa dani yaki wai bazai bar garin iyaye da kakanniba, bayadda na iya dole na kyalesa na sai waya mai kyai na bashi dan murinka gai sawa da juna amma yaki ansa wai baya so yanzu har Ahmadu ya kamu, da chiwo akafa ya daina takawa duk ban saniba, innalillahi wainna ilaihir rajiun gaskiya rashin zumunchi bai yiba wlh nima ina da laifi duk dachewa ba zaman kaina nakeba a kar'kashin wani nake, amma yakamata ko wani ne inrinka ai kowa yana dubamin shi yanzu me amfani haka shekara 7 rabona da dan uwana wanda shi kadai yaragemin aduniya yanzuma babu shi wayyo ni Aisha gaskiya auren nesa Auren gidan sarauta bai yiba mutun ba zaifita yaje yasada zumunchiba hakadai, Allah sarki bayin Allah marayun Alla tayi magana tana shafa kan amrat da kyar ta miƙe ta dubi hiyana tache "ina zuwa ku jirani tana kaiwa nan tanufi waje

Kai tsaye wajen motarsu tanufa jakarta ta ɗauka ta chiro wayar ta ta danna kira takara wayan a kunne kana takoma daga gefe chan ta tsaya tana magana Almost 30mnt tana waya bayan ta gamane tazo tasamu su Doyn achikin motarsu tace "kai kujuya  motochin zamu  koma ta kai karshe maganar tana juyawa, batare da tajira amsar su ba ta nufi chikin gidan su hiyana 
In data barsu awajen tasamesu "kutashi mutafi abun datache dasu ke nan ba musu kuma basu tambayeta ina zasujeba dan ita hiyana tasan Ammi yar Bappan,sune su diyana ne basu san taba mikewa sukayi jiki ba kwari, Ammi takama hannu amrat sukayi gaba su hiyana sukabi bayanta sukabar inna abaje a kasa 
Suna fita suka samu an juya kan motochin kai tsaye motar ta tanufa, buɗe motar tayi san nan  tache da su hiyana "kushiga bamusu suka shiga ita kuma ta juya tanufi motarsu DON
DON naganin Ammi tsaye jikin marfin motan da kansa ya buɗe mata motar tashiga ta zauna kusa dashi
Har anwa  motochin key zasu tafi Ammi tache su tsaya bayan sun tsayane  tache wa sojan da zai tukasu yashiga gidan su hiyana yakira mata maman bello, da sauri sojan yafita yanufi chikin gidan bajimawa yafito maman bello na biye dashi a baya har suka isa wajen motar
Ammi ta kalli DON dake zaune yanata latsa wayarsa hankalinsa ma ba akansu yakeba "kai idan akoi kuɗi ajikinka bani shiru ya ɗanyi kamar mai tunani sai kuma yasa hannnu ya buɗe wani dan karamin waje dake manne da jikin kujerar baya na motar ya zaro rapa rapan 1k Kowani rapa kuwa zai kai 100k  rapa uku yamikawa Ammi, ansa tayi ta sauke glass ɗin motar ta mikawa innar bello ta ɗora da chewa "kibawa bello rapa 2 ke kuma ki ɗauki 1, innar belli ta washe baki sai zuba godiya take, Ammi batache da ita komai ba sai ma ɗaga glass ɗin motar datayi ta bada umarnin sutafi da sauri suka tada motochin suka bar kauye kai tsaye Airport suka nufa.


Innar bello kuwa ta juya ta koma chikin gidan su hiyana ta ɗebo ruwa ta zubawa inna a fuska, a'razane inna tafarka tana faɗin zanga uban da zai hana auren nan idan an isa ache menake, innar bello tache "to ni dai natafi sai anjima tajuya tayi fichewarta, inna kuwa tafara waige waige taga bakowa a gidan duk sun watse mikewa tai ko mayafi babu tayi waje kai tsaye gidansu buba tanufa

Zaune suke dukkansu a tsakar gida har da bello inna tashigo ko sallama babu nan tasamesu ga buba sai faman ihu yake yana fadin aradun Allah bazan barsuba nine zanzama ajalin hiyana indai baayi auren nanba to aradu saina mata asiri ta mutu saina mata sanda
Inna tache meyasamishi
Inna larai maman buba tache mutanen dasuka zo din nanne dasukache  kowa yawatse bazaa daura aurenba shine shi buban yache basu isaba sai wani daga chikinsu ya daga buban yabugashi da kasa kana ya kama kafarsa ya karya
" karaya tayi maganar tana zaro ido
Inna larai tache "karaya kuwa shine yanzu malam yatafi kiran mai dauri

Mikewa inna tayi tana faɗin "zomuyi magana tana tana kai karshen maganar tashige ɗakin innar buba, inna larai tatashi tabi bayanta tana shiga inna habiba tache "kinji meyake faruwa koh kuma kinsan idan yaran nan basu mutuba a dokar kauyen nan ban isa intaba koda kafar kazane a chikin dukiyarsu bakoh
Inna larai tache kwarai kuwa yanzu me abunyi
Inna tache wajen malamin chan na bayan dutse zamu sake komawa mana yasan yadda zaiyi ya kashemanasu a chan ko dai a haukata manasu komaidai me ma amusu dan wlh bazan barsuba
Inna larai tache to kina da kudine " Inna tache zannemo ai zuwa nan da sati mai zuwa sai muje
Inna larai tache yauwa kiyi kokari dan allah
To kawai inna tache mata kana tafito daga dakin tayi waje 


Kano ta dabo

Aunty amarya zaune take a gefen gadanta ita da hajj sadeeya
"sadiya yanzu tafiya Enugu ya kamaki dan bazan taba barin wani yayi mulkiba idan ba danaba 
Sadiya tache gaskiyakam amma bayanzu zanjeba sai wata mai kamawa dan kuwa wlh inada tafiya dayawa a gabana
Aunty amarya tache wata daya baiyi nisaba kinfasan bayan sallah za'a dorasa a mulki nikuma danaga wan nan rana gwanda namutu
Sadiya tache karki damu ai da dan sauran lokachifa abunda idan najema sha yanzu magani yanzu zaamin dankuwa a wajen zansa gagara ba dau ya kashe Safras din kowama yahuta
Aunty amarya ya tache amma sadiya bansan bakida kwakwalwaba sai yanzu kifadamin idan muka kashesa muna da gadansane kina ganinfa yafi kowa kudi a gidan nan ai bakashesa zamuyiba sawa zamuyi gagara badau ya chusa mashi sun yar wajenki kinga dayafara san zulaihat shike nan insunyi aure sai sun haihu sai mukashesa inmun kashesa kinga a lokachin muke da gado
Washe baki sadiya tafarayi tana fadin ashe kinasona har haka bansaniba wayyo allah tayi maganar tana kokarin rungumar aunty amarya
Aunty amarya tache inasanki mana sosaima ai fin hakama yanzu dai kiyimana kokari akan afasa bashi sauratan nan daga nan kuma sai muzo muyi aikin zulaihat da murna hajiya sadiya tamike tana fadin to shike nan ai dolenema ayi aikin nan da gaggawa yanzu dai kawo kudi zanwuche
Wani akwati aunty amarya ta bude ta zaro rapa rapan yan dari biyar biyar 300k tamukawa hajiya sadiya tache inbasu isaba saiki min magana sai nakaro
Karba sadiya tai tanafadin saikinjini kana tafiche daga dakin tai waje
Aunty amarya kuwa kwanchiya tai tana fadin ai dukkanku sai nayi maganinku wlh shima yusuf din ba kyalesa zanyiba aiyana da kudi sosai shima dan haka yarinyar hajiya binta zansa gagara badau ya hadasu dan mukwashe kudin dukka haka dai aunty amarya tai ta surutanta har barchi ya daukesu

Aban garen su Ammi kuwa suna barin kauye airport suka nufa nan suka hau jirginsu sai kano
Suna isa kowa yanufi part Ammi ma ta kama hannun amrat tache su hiyana su biyota part nata suka nufa suna shiga Ammi ta kira zahra a waya tache tazo tasameta a dakinta san nan tachewa su hiyana su zauna
Zama sukayi a kasa Ammi tache aa kutashi ku zauna a kujera bamusu suka tashi suka koma kan kujerar Ammi tache amrat tazo ta zauna kusa da ita ba musu amrat taje ta zauna kusa da ita su diyana kam sai kalle kalle ake
Da sallama zahra tashigo da gudu tatafi tafada jikin Ammi tana fadin harkundawo
Ammi tache tashi ajiki nikam mutun ne sai shegen san jiki " turo baki zahra tayi tache  kai Ammi to niba yar auta bache Ammi tache duk bawan nan yasa nakirakiba
Kibani hankalinki da kyau kinutsu ki saurareni wayan nan dakike gani yayan kawunkine damukaje wajensa a yola sai yanzu zahra ta dago ido tana kallonsu dan shigowarta bata lura da mutane awajenba 
Tache laaa Ammi kingasu kyawawa dasu wlh wanchan tana kama da yaya prince sosai
 "kinga zahra bansan shirme ki saurari abun da zanfada miki yanzu a gidan nan zasu zauna
Zahra tabuga tsalle tache wayyo allah dadi Ammi dan allah kusasu a school namu danna na nunawa freinds dina su tunda suna da kyau sosai Ammi dai baki sake take kallan zahra mikewa zahra tai takoma kusa da Hiyana tamika mata hannu wai suyi musabaha
Bamusu hiyana ta mikamata nata hannu zahra ta kama hannunnata sukayi husabaha tache sunana zahra kefa " hiyana chikin gurbatatchen hausarta tache nikuma sunana Hiyana " zahra ta mai mai ta sunar Hiyana tache nice name kekumafa tayi maganar tana mikawa diyana hannu
Itama diyanar hannu tabata suka gaisa tache nikuma sunana diyana zahra tache hiyana an diyana wow su nan yayi to dayanfa tayi maganar tana nuna lamrat " diyana tache sunata lamrat zahra tajuyo da kallanta kan amra dake kusa da ammi da sauri tamike takoma kusa da Ammi tana fadin kai kaga yar india a naija gata karama da ita ga kyau kamar me to amma itakuma wlh da yaya haidar take kama amma tafishi kyau gaskiya
Ammi dai yau taga ikon allah wajen zahra mutunne sai kaudin tsiya tache zahra'u zakizo kizauna kiji abun da zanfada mikine kodai sai na batamiki rai
Sai lokachinma zahra tatuna ashe magana ammi kemata komawa tai wajen zamanta ta zauna
Ammi tachigaba da chewa yanzu dake da hiyana da diyana dakinku ɗaya ammi zata sake magana taji Zahra na fadin eyeeeee wayyo dadi Ammi ta daka mata tsawa zaki tsaya ki saurarenine ko saina saba miki shiru zahra tayi tanitsu
Ammi tachigaba dachewa lamrat da amrat dakinsu daban dakin dake kusa da nakin nan shine nasu yanzu abun danakeso dake kitashi kuje dakin ki suyi wanka kibasu kayanki susa san nan suyiwa su amrat ma wanka zansa a kawomusu kaya tunda su naki yamusu yawa kuyi sauri dan inasan muje wajen mai martaba mikewa zahra tayi da sauri tache kuzo muje wani dan korrido suka shiga san nan suka dan tafi kadan sai suka shiga dakin zahra
Nanfa zahra ta nunamusu toilet hiyana ne tafara shiga saikuma tafito tache aunty zahra bansan yazanyi amfani da abubuwan chikin toilet din ba " zahra tache dukkansu su biyota san nan tamike tanufi chikin toilet din nanfa tafara nunamusu yadda zasuyi amfani da abubawan dayake suna da kwakwalwa sosai nan take suka gane zahra ta nunawa hiyana towel dake makale awajen tache tayi amfani dasu san nan taja hannun amrat sukayi waje
Diyana da lamrat ma sukabi bayansu " hiyana kuma tafara kokarin chirekaya danyin wankar
Suna fitowa Zahra tafara kokarin fiddo musu kayan hadaddun dogayen riguna abayas tafitar musu masu kyau  ta ajiye a kan gado san nan taje ta daukoh musu plat shoe masu kyau
Hiyana nafitowa wanka diyana tashiga nanfa zahra tache saitawa hiyana make up hiyana bata hanataba
Zahra tafara yimata make up mai kyan gaske bayan ta gamane tachewa hiyana ta dubi kanta a mirrow
 zubur hiyana tamike lokachin data ga kanta taba fuskarta tashiga yi tana fadin anya aunty zahra niche kuwa kodai chanzamin fuska kikayi 
Zahra tache aa hiyana kedai zauna bari nabaki kaya aike din kyakkyawa gaskene kyankine kawai aini simple make up ma namiki dan na lurama make up din rage maki kyau zaiyi shiyasa banmiki dayawaba  
Doguwar riga sky blue zahra ta dauko daga kan gadan tamikawa hiyana hiyana ta karba zatasa " zahra tache to aibakisa bra ba
Hiyana tache me kuma bre " zahra tache breziya mana
Hiyana tache bansanshiba zahra tache to kina nufin baki taba sawaba kai to aiyakamata kirinka sawa bari na daukoh miki nawa
Lokachin da zahra ta daukoh bra ta mikawa hiyana damamaki hiyana ke kallan bra din tache to aunty zahra aina akesa wan nan kuma  taya zansashi
Zahra batasan sanda dariya ya kubche mataba saida tayi dariya sosai san nan tashiga yiwa hiyana bayani akan bra
Hiyana nagane menene bra nantake taji kunya yakamata tayi kasa da kai zahra tache aa karmufara haka dake nidakefa kinganmu kamar yan biyu shekarunmu ma ƙila dayane dan haka karkisake chewa zakiji kunyata juya na daura miki bra
Hiyana tache nifa shekaruna 15  zuhara tache kai shekara 15 kuma shine breast naki sukayi girma haka kinfini komaifa nikuma shekarata 16 amma kingani kam bawani auki tako ina
Hiyana dai shiru tai bata sake magana ba har zahra tagama taimaka mata tasa kayan Zahra tache yabaki wanke kanki ba ingani
Chirewa hiyana dankwalin kanta zahra tai a rude tache kai inna lillahi kinga gashinki har baya wayyo dama niche amma yanaga kannakima ba datti
Hiyana tache jiya anwankemin kai din ai zahra tache mamanku hiyana tache aa makwanchiyar mu che innan bello ta wankemin mukam bamuda mama da baba duk sun rasu
Zaro ido waje zahra tayi tache allah sarki sannu kinji allah yajikansu da rahma
Hiyana ta amsa da ameen
Ribons da mayuka masu kanshi na gashi zahra ta daukoh tazo tafara gyarawa hiyana gashin kannata  da kyar ta tara gashin nata ta daure mata a tsakiyar kanta zuba mata gelar gashin tabaya wadda yakai har kan boos din ta san nan zahra ta daukoh mayafin rigar ta mikamata kana tasamata manya manyan dankunne masu raun sai kyalli suke
Diyanama tana fitowa zahra ta dau yimata kwalliya saidata gyarasu tsab san nan tache ita zatayiwa amra wanka dan daga yau amrat yar tache
Kama hannun amrat zahra tai sukashiga toilet tamata wanka san nan tache lamra tazo tayi wanka da kanta
Sungama shiri tsab Ammi ta kawowa su lamtar blaus mai shegen kyau black colour
Zahra ta karba tasamusu bakaramin kyau sukayiba
A palo suka samu Ammi " Ammi ita da kanta ta tsorata daganin kyan da sukayi dan sunhadu tache to kuzo muje palan mai martaba dan mukadai ake jira sukache to zahra ta kama hannun amrat Ammi kuma tarike lamrat sukayi gaba su Hiyana na binsu abaya
Da sallama suka shiga palan gaba daya mutanen gidan suna palan har da mai martaba ma yana zaune shiru wajen babu mai magana kowa da abun dayake sunajin sallama suka dago kai amma banda Don Aryan Fahad Yusuf Aiman duk sauran su dago suna kallan Ammi 
Wuchewa Ammi tai ta zauna kusa da mai martaba zahra kuwa taja hannunsu sukaje suka zauna kusa da aunty farida "  kasa kasa aunty farida tachewa diyana tazo kusa da ita ta zauna mikewa diyana tai ta koma kusa da aunty faridan ta zauna
Mai martaba yayi gyaran murya saida kowa yadago kai amma banda wayan nan jarumai guda 5 din sudai har yanzu suna duke da kai suna daddan na wayoyinsu
Mai martaba ya nuna amrat da hannu yache tashi kizo mikewa tai tanufi wajensa gyra zama yayi san nan ya dorata a gefensa ta zauna yana shafa kanta yache yasu nanki
Shiru amrat tayi bata amsaba mai martaba yasake mai mai ta mata tambayar
Sai sukaji diyana tanachewa chikin gurba tatchen hausarta tache itakam batajin hausa mune kawai mukeji
Dukka palan saida sukayi dariya banda Don, Aryan,Aiman,Fahad,Yusuf  "  
Khalid ne yache to kema kina ganin kinajin hausake nan
Ummi tache yata rabu dasu hai ai kinyi kokarima dakika iya wan nan hausar abunda ba yarenkaba kuma katasowa kayi a inda ake magana da yarenba kuma a haka har kika iya fadin hakan ma ai masha allah
Zahrane ta matso kusa da diyana tafara mata magana da fullanchi dayake zahra najin fullachin sosai Ammi ta koya mata
Magana take mata a kan idan mai martaba yana nagana baa magana har saiyagama wani mugun kallo umar ke wurgawa Zahra hakan yasa tayi shiru ta daina magana

Mai martaba ya dubi diyana chikin harchen fullanchi wanda bai taba magana dashiba yache to yasu nanta ai basu aunty amarya kawaiba harda jarumai 5 saida suka dago suna kallon mai martaba hankalinsa kwanche yake fullanchinsa
Ammi kam ko ajikinta dan tasan ita  ta koyamasa fullanchi  
Chikin harche fullachin diyana tache su nanta amrat 
Mai martaba yafa ra bayani nan yafadawa yan gidan matsayinsu Hiyana yakara dachewa daga yau sunzama yayansa kuma a nan zasu zauna bayan yagama maganarne yache koh akoi mai magana
Aunty farida tadanyi gyaran murya alamar tanada magana " mai martaba yache to ina jinki
Aunty farida tache dan allah Abba inasan abani wan nan natafi da ita ta zauna awajena tayi maganar tana nuna Diyana
Mai martaba yache aa bazaki rabasuba ki kyakemin yayana anan babu inda zasuje

Nantake aunty mardiyama ta hadiye maganarta jin amsar da mai martaba yabawa Aunty farida daman itama tanasan taroka abata lamrat amma jin Aunty farida da kanta an hanata yasa tai shiru

Aunty amarya kuwa tunani tashigayi ta yadda zata bullowa al amarin dan wlh bazata taba yarda su Diyana su zauna a gidan nanba dan kuwa yaddasuke kyawawan nan karsu Safras sufara sansu domin Safras zulaihat kawai zai aura 

Mai martaba yache to kutashi kutafi Khalid kai kuma ranar monday kaje kamusu registration a makarantar su Zahra
Khalid yache to da ɗai ɗai mazan suka fara fita daga palan 

Ummi ne tachewa Ammi yamukaji da hakuri
Ammi tache hakuri yazama dole " Ummi tache allah yajikansa Ameen Ammi tache san nan su Aunty farida ma kowa yafarayiwa Ammi taziya 

Amrat na zaune kusa da mai martaba suna ta hira dashi da harchen fullanchi
 Aunty amarya kuwa afusache tamike tafita daga palan kai tsaye part nata tanufa
Tana shiga ta kira hajiya sadiya tache ke aiki yakarufa domin kuwa mai martaba yana neman rusa mana shiri
Hajiya sadiya tache mekuma yafa " Aunty amarya tache Aisha che taje kauyensu ta daukoh wasu yara wai yayan kaninta daya rasu to wlh idan kikaga yaran nan kamar susukayi kansu dan kyau gasu da diri da komai kuma biyu daga chikinsu yan matane,yanzu fargabana ɗaya a nan shine kar matasan gidan nan sufara sansufa
hajjiya Sadiya tache wayache maki zasu fara sonsu 
Aunty amarya tache ke wlh koke kikaga yaran nan sai kinsosu saboda kyau ni tsoran danake jima karfa Safras da Aryan su fara son su idan hakan yafaru wlh angama dani
Hajiya sadiya tache angama dakene kokuma angama dani nida har na fadawa zulaihat Safras zata aura yarinya sai murnatake ai yazama dole mutashi tsaye
Aunty amarya tache to yanzu me abunyi
Hajiya sadiya .  tache aiki gagarabadau zai mana ya koresu daga gidan kokuma ya haukata mana su kowa yahuta
Aunty amarya tache wlh hakan kawai za'ayi zankaramiki 500k achikin account naki yanzu ayi aiki mai karfifa wanda idan suntafi suntafi ke nan sufita daga rayuwar kowa sukoma rayuwa a bula
Hajiya sadiya tayi dariya tache karki damu aikinsan aikin gagarabadau badaga nan ba kedai kawai kizuba ido watan nan nakarewa muka shiga wata zanje enugu 
Aunty amarya tache ai shiyasa nake sanki kawata sai munyi waya kekam anjima da daddare zan kiraki bata jira amsar Hajj sadiya ba ta katse kiran ta ajiye wayar a kan gado tanufi toilet

Pls more comments an like     
*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

 💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*
  
Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai




*Episode7*
        


 Zaune suke a palan Ammi  suna hira nan fa zahra take fada musu komai na gidan
Zahra tache karku yarda kuyi wani laifi yanzu dankuwa shekaran jiya su yaya prince suka dawo baruwanku da kowa a gidan nan dan wlh duk yan gidan nan mugaye  ne yaya Khalid ne kawai mutumin kirki dan haka karku kula kowa duk abunda kukeso ku tambayeni yauwa kuma inkun gaishesuma basu amsaba karkudamu kuma karkuyi wata maganar dan basa amsa gaisuwar kowa sukam haka suke
Diyana tache to tunda basa amsa kaisu basai mu kyalesuba dole sai mun gaishe sune
Zahra tache keeee. lallai da zafinki kikazo tab ai wlh idan sukazo suka wuche baki gaishesuba nan ma hukunchi zaki karɓa inkuma kingaishesu bazasu amsaba to zamanki lafi shine ki gaidasu koda basu amsaba karkidamu " yauwa kunga wandayake zaune a kujeran gefen Ammin ɗazun din nan koh wan nan mai kama da Hiyana
Da sauri Hiyana tache daman akoi mai kama dani a gidan nan ne " Zahra tache eh mana ai shine ya zauna kusa da Ammi sunansa yaya prince to dashi da yaya Aryan da yaya yusuf da yaya Fahad  wlh karku yarda hanya ta hadaku inba hakaba zaku jijiki basu da kirki  Zahra zata sake magana taji takun tafiya a tari ta mike tawatsa dakinsu da gudu dankuwa tasan irin wan nan takun mutun ukune kawai a gidan nan keyinsa " Don, Aryan , Yusuf shiyasa ta gudu dan batasan haduwa dasu
Suna ganin Zahra ta gudu suma suka mike da gudu sukabi bayanta
Yana shigowa ya tsaya shiru yana tunanin tabbas yaga wulkawar abu kuma kamar inuwar mutun wuchewa chikin palan yayi yasamu waje kan kujera mai zaman mutun daya ya zauna 
Yachiro wayarsa yafara daddan nawa kana yasa akunne jimkadan sai yache gani nanfa a palo banji me akacheba a dayan bangaren ba kawai naga ya katse kiran
Fitowa Ammi tayi daga chikin betroom tazo ta zauna a kujera mai zaman mutun ɗaya a nitse Safra yache inawuni Ammi ta amsa masa da lfy yache yamukaji da hakuri tache hakuri yazama dole yache allah yajikansa da rahma amin Ammi  amsa kana tache daman kuɗi nakeso kabani su farida zasuje suyiwa kannenka sayayya " shiru yayi bai chekomaiba  kusan 10 mnt tukun nan yache
Ammi dan allah wai meyasa bazaki sabaki a magaAnar nanba nifa bazan iya mulkiba kinsanfa shugaba da adalchi da tausayi 
akasan shi to nikuma sojanefa
Ammi baki sake take kallansa tache au kai bakada tausayi ke nan shiru yayi bai tankaba saima mikewa dayayi yanufi hanyar fita yana fadin Fahad zai kawo miki kuɗin
Ammi dai ido tazuba masa har yafita tukun nan ta sauke wani nauyayyar ajiyar zuchiya afaili tache nida kaina nasan ba iya mulkar mutane zakayiba saboda wan nan irin hali naka bakayi kala da shugabanniba kadaifi dachewa da rike bindigar amma ni babu ruwa kaine zabin mahaifinka bazan chanza masa zabinsaba sai dai inshiyaga dama ya chanzaka da kansa amma zantayaka da adduar Allah yasa  kar abaka mulkin nan dan in akabaka mutane zasusha wahala, zata sake magana sai taji alamar tafiya shiru tayi tana sauraran mai shigowa
Aunty farida che tashigo bakinta dauke da sallama da fara'a Ammi ta Amsa mata sallamar
Shigowa tayi ta zauna a gujerar da Prince yatashi kana tache Ammi barka da hutawa anche kina nemana gani
Ammi tache yauwa sayayya nakesan kuje kiyiwa su Diyana dan kinsan basuda kaya to kisaya musu duk abun daya dache
Aunty farida tache to inasuke suzo muje tare koh dan muzabi size dinsu dakuma colours din dasuke bukata
Ammi tache aa kuɗan jira kadan kanin naki yache zaibawa Fahad kuɗin yakawomin
Aunty farida tache aa basai ankarbi kudi wajen prince ba suzo mutafi kawai ni zan dauki nauyi sayayyar
Ammi tache aa farida kada na daura miki nauyi da kinbari shidai yakawo kuɗin nafisan yamusu da kansane dan kuwa duk wani responsibility su yadawo kansa shi zai dauki komai shiyasama banbiya kuɗinba nache yabiya
Aunty farida tache Ammi dani da prince duk ɗayane idan nabiya kamar shine yabiya kuma kamar yadda nakewa Zahra sayayya da kuɗina suma haka zanmusu saboda yanzu dasu da Zahra duk dayane awaje na
Ammi tache to shike nan badamuwa kuje din
Aunty farida tache Ammi dan allah inaneman alfarman kisa baki mai martaba yabani Diyana wlh tashiga raina ina kaunar yarinyar san nan kuma dan allah kutaimaka kubawa mardiya lamrat takuma da ita Abuja tunda kunga ita Allah bai bata aihuwaba
Ammi tache kwarai ina matukar tausayin mardiya musanman idan kuka haɗu yadda take matikar son junior batasan yayi nisa da ita wani lokachin har kwalla nakemata amma bayadda zanyi inraba marayun allah nan Feeda tare suka taso komai tare suke dukda shekarunsu ba ɗayaba amma dai zan gwada kinji
Aunty farida tache eh Ammi akoi chiwokam murabasu amma dan allah taimaka mana zakuyi muda bamuda yaya Ammi tache to zanyi magana da mai martaba da daddare
Dukyadda mukayi zakiji
Aunty farida tache to saikuma maganan prince Shima dan... Bata kai karsheba Ammi tache kingane tashi kutafi adawo lfy tana kaiwa nan tamike tanufi dakin su Zahra dan takirasu
Girgiza kai Aunty farida tayi tache Ammi " Ammi kinasan samana chiwon kai amma a hankali zanshawo kankine
Fitowa Ammi tayi rike da hannun Amrat su Diyana na biye dasu abaya diyana da hiyana hijabai sukasa zahra kuma abaya tasa da gyalensa sunyi kyau sosai amrat da lamrat kuwa blaus ne ajikinsu mai kyau sai dan karamin gyale dasuka yafa akamsu
Mikewa Aunty farida tayi san nan tache muje koh tayi maganar tana kokarin riko hannun Diyana 
Suna fita kai tsaye parking space suka nufa da sauri driver yazo ya bude musu motar hiyana da diyana da zahra suka shiga mota ɗaya
Aunty farida kuma takama hannun amrat da lamrat suka nufi wata motar suka shiga 
suna shiga wayar aunty farida yafara kara da sauri ta dauki call din tache hello daga ɗayan bangaren yache inakikene insan muyi maganane
Aunty farida tache gani nan yanzu nafito zamutafi shopping kazo karakamu mana sai muyi maganar a hanya " yache aa bazanjeba amma barinasa sojoji surakaminke saboda tsaro" dariya Aunty farida tayi tache kai dai prince allah bansan irinkaba mutunne bayasan shiga jamaa to shike nan tunda bazakajeba saina dawo saimuyi maganar koh zata sake magana ke nan taga waso sojoji guda 4 a gabanta chiki har da abdol
Tache laaaa yanzu muna waya yaushe kayiwa sojojin nan magana
Prince yache lokachin danache bari na hadaki dasu mana alokachin na dannamusu kararrawa dasu nanki
Dariya Aunty farida tayi tache to shike nan ngd saimun dawo
Yache kikula mana da kanki tache to tunkafin takarasama ya katse kiran
Juyowa tayi tabawa driver umarnin sutafi
Abdol  chikin harchen turanchi yache  madan inbadamuwa barini naja motar dan oga yache nabaki kulawa sosai
Aunty farida tache to badamuwa " fita driver yayi yabawa Abdol wajen yashiga sauran sojoji ukun kuma suka shiga wata motar natake suka kunna motar suka miki hanya sai gate " sojojin dake wajen suka bude musu pakekiyar gate din suna fita suka miki hanya
Aunty farida tachewa Abdol to aibaka tambayi ina zamujeba
Abdol yache oga yariga yashigarmin inda zan kaiku a chikin wayata
Shiru Aunty farida tayi tana kallan ikon allah tana jiran taga inda za'a kaisu
Kai tsaye wajen wani katafaren shopping Abdol yashiga yayi parking a parking space nawajen yafito yabudewa Aunty farida tafito kana takama hannu amrat ta tsaya saida su zahrama suka fito sukazo inda take san nan suka nufi chiki Abdol yabi bayansu sauran sojojin suka rufa musu baya Abdol yache su koma wajen mota sujirasu

Kaya dayawa Aunty farida tafara ludan musu kuma tache suma suzaba duk abun dasuka ga yamusu su dauka " Zahra kam duk abun datagani mai dan kyalkyali sai tache wan nan zayyiwa Hiyana kyau ta dauka mata sunyi sayayyar kayan sawa dayawa san nan sukaje wajen takalma da jaka suma dayawa suka dauka suka koma wajen kana nan kaya Hiyana naganin breziya tafa boye fuska Zahra nata mata dariya
Aunty farida kuwa chewa take My Diyana kemafa kin kai sa bra ba Hiyana kawaiba dan kema naga ba bayaba wajen chikar halitta rufe fuska Diyana tayi da hannunta tana murmushi
Amrat ne tayi magana da fullanchi tache zata sha ruwa Aunty farida tache ku fassaramin metache " dariya Zahra tayi tache kai Aunty farida yakamata kema kikoyi fillanchi ruwafa tache zatasha
Aunty farida tache to daga yau hausa zamu rinka yimata dan itama ta iya hausar to waima ya akayi ku kuka iya hausa ita bata iyaba
Hiyana tache mu munazuwa tallan nono ne a chan akoi hausawa suna zuwa saye itakuma kullum tana gida tana aiki bata zuwa ko ina "  a gida kuma ba mai jin hausa sai fullanchi kawai shiyasa bataji
Aunty farida tache to yanzu dai hausar za'ana mata har ta iya to kawai sukache san nan sukachigaba da sayayyar su
Bayan sungama daukan bra da pant suka wuche wajen dankunne da sarka nanma dayawa aunty farida ta dauka musu har da gold saida sukachika keken zuba kaya uku da kaya tukun nan Aunty farida tache ya isheku ne kokuma akoi wani abun dakukeso " da sauri Hiyana tache ya isa "  Aunty farida tache aa kuduba da kyau dai " hiyana tache allah ya isa haka nan " Aunty farida tache to shike nan kutura kayan muje wajen biyan kudi harsun kai wajen biyan kudin kuma sai Aunty farida tache inazuwa chikin shopping din tashiga bangaren always tanufa ta daukoh guda 6 ta dawo ta zuba musu a chikin kayan
Diyana sarkin baki tache aunty menene wan nan kamar breadi Aunty farida tache nakine ke da hiyana da zahra kuma ba bread bane  always ne "  Diyana ta mai mai ta su nan always to me akeyi dashi ko chi akeyi diyana ta tambaya.
Aunty farida dai taga alamar kamar diyana bata fara period ba saitache mata inmunje gida ki tambayi zahra zata fada miki to kawai diyana tache
Nanfa aka fadamusu bill na kuɗinsu Aunty farida ta chiro ATM nata tamikamusu suka chiri kudin san nan aka samusu kayan a leda Abdol yafara kwasan kaya shida yaran shagon suka kai mota
Aunty farida kuwa takama hannun diyana sukayi waje su Zahra suka rufa musu baya
Aunty farida tache Zahra da lamrat da hiyana suje su shiga motar da takawosu itakuma zata shiga motanta itada diyana da amrat .   Tana kaiwa nan tashige chikin motar rike da hannun diyana amrat ma tashigo ta zauna kusa da diyana su
 zahra kuwa suka nufi motarsu suka shiga nantake sojojin suka tada motochin suka nufi gida
Suna isa gida kai tsaye bangaren Ammi suka nufa a palo suka sameta nan suma suka baje kolinsu suka fara nunawa Ammi kaya.   Ammi kam sai sannu da dawowa take musu tana sawa Aunty farida albarka takuma yaba kayan sosai tache su tattara suje su shiryasu a indaya dache, haka suka kwashi kayan sukayi dakinsu dashi

Aunty farida tadawo da hankalinta ga Ammi tache Ammi gobefa zan koma Mai duguri
Ammi tache ai naga wan nan karanma anbarki kindan dade " Aunty farida tache eh wlh shiyasa nakesan komawa dan kar a hanani zuwa sallah kinga azumi yakusa "  Ammi tache ai garakam kikoma kije kikula damijinki yanzu dai kije ki kwanta ki huta a daki sai zuwa dare makarasa hirar
Mikewa Aunty farida tayi tana chewa to Ammi dan allah dai kiyi kokari kishawo mana kan mai martaba daya taimaka yabamu diyana da lamrat
Ammi tache to zanyi kokari   .  Betroom din Ammi aunty farida tashiga ta haye gadanta ta kwanta bajimawa barchi ya dauketa


Zaune suke a tsakiyar gado gaba dayansu hiyana tache aunty zahra dan allah inasan kifara koyamin karatu kinji lokachin muna kanana bappa yana koyamana karatu har munyi nisa danni har nakai izu 10 a karatun qur'ani kuma inasan in iya karatun qur'ani sosai
Zahra tache zan koyamiki hardana bokoma bana qur'ani kawaiba harda addoe dasu hadisai kuma akoi malamin dayake zuwa yana koyamin karatun islamiya kullum dayamma yanzu tare zamuna zuwa ya koyamana
Diyana tache yauwa nima inaso aunty zahra " zahra tache ai gabadayanku ma yazama dole kukoyi karatu yanzuma daga gobe zanfara koyamuku " harsuna hada baki wajen chewa to


Misalin karfe 8 na dare gaba daya family sun hadu a palan mai martaba 
mai martaba da don da aryanne kawai basa wajen shiru kowa yayi daga masu daddanna waya sai wayanda sukayi tagumi suna jiran fitowar Abba 
Aunty farida che ta kalli Fahad tache wai inasu prinse ne kullumfa sune suke bayan zuwa wajen nan " Fahad yayi shiru kamar bazai tankaba kusan 2mnt tukun nan yache nimafa tun dazun damuka rabu bansake shiga wajensuba
Ammi tache au ashe zaka tankamata ai nazachi bazakayi maganaba mutanene yadda kasan wasu kurmaye aimusu magana sunaji amma bazasu amsaba kukan wlh bakuji dadin halinkuba "  Fahad dai shiru yayi kamar baijin me Ammi ke chewaba
Aunty farida tache kai Ammi hakafa akesan namiji yakasanche ba mai surutu barkataiba  " harara Ummi ta watsawa aunty farida kana tache aidaman ke'ki'ke kara injizasu dan kuwa ke awajenki komai sukayi dai dai ne basa laifi " shiru aunty farida tayi bata tankasuba sai sukaji muryan mai martaba yanachewa aa karku dakurawa first born dina ku kyaleta haka nan irin wan nan faɗa haka
Ummi tache ai daman bakinku daya zama mai martaba yayi yana faɗin eh dai munji babu ruwanki farida dawo nan kusa dani
Mikewa Aunty farida tayi takoma kusa da mai martaba ta zauna
Mai martaba yache Amrat ummu waru ( amrat tashi kizo) mikewa tayi taje zaunar da ita mai martaba yayi a kujerar kusa dashi aunty farida kuma tache diyana taso kidawo kusa dani mikewa diyana tai takoma kusa da ita
 Zahra'kam ko ajikinta dan ita koma kusa dawa zama zatayi amma yanzu da hiyana sukazo tare suke komai dan haka yanzuma suna zaune kusa da juna
Takun tafiya sukaji wanda kobasu juyaba sunsan takun manyan boss ne nantake palan ya nitsu tsit wasuma da kyar suke numfashi chiki har da zahra da umar
Su hiyana kam ko ajikinsu dan basumasan masu shigowarba 
Kai tsaye kan table din suka nufa suna sanye chikin fararen jallabiya dukkansu sai kamshi sukeyi kamar anyi barin turare ajikinsu zama sukayi " don ya dauki bottle na ruwan dake kusa dashi ya bude ya tsiyaya ruwa a cup yasha san nan ya ajiye ragowar a kusa dashi  nan take kannen nasu suka fara gaidasu amma babu wanda ya amsa a chikinsu saida kannen nasu suka gama gaidasune
Zahra ta dan zunguri hiyana tamata alamun ta gaidasu chikin gurbatatchen hausarta tache inawuni hamma basu amsaba kuma ko kallanta basuyiba
Diyana kam achikin zuchyarta tache wlh bazan gaishekuba mutane saikache wasu shadanu a muku magana bazaku amsaba kuma kuche inba amukuba zaku hukunta mutun to wlh nikam bazakumin hakan na daukaba yauwa dai dai nake da kowa 

Saida palan yayi shiru san nan chikin nitsuwa don yache inawuni Abba mai martaba ya amsa da lfy " ya dawo da kallansa kan su Ammi suma yabisu ɗaya bayan ɗaya ya gaidasu
San nan aryanma yabi iyayen nasu ɗaya bayan ɗaya ya gaidasu
Shiru kowa yayi a palan sai aunty farida tachewa kuyangun dake tsaye a kansu dasu zubawa kowa rice an beans da sauri suka fara sarving nasu suna turawa kowa
Aunty amarya tache nikam bashi zaku zubaminba kuzubomin semo da miyar agusi
Bawanda ya tankata a palan sai aunty farida ne tache kuzuba mata mana tunda shi take raayi da sauri suka zuba mata suka mika mata
Suna chikin chin abinchi hiyana tafara shakuwa shakuwa yaki tsayawa hannutasa ta dauki cup din ruwan da don ya ajiye kusa dashi daya tana kusa dashi tafara sha kamar daga sama taji saukar mari a fuskarta har saida tamike batasaniba,dafe kunmatunta tayi da hannu tana kallansa hawaye nazuba daga fuskanta wani tsawa ya daka mata wanda yasata zurawa aguje tabar palan tayi sashen Ammi kowa na palan sai daya tsorata banda mai martaba da aryan
Aunty farida ne tayi karfin halinchewa haba prince meyasa zaka mareta bakaga yarinya bache kuma inkalura batasan ruwan shanka ta dauka bafa
Ko kallan aunty farida baiyiba barema yabata amsa abinchinsa kawai yachigaba dachi shiru palan yayi ba abunda kakeji sai karan spoon
Zahra kam jikinta sai rawa yake tanasan tashi tabi bayan hiyana amma tana tsoro 
mikewa diyana tayi tabi bayan hiyana lamra naganin diyana tamike itama tamike da gudu tabi bayansu amrat zata tashi mai martaba ya riketa yache zauna yata kichi abinchinki karki damu  
Kuka amrat ta pashe dashi tana fadin aa nakoshi nikam zanje wajen Aunty hiyana na " mai martaba dayaga haka sai yache zahra dauki abinchin naku kikama hannun amrat kutafi kuje daki kuchi a chan " da sauri zahra tamike ta dauki abinchin nasu takama hannun amrat sukayi waje 

Mai martaba yayi gyaran murya yafara magana " meyasa zaka dora hannunka ajikinta kai bakada tausayine marayunefa ba uwa ba uba haka suka taso chikin kunchi da wahala yanzu kowani kukagani zai bugesu bazaku tsaya kutaremusu sai inda karfinku yakare amma kai da kankane ma zaka bugesu " bakataba batamin rai irin na yauba gaskiya banji dadin hakanba kuma kasan lbr yaran nan babu abun da baka saniba agabanka aka bada lbr wahalar dasukasha, to bansan hakan tasake faruwa kanaji
Kasa kasa don yache sorry Abba rainane yabachi " mai martaba bai sake chewa ko uppanba
Yusuf yache allah sarki wai daman Abba basu da iyayene wlh harsunban tausayi " wani kallan banza aryan da don suka watsawa yusuf amma ko ajikinsa saima chewa yayi Abba gaskiya to indai hakane yakamata mubasu kulawa sosai dan sumanta da bakin chikin rashin iyaye
Ammine tache haidar umar fahad duk kutashi kubamu waje zamuyi magana " da sauri suka mike sukayi waje " suna fita afusache Ammi ta dubi don tache idan kasake sa hannun ka bugi ɗaya daga chikin yaran nan to wlh ban... Bata karasaba mai martaba ya rufe mata baki kana yache aa bansanjin hakan 
Don kuwa dagowa yayi yana kallan Ammi yaga yadda ranta yabachi sosai tabbas baitaba ganin bachin rai a fuskar mahaifiyarsa irin na yau ba hakan yasa jikinsa yayi sanyi haryafara nadamar meyasama yayi sauri marin yarinyar meyasa baya iya controlling zuchiyarsane why gashi tunda yake da Ammi baitaba bata mata raiba sai yau gaskiya bai kyautaba
Chikin nitsuwa da sanyayyiyar voice nashi yache kiyi hakuri Ammi inshaa allah zanrinka kiyayewa " batare da Ammi ta kallesaba tache dazaifimaka
Yusuf dai mamaki yake wai yau don'ne ransa yabachi haka kuma yayi saurin saukowa zuchiyar tayi sanyi tab lallai uwa tawuche wasa duk wani karfin izzan da mutun yake dashi bai isa yayiwa mahaifiyarsaba

Mikewa mai martaba yayi yana fadin Ammi kisameni adaki inasan magana dake ita Ammi tamike tabi bayansa tana faɗin to ganinan ai muje tare tunda mungama chin abinchin
Don da aryan ma mikewa sukayi suka nufi bangarensu
Yusuf yache Aunty farida wlh yaran nan sunban tausayi wai yama su nansune
 Aunty farida tache wanda don yamara itache hiyana wanda tabi bayanta bayan ta gudu kuma itache diyana ta ukun kuma lamrat sai amrat itache karamar tayi maganar tana kokarin mikewa
Yusuf yache ina zakije aunty farida " zanje inyimagana da aryan da don ne dan kaga gobe zankoma 
Yusuf yache to shike nan nima zanbiyoki daganaya bari nasha coffee ina zuwa to kawai tache masa san nan tawuche tafita daga palan

Tana fita palan bangaren aryan tafara zuwa da sallama tashiga palan babu kowa dan haka tanufi betroom dinsa zune tasamesa a kan kujerar mirrow yana hada wasu magunguna jin sallamarta yasa yadago kai yana kallanta 
aunty farida tache mezakayi da waɗan nan magungu nan kuma " yache ina hadawa don ne "  bashi da lfy ne ta tambaya tana kokarin zama a gefen gadansa aryan yache aa banashi bane akoi wasu criminals da zaiwa amfani dasune " aunty farida tache too allah yachechesu daga hannunku " murmushi kadan yadanyi kana yache kai aunty babba muɗin kuma yau
Aunty farida tache kuɗinfa aiku duk wanda yayi laifi kuma a kache kuzaku hukuntashi to wlh garama yachire rai da rayuwa dan kuwa inbai mutuba kadanne zai rage masa aryan zaiyi magana wayarsa tafara kara alamar shigowar kira bai dauki wayarba har kiran ta katse "  aunty farida tache wayake kiranka haka dakaki dagawa a takaiche yache faruq ne " aunty farida tache faruq dai danasani best friend naku  " aryan yache eh shine " aunty farida zata sake magana kira nabiyu yashigo bai dagaba har saida wayar takusa tsinkewa tukun nan yayi picking call din kuma yasata a H-free 
yache hello my tager daga dayan bangaren faruq yache my man ykk yanakira da farkoh baka dagaba . aryan yache  hannuna nachikin wasu chemicals ne shiyasa ban dagaba daman innagama abundanake zankiraka saikuma kasake kira  ykk y mom da dad ina zahra da zaina da maryam faruq yache Suna lfy yasu Ammi. Aryan yache suna lfy ina abdul soja "  faruq yache yana nan lfy " amma katambayeni kowa baka tambayi inteesar ba
Aryan yache wache kuma inteesar" faruq yache matar da zan aura mana " dogon tsaki aryan yaja kana yache kaima auren zakayi " faruq yache eh mana aryan yache tofa karkabari don yajika kaibama don bama nima yanzu..bai karisa maganarba aunty farida ta amshi wayar tana fadin yaushe zaka kawomin amaryan maiduguri inganta " faruq yache aunty babba ashe kina kusa " aunty farida tache eh wlh faruq amma gobe zanwuche " faruq yache ina junior
Aunty farida tache yana wajen Ummi kai bama wannanba yaushene auren,  kuma kasa lokachi kakawomin amaryan inganta,  ai garamaka kayi aurenka karka biyewasu Aryan dakuwa su basusan chewon kansuba
Baki bude aryan ke kallan aunty farida sai zuba hira take da faruq dagajin yayi maganar aure waisu me matsalarsu dasuke san sai munyi auren nanne  
Bayan aunty farida tagama hirarta da faruq ta katse kiran ta mikawa Arayan wayansa san nan tache to daman nazo muyi sallamane gobe zanbi jirginsafe zuwa maiduguri
Aryan yache ok karfe nawa
Aunty farida tache 7 dai dai " Aryan yache okay zanzo inkai ki airport.   Aunty farida tache to ngd bari naje nayiwa donma sallama tayi maganar tana kokarin mikewa
Aryan kuwa baisake tankamataba har tafiche daga dakin tama bar shashen nashi gaba ɗaya tanufi shashen don agurgije tamasa sallama dan tanasan taje ta shirya kayanta shima dai don chewa yayi zaizo yakaita airport


Abangaren su hiyana kuwa tana parin palon dakinsu tanufa tafada kan gadonsu tana kuka diyana nashigowa ta haye kan gadan tana rarrashin hiyana saigasu zahra " nan zahrama tashiga rarrashinta har tayi shiru takuma saukoh kasa suka karisa chin abinchinsu nan suka haye gado zahra ta daukoh takardun makarantar ta tafara koya musu karatun.


Ammi na zaune a tsakiyar gadan mai martaba tana gyara masa gashin kansa suna yar hirarsu chikin nishadi Ammi tache ran'kayadade dan allah katausayawa mardiya kabata lamrat kaga batada ƴa allah baibata Aihuwaba gashi faridama tana san diyana
Mai martaba yache oh bakyasan ganinsu a gabankine to idanma ke bakyasan ganinsu ni inabukatar ganinsu kuma babu abunda zai raba yaran nan sai mutuwa ko aure bazan yarda yarabasuba dan kuwa idan miji ba agarin nan yakeba babashi aurensu zanyiba wlh duk wanda yake sansu tofa saidai  in mazauni kano inba hakaba yahakura kuma wan nan shine hukunchina bansan sake jin wata magana akan yaran nan
Ammi tache to inshaa allah bazan sake magana a kai ba jawota mai martaba yayi tadako kan kirjinsa yana faɗin shiyasa nake sanki sosai kekadaiche a chikin matana innayi magana baki musamin kobakison abun danache haka kike hakura ki amsamin allah yamiki albarka " shafa gefen fuskarsa Ammi tayi tache nima ai inasanka sosaima 
Mai martaba ya ɗan chije hannunta yache yanzu babu fullanchi ke nan
Dariya Ammi tayi tasake ahigewa jikinsa tana faɗin eh kam akoi amma kaɗan kaɗan rungumarta sosai mai martaba yayi yafara raɗa mata magana a kunne 


Misalin karfe 10 dai dai aunty farida tashigo dakin Ammi da sallama abakinta Ammi na kwanche a kan gado tamike daga zaune ta amsa sallamar
Abakin gadan aunty farida ta zauna tache Ammi gobe da asuba zantafi nazone naji yakukayi da mai martaba " Ammi tache wlh feeda har kunyarki nakeji bansan yazanfara yimiki bayaniba " Aunty farida taɗan kakalo murmushi kana tache karki damu Ammi aidaman nasan dawuya mai martaba yabanisu saboda tunfarko yanuna aa bazai bayarba amma bakomai wlh Ammi gobe zanwuche zanbi jirgin karfe 7 
Ammi tache to allah ya tsare hanya feeda Aunty farida tamike tana fadin ameen tanufi hanyar fita tana fita kai tsaye tayi bamgaren Ummi

Washe gari  misalin karfe 9 na safe gaba daya family suna palon mai martaba zaune  akan table din chin abinchinsu gaba ɗayansu har dasu don amma banda su diyana da zahra da mai martaba 
Mai martabane yafito daga ɗakinsa yazo ya zauna a kujera nanfa kowa yafara gaidashi gaba ɗayansu yahadesu yabasu amsa ɗaya san nan yache inasu diyana
Ammi tache suna daki " mai martaba yache to mryafaru basu fitoba
Ammi tache wlh nayi nayi suzo muchi abinchi hiyana tache itakam wlh tana tsoran yayansu bazata iya zuwaba gaskiya kuma daga yauma a daki zata rinka zama to saurankuma dasukaga yayartasu taki zuwa suma sukache bazasu iya zuwaba dana nuna zan matsamusu sai suka fara kuka shine na kyalesu zahra'ma na tare dasu,
Mai martaba yache ai daman nasan zaayi hakan ɗayanku yaje yakiraminsu
Mikewa yusuf yayi yache bari naje da kaina na shawo kansu kila idansuka ganni zasuzo
Wani kallan banza don ke wurgawa yusuf amma yusuf ko ajikinsa aryan kuwa sai hararan yusuf din yake amma yusuf baibi takansuba yayiwaje 

Da sallama yashiga palan lamrat kawai yasamu zaune tana kallo tsayuwa yayi yana kallanta kusan 5 mnt yana tsaye itakuma Sai kallanta take batasan da mutunba
gyaran murya yaɗanyi 
Ta ɗago aiko tana kallansa tamike tawatsa a guje sai chikin ɗaki   ". Dan ita atunaninta don ne dan bata iya rabesu 
Binbayanta Yusuf yayi har chikin dakin da sallama yashiga suna zaune kan gado suna ganinsa dukkansu suka rungume hiyana suka kame jikinsu waje guda banda zahra " zahra kam nitsuwa tayi murya na rawa tache ina kwana yaya yusuf ga mamakin ta sai taji yache lfy baki sake zahra ke kallansa tun datake dashi bata tabajin ya amsa gaisuwar waniba a gidan nan amma yau ya amsa nata tab to kodai mafarki takene tayi nisa chikin tunani saitaji muryan shi yana faɗin
Hiyana tashi kizo " murya na rawa hiyana tache dan Allah kayi hakuri tana magana tana hawaye wlh nibansan ruwanka bane shiyasa na dauka amma dan allah kayafemin karkasake dukana bazanma sake zuwa wajen chin abinchinbama kaji
Tana chikin magana kawai taji ansa hannu ana share mata hawayen dake gangarowa daga fuskarta da sauri ta dagokai murya na rawa tache..


Pls more comments an share 
*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

 💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 8*
          


Tana dago kai suka haɗa ido da yusuf," chikin kuka take faɗin dan allah hamma kayi haku...bata karisaba yadora hannunsa a kan lips nata yana faɗin to ya isahaka kiyi shiru bamai sake bugunki"
"Zahra'kam Mutuwar zaune tayi tashiga duniyar tunani, wai shin daman yaya yusuf haka voice nashi yake, allah yasa dai bawani aljani bane yazo musu a siffar yaya yusuf
Zahra, tayi nisa a chikin tunaninta kawai " "saitaga yusuf yamike tsaye yana rike da hannun hiyana saida sukamike," yache
Yakamata kirinka banban'chemu ni sunana yaya yusuf, wanda yamareki jiya su nansa yaya prince kinji, " cikin shesshekar kuka take faɗin to amma zan iyache muku hamma ," Yusuf yache meyasa kikesan kirinka chemana hakan "
"ai kunada yawane idannache dukkanku yaya zanrinka chewa bazan ganeba, amma idan ina hadawa da hamma abun zanmin sauki "
"Murmushi  yayi san nan yache to shike nan nikirin'kachemin hamman kinji  " to Kawai hiyana tache," dawo da kallansa yayi kansu  diyana,  kutaso muje mana, ba musu suka saukoh daga kan gadan "
"Zahra ma saukowa tayi suka jera yusuf narike da hannun hiyana saida suka fito palon Ammi, batare da yasaki hannun hiyanaba, yasa ɗayan hannunsa ya kamo hannun lamrat yache ke yasu nanki "
"Dawani gurbatatchen hausarta tache lamrat,"  jinjina kai yusuf yayi yana faɗin gaskiya lamrat yamin nisa awajen kira gashi su nan naku nada wahalar kira sosai dole na chanza muku suna ni bazan iya kiran sunan nan nakuba"
"Shiru sukayi kawai suna jinsa, yanuna hiyana ke daga yau su nanki sweet sis, yanuna diyana kekuma little sis, yanuna lamrat kekuma baby yanuna amrat yache my little baby ," 
"Zahra dai binsu kawai take dan ita duk tunaninta aljanine yazo a saffar yaya yusuf dan tun da take wlh bazatache, ga kalan  voice na yaya yusuf  ba, amma yau shine har da magana mai tsawo, kai to kodai umarnin mai martaba yabashine dan nasan mai martaba bazai tabarinsu hiyana a kunchiba

Dasallama sukashiga palan mai martaba," kowa yadago ya zubamusu ido amma banda don da tager Aryan"
"Umar'ne ya taba haidar kasa kasa yake faɗin kai anya kuwa yaya yusuf ne,  kadubafa har da rikemusu hannu," haidar yaɗan kallai gefe da gefe yaga bamai kallansa kasa kasa shima yake magana kaidai kabari muje ɗaki mayi maganar, kar'ajimu amana hukunchi"
"Yusuf kuwa yana shigowa palan ya ɗaure fuska kamar baitaɓa dariyaba sakin hannunsu yayi yakoma wajen zamansa ya zauna"
"Mai martaba ne yadubi su diyana dake tsaitsaiye, kuzokuzauna yache dasu chikin harshen fullachi"
"Diyana da lamrat da amrat sukazo suka zauna sukabar hiyana tsaye tana rakuɓe rakuɓe, dan ita harga allah kallan fuskar don tsoro yake bata, yanzu babban damuwarta ma kujera ɗayane yarage a table din kuma kusa dashi kujerar take, dankuwa kowa bayansan zama kusa dashi shiyasa mafi yawanchin lokuta kujerar kusa dashi zaka sameta babu kowa, yanzuma ita kawai tarage tunani hiyana tashigayi sosai tache to wai ina sauran kujerun ai kujerunma sunfi haka yawa, saboda jiya ai aunty farida da aunty mardiya suna nan kuma duk a nan mukachi abinchi dasu to yaukuma basu nan kuma table din yachika to ina sauran kujerun ke nan , tayi nisa chikin tunanani saitaji muryan mai martaba yanachewa
Kai Safras jekatawomin da ita dan tsoranka yahanata zuwa, " da sauri don yaɗago kai yana kallan mai martaba " dauke fuska mai martaba yayi yache abun dagaji shinafaɗa dan idan bakaikamata maganaba bazata daina tsorankaba"
"Nantake fuskar don ta sauya idansan nan suka chanza launi zuwa jaa sosai jijiyoyin kansa duk suka mike sai wani huchi yake kamar zaki," kannensa naganin haka suka kama hansu, dagudu suka bar palan yarage daga Ammi Ummi Mai martaba Aryan Yusuf Fahad "  Khalid ma guduwa yayi dan yasan halin mutuminnasa Ida ransa yabachi"   aunty amarya'ma ba abarta abayaba ta'tsere " itama hiyana tana ganin sungudu tajuya itama tabisu"
"Mikewa don yayi sai wani huchi yake yanufi hanyar fita," da sauri Aryan ya taresa yana faɗin don bakada hankaline mai martaba nefa yake maka magana " hannu don yasa ya ture aryan gefe guda yanufi hanyar fita haryazo tsakiyar palan "  aryan yasake taresa yana faɗin don kadawo chikin hayyachinka kasan mekake kokarin aikatawa kuwa"  dunkule hannu don yayi yakaiwa Aryan bugu a Kirji "  Aryan bai bari bugun ta sauka ajikinsaba yasa hannu ya tare hannun don," afusache don ya damki wuyar Aryan da ɗayan hannunsa yayi sama dashi kana yayi wurgi dashi gefe gida "  rai a ɓache Aryan yamike yayi kansa shima wani bugu yakaiwa don a bayan wuya " da sauri don yajuya yasake tamkar wuyan Aryan ya shakesa sosai " Aryan kuwa dayaji azaba sai dunkule hannu, ya kai don bugu a bayan kunne saiga jini ta hanchinsa," afusache don yayi wurgi da Aryan kana yanufesa gadan gadan ya damki kafarsa yasake wurgi dashi gefe guda duk dahaka bai kyalesaba yasake yinkansa "   "da gudun gaske Ammi tasha gabansa tana faɗin nizaka fara kashewa ba dan uwankaba " 
Mai martaba kam harde hannu yayi yana kallan Iko  god "  yusuf ma bai damuba dan yasan indai irin wan nan faɗane sunsaba idan taɓachimusu "
Don saiwani huchi yake yache Ammi kibani hanya pls zuchiyata zafi takemin idan ban bugi Aryan'ba mutuwa zanyi " rai abache Ammi ke magana kamutu kamutu nache Ammi bata karasa maganaba yayanke jiki yafaɗi kasa sumame "   Yusuf yamike yana faɗin   alhamdulillah alhamdulillah  tunda yasuma ai shike nan "
"Ummi che tayi kansa ita da Fahad da sauri "  Ammi kuwa juyawa tayi tabar palan tanufi bangarenta abinta " mai martaba yamike da sauri yayi kansa yana faɗin, yusuf kukira sojojinsa a kaisa asibiti " aa Abba basai ankaishi asibitiba idan yasamu barchi zai watsake karka damu kaje kawai kayi shirin zuwa fada dan anajiranka,kaga lokachi yatafi chewar yusuf "
juyawa mai martaba yayi yanufi ɗakinsa jiki ba kwari, yana ta tafiya ya tunanin ,anya ba aure zanwa yaran nanba ko nasami zuchiyar nan tasu ta ragu kai inganin hakan za'ayi nan da bayan sallah dole zanche kowan'nensu  yafito da mata da wan nan tunanin yashige ɗakinsa  

Ummi to yanzu yazamuyi mukaisa daki daman Aryan ɗinne kawai mai ɗaukansa idan abunnasa ta motsa, to yau kuma yayiwa Aryan rauni yusuf baigama rufe bakiba "  "sukaga Aryan ya tattare dukkan karfinsa ya dauki don a kafaɗarsa yayi waje dashi "  
"Ummi tache allah sarki allah yakara haɗamana kanku allah yakaramuku kaunarjuna " ,jinjina kai yusuf yayi kafin yafuta  ameen Ummi  ai kulluma idan sukayi faɗa don ke bugun Aryan amma kuma Aryan ke taimakon don akoyaushe "  murmushi Ummi tayi san nan tamike tanufi nata bangaren " yusuf yadawo da kallansa kan fahad dake tsaye to muje koh "  Fahad yajuya kawai yayi batare dayayi maganaba yanufi hanyar fita


Su zahra kuwa suna zuwa ɗaki suka samu hiyana na kuka zahra tache hiyana meke damunki "  chikin kuka take faɗin  aunty zahra kidubafa kigani nasan abaya ba haka akeyi a gidan nanba amma daga zuwanmu har anfara faɗa "  aa hiyana bawai saboda zuwanku bane ai ku zuwankuma alkhairi ne, bagashi kunfara chanzamana su ba kidubafa kiga yau yadda kukayi hira da yaya yusuf ,to wlh barikiji ni tundanake a duniyar nan bana'chemiki  ga kalar voice na yaya yusuf ba saboda bakin halinsu, komaganama basayi amma a dalilinku yau yaya Yusuf yayi magana, san nan kuma ya amsamin gaisuwata aini wan nan rana tashiga chikin ranakun dazan ajiye a matsayin tarihi " "sallama sukaji daga bayansu Ammi che ta shigo a gefen gadon tazauna tashiga rarrashinsu tana basu baki

Abangaren aunty amarya kuwa tanashiga bangarenta wayarta ta ɗauka takira hajiya Sadiya bugu ɗaya hajiya Sadiya ta ɗauka 
Ko sallama babu kawai tasoma magana"  sadiya inakike munshiga uku " hajj sadiya tache meyafaru Kumar "
"Aibama abunda bai mafaruba chewar aunty amarya  bana faɗamikiba yanzu gashi wlh yusuf da kanshi ɗazunɗin nan yaje har ɗakin Aisha, yakira yaran nan wai suzo muchi abinchi, kinga ke nan hankalin samari gidan yafara juyowa kansu yaran, tunda har yusuf da kansa duk zafin ransan nan ya saukoh yaje yakirasu wlh gobekuma, nasan sai aiman daga aiman sai Aryan da Safra shike nan idan hakan tafaru kuma munshaga uku
Hajj. Sadiya tache aa hakan bazai faruba ki kwantar da hankaliki karki damu kinji nizanyi maganin komai "  to dan allah kiyi sauri kinji "  karki damu inshaa allah aikinki zaitafi yadda kikeso kuma saimunyi maganinsu  chewar hajj. sadiya " aunty amarya  tache to shike nan sainajiki kana ta katse kiran ta zauna abakin gadon tana tunani


Yau yakama Monday tun karfe 6 nasafe Khalid yazo bangaren Ammi, dan ya ɗauki su hiyana suje a musu registration a school ɗin su zahra,  zama yayi a palan Ammi yana jiransu " da'sallama sukashigo palan hiyana na sanye chikin riga da sket na kanti mai kyau ash colour rigar mai dogon hannu yaɗan kamata sai sket din daga sama ya ɗan kamata kasan kuma yabude sosai kayansu iri ɗaya da diyana, sai dai na diyana light green ne, sunsaka hijab da bazata wuchi guiwaba ,amrat da lamrat kuwa riga da wando sukasa rigar zuwa goiwa wandan koma dogo har kasa sky blue sun yafa karamin gyale " 
"Zahra kuma nasanye chikin uniform nasu, riga da wando da dan karamin hijab rigar fara tas zuwa goiwa sai dogon wando navy da ɗan karamin hijabin da baiwuche kirjiba "
"Wow chewar Khalid gaskiyane my sister's kunyi kyau sosai abunku to kuzo mutafi" 
"Ina kwana yaya inji hiyana" lfy lau yabata amsa"
Ganin hiyana ta gaidashi yasa suma su diyana suka gaidashi ya amsa fuska a sake, san nan yache kuzo muje karmuyi latti kunga har  7:4 tayi " gaba yayi sukabi bayansa" suna fitowa harabar gidan suka samu yusuf tsaye jikin mota, yana sanye da white jeans da ash T-shirt bakaramin kyau yayiba sai kanshi ke tashi daga jikinsa kamar anyi barin turare ha gashin kan nan yasa har kam kafaɗarsa ya sha gyara sai kyalli yake daman gashin bakine sosai " 
Gaidashi suka farayi " yana amsawa fuska a sake " inazakaje yusuf Khalid yajefo masa tambaya " rakaku zanyimana " dariya Khalid yayi sosai kafin yache to yau kuma wasa kakejiyimin kenan " daure fuska yusuf yayi yana faɗin wasa kuma to daman muna wasane, inzakazo mutafi kazo muta inkuma bazuwa zakaiba ni sai na daukesu muje namusu registration din " da mamaki khalid ke kallansa kamar bazai tankasaba saikuma yache to muje " mota 3 sukayi zahra hiyana diyana mota ɗaya suka shiga" Khalid lamrat amrat suka shiga mota ɗaya yusuf kuwa nashi motar yashiga " sai wasu motochi 3 kuma dake binsu a'baya dauke da sojojin yusuf guda 9 kowani mota sojoji uku " dagudu gaske motochi suka miki hanya harzuwa bakin gate nan take security suka gangalemusu katafaren gate ɗin suka dauki hanya gudu sosai suke shararawa  chikin kankanin lokachi suka isa school ɗin " sunayin parking sukafito kai tsaye office din principal suka nufa, nan danan batare da ɓata lokachiba suka gama komai kuma suka roki alfarman da akai diyana da hiyana primary 6 tun da sunyi girma amrat da lamrat kuma a kaisu primary 4 da kyar principal ya aminche nanfa  suka mika masa amanar'su diyana san nan Khalid da yusuf suka fito sukabar su hiyana sukaje suka shiga  moto chinsu suka juyo sai gida"

"Kwanche tashi babu wuya awajen allah yau su diyana sunchika 1 month da dawowa kano sunchanza sosai kamar basuba sunyi kyau ga kiba dasukayi sunyi fresh dasu kamar yayan larabawa sunfara wayewa da gogewa "  bangaren karatu kuwa baa magana dan sun dage sosai " sai dai a wan nan bangaren  sunsamu banbanchi dan kuwa ita hiyana tafi maida hankali kan karatun islamiya musamman karatun qur'ani " itakuma diyana tafi dagewa a pannin boko" amrat da lamrat kuwa dukka bangare biyun suna dagewa " 

yauma kamar kullum sun dawo daga school misalin karfe 4 na yamma suna kwanche a ɗakinsu gaba ɗayansu suna hira "  diyana tamike tana faɗin natafi palo nayi kallo " saikin dawo inji zahra " fichewa diyana tai jikinta sanye da doguwar riga fari tas mai kyau amma jikin'rigar bawani kwalliya plen'ne kanta kuwa babu dan kwali ta zuba gashin nan har gadan baya sai sheki da kyalli yake kawar wata yar india " zama tayi a palan abinta ta kunna kallo ta kamo tashar discovering tana kallan daji da abun dake chikinta " daman diyana sarkin san kallone  " "tayi nisa chikin kallan datake batama ji shigowar mutunba " sai dai kawai taji yana faɗin ke jeki kawomin coffee " da sauri ta ɗago tana kallansa" murya na rawa tache ina wuni yaya Aryan " bai amsaba kuma bai sake dagowaba" mikewa tayi jikinta har rawa yake ta saukoh kasa tanufi kichin " coffee ta hada masa yadda taga bintu mai aiki kehadawa ta dora a kan plate san nan ta dauka takoma sama" yadda tabarsa haka tasamesa gabansa tazo ta duka tamika masa cup ɗin batare datayi maganaba " shiru bai ansaba kuma shima baiyi maganaba har kusan 10 mnt tukun nan a shagwabe take magana ayya yaya nagaji wlh hannuna zafi yake kakarɓa mana pls " da sauri yaɗago yana kallanta yadda take maganar hankalinta kwanche,sai daya ƙare mata kallo from head to toe , tukun nan yasa hannu a nitse ya karbi cup ɗin yana faɗin karnasake ganinki babu ɗan kwali " "shiru tayi tana tunanin daman yana kallan mutanene basai mutun yazo yawuchesa sau darima bai ɗaga kai ya kallesaba tayi nitsa chikin tunani " yadaka mata tsawar da sai'dayasa tamike, badake nakeba" murya narawa take maganar eh eh naji yanzu zanjema,na daukoh " batare daya kalli,indatakeba to jiki daukoh kizo " da sauri ta juya tanufi ɗakinsu 

A hankali ya kai cup ɗin coffee ɗin saitin bakinsa ya kurba da sauri yasauko da cup ɗin yadawo dashi saitin idansa yana kallan coffee ɗin,mamakine ya bayyana karara a kan fuskarsa sake kai cup ɗin bakinsa yayi yasake kurba ya lumshe ido,kana yabuɗe sosai yake shan coffee ɗin har takare batare daya saniba,shiru yayi yana tunanin wai bayache yarinyar nan tasa ɗan kwali yazoba,meyasa bata dawoba,ganin tunani babu abunda zaimasa,yasa yachiro wayarsa,yafara neman layin yusuf ringing wayar take amma ba'a ɗagaba har saida kiran takusa katsewa Yusuf,yaɗauki kiran a nitse yake magana yusuf kana da num ɗin zahra ne " eh inadashi lfy faɗin yusuf " eh lfy turomin yanzu " ok inji yusuf  " katse kiran yayi ya ajiye wayar a gefensa saikuma wani tunani tafara shiga zuchiyar wai meya haɗani da itama to dazan'nemeta, wani bangare na zuchiyarsa ke bashi amsar dachewa saboda coffee mana,afili yake faɗin yes saboda coffee,wayar'sane tayi kara alamar shigowar sako yana dubaka,saiyaga num ɗin zahra yusuf ya tura masa

kiran layin yafarayi  ringing ɗaya zahra ta ɗaga " chikin isa take magana wai wayene naga sabuwar number" "kamar daga sama taji muryan Aryan yana faɗin kichewa yarinyar nan tazo palo tasameni, " saura kaɗan zahra tayi fitsari a wando saboda tsoro in ina tasomayi,ina ina inawuni yaya " baijira yaji wata maganaba yakatse kiran " aruɗe zahra ta dubi diyana,tache diyana ke kaɗai che kikafita ɗakin nan mekikaje kika aikata to kiyi sauri yaya Aryan na palo na jiranki " murguɗa baki diyana tayi san nan tafara magana,mekuma zanyi niga iya coffee kawai yache nakawo mar kuma nakaimasa, sai ɗan kwali dayache na saka kuma basawa zanyiba  ato irin zafin nan dake damuna, wlh ni gashinma yankesa zanyi da almakashi dan zafi yakesa naji " Zahra dai a tsorache take, tafara magana kai dagaji muryar tama kasan a tsorache take kitashi to kije dawuri yana palo yana jiranki " batare da'tasake maganaba tamike tayi waje tana murguɗa baki, yadda ta barshi haka ta dawo tasameshi da sallama a bakinta tashigo palan," bai amsaba kuma bai ɗagoba " gabansa tazo ta duka a sanyaye tayi magan gani nan " bai tankataba kuma bai ɗagoba kusan 8 mnt " dan allah yaya kayi magana mana wlh nagaji da dukawan nan kafofina sunnamin zafi chewar diyana " kamar baiji me tafaɗaba yachigaba da daddanna wayarsa saida yakara kusan 10 mnt " tukun nan, ya ajiye wayar a gefe bata re daya kalletaba yafara magana ina dan kwalin danache kisa " shiru tayi batayi maganaba kana ta zuba masa ido tana kallansa " dago manya manyan idan'sa yayi ya saukesu a kanta, saida ta tsorata ganin shikuma kalar idon nasa ash ne, ita tunda takema bata taba kallon idansuba dan basa dago kai " tsawa yamata badake nake maganaba " nantake tafara hawaye tana faɗin dan allah yaya kayi hakuri wlh akoi zufane idan mutun yasa ɗan kwali kuma.. " Bata kai karshen maganarba yaɗaga mata hannu yana faɗin it's ok waya haɗa miki coffee ɗazun " nine dakaina na haɗa tabashi amsa " ke da kanki yayi tambayat yana kawar da idonsa daga kallanta " eh nina haɗa " to tashi kije kiyi nill down a chan " toni menamaka, a shagwabe tayi maganar " mamakine yakamashi, ya mai mai ta maganar nata toni menamaka, nan take ya daure fukar nan kamar baitaba dariyaba, wani mugun kallo ya wurga mata wadda tasata mikewa ba shiri takoma tsakiyar palan tayi nill down,"
Jingina kansa yayi a jikin sofar ya lumshe ido makar mai barchi, kusan 15mnt ya ɗauka a hakan kamar daga sama kuma yajiyo voice na Aiman yana faɗin wai daman nan kazo inata nemanka " batare daya buɗe idoba yake faɗin, to mezaka bani " yusuf dake tsaye a gefe guda ne yache mekuma diyana tamaka " "sai'lokachi yaɗago kai azuchiyarsa yana mai mai ta sunan diyana kallon inda take yayi sai faman haɗa zufa take, ɗauke kansa yayi yamaida,kan su yusuf dake tsaye kusa dashi zaiyi magana " yusuf yarigashi dachewa diyana tashi kitafi ɗaki " ai tun Yusuf bai karisa maganaba tamike da gudu tana hawaye tayi ɗaki " harara Aryan ya wurgawa yusuf kana yache me ruwanka da ita kai kabata punishment ne dazakache ta tashi " "harara yusuf ma ya watsa masa kana yanufi sofar yana kokarinzama yanafaɗin kudai bakuji daɗin zuchiyarkuba wlh ko tausayin yaran nan bakuji kunafa sane da irin rayuwar dasukayi amma baku kyautawa wlh " " kallan banza Aiman yayiwa yusuf san nan yafara magana to kai tunda kanajin tausayinsu ba shike nanba, inaruwanka da zakache musai mungi tausayin nasu, to bamuji kuma bazamujiba " kallan banza shima yusuf ke bin Aiman dashi kawai batare dayayi maganaba " mikewa Aryan yayi yanufi hanyar fata daga palan batare dayayi maganaba " kallo Aiman yabishi dashi har yafiche tukun nan ya dawo da kallansa kan yusuf yafara magana " kamar wani abu nadamun tager fa ko yakagani " eh naga alamar hakan achiwar yusuf " to bari nabi bayansa dan naji me matsalar chewar Aiman " adawo lfy inji yusuf " Aiman bai amsaba yafito kaitsaye bangaren Aryan yanufa.

Zaune take a gefen gadanta tana fuskantar hajj sadiya wasu abubuwa hajj sadiya tafitar daga jakanta guda uku tamika mata tana faɗin angama da batun sarauta, sauran batun wayan nan yaran da Aisha takawo, gagarabadau yachemin infaɗamiki aiki akansu bakaramin aiki bane sai munbashi lokachi dan da alama yaran akoi tsari ajikinsu saiyafara warware tsarin jikinsu,tukun nan zai iya yimasu wani aiki," Aunty amarya ne tasoma magana to wayan nan yarakuma inasukaga wani tsari ajiki saboda allah dai " hannu hajj sadiya tasa tarufewa Aunty amarya baki,tana faɗin ke wlh gagarabadau baya karya kuma kiyi a hankali dan daga nan zai iya jiyo mekike faɗi, batun yara kuma dakike magana duk fulanin nan dakike gani suna zaune a dajin nan chemiki akayi a banza haka kawai suke zaunene ai tun randa suka haifi ƴaƴansu, aranar suke farajijjikasu da magunguna " "chere hannun hajj sadiya Aunty amarya tayi daga bakinta kana tache to shike nan yanzu wayan nan kayan dakika banifa ya za'ayi amfani dasu kuma nan da kwana nawa gagarabadau ɗin yache zaiyi aiki akansu " eh munyi dashi akan zandawo nan da wata 2 chewar hajj sadiya " zaro ido aunty amarya tayi tana faɗin wata biyu kuma zata sake magana komai tatuna sai tache to shike nan ba damuwa,yanzu dai waɗan nan abubuwa yazanyi dasu  " tona rami zakiyi ki binnesu da hannunki chewar hajj sadiya " to shike nan gobe zanje ta bayan gidan nan na binnesu,sai maganar Safras da zulaihat chewar aunty amarya " eh shima sai bayan sallah dan yache aikin nada matukar wahala kuma gashi sallah yakawo kai jamaa sunmasa yawa sosai kowache tana kawo kukanta asa mijinta tafito da ita sallan nan ta haɗu sosai, " mikewa Aunty amarya tayi tana faɗin bari nakawomiki kuɗin motakoh tanufi wajen Waldrop din kayan'sawarta 

Misalin karfe 8 na dare gaba ɗaya family sun haɗu a palo suna chin abinchi kamar yadda suka saba " shiru kakeji bakajin karar komai sai karar spoon, bayan sungama chin abinchin ne " mai martaba yayi gyaran murya yasoma magana yau azumi saura kwana 33 yakamata kufara fitto da kayan abinchi kuna rabawa al umma san nan kuma gaba ɗayan mu zamuje umrah, saiku shirya, akoi mai magana " shiru palan yayi " diyana che tache Abba inasan da'sallah inje kauye ingano yaya bello " wani kallan banza yusuf  ya wurga mata akule yafara magana au yanzu duk azabar dakukasha sake tunanin kauyenma kuke ke nan " mai martaba yayi murmushi yana faɗin to kai ina ruwanka kasan tsakaninsu da bello'ne to barikaji zasuje kuma kuzaku kaisu kukulamin dasu har sudawo " afusache don yamike zaibar palan " sai ina chewar Ammi " shiru yayi baiyi maganaba kuma bai dawo ya zaunaba " mai martaba yayi murmushi yache to ki kyalesamana jeka abinka ammafa kashirya dan dakai zaku kaisu diyana kauye " batare dayache koh uppan ba yayi waje "  kallan Ammi mai martaba yayi chikin harchen fillanchi yake faɗin ki kyalesu inamusu hakane ko zansamu zuchiyar nan tasu taragu inba hakaba akoi matsala " jinjina kai Ammi tayi tana faɗin eh hakanma yana da kyau ai gara murinka koyamusu sanyi kobayawane " mikewa Aryan yayi yanufi waje har yakai bakin kofa saikuma yajuyo yana kallan diyana a nitse da sexy voice nashi nan yafara magana kisameni a ɗaki inzakizo kikawomin coffee yana kaiwa nan yawuche " gaba ɗaya palan mamakine yakamasu baranma yusuf suda sukasan hali, "nan take zahra jikinta yafara rawa ta kalli diyana tafara magana kasa kasa chikin harchen fillanchi wayache kiche zakije kauye to wlh yau babu ruwana dan zaki karɓi hukunchi " murguɗa baki diyana tai tamike tayi waje " baki sake zahra ke kallanta azuchiyarta take tunanin lallai diyana inaga darabon zakisha bugu kilama harda karaya,"
Da ɗai ɗai suka bar palan gaba ɗayansu kowa yanufi bangarensa


Zaune take a gaban murhun wuta tana kokarin hurawa innar buba tashigo gidan da sallama inna ta amsa mata sallamar,tamata iso zama innar buba tazo tayi kusa da inna suka gaisa " innar buba tafara tambayat inna wai har yanzu habiba baki samu kuɗin bane nifa wlh nafara karaya " aa karkikaraya dan kuwa nasamu natara dubu 5 yanzu kuma anjima zansake zuwa tallah kinga da kuɗin sun kai dubu 10 sai muje koh kiɗan kara hakuri kinji chewar inna " to badamuwa allah yakaimu nibari nazo nakoma gida dan mai dubawa buba kafarsa zaizo anjima chewar innan buba " inna habiba tache yajikin nashi " innar buba ta amsa da sauki sosai wlh dankuwa kafar tafara komawa dai dai " mashaa allah chewar inna " to  habiba sai kinshigo tafaɗi hakan tana kokarin mikewa, har kofar gida inna habiba ta rakata san nan ta dawo


 Pls more comments and share
*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

 💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai


*Episode 9*
         


Rike take da cup ɗin coffee datahaɗa masa tafiya take, itakanta batasan ina tanufaba dan bata san  part nashiba tazo dai dai,zata fita bangaren Ammi tachi karo da Fahad " baya taɗan koma kaɗan kana tache ina wuni yaya Fahad " bai amsaba kuma bai ko kalletaba yazo yawucheta " da sauri ta tache yaya Fahad dan allah inane bangaren yaya Aryan " banza yayi da ita yayi wuchewarsa chiki yabarta tsaye " tayi kwafa tana faɗin wlh dani kake zanyi maganin kane tajuya tachigaba da tafiya, sai sauri take kamar tasan inda zata 

kai tsaye palan mai martaba tanufa da sallam tashiga babu kowa awajen dan haka tanufi betroom kai tsaye  sallama tayi  a bakin kofar betroom ɗin tunba'a amsa sallamar kuma ba'abata izinin shigowaba tashige abunta " zaune tasamu Mai martaba da Ummi a kan gado suna hira " mamakine yakama Ummi " Mai martaba kam bai damuba dan yasan halin diyana sosai  " Ummi che tache diyana lfy kika shigowa mutane ɗaki babu sallama " turo baki diyana tayi tana faɗin dakin yaya Aryan nake nema, natambayi yaya Fahad yaki faɗamin " Ummi zatayi magana, mai martaba yarigata dachewa " idan kika fita nan kibi pangaren hannun damanki a nan part nasa yake " to ai kofa biyu'ne awajen wanene nashi chewar diyana " na biyun shine mashi mai martaba yabata amsa " to kawai tache san nan tafiche abunta " dawo da kallansa mai martaba yayi kan Ummi data sake baki take kallan ikon god " ya akayine mai martaba yatambayeta " hmmm su diyana manya mamakin tabani ne itakam ko ajikinta kawai tafaɗowa, mutane daki chewar Ummi " murmushi kawai mai martaba yayi kana ya girgiza kai

Tura kofar part ɗin tayi tashiga tana tafiya tana wakarta chikin harchen fullachi "  (fullo daru midarata fullo daru midarata) " har tashiga palan babu kowa, dan haka sai tanufi kofar datagani a chikin palo kai tsaye tashiga babu ko sallama " jin mutun yashigo yasashi ɗago kai yana kallanta tachikin mirrow, daure,yake da towel a kugunsa da alama wanka yafito,  gawani gashi mai tsantsi bakinkirin a kwanche akan faffadar kirjin'sa, damtsen hannunsan nan kamar zai fashe saboda karfi,tamkar wani zaki, ga gashin kansan nan kuwa ajike, yake da'alama ya wanke kanne, gashin kwanche yake har kafaɗarsa,  zuba mata wan nan  ash eyes ɗin nashi yayi "  sai waige waige  take da alama bata magansaba " shiru ta tsaya kamar mai sauraron wani abu" "zuba mata ido yayi sosai  yana kallanta " sanye take chikin doguwar riga abaya still dai kanta babu ɗan kwali," "juyawa tayi zata fita karaf idanta ya sauka chikin nashi ta chikin mirrow, tsabar tsorata,  wani kara tayi kana tayi wurgi da cup ɗin coffee dake hannunta ta watsa aguje zata nufi waje amma ina, taku biyu yayi ya tamki kugunta " saboda tsabar tsoro nunfashinta ɗaukewa yayi " sai dai kawai yaji tasake jiki zata faɗi  da sauri yariketa da kyau, 

Kallan fuskarta yayi yaga alamar kamar suma tayi, yasa hannu ɗaya ya ɗauke ta Chak sai kan makeken gadansa ya kwantar da ita " san nan yakoma gaban miro yachigaba da abun dayake, bayan yagamane 
yanufi dressing run nashi, saida ya dauki kusan 10 mnt kafin yafito sanye da kayan barchi a jikinsa doguwar wando da riga mai dogon hannu masu laushi farare tas " kai tsaye freij yanufa ya daukoh ruwa, yazo ya zauna a gefen gadan yabuɗe bakin rubar ruwar ya tarfa a hannunsa, ya shafa mata a' fuska " wani nauyayyar ajiyar zuchiya ta sauke haɗe da jan dogon numfashi, 
 batare da tabuɗe idoba tafara sambatu " don Allah kayi hakuri wlh bansan bakaya ajikinka bane nashigo kuma kaikache nazo dan allah karka bugeni " ke kimin shiru chewar Aryan  " da sauri ta buɗe ido tana kallan inda take, mikewa tayi da sauri ta saukoh daga gadan tanufi hanyar fita " kamar daga sama taji yana faɗin " inazakije konache kitafine? " Da sauri ta juyo tana in ina a'a " to zo nan ki zauna yayi maganar yana nuna mata kasan carpet ɗin  " da sauri takoma ta zauna " wayache kizubarmin da coffee " ɗago kai tayi tana kallansa taga bama ita yake kalloba wayarsa yake latsawa " kayi hakuri zankawo maka wani tabashi amsa " kinsan meyasa nakiraki " aa bansaniba " wlh wan nan shine last worming na karshe da zanmiki idan kikasake yimana maganar wan nan shegen kauyen a gidan nan saina babballaki kinajina " murya na rawa diyana tache eh naji " 

kuma inasan kibuɗe kunne ki saurareni idan kika bari nasake ganinki babu ɗan kwali saina aske gashin nan gaba ɗaya " da sauri diyana tache yauwa yaya dan allah ka askemin inka iya wlh banaso daman  " mamakine yakama Aryan tunani yashigayi idanfa yabiyewa yarinyar nan to tabbas zaiya babballata " dan haka sai yache ke yanzu kitashi kije kikawomin wani cofee ɗin san nan kuma kullum dasafe karfe 7 dai dai kikawomin coffee haka da daddarema karfe 9 dai dai shima inabutar coffee idan kika kuskura kika wuche time dana baki,sai jikinki yafaɗa miki kuma banche wani yahaɗa , coffee ɗin ba kezaki rinƙa hadawa kinaji, tashi kije kikawomin wani yanzun nan yayi maganar a kausashe " da sauri tamike tanufi kofar fita har takai bakin kofa kuma saita juyo tana faɗin yaya Aryan to yabatun askin zaka askemin gashin " wani mugun kallo ya wurga mata waddayasata fita a' aguje " 

gyara konchiyarsa yayi a kan gadan yana kokarin ɗaukar wayarsa saiyaji kira tashigo, saida wayar takusa katsewa tukun nan yayi picking call ɗin " hello akache daga ɗayan bangaren " ykk hisham chewar Aryan " lfy y gd, wai meyasa innakiraku Aryan baku san daukar call na  chewar hisham  "  Aryan yache au kakirane ka tambaya, to ra'ayi yanzuma kayi sa'a ne dan inachikin farinchiki badan hakaba bazan daukaba " haka zakachemin koh Aryan to waima menamukune "  kara daure fuska Aryan yayi kamar hisham na kallansa yache kaga hisham mufa duk wanda yahaɗa hanya da mace to bamatare, dashi dan yazama mai rauni, mukuma bamasan mai rauni kusa damu " wani mahaukachin dariya hisham ya kwashe dashi yana faɗin inshaa allah Aryan kaine mutun na farkoh a chikinku dazai fara faɗawa soyayya kuma inshaa allah yadda kuka wahalar da soyayya itama saita wahalar,daku, wahalarma ba.. "Aryan baijira hisham yakare jawabansaba yakatse kiran yayi wurgi dawayar gefe " dai dai lokachin diyana ta dawo hannunta ɗauke da cup ɗin coffee bakinta dauke da sallama " wani mugun kallo ya wurga mata a kausashe yache get out " da sauri tajuya dan yadda taga fuskarsan nan kamar wani zaki "  kichin tanufa ta ajiye coffee ɗin a kan table san nan tafito kai tsaye sashen Ammi tanufa abunta ,

Tana shiga tayi ɗakinsu tasamu su zahra har sunyi barchi hayewa saman gadan itama tayi ta kwanta abunta bajimawa barchi ya dauketa

Washe gari misalin karfe 7 sungama shirinsu chikin uniform naso sunyi kyau sosai abunsu 
Diyana sarkin aiki dachikawa bata daure gashin gantaba tasa hijabi, wutsiyar gashin yalekoh  sosai saboda gashin,yafi hijabin,tsawo

Kai tsaye palan mai martaba suka nufa dan yin breakfast da sallama suka shiga " kowa nagidan yana zaune kan table suna breakfast " mai martaba dakansa ya amsa musu sallamar yana faɗin wow yan matana kunyi kyau gaskiya " Ummi da Ammi ma sai murmushi suke suna yaba kyansu auntu amarya ko sai harararsu take  " yusuf kuwa chewa yayi kai sweet sis yanzunema asalin kamanninki da don kekara bayyana " asukane don ya ɗago kai yana kallan yusuf " yusuf baimasan yanayiba saima karachewa yayi ammafa kinfi don kyau gaskiya, domin kuwa blue eyes yafi green eyes kyau " 

a,fusache don yamike yayi yana faɗin zama danake inachin abinchi,dakuma yafara kawo raini, kana yadawo da kallansa kan Ummi yana faɗin daga yau arinka kaimin, abinchi na bangarena, dagahaka yayi waje " murmushi kawai Mai martaba keyi yana girgiza'kai kana yadubi su diyana dake tsaye, to tsayuwar me kuke kuzo kuzauna kuchi abinchi kutafi karkuyi latti " wuchewa sukayi suka zauna kan kujerun table din " bintu sufara sarving nasu, nantake sukafara chin abinchin " 

ke banache karfe 7 dai dai kirinka kawomin coffee ba yayi maganar kansa na duke yana danna waya kamar bashike maganarba " chikin sanyayyiyar murya diyana, tafara magana, kayi hakuri yaya Aryan wlh nayi tunanin kafasane dan naga jiya kache nafita maka a ɗaki " mai martaba dai baki buɗe yake kallan wan nan ikon allah, Ammi da Ummi ma ba abarsu a'bayaba kowa na falon, mamakine yakamasa "  Aunty amarya kuwa bakinchikine kamar zai kasheta tanasan magana tana tsoron mai martaba " Khalid kam sai murmushi yake abuns,  " basu gama mamakinba sukajiyo , .  muryansa yana faɗin to kitashi kikawomin yanzu " bamusu tamike tanufi hanyar fita " shikuma yadago kai kome zai kalla karaf suka haɗa ido da yusuf daya buga tagumi ya tsaresa da ido " harara ya watsawa yusuf kafin nan yamike shima yafiche daga palan " wani mugun dariya yusuf ya kwashe dashi yana tafa hannu " Aryan najiyo dariyar Yusuf amma bai tsayaba kuma bakaramin haushi hakan tabashiba haryasa yajima yatsani coffee ɗin, baima san sake kallan yarinyar " 

Aiman ne yamike yabi bayan Aryan ɗin  batare dayache komaiba " Ahmad naganin Aiman yamike yafita shima yabi bayansa " Khalid kuwa kallan yusuf yayi kasa kasa yache baka kyautaba kuma ina da magana dakai anjima kasameni a daki " to kawai yusuf ya amsa dashi " mikewa Khalid ma yayi yafita daga palan"

Dawo da kallansa kansu hiyana Yusuf yayi yana faɗin kuyi saurifa time na tafiya yau nizanma kaiku da kaina " tsabar mamaki zahra batama san lokachin da tache wai anya yaya yusuf ne wan nan kuwa " sai dataga yana wurga mata mugun kallo tukun nan ta dawo kan hanya " a'gurguje suke chin abinchin dan kar time yakure " suna gama chin abin suka mike yusuf yace muje koh san nan yayi gaba, sukabi bayansa 

Su hiyana na fita mai martaba yadubi su  haidar yache kubamu waje zamuyi magana " da sauri suka mike sukayi waje,  palan ya rage daga Aunty amarya Ammi dakuma Ummi sai mai martaba " 
calmly mai martaba yafara magana alhadulillah alhadulillah wan nan rana nake jira arayuwata a'che yau Aryan da Safra da Aiman, naga sunfara yiwa wata yamace magana to yau burina yafara chika, nasan yusuf Ahmad Khalid su masu saukin kaine, to maganar danakesan nayi ana shine kar wanda ya kuskura a chikinku yayiwa yaran nan, wata magana dan da alama addua ta a kan Aryan tafara karɓuwa , " Ammi tache ranka yadaɗe ban fahimche kaba " zaki fahimta amma bayanzuba mai martaba yabata amsa " mikewa aunty amarya tayi a fusache tabar palan " binta da ido kawai mai martaba yayi achikin zuchiyarsa kuma yana faɗin nasan zaayi hakan ai amma sai dai kinmakara dankuwa baki isa kihana abun da allah yahukunta ba, a'fili kuwa chewa yayi zaku iya tafiya " mikewa Ammi da Ummi sukayi suka nufi waje.

Da sallama diyana tashiga palan nashi baya nan kai tsaye chikin betroom din tawuche "da sallama tashiga "  zaune yake kan kujera yana aikin chikin laptop " gabansa tazo ta duka kana tache gashi nan yaya Aryan " a'fusache yache bana bukata " mikewa tayi tafita da coffee ɗin a hannunta ta maida kichin abinta,san nan tafito tanufi harabar gidan, tsaye tasamu su hiyana suna jiranta tana zuwa suka shiga mota kamar yadda suka saba, da gudun gaske motochin suka fito daga gidan, dan yusuf ne yache suyi gudu sosai su diyana zasuyi latti,
 
Karfe 10 na'safe

Zaune suke suna fuskantar juna akan sofa Khalid ne yafara magana gaskiya yusuf baka kyautaba meyasa zakayiwa Aryan dariya haka kasanfa abun da muke buri ke nan muga Aryan da don yau sunkula wata ya mace,kuma kafi kowa sanin halinsufa, yanzu dariyar nan daka masa zai iyasawa wlh yakoma ruwa munfara farinchikin yafara dawowa kanhanya,  kana'neman rusamana farinchikin, kuma gashi niɗin nan tun ranar da aka haifi Zahra nake mahaukachin santa amma na bar abun araina saboda'su don dan bansan wata matsala a tsakaninmu Aunty farida kawai na iya faɗawa yanzu ganin abun daya faru a palo ɗazun haryasa nafara ganina a matsayin angon zahra gashi yanzu kanane'man karusamin hakan gaskiya baka kyautaba wlh " 
dogon nunfashi yusuf yaja san nan yache hakane yaya Khalid nasan nayi kuskure dankuwa nikaina burina naga sun chanza amma wlh abunne yabani dariya yanason abu, amma yana wani chicchijewa yananuna halin ko inkula " 
Khalid yache yanzufa Aryan bazai taɓa fahimtar yanasan yarinyarba saboda shi baisan soyayyaba kuma inbanda aunty farida da iyayenmu mata kasan ba wata macen dayake magana da ita Koh,   koh zahra datake kanwarmu bamaga da ita yake ba tunda kaga yayiwa yarinyar nan magana har yache takawo masa abu yachi wlh ba banzaba yana mahaukachin santa amma bazai gane hakanba yanzu ,  tunaninsa bazata taba bashi yana santaba kuma karkayi kuskure faɗa masa yana santama, kabari zuchiyarsa zata faɗamasa, dan inkache zaka faɗa masama hakan zaisa yadaina yiwa yarinyar magana, yakuma tsaneta ka kyalesa kawai "
" murmushi Yusuf yayi kana yache tabbas zan haɗa masa tarko kuwa wanda zaisa yafaɗa son ta gadan gadan batare daya saniba " hannu Khalid yamikawa Yusuf yana faɗin good idea idan kana bukatar taimakoh na a shirye nake " darisukayi gaba ɗayansu suka tafa hannu  san nan yusuf yamike yana faɗin saikajini zanzo na faɗamaka plant ɗin idan nagama shiryawa " to kawai Khalid yache" sannan Yusuf yafiche daga ɗakin.


Kuka take sosai kamar wata karamar yarinya tana waya " wai inba gagarabadau ba bakisan wani malami bane kitausayamin sadiya wlh suna shirin kasheni idan Aryan yafara son yarinyar nan wlh yakasheni nashiga uku " hajj sadiya tace kidaina faɗin hakan kiyi hakuri nan da 2 month ɗin kinji koma yafara sonta idan akamata aiki dole zai tsaneta karki damu pls kidaina kukan haka, toma wayache maki yana sonta " sadiya inasan kisan wani abu  Aryan fa ko Zahra datake kanwarsa bai taba mata maganaba amma yayiwa yarinyar nan  magana kuma hardachewa tarinka kawomasa coffee kullum, " karki damu nidai dan allah kidaina kukan nan zamuyi maganin abun "  tsagaita kukan aunty amarya tayi kana tace shike nan sadiya badamuwa zanjira amma dan allah amusu aimi mai karfi dan yanzuma kara tsanarsu nayi wlh " karkidamu aminiyata kedai kizuba ido kawai chewar hajj sadiya " to shike nan aunty amarya tafaɗa tare da katse kiran ta jefa wayan a kan gado ta zauna tabuga uban tagumi siraran hawaye nabin kunchinta

Karfe 1 na rana

Suna zaune awajen chin abinchi na school nasu sungama chin abinchi rana " hiyana na karatun qur'ani, su zahra suna Assignment ɗin da akabasu ita da diyana  amrat kuwa tana zaune kusa da wata budurwa sai lamrat dake gefe tana rike da littafin Husnul Muslim tana karantawa " sunyi nisa chikin abun da suke saisukaji murya daga bayansu " a tsorache Zahra tajuya a'zuchiyarta  tana tunanin wai meyakawo jabir wajensu tana chikin tunani kwai sai taji yana faɗin " ke zahra,u yaushe a' kakawo wayan nan yan india wan kuma makarantar nan " Zahra sarkin tsoro murya na rawa tace sun kai 2 month " tsaki jabir yaja san nan yace, shine bakizo kinfaɗamin ba, amma gaskiya wanchan tamin itache sabuwar budurwata na wan nan shekarar yayi maganar yana nuna hiyana, " to kawai Zahra tace, " yasunanta jabir ya tambaya " sunanta hiyana chewar zahra " 

jinjina kai jabir yayi ya mai maita su nan hiyana san nan yace, hiyana tashi kizo muje muzagaye  makarantar nan domin kowa yaga sabuwar budurwata dan karwani yache yanasonki, dan duk wanda yayi kuskure chewa yana sanki tofa saidai uwarsa ta haifi wani " zaro ido hiyana tayi tana kallan jabir ba karya kyakkyawane sosai gashi dogo mai chikar halitta sai dai yayi kalar yan daba kuma kwata kwata bazaifi 22 years ba,"
Zahra ne tace, hiyana kitashi kuje " kallon zahra hiyana ke chike da mamakin abun da tache zatayi magana sai tajiyo " diyana nafadin kai waye dazakawani che tazo tabika to babu inda zataje iskanchin banzan nan " wani mahaukachin mari jabir ya sakarwa diyana san nan yace kishiga hankalinki wlh kinmachi albarkachi, naganku tare da gimbiya hiyana ne dabadan hakaba dakin karbi hukunchi kekuma yashi mutafi yayi maganar yana nuna hiyana " da sauri hiyana tamike jiki na rawa tanufeshi " juyawa yayi yayo gaba tabi bayansa 

Diyana kuwa sai kuka take tana faɗin allah ya isana waima Aunty zahra wanene wan nan " wata buduwa dake zaune kusa da amrat ne yace, sunansa jabir " ni ba sunansa nakesan jiba faria wanene shi nakesan sani chewar diyana " Faria tace shima a school ɗin nan yake yana ss 2 yana takama da mahaifinsa mai kuɗin ne kuma mahaifiyarsa kuma tana da yan daba mahaifiyar tasa baturiyar England che, bata da mutunchi shiyasa yake abun da yaga dama " to meyasa malamai basa masa hukunchi saiyarinka yin abun dayakeso a makaranta chewar diyana " faria tace makarantarma na mahaifinsane kuma duk abun dayake so shi iyayen nasa sukeso " shiru diyana tayi kamar bazata sake magana ba chan kuma tace wlh nine zan gyara masa zama " baki buɗe Zahra da faria ke kallan diyana tachigaba dachewa badai hiyana yakesoba wlh zaigane shayi ruwane  
Ita dai zahra aikin gabanta tachigaba dayi dan ta lura diyanafa ba hankali garetaba  

Hiyana bata dawoba har suka koma class " diyana tashiga damuwa sosai da sosai " sai karfe 2:50 hiyana ta dawo lokachima har anbuga belt ɗin tashi school " diyana naganinta tanufeta tarungumeta tana faɗin  ina kukaje " babu ko ina yawo kawai yayi tayi dani a chikin school ɗin chewar hiyana " tsaki diyana taja san nan tace to muje " jerawa sukayi tare suwa nufi inda da suke tsayuwa sujira mai ɗaukansu nan sukayita hirarsu  " har driver yazo ya daukesu kamar kullun motochi 2 kezuwa daukansu diyana hiyana da zahra mota ɗaya  lamray da amrat motarsu daban
Da gudun gaske motochin suka nufi gida dasu ,motochin na danno kai security su wangale musu katafaren gate ɗin kai tsaye parking space suka nufa suna parking drivers ɗin suka fito suka buɗe musu motar " suma suka fito suka rirrike hannun juna sukayi suka nufi bangaren Ammi

Suna shiga tun a palo diyana tafara chire hijabi tana faɗin alhadulillah yanzu zan rabu da hijabin nan haba " harararta hiyana tayi kana tace, kekam wlh watarana sai aljanu sunshiga kankin nan mutunne bata san dan'kwalin " kallon uku 10 diyana taiwa hiyanar san nan tace, to ina ruwanki ai aljanuma abokainane   Zahra zatayi magana sukaji an daka musu tsawa, get out  aguje sukayi ɗakinsu itakuma diyana saida tajuyo dan ganin wanene tana ganin don ne ta watsa da gudu itama dan, shikam batataba ganin alamar wasa a fuskarsaba ,



Pls more comments an share 👌

*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

 💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 11*
         



Mai martabane zaune a fada shida Aryan, Ahmad  Khalid da'kuma Yusuf a nitse mai martaba yafara magana " Aryan meyasa zaka mari diyana kanajin faɗan danayiwa safras fa ranan akan marin dayayiwa hiyana shine kaikuma kasake marin diyana koh wai bakuda tausayine nikam eh " calmly Aryan yasoma magana kayi hakuri Abba wlh tabatamin raine sosai shiyasa " nasani Aryan nasan halin diyana itakuma haka allah yayita hakuri zakurinkayi da ita ban hanaku kumusu faɗaba  amma kurinka ragewa kuma bai'kamata kuɗora hannunku a jikinsuba bakuganin yanayin'sune, yanzu kaje kadubi fuskar diyana da kyau kagani shattin yatsunkane kwanche akai to na'menene hakan gaskiya bansan hakan karna karaji kuma karna kara gani " inshaa allah Abba zan kiyaye chewar Aryan "  Khalid yace Abba yabatun zakkan nanfa " eh kuna barwa ai kukula da komai " Ahmad yamike yana faɗin aa Abba su yaya Khalid dai nikamma bari naje na dubo Aiman " harara Yusuf ya watsawa Ahmad yana faɗin zakasani ne ai dakai da Aiman ɗin gaba daya wlh munkusayin maganinku a gidan nan " Ahmad dai bai sake maganaba yafiche abunsa 

Aryan yace Abba yabatun komawarmu England ne " aikuda komawa kam to banacheba kabari ayi naɗin sarauta tukun nan sai inyi tunani akai chewar Abba " mikewa Aryan yayi yana faɗin to shike nan Abba allah ya kaimu san nan yafiche daga fadan " Khalid da Yusuf ma mikewa sukayi suka fito sunayiwa Abba sai anjima


Gabaɗaya family sun haɗu a palo dan chin abinchin dare amma banda don, dakuma yan matan Ammi subasu zoba , " mai marbata yace waishin ina yan'matana'ne mesukeyi basu fitoba, ko dai daga buɗa baki shike nan bazasuchi abinchin dareba" Ammi zatayi magana sai sukajiyo sallamar'su nanfa kallo yadawo kansu banda  Aryan da fahad kowa na palon kallansu yake, " 

diyana na sanye chikin dogon wando baki da rigansa zuwa guiwa pink colour still dai ba ɗan kwali a kanta ta zuba gashin nan har baya sai kwalli gashin yake nakinkirin dashi har tsakiyar bayanta, dan karamin bakin nan nata yasha janbaki pink ga blue eyes yasha kwalli ta gyara sagenta ga zarazaran gashim idanta, tasa high heel pink kalar rigarta

" hiyana ma dogon wando baki tasa sai riga sky blue zuwa guiwa ta ɗaure gashin Kanta,  tayishi kamar donut ta yafa gyalen kayan akanta paki kalan wando dan bakin nan nata yasha ret janbaki tayi kyau sosai kamar kasacheta  ga blue eyes yasha kwalli sai'yaƙara kyau sosai yana kyalli sajenta kwanche a gefen kumatun'ta  gashin geranta kamar tayi caving tasa flat shoe sky blue kalar rigar 

Zahra ma dogon wando baki tasa sai riga yellow tayafa gyalen kayan akanta shima bakine ɗan karamin bakin tan nan tasanya masa janbaki pink colour tayi kyau sosai itama daman zahra kama take da don sosai wan nan dalilinsaya suka zama kamar tagwaye da hiyana sai dai banbanchin kwayar ido dan zahra idanta bakine kamar nawa


Lamrat kuwa dogon riga baki tasa mai shegen kyau,
 Tasa flat shoe fari, tayi rolling ɗin karamin farin gyale a kanta Zahra tamata make up sosai kamar wata balarabiya tazama

Amrat kuwa dogon wanto fari dasa sai yar farar t-shirt navy blue itama batasa ɗan kwaliba amma zahra tamata pakin na gashin a tsakiyar kanta tazuba jelar gashin a' baya har tsakiyar bayanta booth navy blue tasa a kafarta 


 Yusuf ne yache wow my baby zo " gaba ɗaya kallo yadawo kan Yusuf, a' sukane  Aryan yaɗago yana kallan Yusuf ɗin shi ko ajikinsa kallan su diyana ma yake baisanma jama'a na kallansaba  " bin inda Yusuf ɗin ke kallo Aryan yayi " "Aryan kasa kawar da kannasa yayi daga kallanta ? 

Karisawa wajen table ɗin sukayi sukayi kowa tasamu waje ta zauna lamrat zata zauna kusa da Ammi " yusuf yache zo nan kizauna kusa dani my baby " bamusu lamrat takoma kusa dashi ta zauna " haidar da umar sai gulma suke kasa kasa " Ammi da Ummi kam ko ajikinsu abinchinsu kawai sukechi " Aunty amarya kuwa sai chika take tanata harararsu " ɗaukoh fura ki damamin hiyana chewar mai marbata " da sauri hiyana tamike tanufi kichin, kwarya ta ɗaukoh san nan ta daukoh fura, tanufi freig ta ɗauki ruba ɗaya na nono tajuya takoma palan mai martaba, da sallama tashigo palan ta dawo wajen zamanta ta zauna tafara dama furar 

Sai'hira suke jefi jefi mai marbata yache banso a che muntafi umrah nan mun barkuba amma makaranta basu baku hutuba  " Ammi ne tache sai suje hajji kawai kokuma subari sai wata shekarar " mai martaba zaiyi magana " Ummi tace Fahad tashi ka kaiwa yayanku abinchi " da sauri Fahad yamike yana faɗin ina abinchin " yana kichin Ummi tabashi amsa , " fichewa yayi daga palan

Bayan hiyana tagama dama furan tamikawa mai marbata " karɓa yayi yana murmushi kana yace duk gidan nan hiyanata tafi kowa iya dama fura " turo baki diyana tayi tana faɗin wlh nafita abun dama nina ko.... bata karisa maganaba sakamakon wani mugun kallan da Aryan yake wurga mata " shiru tayi

Mai martabane kuwa sai kallansu yake yana murmushi yana farinchikin burinsa yafara chika aishi haka yakeso kodama hararanne Aryan kewa diyana daɗi zaiji dan daga harara sai kallan mutunchi " Ammi che ta katse masa tunani dache ranka ya daɗe sai da safe " hararar wasa mai marbata ya wuga mata kana yace inada magana dake " to kawai Ammi tache " jin mai marbata yace. yana da magana da Ammi yasa kowa yatashi suka fiche 

Mai martaba yadubi Ammi yafara magana jiya Yusuf yasame damaganar akan Khalid da zahra, Khalid yafaɗawa Yusuf yanasan Zahra tun tana karama ina faɗamiki hakanne bawai dan kifaɗa mataba sai hakkinki a matsayin uwa da'kuma kisamata ido karkibari tawa Khalid kishiya, danni tun da Yusuf yafaɗamin nariga nabawa Khalid auren ta, kokina da wani abun faɗe " ajiyar zuchiya Ammi tayi san nan tace, nikaina inakaunar Khalid nina renesa a hannuna yagirma babu halinsa da bansaniba bawani abun da zanche saidai inmusu fatan alkhairi kawai " to masha allah Amma fa kinsan yau a ɗakin'ki nake amma kikechemin sai da safe koh " murmushi Ammi tayi tana tace tubanake wlh nagajine a'zumin yau ɗin nan ya wahalar dani " haryanzu dai lallanchinki bai raguba Aisha, to muje chiki namiki tausar koh " mikewa Ammi tayi tana faɗin mujedai ninamaka " dariya mai martaba yayi san nan yamike yabi bayanta sukayi chikin betroom

Karfe 10 na dare

Rike take da cup ɗin coffee tanufi bangaren Aryan jikinta sanye da kayan barchi riga da dogon wando pink colour still dai kanta babu ɗan kwali tafiya take tana kunkuni" ni wlh barchi nakeji nagaji saikayitaba mutun wahala dan mugunta " da sallam tashigo palan baya palo kai tsaye ta wuche betroom ɗin " kwanche yake akan makekiyar gadansa yana latsawaya jin shigowarta yasa ya ɗago kai yana kallanta " sai turo baki take tana magana kasa kasa " from head to toe ya karemata kallo san nan ya ɗauke kansa da sauri " karisa shigowa chikin ɗakin tayi tazo gaban gadan ta duka san nan tace. Ina wuni yaya Aryan " shiru yayi bai amsaba kuma bai motsaba " itama shiru ta zauna har kusan 15 mnt, san nan tache yaya Aryan dan allah ka karɓi coffee ɗin mana wlh nagaji " banzah Aryan yayi da ita kamar baiji metake faɗe ba shiru shiru baiyi maganaba ganin bai daniyar magana yasata tamike, tanufi indayake wai dan taga yayi barchine 
Aji cup ɗin coffee ɗin tayi akan dan karamin table ɗin dake tsakiyar ɗakin san nan tanufi kan gado  hawa gadan tayi taga idansa a lunshe , ta turo baki tana faɗin shine dan mugunta kabarni ina duke kan guiwowina har kafata namin zafi kaikuma kayi barchinka koh, to banyafe... Bata karisa maganarba taga ya waro manya manya ash eyes ɗin nan nashi akan fuskarta " a'sukwane ta juya tana kokarin sauka gadan wani damka yayiwa gashin kanta wandayasa tadawo baya tafaɗa kan kirjinsa " kware baki tayi zatayi ihu yasa hannu yarufe mata baki " kasa kasa yace kina buɗemin baki ina harbinki da bindiga meya hauwar dake gadona yayi maganar tare da chire hannunsa daga bakinta "  murya na rawa tace dan allah yaya aryan kayi hakuri kasakemin gashina wlh zafi yakemin " banche karna sake ganinki ba ɗankwali ba eh " kayi hakuri zanrinka sawa chewar diyana tayi maganar chikin muryar kuka " harchikin ransa yaji voice nata na karshe kayi hakuri zanrinka sawa a hankali yazame hannunsa daga kannata, yana faɗin to tashinmin ajiki " da sauri tamike tana faɗin to ga coffee ɗin " mikewa yayi shima kana yace bazanshaba ki mayar kije kisa ɗankwali saiki kawomin " a shagwabe tace ayya dan allah kayi hakuri kasha allah gobe zan daura dan kwalin kafin nakawoma wlh yanzu nagaji kuma barchi nakeji " kallanta yayi from head to toe san nan yache nikam, kekam kinada hankali kuwa kinsan chiwon kanki kuwa " turo baki diyana tayi tana faɗin mekuma nasakeyi " wlh azim idan kikasake fitowa a haka batare da hijabi ko kayan arziki ajikinkiba allah zakiyabawa aya zakinta " binjikinta tayi da kallo achikin zuchiyarta tana tunanin to me laifin kayan nan tayi nisa chikin tunani taji ya daka mata tsawa "  wai badake nake magana bane nache kifitamin a ɗaki koh, da sauri tajuya tabar ɗakin binta yayi da kallo har tafita
san nan yamike yanufi inda ta ajiye coffee ɗin  ya ɗauko cup ɗin yadawo gefen gadansa ya zauna yafara sha,

Bangaren diyana kuwa tana fita bangaren Aryan kai tsaye part nasu tanufa da sallama tashigo palan, da sauri taja burki tana faɗin ya yaya Yusuf kaima bakayi barchiba " murmushi yusuf yayi yana faɗin eh ina hira da baby's nawane suna koyamin fillanchi " karisawa indasuke diyana tayi tana faɗin kema amrat hardake yau bakiyi barchiba sai kije school kiyita barchi a class koh " lamrat tace ainikam ma yanzu zanje na kwanta " zama diyana tayi kusa da Yusuf zatayi magana " Yusuf yace kuje ku kwanta dare yayi kunsan akoi tashin asuba ga zuwa school yayi maganar yana mikewa yanufi hanyar fita " suma mikewa sukayi suka wuche ɗaki


Karfe 4 dai dai na asuba gaba ɗayansu sun haɗu a palon mai martaba danyin sahur amma banda don abinchi sukechi chikin kwanchiyar hankali " Ammi tache hiyana da Zahra kuchi abinchin nan dawuri ku'ɗauki na yayanku ku kaimasa zahra najin Ammi tache sukaiwa don abinchi tafasa kara sai da kowa na palan yaɗago yana kallanta " lfy auta ta chewar Abba " Zahra dai taki magana sai kukanta kawai take " hiyana kam datariga da tasan me Zahra takewa kuka ko kallanta batayiba, su Ammi sunyi tambayar duniyar nan amma Zahra taki magana sai kuka take " Aryan ne ya daka mata tsawa zakimana shirune kosaina babballaki a nan " tsit tayi kamar ruwa yachita "
 Aunty amarya ne tamike tana faɗin kai umar kaje ka dauki abinchin yayan naku ka kaimasa kuma daga yau kai zaka rinƙa kai masa abinchi tana kaiwa nan tafiche tana tunanin aranta  ai bazan taɓa barin yaran nan surinƙa kusantar samarin gidan nanba daga yau har ranar da gagarabadau zai musu aiki ido zan samusu sosai da sosai ɗakinta tawuche ta haye gado babu ko sallah takama barchi

Bangaren"su hiyana kuwa sunajin Aunty amarya tace umar yakai abinchin yayansu nantake suka fara murna sukamike a tare suna faɗin barimuje muyi sallah " Ammi ta kalli hiyana chikin harchen fillanchi tace wani sallah kuma badai kina period ɗin kike sallah ba " shiru hiyana tayi dan ita batama san idan a na period baa sallah ba " ganin tayi shiru yasa Ammi ta dubi zahra tace kije ki koyamata abun daya dace tayi " to kawai zahra ta amsa dashi san nan suka fiche

Mikewa Yusuf yayi yana faɗin gaskiya lokachi yayi dazan koyi fullanchi nima haba yanagama faɗin haka yayi waje " Khalid ma yace tab aiko nima dole naje Zahra ta koyamin irin wan nan wariya daake nunamana kana yamike shima yayi waje " dogon tsaki aiman yaja san nan yamike yafiche " shidai Aryan zaune yake ahiru yana latsawaya har saida yafarajin kiraye kirayen sallah yamike yanufi bangarensa " Ammi da Ummi ma suka fiche sukayi nasu bangaren danyin sallah " palan yarage fahad haidar da Abba " Abba yace wai kunyi arwala'ne kunfasan su safras sunafitowa zamuwuche masallahchi " mikewa haidar yayi yana faɗin aa baridai naje nayi " fahad ko chewa yayi nikam nayi Abba" ok kawai mai martaba ya amsa dashi 
Shiru suka zauna har sauran matasan suka fito sukajera zuwa masallachi 


Aɓan garen inna kuwa da sallama tashiga gidan su buba zaune tasameshi a tsakar gida " buba na ganin inna yafara murmushi yana faɗin inna jamɓandu( inna ina wuni) " lfy buba ya kafar taka " da sauki inna" inna tache to allah yakara lfy ina innarka take " tana garke tanabawa shanu ruwa da abinchi buba yabata amsa " to barina dubota bata jira amsar buba tayi gaba abunta " a garken shanun ta iskoh innar buba da sauri inna ta karisa wajenta tana faɗin albishir rinki yar uwa rabinjiki " ɗago kai innar buba tayi tafara murmushi tana faɗin goro " to kifito muje yau kuɗin sunchika dubu goma dai dai  chewar inna " da sauri innar buba ta ajiye sandar hannunta datake juyawa shanu ruwan gishiri tafito daga garken tana murmushi jerawa sukayi suka koma chikin gida innar buba ta ɗaukoh mayafi suka fiche

Wani ƙungurmin daji suka shiga tafiya suke har suka isawajen wani dutse ga hayaki nafitowa daga chikin kogon dutsen chikin kogon sukashiga " wani kasurgumin bakin bokane awajen ga idon san nan jajawur duk yabi ya huhhuda hanchi yasa wasu karafuna gawani katan karfe mai raun dayasa a kunnensa bashida kyan gani ko kaɗan 
Zama su inna sukayi kusa dashi " zasu fara magana ke nan yayi wani mahaukachin dariya ha, ha, ha, da murya masa daɗin Ji yace aikin ku bazaiyuwu a chikin azumiba saboda duk an ɗaure mana mutanenmu amma kuje sai bayan sallah kudawo ha ha ha yana gama faɗan haka ya ɓache ɓat " da sauri su inna suka mike suka fito inna tace to yanzu barinaje na ajiye kuɗin sai bayan sallah mudawo da haka suka kuche gida.

Kamar kullum yauma zaune suke a wajen chin abinchinsu na makaranta karatu boko hiyana take yaukam tun da bata da tsarki " zahra da diyana da faria kuwa hirar wani film suke waishi love story English movie 
Lamrat da amrat suna rubutu a takardunsu "
Kamar daga sama sukajiyo muryan jabir yana faɗin ke hiyana zo mutafi " ɗogo kai hiyana tayi a nitse tafara magana kayi hakuri jabir wlh yau banida lfy ne chikina namin chiwo " to yakikesan nayi ke nan ga abokaina chan kowa budurwarsa tazo ni bandani ke nan ba zaiyiwuba i don't care koma meke damunki, nidai kitashi mutafi " kamar hiyana zatayi kuka haka tamike tanufeshi tana faɗin muje " kallan uku 10 diyana tawa jabir kasa kasa tache mugu wlh sainayi maganinka  " kallanta zahra tayi san nan taja guntun tsaki  " jabir tunda yakira hiyana suka tafi basu dawoba har saida a katashi nanma saida diyana da zahra sukaje wajen dayake zama da abokan nasa sukache hiyana tazo sutafi mai ɗaukansu yazo " jabir dayaji haka sai yache to taje zasu haɗu gobe " jerawa sukayi suka nufi wajen da suke tsayuwa sujira motochin dake ɗaukansu  "

 suna tsaye awajen sukaji magana daga bayansu " gaba ɗayansu suka juya " hiyana tace uncle Omar ina wuni " da faraa a fuskanshi ya amsa san nan su Zahra suka gaidashi zaisake magana saiyaga motochin ɗaukansu yazo nanfa yamusu sallama yawuche " sukuma suka shiga mota kamar yadda sukasaba hiyana Zahra diyana motarau ɗaya " amrat da lamrat suma motarau ɗaya  "  da gudun gaske motochin sukabar bakarantar" gudu suke sosai suna kan hanyane" zahra tace kinsanme hiyana " girgiza'kai hiyana tai alamar aa " uncle Omar fa wai san diyana yake chewar zahra " kan uban chan niyakeso lallai kuwa yana ruwa wlh dannikam inba sojaba bazanyi aureba " baki buɗe hiyana ke kallan diyana " Zahra kuwa chewa tayi meyasa kikesan soja sojojifa mugayene " eh ae a chikin sojanma mugun nakeso wanda zaiyimin maganin yaya Aryan kuma wanda yake da bindiga shima " zahra tace to me yaya Aryan ɗin yayimaki haka dakike neman mugun soja yayi maki maganinsa " to bashine kullun inna masa laifi saiyache zai ɗaukoh bindiga ya harbeni namutu kowa yahutaba " aikuwa hiyana bata san sanda takwashe da dariyaba tana faɗin kai amma kuwa da yaya Aryan ya kyauta wlh " Zahra kuwa chewa tayi dalla rabu da hiyana kinji faɗamin muguntar me yake miki " bayan harbeni dayake chewa zaiyi saikuma jamin gashi da takuramin nasa ɗakwali dakuma kawo coffee kullun tayi maganar dai dai lokachin da motochinsu ke parking a parking space na chikin gida  
Fitowa sukayi suka nufi chikin gida rike da hannun juna


Misalin karfe 4 na yamma gaba ɗaya yanmatan zaune suke a palon Ammi suna kallo hiyana kuma tana karawa lamrat karatun qur'ani gaba ɗayansu shiga iri ɗaya sukayi duguwar riga abaya dukkansu colour ɗaya baki  " Ammi ma nazaune a gefe tana gyarawa amrat jigidarta da Aunty farida ta saya musu to ya matseta sosai " da sallama Khalid da yusuf suka shigo palan " da gudu Zahra ta mike ta nufi Khalid,faɗawa kan kirjinsa tayi ta rungumesa sosai tana faɗin oyoyo yaya Khalid " Yusuf ne yace my baby kema kizo kimin oyoyo mana " da gudu lamrat ta mike tanufeshi hannu ya buɗe masa tafaɗa kirjinsa yana murmushi " Ammi data tuno abun da mai martaba yafaɗa mata nachewar Khalid na san Zahra yasa da sauri tace ke zahra'u wai yaushe zaki girmane wlh idankika sake wan nan oyoyo zaki chi gidanku " turo baki zahra tayi " Khalid yasa hannu ya ɗan bugi bakin kana yace to wa'ake turowa bakin hannunta yarikoh suka koma kan kujera mai zaman mutun biyu 

Yusuf ma rikoh hannun lamrat yayi suka koma kan doguwar sofan suka zauna " hannu Yusuf yasa yana shafa kan lamrat yana faɗin my baby gashinkin nan kyau yakemin sosaifa " baki buɗe Khalid ke kallan Yusuf, azuchiyarsa kuwa chewa yake amma Yusuf iskanchinka yawuche tunani anya kaima baka kamu da san yarinyar nanba kuwa " afili kuwa chewa yayi ai gashin Zahra yafi nakowa kyau " harara Yusuf ya wurga masa san nan yace yauwa Ammi nikam inasan intambayeki kullum mantawa nake " Ammi tace. Tanbayi inajinka " wai aina mukasamu kalolin idon mun nan ne pls " Ammi tace au kache tarihi kakeson ji to gyra zama " murmushi kawai yusuf yayi yazubawa Ammi ido

Kakanku wato mahaifiyar mai martaba itache asalin wanda takawowa family mu kalan idan nan kakanku namiji babban likitane aiki yakaishi Us, a chan yaje ya auro kakarku ta mace baturiyar Us, amma musulmache sunanta sarah to sarah itache mai ido light green irin naka kaida yayanku " sarah kuwa mahaifiyar ta idonta ash ne mahaifintane mai light green ɗin ido shiyasa gaba ɗaya yayan sarah suka zama masu ido 2 colour wasu ash wasu green gashi abunkuma yabisu har kanku jikokinta, " Khalid yace no wonder, shiyasa muke da kyau kamar yayan larabawa ashe ashe " dariya Ammi tayi tana faɗin abun harda yabon kai " Khalid zaiyi magana yusuf yache to ammi su hiyana fa ya akayi suka samu blue eyes

Ammi tace sukuma sungadone daga wajen kakanmu namiji kuma duk family mu ma sukaɗai sukayi saar samun blue eyes ɗin kakanmu namiji shi ɗan asalin kasar sudanne yazo nageria, a garin jimeta yola, yahadu da kakamu mace yana santa sosai iyayenta sukache bazasu bashi itaba, sai dai idan zai zauna a rugarasu haka yayarda ya auri kakanmu kuma suka zauna a ruga harsuka haifi babana, da kanwarsa ɗaya allah yayiwa kakanmu rasuwa, kakanmu mace kuwa babana yayi auri umma'ta Kuma duk a'ruga ɗaya suke kuma a chan suka zauna an haifenima bajimawa kakanmu tarasu itama, kanwar babana kuwa bayan an haifi kanina Ahmadu babansu hiyana ke nan itama tarasu daga nan babanmu ya ƙaura daga rugar chikin yola yakoma rugar jimeta, a nan mukachigaba da rayuwa 
Rayuwar farinchiki muke sosai kanina da babana suje kiwo nikuma naje tallar nono a wajen tallar nono na haɗu da Mai martaba yabini  har gida, da kyar babana yabasa aurena to na bayan aure ba jimawa innata tarasu,  yarage saura baba da Ahmadu haka mukachi gaba da rayuwa bayardda mai martaba baiyi dasuba akan sudawo nan kano sunki har gida yasaya musu Amma sunki wai babu inda zasuje da waɗan nan uban shanaye babanmu yana da shanu dayawa kusan 700 ga awaki da raguna kaji da zabbi hakadai sukachigaba da zama a ruga
Kolokachin dana haifi yayanku sunki zuwa mota mai martaba yatura a ɗauko su amma sunki zuwa, babana ko yaki zuwane saboda niche yar fari Ahmadu kuma yaki zuwane saboda shine mai zuwa kiwon dabbobinmu kai intakaichemuku har babanmu yarasu Ahmadu yayi aure basu taba zuwa wajena ba saidai ninaje 
Nidinma kunsan yanayin gidan nan sainafi shekara uku banjeba nanma saina matsa da kyar mai marbata yake barina, akoi lokachin dana ɗauki tsawon shekara 6 banje naduba Ahmadu ba a shakara ta 7 ɗinne nayita rokar mai martaba da kyar ya'yarda yabarni naje"
Danajene masamu fati matar Ahmadu ta haifi ƴaƴa har uku hiyana diyana dakuma lamrat san nan ga chikin na hudu ajikinta nasha mamaki sosai shine nachewa Ahmadu tunda yanzu bamuda iyaye yadawo kano kusa dani yaki yarda, wai inyadawo yazaiyi da dabbobinsa, nachemasa musayar yaki yarda wai bazai bar garin iyaye da kakanniba haka na hakura na kyalesa nasaya' waya nabashi amma yaki karɓa wai baiso bayadda na iya haka nadawo na kyalesa 
Sai danasake ɗaukan shekara 4 kafin nasake komawa kauye alokachin danaje nasamu mamansu hiyana tarasu wajen aihuwar amrat Ahmadu kuma ya auri habiba dan tachigaba da kulamasa da yara alokachinma saidana roki Ahmadu daya dawo kano amma yaki narokesa yabani hiyana da diyana nanma yaki ninasan halinsa da kafiya shine na kyalesa kuma tundaga wan nan lokachin dana dawo bansake zuwa kauyeba sai zuwan nan danayi na samu Ahmadu yarasu na daukoh su hiyana " dogon numfashi yusuf yaja san nan yace. Tab lallai Ammi kina da hakuri sosai wlh allah dai yajikansu da rahma " gaba ɗaya palon suka amsa da amin  " duba time yusuf yayi san nan yace.  da Khalid muje koh mangariba ta kawo kai " mikewa sukayi a tare yusuf narike da hannun lamrat sukayi wajen " Ammi tace'wa su hiyana kutashi kuje kufara shirye shiryen kayan buɗa baki tare suma sukamike suka nufi palon kasa" Ammi ma tamike tayi ɗakinta 


Misalin karfe 7 na dare gaba ɗaya family suna palo dan yin buɗa baki amma banda don  abinchi sukechi chikin kwanchiyar hankali shiru ba mai magana saidai karan spoon " diyana tace. Abba kasan me " sai dakowa yaɗago yana kallanta da mamaki " mai martaba kuwa chewa yayi aa diyana ta bansaniba sai kinfaɗa " dariya diyana tayi tace wai uncle Omar na makarantar mune yace yana sona " what chewar mai marbata  " a'sukwane Aryan yaɗago manya manyan idan nan nanshi yana kallanta a jafafe yabuɗe baki.....✍️✍️



Amin afuwa masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kaimu more love



Pls more comments an share

 
*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*



            

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai




*Episode 12*


A zafafe Aryan yace ke kima mutane shiru a nan "idon kowa na palon yadawo kan Aryan ya turnuke fuskar nan tamkar an aiko masa da sakon mutuwa " Yusuf da Khalid kuwa sai murnushi suke "Abba ya dube'sa kana yace "ina ruwan ka,  kai takewa hirane,  chigaba da faɗamin ƴata ya kukayi kasanima ko dashi zaayi bikin " Aryan zai sake magana idonsa yasauka kan aunty amarya dake wurga masa mugun kallo ganin hakan yasa yamike yabar palan 

.....dariya diyana tayi san nan tace "Abba nifa matar sojane soja zan aura irin mugayen sojojin nan masu manya manya bindiga " Ammi ganin diyana tafara sakin layi yasa tamata magana da harchen fullanchi tache tatashi suje suyi sallar mangariba " ba musu suka miƙe suka nufi ɗakin su  " Aunty amarya mikewa tayi tafiche sai huchi take " mai martaba yace dasu Yusuf kutashi mutafi masallachi mikewa sukayi gaba ɗaya matasan suka fiche " Ammi ta dubi Ummi tace yakamata muma muje muyi sallah Koh, atare suka mike suka fita

Misalin karfe 8 na dare gaba ɗayansu sunhadu a palo dan chin abinchin dare amma banda DON da kuma Aryan basuzoba " yusuf ne yakalli diyana yace sister jiki dubo yaya Aryan a daki kiche yazo muchi abinchi " to diyana tace tare da mikewa zata fita " kamar daga sama sukaji Aunty amarya tana faɗin ke dawo kizauna Umar tashi kaje ka kirashi " kallo mai martaba yusuf yayi kana yajuya ya kalli Khalid zaiyi magana ke nan Abba yarigasa da chewa "jeki kirasa diyana da sauri ta fita daga palon dan ganin mugun kallon da Aunty amarya ke mata " farinchikine ya lulluɓe Khalid da Yusuf sai murnushi suke

Da sallama tashiga palon babu kowa kai tsaye tawuche betroom batayi sallama tashige kwanche yake a kan gado idansa a lunshe har bakin gadon taje ta duƙa a nitse tace yaya Aryan shiru bai amsaba dataji shiru sai tamike ta zauna a gefen gadon tasa hannu tana bubbuga hannunsa tana kiran su nansa, shiru shiru bai amsaba baikumayi motsiba  ganin hakan yasa,  tasa hannunta tana kokarin buɗe idon'sa dakarfi  " a zafafe ya damki hannun nata batare daya buɗe idon ba " aruɗe take kokarin kwache hannunta dan tagudu " slowly ya ware manya manya ash eyes ɗin nan nasa akan face ɗinta " sanye take chikin jallabiya baki still dai kanta ba ɗan kwali " a tsorace tasoma magana dan allah kayi hakuri allah bazan sakeba " kara daure fuska yayi sosai yafara Magana, meyakawoki ɗakin nan " Abba ne yace nakiraka tabashi amsa " jinjina kai yayi tare da mikewa zaune ya saki hannun nata, aiko kamar jira take yasaketa ta yunkura aguje zata sauƙa gadon " a zafafe Aryan ya damkoh gashin kanta ya jawota baya har saida tafaɗa kan chinyarsa " kware baki tayi zatayi ihu yasa hannu da sauri ya rufe mata baki yana kallanta " girgiza masa kai tafarayi tana hawaye " calmly yafara magana wani uncle nakune yace yana sonki kuma dayace yanason naki mekikache masa yayi maganar tare da zame hannunsa daga bakinta dakuma rikon dayayiwa gashin kanta " chikin shesshekar kuka tace uncle Omar kuma ni bani yafaɗawaba Zahra ya faɗawa kuma ninache'wa Zahra tafaɗa masa soja nakeso soja zan aura " kara waro ido waje Aryan yayi yana kallanta yadda take magana a nitse yama rasa me zaiche mata " bayan tagama magana'ne " yace to tashimin a kafa" da sauri tamike tana kokarin sauka daga gadan " ai banchi ki sauka bakoh chewa nayi kitashimin a kafa kawai juyo nan ki kalleni kuma ki saurari abunda zan faɗamiki chewar Aryan " a hankali ta gyara zamanta a kan gadon san nan tajuyo tana fuskantarshi " Aryan yace sau'nawa yanzu inamiki magana a kan ɗan kwali eh, " shiru tayi kana ta sunkuyar da kai " meyasa bakyajin maganata meyasa kikesan ɓatamin raine eh " ɗago kai tayi ta ɗan kallesa taga ita yake kallo a hankali tace kayi hakuri zan rinka sawa " jinjina kai yayi yana faɗin to meyasama bakisan ɗan kwali ne " turo dan bakin nan nata tayi tana faɗin Allah yaya Aryan zafi nakeji idan nasa ɗan kwali gashinne yayi yawa shiyasafa nache ra nan ka askemin kaki  " shiru yaɗanyi kafin nan yace Aunty amarya na falone " eh tana nan tabashi amsa " ok to tashi kije inazuwa chewar Aryan " da sauri tamike dan daman kamar a kan ƙaya take har takai bakin kofa kome tatuna saikuma tajuyo ta fashe da kuka" da mamaki Aryan ke kallonta" kuka take sosai gashi tana tsaye taki tafiya " alama yamata da hannu a kan tazo " ba musu tazo kusa da gadan ta duka tana kuka " meyafaru kuma meyasaki kuka Aryan ya tambayeta " chikin kuka tace innar yaya bello tafaɗamin idan nabari namiji yataba jikina to zansamu chiki shine kuma gashi kai kataba jikina " Aryan baima san sanda dariya ta kubche masaba " ganin yana mata dariya yasa tasake kara sautin kukan nata " shiru yayi yana kallan yadda take rera kuka tsakaninta da allah yama rasa me zai chemata kusan 10 tukun nan idea tazo masa, ya sa hannu ya ɗago habarta kasa kasa yace kidena kuka ni ai yayankine ko nataɓaki bazaki samu chikiba amma idan kikayiwa wani namiji magana ko kikabari yataba hannuki tabbas zaki samu chiki " da sauri tace to yanzu yaya Aryan bazan samu chikiba " eh bazaki samuba ai nafaɗamiki ni yayankine babu abunda zaki samu dan natabaki " mikewa tayi tana dariya kamar ba mai kuka yanzun nanba " zuba mata ido yayi yana kallanta chan kuma yace sannu mai kuka da dariya lokachi guda " hannutasa ta rufe fuska tajuya tanufi hanyar fita " binta yayi da kallo har tafiche wani nauyayyar ajiyar zuchiya ya sauke san nan 
yamike yanufi toilet danyin wanka
A gurguje yayi wanka yafito yasa farar jallabiya yafito yanufi palan mai martaba " da sallam yashiga lokachin kuwa duk matasan sungama chin abinchinsu kowa ya watse sauran Ammi da Ummi sai mai martaba  
Zama yayi tare da gaidasu " Ummi takira masu aiki sukazo suka zuba masa white rice an beans da steew yaji kaji sai wani ferfesu a ɗayan plate ɗin suka tura masa gabansa " a nitse yafara chin abinchin " mikewa Ammi tayi tanawa Ummi da mai martaba sai dasafe " Ammi pls kifaɗawa yarinyar nan takawomin coffee dawuri dan inajin barchi chewar Aryan "to kawai Ammi tace san nan tafice 

A bangarensu diyana kuwa zaune suke a ɗaki  zahra da hiyana sunna karatun boko amrat na karatun qur'ani lamrat na buga game a wayar Zahra Aunty diyana kuwa tana zaune gaban mirriow,  wai taga wani kwalli a wayar zahra zatayi irinsa sai faman pente pente takewa fuskarta " ba ƙarya tayi kyau sosai dan diyana daman akoi san kwalliya shiyasa ta dage takoyi kwalliya sosai awajen Zahra
Bayan tagama kwalliyar ne, tamike tanufi wajen kayansawarsu wani wandon jeans blue ta daukoh da t-shirt pink tanufi toilet jim kaɗan saigata ta fito wow bakaramin kyau tayiba ga wandon ya ɗan kamata shape nata yafito sosai yaukam tatara gashin kanta ta ɗaure a tsakiyar, high heel blue ta daukoh kalan wandon tasa a kafarta diyana akoi san high heel sosai " hiyana che ta ɗago tana kallanta kana tace diyana kwalliya da daddaren nan inazakije, gaba ɗaya su zahra ma suka ɗago suna kallanta " babu inda zanje kawai dai yau naji inasanyin kwalliyar darene " wow my diyana kinyi kyau sosai chewar Zahra " Allah aunty zahra to pls ki ɗaukeni hoto mai kyau a wayarki kinji " to zahra tace. San nan ta karɓi wayar daga hannun lamrat tafara yiwa diyana hotona " da sallama Ammi tashigo ɗakin tasamesu sai hoto Zahra ke ɗaukan diyana girgiza kai kawai Ammi tayi kana " tace ke diyana kije kikaiwa yayanku Aryan coffee yanzun nan " to kawai diyana tace Ammi kuma tayi waje tanufi betroom ɗinta " ya isa  hotan haka Aunty zahra bari naje nakaiwa yaya Aryan coffee karna ɓata lokachi ya bugeni idanna dawo saiki kara ɗaukana wasu " to kawai zahra tache " juyawa diyana tayi tanufi hanyar fita hartakai bakin kofar fita saikuma ta juyo ta dawo ta daukoh dan karamin gyale pink tasa a kanta tafiche tanufi kichin " a gurguje ta haɗa coffee ɗin ta ɗaukoh tanufo bangaren Aryan

Da sallama tashiga palon babu kowa kai tsaye betroom ɗin tanufa basallama tashiga babu kowa a chiki dan haka tanufi kan table ɗin ta ajiye coffee ɗin har zata juya tafita saikuma idanta ya sauka kan hotunan Aryan dake kan drowar gefen gado ansasu chikin freme kanana, 
zagayowa tayi tawajen ta zauna a bakin gadon tasa hannu ta ɗaukoh hotu nan dukka ukun ɗaya shida don ne sunsa kakin sojoji ɗayan kuma shi kaɗai ne sanye da jeans baki da white t-shirt ɗayan kuma shida don da yusuf ne dukkansu da wandon sojoji ajikinsu da green t-shirt, shiru tayi tana kallansu chankuma tace kai ashe da gaskenefa hiyana nakama da wan nan mugun tayi maganar tana nuna don kai kuma yaya Aryan inshaa allah soja zan aura wanda zaimin maganinka da kai da bindigar taka, allah sarki yaya yusuf wlh a gidan nan shida yaya Khalid ne kawai mutanen kirki hakadai diyana tayita surutun ta ita kaɗai har ya isheta san na ta ajiye hoto nan tamike tajuyo zata nufi waje idanta ya sauka chikin nashi tsaye yake abakin kofar shigowa betroom ɗin ya harɗe hannu a kirji ya zuba mata ash eyes nashi kallanta kawai yake yakasa ɗauke kai
Murya na rawa tace ina wuni yaya Aryan " ajiyar zuchiya Aryan ya sauke san nan yakarisa shigowa ɗakin yazauna a bakin gado  " diyana naganin ya matsa a hanya yazo ya zauna a bakin gado ta watsa a guje zatayi waje saidai tamanta high heel tasa bazata iya gudu sosaiba,
 taku biyu Aryan yayi ya damki kugunta ta baya tsabar tsoro da razana yasa nunfashinta ɗaukewa ɗif " jin jikinta ya sakine yasa ya riketa da kyau kana ya juyo da ita yana kallan fuskarta da alamar ta sume fa ɗaukan ta yayi ya kaita kan faffaɗar gadansa ya kwantar da ita, zubamata ido yayi sosai yana kallanta from head to toe wow ya furta a filli kana yace masha allah koba komai yaudai ansa ɗan kwalin nan  shafa gefen fuskarsa yayi tare da sauke ajiyar zuchiya yajuya yanufi inda ta ajiye masa coffee ɗin  
Daukan cup ɗin yayi yabar plate ɗin yanufi saman sofa ya zauna yafara sha a nitse sai dayaga sha san nan yamike yanufi freig ruwan faro ya ɗaukoh yadawo kan gadan zama yayi a gefen gadan san nan yabuɗe robar ruwan ya tarfa a hannunsa ya shafa mata a fuska dogon numfashi taja tareda sauke nauyayyar ajiyar zuchiya a hankali tafara buɗe idanta karaf ta saukesu a chikin nashi dankuwa shima kallanta yake " da sauri ta rufe idan ta tana faɗin dan allah yaya Aryan karka bugeni natuba bazan sake taba maka komai na ɗakin kaba " wai ma menamikine dakike chemin mugu akoda yaushe chewar Aryan " batare data buɗe idoba tace natuba bazan sake chewaba " to idan kikasakefa " da sauri tace kamin duk abun da kakeso " kintabbatar inkinsake namiki kome nakeso chewar Aryan " eh nayarda kamin kome kakeso amma dai yanzu kayi hakuri wlh barchi nakeji "  Aryan ya jinjina kai yana faɗin to buɗe idon ki, ki kalleni " slowly tabuɗe idon still dai ita yake kallo ganin bazata iya haɗa ido dashi bane yasa ta juya idonta tana kallansama " murmushi kaɗan Aryan yayi a'zuchiyarsa kuwa yana faɗin a shedai tanajin kunya " jin yayi shirune yasa tace yaya Aryan intafi ɗaki " kinasan tafiyane chewar Aryan " da sauri tace eh " ok to tashi kije dasafe zamiyi maganar danake san muyin " da sauri tamike har takai bakin kofa sai taji Aryan yace ke, da sauri ta juyo tana kallansa " a hankali yafurta kinyi kyau sosai dakikasa ɗan kwali " murmushi tayi san nan tace to yaya Aryan tunda nayi kyau pls kamin hoto idan kamin ni kaɗai sai kuma kamana mubiyu " ok to zokitsaya namiki " da sauri ta dawo chikin ɗakin wayarsa ya ɗaukoh yafara daukanta hoto duk san hotonta sai da, da kanta tace to ya isa yaya Aryan saura nida kai kama ko guda ɗayane tare  " Aryan yace ok to zoki zauna yayi maganar yana nuna mata gefensa " zama tazo tayi a gefensa " ɗan karkatowa kaɗan yayi yarage tsawonsa ya haɗe kansu ya saita wayar yafa ɗaukansu hoto sai daya musu kala 10 tukun nan yace to jeki kwanta " to tache masa san nan tamike tafiche daga ɗakin " ajiyar zuchiya mai nauyi ya sauke san nan a fili yace Aryan waishin meyake damunkane shiru yayi yana tunani dayaga tunanin nan bawata mafita dazata bashi sai ya karisa hawa gadon kawai ya kwanta ya ɗauki remote  ya rage gudun AC yayi shiru kamar mai tunani yana fuskantar sama har barchi ɓarawo  ya ɗaukesa  

Diyana kuwa tana fita tayi bangarensu basallama kawai tafaɗa ɗakinsu zaune tasamu zahra a kan gado zahra naganinta tamike tana " faɗin diyana lfy kika Jima allah dai yasa yaya Aryan bai bugekiba"guntun tsaki diyana taja san nan tace eh bai bugeniba" Alhadulillah zahra tace san nan takoma ta kwanta " itama diyana kayan jikinta tachire tasa na barchi ta haugado tana faɗin hmmmm wato hiyana kam barchinta ma tayi koh " to me zata zauna tamiki barchita zatayimana chewar zahra " diyana bata sake magana ba saima juyawa datayi tana fuskantar yamma har barchi ya ɗauketa 


Misalin karfe 4 na asuba gaba ɗaya family sun haɗu suna sahur ban da don  " Aryan ya dubi diyana yace ke jeki kawomin coffee " diyana na kokarin mikewa " aunty amarya ta dakamata tsawa ke yizamanki bazata kawoba kuma daga yau nahana maganar coffee idan kannenka maza bazasu kawoma ba to kahakura da sha " shiru palon yayi babu wanda ya tanka diyana kuwa tsayuwa tayi tarasa maganar wazata bi, idan taje takawo coffee aunty amarya zata hukuntata, idankuma bata kawoba yaya Aryan zai hukuntata kawai sai tafasa ihu " gabaɗaya jamaa'ar palon suka ɗago suna kallonta " a nitse Aryan yace kukan ya isa zokiyi zamanki kyale coffee ɗin " ai tunbai gama maganaba ta zauna abunta takuma yi shiru " dogon tsaki fahad yaja san nan yace darabon wlh nizan babballa yarinyar nan yanzu dan iskanchi me aka.... bai karisa baganarba sakamakon mugun kallon da Aryan ya wurgamasa " aunty amarya kuwa mike tayi tana faɗin kai idan kagama kazo ɗaki inada magana da kai tayi maganar tana nuna Aryan san nan ta fice " dogon tsaki aiman yaja san nan shima yamike yana faɗin dole nabar kasar nan gobe yayi waje " mai marbata kam ido kawai yake binsu dashi " Ummi tace ba akaiwa prince a'binchinsaba'fa " Ammi tace to su tashi sukai masa mana " fahad yamike yana faɗin barinaje na kaimasa san nan yayi waje 

Mikewa aryan yayi zaiyi waje " Mai martaba yace inazaka " alwala zanje nayi Aryan yabashi amsa " ok idan mundawo masallahchin kasameni a ɗaki chewar mai marbata " ok kawai Aryan ya amsa dashi san nan yayi waje " mai martaba ma mikewa yayi yana faɗin to yakamata kuje kuyi alwala dan sauran 20 mnt afara kiran Sallah yana gama faɗin haka yanufi ɗakinsa " mikewa sukayi da ɗai ɗai sukabar palon 


Misalin karfe 9 zaune take a chikin class nasu uncle nasu yashigo yana tambayat wacece fateema abubakar saraki " da sauri zahra tace nine" oh to kifito zakuje duba uncle nakune bai da lfy kowani class zamu ɗauki mutun ɗaya " to kawai zahra tace san nan ta ɗauki jakarta tafito sukayi waje da uncle nasu yan mata 7 tasamu tsaye a wajen tare suka jera har wajen motar makarantar suka shiga da gudu motar tabar makarantar " suna tafiyane Zahra ke tambayar yanmatan wani uncle ne bai da lfy 
Sukache mata wlh suma basu saniba " shiru zahra tayi batasake maganaba har suka isa gidan uncle ɗin  driver na parking suka fito uncle Aminu yamusu jagora zuwa chikin gida ga mamakinta saitaga uncle Omar nefa nan tafa tunanin wai ba jiya suka rabu lfy'ba kodai accident yayine ga kafarsa duk bandeji gashi har goshinsa, tayi nisa chikin tunanin sai taji muryan uncle Omar yana faɗin fateema har dake a kazo " eh uncle inawuni yajiki zahra tabashi amsa " lfy fateema jiki da sauki " to allah yakara sauki chewar Zahra gaba ɗaya suka amsa da amin san nan suka mike suka masa sallama yana musu godiya har suka fice sukaje sukashiga motar makarantar ta maidasu


Misalin karfe 5 na yamma zahra hiyana diyana amrat lamat suna zaune a palon Ammi suna kallo " hiyana tace lamrat kije kikawomin fura da nono a palon mai martaba dan na freig ɗin Ammi yakare " hararar wasa Zahra tawa hiyana tana faɗin yanzu sai'kisha furar a gabanmu bazakiji kunyaba idan wani yashigo yaga baki a'zumifa "  murmushi kaɗan hiyana tayi amma saida ɗimple nata ya lotsa tace aa aunty zahra bafa a nan zansha ba ɗaki zantafi mana " Zahra zatayi magana " diyana tarigata dachewa to ina ruwan wani dake inbaki azumin ma ina ruwansu nifa wlh inniche koh har tsakar gida zanje inachin chingom " baki buɗe Zahra da hiyana ke kallon diyana itakam ko ajikinta dan batamasan abun datake faɗinba kawai duk maganar dayazo bakinta take faɗi  " lamrat kuwa mikewa tayi tafita tanufi palon mai martaba " daukoh fura biyu tayi da nono roba 1 san nan ta ɗauki kwarya yajuye nonon a chiki tajefa furar a chiki kwaryan san nan tasa ludayi ta dauka tafito tanufi part din Ammi " daga nesa yusuf ke kallanta tana tafiya a nitse chikin kwanchiyar hankala sai murnushi yake " tazo dai dai zata shiga ɓan garen Ammi tayi karo da haidar nono yazube masa ajiki " wani wawan mari ya sakar mata a kumatu " wani ƙara tafasa ta kwasa aguje tai chikin gidan kai tsaye palo Ammi tanufa " shikuma haidar yanaganin ta tafi yaja doguwar tsaki yajuya zai wuche part nasu kamar daga sama yaji saukar mari shima, a razane ya ɗago kai, " ido huɗu sukayi da Yusuf fuskar nan tamkar an aikomasa da mutu a kausashe yace metamaka kamareta eh " murya narawa haidar yace kayi hakuri yaya yusuf wlh raina ne yabachi " shoot up wai kubaku da tausayine eh yanzu kowani kagani zai mareta bazaka hanashiba to wlh idan kasake gigin taɓa yarin yar nan sai ranka ya ɓachi wuche kabani waje chewar yusuf  " jiki ba kwari haidar yawuche " yusuf kuwa yabi bayan lamrat 

Da sallama yashigo balan kwanche kan kafar hiyana yasameta sai kuka take " a nitse yace my baby taso kizo " aiko tanajin muryansa tamike da gudu tanufeshi hannu yabuɗe mata tafaɗa kirjinsa tana kuka kasa kasa " hannu yasa yaɗago habarta kasa kasa yafara magana ya isa haka kukan kinji goge hawayenki yayi maganar tare da ɗan sakinta kana yazaro hand'kee daga aljihunsa yamiƙa mata " hannu tasa ta amshi hand Kee ɗin tagoge hawayenta" shikuma yarikoh hannunta suka  fiche daga palon "

Su zahra dai baki bude suke kallan yaya Yusuf har ya fice rike da hiyana " mikewa Zahra tayi tana faɗin lokachin shirya kayan buɗa baki yayi tayi gaba su hiyanama suka mike sukabi bayanta

 yusuf kuwa suna fita shida lamrat sukayi bangaren Ummi " da sallama suka shiga palon " Ummi dake zaune kan kujera mai zaman mutun biyu ta amsa da waalaikassalam, shigowa chiki sukayi yana rike da hannunta " Ummi naganinsu tafara murmushi tana faɗin waya taɓomini lamra'ta Naga alamar tayi kuka " murmushi yusuf yayi kana yace babu kowa shagwaɓa chekawai " Ummi tace to taso kizo kusa dani " da sauri lamrat ta mike takoma kusa da Ummi " yusuf zaiyi magana sai aka kirasa a waya mikewa yayi yace Ummi inazuwa yayi waje.



To a kwana a tashi babu wuya awajen allah yau jirginsu mai martaba yatashi zuwa Umrah gaba ɗaya yan gidan suntafi sauran yammatan Ammi kawai suma dan ba abasu hutun makaranta bane shiyasa dagasu sai masu aiki aka bari a gidan sai security dakuma wasu daga chikin sojojin yaya prince da yaya Aryan da yaya yusuf   
  "yauma kamar kullun shirinsu sukayi tsab nazuwa school  suka fito harabar gidan nantake drivers ɗin su, sukazo da gudu suka buɗe musu motochin suna shiga suma drivers ɗin suka shiga dagudu suka tada motochin suka bar gidan gudu suke da motochin sosai chikin ƙanƙannin lokachi suka isa school ɗin, suna parking su hiyana suka fito suka nufi wajen dasuke zama kafin a shiga class " drivers kuma suka juya kan motochin suka koma gida " 

misalin karfe 9 na safe bayan antashi break zaune suke sunata hirarsu awajen game na makarantar kamar daga sama sukaji jabir yana faɗin "hiyana taso muje,  chikin tsiwa diyana tace wlh yaukam babu inda zataje Exam fa akeyi bata gama rufe bakiba taga jabir yaɗaga hannu a fusache zai..

more comments an share 

*💫STAR LADY💫*

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*




Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 13*
            


Tana ganin jabir ya ɗaga hannun zai mareta tafasa kara tafaɗi kasa tana birgima kamar mai aljanu " bashiri jabir ya jabirki ya tsaya yana kallo ikon allah " da sauri su hiyana sukayi kanta suna kiran sunanta " chikin tsawa diyana ke magana ni basunana diyanaba ni sunana bilkisu, ha,ha,ha ta kwashe da dariya " a tsorace Zahra ke faɗin munshiga uku yaukam me kuma yasamu diyana " hiyana kam ko ajikinta dan tasan iskanchin diyana yawuche hakan " chikin tsawa diyana tace kai jabir zo nan ai nafaɗamaka daman niche zanyi magananin'ka " jabir najin haka ya kwasa aguje  yabar wajen  " Zahra kam tagama tsorata baya baya tafara jaa tana salati " hiyana lamrat amrat kuwa ko ajikinsu saboda sunsan halinta daman " diyana naganin jabir ya gudu tamike tana faɗin nizakawa iskanchi wlh nafika iyawa muzuba mugani ae kai karamin ɗan iskane " a sukwane Zahra tamike tana kallon ikon allah " mekuma kuke kallona haka chewar diyana tayi maganar tana kokarin mikewa, bayan tamike tsaye ta dubi su hiyana tace sai kutashi mutafi class ae tun da ɗan iskan ya gudu,
 hanyar class nasu tanufa abunta tafiya take hankali kwanche, hartakai kusa da class nasu saikuma ta juyo yadda tabarsu haka tajuyo ta gansu ko motsi basuyiba Sun zuba mata ido " murguɗa baki tayi kana tace kuchigaba dazama allah yasa yadawo yasameku nikam kunga shigana class tana gama faɗin haka tasa kai tawuche chikin class nasu abunta 

Hiyana ta mike taje ta dafa Zahra tafara magana Aunty Zahra naga kin tsorata to wlh indai diyana che kaɗanma kika gani dan wlh abun dayafi wan nan zata aikata " dogon nunfashi zahra taja haɗe da sauke nauyayyar ajiyar zuchiya kana tace yanzu hiyana kina nufin kichemin ba aljanubane sukayi magana yanzu diyana che,  kuma yanzu diyaya ita ta iya zama ta shirya wan nan wasan kwai kwayon " shakka babu Aunty zahra duk abun da kika gani shiryashi diyana tayi ba gaskiya bane chewar hiyana " shiru Zahra tayi tana tunanin itafa lamarin diyana yafara bata tsoro tayi nisa chikin tunani taji, lamrat ta taɓata tana faɗin Aunty Zahra muje dan idan kika biyewa Aunty diyana wlh yau bazaki shiga class ba jiki ba kwari Zahra tafara tafiya tana faɗin yanzu idan jabir yaganefa " wan nankuma matsalarsu, che shida diyana tunda ita tamasa chewar hiyana " lamrat kuwa chewa tayi wlh ninasan ko jabir yagane Aunty diyana zata nemawa kanta mafita " ajiyar zuchiya Zahra ta sauke san nan tace to shike nan allah ya karemu gaba ɗaya tayi maganar tana kokarin shiga class nasu sai anjima sukawa juna hiyana ma tawuche nasu class ɗin suma su lamrat kowache tawuche class nasu 

Karfe 3 na rana anbuga bell na tashi gaba ɗaya ɗalibai sun fito suma su hiyana sun haɗe kansu suka nufi wajen dasuke tsayawa sunajiran drivers nasu,  suna tsaye suna yar hirarsu sai ga faria ma da fara'a suka gaisa da hiyana dakuma diyana lamrat da amrat kuma suka gaisheta ta amsa da fara'a " daga bayansu sukaji an daka musu tsawa, a na faɗin  ke nizakiwa karyan aljanu koh to wlh yau sai kin gommace da'baki zo duniyar bama da sauri gaba ɗayansu suka juya " diyana zatayi magana sukaji jiniyar motochin ɗaukansu  " hiyana na ganin motochin ɗaukar'su, batasan lokachin datache alhamdulliah ba " Zahra kuwa tun motochin basu gama parking ba ta zura a guje tabuɗe kofar motar tashiga tana sauke ajiyar zuchiya " lamrat da amrat ma motar'su suka nufa da sauri sukabar hiyana da diyana tsaye awajen " jabir naganin motochin'su yaju yabar wajen yana faɗin zamu haɗu gobene wlh zakisani inna rikeki "  diyana naganin jabir ya tafi ta murguɗa baki tana faɗin kadaɗe baka dau matakiba wlh ɗan rainin wayyo zanyi maganinkane allah yakaimu goben kagani nidakai wazaiyi winner " baki buɗe hiyana ke kallan diyana tana tunani a chikin zuchiyarta wai diyana kam bata da tsorone a rayuwarta " tayi nisa chikin tunaninta tajiyo muryan diyana na faɗin to kekuma me yatsayar dake inbazaki zoba saimu tafi mubarki da jabir ɗin " mamakine yakama hiyana wai yaushe diyana ta barwajen nan jiki ba kwari tanufi motar drivers ɗin na tsaye suna kallonsu sunasan tambayatsu lfy amma suna tsoro dan hakan bata shafi aikinsuba " hiyana nashiga motar suma drivers ɗin suka koma chikin motar suka tayar da' gudu sukabar makarantar.


Yau kwana biyar ke nan datafiyar su mai martaba Umrah

SAUDIA


Misalin karfe 10 na dare Aryan Aiman yusuf Ahmad Khalid suna zaune a palon hotel ɗin da suka sauka hirasuke gaba ɗayansu ban da Aryan daya zauna shiru kamar bashi a ɗakin " Khalid ne ya ɗan taba shi " a ɗan firgiche ya ɗago ash eyes ɗin nan nasa yana kallan khalid " lfy meke damun ka gaba ɗaya naga kamar mood naka ya chanza chewar Khalid " iska mai zafi Aryan ya fuszar daga bakinsa kafin yasoma magana babu komai kawai inatunanin intashi inje induba prince ne naga wunin yau shiru banji motsinsaba  " satar kallan yusuf Khalid yayi san nan yace ok to kaje kadubashi mana " mikewa Aryan yayi yanufi staircase ɗin ya haura sama "  murmushi Yusuf yayi yana kallan Khalid " harara  Aiman ke wugawa yusuf tare da faɗin me kuke kullawa " shima Yusuf yadawo masa da harara yana faɗin mekuma zamu kulla " tsaki Aiman yaja san nan yamike yana faɗin zakusani dai kubi a hankali dankuwa idan ta kwaɓe muku kunsan sauran " kallan sama da kasa Khalid yawa Aiman san nan yaja tsaki yace. To kayi rashin sa'a nine babba ba kaine babba a kainaba dazaka tsaya kana faɗamin zanchen banza ni wuche kabani waje hai " tsaki Aiman yaja san nan ya wuche yanufi staircase ɗin " dawo da kallansa Khalid yayi kan Ahmad dake zaune ya zuba musu ido to kaima mekake jira dabaka'wuche kabi husainin nakaba  " dariya Ahmad yayi san nan yace gulma natsaya jimana ai yau munraba gari da husainin nawa dannikam sainaji gulmar " Khalid bai sake maganaba sai daima yachiro wayarsa yafara neman layin Zahra " wayar nafara ringing yamike yana chewa Yusuf kasameni a ɗaki san nan yawuche  " mikewa Yusuf ɗinma yayi ya kyale Ahmad awajen yanufi staircase ɗin shima kai tsaye ɗakin Khalid yanufa da sallama yashiga zaune yasamu Khalid yana waya da zahra,  hannu kawai Yusuf yasa ya amshi wayar kana yasa akunnensa yana jiyo hayaniyar, kannen nasu " ina my baby abunda Yusuf yace da zahra ke nan " da sauri zahra tace gatanan tamikawa lamrat wayar " hello yaya Yusuf ina wuni " lunshe ido Yusuf yayi san nan yabuɗe yana faɗin lfy my baby ya school " alhamdulillah lamrat tabashi amsa " shiru yaɗanyi kafin yafurta tsarabar me kikeso inkawo miki " babu komai yaya Yusuf Allah dai yadawo daku lfy shine fatanmu chewar lamrat " bakaramin daɗi Yusuf yajiba azuchiyarsa yafa tunanin yarinya karama da hankalin manya yana chikin tunani yajiyo muryarta tana faɗin allah yaya Yusuf kewarka nake sosai da sosai  " sake lunshe ido Yusuf yayi yana murnushi farinchiki kasa kasa yace my baby nima nayi missed naki sosaifa " a shagwabe tace to yaushe zaku dawo " Yusuf zaiyi magana Khalid ya amshi wayar yana faɗin inyamaka zafi kasaya mata nata wayar yayi maganar tare da mikewa yanufi waje  " murnushi Yusuf yayi san nan yafurta nice idea yana gama faɗin haka ya haye gadan Khalid yayi kwanchiyarsa

Khalid kuwa yana fita kai tsaye ɗakin Aryan yanufa da sallama Khalid yashiga Aryan baya ɗakin dan haka khalid yafito yanufi ɗakin DON da sallama yashiga zaune yasamesu kan kadon,  suna fuskantar juna da alama  magana mai muhim'manchi suke " jin sallamar Khalid yasa dukkansu suka juyo suna kallansa " ƙarisa shiga chikin ɗakin Khalid yayi shima ya haye gadan ya zauna a nutse yafara magana 
Aryan wai meke damun kane naga gaba ɗaya yau ka chanza ne gashi ka ɗan rame kamar baka da lfy chewar Khalid " daga  green eyes nashi sama DON yayi kamar mai kallan wani abu kamar kuma mai tunani  " zuba mishi ido Aryan da Khalid sukayi suna kallansa " jimkaɗan ya sauke kansa tare da furzar da iska daga bakinsa ya tsare Aryan da ido sosai yake kallansa " nantake Aryan ya mike kamar mara gaskiya yana kokarin sauka daga gadon kamar daga sama yaji muryan DON yana faɗin me kake ɓoyemin ashe akoi abunda bai kamata nasaniba a dangane da kai,  kodai matsayina bai kai bane " jin maganar DON yasa Aryan saurin juyowa yana kallansu shiru yaɗanyi kafin nan yace. Taya kake tunanin akoi abun da zan boyemaka dangane dani kai'nefa ni kuma nine kai SO bawani abun boye boye a tsakaninmu wlh kawai bana jin daɗine ni kaina bansan meke damuna ba kwata kwata nakasa samun nitsuwa " shin akoi wani abu mai mahim manchin daka rabu dashine dazaisa kakasa nitsuwa DON yajefo ma Aryan tambayar bazata " aa nikuma ina dawani abu mai muhim'manchi dayawuche kune ai kune kawai masu muhim'manchi a rayuwata " Khalid dai ido kawai yake binsu dashi yadda suke maganar burgesa suke DON akoi kokolwa sosai akoi basira Aryan kuwa akoi wayau sosai shiyasa haɗin nasu yake bada chitta " barchi nakeji kaina chiwo yake min zanje na kwanta chewar Aryan yayi maganar tare da juyawa yachigaba da tafiya har yakai bakin kofa sai yaji muryan DON yana faɗin idanma baka faɗamin yanzuba nasan dole gaba zanji ai " shiru kawai Aryan yayi bai tankaba saima kara sauri dayayi yabar ɗakin 

Dawo da kallansa DON yayi kan Khalid yana faɗin akoi abun dake damun ɗan uwana tabbas ba lfy yakeba " murmushi kaɗan Khalid yayi a zuchiyarsa kuwa yace baridai ya ɗan latsa DON yaji yazasu kare ajiyar zuchiya ya sauke san nan yadubi DON yace kasani kodai yafaɗa soyayyane " a zafafafe DON yace what ?  hauka yakene kataɓa ganin yana magana da watane ma NO hakan ma bazai yuwuba " mamakine yakama Khalid ganin daga maganar mace DON ya sauya kamar bashiba " nantake ya kara ɗaure fuskar nan kamar baisan me dariyaba Khalid yayi nisa chikin tunani muryan DON takatse masa tunani "  Khalid i said  get out  " kallon DON Khalid yake da mamaki ba musu ya sauka daga gadan dan yasan halin DON yanzu idan yace zai biye masa sai abun yakai'su ga ɓachin rai " fitowa Khalid yayi daga ɗakin DON kai tsaye yanufi ɗakin Aryan 

Da sallama yashiga zaune yasamu Aryan a tsakiyar gado " ba karamin mamaki Khalid yayiba ganinsa zaune karisawa chikin ɗakin yayi ya zauna a bakin gadon " sai lokachin Aryan ya juyo yana kallansa " lfy bakayi barchiba aryan Khalid yajefo masa tambaya " iska mai zafi ya furzar daga bakinsa calmly yafara magana nasaba da shan coffee kafin nayi barchine Khalid dazun nayi order coffee sun kawomin amma ɗan ɗanon bai minba kwata kwata na gida nake buƙata shiyasama kaga nakasa barchi " hannu Khalid yasa a aljihun wandansa ya ɗauki wayarsa yafara kiran layin zahra dan kuwa yanzu yagane matsalar Aryan " bugu ɗaya Zahra ta ɗaga tana faɗin yaya Khalid ɗazun muna hira ka gudu " yanzu me kuke bakuyi barchiba Khalid yajefo mata tambaya " karatu mukayi amma yanzu zamu kwanta ai  tabashi amsa " ok ina diyana " gata nan inbatane chewar Zahra " eh bata yayi maganar tare da mayar da wayar a H-free  " ansar wayar diyana tayi chikin voice kamar mai jin barchi tafa magana yaya Khalid shine baka nemeniba tun ɗazun inajin kana magana dasu zahra inasu Ammi " suna lfy allah sarki na mantane amma ai gashi yanzu na nemeki Koh " yauwa yaya Khalid daman inasan in'tambayeka chewar diyana " ok tambayi " wai a chan makkan wake kaiwa yaya Aryan coffee " jin tambayar nata yasa Khalid ɗago ido yana kallan Aryan shima Aryan ɗin shiyake kallo " dawo da kallansa Khalid yayi kan wayar san nan yace bari nabawa yaya Aryan ɗin sai ki tambayesa Koh bai jira amsar taba yamikawa Aryan wayan " ba musu yasa hannu ya karɓi wayar yana sauke ajiyar zuchiya " Khalid na mika masa wayar ya mike yace kuyi magana inazuwa yana gama faɗin hakan yafiche daga dakin da sauri yana murmushi

Calmly Aryan yafara magana hello " ina wuni yaya Aryan chewar diyana " wani murmushi Aryan yayi kafin tace lfy y school " alhadulillah tabashi amsa " good yace saikuma sukayi shiru dukkansu " chankuma sai diyana tace yaya Aryan wayake kawo maka coffee a makkan " murmushi ya ɗanyi kafin ya burta babu kowa " yanzu ke nan bakashan coffee ɗin " eh bana sha yabata amsa a takaice " Allah sarki da ina nan dana rinƙa kawoma ai " Aryan baimasan san da dariya ta kubche masaba dan yadda ta furta Allah sarki bakaramin dariya tabashiba amma sai ya danne dariyar yace ashe kinaso na bansaniba ashe kina tausayina " aa bana sonka inadai tausayinka chewar diyana " to meyasa bakisona  " shiru ta ɗanyi san nan tace kai'ma ai bakasona ne shiyasa nima bansanka " to wayace maki ni banasonki  " Allah yaya Aryan basai anfaɗaminba ni da kaina nasani baka sona dan inkana sona bazakache zaka harbeni da bindiga namutu kowa yahutaba " shiru yayi yana tunanin sai yanzu yagane kuskurensa namata barazana da hakan shi yamata chikin wasa itakuma ashe tarike a matsayin gaske yayi nisa chikin tunani sai yaji tana faɗin yaya Aryan sai da safe su zahrafa har sunyi barchi sun kyaleni " ok kawai yace da ita san nan ya katse kiran ya ajiye wayar a gefe ya kwanta  bajimawa barchi tayi awon gaba dashi

Lokachin da Khalid yadawo ɗakin dan karɓar wayarsa yasamu aryan yayi barchi murmushi yayi a'fili yafurta ai daman ninasan meyahanaka barchi kai da kanka kake neman kashe kanka anfaɗa maka SO wasane ganin Aryan yana ɗan motsi yasa Khalid ɗaukan wayarsa da sauri yayi waje yana murmushi


Washe gari dawuri suka tashi sukayi shirin zuwa school kamar yadda suka saba haka suka fito yauma kai tsaye wajen motochinsu suka nufa da gudu drivers ɗin suka karaso wajen budemusu motochin drivers ɗin sukayi
Su diyana Suka shiga suna shiga drivers ɗin ma suka shiga da gudun gaske suka tada motochin suka bar gidan gudu suke sosai chikin kan kanin lokachi suka isa school ɗin awajen dasuka saba parking sukayi yauma fitowa su hiyana sukayi suka jera zuwa wajen tsayuwa suyi hira kafin a shiga class " drivers kuma suka shiga motochin suka juya suka koma gd 

Tsayuwa sukayi kamar dai jiya Suna hirar'su daga bayansu sukaji andaƙa musu tsawa " ke zonan ni jiyazakiwa karayan aljanukoh to wlh sai kinyabawa aya Zakinta dan yau saina babbalaki a school ɗin nan " gaba ɗayansu suka juya ganin jabir yasa Zahra ta kwasa da gudu abunta tayi hanyar class nasu " diyana kuwa tsayuwa tayi kamar mai tunani ta harɗe hannu a kirji babu ko alamar tsoro a tattare da ita " hiyana kuwa juyowa tai ta dubi' su lamrat kasa kasa tace musu kuje class " a tare suka juya suka nufi class " jabir ganin alamar diyana ko tsorata batayi ba dajin maganar da yayi yasa ya nufeta gadan gadan ya duncle hannu zai kai mata naushi da sauri...✍️✍️





More comments an share pls 🙏






*💫STAR LADY💫*

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai





Episode 14


A fusace jabair yanufi diyana, tana tsaye ko motsi batayiba kuma babu alamar tsoro ko kaɗa a face nata " hannu Jabir ya ɗaga zai'kaiwa diyana bugu  " da sauri hiyana tarike hannun nasa " a zafafe Yajuyo yaga waye yarike masa hannu,  ganin hiyana che yasa ya watsa mata harara yana faɗin sakeni " ita ma rai a bace tache wlh bazan sakekaba kafara buguna tukun nan kafin kabugi diyana " fisge hannunsa yayi yasake ɗaga hannu zai mari diyana " da sauri hiyana tashiga tsakanin' su tana faɗin diyana kiwuche class naku " diyana dake tsaye babu alamar tsoro a face ɗin ta tace babu inda zanje hiyana sai dai duk abun da zai'mana yamana tare " ganin haka yasa jabir yajuya yabar wajen dan kuwa bazai iya bugun hiyana ba dan yana sonta itakuma bazata taɓa barin abugi diyana ba " suna ganin jabir yatafi suka rungumi juna  " diyana nafaɗin wlh sauran kaɗan nayi fitsari a wandona dan tsoro, dayanzu  jabir yabugeni da wan nan katakon hannun nasa ai nashi uku " dariya hiyana tayi sosai san nan tace wlh ba kyaji diyana ae nima nakusa fitsarin saboda tsoro kawai dagewa nayi dan bazan iya ganin ya sauke wan nan jibgegen hannun nasa a jikinkiba " dariya sukayi gaba ɗayansu san nan suka saki juna suka reke hannun'su chikin na juna suka nufi class, 


KASAR SAUDIA

Tsaye yake gaban mirrow yana gyara gashin kansa sanye yake chikin wandon jeans Navy Blue da White t-shirt, bakaramin kyau kayan suka masaba sosai ya gyara gashin kan nan nasa ya tara ya ɗaure ta baya, yasake ɗaukan turare yafeshe jikinsa,ga sajen nan nasa kwanche a kan face nashi kamar wani balaɓe wayarsa ya ɗauka yafito wajen kai tsaye palon kasa yanufa, zaune yasamu yan uwan nasa gaba ɗayansu har dasu haidar, kallan DON yayi yafara magana " zan fita inasan inje wani wajen " da mamaki DON ya ɗago green eyes nashi yana kallan Aryan  ya mai maita maganar zai fita inasan inje wani waje shiru yayi kamar mai tunani " Aryan dai ido yazuba masa kawai yana kallan'sa " zarginafa yafara tabbata a kanka Aryan chewar DON " murmushi kaɗan Aryan yayi san nan yace au daman zargina kake ke nan " yap zuchiyata na zargin wani abu " matsowa Aryan yayi kusa da DON sosai san nan yafara magana karkabar zuchiyarka tana raya maka wani abu a kaina kasan dai wlh babu wani abun dazanyi batare da saninkaba yanzunma kasawu zanje kuma nasan bazuwa zakaiba konache muje, shiyasa banche mujeba nayi shirina na zuwa nikaɗai " dogon numfashi DON yaja san nan ya jinjina kai yana faɗin ok to shike nan nayarda ba komai Allah ya tsare a dawo lfy yayi maganar yana kokarin mikewa kai tsaye stairs ɗin yanufa " binshi da ido Aryan yayi har yakurewa ganinsa san nan ya dawo da kallansa kansu Khalid " a nitse yache na wuche " adawo lfy suka masa gaba ɗayansu " san nan face yana amsawa da Amin 
Mikewa Khalid yayi yana faɗin Yusuf muje Koh " mikewa Yusuf ɗinma yayi zasu wuche waje sukaji Ahmad na faɗin wlh akoi abun da kuke shiryawa,  wani harara Khalid ya wurgawa Ahmad batare da sunyi magana ba suka nufi hayar fita palon " kallan Aiman Ahmad yayi yana faɗin tabbas yaya Yusuf da yaya Khalid suna shirya wani abun " mikewa Aiman yayi yanufi staircase ɗin yana faɗin zanyi binchike a kansu ae zan samusu ido sosai yanzu " mikewa Ahmad ma yayi yabi bayan Aiman " dogon tsaki fahad yaja san nan yace wlh yaya Ahmad da Yaya Aiman kunchika gulma ni barima naje na gaida su ammi yayi maganar yana kokarin mikewa " haidar da umar suna ganin fitar fahad suka kwashe da dariya kamar abun haɗin baki sai dasukayi mai isarsu, tukun nan suka tsagaita " kasan me haidar da alama fa akoi dirama a gd nan wlh chewar umar " jijjina kai haidar yayi yana faɗi babbama kuwa, amma naga alamar yau yaya Aryan nachikin farinchiki sosai bakamar jiyaba " kai dai tashi muje mu gaidasu Abba inmunje ɗaki makarisa magana chewar umar a tare suka mike sukayi waje,

Mai martaba Ammi Ummi Aunty amarya  zaune suke a nasu palon suna hira "Fahad yashigo da sallama" amsa masa sallamar sukayi yashigo chiki ya zauna saman sofa ya fara gaida iyayen nasu " da fara'a suka masa "
 
Ummi ta dubi mai martaba tace ranka yadaɗe wai yabatun komawar yaran nan bakin aikinsune " shiru Abba ya ɗanyi kafin yace bayan zuba sai bayan naɗin sarauta " eh hakanma yayi chewar Ammi " aa baiyibakam gaskiya sukoma wajen aikinsu chewar Aunty amarya "  jinjina kai mai martaba yayi yana faɗi aa aini ba zaɓinku nanemaba bare kufara musu hukunchina kawai nayanke sai anyi naɗin sarauta " calmly Fahad yafara magana Abba inasan zuwa Us " da sauri Ammi ta ɗago tana kallansa zatayi magana mai martaba yarigata dachewa sai kayi aure tukun nan dan inbakiyi aureba bazaka sake fita Nigeria ba " baƙaramin daɗi Ammi tajiba jin amsar mai martaba " Fahad kuwa a razane yace Abba Aure fa kace " eh aure a kache auren wani mugun abune Ummi tabashi amsa rai a bace " bahaka bane Ummi bawai auren ne mugun abuba taya zanyi aure su DON basuyiba " dogon numfashi mai martaba yaja san nan yace ae suma a nayin naɗin sarauta, zansa su sufito da mata dan ya isheni ganinku haka " dariya Fahad ya kwashe dashi yana faɗin wayyo duniya wayaga DON da mata chab to wai suda ko yanmata basu taɓayiba ai na zasu samo matar " Ammi tace kai banfa san iskanchi kasani ne dasu kake fitane " ae Ammi infaɗamiki duk wanda yasan yaya Aryan yaya Prince yaya Yusuf yaya Khalid yaya Aiman yaya Ahmad yasan basuda budurwa kuma basu taba chewa ko chikin wasa sunasan wataba suda ko kalloma mace bata ishesuba " tashi kafita mana a ɗaki chewar Ammi " fahad zai sake magana sai sukaji sallamar Haidar da umar " Abba yace yauwa kuzo nan kuma daga yanzu kuje kufara neman matar aure dan wlh bayan naɗin sarauta duk aurar daku zanyi na huta " ɗaure fuska haidar yayi san nan yajuya yanufi hanyar fita yana faɗin inazuwa " salati Aunty amarya tayi kana tace yanzu maganar auren ne tasa kajuya kafasa shigowa koh haidar " haidar dai baibi ta kansuba yayi waje da sauri " da sauri umar ma yajuya yabi bayansa " mikewa Ummi tayi tana faɗin kai jama'a zama bai gammuba wayan nan yaran sai na danganasu da ɗakin kaba barima naje nafara musu addua tun da sassafen nan yara saikache wadda aljana ta aura, " Mikewa Ammi tayi tace muje tare wlh sai mun haɗa da sallar darema dan abun nasu yafara wuche hankali " mai martaba ma yamike yana faɗin muje tare dan nima naga alamar sai na haɗa da tawa adduar " a tare suka nufi waje Aunty amarya kuwa tamike tanufi ɗaki ta haye gado ta kwanta " baki buɗe fahad ke kallansu Abba har suka fice afili yace wai muza'awa tsayuwar dare harma da danganamu da kaba yanzu mai mukayi hmmmm baridai naje nafaɗawa DON halin da ake chiki yamike ya fito ya haye lifter yakoma sama 

Da sallama yashiga ɗakin don kwachi yasameshi a kan makekiyar gadon sa yana latsa waya karisawa chikin ɗakin fahad yayi ya haye gadon ɗago kai DON yayi yana kallansa  " kwaɓe fuska fahad yayi kamar wadda ya taka kashi " lfy kazo kana bata rai DON ya tambaya " daman kamar jira Fahad yake a tambayesa nan take yafara faɗawa DON abun da yafaru a ɗakinsu Ummi yanzu " dogon tsaki DON yaja yana faɗin to suyi tsayuwar asubama ba na dareba ni dallah tashi kabani waje na daukama wani abinne nine za'achewa na kawo mata aure niɗin never wlh babu aure a tsarin rayuwata " da karfin guiwar fahad yamike yafito dan shi a tunaninsa DON zai watsa maganar auren 


 KANO STATE NIGERIA


Misalin karfe 4 na yamma suna zaune a palon Ammi hiyana na karatun qur'ani diyana na game a wayar Zahra " Zahra kuma tana gyarawa amrat gashi " lamrat kuma tana Assessment na English da a kabasu a school kawai sukaji diran motochi gidan jiniya kakeji ta ko ina ya karaɗe gidan " diyana tamike tana faɗin kodai su Abba ne suka dawo " aa basu bane chewar zahra " hiyana zatayi magana " Zahra tace kutsaya kutsaya naji kamar busan gidan sarautane hakan nanufin Aunty maryam ne tazo tab " da sauri Hiyana ta ɗago tana kallan Zahra wacece Aunty Maryam hiyana ta tambaya tana kallon Zahra " babban yarinyar Aunty amaryan che chewar Zahra " tab wlh tun danaji yarinyar Aunty amarya che nasan muguwache irinsu yaya Aryan  chewar diyana " baki buɗe hiyana ke kallanta san nan tace ke diyana nikam taushe zakiyi hankaline haka a kachemiki ita muguwace " da sauri zahra tace aa hiyana diyanafa batayi karyaba tabbas aunty maryam muguwace nabugawa ma a jarida " lamrat tace to Aunty Zahra to daman ina Aunty maryam ɗin take " tayi aure ne a gombe  kinsan Aunty amarya yar sarkin gombe ne to yayan Aunty amarya shine yake rike da mulki yanzu yana da babban ɗa mai suna Mahmud to Mahmud ɗin ne mijin Aunty maryam shiyasa kukaji karan irin busar da akewa Abba idan zai fita ta ko ina ai mijin Aunty maryam ɗin shine yarima mai jiran gado " to Aunty Zahra me tazoyi gidan nan yanzu chewar diyana " itakam hiyana baki bude take kallan diyana tana tunani mutun da gidansu amma diyana ke tambayar me yakawota " murmushi Zahra tayi san nan tace ai daman kowani sallah suna zuwa ammafa sai anyi sallah da kwana ɗaya suke zuwa " to ai yanzu Sallah sauran kwana 10 meyasa tazo chewar diyana " Zahra zatayi magana hiyana tarigata dacewa zaki iya zuwa ki tambayeta ai meyasa tazo " mikewa Zahra tayi tana faɗin kuzo muje mumata sannu dazu kartace munajin zuwanta mun shareta " mikewa sukayi gaba ɗayansu suka bi bayan zahra

Kai tsaye bangaren Aunty amarya suka nufa da sallama suka shiga wasu yan mata guda 3 suka samu da alama kuyangun Aunty maryam ne " yanmatan suna ganin su Zahra suka fara gaidasu " lfy kawai Zahra ta amsa musu dashi san nan  kai tsaye ta wuche tanufi wani ɗaki "  su hiyana suka rufa mata baya " sallama zahra tayi a bakin kofar kusan 5 mnt tukun nan a ka amsa tare da izinin shigowa " diyana kam sotake kawai taga wan nan Aunty Maryam ɗin " shiga chiki sukayi gaba ɗayansu zaune a gefen gado suka samu Aunty Maryam dukawa kasa zahra tayi tace sannu dazuwa Aunty Maryam ya hanya " ganin Zahra ta duƙa yasa hiyana da lamrat da amrat suma suka ɗuƙa " diyana kuwa tana tsaye " ɗago kai Aunty Maryam tayi tana kallansu itama kamanninta ɗaya da Aiman sosai " bata amsa sannu da Zahra tamataba sai daima tsawar data dagawasu diyana ke kuma wacece, wasu kazamai'ne Zahra kika kawomin ɗaki  " murya na rawa Zahra tafara magana yan uwa na ne yayan kawuna.." a fusache Aunty Maryam tace get out of my room " da sauri Zahra tamike tarike hannun amrat tana faɗin kuzo muje, mikewa hiyana da lamrat ma sukayi suka nufi kofar fita, har sunkai kofa sai kuka juyo sukaga diyana a saye bata ko motsaba " diyana kizo mutafi mana " firgigit diyana tayi alamar dai tunani tashiga maganarsu che tadawo da ita daga duniyar tunani datashiga juyawa tayi tanufesu tana faɗin dan kinsamu munzo kaisheki zakiwani che mufita to wlh badan Zahra bama bazuwa zanyiba " what ?  Ke dan uban ki zo nan chewar Aunty Maryam " ba musu diyana ta juya takoma wajen Aunty Maryam ɗin " dago ido Aunty Maryam tayi ta kalli su zahra ai tunkan tayi magana Zahra taja amrat sukayi waje hiyana da lamrat suka rufa musu baya " 

dawo da kallanta kan diyana tayi from head to toe take kallan diyana, wayarta ta ɗauka ta danna kira jim kaɗan a ka daga kiran " kushigo iya abun datache ke nan ta katse kiran ta ajiye wayar  " jim kaɗan saika wayan nan ƴanmatan dasuke palo zaune dazun sun shigo  har ƙasa suka duƙa suna faɗin rankiya'daɗe kamu " chikin izza danuna isa Aunty Maryam tafara magana kumike ku bugammin yarinyar nan " diyana najin hakan ta watsa a guje tayi waje sukuma yan matan sukabi bayanta " Ajiyar zuchiya Aunty Maryam ta sauke san nan tace ai ko ban tambayaba nasan kune Aunty amarya ke bani lbr kuma danku nazo gidan nan ubanku zakuchi wlh sai kungudu da kafarku kafinsu Abba su dawo 

Diyana kuwa tana fita kai tsaye wajen security tanufa da gudu kai tsaye bayan shahram tanufa ta ɓuya yan matan na isowa suma tsaya chirkoh chirkoh " shahram da bajin hausa yakeba sai tambayar diyana yake what happened itakuwa diyana ba wani turanchin kirki takejiba " ganin yammatan suna kokarin kama diyana yasa shahram ɗaga musu hannu kana yachiro wayarsa yafara neman layin ogansa " tsayuwa yan matan sukayi shiru sunasan zuwa sukama diyana subuga dan inbasu bugetaba Aunty Maryam zata hukuntasu gashi sukuma suna tsoron sojojin nan ga Shahram fuskarsa babu annuri " shahram kuwa kiran layin Aryan yashiga yi wayar tanata ringing har sai da takusa tsinkewa tukun nan Aryan yayi picking call ɗin " a nitse shahram yafara masa bayanin abun dake faruwa chikin harshen turanchi " give har the phone abun da Aryan yache kawai " da sauri Shahram yamikawa diyana wayar, hannu tasa ta amshi wayar tamanna a kunne  tana faɗin hello " ajiyar zuchiya Aryan ya sauke yana faɗin ae daman nasan ke'che dan duk gidan nan ba mai neman faɗa sai ke meya haɗaki dasu , suwaye nema " murya na rawa tace wlh yaya Aryan babu abun dana musu kawai dan munje gaishe da Aunty Maryam ne sai tace wai mu kazamaine mufita mata a ɗaki shine nukuma nace dan tayi sa'a ma.... Bata karisa maganarba Aryan ya dakatar da ita dachewa ya isa haka bawa shahram wayar mika masa wayar diyana tayi bata san me suka tattau naba sai dai taji Shahram yace let's go  madam " gaba tayi yabi bayanta sukazo suka wuche yammatan " da sauri yammatan suka juya zasubi bayansu shahram ya dakamusu tsawa bashiri suka tsaya, har bangaren Ammi shahram ya kai diyana san nan yajuya yakoma bakin aikinsa  "
 yan matan kuwa jiki na bari suka juya suka koma inda suka fito chike da zullumin hukunchin da Aunty Maryam zata musu dan basu bugi diyana ba da sallama suka Shiga ɗaki waya suka samu Aunty Maryam keyi duƙawa sukayi gaba ɗayansu a kan guiwowinsu suna jiran hukunchi " bayan tagama wayarne ta ajiye wayar a gefenta afilli take faɗin bazanyi jayayya da kaiba Aryan amma kuma a chikin ruwan sanyi zan dafa yaran nan,  dankuwa Aunty amarya bata sonsu suna sata baƙin chiki nikuma duk abun da zaisa Aunty amarya baƙin chiki bana sonshi, kuma dole na kawar mata dashi shiru ta ɗanyi san nan tadubi yanmatan tace kutashi kutafi , " mamakine yaka masu mikewa sukayi suka bar ɗakin suka koma palo suka zauna

A bangaren diyana kuwa shahram na shigar ta ita ɓangaren Ammi ta kwasa da gudu tayi chikin palo kai tsaye ɗakinsu tanufa ba ko sallama tashige " Zahra na ganinta tamike tana faɗin bata bugeki bakoh diyana " dariya diyana tayi san nan tashiga basu lbr abun dayafaru " ajiyar zuchiya hiyana ta sauke san nan tace kai Allah yayiwa yaya Aryan albarka kekuma sai ki kiyaye bakinki " shiru diyana taɗanyi kamar mai tunani " Zahra ta dafata tana faɗin to tunanin me kuma kike diyana " dariya diyana tai san nan tache ina tunanin yau wache rana yaya Aryan yayi abun arziki  " tsaki hiyana taja san nan tace ni kunga tafiyata lokachin shirya abun ɓuɗa baki yayi tana kaiwa nan tafice " mikewa su lamrat sukayi gaba ɗayansu s Yanzu wasan zai fara k

Pls more comments an share



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 15*
            

Bayan sungama shiryawa kamsu abubuwar dasuke buƙata na buɗa baki nan take masu aikima suka fara shigo da kulolin abinchi suna jerawa a kan table ɗin  komawa ɗaki sukayi ɗaya bayan ɗaya sukayi wanka suka ɗauro alwalla hiyana diyana Zahra dogayen riguna na material sukasa maroon colour " lamrat da amrat kuwa riga da sket na atamfa suka sa kai tsaye palon mai martaba suka nufa danyin buɗa baki da sallam suka shiga suka wuche kai tsaye kan table zama sukayi suna jiran  time yachika a kira sallah " shiru suka zauna kowa da tunanin dayake " diyana che ta katse musu shirun dachewa Aunty Zahra sai narinƙa jin gidan ba ɗaɗi wlh saboda ba kowa ki kalla kan table ɗin nanfa da chika muke muna chin abinchi amma yanzu saura mukaɗai kai gaskiya na kosa su Abba sudawo " Zahra zatayi magana saitaji an daƙa musu tsawa daga bakin kofar shigowa " da sauri suka ɗago kai suna bin bakin kofar da kallo " Auntyn Maryam suka gani tsaye fuskar nan babu annuri ko kaɗan nan take jikin Zahra yafara ɓari dan tasan halin Aunty Maryam sarai " diyana kam kawar da idon ta tayi tachigaba da abun datake kamar bata san da wata Aunty maryam awajen ba "a nitse chikin sanyin murya hiyana tafara magana ina wuni Aunty Maryam " wani mugun kallo Aunty Maryam ta wurgawa hiyana batare da ta amsa gaisuwarba chikin tsawa tafara magama uban waya baku izin kurinƙa zuwa nan kuchi abinchi inachewa Aisha itace yar uwar ku a gidan nan " shiru sukayi basu che ko kalaba "  Aunty Maryam tachigaba dachewa to tunda wajen Aisha kukazo ku tsaya a iya ɓangarenta idan nasake ganinku a wani ɓangare na gidan nan, ba bangaren Aisha ba wlh sai na babballa yarinya kuzo kuficemin daga nan ko nashiga na muku mugun duka " tunkan takai karshen maganarta suka mike  gefenta sukabi zasu wuche " hannu tasa ta damkoh wuyar rigar diyana tana faɗin ke ki buɗe kunnenki ki saurare ni da kyau daga yau bawanda zai sake share bangaren Aunty amarya keche zaki rinƙa yi har nabar gidan nan,  ke bama shara kawaiba wankin kanana kayana wankin toilet mopping da yimini tausa kinajina bakinche ke bakida kunyaba to wlh zan gyara miki zama " diyana binta kawai take da ido  batace komaiba  tayi shiru  " su Zahra kuwa wuchewa bangaren Ammi sukayi jiki ba kwari " hannu Aunty Maryam tasa ta tsolewa diyana ido tana faɗin shegen ido kamar na mayu ai kedaga ganinkuma dangin mayune shiyasa aka faɗamin kun lashe zuchiyar kowa na gidan nan to nikam nafi karfinku " hannu diyana tasa tana goge idonta tana hawaye zafi idon yake mata sosai  " sakin rigar nata Aunty Maryam tayi san nan tace yanzun nan kije ki wanke toilet's dasuke bangaren Aunty amarya dukka san nan ki shiryamin abinchin buɗa baki " ba musu diyana tanufi bangaren Aunty amarya tana hawaye Aunty Maryam kuwa ta wuche chikin ɗakin mai martaba

Abangaren su Zahra kuwa palon Ammi suka koma suka zauna a kan sofa nan take Zahra tafara hawaye " hiyana tamike ta dawo kusa da ita tana faɗin lfy Aunty Zahra kike hawayen " chikin kuka Zahra tace diyana nakewa kuka wlh dan nasan tun da Aunty Maryam ta tsai da ita wani muguntar zata shirya mata " kiyishiru Aunty Zahra ninasan duk abunda Aunty Maryam zatawa diyana bazai kai kaso ɗaya chikin goma na wadda inna tamana ba dan haka ki daina damuwa ba irin muguntar da'bamuganiba chewar hiyana " mikewa Zahra tayi tana faɗin kuzo muje muyi buɗa baki gashi chan ana kiran sallah ba musu suka nufi kichin na Ammi " ruwa ko wannensu yafara sha san nan sukachi dabino " zahra tace ku zauna a palo kujirani bari naje palon mai martaba ba ɗaukoh mana abinchinmu " inkinje Aunty Maryam bazata bugekiba chewar hiyana " eh bazata bugeniba ai duk dokar datake kafawa ku take kafawa baniba nikam ai bata isa tahanani yawo a gidan babana ba tana gama faɗin haka yanufi hanyar fita .


KASAR SAUDIA ✈️

Gaba ɗayansu suna chikin masallahchin a nan sukayi buɗa baki bayan sungama sunyi sallane suka zauna hira " Ammi ta dubi Ummi tace Maryam fa tazo " yaushe tazo chewar Ummi "  yau tazo Mai martaba yabasu amsa " ya akayi wan nan karon tazo dawuri chewar Ummi " tsaki Aunty amarya taka san nan tace oh bakisan tazo daman koh to tazo kuma bayadda zakuyi da ita " mikewa DON yayi zai bar wajen " Aryan yace jirani muje tare, tare ya faɗin hakan yana mikewa tare suka jera suka nufi hotel ɗinsu " mai martaba yama Ammi magana da fillanchi Mikewa tayi tana faɗin Ummi muje Koh,  mikewa Ummi'n tayi dan tasan mai Martaba ne ya umarchi Ammi dasu tafi ɗaki dan baisan hayani kuma baisan subiyewa Aunty amarya  " Khalid Aiman Ahmad suma suka mike a tare sukabi bayan DON da Aryan " dawo da kallansa mai martaba yayi kan haidar da umar dake zaune basu tashiba,  to me kuke jira, ai tun bai karasa magana'ba suka mike suka bar wajen " 
dawo da kallansa kan Aunty amarya daketa chika tana batsewa yayi a nitse yafara magana wai meyasa Hajara bakyasan zaman lfy'ne eh meyasa kullun ke kike tada husuma a chikinkune tunfa kina amarya kike irin wan nan hali wadda kikazo kusamuma baki kyaletaba haka wadda tazo tasamekima  " zatayi magana  ya ɗaga mata hannu banasan inji komai daga gareki kawai abun danakeso karnasake jin wata fitina tatashi ," ke ko kunyar ƴa'ƴanku ba kyaji kitashi muje mu kwanta yaƙarisa maganar yana kokarin mekewa  hanyar ɗakinsu yanufa itama tamike tabi bayan'sa tanata chika tana batsewa


NIGERIA ✈️


Har wajen karfe 9 na dare diyana ta dawo ɓangarensu da kyar take tafiya saboda yinwa ko buɗa baki batayiba ko sallama babu ta shiga ɗakinsu " tasamu su Zahra har sunyi wanka sunyi shirin barchi "Zahra na ganinta ta mike tana faɗin sannu diyana san nan tayi waje da sauri " zama bakin gado tayi  ta ɗago blue eyes nata dasuka sauya izuwa ja saboda yinwa da gajiya, tana kallan hiyana dake tsaye tana mata kallan karin bayani takeso " diyana zatafara magana saiga Zahra ta dawo hannunta ɗauke da plate ɗin abinchi da cup mai ɗauke da tea mikawa diyana tai nantake ta karɓa tafara chi " zama sukayi kusa da ita shiru itakuwa sai ɗura abinchi take hannu baka hannu kwarya  

Wayar Zahra tasoma ringing da sauri amrat dake rike da wayar tamiƙa mata my lovely bro ne yabayyana a kan screen ɗin wayar da sauri Zahra tayi picking call ɗin tare dasa wayar a H-free tana faɗin hello yaya khalid " wani dogon numfashi Khalid yaja tare da sauke ajiyar zuchiya kana yace my lovely sister ykk ya makaranta " muna lfy makaranta alhamdulillah Zahra zata sake magana taji " diyana takwache wayar tana faɗin yaya Khalid ina yaya Aryan dan Allah inasan inyi magana dashine " baki buɗe'su Zahra ke kallanta " Khalid kuwa chewa yayi ai daman dan ke nakira shima magana yakesanyi dake " yauwa to bashi,"miƙawa Aryan dake zaune kusa dashi wayar Khalid yayi " ansa Aryan yayi yasa a kunnensa yana faɗin hello " yauwa yaya Aryan ina wuni " lfy lau y school " 
khalid kuwa miƙewa yayi yana faɗin inazuwa hannunsa Aryan yakama yamai'dashi ya zauna yana harararsa  " yaya Aryan wlh yau wan nan Aunty Maryam ɗin takusan kasheni chewar diyana " a zafafe Aryan yace what ? bana rabakuba mekuma yasake kai ki wajenta " turo baki tayi kamar tana gabansa tafara bashi lbr abun daya faru daga farko harkarshe " shiru yaɗanyi yana tunani daman yasan za'ayi hakan tunda yaji Aunty Maryam tazo ba lokachin zuwansuba yasan da dalili yayi nisa chikin tunani " muryan ta ta katse masa tunanin dacewa " yaya Aryan dan Allah kudawo kaga idan kun dawo Abba bazai bari tarinƙa buguna ba " karki damu saura kwana 10 mu dawo kuma I next week Aunty farida zatazo domin tarbarmu idan Aunty farida tana nan bazata bari a muku komaiba,  amma duk dahaka zanmata magana " to shike nan sai dasafe " murmushi kaɗan yaɗanyi kafin yace bakyasan hira danine kikechemin sai da safe "  khalid dake zaune kusa dashi  ya ɗago a sukwane yana kallansa fisge hannunsa yayi daga rikon da Aryan yamasa yamike yana faɗin idan kagama hirar, kasameni a ɗaki kaga tafiyata " harara Aryan ya wurga'masa  " khalid bai bita kansaba yayi waje
Diyana kuwa dariya tai san nan tace to ai abinchi nake chi nifa yanzu nake buɗabaki " shiru yayi zuchiyarsa tana masa zafi sosai yafara tunanin matakin daya kamata ya ɗauka wan nan wani irin zalunchi'ne yarinya tayi azumin san nan kijib'ga mata wan nan uban aiki kuma ki hanata buɗa baki yanzu kusan karfe 10 nadare wai batayi buɗa bakiba, dole na ɗau mataki " jin yayi shirune yasa diyana cewa yaya Aryan kodai kayi barchine " aa banyiba kawai ina ɗan tunanine " to shike nan sai anjima bari nagama chin abin china " ok kichi a hankali dai kuma banda chin fruits dayawa dan inchikin'ki yafara chiwo kinga bamunan bare namiki allura " dariya tayi san nan tace to bazan chiba " ok kawai yace san nan ya katse kiran ya ajiye wayar a gefe ya dafe kansa yana tunani  " dayaga dai tunanin ba wata mafita, sai yaike ya nufi kan katafaren gadansa ya konta yajawo wayarsa yafara latsawa 


Bayan diyana tagama chin abinchinta tamike tanufi toilet wanka tayi tafito daure da towel kayan barchi tasa doguwar riga mai siririn hannu yar shafal mara nauyi kwanche ta iske su Zahra sunata yar hirarsu,  dayake yanzu su amrat ma sun dawo ɗakinsu, saboda  suna tsoro tunda ba kowa a gidan sai suka haɗu suka chure waje guda 
Hayewa samar gadon nasu tayi itama tana faɗin Aunty Zahra kunna mana kallo " to kawai Zahra tace tare da dauko wayarta dake gefenta ta shiga gallery tana kokarin neman film sai taga kira yashigo " da sauri tayi picking call ɗin tana faɗin yaya Khalid bakayi barchiba " eh banyi barchiba ya'za'ayi nayi barchi bamuyi wayaba " Zahra zatayi magana sukaji an banko kofar ɗakin nasu da karfi gaske " zubur suka mike gaba ɗayansu har sai da wayar Zahra tafaɗi kasa dan tsorata dasukayi   " a zafafe Aunty Maryam ta shigo chikin ɗaki kai tsaye wajen diyana tanufa damkoh wuyarta  tayi tafara bugunta ta ko ina "  diyana tafara ihu " nizaki haɗa faɗa da ɗan uwana koh to wlh yau sai na kasheki,  tun danake dashi baitaba kirana a wayaba amma yau saboda'ke sau biyu yana kirana bugunta Aunty Maryam keyi tana surutai  "  diyana kuwa sai ihu take "  hiyana naganin Aunty Maryam na kokarin kashe diyana da gaske ta kwasa a guje tayi wajensu tana kokarin kwache diyana a hannunta " hankaɗe ta Aunty Maryam tayi da karfi ta tafi ta bugu da bango nantake kanta yafashe " ihu mai karfi Zahra tabuga tayi kan hiyana tana kiran su nanta " lamrat da amrat kuwa sai kuka suke " duk da raunin da hiyana taji bai hanata sake mikewa a zafafe tayi kan Aunty Maryam tana faɗin karki kashemin ƴar uwa dan allah " wani bugu Aunty Maryam tasake kaiwa hiyana a baki " kukan kura hiyana tayi a fusace ta damki wuyar Aunty Maryam ta baya " bashiri tasaki wuyar diyana ta juyo ta damki hiyana tashiga bugu " da gudu Zahra tazo ta duƙa takama kafar Aunty Maryam tana rokonta " dan allah Aunty Maryam kiyi hakuri ki kyalesu wlh marayune basu da uwa basu.. Zahra bata karisa ba taji saukar mari a faskar ta a zafafe Aunty Maryam tace. Kifita a ɗakin nan zahra'u kokuma na haɗa dake " mikewa Zahra tayi tana kuka takama hannun amrat da lamrat tace muje " kwache hannunta lamrat tayi tayi gun Aunty Maryam da gudu tana faɗin dan allah ki kyalemin yan uwana haka " kafa Aunty Maryam tasa ta amɓare lamrat tafaɗi kasa tana kuka " da kyar diyana tamike tana ɗingisa kafa ta karisa wajen ta duka gaban Aunty Maryam tace ninamiki laifi basuba kiyiwa Allah kisakemin yar uwata ni ki kasheni inkinaso " juyowa tayi ta damki wuyar diyana ta damkoh hiyana ta haɗe kansu ta buga da karfin gaske wani kara suka sake a tare  " Zahra da amrat dake tsaye a bakin kofa da gudu suka dawo chikin ɗakin " Aunty Maryam kuwa duk da hakan bata kyalesuba sake damkar gashin kan diyana tai tana janta a kasa har zuwa wajen mirrow tasa hannu kan mirrow ta dauki wani kwalbar turaren humra zata buga mata ke nan taji anche STOP chikin tsawa  da sauri ta ɗago kai idanunta suka sauka akan...✍️✍️✍️




More comments an share pls 🙏
 




*💫STAR LADY💫*27*

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 16*




Idanta ya sauka, a kan shahram dake tsaye fuskar nan tamkar an aiko masa da mutuwa babu alamar wasa a tattare dashi " sakin diyana,  tayi tana mai da nunfashi " karisa shigowa ɗakin yayi yana faɗin get out yayi maganar yana nuna Aunty Maryam " kallan raini ta tsaya take masa daga sama har katsa dogon tsaki taja,  tanunashi da ɗan ya tsa tace kai karamin marakunya ni kake chewa nafita to kashirya karɓan hukunchi " shikam Shahram ko ajikinsa, dan daman bajin hausa yakeba bare yaji me tache, sai ma kallan Zahra dayayi yace all of U follow me yana gama faɗin hakan yajuya ya koma bakin kofa ya tsaya " wuchewa Zahra tayi taje ta taimakawa diyana tamike " Aunty Maryam na tsaye suka raɓa gefenta suka wuche, tanasan ta damkoh diyana tachi gaba da bugu kuma tana tsoron yadda taga fuskar Shahram ba wasa hakan yasa ta fiche a ɗakin a fusache " Shahram ganin sun mike sun nufosa yasa yayi waje, suka bi bayansa bai tsaye wajen motochin gidan suka nufa da kansa ya buɗe musu marfin family car suka shiga gaba ɗayansu " shima shiga yayi yaja motar da gudun gaske nan take security dake tsaron gate suka wangale masa gate ɗin " dagudu ya danna hanchin motar yayi waje doguwar titi yamiƙa dasu gudu yake sosai chikin ƙanƙannin lokachi suka isa wani katafaren asibitin DON dake  kan titin zoo road " suna parking ya fito yabuɗe musu motar bayan sun fito yayi gaba suƙa bishi a baya " diyana daker take ɗinkisa kafa " hiyana kuwa goshi sai jini yake, gaba ɗaya jinin ya wanke mata face " kai tsaye office ɗin baban dr yanufa " security dake tsaye a bakin office ɗin suna ganin Shahram suka shiga sara masa kamar sunsan juna buɗe musu kofar office ɗin sukayi suka shiga " babban dr naganin Shahram yamike yana miƙa masa hannu, miƙa masa hannu Shahram ma yayi suka gaisa san nan yakora mara bayani a kansu diyana " da sauri dr peter ya ɗauki waya yakira nursing " nursing na shigowa dr peter yabata umar a kan ta tafi dasu diyana tabasu gado gashi nan zuwa yadubasu " har ɗakin da a ka kaisu sai da Shahram ya bisu sai da ya tabbatar sun fara samun kulawar Dr san nan yafito ya nufi motarsu yatayar yanufi gd

A bangaren Aunty Maryam kuwa tana komawa ɗaki ta ɗau'wayarta tafara kiran layin Aryan dan taji ko shiya aiko Shahram amma ba'a ɗagaba sai data kira miss call 10 amma ba'a ɗagaba san nan ta hakura ta ajiyewayar tana ta surutai wlh Aryan kazo gaɓar da bazan kyalekaba, ina ruwanka dan nabuge yaran nan toma waya faɗamaka ina bugunsu dole na binchiko ta ina kasamu lbr, haka dai take ta surutun'ta 


Yadda akayi Aryan yasamu lbr Aunty Maryam na bugunsu diyana har ya'turo Shahram

Lokachin da Khalid ke magana da Zahra yaji tayi shiru sai hello, hello kawai yake amma ba amsa har zai katse kirankuma sai yaji ihu, nantake hankalinsa yatashi yamike yanajin yadda Aunty Maryam ke bugunsu, da sauri yanufi ɗakin Aryan rike da wayarsa yana zuwa yamikawa Aryan wayar " muryan Aunty Maryam sukaji tana faɗin nizaki haɗa faɗa da ɗan uwana," bai taɓa kirana a wayaba amma yau yakirani har sau 2 saboda ke " a fusace Aryan yayi wurgi da wayar Khalid yamike, nan take fuskarsa ta Sauya idon nan suka chanza sukayi jawur dasu kamar an watsa barkono, wayarsa ya ɗaukoh sai huchi yake kiran layin Aunty Maryam ɗin yafarayi Amma shiru shiru har 3 time rai a ɓache yayi wurgi da wayar,  yanufi hanyar fita " da sauri Khalid yarikesa dan ya lura baya chikin hayyachen'sa inazakaje Aryan chewar Khalid " Nigeria zanje mana " dariyane sabo kuɓchewa Khalid amma sai yadanne yace ai kokatafi yanzu ba yanzu zaka isaba kafin kaje kuma duk abun da zai faru yarigada yafaru,  yanzu dai kakira wani daga chikin security nan suje su kashe wutar, ai tun Khalid bai kai karshen magana ba "Aryan yanufi wayarsa da sauri ya ɗaukoh yafara kiran layin Shahram, " Shahram nayin picking call ɗin " Aryan yabashi umarnin yaje ka dakatar da Aunty Maryam daga bugun su diyana datake san nan ya ɗaukesu ya kaisu asibiti, yana gama faɗin haka ya katse kiran ya zauna a bakin gado ya dafe kai 
Kusa dashi Khalid yazo ya zauna ya sa hannu ya dafa kafaɗarsa zaiyi magana ke nan sukaji sallamar DON 

Kallonsu DON yake sosai kamar mai nazarin wani abu a fiskokinsu  wuchewa yayi ya zauna a bakin gadon " calmly yafara magana me yake damunka Aryan wan nan shine tambaya ta karshe da zanmaka idan baƙa faɗaminba kasan sauran " kakalo murmushi dole Aryan yayi yana faɗin wai meyasa kakesan saka wani tunanin banza a zuchiyar kane, nifa nafaɗama kwanan nan ina yawan fama da chiwon kaine amma bari namaka mai kankat wlh Allah nikam bawani abun dake damuna,  kawai jinake tamkar a takure nake banajin daɗin ƙasar  nan narasa meke min daɗin banda haka wlh babu wani abun " jinjina kai kawai DON yayi batare dayache komaiba, dan yasan iya gaskiya ke nan Aryan yafaɗa masa dan bayadda za'ayi Aryan yayi rantsuwa a kan karya kuma tabbas zai iya shedan Aryan a ko ina baya faɗin maganar da ba hakaba, to amma tabbas yana da damuwar da shi da kansa baisan da itaba " ganin DON yayi nshirune yasa gaba ɗayansu suka dawo kusa dashi, dafa kafaɗarsa Aryan yayi yana faɗin baka yarda da magana ta bane " juyo green eyes ɗinsa yayi kan face ɗin Aryan tare da ɗanyin murmushi gefen fuska nayarda mana na yarda da duk abun da kafaɗa domin baƙa taba yimini karyaba matsalar ɗaya a nan shine tabbas akoi abun da kedamunka wanda kai da kanka bakasan meneneba " zuba musu ido khalid yayi yana tunani a chikin ransa gaskiyane DON kachi su nanka Safras indai wajen basirane kai karshene ba abanza mai marbata ya dage sai kai za abawa sarauta'ba, yayi nisa chikin tunani sai yaji Aryan nataɓasa firgigit yayi ya ɗago yana kallonsu duk sun zuba masa ido "  lfy Khalid kodai kaima kana da damuwane DON yajefo masa tambaya " aa bani da damuwar komai nikam kawai tunanin meke damuna ɗan uwana nake " nifa babu abun dake damuna na faɗa muku "  DON zaiyi magana wayarsa tafara ringing hannu yasa chikin aljihunsa ya fitar da wayar, sunan Sadiq yagani ta bayyana a kan screen ɗin wayar dogon tsaki yaja tare da jefar da wayar a kan gado "  da sauri Khalid yasa hannu ya ɗauki wayar yana duba wanene yakira DON yake jan tsaki haka ganin sunan Sadiq yayi a kan screen ɗin bai yi mamakiba,  dan DON yaki ɗaukar wayar Sadiq dan kuwa Sadiq yayi aure " murmushi yayi yana kokarin picking na call ɗin kiran tayanke  chire pin na wayar  yayi dayake yasan pin na wayoyinsu dan ba abun dasuke ɓuyewa juna 
Kiran layin Sadiq ɗin yafarayi wayar nafara ringing Sadiq yayi picking call ɗin yana faɗin yau wace rana nayi sa'a an ɗauki wayata " dariya Khalid yayi san nan yace ai kasan shikam bazai ɗauki wayarkaba  " my Khalid ykk " lfu lau ya amarya suhaima " first dai yanzu albishirinka " da sauri Khalid yace goro " my baby ta haifamin baby boy yanzun nan daman shi nakira nafaɗa muku " wow my man inatayaka murna bari nabawa Aryan ma yatayaka murna " Khalid bai jira amsar Sadiq ba yamiƙawa Aryan wayar " satar kallan DON Aryan yayi yaga bama su yake kalloba yasa hannu ya'karɓi wayar yawa Sadiq congrat san nan yace ga DON nan, kuma da gangan yayiwa DON ɗin haka dan yasan idan shi yamiƙawa DON wayar tofa dole zaikarɓa kuma gaskiya yanasan DON yataya Sadiq murna kodan halakchin da Sadiq ɗin yamusu, yanzu matarsa na aihuwa tun bai sanar da kowaba yafara sanar musu, aiko basaso dole zasu danne sumasa congrat " karbar wayar DON yayi badan yasoba kawai dan bazai iya kwasale Aryan a idon kowa bane 

Congratulations inatayaka murna chewar DON " da murna Sadiq yace thanks ykk y gd " lfy yasu mom " alhamdulillah Sadiq yabashi amsa " ok kawai DON yace san nan ya katse kiran ya ɗago green eyes nashi yana kallonsu " zuba mishi ido Aryan da khalid sukayi sosai suna kallansa Khalid na mamakin hali irin na  DON "  kallon me kukemin haka " murmushi Khalid yayi san nan yace kyau kamana mana shiyasa muke kallanka " mikewa yayi yana faɗin to aiki yasameku kuda kukasanma me kyau yake nufi, yana gama faɗin hakan yayi waje " dariya Khalid yayi sosai san nan ya dubi Aryan yana faɗin wai gaji DON baisan me kyau ba kajimin iskachi " tsaki Aryan yaja yana faɗin kai ma kake biye masa ae,  to daman inban da kai da neman magama ina DON yasan maka wani abu Wai shi kyau,  ko kuma mara kyau ai shi inba Bom, bindiga, bullet,ba to bawani abun dayasani mai kyau " mikewa Khalid yayi yana faɗin good night anjima kakira Shahram kaji ya ake chiki " da sauri Aryan yafara lalubar wayarsa yana faɗin yanzu dai wani anjima kuma,  wan nan ke nan


Nigeria DON hospital


Washe gari misalin karfe 8 dinaya na kwanche a gado da drip a hannu " hiyana ma kwanche a nata gadon ansamata bandeji a goshi " sai lamrat da amrat dake zaune gefen gadon hiyana,  zahra kuma tana kan kujera plastic dake chikin ɗaki " shiru sukayi gaba ɗayansu na tsawon lokachi " sallama sukaji a bakin kofar ɗago kai sukayi gaba ɗayansu Shahram suka gani tsaye shida Dr Peter karisa shigowa chiki ɗakin sukayi suna tattaunawa " mikewa Zahra tayi daga kan kujerar ta koma gefen gadon diyana tana kana tacewa Shahram,  uncle have a seat " thanks dear san nan ya zauna a kujerar " miƙamasa takardar magani Dr Peter yayi san nan ya juya yanufi waje " Shahram kuwa wayarsa ya ɗaukoh daga aljihun wandansa yafara kiran layin Aryan,  har saida wayar takusa tsinkewa tukun nan a ka ɗaga 
Chikin girmamawa Shahram yafara magana hello sir good morning " morning how are U " am fine sir " where is she da sauri Shahram ya mikawa diyana wayar " hannu tasa ta amsa ta ƙara a kunne hello yaya Aryan ina kwana " lfy y jiki " da sauki ina Ammi dan Allah yaya Aryan kafaɗawa Ammi ta dawo dan Allah wlh tsoran Aunty Maryam nakeji, nikam Ammi tazo taje tasayar da shanun Bappa gaba ɗaya tasaya mana gida mukoma " shiru kawai Aryan  yayi yana sauraron'ta har ta kai karshe " chikin sanyin murya yafara magana karki damu ae munkusa dawowa saura 9 days ne kawai kuma kinga nafaɗa miki Aunty farida zatazo next week idan Aunty farida na nan babu abun da Maryam zata muku, yanzuma bazan barku hakaba kinji bazata sake taɓakuba  " to shike nan Amma pls yaya Aryan ka haɗani da Ammi da Abba mana " mezakiche musu idan na haɗaku " zanfaɗamusu abun da Aunty Maryam tamana " aa to bazan haɗakuba gaskiya " ayya yaya Aryan kayi hakuri ka haɗamu tunfa shakaranjiya da Ammi ta kiramu ta wayar Aunty Zahra bamu sake maganaba, jiyama ina wanka  naji su hiyana na magana da ita, kafin nafito kuma sungama magana pls ka haɗani da ita takarisa maganar kamar zatayi kuka " to zan haɗaku amma saikin min alƙawarin bazaki faɗamusu komaiba gaisawa kawai zakuyi " da sauri tace eh namaka alƙawari wlh bazan faɗaba " ok to yanzu bawasu Zahra wayar bari naji yanasu jikin idan mungama magana sai na haɗaki dasu " to kawai tace san man tamiƙawa zahra wayar " karɓa Zahra tayi suka gaisa san nan tamiƙawa hiyana " ansa hiyana ma tayi suka gaisa ya tambayeta jikinsu tace da sauki san nan yace to tabawa diyana wayar, miƙamata wayar hiyana tayi " da sauri diyana ta ansa tana faɗin hello " idan ruwan da a'kasamiki yaƙare Shahram zai maidaku gd, dan na chanza shawara zan ƙira mijin Aunty farida na faɗamasa ya bar Aunty farida tazo goɓe kinji " to shike nan yaya Aryan amma kuma, kuyi sauri ku dawo dawuri tayi maganar a shagwaɓe " meyasa kikesan mu dawo dawuri kodai kina san ganina' ne " eh ba kai kaɗaiba dukkan kuma inasan ganinku, gd babu daɗi dabaku nan " shiru yaɗanyi kafin yace ok inshaa Allah munkusa dawowa ae " to Allah ya dawo daku lfy tana gama faɗin hakan bata jira amsar shiba tamiƙawa Shahram wayarsa " koda Shahram ya ansa wayar yasa a kunnensa, sai yajiyo Aryan na faɗin nima inakewarki my sister ina kewar coffee ɗinki mai daɗin nan" a sukwane Shahram ya miƙa mata wayar  kallansa diyana ta tsaya take damamaki batare da ta ansa wayar'ba " mikewa Shahram yayi yazo har kusa da ita yasa mata wayar a kunne " muryan Aryan taji yana faɗin sister ba kyajinane " hannu tasa ta ansa wayar tana faɗin inajinka yaya Aryan  "to ae naji inata magane kinyi shiru " eh dazun banji me kafaɗa'bane " ok to shike nan Shahram zai jira idan ruwan da a'ka ƙaramiki ya ƙare  zai mai daku gida, nurse ɗaya zata biku tachigaba da kula daku " to yaya Aryan makaranta'fa " makaranta sai kunji sauri ba naji kun gama exam bama " laaa waya faɗamaka to " zuchiyata mana itace tafaɗamin " to zuchiyar'ka tafaɗi gaskiya mungama " to bazaku sake zuwaba sai  ranar da za'ayi hutu yanzu kam ku huta kuyi jinyar jikinku " to ka haɗani dasu Ammi mana " sai da daddare idan kun koma zankira layin Zahra na haɗaku amma karki karya alƙawari'fa " to bazan karyaba " ok sai munyi waya anjima koh, yana gama faɗin hakan ya katse kiran " jin ya katse kiran yasa ta mikawa Shahram wayarsa,

Sai 12 :45 a ka sallamesu daga asibiti hiyana dai ba a chire mata bandejin'ba, saboda sosai taji chiwo a goshinta dan har ɗinki 6 a kamata awajen " Shahram dakansa yabuɗe musu motan suka shiga tare da nurse ɗaya kai tsaye gd Shahram ya wuce dasu " yana parking yafito ya buɗemusu motar suka fito, daka gansu kaga wayanda suka sha wahala, har ɓangaren Ammi Shahram ya rakasu sai dayaga shigansu palo tukun nan yajuya yakoma bakin gate 
Suna'shiga ɗakin'su suka nufa wanka suka farayi ɗaya bayan ɗayan suka sanya dogayen riguna abaya baki " hiyana kam dakyar tayi wankan saboda zafin da kanta ke mata shiru suka zauna " jim kaɗan Zahra tamike tana faɗin ina wayata bari nakira masu aikin sukawo mana abinchi nanfa tashiga nemar wayar'ta, chan gefen drawer ta gano wayar, da sauri ta ɗauka ta duba taga wayar ta mutu ba charji jonata a charji tayi san nan ta kunnata tafara neman layin binta 
Bugu ɗaya binta ta ɗaga Zahra tabata umarni kan ta kawo musu abinchi " 

Chikin kankanin lokachi saiga binta tashigo da sallama, hannunta ɗauke da babban trey mai dauke da kulolin abinchi da plate a kai a tsakiyar ɗakin taajiye san nan ta gaidasu tafita " saukowa kasa zahra da diyana sukayi " Zahra ta dubi nurse ɗin tace kizo kichi abinchi sister, bamusu itama nurse ɗin ta saukoh " kuma kunajiran saina kirakune? Zahra tayi maganar tana kallansu lamrat " jiki ba kwari suka tsaukoh, " Zahra da kanta tayi sarving na kowa kallan, hiyana dake zaune tayi ke bazaki zo muchi'bane " Aunty Zahra nifa bazan iya chin komai"ba dan kaina chiwo yake min sosai " aa hiyana karmuyi haka dake kawai ki saukoh ki daure kichi ko kaɗanne " hiyana badan tasoba haka ta saukoh suka fara chin abinchin,  jitake kamar magani takechi dan bakinta ba tes ko kaɗan 
" Bayan sungama chin abinchi ne nurse ta basu  magunguna san nan suka haye gado " zahra a ita da hiyana a gadon'su, dayana da amrat da lamrat suma a gadon diyana " nurse nasu kuwa suka kaita ɗakin'su amrat,  suna kwanchiya ba jimawa barchin wahala ya ɗaukesu


SAUDIA 


Wayarsa ya ɗauka yafara neman layin Aunty farida ringing ɗaya ta ɗauka " hello my bro " na'am lovely Aunty ykk " lfy lau yasu Abba ya shirye shiryen dawowa " alhadulillah ina junior " yafita da baban'sa " ok Aunty farida daman ina san magana da'kene "ok to inajinka " sonake kije gd gobe " ae sai ranar Monday zantafi amma meyasa kakesan naje dawuri " Aryan zai sake magana idonsa suka sauka chikin green eyes wato DON tsaye yake a bakin kofar shigowa betroom ɗin, sanye yake da suite ash colour, bakaramin kyau yayi yatara gashin kansa ya ɗaure,  fuskar nan tamkar an aiko masa da mutuwa ya harɗe hannu a kirji ya zubawa Aryan green eyes nan nashi " hello bro baka jinane " sorry lovely Aunty inajinki wlh hankalina yatafi wajen DON ne " ok to injinka meye dalilinka nacewa naje'gidan gobe " babu komai kawai dai inasan kijene " jinjina kai Aunty farida tai kana tace ok badamuwa zanyi magana da dadyn junior idan yadawo " ok kawai Aryan yace batare daya jira kozatace wani abuba ya katse kiran " 
dawo da kallansa yayi kan DON yafara magana to meya tsayar da kai kuma a bakin kofa " dogon numfashi DON yaja tare da sauke ajiyar zuchiya a hankali yafara takowa izuwa chikin ɗakin gefen gado ya zauna yana fuskantar Aryan " ayayin da Aryan ɗinma shiyake fuskanta shiru sukayi na ɗan lokachin suna kallan juna " DON ne ya katse musu shirun dacewa munyi magana da Aunty farida tace tafara magana da Abba a kan maganar sarauta amma kanaganin Abba zai chanza ra'ayi kuwa " gaskiya dakamar wuya Aryan yabashi amsa a takaice " mikewa yayi ya kwanta a gadon yana kallan Aryan ɗin batare dayace kalaba " Aryan kuwa dayaga kallanda DON yake masa kamar kallan tuhumane, sai yamiƙe yana faɗin bari na dubo khalid yanufi hanyar fita " meyasa kake guduna ne yanzu Aryan " chak Aryan ya tsaya kirjinsa na bugawa da karfi a hankali ya juyo idansa suka sauka chikin na DON dan kuwa ya tsaresa da ido sosai yake kallansa " meyasa zanrinƙa gudunka kuma " wan nan dai kai kasan dalilin amma dai ninasan ba haka kawaiba " nibawani gudunka danake yama za'ayi kace ina gudun kane bayan tare muke komai, har chin abinchi, wanka da barchine kawai ke rabamu, " ok to yanzu dakamike ina zaka,  eh bawai bani da aikin yi banefa nabari nazo wajenka muyi hira amma ko kara bakaminba kamike wai barika dubo khalid 
Shiru Aryan yayi yana tunani kuma yagane kuskuren dayayi nacewa bari yadubo Khalid dan haka sai yajuya ya dawo chikin ɗakin kusa da DON ɗin yadawo ya zauna yana faɗin am sorry bro  " jinjina kai kawai DON yayi batare dayayi maganaba " shiru sukayi gaba ɗayan'su kowa da abun dayake tunani 


YOLA NIGERIA ✈️

Zaune take a tsakar gida ta buga uban tagumi sai tunani take tayi nisa chikin tunaninta taji ana Sallama a kofar gd, amsa sallahar tayi san nan tamike ta ɗauko mayafi ta rufa a kanta tayi waje,  tana fita tachi karo da bello " aa Bello kaine mai doka sallama haka to ya akayi " eh nine inna inawuni " lfy meyakawoka " daman goggon'su hiyanace wadda ta ɗaukesu ta aiko wani yazo yafaɗamin intattara dabbobin'su hiyana na haɗa da nawa narinka kula dasu bayan Sallah zasu zo " wani tsalle inna tabuga tana faɗin banga uban daya isa ya taɓa dabbobin nan ba wlh " to inna ae'ga yan sakon nan basu tafiba sai kifaɗamusu " juyawa inna tayi tana kallan inda bello ke nunawa, wasu sojoji taga guda 3 sanye da kaki, fuskar nan tasu babu alamar wasa aguje inna takwasa tayi chikin gida " juyawa bello yayi yanufi garken dabbobin yana faɗin muje " bin bayansa sojojin suka har zuwa wajen dabbobin " ƙirga dabbobin suka shigayi bayan sun gamane "bello yadubi sojan yace a nawa lissafin dukka dabbobin banda kaji, da zabbin, nan iya shanu, da raguna, da awaki, 1007 ne amma kufa nawa kuka samu a naku lissafin " ɗayan daga chikinsu yace 1005 nasamu dayanma yace 1005  " kai kumafa bello ya tambayi ɗayan da baiyi maganaba " amsata iri ɗayane danake 1007  shiru sukayi chankuma Bello yace to kozamu sake ƙirgawane " aa basai mun sakeba a barshi a lissafinka domin ina da tabbachin shine dai dai, dan kafimu iya ƙirga dabbobi,  nasan kana kirga wayanda sukafi wan nan yawa to ni da kyarma na iya irgawa wlh sai rikiitani suke " murmushi kawai bello yayi san nan yace to muje wajen kajin nan kuma " no kaji da zabbi madam tace ka ɗauka bata buƙata " nan take fara'a ta bayyana a fiskar bello sai godiya yake zubawa har suka fito " sojojin sukaje suka shiga motar'su suka kama hanya " bello kuwa da sauri yajuya yanufi gd dan yafaɗawa innnar'sa abun dake faruwa 


KANO STATE

Misalin karfe 4 hiyana ta farka daga barchi tana duba time da sauri tafa tashin'su Zahra dan ko sallar azhar basuyi'ba, koda suka tashi sai faman yamutsa fuska suke " hiyana naganin sun tashi tamike tanufi toilet danyin alwala zahra kuma wayarta tachiro daga charji ta kunna wutar screen ɗin nanfa tasamu miss call kusan 17 yaya Aryan 4 miss call, yaya Khalid 3 miss call, Ammi 3 miss call, mai Martaba 5 miss call, yaya Yusuf 2 miss call, "  tunani tashiga'yi wazata fara kira saiga wata kiran tashigo tana dubawa taga yaya Aryan , da sauri tayi picking call ɗin tana faɗin hello yaya Aryan ina wuni " daga ɗayan ɓan garen Aryan yace lfy ykk yajikinku " da sauki barchi, mukayine shiyasa kakira bamu ɗagaba " ok ina sauran'suke " miƙawa diyana wayar Zahra tai" ta ansa taba faɗin wanene  " idan kinsa a kunnenki ae zakiji koma wanene Zahra tabata amsa " kara wayar tayi a kunnen'ta tana faɗin hello " ya jikin naki " laaa yaya Aryan daman kaine jiki ba sauki gaskiya dan har yanzu zafi kaina da kirjina yakemin sosai " saura kaɗan ya kwashe da dariya amma sai ya danne yace to inshaa allah zai daina yimiki zafi kinji " diyana zata sake magana sukaji an turo kofar ɗakin nasu da farfi anshigo a razane suka ɗago ganin Aunty Maryam yasa diyana fasa...✍️



Pls more comments an share 🙏








💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 17*





Ganin Aunty Maryam yasa diyana ta fasa ihu tana faɗin,  dan Allah Aunty Maryam kiyi hakuri karkisake bugu wlh yanzuma chiwo kaina kemin, " a zafafe Aryan yamike tsaye yana faɗin sister kibata wayar kinitsu" ina diyana batama jinsa ihu kawai take tana surutai  " zama Aunty Maryam tazo tayi a gefen kadan nasu tana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya  " hiyana ma jin diyana tayi ihu tana faɗin kar Aunty Maryam tabugeta yasata tafito daga toilet da gudu, " Zahra ma mikewa tai tana kallan Aunty Maryam ɗin " da gudu nurse nasuma tafito daga nata ɗakin tashigo nasu, tsayuwa tai daga bakin kofa tana kallan'su " amrat da lamrat kuwa rungume juna sukayi suka rufe ido " sai magana Aryan keyi tacikin wayar amma shiru dan diyana tama chire wayar daga kunnen'ta " ina wanchan dan iskan ya kaiku jiya da'baku kwana a gidan nanba chikin tsawa tayi maganar  " tsagaita kukan da take diyana tayi tunda taga Aunty Maryam ɗin bata fara bugunsuba, san nan murya na rawa tafara magana asibiti ya kaimu, " shiru Aryan yayi yana sauraron maganar tasu" waye jiya a chikinku yasanar da Aryan na bugeku" har suna haɗa baki wajen chewa wlh bani bace bani bace "  shoothup idan baku kukagaya masaba taya akayi yasani " shiru sukayi gaba ɗayansu "  ke tashi kije ki wanke toilet's ɗin bangaren Aunty amarya dukka san nan ki wankemin kana nan kayan dana chire ɗazun inkin gama ki wuche kitchin ki shiryamin abun buɗa baki tayi maganar tana nuna diyana " mikewa diyana tayi san nan ta'ajiye wayar Zahra dake hannunta,   tanufi hanyar fita tana faɗin to " itama Aunty maryam ɗin mikewa tai tana hararar su hiyana tai waje " girgiza kai kawai Zahra tai tana hawaye " hiyana ta tako a hankali tazo ta zauna kusa da zahra tashiga rarrashinta " chikin ɗakin nurse ɗin nasu ta karisa shigowa itama ta zauna, suka fara sharewa Zahra hawaye " dan Zahra akoi saurin kuka " amrat da lamrat ma suka dawo kan gadon suka zauna " 

Shiru sukayi kusan 30 mnt " hiyana tana kokarin mikewa ke nan sai ga diyana tashigo ɗakin " da mamaki a fuskar Zahra ta mike lfy diyana kika dawo, kodai har kingama aikin ne, zahra ta tambaya murya na rawa " aa nidai kawai ina wankin toilet ne, saikuma Aunty Maryam ɗin tace nabari natafi ɗaki, shine nadawo " baki buɗe zahra tace kai to ya akayi tace kidawo, anya kinji metace ta kyau kuwa " eh mana Aunty Zahra naji wlh diyana tabata amsa " hiyana dake tsaye tace to saikutashi muyi sallah ae tunda kin dawo ga lokachi ya kure " mikewa sukayi baga ɗayansu har nurse nasun " diyana tashige toilet nasu" lamrat kuma tafito tanufi toilet na ɗakinsu " zahra kuma tanufi toilet na ɗakin Ammi " hiyana kuma ta ɗaukoh dadduma ta shinfida dan ita already tariga tayi alwala tun ɗazun " 

Washe gari misalin karfe 3 na yamma gaba ɗayansu suna zaune a ɗakinsu " hiyana dai karatun Al qur'ani mai girma take " diyana kuwa sarkin kallo, kallon film take a wayar Zahra,  ita da lamrat " amrat kuwa tayi barchi abunta , Zahra na hira da nurse ɗinsu " sunyi nisa chikin abubuwar dasuke," sukaji diran motochi chikin gidan nan, take jiniyar motar yan sanda ya karaɗe ko ina na gidan " da sauri Zahra tamike tana faɗin Aunty farida oyoyo, zata nufi waje diyana tariketa tace Aunty Zahra ya akayi kikasan Aunty farida che idan kuma kikaje ba itabace Aunty Maryam che zata komafa " Aunty farida ne dan kuwa ita kaɗaice mai zuwa da kiniyar motar yan sanda, Aunty Maryam kuma da busar gidan sarauta take zuwa, ki gane bambanchin mana , Aunty Maryam ɗan sarki take aure, Aunty farida kuma ɗan tsohon gwamna kuma gwamna mai chi yanzu take aure, zahra na gama faɗin hakan tanufi waje da gudu " da sauri su diyana'ma sukabi bayanta amma banda hiyana da nurse nasu, dan hiyana bazata iya wani dogon tafiyaba saboda jiri datakeji ,
Aguje Zahra ta tafi tafaɗa jikin Aunty farida dake tsaye tana kokarin fidda kuɗi daga jakarta,  bazato ba tsammani kawai taji Zahra ta faɗo mata a jiki saura kaɗan su faɗi " haba auta sokike ki kadanine " dariya Zahra tayi san nan tace. To Aunty farida ae murnane yasa na faɗo jikinki, ina junior " yana wajen baban'sa sai ranar Sallah zasu zo zata sake magana idanta ya sauka akan diyana dake tsaye murmushi ta sakarwa diyanar tare ta yimata alama da hannu a kan tazo " da sauri diyana tanufeta itama tana murmushi " haɗesu Aunty farida tayi ta rungume tana faɗin nayi kewarki my sister's " muma munyi kewarki wlh chewar Zahra " sakinsu Aunty farida tayi san nan ta karisa wajen da lamrat ke tsaye, itama ta rungumeta tana faɗin kebazakizo kimin oyoyo ɗin bane ko dai kunyata kikejine, nifa ba surukarki bace " inawuni y hanya chewar lamrat ɗin " lfy lau Aunty farida tafaɗa tare da sakinta, ta chiro kuɗi masu yawa tamikawa security ta san nan ta rikoh hannun diyana suka nufi bangaren Ummi " security na biye dasu da manya manyan trolley a hannu " su Zahra suka rufa musu baya " ina hiyana da amrat Aunty farida ta tambayi diyana tana kallan fuskarta " hiyana na ɗaki tana karatu, amrat kuma tayi barchi , " ok to meyasameki a baki naga bakin ki yakunbura kodai wajen rawan kan'kine kika fasa bakin ta karisa magamar suna kokarin shiga palon Ummi " aa Aunty Maryam che ta fasamin " Aunty farida na kokarin zama a kujera tace.what me ya haɗaki da Maryam kuma tayi maganar tana kokarin zaunar da diyanar kusa da ita " nan fa diyana tashiga bata lbr abun daya faru tun ranar da Aunty Maryam tazo har yau sai da tafaɗa mata komai " Zahra dai a tsorace take sosai dan yanzuma basu faɗawa kowaba, Aunty Maryam tace sun faɗa barekuma diyana tazo tafaɗa'ɗin " Aunty farida ma shiru tayi kuma sai  yanzune tagane dalilin daya Aryan yace tayi zuwar gaggawa,  kuma batayi mamakin abunda Aunty Maryam ɗin tayiba dan tasan fiyeda hakama Maryam zata iya aikatawa " 
Am sorry my diyana kiyi hakuri kunji yanzu kutashi muje kurakani na dubo jikin hiyanar Koh ta karisa maganar tana mikewa " suma mikewa sukai, tafita sukabi bayanta

Da sallama suka shigo palon kai tsaye ɗakin'nasu.suka nufa  hiyana dai tana zaune inda suka barta, rike da qur'ani tana karatu " ganin Aunty farida yasa tamike da kyar, tana faɗin sannu da zuwa Aunty farida" karisa shiga chikin ɗakin Aunty farida tayi taje ta rungumi hiyana,  tana faɗin am sorry my dear y jikin "da sauki sosaima " murmushi kawai Aunty farida tayi san nan ta saki hiyana, takama hannunta suka koma baƙin gadon suka zauna " kin.sha maganin rana kuwa Aunty farida ta tambaya tana kallan fuskar hiyanar " eh nasha " ok to zaki iya tafi dan Ina san inje inyi wanka, kuma zanso mutafi tare gaba ɗaya, dan daga yauma har ranar dasu Ammi zasu dawo tare zamu zauna daku a ɓan.garen Ummi " eh zan iya " ok to kutashi muje, har sun mike zasu fita sai idan Aunty farida ya sauka kan nurse ɗin'su dake tsaye a gefen drawer " wacece wanchan kuma " juyawa sukayi suna kallan inda Aunty farida ke nunawa " laaa. Aunty farida nurse ɗin.muce chewar diyana " oh to itama tazo muje tare tunda daman kula daku take  yanzu tunda zaku koma ɓan.garen Ummi itama ae dole tabiyo'ku dan kula daku, " to sukace san nan diyana ta tashi amrat daga barchi ta rikoh hannunta  " ska tanufi waje  " Aunty farida na rike da hannun hiyana 

Misalin karfe 6:45 Aunty farida tafito daga ɗakin Ummi a palo taisko'su diyana "suna ganinta suka fara gaishe.ta " da fara'a ta amsa san nan ta ɗora dacewa kutashi kuje palon Abba muyi buɗa baki " bamuyi azumibafa dukkanmu Zahra chewar Zahra " eh nasan baku azumi amma ae zaku chi abinchin dare koh, bama wan nan ba dole muje kutayani chi abinchin ae " har suna haɗe baki wajen chewa to Aunty Maryam ta hana'mu zuwa palon Abba " dogon tsaki Aunty farida taja san nan tace.kutashi mutafi hai " ba musu suka mike gaba ɗayansu " Aunty farida takama hannun diyana sukayi gaba, su hiyana suka rufa musu baya 

Da sallama suka shiga duk da sunsan babu kowa a palon.mamakine yakama diyana da sauri tace.Aunty farida yanaga table ɗin chin abinchin yazama biyu, kuma ankaro kujeru " eh saboda sallah gaba ɗayan muna zuwane shiyasa, da sallah yakusa ake fito da ɗayan daman table biyune, kinga ae guda ɗaya bazai isshemu, mu dukka bakoh muna dayawa kuma kowani table kujera 12 to kinga ae kujera 12 yamana kaɗan ta karisa maganar tana kokarin zama " zama gaba ɗayan'su suka zo sukayi " Aunty farida tana faɗin my diyana kekam sai yaushe zaki daina surutune " sosai diyana tai dari sai datayi mai isarta san nan tace ae nibana surutu " Aunty farida dai bata kuma'chewa komai'ba ta kira masu aiki tabasu umarnin suzo su shirya musu abinchi " chikin hanzari sukafara jeramusu a'binchin san nan suka shiga sarving nasu 

Sunyi nisa chikin chin abinchinsu, ba wanda yake magana a chikinsu shiru palon sai dai karan spoon zakaji " babu ko sallama ta faɗo chikin palon fuskar nan a tamke " jin motsin anshigo palon yasa dukkan'su suka ɗago suna kallanta " nan take hiyana ta kankame Aunty farida " mai da kanta Aunty farida tayi tachigaba da chin abinchinta kamar ma bata san da mutun awajenba " chikin tsawa Aunty Maryam tafara Magana "banache kada nasake ganinku a kowa bangare na gd nan ba, inba bangaren Aisha ba,"  a sukwane Aunty farida ta ɗago kai jin Aunty Maryam tace. Aisha kai tsaye kallan'ta Aunty farida take sosai batare da tace uppan ba " jin abun da Aunty Maryam tace yasa'su hiyana kokarin mikewa dan subar palo "  muryan Aunty farida ta katse'su dacewa ina kuma zakuje " juyowa sukayi suna kallan Aunty farida kanta na kallan kasa tana chin abinchin'ta chikin kwanchiyar hankali,  kana suka juyo sukaga Aunty Maryam dake tsaye tana jiran, suzo su fiche daga palon nan,  ga fuskarta babu annuri " sun rasa me ɗaya zasuyi kawai suka tsaya chirko chirko " ganin hakan yasa Aunty farida ɗagowa ta dubi Aunty maryam a kausashe tace kifita a ɗakin nan Maryam " kara ɗaure fuska Aunty Maryam tayi tace akanme zanfita " a kan na isa inche kifita kuma kifita dole " shiru Aunty Maryam tayi tana tunani bazata iya jayayya da Aunty farida ba dan kuwa idan tace zatayi hakan tofa gaba ɗaya gidan nan sai sun hukunta'ta "gashi kuma Aunty farida na neman kunyata'ta  a gaban yaran nan,  ganin Aunty Maryam ta tsaya shirune yasa Aunty farida chewa " ke Maryam badake nakeba nace kibar wajen nan koh " a fusace Aunty Maryam tajuya fuuu kamar wata kunfa tayi waje " dawo da kallanta kansu hiyana tai tana faɗin ko zauna kuchi abinchin ku" ba musu suka zauna sukachigaba da chin abinchinsu

SAUDIA ✈️

Kwanche yake saman faffadar gadon'sa ya zubawa wayar hannunsa ido sosai yake kallan hoton'ta wani nauyayyar ajiyar zuchiya ya sauke " a hankali da murya kamar mai'raɗa yafurta ke kyakkyawa'ce my sister ina kewarki sosai ina butatar, shan coffee " takun tafiya yaji kuma ko ba a faɗamasaba yasan wan nan takun DON ne " da sauri yafita wajen hoto ya kashe hasken, screen ɗin wayar ya ajiyeta a gefensa  " da sallama ɗauke a bakinsa yashigo betroom ɗin " mikewa Aryan yayi zaune yana amsa masa sallamar " kallansa Aryan keyi daga sama har ƙasa da mamaki yache inazakaje haka naga kasa kaki " calmly DON yafara magana I need Ur prayer zan dawo jibi sai muwuche naija tare " like how bangane U need my prayer ba inama zakaje yayi maganar yana kokarin sauka daga gadon " London zanje yanzu kiran gaggawane, kar kafaɗawa'su Abba dan bansan hankalin'su yatashi " no gaskiya sai dai muje tare " aa Aryan taya zamu tafi tare kuma ae idan muka wuce tare dole su Abba su sani kawai ka tsaya ka taremin, insun tambayi ina nake kasan mezaka faɗa musu " badan Aryan yasoba haka ya hakura yaraka,DON har airport san nan yadawo.


NIGERIA 

Bayan sun gama chin abinchinsu ne Aunty farida tace to kutashi muje ɗaki muyi sallar mangariba da issha sai nabaku tsarabarku " da murna suka mike Zahra na faɗin Aunty farida dan allah kinkawo'min lalle kuma zakimin koh " sosaima kuwa auta ai daga jibi zan fara muku lalle mai kyan gaske " da sauri diyana ma tace Aunty farida nima inasan lallen sosai zakimin" eh mana my diyana dukkanku zan muku " jerawa sukayi Aunty farida na rike da hannu diyana " sunzo zasufita palon ke nan " jiri ya kwashe hiyana tatafi luuuu zata faɗi da sauri nurse ɗin tarike ta tana faɗin  " wlh yarinyar nan ta bugu sosai a kantan nan tana bukatar kulawa sosai " a sukwane Aunty farida ta juyo hannu tasa ta taimakawa nurse ɗin suka rike hiyana sukayi bangaren Ummi, 
A kam doguwar kujera suka kwantar da ita nan take nurse ɗin ta koma bangaren Ammi ta haɗo musu magungunar'su ta dawo " ɗaya bayan ɗaya tabisu da kanta ta basu maganin sai da ta tabbatar sunsha san nan takoma kan nata kujerar itama ta zauna " Zahra ki shiga chikin ɗakin ki ɗaukoh min babban trolley na ɗin nan kuje da diyana ta kama miki chewar Aunty farida " to su'kace a tare suka mike suka nufi chikin ɗakin 

Jim kaɗan suka fito da katan akwatin Aunty farida da kyar suke jan trolley ɗin " a tsakiyar palan suka ajiye sai nishi suke kamar wayanda sukayi wani aikin wahala " saukoh wa kasa Aunty farida tayi tazo ta buɗe trolley, ɗin  nanfa tafara fitar musu da tsarabar'su komai iri ɗaya ta sai musu " manya manyan lufaya na kanuri ta sai musu masu kyau da tsada kowa kala bibbiyu Pink da blue " sai dogayen riguna masu manya manya mayafi kala uku² tabawa kowa da baki da ja dakuma porpul colour " ga wasu manya manyan ribons na ɗaure gashi da manya manyan bit " sai turare masu kanshi da kayan kwalliya sai takallama kafa uku 2
Sai murna suke sunamata godiya musamma ma diyana nata murnan daban ne dan an kawo mata kayan kwalli kit guda sai dariya take " daukoh turare mai tsada da dogon riga mai kya Aunty farida tayi taba nurse ɗin, ansa tai tanata godiya
To kutashi ku kai kayan ɗaki ku ajiye sai rananr sallah yanzu jibi zamuyi lalle raanar Friday kuma zanmuku gyaran gashi dan gashin kun nan bazai kitsuba yayi tsantsi dayawa shiyasa na sai'muku wayan nan bit ɗin dan namuku kitso guda biyu a gaban goshi kawai nasamuku bit ɗin nan, sauran gashin kuma ayi parking ta baya " sai murna suke har suna haɗa baki wajen chewa to tare da mikewa gaba ɗayan'su  kowa rungume da kayansa zasu fita " Aunty farida tace. Inakuma zakuje " dakinmu zamu kai kayan zahra tabata amsa " aa ae nafaɗamuku sai Ammi ta dawo zaku koma bangarenta dan haka kuzo ku kai ɗakin Aunty mardiya ku ajiye, kuma a nan zaku rinƙa kwana " ba musu suka juya suka nufi ɗakin Aunty mardiyar suka ajiye kayan nasu chikin sip san nan suka dawo Palo


YOLA

Abun duniya ya ishata yau anwayi gari babu komai na chi a gidan ga azumi ba abun chi idan anyi buɗa baki, zama tayi tana tunanin yazatayi, chankuma tayanke shawarar ta ɗaukoh 1k a chikin kuɗin data ajiyewa boka tayi chefanen abun da zatachi,  Allah barshi kafin lokachin komawarsu wajen bokar sai tanemo wani kuɗin tachikasa  da wan nan tunanin tamike tanufi ɗakinta " ɗaga gadon chiyawarta tayi ta ɗaukoh kuɗin ta chiri 1k ,ta maida sauran, ta ɗauki mayafita tayi waje dan zuwa yin chifene 


KANO

Ku tashi kushiga ku kwanta dare yayi kunji chewar Aunty farida " to kawai suka amsa mata tare da mikewa gaba ɗayansu har sun kai bakin kofar betroom ɗin Aunty mardiya" Aunty farida tace. aa to ae gadon yamuku gaɗan diyana da amrat suzo mukwana a ɗakina itakuma nurse naku taje wan chan ɗayan ɗakin ta kwana, tana gama faɗin hakan tamike tanufi hanyar fita " harta kai kofar fita tsaikuma ta juyo tana faɗin diyana kuashiga ɗakina keda amrat ku kwanta ina zuwa zanje wajen Maryam " to kawai sukache san nan suka nufi ɗakin nata itakuma tayi waje, su Zahra ma nuka shige ɗakin Aunty mardiya nurse nasu kuwa tawuche ɗakin da Aunty farida ta nuna " 

Da sallama Aunty farida ta shiga palon Aunty amarya babu kowa dan haka kai tsaye tawuche ɗakin Aunty Maryam da sallama tashiga kwanche ta isko ta tana latse latsen " ko amsa sallaman ma batayiba bare ta ɗago kai " Aunty farida bata damu da hakanba wuche tayi ta zauna a bakin gadon a nitse tafara magana " tashi inasan magana dake " mikewa Aunty Maryam tayi zane, a kausashe tace to me kikeso yanzu kuma "  daure fuska sosai Aunty farida tayi san nan tafara magana " meyasa kika bugi yaran nan mesuka miki " dogon tsaki Aunty Maryam taja san nan tace abun da kikazo jike nan to na buga kuma babu abun da sukamin kawai naji inasan bugun'sune shiyasa na bugesu, ko zaki rama musune " juyowa Aunty farida tayi a fusace ta ɗauke Aunty maryam da mari tana faɗin ni sa'ar kice dazaki zauna kina faɗamin magana " a fusace Aunty Maryam ma ta ɗaga hannu..✍️✍️


More comments pls 🙏🙏



💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 18*



Hannu Aunty Maryam ta ɗaga, har zata kai mata mari sai kuma ta dakata " zuba mata ido Aunty farida tayi sosai," me ya dakatar dake kimare'ni mana, ae kin girmane shiyasa har kike tunanin ramawa, kimare'ni nace koh tayi maganar a fusache" dan Allah Aunty farida kifita a ɗakin nan "hmmmm wlh Maryam bansan baki da hankaliba sai wan 'nan  karan,to kisani idan su Abba suka dawo kinemi abun da zaki kare kanki,dan kuwa babu wanda zaiga abun da kika'wa yaran nan ya kyale'ki, naso hukun taki da kai na, amma zan bari,  ƴa'ƴayn Aisha dakike ikrari su hukuntaki, dan awan nan gaɓar su kikataɓa, "tana kaiwa nan tamike tafice daga ɗakin " ganin Aunty farida tafita, yasa  Aunty Maryam, tayi kwafa  tana faɗin to inaruwan'ki inba shisshigiba duk chikin ƴa'ƴan Aisha akoi wanda ya isa yamin hukunci'ne, yara kuma na buga innasake samun dama'ma bugun zanyi, dan nayi alkawarin rabasu da gidan nan tunda Aunty amarya bata san'su, juyawa tai ta gyara kwanchiyar sai surutai take

Da sallama ta dawo palon Ummi, duk datasan ba kowa, kai tsaye ɗakin'ta tawuce, tasamu diyana da amrat sunyi barchi ,"kayan jikin'ta ta chire san nan nufi toilet, after 45 mnt tafi ɗaure da towel da'alama wanka tayi, trolley ta tajawo, ta buɗe ta ɗauki kayan barchi, masu kyau da tsada farare tas masu laushin gaske, sai kamshi kayan keyi yasha turarukkan maiduguri,san nan ta ɗauko mayukan'ta masu kanshi da tsada sai dataɓi ko'ina na jikinta ta shafeshi da mai san nan,tasanya kayan barchi  ta'sake feshe jikinta da turare sai kamshi take kamar anyi ɓarin turare a jikinta, "ta mai da mai da tureren chikin trolley ɗin ta rufe ta mai'dashi wajen zamansa, tadawo kan gadon ta gyarawa amrat kwan chiya, san nan ta kwanta a gefensu, tare dayin adduar barchi asuba ta gari 


Yau yakama Wednesday tun safe Aunty farida ta shirya chikin tsadaddiyar lace mai Bala'i kyau baki, da ratsin ja ta zuba sarkan gold a wuya da hannunta, ta jera wasu tsadaddun zobuna uku na gold a hannunta, tayi simple make up bakaramin kyau tayiba sai kamshi take zubawa kamar anyi ɓarin turare ajikinta, tasa plat shoe ja da mayafi ja san nan  tayiwa yan matan Ammi kwalliya sosai, "diyana hiyana Zahra tasasu sukasa wani haɗaɗɗen duguwar riga mai kyan gaske, da pink colour an masa kwalliya da wasu duwatsu golden colour, bakaramin kyau sukayiba amrat da lamrat kuwa sun sa wandon jeans baki da yellow t-shirt," gaba ɗayan'su ta ɗaure musu gashin nasu a tsakiyar kai ta zuba musu jelar  a baya, sai dai ita hiyana har yanzu ba a chire bandejin dake goshinta'ba "Aunty farida ina zamuje kika mana kwalliya haka diyana ta tambaya tana kokarin gyara mayafin rigar" wajen lalle da gyaranjiki zan kai ku,  da naso namuku lalle da kaina to amma nayi tu nanin gara na kai'ku ae muku har da gyaran jiki " tsalle diyana tayi ta rungume Aunty farida tana faɗin mungode sosai" to sakeni mutafi kar lokachi ya kure mana " to diyana tafaɗi tare da sakin Aunty farida" rike hannunta Aunty farida tayi sukayi gaba, su Zahra suka rufa musu baya,
  suna fita harabar gd da gudu Shahram  yanufo'su " ɗan dukar da kai yayi ya gaishe da Aunty farida chikin harchen turanci" bayan yagama gaishe da Aunty farida,su Zahra ma suka gaidashi " bayan yagama amsa gaisuwar'su Zahra ne, ya tambayi Aunty farida ko zai iya kaisu inda zasuje da kanshi " Aunty farida tace badamuwa ya fito da family car dan tafisan sutafi dukkan'su a mota ɗaya " da gudu yajuya yanufi parking space na gidan," har gabansu yazo yayi parking,"zai fito yabuɗe'musu " Aunty farida ta ɗaga masa hannu, alamar yabari zasu ɓuɗe da kansu " da Kanta tasa hannu ta buɗe kofar motar," a nitse suka fara shiga sai da suka gama shiga san nan tabi bayansu " da gudu gaske Shahram yaja motar yana zuwa bakin gate ya ɗan rage gudun motar nan'take securitys dake wajen suka wangale masa gate ɗin da'gudu ya danna hanchin motar waje, gudu sosai, Shahram ke shararawa a kan mikakkiyar titi " ranki ya daɗe ina muka nufa yayi tambayar yana kokarin fita daga asalin babban gate ɗin gidan " A&S muka nufa tabashi amsa ta kokarin picking call ɗin daya shigo wayarta " miƙar hanya Shahram yayi sosai yake sharara gudu 
Yana hawa kan titi dazata sadashi da gate ɗin A&S ya rage gudun motar,horn ɗaya yayi wani dattijo ya taso ya  wangale masu gate ɗin da'alama shine mai gaɗin " A nitse Shahram ya danna hanchin motar chiki, parking space na wajen yanufa yana kashe motar  yafito da sauri ya buɗewa Aunty farida" a hankali ta zuro kafafunta waje ta fito "su hiyana ma sukabi bayanta hannu diyana tariƙe suka nufi chiki " wani haɗadɗen wajen gyaran jikine da lalle da kitso, wajen ya tsaru sosai iya matane kaɗai ke shiga koka'kawo wani naka sai dai katsaya awajen zaman baki, suna da ma aikata sosai inkaje basai kabi layiba, " hannu bibbiyu a ka tarbi su Aunty farida " chikin ƙankanin lokachi aka fara gyara musu jiki


YOLA


Da gudu inna tafito daga ɗaki, tayi kichin, da sauri ta sauke tukunyar ɗumamen, dake kan wutar abinchin har  yayi bakin'kirin, zama tayi dirshan awajen kamar zatayi kuka tafara surutai,"oh ni habiba yanzu me zanchi wayyo Allah gashi ba azumi nake ba dole naje nasake ɗaukar 1k a chikin kuɗin nan na sawo masara nazo na surfa na niƙa nayi wani tuwon,  mikewa tayi ta jawo itacen wutar ta kashe san nan ta wuche ɗaki ta ɗaga katifar chiyawar'ta ta irga kuɗin taga saura 6k ta zari 1k ta mai da sauran kasan katifar ta ɗau mayafinta tafuto tanufi waje dan zuwa yin chefene

KANO

A bangaren'su Aunty farida kuwa sai gyaranjiki ake musu an gama yiwa diyana da zahra da amrat bakaramin kyau sukayiba, kamar wasu larabawa haka suka zama daman, dukkansu fararene tas jikinsu sai kyalli yake gwanin ban sha'awa, 
yanzu aka fara yiwa lamrat da hiyana kuma,"Aunty farida kam already tariga da tayi nata a Maiduguri kafin tazo, " yanzu lalle  za'afara yiwa diyana da zahra " sai zolayar'su Aunty farida keyi " my diyana kingan'ki kuwa kamar wata sarauniyar kyau fa kinga fatar nan taki kuwa saikace na jariri gaskiya dole..bata karisaba,  wayar'ta tafara ƙara  alamar shigowar ƙira da sauri ta chiro wayar kiran iphone 14 daga jakarta " laaa Aunty farida yaushe kika chanza waya chewar diyana " last week tayi maganar tana kokarin picking call ɗin " hello my bro ykk "lfy lau my lovely Aunty ykk y gd " lfy lau alhamdulillah gamu nan ma awajen gyaran jiki ae ina Prince " baya nan yayi tafiyar sirri " murmushi tayi kafin tace kai Aryan dayayi tafiyar sirri nasan yace karka faɗawa kowa, shine  kuma kafaɗamin  " murmushi kaɗan shima ma yayi san nan yace ae ke da kankima sirrinmu'ce ko bazamu faɗawa kowaba yazama dole ke kisani, " inasu Khalid to " suntafi kasuwa " to yau kuma da kansu sukaje kasuwar " eh wlh nima dai na ɗanyi mamaki " kodai Zahra yaje yiwa tsaraba " to waya sanin musu zaki gane kan Khalid da Yusuf ne " to shike nan bari innakima gd mayi magana " ok ya'jikin yaran nan " da sauki sosai gasu nan ma ana musu lalle " lalle kuma ya tambaya yana taɓe baki " eh lalle mana kona baku ku gaisane " eh to dai kibari sai kun koma gd zaifi tunda yanzu kince lalle ake musu " ok to shike nan sai munyi waya," ta karisa maganar tana chire wayar daga kunnen'ta " katse kiran tayi tamaida wayar chikin jaka san nan ta ɗago tana kallan'su diyana da akewa lalle " wow my sister's kunganku kuwa kaman wasu amare gaskiaya idan Ammi suka dawo bazasu gane kuba wow " diyana dai baki yaki rufuwa sai murmushi take " Zahra kuma hannu tasa ta rufe fuska tana dariya " bayan angama yiwa Zahra da diyana lalle " aka fara yiwa amrat da lamrat 

SAUDIA

Ammi che kwanche a kan chiyar Abba a ɗakinsu tana shafa fuskar'sa yayinda shikuma yake shafa gashin kanta " ranka yadaɗe nayi kewar yanmata'na sosai, " hannu Abba yasa yaɗan ja dogon hanchin nan nata yana faɗin to kwana nawa yarage mukoma, ɗazun ma munyi waya da farida take chimin zasuje wajen gyaran jiki " Allah sarki feeda baiwar Allah, Allah yamata albarka na mata adduar samun aihuwa sosai jiya danaje masallaci " kullun sainayiwa farida adduar bama ita kaɗaiba har da maryam da mardiya ba garama faridan tasamu ɗaya ba sauran kam aiko ɗayan basu samuba,chewar Abba " wlh tausayi suke bani tayi maganar tana kokarin mikewa " da sauri Abba ya rikota yana faɗin ina zakije kuma " so nake naje nayi magana da yaron nan " kallan chikin kwayar idonta sosai Abba yayi san nan yace wani yaro kuma, da gangan yamata tabayar, dan yanasan yau yaji takira sunan Safras da bakinta " yaron Ummin nan mana tabashi amsa tana mai kawar da kai gefe " to shi yaron bai da sunane " juyo da kallan'ta tayi kansa san nan tasa hannu taja gemunsa chikin wasa take faɗin, bazadai kaji su nan a baki'naba " murmushi yayi yana faɗin to idan inasan inji kumafa " sai na kira maka mana ae duk abun da kakeso matikar bai saɓawa Allah da manzon'saba dole namaka " rungumeta Abba yayi chikin farinchiki yafara magana ina kaunarki Aisha'ta nima bazan saki yin abun da baki so ba, tunda ba kyasan kiran su nan bazan saki kiraba aje a yaron kinji " chusa kanta tayi kirjin'sa tana faɗin nima ae ina kaunarka sosaima " nasani Aisha nasan kina kauna'na sosai nasani wlh " to shike nan kamin izzini naje na dubo'shi dan jiya banganshi'ba kwata kwata kuma inasan magana dashi a kan yaran nan " aa Aish ba yanzuba dan yanzu bansan ki raba jikinki danawa kibari sai anjima " to kawai Ammi tace takara shigewa jikinsa ta lafe 

Da sallama Khalid da Yusuf suka shigo palon hannun'su ɗauke da manya manyan jakun'kunar sayayya Aiman da Ahmad dake zaune saman Sofa suka amsa sallamar suna binsu da kallo " daga ina kuke haka Aiman ya tambaya yana ɗaure fuska " to dakake ɗaure mana fuska, saiyasa muji tsoranka mufaɗa'maka  inda mukaje ne chewar Khalid " dariya Ahmad yayi yana faɗin nidai babu ruwana " tsaki Khalid yaja yawuce yanufi hanyar ɗakin'sa " da sauri Yusuf ma yabi bayansa " miƙewa Aiman yayi yana faɗin lokachi yayi da zan gano mekuke kullawa kuma sai nayi maganin'ku " Ahmad kam binsa kawai yake da ido har yafice daga palon ,yana ganin Aiman yafita " ya kwashe da dariya, chikin dariya yake magana wlh nidai nawa ido kawai zanga wan nan game ɗin yasake kwashewa da dariya yana mai kwanchiya a kan kujerar 


NIGERIA

Sai milalin karfe 4:50 aka gama yiwasu hiyana gyaran jiki da lalle sunyi kyau sosai kamar su'sukayi kansu yaran nan gawani kitso guda biyu da aka musu a gefe da gefen kunnen'su ansa manya manyan bit an zuboshi ta gaba har kan chikinsu tsawon gashin, sauran gashin an ɗaure musu a tsakiyar kai,anzuba jelar gashin ta baya har gadan bayan'su,  musammanba hiyana da diyana gashinsu yafi tsawo da baki ga tsantsi, ba karamin kyau sukayiba kamar, ƴa'ƴan larabawa " bill akayiwa Aunty farida ta biya san nan suka nufi waje " 
Shahram dake zaune chikin mota,yana ganinsu ya fito da sauri yana faɗin wellcome ma " da murmushi a fuskarta  tace sorry Shahram for keeping U waiting  " buɗemusu kofar motar kawai yayi batare daya sake maganaba, suna shiga yarufe motar yashiga gaba yabawa motar wuta sai bakin gate mai gaɗin ya wangale masa gate ɗin ya danna hanchin motar waje da gudun gaske ya miƙi titi, gudu yake shararawa sosai,  sai daya kusa isa bakin babban gate na gida tukun ya ɗan ragewa motar gudu horn ɗaya yayi nan take security suka wangale masa gate ɗin a nitse ya kutsa chikin gidan,  kai tsaye parking space yanufa ," yana kashe motar yafito da sauri ya buɗe musu " fitowa sukayi gaba ɗayan'su suna faɗin thank U uncle " Aunty farida ta rike hannun diyana sukayi chikin gd " da sallama suka shigo palon " da sauri nurse nasu dake zaune saman Sofa tamike tana faɗin ina kukaje natashi barchi ban gankuba, " wajen gyaran jiki mukaje diyana tabata amsa " dukawa tayi kasa ta gaida Aunty farida " da fara'a ta amsa san nan tanufi ɗaki dan yin wanka tana faɗin sister's kuje kuyi wanka kozo kubiya bashin sallar Azhar da la asar dake kanku " har suna haɗa baki wajen chewa to san nan suka nufi ɗakin Aunty mardiya 


 yau  saura kwana ɗaya sallah sai shirye shiryen tarban su Abba ake, manya manya shanu 4 aka'yanka da raguna 5  " hayar masu soya nama Aunty farida ta ɗaukoh mata'ne masu jini ajiki masu ji da karfi da lfy,  san nan tasa aka fitar da manya manyan gas daga store, aiki ake babu kama hannun yaro ,gamasu yin chin chin a gefe, gamasu donut dubula alkaki da dai sauransu, Aunty farida yau bata zauna ba sai hidima take da jama'a " Aunty Maryam kuwa tana ɗaki kwanche abunta

Misalin karfe 1:50 diyana na zaune a ɗakin Aunty farida tadage sai make up take,  wayar Aunty farida dake kan gado yafara ringing," da sauri ta ajiye jan bakin dake hannuta tanufi wayar, ɗaukar wayar tayi zatayi waje dan takaiwa Aunty faridan, sai taga pic na Aryan ne ya bayyana a kan screen ɗin wayar, sanye yake da kayan sojoji baƙaramin kyau yayiba fuskar nan tashi kamar bai taɓa sanin me dariya'ba," da sauri tayi picking call ɗin " daga ɗayan ɓangaren Aryan yace,"hello my lovely Aunty " ba itabace yaya Aryan ni che ina wuni " lfy lau y jikin naki " nasamu sauki hiyana che kawai tarage bata samu sauki'ba " subhanallah me ke damunta ina nurse naku " nurse ta koma jiya wai zataje tayi shirye shirye sallah " to meke damun hiyanar " chiwon kai da jiri " ok jibi zamu dawo ae sai na dubata amma duk da haka zansa a kawo mata magani " to bari na kaiwa Aunty farida wayar " daman kinsan zaki kai mata wayar'ne kikayi picking call ɗin " eh ae nayine daman dan na gaisheka tun da mun daɗe bamuyi magana'ba " to ae kece kika manta dani shiyasa " dariya diyana ta ɗanyi kafin tace, ni ban manta da kaiba dan bani da waya'ne Allah dana kiraka " wani ajiyar zuchiya ya sauke"to amma kina kewata kuwa " eh mana ina kewar'ku dukkan'ku " ok to shike nan ki ajiye wayar kawai anjima idan Aunty farida tazo ta kirani dan naji Abba na nemana " to kawai tace tare da chire wayar a kunnen'ta ta mayar kan gadan ta ajiye,"takoma gaban mirro tachigaba da kwalliyar'ta 


YOLA

Inna na ɗaki kwanche a kan yar gadon chiyawar'ta taji sallama daga kofar gd mikewa tayi daga kwanchiyar datake tana amsa sallamar,"ɗaukar mayafinta tayi tanufi waje " ganin bello ne ke sallamar yasa inna ta ɗaure fuska sosai tafara magana to yau kuma dame kazo funafiki " ina wuni inna " daban wuniba zaka ganni'ne " to Allah yabaki hakuri daman naga gobe sallane shine nache bari na sauke hakkin ma kwabtaka na kawo miki wan nan,"yayi maganar tare da ajiye wa inna gaji guda uku a gaban'ta, batare daya jira amsar'taba yayi wuce warsa gidan'su " da mamaki inna ke kallansa har yashiga gida, duƙawa tayi ta ɗauki kajin tayi chikin gida," a tsakar gida ta ajiyesu san nan ta ɗaukoh wuƙa tayanke igiyar da aka haɗesu aka ɗaure, ta samu wani igiya ta ɗauresu ɗai ɗai ta kaisu kichin tafito takoma ɗaki ta kwanta," tana kwanchiya babu jimawa buba yashigo gidan da sallama yana ɗingisa kafa da sanda " tana daga chikin ɗaki ta amsa masa san nan tace yashigo " shiga ɗakin yayi hannunsa riƙe da buhu  " lfy buba ina zakaje da buhun nan " bappa'ne yace na kawo miki, shin kaface wai kiyi girkin sallah " da murna inna tamike zaune wayyo Allah kacewa bappa ngd sosai Allah yaƙara arziƙi " amin yafaɗa tare da ajiye mata buhun ya juya yafita " buɗe buhun tayi taga shin kaface mai kyau da murna ta tura buhun bayan kyaure ta ɓuye 

KANO

Misalin karfe 7 na dare, sun haɗu a palon Abba suna buɗa baki " kai my diyana sarkin san kwalliya chewar Aunty farida tayi magabar tana ɗan jan kumatun,diyanar " ae kwalliyar dazanyi gobema sai yafi wan nan kyau " Allah ko ae haka akesan mace takasan'ce mai tsabta da kwalliya " Zahra tace Aunty farida ae muma munayi " eh kunayi amma my diyana tafikuyi sosai, kuma kuƙara dagewa " to shike nan zamu rinƙayi sosai " ok to kuchi abinchin'ku dawuri muje mu kwanta dan kunga gobe sallah zamu tashi da wuri " har suna haɗa baki wajen chewa toh " shiru kakejin palon babu mai magana sai paran spoon kawai zakaji " sallama sukaji anyi a bakin kofar palon " amsa sallamar Aunty farida tayi san nan taba da izinin shigowa " ɗaya daga chikin security bakin gate ne,har ƙatsa ya duƙa ya gaida Aunty farida " ta amsa tare da tambayar'sa ko lfy " eh lfy wani likitane yakawo saƙon nan wai inji oga yace abawa hiyana " ok to ajiye a saman table ɗin gaban kan nan " mikewa yayi ya ajiye sakon san nan yanufi waje 
Bayan sun gama chin abinchine suka mike zasu tafi ɗaki, Aunty farida tasa hannu ta ɗauki sakon tana faɗin muje ɗaki kisha maganin hiyana " toh kawai hiyana tace, san nan suka nufi waje  " sai da Aunty farida ta tabbatar hiyana tasha magani san nan takama hannun diyana da amrat suka nufi,dakinta, a gurguje sukayi wanke sukayi sallar issha suka kwanta asuba tagari 

Tunda sukayi sallar asuba yau basu mai da barchiba " diyana tun karfe 7 take gaban mirro ta goga wan nan ta fenta wan nan ba karya tayi kyau sosai tamkar zataje gasar sarauniyar kyau " da sallama Aunty farida tashigo ɗakin tana waya da Aryan, wow my diyana kin ganki kuwa kamar wata sarauniya " dariya diyana tayi tana faɗin ngd Aunty farida " dawa kike magana kuma Aryan ya tambaya " hmm nina mantama muna waya wlh, kyan my diyana ne ya rikitani " shiru ya ɗanyi kamar mai tunani chan kuma sai yace to ɗauke'ta hoto ki turomin naga kyan daya rikitakin " ae kuwa kai ma idan kagani sai ka rikiche " to shike nan turomin ɗin dai kekam " ok tace tare da chire wayar daga kunnen'ta ta katse kiran" tadubi diyana tace to tashi kisa kaya namiki hoto " yauwa Aunty farida Allah yamiki albarka daman inasan inje in anshi wayar Aunty Zahra  nazo nayi hotan, tayi maganar tana kokarin mikewa..✍️





💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 19*



Lafayar da Aunty farida ta kawo musu ta ɗauko, Aunty farida da kanta ta ɗaura mata baƙaramin kyau tayiba ga kitso guda biyu a gaban goshita, kamar wata amarya ga lallenta ja da baki " wow my diyana kin haɗu iya haɗuwa yanzu muje wajen flowers ɗin garɗing muyi hotan koh zaifi kyau " to Aunty farida amma sai na ɗaukoh takalmi a ɗakin Ammi " ina takallamar dana kawo muku " aa shikam sai gobe zansa yanzu high heel nakeso " murmushi Aunty farida tayi tare da jan hannunta tana faɗin to muje " fitowa palon sukayi nan suka isko su Zahra suma sun sha kwalliya sosai sai dai su dukkansu hijabi suka'sa dan zuwa sallar idi " Aunty farida ina zakuje Zahra ta tambaya " hoto zamuje muyi a garding, ko zakuyine kuma " aa nikam banso chewar Zahra " to kufa tayi maganar tana nuna su lamrat "har suna haɗa baki wajen chewa aa bamusu " da kyar hiyana tamike dan sarawar da kanta ke mata tana faɗin Aunty farida muje kimana tare ni kam ina so " riko hannunta Aunty farida tayi dan yadda taga yanayinta kamar zata faɗi da kyarma take tafiya"  a harabar gidan suka tsaya san nan Aunty farida tace my diyana kije ki ɗauko ta kalmar naki kinji, kiyi saurifa dan kinga hiyana bazata iya tsayuwa sosaiba " da sauri diyana ta juya tanufi bangaren Ammi " Shahram na ganin'su yazo wajen da sauri ya gaida Aunty farida san nan ya tambayeta ko fita zasuyi'ne ya kaisu " aa tace masa " juyawa yayi yakoma bakin gate " suna tsaye har diyana ta dawo kwas, kwas, kwas, take tafiya, a nitse take zuba takunta da yanga " daga nesa Aunty farida tafara ɗaukarta video sai faɗin wow take, sai da ta iso kusa dasu tukun nan Aunty farida ta tsai da video, suka nufi chikin garding ɗin " hotona sosai,  tamusu a tare san nan tawa diyana ita kaɗai kala kala, bayan sun gamane suka nufi chikin gd Aunty farida na faɗin to my diyana sai kije ki ɗaukoh hijabinki muje masallachi koh " to diyana tace tare da wucewa ɓangaren Ammi " Aunty farida da hiyana kuma suka nufi ɓangaren Ummi 

SAUDIA

Tsaye yake a gaban mirrow ɗaure da towel a kugunsa da alama wanka yafito, yana shafa mayukan'sa masu kanshi da tsada' bayan ya gamane ya gyara gashin kansa ya sake feshe jikinsa da turare mai kanshi da tsada, trolley'sa ya jawo ya buɗe ya ɗaukoh farar jallabiya, ya juya a jikinsa yayi kyau kamar balarabe,tsayuwa yayi a gaban mirrow yana kallan kansa,  wayarsa dake kan gado tayi kara alamar kira yashigo, a hankali yake takawa kamar yana tsoran taka kasar ya isa gaban gadan,hannu yasa ya ɗauki wayar my blood ne ya bayyana a kan screen ɗin wayar, da sauri yayi picking call ɗin tare da manna wayar a kunnen'sa " hello " daga ɗayan ɓangaren DON yace jirginmu zai sauka  9:30 dai dai "ok by the i will be they " thanks ya faɗa tare da katse kiran' Aryan zai ajiye wayar ke nan yaji tasake kara alamar shigowar sako, ganin my lovely Aunty yasa ya buɗe sakon,  
da sauri ya zauna a bakin gado tare ta kara waro ash eyes nashi a kan'wayar,Sosai yake kallan wayar kamar zai chinye,  wow dole Aunty farida ki ruɗe irin wan nan kyau haka,yarinya kamar wata aljana, yayi maganar yana manna wayar a kirjinsa, jinake kamar jibi yamin nisa jinake tamkar ranakun tsawo suke karawa, kusan 10 mnt yana zaune yana surutai, san nan a hankali ya miƙe yanufi hanyar fita,wayar na manne a kirjin'sa

Kai tsaye ɗakin khalid ya nufa nan yasami Yusuf ma a chan dukkan'su sun shirya chikin fararen jallabiya bakaramin kyau sukayiba " muje koh lokachin sallama yakusa ae chewar Aryan" Khalid yace wai Aryan ina DON ne tun shekaran jiya nake tambayar'ka kakemin wani kauce kauce koh " nafaɗama'ka Khalid yana nan kawai yaje chikin madina ne " lallai Aryan to karyan ma bai dace da kaiba, baka sabayi'ba shiyasa ma dakayi yanzu, karyan bata zauna ba " dogon tsaki Aryan yaja tare da faɗin inkun gama kusameni a masallachi nayi gaba tun da naga baku da niyar tafi, yana gama faɗin hakan yayi waje " kallan Yusuf dake zaune ya zuba musu ido Khalid yayi"muje koh " hmmmm kasan'me Khalid wlh DON baya kasar nan wani lokachi sai Aryan yarinƙa magana kamar ba tare muka tasoba ina da tabbachin DON yana London zai wani chemana yana madina shi ko karyan ma bai iyaba " kaga Yusuf kafita maganar Aryan da DON kazo mutafi masallachi kar murasa sallah, yakai karshen maganar yana nufar hanyar fita " mikewa Yusuf yayi yabi bayan'sa " suna fita waje suka samu gaba ɗaya family sun haɗu amma banda Aryan " Khalid ina Aryan da Prince Ummi ta tambaya tana kallan fuskarsa " sunyi gaba Ummi " to muma ae sai muje koh dan kar lokachi yakure " tare suka jera dayake masallachi kusane da masaukin'su " suna isa suka rabu su Ammi sukayi ɓangaren mata su Abba kuma sukayi ɓangaren maza 


Nigeria

Zaune suke a palon Ummi diyana yau baƙi ya buɗu ta tasa fruits a gaba sai chi take " hiyana na rike da littafin addu'oe tana karatu " lamrat na game a waya Zahra " amrat na kallo a wayar Aunty farida " Zahra kuwa ta kwanta ta tada kai da chinyar Aunty farida sai hira suke kamar saannin juna " da sallama Aunty Maryam ta shigo palon " Aunty farida ta amsa mata fuska ba yabo ba fallasa " zama tayi a saman sofa mai zaman mutun 1 tare da faɗin, ina wuni Aunty farida anyi sallah lfy " lfu lau ykk "lfy Alhadulillah ta faɗi hakan tana mikewa " inakuma zakije kitsaya muci abinchin rana tare mana tun da lokachin yayi chewar Aunty farida " aa bana buƙata a inda,na fitoma akoi abinchi dama dai kawai nabi dokar gd nanne nazo na gaisheki kuma namiki barka da sallah a matsayinki ta babba, SO no need na tsaya yin wani abun, tana gama faɗin hakan tayi waje " Allah ya shiryaki Maryam Allah yasa ki gane.. bata garisa maganar'ba sukaji diran manya manya motochi a gd " da fara'a Aunty farida ke faɗin oyoyo Aunty salma oyoyo Aunty mardiya" tun Aunty farida bata karisa magarba Zahra tamike a guje tayi waje, mikewa Aunty farida ma tayi tabi bayan Zahra suka bar su diyana a ɗakin " hiyana ta dubisu diyana" kukam bazakuje kumusu oyoyo bane " ni kam bazanjeba dan bansan'suba kilama halinsu irin na Aunty Maryam ne chewar diyana" lamrat da amrat ma sukache muma bazanjeba " baki hiyana ta taɓe tana kallansu zata yi magana sai gasu Aunty farida sun shigo" Aunty farida rike da hannun Aunty Salma "Aunty mardiya rike da hannun Zahra da wani baby boy mai kyau dashi mai kama da yaya khalid,saman sofa suka zauna " da sauri hiyana tafara ɗaga musu gaisuwa" wow Aunty farida wayan nan ƴa'ƴan larabawan fa kodai sune ƴaƴa Abba da ya faɗamin yasamu wasu ƴaƴa daga Allah Chewar Aunty salma " eh wlh salma sune " kai gaskiya bari Abba yadawo ya taimaka yabani wanchan da wan nan tayi maganar tana nuna hiyana da diyana " tab ae kuwa wayan nan yaran nan gani nan bari, inji Abba dan tun farkon zuwar'su nida mardiya mun roka ya hanamu " aa ae ni nace masa zanyi wlh har sai yabani " to Allah yaba da sa'a chewar Aunty farida " ameen Aunty salma ta amsa tare ta chewa ya su nanku ɗaya bayan ɗaya suka faɗa mata su nansu sai wow nice name kawai take faɗi " kutashi kuje kuyi wanka kuzo muchi abinchi " a tare Aunty mardiya da Aunty salma suka mike suka nufi dakinsu " inakuma zakuje Aunty farida ta jefo musu tambaya " ɗakinmu mana " wani ɗakin ae sai dai kuje ɓangaren Ammi dan kuwa ɗakinku yazama ɗakin Yan mata'na har sai randa Ammi ta dawo zasu barmuku ɗakin sukoma nasu " to ae danan da chan duk ɗayane badamuwa chewar Aunty mardiya tayi maganar tare da juyawa tanufi hanyar fita, bin bayanta Aunty salma ma tayi  " Auta ki kiramin masu aiki suzo ku shirya mana abinchi ina zuwa mikewa tayi tanufi ɗakinta " Zahra kuma tasa hannu ta anshi wayar ta a hannun lamrat, tafara kiran layin binta, bugu binya ta ɗaya Zahra tabata umarni tazo ta shirya abinchi tana gama faɗin hakan ta katse kuran tamikawa lamrat wayar

 
SAUDIA

abinchi sukechi chikin nitsuwa shiru palon babu mai magana " Abba me zai hana mutafi gobene dole sai jibine, Chewar Aryan "a sukwane DON ya ɗago yana kallan'sa, shi ko ajikinsa saima latsa wayar'sa yake " meyasa kakesan mutafi gobe Aryan kodai ƙasa mai tsarkinne bakaso chewar Abba " aa Abba bawai bansan kasan bane wlh nagajine inasan inkoma gida " Khalid ya ɗago ya sachi kallan Yusuf sai murmushi suke " Aiman kuma ya kalli Khalid san nan yajuya ya kalli Yusuf yana girgiza kai a zuchiyar'sa yana faɗin muna fukai asirinku yakusa tonuwa ae idanma wani abu kuke shiryawa ɗan uwana to kanku zai dawo " Ahmad kam abinchin'sa kawai yake chi hankalin'sa kwan'che " haidar ya matso kusa da Umar yafara masa magana katsa katsa anya yaya Aryan lafiyar'sa kuwa "umar ya ɗago kai zaiyi magana karaf idon'sa ya sauka chikin na Fahad dake gurga musu mugun kallo " to shike nan Aryan tun da haka kakeso kukira'su farida ku faɗamusu gobe zamu dawo chewar Abba yayi maganar tare da mikewa yanufi hanyar ɗakin'sa " mikewa Ammi da Ummi sukayi sukabi bayan'sa "Aunty amarya kuma tamike tanufi nata ɗakin " kallan Umar da haidar DON yayi yana faɗin me kukejira ae tun bai kai karshen maganar'ba suka mike suka nufi waje, dawo da green eyes nashi yayi kan Fahad, tun baiyi magana'ba Fahad yamiƙe shima yayi waje " green eyes nashi ya jubawa Aryan sosai yake kallansa" Aryan nasane da kallan da DON ke masa amma yaki ɗago kai dan bai da amsar tambayar da DON ɗin zai masa " bazan sake tambayar meke damunka ba dan nalura kaima bakasan meke damun nakaba binchike mai kyau zanyi kawai a kan hakan " sai loakchin Aryan ya ɗago yana faɗin da ka taimakamin bro dan koba komai zaka daina tunanin chewa ina ɓoyemaka wani abu " ajiyar zuchiya ya sauke san nan yamiƙe yana faɗin to sai kuje kushirya ae tunda komawa gobe yakamamu gashi yanzu kusan karfe 4, da ɗai ɗai suka miƙe suka bar palan 


Yola Nigeria

Inna tachi wankan ta tasa wata atampha da bappan, bubu ɗinka mata mayafi ta ɗauka tayi waje, kai tsaye gidan'su buba tanufa, da sallama tashiga gaba ɗayan'su suna tsakar gd " inna sannu da zuwa chewar buba" yauwa buba ya kafar taka " naji sauki ae yanzukam ina ɗab iya takawa batare da sandaba " to alhamdulillah Bappa ina wuni" bappa dattijon arjiki halinsa iri ɗaya da bello mutumin kirki yace lfy habiba anyi sallah lfy " lfy lau bappa inna larai mushiga daga chiki koh" inawuni inna chewar bello " yamutse fuska inna tayi kafin ta amsa da lfy, san nan tawuce ɗaki da sauri dan karma wani ya gaisheta, bello ma albarkachin bappa yana nanne shiyasa ta amsa gaisuwar" miƙewa innar buba tayi tabi bayan inna, innar bello dai dake zaune kan tabarma ta taɓe baki tai tana kallansu har suka shige ɗaki a zuchiyar'ta tana faɗin Allah ya kare mutun daga sharrinku dan kuwa wayan nan idan suka haɗu ko sheɗan suransu yake "

Lfy inna chewar innar buba" lfy ba lau'ba kinga anyi sallah yau yakamata gobe mukoma wajen malam koh dan asamu ayi aikin nan dawuri " aa to mezai hana muje yanzu chewar innar buba " to me zakice wa bappan buba idan zamu fita " aa ae yanzu zai fita dakin ɗan tsaya kaɗan'ma bazaki samesa'ba yanzu dai mujira fitar'sa " to shike nan bari naje gd na ɗaukoh kuɗin nadawo,bata jira amsar innar buba ba tayi waje " da sauri sauri ta shiga gd ɗakinta tanufa tana shiga ta ɗaga yar katifar chiyawar'ta ta ɗauki kuɗin ta kirga sauran 5k ,ta juya tanufi waje, a dab da bakin kofa tayi karo da bappan buba zai fita, matsa masa tai tana faɗin Allah ya kiyaye hanya adawo lfy " amsawa yayi fiska bayabo ba fallasa yayi waje da sauri " ita kuma tayi chikin gd

Tare suka fito da innar buba sai sauri suke zubawa suka nufi hanyar kungurmin dajin nan tafiya mai tsawo sukayi, kafin su kai  wajen duwatsun chikin kogon suka shiga, zaune yake kan wata ƙatuwar dutse ga tukunyar hayaki a gaba sa " da baya baya su inna suka karisa wajen dan dokar wajenne shiga da baya baya

 (ma'anar shiga da baya baya kuwa shine kajuyawa Allah baya kajuyawa alkibla baya kabar halak ka kama haram kabar Allah ke nan ka fiskanchi boka, ya Allah ka tsare mana imanin'mu ya Allah duk halin da zamu shiga ka tausaya mana kabarmu da imanin'mu) 

Kan wani jar shinfiɗa suka zauna, wani mahaukachin dariya bokan nasu yayi ha, ha, ha, san nan yace kuɗin da kika rike ko warware tsarin jikin'su bazai yiba bare har aje gamaga nagaba " to don Allah alagafarta malam.." ke dakata banace baa kiran su nan Allah a nan'ba ko ance maki aikin Allah muke a nan, sheɗan kawai zaki kira mana dan kuwa aikin'sa muke " kayi hakuri to kataima'kamin ina chikin damuwane idan yaran nan na raye " zan iya taimakawa na kunce tsarin dake jikinsu ke kuma sai kinemo kuɗin aikin daza'a amusu amma da sharaɗi " menene sharaɗin komanene zanyi" to farko dai ajiye kuɗin dakikazo dashi, na biyu kuma zaki bani kanki " to inna tace tare da ajiye kuɗin chikin wata kwarya, idon ta yarufe bataji bata gani" boka kuwa ganin inna ta aminche yasa ya umarchi innar buba da taje waje, ba musu ta tashi ta fice " nanfa boka yafara biyar bukatar'sa da inna sai dai abun da bata saniba shine ta baya bokan zai nemeta, ba karamin wahala ta shaba tayi ihun azaba shiko ko ajikinsa bukatar'sa kawai yake biya bayan sun gamane, ya umarce'ta da taje gd bayan kwana uku ta dawo " da kyar inna tamike tana hawaye, tanufi waje nan tasamu innar buba zaune a kan wani dutse " innar buba na ganinta ta mike da sauri tanufeta, tana faɗin sannu, jerawa sukayi suka nufi gida dan yamma tayi sosai " yanzu shike nan zai mana aikin chewar innar buba" aa wan nan abun damukayi iya warware tsarin jikinsu kawai zaiyi nikuma sai nasamo kuɗin aiki " to yanzu ae na zaki samo kuɗin " nima wlh ban saniba amma koma sata zanyi wlh sai na nemo kuɗin " to shike nan amma nawa yace maki kuɗin aikin " 15k yace " tab lallai to Allah dai ya dafa'mana 

(nikoh nace aikin Allah kukene dazakuce Allah ya dafa muku)
inna sai ɗingisa kafa take har suka isa, inna tayi gidanta innar buba ma tayi gida

KANO


Misalin karfe 8 na dare zaune suke a kan table ɗin chin abinchi, Aunty farida ta ɗago tana kallansu tafara magana " Abba yakirani ɗazun yasanar dani gobe damisalin karfe 5 na yamma jinginsu zai sauka a airport" chike da murna Aunty mardiya ke faɗin alhadulillah alhadulillah " ae chanake sai jibi zasu dawo Koh chewar Aunty salma" eh daman dawowar'su jibi ne bansan meyasa Abba yace sudawo gobeba Aunty farida tabata amsa tana kokarin goge bakinta  " to kunga yakamata muje mu kwanta dawuri dan mutashi dawuri saboda aiki  shirye shiryen chewar Aunty Salma " eh hakane yanzu mardiya keda salma kutafi bangaren Ammi nikuma zamuwuce nida sister's ɗinna kamar yadda muka saba, kutashi muje my diyana " ba musu suka mike gaba ɗayan'su sunai'wa juna sai dasafe 

Washe gari tun da sukayi sallar asuba basu mai da barchiba "Aunty farida ta shirya ta tsab chikin a tanfa mai tsadar gaske blue colour wuyarta da hannunta shaƙe yake da manya manya gwala gwala mai kyau da tsada tayi simple make up, plat shoe baki tasa da mayafi baki wayar'ta da ATM kawai ta ɗauka tayo waje, a palo tasamu su diyana" diyana sarkin kwalliya kullun tana chikin kwalliya tana saye da doguwar riga ash colour tayi rolling gyalen rigar a kanta, tayi kyau sosai " Aunty farida ina zakije diyana ta tambaya" shopping zanje kozaki rakanine " eh zanje" to duk wadda zataje tazo muje " diyana da lamrat ne  suka mike, suka nufi Aunty farida" Aunty farida na ganin hakan ta juya tayi waje, suka bi bayanta yau ma dai kamar kullun Shahram ne ya jasu da matsakai'chin gudu yafita gidan 

Sai karfe 4:30 su Aunty farida suka dawo, su Aunty mardiya gaba ɗayan'su sunyi kwalliya sunyi shirin tarban'su Abba " a gurguje Aunty farida ta tanufi ɗaki dan yin waka itama tana faɗin my diyana kuyi sauri ku shirya kuma, tana gama faɗin haka tayi ɗakinta "ɗakin Aunty mardiya diyana da lamrat suka nufa a gurguje sukayi waka dan kar a tafi tarban'su Abba a barsu, diyana dai duk saurin datake sai da ta tsaya tayi make up" gida yachika da jama'a sosai karfe 5:10 dankara dankaran motochi masu numfashine suka jero guda 20 "guda 5 suka fito daga gidan Abba suka tadda 15  afarfajiyar babban get jerawa sukayi suna sharara gudu dan sunyi latti da 10 mnt, gudu suke shararawa sosai chikin ƙanƙanin lokachi suka isa airport, lokachin har jirginsu Abba ya sauƙa sai dai basu fara fitowaba, 

Fitowa daga motachin, su Aunty farida sukayi suka jingina da jikin motar suna jiran fitowar su Abba gaba ɗayan'su,  sun kurawa jirgin ido 
Abba ne yafa saukoh wa a nitse yake takawa Aunty amarya na biye dashi sai Ummi da Ammi a baya " da gudu Aunty mardiya tayi wajen Abba ta rungumesa ita kuma Aunty salma wajen Ummi tanufa, Aunty Maryam kuwa wajen Aunty amarya tanufa, su diyana kam wajen Ammi suka nufa suka rungumeta itama rungumesu tayi tana hawaye " Aunty farida kam tana tsaye jikin mota ko motsawa batayi'ba 
Rike yake trolley a hannunsa yana taku irin na jaruman maza ya saukoh daga jirgin sanye yake da jeans da t-shirt bakake yasa p-cap baki, fiskar nan kafar an aiko masa da mutuwa,Aryan na biye dashi a baya shigarsu ma iri ɗayane  basubi ta kan kowaba sukanufi wajen da motochin ke tsaye," da sauri security dake tsaye a awajen ya buɗe masu kofar ɗaya daga chikin motochin san nan ya anshi trolley hannunsu, " Aunty farida naganinsu tayi gunsu da sauri " DON zai shiga motar ganin Aunty farida na zuwa sai ya ɗan dakata ya juyo tare da buɗe mata hannu, da sauri tafaɗa jikinsa, tana faɗin Wellcome my blood " rungumeta  yayi yana faɗin mun sameki lfy"sakin'sa tayi ta juya ta rungume Aryan dake tsaye tana faɗin, lfy ya hanya " nayi kewarki lovely Aunty chewar Aryan " nima nayi kewarku sosai wlh ta karisa maganar tana sakin Aryan, 
Chikin motar suka shiga gaba ɗayansu ukun, sukasa Aunty farida a tsakiya " DON yabawa driver umarnin yawuche dasu gd " ba musu driver yata da motar da ma tsakaichin gudu yabar airport ɗin " mamakine yakama Abba har yake faɗin kai Allah ya shiryamin Safras da Aryan da farida, wato ita farida tunda taga yan uwanta shike nan batada wata damuwa to Allah ya kara haɗamin kanku, Amin dukkan jama'ar wajen suka amsa dashi san nan suka ranƙaya gaba ɗayan'su suka shiga motochin lokachin har anfara kiraye kirayen sallar mangariba,
A jere kuma a nitse motochin suka bar airport ɗin suka miki titin gida 
A dai dai bakin katafaren babban gate motochin suka rage gudun nan take security suka wage musu gate ɗin, suka kutsa chikin gd, 15 daga chikin motochin sukayi parking a harabar wajen 4 daga chiki kuma suka kusa garamin gate suka shiga chikin gd gaba ɗaya,kai tsaye parking space sukanufa " suna kashi motochin da sauri security suka fito suna bubbuɗe kofar motochin " Su Abba suka fito, Abba ya dubesu yana faɗin kuyi sauri kuyi alwala gashi har za'a tada sallah, yana gama faɗin haka yajuya yayi ɓangaren'sa da sauri " Ammi ma ɓangaren'ta tanufa rike da hannun amrat da lamrat dayana  hiyana da Zahra na biye da ita a baya " Ummi kuwa rungume da salma tana rike da Aunty mardiya da ɗayan hannun'ta suka shiga ɓangaren'ta "Aunty amarya rike da hannun, Aunty Maryam suma suka nufi nasu ɓan garen" su Khalid kuwa kowa yanufi nasa ɗakin 

Ammi nashiga palo ta saki hannun'su tana faɗin kuyi sauri kuyi alwala koyi Sallah sai muje palon Abba mu gaisa koh tana gama faɗin haka ta nufi hanyar ɗakin'ta  suma kowa tayi ɗakinta hiyana diyana dakuma Zahra suka nufi ɗakinsu, Amrat da lamrat ma sukayi nasu ɗakin 

Bayan sunyi sallah sungamane gaba ɗayan'su suka nufi palon Abba already Ammi tariga da tatafi chan " da sallama suka shiga gaba ɗaya family suna zazzaune kan table ɗin chin, abinchi ido kowa ya ɗaga yana kallan'su banda DON dayake duke yake latsa wayar'sa " a hankali Aryan ya dago ash eyes nashi yana kallanta still dai da light make up face ɗin ta ɗan karamin bakin nan yasha lips'gloss, kasa ɗauke kansa yayi daga kallanta sosai ya zuba mata ido sai taunan chingom take " yusuf ne ya dawo dashi hayyachin'sa dacewa oyoyo my baby ku karaso mana, wajen table ɗin suka karisa gaba ɗaya ba wanda ya lura da chiwon goshin hiyana dan dasafe anchire mata ban dejin
Zama sukayi " Aunty farida tabawa masu aiki umarnin su zuba musu ferfesu kayan chikin SA da chips " sannu da dawowa Abba ya hanya chewar hiyana " Ammi tace kibari mana sai angama chin abinchi sai ayi gaishe gaishen Koh " aa Aisha karki takurawa ƴa'ƴana yayi maganar yana kallan Ammi, dawo da kallansa yayi kan hiyana lfy ya..... Bai karisaba maganar ba idonsa daya sauka kan goshinta, subhanallah hiyana meyasameki a goshi haka a razane yayi maganar " gaba ɗaya idon mutanen palon yadawo kanta har shi kanshi DON sai daya ɗago kai dan jin yadda Abba yayi maganar " sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da yan yatsun hannunta," Abba faduw... Bata karisaba tajiyo," diyana na faɗin Aunty Maryam che tamana bugun mutu har sai da aka kaimu asibiti " nan take ido jama'ar palon yadawo kan diyana lbr tashiga basu dalla dalla kamar antam bayeta" what? Abba yafada yana mikewa " shiru palon yayi ba mai magana, Abba zai sake  magana ke nan sai sukaji sallama a bakin kofar palon, amsa sallamar Abba yayi tare da faɗin shigo mana " ɗaya daga chikin security ne kasa ya duka yana faɗin yallaboi kana da baki a waje " ok nasan da zuwan'su gani nan zuwa yana gama faɗin hakan yakama hanyar fita " Abba nafita Ummi ta dubi Aunty Maryam dake zaune hankalinta kwanche tace haba maryam me yaran nan suka miki zaki musu irin wan nan bugun " dogon tsaki Aunty Maryam taja san nan ta ɗora dacewa na tsanesu ne shiyasa na bugesu ko zaki rama musune" gaba ɗaya palon kallon Aunty Maryam suke " me yasa kika tsanesu Maryam, laifinme suka miki Ammi ta tambaya a nitse " ke Aisha badake nakeba banzo kankiba tu kun nan tsanar dana ke mikine ae tasha fesu " a fusache DON ya mike ya ɗaga yasu biyar zai zabga mata mari green eyes nashi ya sauƙa chikin na Aryan dake zaune ya zuba musu...✍️✍️


Yau nayi kokari namuku long page to ina buƙatar more comments

Iya comments iya read more amma jiyama kunyi kokari kunmin comments dayawa ina godiya 🙏

*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*


*Episode 20*
            



A fusache DON yamike ya ɗaga yatsu biyar zai zabga mata mari green eyes nashi ya sauƙa a kan face ɗin  Aryan dake zaune ya zuba musu ash eyes nashi " da sauri Ammi tace karka kuskura ka kai hannunka jikinta takarisa maganar a fusache"a hankali DON ya sauke hannun'sa sai huchi yake tamka wani zaki, bai karisa sauke hannun'sa ba, yaga Aryan ya miƙe ya ɗauke Aunty Maryam dawani gigitachen mari yasake kara mata ta ɗayan gefen kumatun a fusache yayi kanta daniyar bugunta " da sauri DON  ya rikesa yana faɗin NO Aryan NO idan kace zaka bugeta a yanayin dakake'n nan wlh zaka iya kasheta " Prince kasake kasakeni nacema Aryan yayi maganar chikin tsawa da zafin rai " bazan sake kaba Aryan kadawo chikin hayyachin'ka mana kasan me kakesan aika tawa kuwa " Aryan idon'sa ya rufe chikin tsawa yake magana Safras nache kasakeni koh "DON yalura Aryan baya chikin hayya'chensa, dan kuwa baitaba kiransa da Safras ba sai dai yace DON kokuma prince dan haka sai yayi kokarin jansa sutafi ɗaki " Aunty Maryam kuwa rungume Aunty amarya tayi tana kuka " Ammi tamatso kusa da Aunty amarya tana faɗin kiyi hakuri Maryam " chikin kuka Aunty Maryam ke faɗin munafuka ina ruwanki dani duk bake kika haddasa fitinarba " wani kukan kura Aryan yayi ya kwache daga rikon da DON yamasa yanufeta gadan gadan fiskarnar tasa gaba ɗaya ta sauya idon'sa sun ƙaɗa sunyi jaa sai huchi yake jijiyoyin kan nan nasa duk sun miƙe gadan gadan ya tun kareta kamar wani mayinwachin zaki " aguje kannen nasu sukabar palon, yarage iyayen nasu sai Aunty farida  Khalid da kuma yusuf  Aiman da Ahmad ma sun gudu dan sun san hali Aunty salma Aunty mardiya ma duk sungudu " harɗe hannu a kirji DON yayi a zuchiyar'sa yana faɗin awan nan karon kam bazan  hanaka ba Aryan dan kuwa ta tsallake iyakarta ka bugeta kai ɗin  zaifi domin ni innace zan bugeta tofa sai dai a ɗau gawarta shiyasa tun ɗazun nake kokarin danne zuchiyata karta haura

  Aunty Maryam ganin Aryan ya nufota gadan gadan ne yasa ta zame jikinta daga na Aunty amarya zata gudu "wani damƙa Aryan yawa wuyar'ta, ta baya yajata ya bugata da jikin table,ya sake damkoh wuyar'ta yana kokarin kai mata wani bugun" ganin Aryan na kokarin kisan kai yasa Aunty farida ta nufesa da gudu " a fusace yaɗaga hannu zai 'kaiwa Aunty Maryam bugu a fuska da sauri Aunty farida ta kama hannun ta baya " azuchiye yajuyo yana faɗin kasakeni DON tun bandawo kankaba ganin Aunty farida che ta rikesa yasa ya sassauta murya,pls pls Aunty farida sau ɗayan nan kawai ki kyaleni na hukunta Maryam, tun batayi aure ba takewa su Ammi wan nan rashin kunyar, dan Allah yau kubarni na dawo da ita kan hanya " 

Aryan idan kasake ɗaura hannunka a jikin Maryam dasu nan duka ban yafemaka ba chewar Aunty amarya tayi maganar rai a bace, "runtse ido Aryan yayi ya kwache hannun'sa daga chikin na Aunty farida zuchiyar'sa na tafasa  yajuya a fusace yanufi hanyar fita daga palon " Abba dake tsaye a bakin kofa tun ɗazun yana kallan'su yakasa shigowa yasa hannu ya tare Aryan yana kallan fuskar'sa" juya mukoma chiki chiwar Abba,  gaba ɗaya jama'a dake chikin falon suka juyo suna Abba " a nitse Aryan yajuya ya koma ya zauna a kan kujeran table ɗin " Abba bi bayan'sa da kansa ya buɗe robar ruwan faro mai sanyi ya zuba a glass cup yamiƙawa Aryan " ba musu ya karɓa ya sha" ku zauna gaba ɗayan ku Abba yabasu umarni rai a bace " zama sukayi a kan kujerun" tashi kema ki zauna chewar Abba yayi maganar yana nuna Aunty Maryam dake kwanche kasa tana kuka, da kyar tamike ta zauna a kan kujeran itama kusa da Aunty amarya, ga shatin yatsun Aryan biyar a kan kunchinta gefe dukka biyu "A nitse Abba yafara magana abu biyu zuwa uku nakesan faɗa a nan kubani hankalin'ku ta farko  nan umarni'ne ba shawara ba duk wan da yayi laifi a gd yazama dole a hukuntashi dan haka hajara kijanye kalamanki nachewa kar Aryan yasake,taɓa Maryam yazama dole intayi laifi sumata hukunchi,duk datake babba a kansu intayi ba dai dai ba zasu mata hukunchi, na biyu wan nan maganar ta mutu daga nan "  na uku ke Maryam wlh kinji na rantse ko ko kallan banza kika sake yiwa yaran nan to ban yafe'miki ba, ba ruwanki dasu tunda bazuwa ɓan'garen'ku sukeba, ya karisa maganar chikin faɗa,sai dayaja, kutashi kuje kuyi sallah lokachin sallar issha yayi " da sauri Aryan ya miƙe daman kamar a kan kaya yake dan baisan ganin Aunty Maryam, miƙe'wa DON ma yayi da sauri yabi bayan'sa, dan yaje ya taushesa, yadaɗe baiga Aryan a irin wan nan bacin ranba "Khalid da Yusuf ma suka mike sukabi bayan'su DON " Aunty farida takama han'nun Aunty Maryam sukayi waje,"Ammi da Ummi ma suka mike a tare " Abba yace Aisha keda hajara ku zauna zanyi magana daku,"Ummi  najin haka tayi waje" Ummi nafita 

A nitse chikin sanyin murya Abba yafara magana," ke Hajara banace kijanye maganar dakikayi tsaka'nin Aryan da Maryam ba,banji kinche komaiba " na janye Aunty amarya tafaɗa tana ɗaure fuska " to tashi kije kiyi alwala kiyi sallah,"mikewa tayi tana kunkuni tafice daga palon 
sai da Aunty amarya tafice san nan Abba yadawo da kallan'sa kan Ammi yafara magana, idan yaran nan sunyi sallah kisa diyana ta kaiwa Aryan coffee kinji " to amma ranka shi daɗe kagafa ran'shi a ɓache kuma kusan diyana'ce ta hadda'sa masa ɓachin ran, idan taje bazai bugeta ba kuwa Ammi ta karisa maganar kamar zatayi kuka "  Abba yace aa Aisha bantaɓa magama kimin musu ba komai nace to kawai kike chewa yanzu'ma to kawai nakesan kice kuma ki isar wa diyana da sakoh na, ya karisa maganar yana kokarin mikewa a chikin zuchiyar'sa kuwa yana faɗin ae diyana ce kawai zata iyasa Aryan ya saukoh domin kuwa duk wani motsi na ƴa'ƴana ba wan da ban sani'ba duk wani abun da Aryan keyi ina sane dashi yanzu haka ba abun dayake bukata daya wuce yaga fuskar'ta  da wan nan tunanin yashiga ɗaki, " Ammi kuwa jiki ba kwari ta miƙe tafice daga palon tanufi ɓan'garen'ta

 Ammi na fita palon Abba kai tsaye,ɗakin'su diyana tanufa, da sallama tashiga " kwanche suka su uku a kan gadon'su hiyana diyana Zahra, su amrat sun koma ɗakin'su " suna ganin Ammi suka miƙe zaune,karisa shigo chiki Ammi tayi a bakin gadan ta zauna tasa hannu dafa hiyana tana faɗin sannu koh, Allah ya baki lfy " hiyana tace amin, Ammi ina wuni " murmushi Ammi tayi kafin tace lfy kunyi sallar issha'ne "aa bamuyi ba chiwar diyana " to kutashi kuyi sallah zansa a kawo muku a'bunchi kuchi sai ku kwanta ku huta koh " har suna haɗa baki wajen chewa to Ammi a tare suka miƙe,  
Ammi ma tamiƙewa tayi tanufi hanyar fita, har ta kai bakin kofa kuma sai tajuyo ta dubi diyana, ke diyana idan kinyi sallah kikai'wa  yayan'ku Aryan coffee " kaiii Ammi tsoran'sa fa nake ji kar naje ya bugeni " aa diyana bazai bugeki ba kiyi sallah kije ki haɗa masa da sauri " to Ammi amma zanyi wanka tukun nan " to koma me zakiyi dai kiyi dawuri ki kai masa takai karshen maganar tana mai fichewa daga ɗakin 

Toilet diyana tashiga tayi wanka a gurguje ta ɗauro alwala tafito, tana fita Zahra tashiga itama danyin wanka," shifiɗa dardu'ma diyana tayi ta ɗaura zani tasa hijab, kawai tatada sallah,"tana sallame, sallar tayi adduar, ta sosai tashafa ta mike zata naɗe, daddumar " hiyana tace aa kibarmin zanyi Sallah" to kawai tace tanufi gaban mirrow " diyana mezakiyi hiyana ta tambaya tana taɓe baki " kwalliya,mana me zanyi,kuma " kwalliya da daddare to Allah ya shirya'ki " Ameen to tun da addua che diyana tafaɗa tana kokarin shafa foundation a fuska " light make up tayi a face nata ta ammafa bakamin kyau tayiba, jan baki pink colour tasa a ɗan karamin bakin nan nata, sai kallan kanta take,a mirrow "Zahra dake zaune bakin gado tana jiran diyana ta matsa, awajen mirrow, itama tazo tashafa'mai," tace kai diyana kinyi kyau har kingaji da kyau dan Allah kije, kisa kaya kikai'wa yaya Aryan coffee sa karyazo ɗakin nan ya same'mu " dariya diyana tayi tana faɗin, Allah Aunty Zahra nayi kyau " eh mana sosaima yanzu dai jekisa kaya," da farinchiki a face ɗinta tajuya tanufi sip ɗin kayan'su doguwar rigar da Aunty farida ta kawo musu ta ɗau koh, zatasa  ke nan " Zahra tace diyana yakamata kisa bra kafin kisa rigar nan zaifi zama maki da kyauu  dan kinga yana da igiya inba bra, aka ɗaure igiyar baya kyau " yauwa Aunty Zahra idan dai zanyi kyau kawai kisamin diyana tafaɗa tana murna " shiru Zahra tayi tana tunanin wai ita'kam diyana inazata kai kyau'ne, duk wan nan kyan da Allah yamata, bai isheta'ba take neman kari, duk wani abun da kacewa diyana zai ƙara mata kyau tofa koda abun bai mataba sai tayi amfani dashi itadai kawai taji anche taƙara kyau, Zahra tayi nisa chikin tunani bata an'karaba kawai sai taji " diyana na taɓata Aunty Zahra kisamin abubuwan bra ɗin " to juya nasa miki " juyawa diyana tayi zahra tasa mata karfen bra ɗin " hiyana dai baki ta taɓe tana ganin ikon god" komawa diyana  tayi gaban sip ɗin ta ɗauki rigarta tasa, ta ɗaura  igiyar rigar  tayi kyau sosai ta ɗauki mayafin rigar ta rufa akanta tanufi wajen shoe rack nasu high heel blue kalar rigar ta ɗauƙa tasa tanufi waje kwas,kwas,kwas, abunta " 
baki buɗe hiyana ke kallan diyana har tafita ajiyar zuchiya ta sauke ta dawo da kallanta kan Zahra"Aunty Zahra kinsan me " Zahra tace aa bansaniba hiyana am sai kin faɗa " wlh inaga nan gaba kasuwa kwalliya gaba ɗaya za a'ɗaukowa diyana " dariya Zahra tayi tana faɗin eh gaskiya kam naga alama nima " hiyana zatayi magana sukaji kwas,kwas,kwas, " ba ko sallam diyana tashigo da sauri gaban mirrow takoma ta ɗauki kwal'bar turare hunrar da Aunty farida ta bata ta shafa a jikinta dan Aunty farida ta faɗa mata indai batasa turare bazatayi kyau ba da sauri ta ajiye kwal'bar tanufi waje " su dai su hiyana sunga abun dayafi karfin'su " miƙewa hiyana tayi daga kan daddumar takoma kan gado ta kwanta " zahra Kuma ta ɗauki hijabin'ta  tasa tatada sallah

A gurguje ta haɗa masa coffee ta ɗauka tanufi ɓangaren'sa da sallama tashiga palon babu kowa kai tsaye tanufi betroom ɗin sallama tayi a bakin kofa, bata jira an amsa'ba kawai tashige chiki " kwanche yake a katafaren gadonsa idonsa a lumshe farin singlet da short ne kawai a jikinsa asalin kirar'sa na jaruman maza ya bayyana ga wani gashi baki kwanche a chin yoyin'sa har zuwa kafofin'sa damtsen hannun'san nan kuwa kamar zasu fashe saboda karfi " kan ɗan karamin table na chikin ɗakin ta ajuye coffee ɗin tanufi bakin gadon, zama tayi kusa dashi a nitse da cool voice kamar mai raɗa tafara kiran sunansa, tana ɗan bubbuga hannun'sa yaya Aryan, yaya Aryan katashi na kawoma coffee karyayi sanyi " slowly yafara ware ash eyes nashi wanda suka chanza zuwa launin jaa, sauke idan nashi yayi a kan face ɗin ta, ƙara waresu sosai yayi yana kallan'ta " diyana sai data tsorata ganin yadda idonsa suka chanza launi" mikewa tayi zata gudu " hannu yasa da sauri ya riƙo hannun'ta,  ya jata baya, ta koma ta zauna" kallanta yake sosai, nan take yaji wani sanyi na ratsa zuchiyar'sa wani farinchiki yaji, jiyake wani bakon yanayi na ziyartar zuchiyar'sa" turo ɗan bakin nan nata tayi kamar biro a shagwaɓe tafara magana yaya Aryan kayi hakuri kaji dan Allah karka bugeni, ta karisa maganar kamar zatayi kuka "shiru yayi yana kallan'ta, yakasa magana almost 10 mnt suna zaune haka yanata kallan'ta,kamar yamai data cikin'sa yakeji"turo baki diyana tasakeyi tana faɗin yaya Aryan dan Allah fa nace kayi hakuri ba dan niba" ɗan firgita yayi yadawo daga duniyar tunanin dayashiga" calmly yafara magana baki iya gaisuwa bane kuma wayace kiyi kwalli da daddaren nan" kayi hakuri to, ina wuni tafaɗa tana kun bura kumatu" sakin hannunta yayi tare da mikewa zaune " itama ganin yasaketa tamiƙe tana kokarin tafiya " ina zakije ya tambaya yana kallan'ta from head to toe " ɗaki zanje " nace kitafine " aa kayi hakuri "to dawo nan ki zauna yayi naganar yana nuna mata drawer kefen gadon " saman drawer taje ta zauna tana fiskantar kofar toilet 
"juyo nan ki kalleni magana zanyi dake, a nitse ta juyo tana fuskantar'sa,ganin itayake kallo yasa tayi ƙasa da kanta tana murza yan yatsun hannun'ta " dawo da kallan'sa yayi kan hannun'ta sosai yake yakara waro idan'sa yana kallo lallenta, ba'ƙaremin kyau lallen yayi masaba " wayamiki wan nan abin yayi maganar yana nuna lallen nata " laaa Aunty farida ta kaimu a kamana mana kuma kasanme takawo min kayan kwalliya dayawa" zuba mata ido yayi yana kallan yadda take murmushi take magana a zuchiyar'sa yace thank God nima nasaya kayan kwalliyar 
afili kuwa yace baki bani amsa taba nace wayace kiyi kalliya da daddaren nan" nan take ta ɓata fuska ta daina murmushi ta turo baki tana faɗin yaya Aryan baa kwalliya da da'ddare'ne  "anayi mana kuma kinyi kyau sosai kawai dai nine banasan kirinƙayi " nan take kuma tafara murmushi tace laaaa yaya Aryan da gaske nayi kyau ta tambaya " girgiza kai kawai yayi ya zuba mata ido yana kallan yadda take dariyar azuchiyar'sa yake faɗin kekam komai kikayi kyau yake maki inkina dariya ki ƙara idan kina murnushi makura che ke, kai ko kuka kike kyau yake miki " katse mishi tunani tayi dachewa yaya Aryan intafine" girgiza mata kai yayi alamar aa "kallansa tayi sosai sai kuma tace laaaa Yaya Aryan kayi rashin lfy ne" me kikagani yayi maganar da ɗan mamaki a face nashi " ae Naga karame'ne tafaɗa tana kara kallan'sa sosai  " yayi mamakin sosai da jin abun da tace,a zuchiyar'sa yake faɗin wow intelligent girl,tabbas ni kai na nasan na rame amma bawan daya gane hakan ko DON damuke tare bai gane hakan ba sai ke wow,  

Ajiyar chiya ya sauke ya ya juyo da idansa yayi kanta yaga itama shi take kallo," sai yace aa banyi rashin lfy, jeki kawomin coffee ɗin karyayi sanyi " da sauri ta mike tanufi inada ta ajiye coffee ɗin ta ɗaukoh,ta dawo tamiƙa masa " ansa yayi yana faɗin to zauna muyi magana" zama tayi a inda tatashi ta zuba masa ido tana kallan,yadda yake shan coffee ɗin,"yaya Aryan kasan me" ɗago ido Aryan yayi yana kallanta batare dayayi magana'ba " tachigaba dacewa Allah yaya Aryan kana kama da wan da yayi film ɗin Bahubali, nan Amma fa kafishi kyau, yama sunan shi, taƙarisa maganar tana ɗaga kai kamar mai tunani" da mamaki yake kallanta yana tunani wae daman yarinyar nan tana kallan mutane ne, murmushi kaɗan yayi yace nima bansan sunan shi ba ae " to zan tanbayi Aunty Zahra sunan shi sai nazo nafaɗama " batare da ya amsa mataba yace tashi kije ki ɗaukoh min trolley ɗin chan yayi maganar yana nuna mata inda trolley yake da hannun'sa " da sauri ta miƙe tanufi wajen tayi tunanin trolley bai da nauyi, sai tasa hannu ɗaya zata ɗauka amma sai taji a'kasin hakan dan kuwa ko motsa trolley ta kasa, shi kuwa Aryan ya zuba mata ido yana kallan'ta 
Dad dagewa tayi da iya karfin ta ta jawo trolley baya baya tayi tafaɗi trolley ya faɗo mata a kan kafa kara ta fasa mai sauti " a sukwane Aryan ya ajiye cup ɗin hannunsa ya ya miƙe ya nufuta hannu ɗaya yasa ya ɗaga trolley ya ajiye a kan gado, ya dawo kusa da ita ya duƙa yasa hannu ya kama kafar nata yana faɗin, menene abun kuka kuma, " yaya Aryan wlh da zafi tafaɗa chikin muryan kuka" a haka kike chewa zaki auri soja matan sojoji fa jarumai ne " turo baki tayi ga hawaye na zuba a kunchin'ta chikin shagwaɓa tace Allah yaya Aryan nima jaruma'ce " zuba mata ido yayi yana kallan yadda take Magana gwanin burgewa, hannu ya kai kan fuskar'ta zai share mata hawayen sai dayaji wani shock saboda laushin da tsasin fatar ta, da sauri ya janye hannun'sa baya yamiƙe tsaye yana faɗin to tashi kizo ki karɓi tsaraba yayi maganr yana hawa kan gadon'sa " a sha'gwaɓe tace wayyo Allah yaya Aryan Allah bazan iya tashiba "a sukwane Aryan ya juyo yana kallan'ta, dan yadda tayi maganar, " a hankali kamar bayasan buɗe bakin nasa yace ki daina kukan nan ko gashi nan ae kina ɓata kwalliyar'ki " da sauri tasa hannu ta goge hawayen tana faɗin yaya Aryan kwalliyar ya bacine " dariyace ta kubche masa dan yadda tayi maganar,"bai bachiba yabata amsa yana murmushi " da kyar tamike tanufi kan drawer tana ɗingisa kafa ta zauna "hayewa gadan yayi yajawo trolley ya ɓuɗe, wasu ma tsakaitan jakun kuna guda uku yachiro, daga chikin trolley ɗin, ya juyo ya dubeta yafara magana,"wan nan farin tsarabar kine a chiki, wayan nan bakake biyun kuma kibawa'su Zahra "da sauri tamiƙe ta haye kadon itama ta jawo jakunkunan tana faɗin Yaya Aryan har da kayan kwalliya"kallan'ta kawai yake yadda take zumuɗi, da farinchiki, bai ma san sanda yace, daman farinchikin da dariyar ki kawai nake burin, gani "sai jin diyana yayi tana faɗin to Yaya Aryan dariyana yana da kyau'ne " firgigit yayi yana kallan'ta kwashesu kije ɗaki kiɓuɗe a chan" to kawai tace san nan ta saukoh daga dagon tasa hannu tajawo jakunan amma takasa ɗauka sunyi nauyi bazata iya ɗauka dukkaba" ido yazuba mata yana kallan'ta" turo baki tayi zatayi kuka " da sauri yace aa karkimin kuka ki ɗauka mana ɗai ɗai ae bawanda yace dole ki haɗa'su koh " nasu Zahra ta ɗauka ta bar nata zataje ta dawo suma da kyar ta iya ɗauka gakuma high heel a kafarta 
har tafita kallanta Aryan yake, wani ajiyar zuchiya ya sauke yamike yanufi toilet dan yin wanka

lokachin da diyana ta dawo ta ɗauki ɗayan jaka'r Aryan na toilet yana wanka bai fitoba ɗaukar jakar tayi yajuya har takai bakin kofa saikuma tajuyo ta ɗaga murya yaya Aryan sai da safe tana gama faɗin hakan tayi waje, ko data'dawo ɗakin'su su Zahra har sun buɗe jaka'r nasu tsarabar dogayen riguna'ne masu kyau da perfumes masu kanshi da tsada sai murna suke, zama tayi a bakin gado itama tafara kokarin buɗe nata jakar amma sai'taga nata jaka'r an sawa zip ɗin kwa'ɗo,  tayi tayi yaki,ɓuɗuwa sai ta ɗauki jakar tanufi sip dashi tana faɗin sai da safe na kaiwa yaya Aryan ya buɗemin,ajiye jakar tayi,tachire kayan jikinta ta ɗaura towel tashi toilet tayi wank atazo gurguje tasa kayan barchi tanufi kichin ta haɗa coffee tasha tadawo ɗaki  ta haye gadon'ta nan take barchi awon gaba da ita


Yau tun asuba ake shirye shiryen walima da naɗin sarauta " Ammi tasha kwalliya da wata ɗankarekiyar,shadda tasha aikin har kasa Blue colour tasa wasu shaggun sarkan da abun hannu na gold mai shegen tsada ta ɗaukoh wani ɗankareriyar al'khaiba baki anmasa kwalliya da wasu suwasu mai kyalli fari tasaka a jikinta kai kace yar shekara 20 sosai kyanta yasake bayyana,"wayar'ta ta ɗauka tafa kiran layin Zahra, kira ɗaya Zahra ta ɗaga tare da faɗin hello Ammi" Ammi tace kuzo gaba ɗayan'ku kusameni a ɗaki tana gama faɗin hakan ta katse kiran, ta zauna a kan gado tare da ajiye wayar'ta a kusa da ita

Da sallama su Zahra suka shigo sunsha kwalliya sosai riga da sket na atamfa Zahra hiyana diyana sukasa,"amrat da lamrat kuma duguwar riga, karisa shiga chiki ɗakin sukayi " Ammi tace aa harkun shirya ne" har suna haɗe baki wajen chewa eh "ae ba wan nan kayan zaku saba Zahra'u tashi ki buɗe drawer kayana ki ɗaukoh muku kwalin kayan da zakusa, sai ku koma ɗaki ku chanza " da sauri Zahra tamiƙe ta ɗaukoh musu sarine irin na indiyawa, kwali biyar kowa da kalan nasa " Zahra baki,hiyana pink, diyana blue,lamrat jaa,amrat maroon" da zumuɗi diyana ta ansa nara tana faɗin Aunty zahra irin kayan danake ganin indiyawa suna sawa a TV nan ne " Zahra tace eh shine" to ae Aunty Zahra ban iya sawaba tayi maganar kamar zatayi kuka " dariya Zahra tayi tace to muje na koya miki" da fara'a diyana tamiƙe har suna haɗe baki wajen chewa Ammi mungoɗe 

Dakin su suka koma Zahra tafara nuna musu yadda ake sawa wow kayan yamusu kyau sosai da sosai hiyana da amrat nasu najaa a kasa sosai dan yafi tsawon'su
  yau make up sosai sukayi dukkan'su baƙaramin kyau sukayiba, hiyana kamar ita tayi kanta yau asalin kyanta ya bayyana datayi make up, Zahra sai santin kyan hiyana take har ita kanta diyana sai da tayaba kyan da hiyana,tayi" Zahra tace kai kuzo mutafi fada dan nasan yanzu gaba ɗaya an haɗu awajen kar ayi bamu kuyi sauri tayi maganar tana kokarin fita ɗakin " da sauri suka bi bayan'ta

Yau fada chike yake tab da jama'a baki dayawa sunzo dan naɗa sabon sarki da za'ayi Abba yasha kwalliya irin na sarakuna sosai yayi kyau yana zaune a kan kujerar sarauta Ummi Ammi Aunty amarya suna gefensa ga wasu kugeru a gefe dama da a ka jera wanda su Khalid, Aiman, Ahmad, Yusuf, Fahad, Haidar  umar Aunty farida Aunty salma Aunty, mardiya, Aunty, Maryam, ne zaune awajen, "kujerun gefen hagu kuma manya manyan saraku daga sassa daban daban na Nigeria da ma makwabtar kasashe irinsu niger,Cameron, Ghana,chadi, da dai sauran'su , ga manya manyan  yan siyasa a gefe guda " DON da Aryan ne kawai basa wajen,  fada yayi tsit kamar babu mutane a chiki kowa yayi shiru suna jiran juran jawabin Abba 

Da sallama ɗauke a bakinsu suka shigo fadan, gaba ɗaya jamar waje suka ɗago suna kallan'su kamar wasu taurari sai wal'wali  da kyalli suke " gaban Abba sukaje suka duka hiyana'ce tafara ɗagawa Abba gaisuwa "yusuf sai kallon lamrat yake yakasa ɗauke idonsa haka shima Khalid sai kallan Zahra'n sa yake " da fara'a Abba ya amsa gaisuwar tasu ya ɗora dacewa kutashi kuje kuzauna kusa dasu farida, to sukache tare da miƙewa suka nufi wajen'su Aunty farida " diyana kije ki kiramin Aryan ke kuma hiyana kije ki kiramin Safras Abba yafaɗa yana ɗaure fuska dan Aryan da DON sun ɓata masa rai tun dazun ake juran'su amma shiru" da sauri diyana ta juya ta fita, itakuma hiyana tafiya take kamar wadda kwai yafashewa,a chiki kamar zatayi kuka tafito daga fada ta nufi chikin gd

A hankali ta tura kofar ɓangaren nasa tashiga, sallama tayi a palon, kasa babu kowa kamar zatayi kuka ta shigo chikin palon babu kowa, a nitse ta haura stair ɗin tsayuwa tayi a bakin kofar betroom ɗin tanata doka sallama amma shiru shiru almost 20 mnt bataji wani motsi'ba, a hankali ta hannu ta tura kofar tashiga, tana shiga taji kofar yayi kara alamar ya rufe kanshi juyawa tayi tana bin ɗakin da kallo wani katafaren gadone mai girma da kyau yana shinfiɗe da betshit na alfarma Sky Blue ga wani haɗaddɗen sofa guda ɗaya a gefe sai wasu tagwayen kofofi  da alama ɗaya kofar toilet ne ɗayan kuma kofar shan iskane,

 shiru ta tsaya tana tunanin,kuɗin da aka kashe a ɗakin nan jin karar buɗe kofa yasa tayi saurin kai kallanta wajen zubawa kofar ido tayi dan taga wanene zai fito " DON ne yafito ɗaure da towel a kugun'sa ga jikinsa da ruwa da alama wanka yayi "  wani kara hiyana tayi wadda yasashi juyowa a sukwane dan baiyi zatan da mutun a ɗakin'ba " juyowar dayayi bakaramin rikitata yayi ba a guje ta juya taruɗe tama rasa ina zata nufa kawai sai tanufi kofar bangaren hagu tunda taga kofar a buɗe yake tana fita tayi rashin sa'a ta taka sarin'ta dake jaaa a kasa ta kai kai ta tafi kasan bene kallamar shahada kawai take dan tasan mutuwa zatayi..✍️✍️


Tanbaya a nan shin hiyana zata faɗi kasan benen nan kuwa? Shin intafaɗa zata rayu kuwa? ko'ko kar ku manta bene hawa ɗaya tafaɗo daga sama kudai sai mun haɗu



More comments pls 🙏🙏

*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*


*Episode 21*
            


💖الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر💖



Kalmar shahada kawai hiyana take tagama saddakarwa mutuwa zatayi "kamar daga sama taji an damki kafarta ɗaya,wani dogon numfashi taja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuchiya" gaba ɗaya kayan jikinta ya zame ya dawo wuyar'ta daga ita sai ɗan karamin wandon da iya chinya ya tsaya mata ko bra bata saba tula tulan boobs nata awaje "da sauri, DON ya kawar da kan'sa kefe,yana faɗin mikomin hannunki yafaɗa yana ɗaure fuska, hiyana kuwa kayan jikinta ya rufe mata fuska bata ganin'sa hannu kawai ta ɗaga masa " dogon tsaki yaja san nan ya kama hannu nata ya saki kafarta,ta juya suna fiskantar Juna amma idon ta a lumshe "a hankali ta buɗe ido karaf idonta ya sauka chikin nashi, da sauri ta kawar da idon'ta daga kallansa " Ke taka karfe ki hauro yafaɗa yana kara ɗaure fuska " dan Allah yaya prince kayi hakuri wlh bazan iya takawa'ba tayi maganar kamar zatayi kuka " shiru yayi yana tunani wai meyasa ma naka matane, meyasa ban barta, tafaɗa ba wlh badan yanzu idan nasake'ta ta faɗa tamutu nina yi kisan kae ba da sai na saketa, yayi nisa chikin tunani yaji hannunta na zamewa daga chikin nasa,zata faɗa kasa, da sauri yajawota da karfi tafaɗa kan faffaɗar kirjin'sa" hiyana duk tunanin'ta sakin ta yayi tsabar tsorata datayi sai da numfashin'ta ya ɗauke "jin jikinta ya saƙi ne yasashi kallan fuskar'ta hannu yasa ya ɗago haɓar'ta da'alama ta sume "dogon tsaki yaja yana turnuƙe fuska ya saɓeta a kafaɗar sa yajuya chikin ɗakin da ita a saman sofa ya kwantar da ita ya juya yanufi wajen mirrow
Mayukan sa masu kamshi da tsada ya shafa ya feshe jikin sa da perfumes masu kamshi da tsada a nitse ya gyara gashin kan sa sai sheki da kyalli gashin keyi, gashi dark black ga tsansi, a hankali yake takawa kamar baisan taka kasan yanufi dressing room almost 30mnt yayi a chiki san nan yafito chikin suite baki sosai kayan suka masa kyau asalin kirar kijin'sa na jarumin namiji ya bayya half cover baki yasa a kafarsa ga wata ɗankareriyar agogon daimon a hannun sa sai kyalli yake yana ɗaukr ido ya sake fesa,Dubai perfume a jikinsa yadawo gaban drawer ya ɗau wayar'sa yanufi waje, a hankali yake takawa kamar baisan tafiya dakaga fuskar nan tashi kasan yana chikin bachin rae

A bangaren diyana kuwa da sallama ta shigo palon Aryan baya palo Kai tsaye  tawuce betroom nashi, sallama tayi a bakin kofa bata jira ya amsaba,tashiga tsaye yake a gaban mirrow, yagama shiri yana fesa turare, dressing iri ɗaya da DON sukayi,jin anshigo ɗakin'ne yasashi ɗago kai ya kalle'ta tachikin mirrow, "asukwane ya juyo domin ya tabbatar wa da idon itace ko aljana che sosai yake kallan ta "itama shi take kallo dan yau baƙaramin kyau yayi ba " ina kwana yaya Aryan tafaɗa tana kawar da kanta daga kallan sa "kasa amsa gaisuwar nata yayi ya zuba mata ido yakasa ɗaukewa "Abba yace wae kazo da sauri tana gama faɗin haka ta juya daniyar tafiya,"da kyar ya iya buɗe bakinsa yace inazakije kuma "juyowa tayi a hankali fada zan koma tafaɗa tana turo baki,"ok to jira muje yana gama faɗin hakan ya ɗauki wayar sa,ya nufota "a tare suka jera kamar wasu taurari, kyau iya kyau "kayan nan sun miki kyau sosa, yafaɗa yana kokarin jan kofar palon "Yaya Aryan to tunda sunmin kyau kamin hoto dan Allah ta karisa maganar a shagwaɓe "to tsaya namiki guda biyu da wuri kinga Abba na jiran mu,"to hutona wajen guda 15 ya ɗauke'ta batare daya sani ba,"har sai da tace Yaya Aryan baka gama bane," nagama amma matso nan na mana mu biyu "da sauri ta matso kusa dashi,ya juyo da wayar yamusu selfie kala 5 san nan yace,to muje "to ae baka nunamin hoton ba a shagwaɓe tayi maganar tana turo baki "mika mata wayar yayi yana faɗin,to muje muna tafiya kina kalla har mu iso, "to tace tare da fara tafiya

Da Sallama suka shiga fada,gaba ɗaya kallo yadawo kansu," a sukwane Khalid ya ɗago yana kallan su kama yajuyo yana kallan Yusuf yayi da shima Yusuf ɗin kallo Khalid ɗin yake," Abba naganin su atare ba faɗa ba ɓachin rae a fuskar Aryan sae ma annashuwa daya gani a tattare da Aryan ɗin gawani ɗan murnushi da Aryan ɗin keyi yakai kallansa,kan diyana dake gefensa sun gera kafaɗa rike take da wayan Aryan tanata sakin murnushi"wani daɗi Abba yaji ya lulluɓe sa baima san lokachin daya fara sakin murmushi ba,chikin ransa yana faɗin alhamdulillah alhamdulillah, Allah na goɗema saura Safras kuma ya Allah ka kar'katomin da hankalin sa shima yadawo mutun
 "kasa kasa Umar yace wa haidar wai haidar ba wayar,yaya Aryan bane a hannun yarin yar nan,"shine mana haidar yaba shi amsa yana taɓebaki,"Aunty amarya kuwa kamar zata mutu dan bakin chiki tayi kwafa a zuchiyar'ta tana faɗin wlh,nakusa kawo karshen ku,"Ammi da Ummi kuwa ko ajikin su 

"jerowa Aryan da diyana sukayi kamar wasu taurari,sae taku suke a nitse diyana na kallan waya Aryan kuwa ya ɗaure fuska yana kallan kasa sai da suka iso tsakiyar fada, Aryan ya juya yanufi wajen zaman su " da sauri diyana tace yaya Aryan wayan,kafa ta tambaya tana kallan'sa "baga ɗaya jamar wajen ido kawai suka zuba musu "Aryan baiyi magana ba har sai daya kae wajen zaman'l su ya zauna kusa da Khalid san nan ya ɗago ya dubeta kije da wayar idan kingama kallan hoton sai ki kawomin,"mamakine yakama gaba ɗaya family Abba musan man Aiman Aunty mardiya Aunty salma Umar haidar Ammi dakuma Ummi,
"Abba da Khalid da Yusuf kuma sae murmushi suke,"Aunty farida kam tafi kowa murna da hakan, "Aunty amarya na sanyin magana tana tsoran Abba gakuma taron jama'a kar aji kunya,Amma tachi al'washin yin maganin abun " Aunty Maryam kuwa kamar,zata mutu take ji dan bakin chiki,"kusa da Aunty farida diyana taje ta zauna tana faɗin Aunty farida ki kalla tayi maganar tana nunawa Aunty farida wayar Aryan,dake hannun'ta "ansar wayar Aunty farida tayi tafara kallan hotu nan, mamakine ya bayyana a kam face ɗin ta a hankali ta ɗago kae tana kallan inda Aryan ke zaune,"shima ita yake kallo, suna haɗa ido yama alama da ta kashe masa wayar kar tabari kowa yaga hotan, Jinjina kai kawai Aunty farida alamar to san nan ta kashe wayar  ta sa chikin jakarta,"ta chiro wayar ta tamikawa diyana "da sauri diyana ta amsa tana murmushi tafara buga game " tunani Abba yashigayi ba hiyana ba DON anya lfy kuwa buɗe baki yayi zaiyi nagana sae ga DON yashigo shi kaɗai "taku yake irin na jaruman maza gaba ɗaya Jamaar wajen,sai kallansa suka dan yahaɗu sosai mazama burge'su yake bare mata, kusa da Aryan yaje ya zauna " gyaran murya Abba yayi ya dubi DON yafara magana Safras ina hiyana take " shiru DON yayi yana ɗan tunani wacece kuma hiyana,kodai wan nan yarinyar da aka aiko takirani " Abba ne ya katse masa tunani dachewa wai ba kai nake tambaya ba "da sauri yace tana ɗaki Abba yafaɗa yana turnuƙe fuska "gaba ɗaya idon kowa yadawo kansa "to meyasa kabarta a ɗakin Abba ya tambaya yana karewa DON kallo " akule yace suma tayi Abba zan zuba mata ruwa kuma na manta Fahad yaje ya'zuba mata ruwa yayi maganar yana nuna Fahad da hannu " a ruɗe Ammi tace me kamata tsorata kayi koh " ka daure fuska yayi yana faɗin tazo zata faɗine na riketa ta tsorata da yawane shiyasa ta suma, ya karisa maganar kamar zae fasa ihu dan haushi,a ransa yana chewa wlh badan iyayena,ke min wan nan tambayarba da bazanyi maganaba haba dan Allah ayita sa mutun magana, "Ammi zata sake magana,Abba  ya ɗaga hannu alamar tayi shiru "mikewa Fahad yayi daniyar yaje ya zubawa hiyana ruwa "Abba yace kae Fahad dawo kayi zaman ka shi daya razana ta tasume shi zae farfaɗo da ita idan an gama taro sae kaje ka zuba mata ruwan yakarisa maganar yana nuna DON "wani kululun bakin chikine,ya tokarewa DON makoshi a ransa yake wae shin meyasa na tai'maki yarinyar nan ne, meyasa ban  barta ta faɗi ta mutu kowa ya huta'ba wlh na tsani yarinyar jifa yadda Abba yake wani magana sae...bae karisa tunanin ba yajiyo muryan Abba na magana, gaba ɗaya fada tayi tsit kowa ya zubawa Abba ido yana jiran yaji wanene sarki 

Ina mai farin chikin sanar da al'umma a yau ni Abubakar Khalid saraki zan sauka daga kujerar mulki na miƙawa ɗaya daga chikin ƴa'ƴana "asukwane DON Aryan Aiman Yusuf Fahad suka ɗago suna kallan Abba ido chikin ido suna jiran suji su nan wa zai kira gaba ɗayan su kirjin su sae dukan uku uku yake dukkan su kowa na adduar Allah yasa bashi,bane "Aunty amaraya kuwa sae murmushi take dan tasan abun dasuka kulla" Abba kuwa sake gyara murya yayi hankalinsa kwan che yachigaba da magana,a chikin ƴa'ƴan nawa bakowa bane face Ahmad "dam dam gaban Aunty amarya ya buga " DON da bai taɓa murmushi ba a rayuwar sa,yau sae daya saki wani cool murmushi "wani nauyayyar ajiyar zuchiya Aryan da Yusuf suka sauke a tare "Aiman kam har da faɗin alhlillah " nan take zufa yafara ketowa Aunty amarya"Aunty farida kuwa sai alhamllh munyi nasara take faɗi " zubur Ahmad yamiƙe zai yi magana, Abba ya watsa masa harara, bashi yakoma ya zauna "Abba yachi gaba dacewa " kubani hankalin ku ban gama magana ba ae,shiru sukayi suka saƙe nitsuwa yanzu ba sae anjima ba waziri kutashi ku naɗa Ahmad a matsayin sabon sarki,Abba nagama faɗin hakan yamiƙe nanfa jama'a suka fara hira masu murna sunayi masu,blach stomach sunayi, "jama'a suka fara turu ruwa wajen gaisawa dasu DON, "a kafara shigo da abin chiye chiye da shaye shaye 

"sauri sauri gudu gudu Aunty amarya ta bar fada tanufi chikin gida ɓangaren ta tawuce tana shiga ɗaki tafashe da kuka mara sauti ta ɗaukoh wayar ta tana kuka tafara kiran layin sadiya,"bugu ɗaya sadiya ta ɗaga "chikin kuka Aunty amarya tafara magana sadiya mun shiga uku aikin gagarabadau baiyiba sadiya ba Aryan ko Aiman a kabawa sarautaba, Ahmad akabawa "dan Allah hajiya hajara kiyi shiru kidai na kukan nan,mubi komai a sannu,dan anbawa Ahmad sa rauta sae akache maki bazamu iyasawa a chan zashi bane,chewar hajj sadiya" Aunty amarya ta goge hawayen ta tana faɗin to dan Allah sadiya kikoma wajensa gobe inkinje ki tuna masa da batun aikin yaran nan kinji,dan suma yanzu sun fara wuche gona da iri a gidan nan,bakiga yadda samarin gidan nan suka fara shisshige musu bane har da Safras fa wai yanzuma ɗayar yarinyar tana ɗakin'sa ga shigiyar ɗayar kuma ta makalewa Aryan harda bata wayar sa gashi uban su shi ya ɗaure musu gindi yahana kowa magana a kan yaran takarisa maganar chikin ɓachin rai "kai, kai, abun har yakai haka to wlh dole mutsaya muyi maganin  karki damu ae wan nan ni aka taba ba keba dan Safras na zulaihat che dole gobe zan tafi Enugu idan ma gagarabadau bazae iya aikin ba zan tsallaka niger dan ayi mana sha yanzu magani yanzu " to shike nan sadiya badamuwa bari naturo miki kuɗi yanzu batare data kira amsar Hajj sadiya ta katse kiran ta zauna a bakin gado tachi gaba da kukanta

Sai misalin karfe 1:30 a kagama taro jama'a suka fara watse'wa 

diyana kuwa sae chin chocolate suke itada Zahra da amrat "lamrat kuwa tana zaune kusa da yaya Yusuf suna hira kamar wasu kawaye,hiyana kam har yanzu bata farfaɗo ba tana ɗakin DON
Diyana ta ɗaukoh wani carton na chocolate zata buɗe karaf idon ta ya sauka chikin na Aryan dake zaune kusa da Aunty farida suna hira, wani mugun kallo ya wurga mata da sauri ta ajiye chocolate ɗin tana turo baki " diyana lfy kika ajiye chocolate ɗin ki buɗe mana musha mana chewar Zahra "ni Aunty Zahra bana sha sai dai ku kusha tafaɗa tana kunbura kumatu "Aryan daga inda yake zaune bai san san da yayi murnushi ba dan yadda tayi maganar "
 Daga bayansu sukaji a na faɗin, meyasa bazakisha ba yammata da sauri suka juya dan suga wanene wani hadadɗeb saurayine kyakkyawa mai chikar sura "lfy malam Zahra ta tambaya tana kallan face nashi "zama yayi a ɗaya daga chikin kujerun wajen yana faɗin lfy wajen sister ki nazo" wace sister nawa daga chiki Zahra ta tambaya "gata nan yayi maganar yana nuna diyana da hannu "ɗago fiska diyana tayi zatayi magana caraf suka haɗa ido da Aryan, " da mamaki diyana ke lallan yadda ya chanza lokachi guda ta shiga tunani wae Bayanzu naga yaya Aryan na ɗan murnushi ba to me aka masa kuma naga idon sa sun sauya sunyi jaa gashi yawani ɗaure fuska"Zahra che ta katse mata tunanin datake dachewa diyana ana miki magana "firgigit tayi tare da sake kallo inda Aryan yake sae taga bashi a wajen dawo da kallonta tayi kan saurayin,dake zaune gabanta "kallon shi tayi from head to toe a gatsale tace waye kai "ajiyar zuchiya ya sauƙe san nan yafara magana nidae sunana walid ni ɗane ga sarkin zaria,kuma maganar gaskiya son ki nake kuma so irin na aure ba wasaba " wani dariya diyana tayi kafin tace ni kake so amma dai baka da hankali koh to ni matar soja che sojan ma mai manya manyan bindigu "da sauri walid yamike yana faɗin kiyi hakuri wlh ni bansan ke matar aure bace "baki diyana ta taɓe tana mamakin kowaye yafa ɗa masa ni matar aure che daga chewa ni matar soja che to ae ban auri sojan ba tukun nan tayi nisa chikin tunani taji, Zahra na faɗin tashi muje chikin gd muyi wanka muyi sallah "Aunty Zahra wae har yanzu hiyana bata dawoba diyana ta tambaya tana kwaɓe fuska "eh bata dawo ba amma kar ki damu bakiji yaya prince yace tana ɗakin saba "mikewa diyana tayi jiki ba kwari suka nufi chikin gd

Misalin karfe 8 na dare gaba ɗaya family Abba sun haɗu a table ɗin chin abinch har da DON,"Abba yayi gyaran murya yafara magana,ina hiyana take ne yayi tambayar yana kallan Ammi"da mamaki Ammi tace kae badai tun safe yarinyar nan tana sume ba takarisa maganar tana watsawa DON harara "miƙewa DON yayi da sauri dan bai san Abba yafara faɗa yanufi hanyar fita dan shi wlh kwata kwata ya manta da yarinyar,yau kwata kwata bai koma ɗakiba tun daya fita, da sauri yanufi betroom nashi kamar yadda ya kwantar da ita da safe haka ya sameta "dogon tsaki yaja, yajuya yakoma palo ya ɗauko ruwan Faro mai sanyi a freij ya dawo betroom ɗin a gaban gadon ya tsaya,ta buɗe bakin robar ruwan gaba ɗaya ya duddule mata a fuska,"a razane tamike zaune tana ihu,"wani tsawa ya daka mata shoothup, "shiri tayi ta ɗago ido a hankali tana kallansa jikinta sai kerma yake "kawar da kansa gefe yayi yana faɗin tashi kifita min a ɗaki tun ban babballaki ba "da sauri ta miƙe danufin tatafi amma ina wani jirine ya kwashe ta tafaɗi kasa kanta ya bugu da jikin gadon, wani marayan kara tasake dan yinwar datake ji bazai bari tayi kara sosai ba "a fusace DON yace ke me haka kitashi kifita a ɗakin nan nace "chikin kuka da dashewar murya tace dan Allah yaya prince ka taimakeni wlh bazan iya tashiba jiri nake ji ga... Bata karisa maganar ba sakamakon wani mugun kallan daya wurga mata chikin tsawa yace wlh idan baki fita a ɗakin nan ba sai na ballaki "da kyar ta miƙe tana dafa bango tana tafiya, kamar zata mutu ga yinwa ga sarawar da kanta ke mata wasu siraran hawayen bakin chiki da azabar chiwon kae ke bin kunchinta ta kyar ta fito tanufi ɓangaren Ammi "shikuwa DON kwanchiyar'sa yayi a kan katafaren gadon'sa

Abba yaga shiru shiru ba DON ba hiyana sae yace ke diyana tashi kije ki kiramin Safras "da sauri Aryan yace bari na kirasa Abba, batare daya jira amsar Abba ba yayi waje da sauri,"itakuma diyana takoma ta zauna jim kaɗan sai ga Aryan da DON sun shigo a jere tun basu zauna ba Abba yafara tambayar ina hiyana "tatafi ɗakin'su DON yabasa amsa yana ɗaure fuska "da sauri Ammi ta miƙe ta ɗauki plate ta zubawa hiyana abinchi da kanta ta fice daga palon " Abba yayi gyaran murya yafara magana kubani hankalin ku, kai Safras da kae da Aryan da Khalid da Yusuf wan nan ba shawara bane umarnine gobe inasan kuraka  Aisha dasu diyana kauye "a sukwane DON ya ɗago zaiyi magana ganin babu wasa a fuskar Abba ne yasa yayi shiru "nima zanje Abba chewar Aunty farida "aa my daughter bani zaki tambaya ba ae mijinki zaki tam baya," to shike nan Abba zan tambaye'sa
 shiru palon yayi sae karan spoon kawae kakeji "Mikewa DON yayi rae a ɓache ya fita palon"miƙewa Aryan ma yayi yabi bayan sa har yakai bakin kofa sae kuma yajuyo yana kallan diyana ke kikawo min coffee da wuri yana gama faɗin hakan yayi waje da sauri "da ɗai ɗai suka watse kowa yanufi ɓangaren'sa

Da sauri diyana tayi wanka ta shirya chikin wandon jeans blue da yar t-shirt fari, light make up tayi tasa lipsgloss a ɗan jaramin bakin nan nata ga kitso guda biyu a gaban goshi yakai har kan chikinta tasa turaren da Aunty farida ta bata tanufi shoe rack ta ɗauko high heel fari "hiyana na kwanche kan gado tana ta binta ta ido duk a galabaice take, Zahra kuwa tana palo suna hira dasu yaya Khalid da amrat da lamrat," hiyana na tafi diyana tafaɗa tana kokarin fita da sauri "diyana bakisa ɗan kwali bafa chewar hiyana tayi maganar kamar zatayi kuka dan yadda kanta ke sara mata,"aa hiyana kyale ɗan kwalin nan zafi nakeji bata jira amsar hiyana ba tayi waje "a palo tasamu Zahra yaya Khalid yaya Yusuf lamrat da amrat sae hira suƙe " har kasa ta duƙa ta gaida su Yusuf " "khalid yace wow my sister irin wan nan kwalliya haka ina zakije "hannu diyana tasa tarufe fuskar'ta ta mike tana faɗin zanje na kae wa yaya Aryan coffee ne "kallon Yusuf khalid yayi suka haɗa ido suna ɗan murmushi Yusuf yajuyo ya kalleta yace to yi sauri kije kinji sister "bata jira ya karisa maganar ba tayi waje,dan daman yaya Aryan yace tayi sauri takawo mar gashi ta ɓata lokachi wajen wanka da kwalliya "kichin tanufa a gurguje ta haɗa masa coffee ɗin,ta ɗauka tanufi ɓangaren'sa 

Da sallama a bakin ta tashiga palon zaune yake saman sofa yana latsa waya karisa shigowa palon tayi gaban sa tazo da ɗuƙa a nitse tace yaya Aryan ga coffee ɗin,"shiru yayi tamkar baiji me take faɗe ba, yachi gaba da latsa wayar sa shiru shiru almost 10 mnt "a shagwaɓe takuma chewa yaya Aryan pls ka ansa mana wlh nagaji "tam kar bai'san da mutun awajen ba ko motsi bai yi ba wayar sa kawae yake latsawa shiru shiru almost 15 mnt again"a hankali tamiƙe tanufi ɗan karamin table ɗin dake tsakiyar palon ta ajiye coffee ɗin takama hanyar fita daga palon "ke zo nan yayi maganar chikin tsawa wadda yasa sai da ta tsorata "da sauri ta juyo tana kallan sa fuskar nan tasa kamar bai san menen dariya ba ga idon sa sun jaa, wani tsoran sane ya dira mata a rae da,gudu gaske ta juya zatayi waje amma sae dae ta'manta high heel tasa "a zafafe yamiƙe taku ɗaya ya ɗamko gashin kanta ta baya"kware baki tayi zatayi ihu yasa hannu ya rufe mata baƙi,a fusace yake faɗin kimin shiru ko na ɓabballaki a chikin ɗakin nan " shiru tayi tana zare ido"sakin ta yayi yana kallan face nata chikin tsawa "yace me yahaɗaki da wan chan yaro "wani yaro kuma tafaɗa tana zare ido" nikiƙe tambaya wani yaro, dawaye kukayi hira ɗazun a fada "baya baya ta farayi yana binta har suka kure bango "bazaki bani Amsa ba sai na ɓallaki yayi maganar chikin tsawa "muryana na rawa tafara magana,wlh yaya Aryan,ban san shiba shine kawai yazo yace yana so na kuma ni nafaɗa masa ni matar sojane "ido kawai ya zuba mata yana kallan yadda lips nata ke motsi,wani irin sabon yanayi yake ji yana ratsa jini da kowanni jijiya na jikin sa har izuwa zuchiyar sa "yatsa ɗaya ya ɗora a kan lips nata yana faɗin shiiiiiii alamar tayi shiru dan inta chigaba da magana zata iya zautar dashi "ɗago ido tayi tana kallan sa shima ita yake kallo, da kyar ya iya buɗe baki muryan sa har sarke wa yake "wae bana hanaki yin kwalliyar dare ba yayi maganar tare da chire yatsar sa daga kan lips nata "murya na rawa tafara magana kayi, kayi,kayi,hakuri ba.... chikin sauri yasake ɗora yatsan sa a kan lips nata yana girgiza kai  " ido kawai ya zuba mata yana kallon ta a hankali ta ɗago idon ta itama tana kallan sa matso da fuskar sa yayi dab danata har suna iya jiyo nunfashin Juna "zaro ido waje diyana tayi tana..✍️✍️

Sorry masu karatu sai mun haɗu gobe

*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*


*Episode 22*
           



Sosai Aryan ke kallan chikin idon ta, kasa tayi da kai dan bazata iya chigaba da haɗa ido da shi ba, sake matsowa kusa da ita sosai yayi, ya matse ta da jikin,bangon "murya na rawa tace dan Allah yaya Aryan kayi hakuri, maganar da tayin nan yasa yaji tamkar an chan ka masa mashi a zuchiya,da kyar ya iya buɗe baki kamar mai raɗa yake faɗin "wae banace karki sake magana ba, hannu tasa ta toshe bakin ta, a hankali ya haɗe fuskar su waje ɗaya,hanchin su na gogan na juna rutse ido tayi dan baza ta iya  kallan chikin idon saba,calmly yafara magana "daga yau karki sake kwalliya da daddare,kuma idan wani yasake yima ki magana kika amsa shi sai na ɓab'ɓallaki, yau kuma ina ɗan kwalin ki, a tsorache ta buɗe baki har kerma lips nata keyi tana faɗin kayi hakuri...bai bari ta karisa ba da sauri ya ɗora ya'tsansa a saman lips nata, yana girgiza mata kai yana faɗin "ae banche kiyi magana bako, kiyi shiru ki saurare ni, kawai, shiru ya ɗanyi yana kallan yan da lips na ta ke kerma dan tsoro  jiyayi tamkar yayi kissing nata, amma ba zai iya hakan ba itakuwa kara runtse ido tayi dan sai kerma gaba ɗaya jikin ta yake,  almost 10mnt suna saye a haka, da kyar ya iya buɗe baki dan yadda yake ji,  ya chigaba dace wa "me yasa bakya jin magana tane eh? ko dan kinga ina damuwa da kirinƙa sa ɗan kwalin shiyasa kike kin sawa, to shike nan zan fara hukun taki,a kan hakan,yanzu dai zo nan kifara tsallen kwaɗo yana kai karshen maganar a zafafe ya sake ta da sauri ya juya ya koma saman sofa ya zauna sai lumshe ido yake 

ahankali ta duka yafara frog jump tana kewaye palon tana hawaye,tun tana kuka a hankali har tafara da ɗan sauti, yana zaune yana jin ta sai faman runtse ido yake,yana chiza laɓɓan SA, dan har chikin ransa yake jin kukan nata, amma yazama dole yarin ƙa hukun tata, kodan tarin ƙa jin maganar sa,  frog jump take sosai ga high heel a kafarta kamar an hanata chirewa, sai kuka take,kaɗan kaɗan tafara jin chiwon chiki,amma tana tsoran faɗawa faɗa masa, azaba yayi azaba,sae faman nishi take numfashin ta na fita da sauri sauri jinyadda take numfashine yasa Aryan ɗagowa, ya kalle'ta,Subhanallah, da sauri yamiƙe yanufeta yana faɗin lfy kike kuwa sis,bai kai ga karisawa wajen taba yaga ta sulale kasa kamar bata numfashi,da sauri ya karisa wajen ya duka, a ruɗe yasa hannu ya tallabo kanta yana faɗin Ke,ke,lfy kike kuwa,ɗayan hannun'sa yasa,a saitin kofar hanchin ta dan yaji shin tana numfashi, jin bata numfashi alamar ta sume,ne yasa ya miƙe da sauri ya ɗauke'ta chak yaɗora ta  saman sofa, yanufi freij ya ɗauko robar ruwan Faro mai sanyi yadawo ya zauna a gefen ta, buɗe robar ruwan yayi ya tarbo a hannun'sa ya shafa mata a fuska,dogon numfashi taja, a hankali ya furta "ke kina lfy kuwa slowly ta buɗe idon ta a kan face nashi,da sauri ta sake runtse idon tana matsar kwalla, shiru yayi yana kallan'ta wasa wasa tafara juyi tana kara sautin kukan,"ke wae meke damun ki'ne,ya tambaya a ɗan ruɗe dan a'yanayin dayake kallanta kamar period nata ne ke san zuwa chikin kuka take faɗin "chiki yaya Aryan chiki'na wayyo Allah,hiyana ta kizo zan mutu, da sauri yasa hannu ya chire hannu'ta daga rikon datawa chikin nata,ya dora hannun sa awajen,a sukwane kuma yachire hannun nasa dan wani irin shock da yaji, kallan face nata yake dan ya tabbatar da abun dayake zargi shin period ko dai nomal chiwon chikine, ita kuwa sae kuka take, bazai iya jure kukan nata ba, a zafafe ya miƙe ya koma chikin betroom ɗin sa, jim kaɗan sae gashi ya fito riƙe da sirinjin allura,idon ta a lumshe sae kuka take tana juyi a saman sofan, a gefen ta ya zauna ya kama hannun ta a hankali,dan yasan in ta buɗe ido bazata tsaya ya mata allura ba,gashi tana bukatar alluran kodan period ɗin yazo mata da sauki,chikin dabara ya ɗaure hannun nata ya fara ne man jijiya,itakam sae kuka take dan ba tama san yana kusa da ita ba, gyara zaman'sa yayi da kyau, chikin dabara ya tsira mata alluran da sauri ya mata ya zare,sirinjin, a'sukwane ta buɗe ido tana ko'karin ihu,hannu yasa ya rufe bakin nata yana girgiza mata kae,"tashi kije ɗaki ki kwanta yayi maganar yana zame hannun sa daga bakin'ta, chikin dashe war murya take faɗin "yaya Aryan wlh bazan iya tafiya ba,ta karisa maganar tana sakin wani,kuka mara sauti,dafe kae yayi yana faɗin"wae banace kukan nan ya isaba kiyi shiru haka nan,yana gama faɗin hakan yamiƙe,ya ɗauke ta chak ya saɓa'ta a kafaɗar'sa yayi waje da ita,da sauri sauri yake tafi kai tsaye ɓangaren Ammi,yanufa da ita,da sallama ya'shigo palon babu kowa,a hankali yafara takawa izuwa ɗakin su kamar bai san taka kasan, kodaya shiga sae daya sauke wani nauyayyar ajiyar zuchiya,dan ganin su Zahra sunyi barchi, saman sofa ya kwantar da ita, ta buɗe baki zata masa godiya da sauri ya juya ya bar ɗakin,har yana tun tuɓe, chire takalman kafar ta tayi ta kwanta,ta dafe chikin ta ba jimawa barchi yayi awan gaba da ita

Aban garen Aryan yana fita ɓangaren Ammi ɗakin sa ya koma,a gurguje ya shiga, toilet wanka yayi ya shirya chikin kayan barchi,riga zuwa goiwa mai igiya,  gaban rigan a buɗe take faffaɗar kirjin nan nasa awaje rigar fari ne tas,mai laushi sae kamshi yake zubawa fitowa palo yayi ya ɗauki coffee ɗin da diyana ta kawo masa,ya koma betroom,kaɗan yasha saboda coffee ɗin yayi sanyi, ajiyewa yayi kan table ɗin tsakiyar ɗakin,ya haye saman katafaren gadan'sa ba jimawa barchi yayi awon gama dashi 


Washe gari tun asuba su Ammi suka shirya, Ammi Aunty farida hiyana diyana Zahra yusuf Khalid Aryan da kuma DON, lamrat da amrat kuma Anbar su wajen Aunty mardiya "wasu dan ƙara dan karan, motochi masu numfashi guda 5 suka ɗauƙesu zuwa Airport, ajere motochin suka jera har Airport, Ammi da Aunty farida mota ɗaya suka shiga,DON da Aryan motar'su ɗaya,hiyana diyana da kuma Zahra motar ɗaya Khalid da Yusuf ma motar'su ɗaya,ɗayan motan kuma sojoji ne a chiki,diyana sae murna take yau zataga yaya bello da innar yaya bello, Zahra ma sae murna take yau zataje kauye dan inba makaranta ba bata taba zuwa ko inaba,shiyasa ta dage sae tabisu, idan muka koma ɓangaren DON kuwa kamar zai mutu dan bakin chiki sae wani ɓata fuska yake kamar anche masa kwasan kashi zaije,Aryan Khalid Yusuf kam ko ajikin su basu damuba,

"da private jet na yaya Aryan suka tafi,tun jirgin'su bai sauƙa ba motochi 6 daga gidan sarkin yola ke jiran'su a Airport karfe 10 na safe jirgin'su ya sauƙa, basu wani ɓata lokachi chikin jirgin ba suka fito,DON yafara fitowa fiskar nan tamkar wani mayin wachin zaki taku yake irin na jaruman maza,daka kansa kaga wadda akai wa zuwa dole,Aryan na biye dashi a baya,sai Khalid da Yusuf,Aunty farida rike da hannun diyana suma suka sau'ko Ammi na biye dasu Abaya,sai Zahra da hiyana,Shahram da Abdol ne karshen fitowa,kae tsaye wajen motochin suka nufa, da sauri Shahram da Abdol suka fara buɗe musu kofar motochin, Aunty farida da Ammi mota ɗaya suka shiga,DON da Aryan motar su ɗaya, Khalid da Yusuf suma motar su ɗaya,hiyana diyana Zahra matar su suma ɗaya,sai Abdul da Shahram suka shiga ɗayan motar suma,kamar dai yadda sukazo,a jere motochin suka bar Airport ɗin da ma tsakai chin gudu,

 kai tsaye kauyen jambutu suka nufa, wato kauyen su hiyana haka suka rinƙa keta dajin nan har kofar gidan su hiyana sukayi parking,na motochin, da yake yau kasuwar garine, shiru garin yayi ba jama'a duk sun tafi kasuwa,da sauri Shahram da Abdol suka fito daga nasu motar, Shahram yazo ya buɗewa Aryan, Abdol kuma ya buɗewa DON,kafa DON ya zuro waje batare daya fitoba yana zaune chikin motar,yana latsa waya yana wani kwaɓe fuska,  Aryan kuwa,fitowa yayi yana kallan yanayin garin,Ammi da Aunty farida suka fito suka jera zuwa chikin gd "Ammi nikam bari naje dubo yaya bello tukun nan chewar diyana tafaɗi hakan tana murnushi,"bazakije ba wuche ki koma chikin moto Aryan yafaɗi hakan chikin tsawa,"Ammi dake tsaye a dai dai bakin kofar shiga gidan su hiyana, tace "a'a ina ruwan ka da ita, kasan halak chin da bello yamusu ne jeki abun ki diyana muma muna zuwa ai,bari mu gama da nan tukun nan, Tun Ammi bata kae karshen maganar ba diyana ta kwasa Aguje ta tanufi hanyar gidan su yaya bello, kwafa Aryan yayi a zuchiyar sa yana faɗin zamu haɗune, hiyana da Zahra ma fitowa sukayi su kabi bayan su Ammi, "to ni dai tun da Allah ya kawomu kauye yau barinaje naga gari chewar Khalid da sauri  Yusuf yace "a'a jirani muje tare jerawa sukayi tare sukanufi chikin gonaki, wani dogon tsaki DON yaja yana faɗin "ni gaskiya an chucheni wlh da akasani dole nazo garin nan, Aryan dake tsaye kusa dashi bai san sanda dariya ta kub'che masa ba dan yadda DON yayi maganar, wani mugun kallo DON ya watsa masa yana faɗin me kakewa dariya to "kai nakewa dariya mana yanzu dan Allah prince menene laifin garin nan, ae kodan albarkachin a nan aka haifi Ammi ka girmama garin koh, tsaki kawai DON yaja batare daya sake chewa komai ba 

Diyana kuwa da gudu ta faɗa gidan su bello ko sallama babu tun a kofar gida take faɗin "yaya bello ina kake yaya bello ina kake, bello da buba suna zaune a kan tabar ma  a tsakar gida innar bello na girki, inna buba bata nan, hasana matar bello tana Shara,a tsakar gd,  da sauri bello ya miƙe jin muryan diyana,dan kuwa ko mutuwa zaiyi ya dawo bazai manta voice na diyana ba, da gudu diyana ta kariso chikin gida kai tsaye wajen yaya bello tanufa zata rungume'sa kome ta tuna sai kuma taja birki, tana kallan sa shima ita yake kallo chike da farinchi yace "diyana kece?  diyana baki yaki rufuwa sai dariya take tace "yaya bello ina....bata kai karshen maganar ba ta sake wani ihu sakamakon san dar da bubu ya buga mata a goshin'ta, kan kache me jini ya wanke mata fuska ihu take sosai shi kuwa buba kamar mahaukachin ya sake ɗaga sandar ya buga mata a kafa, nan take ta faɗi kasa tana ihu, a zafafe bello ya ɗamki sandar yana kokarin kwache wa buba kuwa yaki saki nan take suka kaure da faɗa, da gudu innar buba tafito daga kichin tana salati, hasana kuwa jefar da tsintsinyar hannun ta tayi tanufi ɗaki da gudu dan tsoro, ganin buba da bello sun kaure da faɗane yasa diyana ta miƙe da kyar, tanufi hanyar fita daga gidan,asukwane buba ya sakarwa bello sandar yabi bayan diyana da gudu yana faɗin yau sai na kashe'ki shegiya, diyana kuwa ganin buba na zuwane yasa ta tattara iya sauran karfin ta ta watsa da gudu tayi waje tana ihu 

Jin ihun diyana yasa Aryan ɗagowa a'sukwane, ganin diyana na gudu ga jikinta duk jini yasa Aryan ya nufe ta da sauri, da gudu su Ammi ma sukayo waje jin ana ihu, 

Diyana na kokarin faɗuwa Aryan ya karisa a zafafe batare da ya damu da jinin dake jikin taba ya rungumeta a kirjin'sa yana faɗin "lfy me yasa me ki eh.. bai kai ga rufe baki ba sai ga buba ya fito da gudu yana faɗin "sai na kashe ki ni zanyi ajalin ki a zuchiye Aryan ya saki diyana tana tangal tangal zata faɗi bai ma luraba  idon sa ya rufe gadan gadan ya nufi buba,da gudu Aunty farida ta kariso wajen ta riƙe diyana dake kokarin faɗuwa,ta rungumeta suka koma chikin gidan su hiyana na,  bello daya biyo bayan buba dan ya dakatar dashi kar ya bugi diyana ganin dasu Ammi tazo yasa ya koma gefe ya harɗe hannu a kirji yana kallonsu, DON kuwa yana zaune ko kallan inda su diyana suke bai yiba bare ma ya tanka sai latsa wayarsa yake, dayaji hayaniyar jama'a na damun sa sai ya ɗauko bluetooth yasa a kunnen sa ya kunna kira'an Al qur'ani mai girma na minshawi ya kure volume ya jingina da kujerar motar ya lunshe ido

Buba ganin Aryan ya tin'karosa gadan gadan ga fiskar nan tasa kamar wani,mayinwachin zaki, a'sukwane buba ya juya zai koma chikin gd, sai dai ina taku biyu Aryan yayi ya dam ki wuyar'sa ta baya ɗagashi sama Aryan yayi, yayi wurgi dashi gefe wani ihun azaba buba ya saki,  gadan gadan Aryan ya nufeshi dam kar wuyar sa yayi ya kai masa wani naushi a fiska nan take wajen ta kunbura, ihu buba yake kamar makoshin sa zata fashe, baji ba gani Aryan ke kai masa bugu ta ko ina, jin yadda buba ke ihu da kyar muryar sa ke fita ne yasa Ammi ta nufesu da sauri dan kar Aryan yayi kisan kai, daga ɗan baya Ammi ta tsaya,a tsorache tace "Aryan ka kyalesa haka ya isa, Aryan bai ma san tana yi ba dan baya ji baya gani bugu kawai yake kai wa buba duk ya fashe masa jiki ga fuskar sa ta kun bura sun tum,

Ammi ta ruɗe sosai dan Aryan baya chikin hayyachin'sa kotayi magana bazai jiba gashi Aunty farida tayi chikin gd da diyana, bare ma tayiwa Aryan magana, da sauri ta juya tanufi wajen DON zaune yake a chikin motar idon sa a lunshe hankalinsa kwanche, dan yada Bluetooth bai ma san meke faruwa ba"kai katashi kaje ka dakatar da Aryan daga bugun ɗan mutane Ammi tafaɗa tana kallo face nash,  shiru DON bai amsa ba kuma bai buɗe ido ba, ganin hakan yasa Ammi tayi tunanin kodai barchi yake, da sauri tasa hannu tana ɗan bubbuga Shi, slowly ya ware green eyes nashi a kan face ɗin Ammi, da sauri ya chire bluetooth dake kunnensa yana faɗin Ammi lfy,  "ina fa lfy ga Aryan chan yana kokarin kisan kai, katashi kaje ka dakatar da shi daga dukan ɗan mutane, ɗaure fuska DON yayi yana faɗin "to ni Ammi ina ruwana basu suka ja ya bugesu ba daman ai mutanen garin nan da dabbobi suke..wani birki ya jaaa da maganar asukwa'ne ya daɗa waro manya manyan green eyes nashi yana kallon Ammi, data ɗaga yatsu biyar zata zabga masa mari sai kuma itama ta dakata tana kallonsa, chikin fushi Ammi tafara magana "to a nan aka haifi uwar idan mutanen garin nan dabbobi'ne to fa kasa har dani ina daga chikin dabbobi nima ko naso ko baka so nan shine tushen ka ta ɓangarena kuma ina alfahari da hakan,idan kaga dama katashi ka dakatar da ɗan uwan ka idan kuma bakaga dama ka barshi yayi kisan kai tana kai karshen maganar ta juya a fusache ta koma chikin gida, 

dafe kai DON yayi yana faɗin "dan Allah Ammi kiyi hakuri na tuba, why  why zan  ɓatawa mahaifiya'ta rai sosai haka, har take kokarin yin abun da bata taba kotan tawaba mari Ammi, kuma ni NO yau gaskiya na kure ta, sosai dole naje na nemi yafiyarta ya karisa maganar yana miƙewa kai tsaye wajen su Aryan yanufa,yana taku irin na jaruman maza,
yana zuwa yasa hannu ya damki damtsen hannun Aryan ya jashi baya, a fusache Aryan yasake nufar buba gadan gadan, rikesa DON yayi yana faɗin "wai wan nan dukan na menene haka ya isa baka ganin ya suma ne  wai ma me ya haɗaku kune, shiru Aryan yayi yakasa magana sai huchi kawai yake ga wani iska mai zafi dayake furzarwa daga bakinsa, hannunsa DON yaja har wajen mota, ɗauko robar ruwa DON yayi a chikin motar ya buɗe bakin robar ya miƙawa Aryan, ansan ruwan Aryan yayi ya kafa robar a bakinsa ya farasha, ganin yakusa shanyewa'ne yasa DON ya ɗauko masa wani yabuɗe yana jiran ya karisa shan'yewa, tas Aryan ya shanye ruwan, yayi jifa da robar, yasa hannu ya anshi wanda DON ke riƙe dashi ya duƙa ya zuba ruwan gaba ɗaya a tsakiyar kansa,shiru yayi Almost 7mnt sai faman  furzar da wani iska mai zafi daga bakin'sa yake, ganin Aryan bai da niyar miƙewa yasa DON kamo hannunsa ya mikar dashi ya zaunar dashi chikin mota yana kallon face nashi "are U okey bro DON ya tambaya yana nazarin face ɗin shi, jinjina masa kai kawai Aryan yayi batare dayayi magana ba "me ya haɗaka da mutanen kauyen nan,har ka masa irin wan nan duka, a zafafe Aryan ya ɗago kamar wadda akawa allura yasake miƙewa yana kokarin nufar buba, da sauri DON yasake kamo hannunsa, yana faɗin "it's ok zo kayi zaman ka ya isa haka kodai so kake ka ɗau doka a hannun kane ya isa pls, da kyar DON ya shawo kan Aryan ya hakura ya kyale buba, shiru sukayi Aryan na zaune chikin mota DON na tsaye a kusa dashi yana kallansa, almost 15mnt san nan Aryan ya ɗago yana faɗin "ina su Ammi, wani dogon numfashi DON yaja tare da sauke ajiyar zuchiya kana yace, thank God daka dawo chikin hayyachin ka, tsaki Aryan yaja kafin yace "ni bansan wulakanchi da che maka akayi bana chikin hayyachi nane pls ka faɗamin ina su Ammi "suna chikin gidan chan mana yayi maganar yana nuna gidansu hiyana da hannu, shiru Aryan yayi kamar mai tunani jingina kansa yayi da jikin kujerar motar ya lumshe ido, zuba mi shi wan nan manya manya green eyes nashi nan DON yayi yana ta kallonsa kamar mai son gano wani abu a tattare dashi.

A ɓangaren buba kuwa, a sume yake ga jiki duk jini, bello ya ɗauke sa Chak ya saɓasa a kafadar'sa yayi chikin gida dashi, saman ta burman dake shinfiɗe a tsakar gidan bello ya kwantar dashi san nan yakira hasana, yace ta kawo masa ruwa, da sauri hasana ta kawo ruwan a kwano bello ya ansa ya ɗiba a hannun'sa ya shafawa buba a fuska, shiru bai farfaɗo ba,  sake ɗibar ruwan bello yayi yasha fa masa nan ma shiru, bai farfaɗo ba zuba masa ruwa mai ɗan yawa bello yayi shiru buba ko motsi baiyi ba, dukar da kai bello yayi sai tin kirjin buba yasa kunnensa dan yaji shin mutuwa yayi ne, tabbas zuchiyar buba na har bawa to amma an zuba ruwa an zuba bai farfaɗo ba, shiru bello yayi yana tunani a wan nan yanayi innar bello tafito daga bayi ta same'su chikin ruɗu da kiɗima  ta nufe'su tana tana faɗin "bello me ka masa badai dukan'sa kayi ba "a'a inna bani na dake sa ba yan uwan'su diyana ne suka masa hukunchi "to yanzu bello ya zamuyi kasan, san dai bala'e mahaifiyarsa yanzu ko zamu tsallake inuwar mu bazata taɓa yarda ba kai ka bugesa ba, shiru bello yayi bai sake chewa komai ba ya zubawa buba ido .

A bangaren su Ammi kuwa zaune suke a tsakar gd diyana na kwanche a kan chinyar Aunty Farida tayi barchin wahala duk da an wanke mata goshin nata jinin bai daina zuba ba, miƙewa hiyana tayi tana faɗin "Aunty Zahra kizo muje ɗakin bappa,"to Zahra tace san nan ta miƙe suka nufi ɗakin bappa, kamar yadda suka bar ɗakin haka yake ba'a taɓa komai ba sai uban kura da datti da ɗakin yayi, nan fa hiyana ta shiga kakkaɓe kurar ta fito ta ɗauki tsintaiya a waje ta koma chikin ɗakin ta hau gyaran ɗakin 

Gyara zama Ammi tayi tana fuskantar Inna tafara Magana "habiba kinsan kafin Ahmadu ya rasu babu Aure a tsakanin ku Koh, to yanzu mu ba wan nan che ta kawo muba, yanzu dai wan nan gida da kike chiki kirike mun barmi'ki, ki chigaba da zaman'ki a chiki da sauri Aunty Farida tace "Ammi ya zakiche kin bata gidan kuma ina che ae ba zai yiwu kiyi kyauta da dukiyan  marayu, batare da izinin suba, murmushi Ammi tayi nasu irin na manya kafin tace "feeda wan nan dukiyar dakike gani bana su hiyana su kaɗai bane har da nawa a chiki nima ina da kaso, dabbobi 60 baban mu ya rasu ya bari ga filaye da gonaki,  ba yadda za'ayi nayi kyau ta da abun da ba na waba Aunty farida zatayi magana hiyana tafito daga ɗakin bappa da gudu tana faɗin Ammi ki..



*💫STAR LADY💫*



*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*


*Episode 23*
           




Da gudu hiyana ta kariso wajen su Ammi tana faɗin "Ammi ki kalla, "manene wan nan kuma hiyana, Aunty farida ta tambaya da mamaki a fuskarta, da sauri Ammi tasa hannu ta ansa wani ɗan karamin tsohon a kwatine irin na ajiye abu mai mahim manchi  "hiyana ina key ɗin a kwatin Ammi ta tambaya tana goge kuran jikin a kwatin, "nima ban gani ba iya wan nan kawai nagani "ok to kutashi muje mu duba key ɗin kuyi sauri dan karmu bata lokachi kunsan yau zamu koma tana kai karshen maganar ta miƙe,tanufi ɗakin bappa  

a hankali Aunty farida ta sauƙe kan diyana daga kan chin yar ta ta kwantar da ita a kan tabar man ta mike itama tabi su Ammi binchike suka shiga yi a ɗakin bappa,su duba nan su duba chan,  sun bin chika ko ina amma basuga key ɗin ba Ammi tace "muje kawai tun da babu key ɗin dan ajiye a kwatin a hannu na dan nasan abu mai mahim man chine Ahmadu yasaka a chikin wannan a kwatin,domin a kwatin asali na baban mu ne abubu masu muhimmanci ake ajiyewa a chiki tana kai karshen maganar tanufi waje, suka bi bayan ta har sum fita hiyana ta dawo da gudu ta ɗauki wata jakar bappa mai ɗan girma jakar chike take da Qur'ani da hadisan, ta karkaɗe kuran dake jikin jakar ta ɗaki tsumma da goge jakar tas san nan ta ɗauka ta nufi wajen, kuɗi Ammi ta ɗauko a jakar ta ta kirga 50k ta mikawa inna, sai washe baki inna take tana hannu ta amsa a zuchiyar ta, tana faɗin kuɗin zuwa wajen malam sun samu Ammi ta dubi Aunty farida tace "feeda ki tashi diyana mutafi Koh kinga rana nayi'fa, kuma mai martaba yace kar muwuche karfe 2  "a'a Ammi dan Allah kar a tasheta kingafa wahalar da yarinyar nan tasha hiyana kije ki kiramin Aryan ko prince ɗayansu yazo ya ɗauke'ta Aunty farida ta karisa maganar tana kallon hiyana, jiki ba kwari hiyana ta juya tanufi wajen a zuchiyarta tana tuno abun da DON yamata jiya, a tsorache ta karisa wajen motar nasu, zaune suke a chiki,sunyi shiru DON na latsa waya, Aryan na jingine da jikin kujerar mota idon sa a lunshe kamar mai barchi, jikinta har kerma yake ta karisa wajen su ta duka har kasa chikin sanyin murya da tsoro tace " yaya prince Aunty farida tace na kira ɗaya daga chikin ku, kamar basuji me tace ba, bawan da ya ɗago barema tasa ran zai mata magana, tsorone yasake kamata tashiga tunani, in tashi in tafine ko dai basu ji bane nasake mai mai tawa, chike da fargaban abun da zai biyo baya ta kuma chewa "yaya prin...bata kai karshen maganar ba Aryan yayi saurin che mata "kije ina zuwa dan yasan in ya bari ta karisa maganar DON zai daka mata tsawa ya firgitata,da sauri ta mike har tana kokarin faɗuwa takoma chikin gida, 

Slowly ya buɗe idonsa tare da ɗagowa daga jingina da yayi da jikin kujerar, a nitse a zuro kafarsa waje kafin yafito daga motan gaba ɗaya, sai daya fito ya juyo ya kalli DON yace "bari naje naji menene yasa Aunty babba ke kiran mu, batare daya jira yaji me DON zai che ba ya nufi chikin gidan, dan yasan DON ba tan kashi zai yiba, da Sallama ya shiga chikin gida daga ɗan baya ya tsaya yana faɗin "Aunty babba lfy kike neman mu, "lfy diyana zaka ɗauka ka kai min ita mota tayi barchine kuma bansan a tashe'ta dan kukan da ta sha yaka mata ta huta "shiru ya ɗanyi yana kallan face ɗin diyana yadda jinin ke zuba kaɗan kaɗan ga wajen ya kunbura sosai, nan take yaji wani ɓachin rai jiyake zuchiyar sa na tafasa sosai tunani yake anya idan nabar wan chan kazamin yaran haka bai chucheta dayawa ba kuwa, "Aryan lfy kuwa Aunty farida ta tambaya tana kallon fiskar'sa  ɗauke kai yayi daga kallon diyana ya dawo da idan sa kan Aunty farida "ba komai Aunty babba ya bata amsa tare da nufar inda diyana ke kwanche hannu yasa a aljihun'sa ya chiro hanky ya duƙa a hankali yafara goge nata jinin, mamakine yakama su Ammi musamman Zahra shiru sukayi suna kallon ikon god, Aunty farida kam sai murmushi take tana adduar Allah yasa Aryan ya kamu da sin diyana dan ita har cikin zuchiyar ta tana kaunar diyana sosai 
ganin diyana na ɗan motsi tana kokarin farkawa yasa Aryan chire hanky ɗin daga kan goshinta,ya zuba mata ido sosai yana kallon ɗan tsagun dake kan gerarta ta raba gerar gida biyu, bakaramin kyau gerar ta masa ba wani dogon numfashi yaja kafin ya miƙe ya tsaɓeta a kafaɗarsa yanufi waje da ita

gaba ɗayansu suka rufa masa baya Ammi tana faɗin "to habiba mun tafi idan da rabo sake haɗu Allah ya haɗa fuskokin mu idan kuma babu to Allah yabamu dachewa tana kai karshen maganar tayi waje, ita dai Inna ko ajikin ta sae murna take tasamu kuɗin zuwa wajen malam 

Chikin mota Aryan ya kai diyana ya kwantar san nan ya dubi Zahra da hiyana dake tsaye a bayan sa yache "ku koma ɗayan motar chan ku barta a nan ita kaɗai tun da barchi take, hannun hiyana Zahra ta kama suka nufi ɗayan motar, shi kuma ya juya ya nufi motar'su yadda ya bar DON haka ya dawo ya same'sa sai latse latsen waya yake, zama yayi a gefen sa ya kwantar da kansa a jikin kujerar motar yana kallon sama slowly ya lumshe manya manyan ash eyes nashi nan 

"Ke zahra'u ina zaku je baga motar ku chan ba Ammi ta tambaya tana kallon su Zahra dake kokarin buɗe motar da yaya Aryan yace su dawo chikin ta tace "yaya Aryan yace mu dawo nan mu kyale diyana a chan tun da barchi take "ok to bari mu shiga gidan su bello, jin an ambachi sunan bello yasa Aryan ɗagowa tare da waro ido asukwa'ne, ɗaure fuska yayi sosai yafara magana "Ammi ki bari dai a kira bello yazo nan ya sameki ban yar da kuje gidan ba, sai lokachin DON ya ɗago green eyes nashi dan jin yadda Aryan yayi magana yasan ranshi a ɓache, zai yi magana sai ya jiyo Ammi na faɗin "aa Aryan ni ina mutunta mutanen garin mu dan na Aure jinin sarauta ba shi'zaisa na wulakanta mutane ba, innar bello ta girmeni sosai ita zanje zanje in gaisar, sai muyi magana da bello san nan ga bappa bello shima zan gai dashi, tana kai karshe maganar ta wuche tanufi gidan su bello da sauri Aunty Farida ta bi bayan'ta, Aryan kuwa kamar zai yi kuka saboda bakin chiki sai huchi yake, 

wani iska mai zafi DON ya furzar daga bakinsa tare da juyo da green eyes nashi yana kallon Aryan calmly ya fara magana "kai me kake wani ɓata rai haka ae kaɗan ma ka gani in dai Ammi che Allah dai ya rufa mana asiri kar tache mu kwana a garin nan, wani dogon tsaki Aryan yaja kafin yace "wlh nima naji gaba ɗaya na tsani garin, da sauri DON ya juyo da kyau  yana kallon Aryan from head to toe wani dogon numfashi taja tare da sauƙe ajiyar zuchiya, yayi shiri kamar mai nazarin wani abu "lfy kake kallona haka Aryan ya tambaya yana kawar da kai gefe "Aryan are U okey kuwa? Wai meyasa tun ɗazun ka keta wani fushi da ɓata rai ne? 
Dawo da kallan sa Aryan yayi kan face ɗin DON ya ɗaure fuska sosai yace "wai ni prince wani irin iskanchin ne wan nan sai ka'rinƙa wani tambaya ta ina lfy ina lfy to am not okey haba dan Allah ni yarone, "yanzu nasake tabbatar wa tabbas akoi abun da ke damun ka daga magana sai fushi sai kache ba lfy ba "tsaki Aryan yaja a kule yace "to sai ka bincike ko wace chuta che ke damu naɗin ai, shiru DON yayi bai sake magana ba kuma bai dai na kallon face ɗin Aryan ba, ganin haka yasa Aryan juro kafarsa waje yana kokarin fata daga motar, da sauri DON ya rikoshi, "where are U going yayi tambayat still dai yana kallon face ɗin sa, wani dogon tsaki ya kuma ja kafin yace "wai dan Allah prince meyasa kakeson takura min ne, me namaka dan Allah ka kyaleni haba, ɗaure fuska sosai DON yayi yafara magana "saboda ina kaunarkar mana Aryan ka nitsu kadawo chikin tunanin'ka kabani hankalin ka bari'ma na maka wasu tambayoyi, kara ɓata fuska Aryan yayi yana kawar da kai gefe  "me ya haɗaka da wan chan mutumin da ka buga har ya suma? Na biyu me ya fusata'ka chikin ɗan  kankanin lokachin,bayan ni nasan baka sauri hawa haka, na uku meke damun ka, yau naga abubuwa dayawa a chikin kwayar idon ka, juyowa Aryan yayi da kyau ya rungumi DON yana faɗin "ban saniba my blood ban saniba wlh nima na rasa meke damuna kwata kwata gaba ɗaya sai in rinƙa ji kamar ba niba,ya karisa maganar chikin rau'nanniyar murya,  hannu DON ya ɗora a saman bayan shi yana ɗan bubbuga shi a'hankali kamar karamin yaro yana  faɗin "it's okay ya isa, nima nasan ba abun da kake ɓoyemin kuma babu wani abun  da zaka iya ɓoyemin, kawai abunne yana bani mamaki gaba ɗaya ka sauya kuma nayi binchike a kan lafiyar ka baka da wata matsala duk wani binchiken daya dache nayi nayi, amma bawani abun dake da munka,  inajin ba daɗi inganka hakan shiya nima abun yake damuna, ya karisa maganar yana raba jikin su, mayar da kai Aryan yayi ya kwantar a jikin kugerar ya lumshe ido yana mai ds numfashi, shiri DON yayi kamar mai tunani.

 

A bangaren su Ammi  da Sallama ita da Aunty farida suka shiga gidan su buba da suri Inna bello taminƙe ta nufosu tana murnushi, "subhanallah Ammi ta furta ganin buba a kwanche ko motsi ba yayi da sauri ta karisa wajen tana faɗin "bello ku kai shi asibiti mana, shiri Inna yaya bello tayi tana mamakin kyawun hali irin na Ammi "zamu kai shi Ammi yanzu nake son tashi inje in kira mai mashin bello yafaɗa yana kokarin tashi "a'a dakata bello magana nakesan yi da kai daman, bayan mun gama maganar sai ka kai shi asibitin "to Ammi chewar bello yayi maganar yana gyara zaman'sa, kujeran katako innar yaya bello ta ɗauko wa Ammi da Aunty farida, ansa sukayi suka zauna suna fuskantar juna, Ammi ta fara magana "bello ka chigaba da kula da dabbobin nan inshaa Allah idan muka gama magana da Mai Martaba zamu wai waye'ka, san nan kabawa habiba shanu uku biyu mata da ɗaya namiji  gonakin bappa kuma duk mun barma ka chigaba da amfani dasu gidan da habiba ke chiki mun bar mata, yanzu sauri muke lokachi ya kure banajin zamu sake zuwa nan kusa amma ko ban zoba duk shawarar da Mai Martaba ya yanke zan aiko ɗan aika,ya sanarma ta kai karshen maganar tana miƙewa, miƙewa Aunty farida ma tayi suka sufi hanyar fita su nawa Inna sallama, har wajen mota yaya bello ya rako su Ammi, 
 kuɗi mai yawa Ammi da Aunty farida suka bashi san nan Ammi tace "ka ɗauki buba ka kai shi asibiti yanzu nan "to kawai yaya bello yace tare da yajuya ya koma chikin gida, Aunty farida ta dubi Ammi tace "muje mana kodai akoi wani abune "a'a ban san meyasa basu tada motocin ba jeki tambayo yan uwan naki, wuchewa Aunty farida tayi tanufi motar su DON,Ammi kuma tashiga motar su ta zauna.  

zaune suke shiru DON na latsa waya Aryan ya jingina kai da jikin kujerar motar ya lumshe ido "Prince mutafi mana kodai akoi abun da kuke jirane Aunty farida ta tambaya tana kallon face ɗin Aryan dake lumshe da ido, slowly ya ware manya manyan ash eyes nashi a kan face ɗin ta, a hankali ya buɗe baki zai yi magana DON yaja dogon tsaki yana faɗin "wayan chan kafar yawon mana muke jira na kirasu sun che suna zuwa, su waye kuma Aunty farida ta tambaya tana taɓe baki "Khalid da Yusuf mana chewar Aryan, DON kuwa kawar da kai gefe yayi bai sake magana ba, murmushi Aunty farida tayi kafin tace "ae da sun jirani munje ganin garin tare, a sukwane DON ya dawo da kallansa kanta, sai murmushi take,  Aryan zai yi Magana sai ga Khalid da Yusuf kariso wajen sai dari suke kamar ba lfy ba, dogon tsaki DON yaja san nan ya rufe kofar motar yawa Shahram umarni akan sutafi juyawa Aunty farida tayi tana kallon su Khalid "lfy Khalid kuke dariya haka, da ido Khalid yamata nuni da DON yasake kwashewa da dariya harara wasa tawa Khalid san nan ta wuche ta mota motan su wuchewa su Khalid ma sukayi nasu motar sai dariya suke,

 a tare motochin suka tashi da gudu gaske saboda sunyi latti Abba yache kar su wuche karfe 2 yanzu kuma Almost  12:30 kai tsaye Airport suka nufa, suna parking, ba tare da ɓata lokachi ba suka fito 
Aunty farida taje ta buɗe motan da diyana ke chiki tasa mu already tatashi daga barchin riko hannun ta tayi tafito da ita daga chikin motar duka nufi jet ɗin, ahankali diyana ke takawa saboda jiri da take gani ga chiwon kai har yanzu jini na zuba kaɗan kaɗan daga goshin ta ga wajen sai daɗa kunbura yake, 

tun da tafito daga mota Aryan ke kallonta jiyake kamar kamar yaje ya ɗagata ya shigar da ita jet ɗin amma ya danne dan karsu che wani abu zuchiyar sa sai tafasa take wani raɗaɗi yake ji haka dai har suka isa wajen  katafaren jet ɗin PRINCE SAFRAS suna shiga  batare da ɓata lokachi'ba Jirgin ya ɗaga zuwa kano

A bangaren Inna kuwa su Ammi na tafiya ta ɗauki nayafin'ta ta fiche daga gidan gidan su bello tashiga da sallama da murnan ta, tana faɗin ina mutanen gidan hasana dake ɗaki tafito ta duka kasa tace "ina wuni Inna ɗaure fuska Inna tayi kafin ta amsa da lfy ina mutanen gidan "sun tafi kai buba wajen malam, dafe kirji Inna tayi tana faɗin "buba kuma me ya sameshi, shiru hasana ta ɗan yi kafin tace "nima ban saniba kawai naga hamma ya shigo ɗauke dashi a kafaɗarsa ya suma, Inna bata tsaya jin karshen maganan hasana ba tayi waje da sauri, tafiya take sauri sauri gudu gudu har takai wajen wani ɗanin bukka mai girman gaske,  ba ko sallama ta faɗa chiki tana faɗin "ina buba'n yake,  wani dattijo dake zaune saman fatan rago wadda a kalla zai kai shekara 70 ya ɗago kananan idon san nan ya ɗubi Inna yace " ga buba nan ya faɗa doguwar suma, dafe kirji Inna tayi ta mai mai ta doguwar suma kuma mun shiga uku kai bello ina innar buba take, Bello dake zaune kusa da buba yace "tana wajen bappa a gona yana kai karshen maganar Inna ta juya tayi waje tsabar sauri har tana kokarin faɗuwa tanufi hanyar wajen malamin su tafiya tani mai nisan gaske 

kamar dai kullum zaune ta samesa a saman dutsen dayake zama kullum, da baya baya ta shiga ta zauna akan jan kyallen da suka saba zama sae washe baki take, wani dariya bokan yayi da sauti mara daɗin ji kafin yace "kin kawo kuɗin koh to ajiye inda kuka saba ajiyewa kishiga masauki ina zuwa, chikin tsorata Inna tace in shaga masauki kuma ba kuɗi kawai kache na kawo ba, chikin tsawa bokan yafara magana "aiki kike san amiki'ne ko dai tambaya zaki tsaya kina min to bari kiji aljanun da zasu miki aiki sun che, aikin nada wahala domin ba karamin abu bane zai warware tsarin jikin yaran nan dan kyakkyawan shiri aka'musu, kuma ita ɗayan babban chikin su ba lallai bane mu iya yimata wani abun saboda tana yawan sallar dare ga karatun Al qur'ani da take,  kullun jikin ta da tsarki tana askar sosai bata zama ba alwala,  kuma babban matsalat ma shine bata neman faɗa bata shiga harkar kowa, kinga idan da tana faɗa da mutane to kota jikin su zamu iya raɓar'ta, Amma bata shiga har kar kowa ba mu isa mu kusan cheta ba, barema har mu iya yimata wani abin amma dai muna nan muna aiki mun samata ido duk lokachin da muka samu dama kamar in tana al'ada kinga bata da sarki, kuma mafi yawanchin lokuta idan mace na al'ada bata damu dayin askar ba basu zama da alwala, to in dai muka samu dama zamuyi aiki a kanta, yanzu dai kitashi kishiga ma sauki ina zuwa yau bani zanyi amfani dake ba duna ne wan da zai miki aikin shine zai yi amfani dake, murya na rawa duk tagama tsorata yanzu da aljani zata kwanta wani gefe na zuchiyar ta yace kai ba dai za'amiki maganin su hiyana ba ai kawai kiyi koma me "amma dai yau bata baya za'ayi bako? da kyar ta iya karisa maganar dan rawar da muryar ta keyi da kaji kasan a tsorache take, chikin tsawa bokan yace "idan baki bukatar aikin ne kitashi ki bani waje ni zaki chewa ba tabaya ba to ai bake zaki zaɓi ta inda duna zai kwanta da ke ba ki tashi ki shiga kuma ki rufe ido domin idan kika haɗa ido da duna mutuwa zakiyi, chike da tsoro da karyewar zuchiya Inna ta miƙe tana tunanin, anya zan iya aikin nan kuwa bazan hakura ba kuwa konchiya da aljani, ɗayan ɓangaren zuchiyar tane yace, a'a me a chiki in dai za amiki maganin su hiyana ai komai ma kiyi, nan take taji karfin guiwa yazo mata ta yaye wani jan labule dake wajen kamar ɗaki a chikin kogon ta shiga wata yar figaggiyar katifa che awajen sai kayan tsafe tsafe , chire mayafin'ta tayi ta haye kan, katimar ta rufe ido kamar yadda bokan ya umar cheta Almost 10mnt tana kwanche haka kafin bokan ya shigo zin dir ba kaya ajikinsa hayewa yayi kanta yafara aiki tun Inna na kuka a hankali har tafara ihu sosai shiko ko ajikinsa sosai ya nemeta ta baya da ta gaba bai kyaleta ba har sai da yaga bata wani motsin kirki tukun nan ya sauka a kanta ya fiche daga wajen, ya barta awajen kwanche bata wani motsin kirki taji wala da kyar take numfashi, komawa yayi wajen aikin sa yana ta murmushi mugunta.

KANO

karfe 4 dai dai jirgin su Ammi ya sauka A Malam Aminu international Airport kano, already gaba ɗaya family gd Abba sunzo tarban su ban da iyayen nasu sai Aunty maryam itama bata zo ba basu ɓata lokachi ba suka fito daga chikin girjin DON sai sauri yake kamar zai tashi sama Aryan na gefen sa a jere suƙe tafiya suka nufi motar da aka tanadar domin su, Khalid da Yusuf dai sai dariya suke kamar sun kulla wani abun rashin gaskiya, Zahra na riƙe da hannun hiyana, Aunty farida na rungume da diyana tana faɗin "sorry my diyana muna zuwa gida yaya Aiman zai duba'ki, diyana dai ko magana ta kasa saboda azabar chiwon kai, sai lunshe blue eyes nata kawai take har suka isa wajen mota, rungume da ita suka shiga motar, Ammi na musu dariya tana faɗin "au to ki zauna da diyana a nan ni bari na koma ɗayar motar, batare da tajira amsar Aunty farida ba ta wuche ta shiga motar kusa da nasu Khalid, 

a tare driver's ɗin su kawa motocin key da matsakaicin gudu suka bar Airport ɗin suna fita suka karawa motochin gudu, gudu suke sosai chikin ƙan kanin lokachi suka iso security suka wangale mugu katafaren gate ɗin, a hankali su ka kutsa motochin chikin gidan, kai tsaye parking space suka nufa, suna kashe motocin DON yafito da sauri bai bi ta kan kowa ba yanufi ɓangaren'sa da sauri Aryan ma ya nufi ɓangaren'sa don bai san kowa ya lura da jinin diyana dake jikin rigar sa dan rigar ma launin ta ba mai haske bane, Khalid da Yusuf kowa yanufi ɗakin sa, Ammi da bataliyar ta suma suka nufi nasu ɓangaren.

 
*DUK ƘARFIN IZZATA*

         👑UK Writers👑

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*
                           


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai





*Episode 24*
          

A gurguje Aryan ya karisa ɓangaren sa, kayan jikinsa yafara ragewa, ya rage da gashi sai shot ya nufi toilet dan yin wanka, after 45mnt yafito ɗaure da towel ya nufi gaban morrow, wayar sa dake saman drawer mirrow ya ɗauka yafara kiran layin Aunty farida, budu ɗaya Aunty farida ta ɗaga tare da faɗin "hello bro, "Aunty babba pls ki turomin yarin yar nan bari na dubata "ok bari na kawota da kai na dan bazata iya tafiya ba tana ganin jiri, batare daya sake magana ba ya katse kira da sauri sauri ya shafa mayu kan sa masu kamshi da tsada feshe jikinsa yayi ta haɗaɗɗiyar parfume nashi mai shegen kamshi da tsada, gyara haɗaɗɗen kuma lallausan bakin gashin kanna nasa yayi, ya ɗaure a bayan ya zuba jelar gashin a bayan wuyar sa sai kelli gashin keyi,  

zubawa mirrow sosai ido yayi yana kallan kansa, shiru yayi kamar mai tunani, jin motsi a pallo ne yasa ya juya da sauri yanufi dressing room nashi dan shiryawa, 

da sallama Aunty farida ta shigo ɗakin rike da hannun diyana sai faman lumshe ido take, ganin ɗakin ba kowa yasa Aunty farida tace  "my diyana jeki zauna a saman sofa ki jirashi kinji, "to kawai diyana tace tanufi sofan da kyar take tafiya saboda sarawan da kan ta ke mata, Aunty farida kuwa juyawa tayi ta fice daga ɗakin, 

Zama diyana tayi ta jingina da jikin sofar ta kwantar da kanta ta lumshe ido kamar mai barchi,  Almost 12mnt tana zaune shiru,har barchi yafara ɗaukar ta, wani fitinannen kamshi ne ya daki hanchin ta wadda yasata sauri waro ido karaf blue eyes nata suka sauka cikin ash eyes nashi, tsaye yake sanye da jallabiya Black colour zuba mata ido yayi sosai yake kallonta, da kyar ta iya buɗe baki tace "ina wuni yaya Aryan, juyawa yayi batare da ya amsa ba yanufi wajen drawer 

A box ya ɗauko ya dawo kusa da ita ya zauna,spirit and cotton ya fitar yafara mata dressing wajen, chikin shagwaɓa da murya kamar na mai kuka tace "yaya Aryan zafi ya'kemin sosai ta karisa maganar tana turo baki, subhanallah wani irin shock yaji saboda yadda tayi maganar, zuba mata ido kawai, yayi ya dakata da aikin da yake har takai karshen maganar, da kyar ya iya sai ta tunanin sa, ya buɗe baki murya kasa kasa kamar mai raɗa "sorry kinji dole zai miki zafi amma zan miki a hankali, 

Sake turo baki tayi tana faɗin "to ni kawai kabari tun da akoi zafi  "kinfi san ki zauna da chiwon ke nan, gyaɗa masa kai tayi alamar eh "bakisan yin kwalliya ke nan, da sauri tace "a'a inasan kwalliya "to in baki tsaya an miki magani ba to fiskan ki zai ɓachi bazaki rinƙa kwalliya ba, chikin marairai chewar murya tace  "to ayya yaya Aryan kamin a hankali kaji wlh akoi zafi, ta karisa maganar kamar zatayi kuka, shiru yayi batare daya sake magana ba ya mai da hannunsa kan goshin'ta ya chigaba da dressing na wajen, 

sai mutsu mutsu diyana keyi taki tsayawa zafi wajen ke mata sosai nan take tafara ruwan hawaye, dafe kansa yayi da hannun sa ɗaya yana faɗin "kinsan ban san kuka ko kiyi shiru ae nakusa gamawa kinji, gyaɗa masa kai kawai tayi amma bata dai na hawaye ba  "wai ba ke che kika che zaki auri soja ba,ya tambaya yana kallan face nata, da sauri ta ɗaga masa kai alamar eh "to ai matan sojojin jarumai ne basa kuka, cikin shesshekar kuka tace "Allah yaya Aryan zafi yake yi mini ne shiyasa amma na daina kukan ta karisa maganar tana goge hawayen ta, girgizar kai kawai yayi ya chigaba da aikin sa sauri sauri yake mata dan karta chigaba da kuka bai san kukan nata ko kaɗan,in tana

Bayan ya kammala ya mai da komai ya rufe Box ɗin ya ajiye a gefe ya miƙe ya koma bakin katafaren gadon sa ya zauna yana kallan ta, sai faman yamutsa fuska take tana turo ɗan bakin. "me ya haɗaki da wanchan wawan mutumin har ya bugeki haka, yayi maganar yana ɗaure fuska , dama kamar jira take tafara bashi lbr tun shigan ta gidan da yadda ya buga mata sandar duk sai data bashi lbr komai, tun da tafara magana ya kafeta da ash eyes nashin nan, ya kasa chire idon sa a kant,  yadda take motsa lips nata nan jiyake kamar yamiƙe yaje yayi kiss na lips ɗin ko zai samu sauƙi abun da yake ji a zuchiyar sa, da sauri ya kori sheɗan ta hanyar furta a'uzubillahi minasshe ɗanir rajin kafin yace "to daman tun asali me tsaka nin ku kuna da dan gantaka da shine, "aa bamu da dan gan taka ɗan yayan Inna che, "what kara waro ash eyes nashi yayi sosai  a kanta, nan take ya ƙara ɗaure fuska rai a ɓache yace "to daman kun taɓa samun matsala da shine a baya da har yake ikirarin zai kashe ki, "eh kullun idan inna ta aike mu ɗiban ruwa sai ya tare mu ya zubar mana da ruwa, nan dai diyana tashiga bashi lbr duk abun da yataɓa haɗa su da buba from A to Z har fyaɗen da yaso yayi mata, 

shiru yayi, nan take fuskar sa ta sauya kamanni idon sa suka sauya su kayi jaaa sosai, lokachi guda, a fusache ya furta "fyaɗe, a tsorace diyana ta gyaɗa masa kai alamar eh  gaban sai faɗuwa yake dan ganin sauyawar yaya Aryan lokachin guda gawani huchi da yake duk jijiyoyin kansa sun tashi sosai, gawani zufa da yake kamar ba A.c a ɗakin jikinsa har wani tsuma yake gaba ɗaya ilahirin jikinsa ɓari yaƙe gashin hannun sa duk sun mimmiƙe,Sai faman chizan red lips nashi yaƙe da karfi kamar zai fasasu, kamar alluran sojan nashi ne ya tashi,  nan take matsanan chin tsoran sa ya dira mata a rai, tunani ta shigayi anya bazan tashi in gudu ba kuwa karya bugeta,

 dafe hannun sofa tayi ɗakyar tamike wai dan ta gudu kar ya bugeta, cikin tsawa ya furta "ina zakije, jikinta sai kerma yake chikin wata iriyar voice kamar zatayi kuka tafara magana "dan Allah yaya Aryan kayi hakuri karka bugeni wlh ni bana san duka kaji ta karisa maganar tare da sakin wani marayan kuka mai ratsa zuchiyar mai sauraro, runtse ido yayi dan har chikin zuchiyar sa yake jin kukan nata, ya dafe kai,dan bai san kukan data keyi ko kaɗan sassauta sexy voice nashi yayi calmly  ya fara magana "nache zan bugeki ne  kimin shiru ki koma ki zauna, "yaya Aryan to kishi nake ji ina san in sha ruwa, Slowly ya waro ash eyes nashi a kan face ɗin ta, sai hawaye take wani na bin wani "ok jiki ɗauko ruwa a freij kizo, to kawai tace san nan tanufi palon tana jan kafa a hankali, ido ya zuba mata yana kallonta sosai har ta fice daga ɗakin, wani nauyayyar ajiyar zuchiya ya sauke, kana yasa hannunsa yana yamutsa gashin kansa, wani iska mai zafi ya furzar daga bakin sa a hankali yafara magana "Aryan wai meke damun kane meyasa na kesan yarinyar nan ta rinƙa kasan chewa kusa dani, yanzu dache ta zauna me zan bata,anya ina lfy kuwa? meyasa nake ɓata rai na dan wani ya taɓa chewa zai mata fyaɗe? Meyasa zan bugi malamin makaranta su dan yache bazai dai na Son taba? why me ruwana da ita, shiru ya ɗanyi kamar mai tunani, 

sai jin voice nata yayi tana faɗin "yaya Aryan in tambaye'ka, ɗago ido yayi yana kallanta dan bai ma san ta dawo ɗakin ba, mamaki ne ya kama shi wai wan nan wace iriyar yarinya che yanzu nan fa take kuka a nan wai daga fitan ta palo ta dawo shike nan takoma fara'ar ta, jin yayi shiru yasa diyana sake chewa "yaya Aryan kasan me nake son tambayar ka bata jira amsar shi ba, ta chigaba da chewa, mata ma suna aikin soja ne?  Tsaki Aryan yaja yana kawar da kansa gefe, dan ya lura in ya biyewa diyana zata chaza masa ƙwaƙwalwa  "ke ban sani ba tashi ma ki tafi ɗaki yayi maganar da ɗan tsawa, miƙewa tayi da kyar ta kama hanyar fita, har ta kai bakin kofa sai kuma ta juyo karaf suka haɗa ido dan kuwa ita yake kallo, a shagwaɓe tace "yaya Aryan to pls ka faɗa min mana idan mata na aikin soja nima zan shiga ne dan Allah ina san riƙe bin diga kuma kayan sojoji na burgeni,  ido kawai ya zuba mata ba tare daya bata amsa ba, ganin bai da niyar magana yasa ta fara bubbuga kafa ta turo baki tana yarfe hannu tafara magana "dan Allah yaya Aryan ka faɗa min kaji kodai zaka bani naka kayan sojojin da bindigar kane nasa nima, kallan ta kawai yake dan ya kasa magana tunani yake wai anya wan nan mutunche yarinya bata da tsoro ko kaɗan jiba yadda take min magana, "yaya Aryan na tafi tun,da bazaka faɗa min ba bari naje na tambayi wan chan mai kama da hiyana, yama sunan shi wan nan da baya dariyan nan, tayi maganar tana ɗaga kai sama kamar mai tunani, jin ta ambachi zataje ta tambayi DON ne yasa Aryan saurin chewa "mata basa aikin soja sai dai susa uniform ɗin mazajen su, wai bakin che kema soja zaki Aura ba, da sauri ta gyraɗa masa kai alamar eh "to kibari idan kin Auri sojan sai ki rinƙa saka uniform nashi, "to shike nan natafi ta karisa maganar tana ficewa daga ɗakin, girgiza kai Aryan yayi yana faɗin "da kinje kin tambayi DON kuwa da baki sake yiwa kowa magana a gidan nan ba, dan ina da tabbachi hakoran ki ko ɗaya ba zai rage a wan nan ɗan bakin surutun ba, wai yarinya'ne ba zaka ga baki ba sai magana, yayi maganar yana karisa hayewa saman gadon sa, ya kwanta tare da lunshe ido yana sauke ajiyar zuchiya.

YOLA

almost 30mnt inna na kwanche takasa miƙewa sai nishi take da kyar da kyar, a wan nan yanayin bokan nata ya shigo ya same ta hannunsa riƙe da wata bakar kwarya mai ɗauke da wani jan ruwa a chiki, kanta ya ɗago ya kafa mata kwaryan a baki yafara ɗura mata maganin, bashi tafara ha'ɗiyewa sai da ta shanye tas san nan yasaki kanta, ya miƙe ya fita ya koma wajen tsafe tsafen sa ya zauna jim kaɗan, sai ga Inna tafito da kwarin ta, tazo gaban sa ta zauna tana faɗin "zan iya tafiya, wani mahaukachin dariya yayi ha,ha,ha, kafin yace "eh ammafa gidawo bayan sati ɗaya dan kiji saka makon aikin ki  "to tache tare da miƙewa tanufi hanyar fita har ta kai bakin kogon zata fita sai kuma dai ta juyo tace "zan iya zuwa anjima musake yin abun da mukayi ɗazun, wani dariyar mugun ta yayi a zuchiyar sa yana faɗin aiki ya fara kamaki ke nan abu yayi kyau kinshigo hannu, a fili kuwa che'mata yayi "eh idan kina soma yanzu ma ai sai muchi gaba, da sauri ta juyo ta nufoshi tana faɗin "eh ina so, sake kwashewa yayi da dariyar mugun ta kafin yace "to shiga chiki ina zuwa, tun bai karisa maganar ba ta shige chikin ɗan kewayayyen wajen nashi, ta chire mayafinta ta haye kan yar figaggi yar katifar nashi, 

ba jimawa shima ya shigo zindir babu kaya ajikin sa hayewa kanta yayi sai wani faman murmushi take, shima murmushi yake sai dai shi na mugunta yake, chire mata kaya yayi yafara aiki, awan nan karon ma sosai ya nemeta gaba da baya sai dai bata ji zafi kamar na ɗazun ba hakan kuma ya samo asali ne, saboda maganin daya bata, awan nan karon tare suka murji juna sai wani nishi suke dukkan su biyu, 

Bayan sun gama shike ayan sune ya kwanta a gefenta yana mai da numfashi, itama sai wani mai da numfashi take, sai misalin karfe 7 na dare Inna ta koma gida sai farinchiki  da murna take tana faɗin "gobema komawa zanyi wlh irin wan nan abu haka, ko sallar mangariba babu bare issha batare da tayi wanka ba ta haye yar katifar chiyawar'ta ba jimawa barchi ya ɗauke ta ko abinchi bata nema ba.

KANO

Misalin karfe 8 na dare gaba ɗaya family Abba sun haɗu a palo ban da DON shi bai fito ba, gyaran murya Abba yayi, yana kallon diyana dake zaune kusa da Aunty farida tana chin ayaba, yafara Magana "naji duk abun daya faru zuwan ku Yola, sorry my daughter kinji ba zaku sake zuwa garin ba inshaa Allah. Shiru ya ɗanyi kafin ya dawo da kallan sa Abba yayi kan Ahmad dake zaune kusa da Aiman, ya chigaba da Magana, "kai Ahmad kashirya daga gobe zaka fara hawa kujerer mulki gobe misalin karfe 9 zaka fita fada,waro ido waje Ahmad yayi yana san magana, amma ba hali dan idan Abba yana magana ba wan da ya isa ya tanka har sai ya gama,

 ɗaure fuska Abba yayi ganin yadda Ahmad ya zaro ido, dawo da kallansa kan Khalid yayi ya chigaba da magana, "kai kuma baba jibi Monday su Zahra zasu koma school kaje kamusu abun daya dace, 

Shiru Abba ya ɗanyi yana mai da numfashi san nan ya ɗora dachewa sai magana ta gaba kuma,  ke hiyana tashi kije ki kiramin Safras, ya karisa maganar yana kallan hiyana,  mikewa hiyana tayi kamar zatayi kuka jikinta har ɓari yaƙe saboda tsoron DON, shi kanshi Abba ya lura da yanayin data shiga, amma dole ne taje ta kira masa DON dan haka sai ya shareta, tafiya take kamar wadda kyau ya fashiwa a ciki ta fito daga palon

Part na DON ta nufa tun a bakin kofar palon kasa take sallama, amma shiru babu wadda ya amsa chikin palon ta shiga babu kowa, a'hakali kamar bata son taka kasa tanufi stair ɗin, ta haura a bakin kofar palon daman ta tsaya tasake, doka sallama, nan ma shiru, hannu tasa a hankali ta tura kofar palon, ta shiga shiru shima babu kowa, kofar betroom ɗinsa ta nufa a bakin kofar ta tsaya da murya kamar mai shirin fashewa da kuka tayi sallama shiru bai amsa ba, sake sallama tayi nan ma shiru bai amsa ba, shiru tayi tana tunanin, yanzu ya zanyi, in koma palo ne to idan ma na koma palo in che me, ban isa in che baya nan ba tun da sun san yana gida, to idan kuma na koma na chewa Abba na faɗa masa, kuma bayan ban faɗaba zasuji shiru bai zoba kar Abba ya masa faɗa shikuma ya hukun tani, idan kuma nashiga nan ma zai iya hukun tani, Almost 30 hiyana na tsaye tana tunanin mafita data ga dai tsayuwar ba abun da zai tsinana mata sai tayi shahada ta tura kofar betroom ɗin a hankali ta shiga da sallama.

subhanallah kara waro blue eyes nata tayi sosai a kansa, kwanche yake saman katafaren gadon sa idon sa a lunshe kamar barchi yake, daga shi sai short a jikin sa faffaɗar kirjin nan nasa awaje,ga wani bakin gashi mai kyan gaske kwanche a kan kirjin, lallausan bakin gashin kan nan nasa kuwa duk ya bar bazu a kan face ɗin sa ya rufe masa ido, zubawa ɗamtsen hannun sa ido hiyana tayi tana kallo kara waro blue eyes nata tayi da kyau a chikin zuchiyar ta yana faɗin "kai ai wan iri hannun na sa ai ya kusa chin yata, tab idan ya bugeka da hannun nan sai ka mutu, dawo da kallonta tayi kan faffaɗar kirjin sa, gashin dake kwanche a wajen kawai take kallo tana faɗin, wow a chikin zuchiyarta, Allah ka bani miji mai kashi a kirji nima yana min kyau, sauko da blue eyes nata tayi izuwa kan chin yoyin'sa, wani bakin gashi ne mai kyau da sheki  kwanche a kan chinyar nasa, sosai ta zuba masa ido tana kare masa kallo from head to toe, tana yaba irin kyansa da kyan jikin sa, tayi nisa chikin tunani sai taga alamar ya  ɗan motsa hannun sa, a ruɗe ta ja da baya ta koma jikin kofa, a tsorache tace "yaya Prince Abba na kiran ka, shiru bai amsa ba cikin tsoro ta sake mai mai ta maganar, batare daya buɗe ido ba ya furta "get out chikin tsawa, ai tun bai gama faɗeba tayi waje daman ita burinta kawai yaji sakon Abba, tun da yaji shike nan 

da gudu tabar ɓan garen nasa ta koma falon Abba, sai numfashi sama sama take, gaba ɗaya idon mutanen falon ya dawo kanta ban da Aryan da Fahad abin chin su kawai suke chi "sister lfy kike numfashi kamar wadda tayi gudu chewar Yusuf ya yayi maganar yana kallon face nata, ita kam Zahra ko ajikin ta dan tasan dalili, Abba ma yasan hakan zata iya faruwa yasan sai DON ya kore'ta, da gangan yake aika ta daman dan yasan duka dai DON bazan duketa ba tun da yamasa gargaɗi a kan haka, dawo da kallansa Abba yayi kan su Yusuf yayi yace "kai ina ruwan ku da ita zoki zauna ki chigaba da chin abinchi ki kinji my daughter, ɗaure fuska Aunty Amarya tayi dan taso jin me DON yawa hiyana take numfashi haka ko marin'ta yayi, 

Zama hiyana tazo tayi awajen da ta tashi ta ɗauki spoon a hankali tafara chin abinchin ta, shiru shiru DON  bai zoba da har suka gama chin abinchin, Abba ya dubi Khalid rai a ɗan bace yace  "kai baba tashi kaje ka chewa Safras nifa na haife shi ba shi ya haifeni ba da zai ajiye'ni ina jiran sa, Khalid na kokarin mikewa, sai ga DON ya shi go sanye chikin jallabiya fari, yana taku irin na jaruman maza, fuskar san nan kamar bai san menen dariya ba sai wani kakkau da kai yake, gaba ɗaya su Aunty Maryam kowa ya shiga taitayin sa, har da Aunty amaryan,  kujerar dake fuskantar Abba yaje ya zauna da sauri kannen nasu suka fara ɗaga masa gaisuwa, bai ko kalli inda suke ba bare ya amsa musu gaisuwar sai ma kara ɗaure fuska da yayi, sai da suka gama gai suwar nasu sukayi shiru kowa ya nitsu suna sauraren suji abun da Abba zai che.

A hankali DON ya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi kamar bai san motsa lallausan lips nashi,  ya fara gaishe da iyayen nasu, fiska ba yabo ba fallasa Abba ya amsa haka Aunty amarya da Ummi, Ammi kuwa ɗaure fuska tayi sosai kafin ta amsa masa,Shiru yayi san nan ya sun kuyar da kai, shiru palon yayi gaba ɗaya Abban ne ya katse musu shirun da chewa "Zahra kutashi kuba mu waje, tun bai kai karshen maganar ba Zahra hiyana diyana lamrat amrat suka miƙe suka bar palon,

 dawo da kallansa kan su DON Abba yayi yafara Magana "abun da yasa na taraku a nan shine, duk kanku lokachi yayi da zakuyi Aure, a sukwane DON Aryan Fahad haidar Aiman da kuma Ahmad suka ɗago kai a tare suna kallon Abba kamar zasuyi ihu musam man DON Aryan Fahad Aiman,su nasu ɓachin ran na da ban ne kamar wayan da aka chewa uban su ya mutu, Khalid Yusuf Umar kam ko ajikinsu, Aunty farida ma ɓata rai tayi sosai dan tasan wan nan maganar da Abba yayi ba karamin ɗagawa su DON hankali zai yiba, dan babu hakan a tsarin su, tafiso a barsu sunemi mata chikin nitsuwa, dan idan akache za'a tilasta musu wlh duk wadda aka aura musu tashiga uku, 

"No Abba No gaskiya kabar wan nan maganar ni babu mace a tsarin rayuwa kamin wani hukunchin dai amma banda batun mace pls Abba, chewar DON, ya karisa maganar chikin wata iriyar voice wadda da kajita kasan tsantsar kiyayyar macece a ranshi,ga fiskar nan kamar an aiko masa da sakon mutuwa, shiru Abba yayi ya zubawa DON ido har yakai karshen maganar tashi, shi kanshi Abba yasan chewa mawuya chin abune DON Aryan su  yarda da batun Aure, domin babu hakan a tsarin da sukayi wa rayuwar su,shiyasa ma bai takura musu ba tsawon lokachi ya bar su, to amma yanzu yazama dole suyi Aure dan chika sunnan ma aiki, kuma yafi son su kawo matan da zasu Aura da kansu dan idan yace zai Aura musu zaɓin sane, yasan matan sun shiga uku

sosai Abba yashiga tunani, gaskiya bai kamata nayiwa DON dole ba idan yayi haka tofa akoi babban matsala tsabar tsanar mace dayayi ne jiba agaban kannen sa yau ya buɗe murya haka yana magana har da chewa sorry mutumin da magana wahala yi take masa, lallai bai kamata na takura masa ba idan kuwa nayi haka zanyi dana sani mai girma, addu'a kawai ya kamata na masa. 

Ganin Abba yayi shirune yasa Aryan chewa "Abba pls kabar maganar auren nan wlh ba muso babu mace a tsarin rayuwar mu pls my Abba kaji ya karisa maganar yana ɗan dafa hannun Abba, chikin fushi Ammi tace "babu mace a tsarin rayuwar ku ko, to ku chiremu muma a tsarin rayuwar ku tunda muma matane tana kaiwa nan ta miƙe ta fiche daga palon chikin fushi da ɓachin rai, dafe kai DON yayi a zuchiyar'sa yana faɗin jiya nayi ɗaya yau kuma na biyu am so so sorry Ammi ammafa aure kam ba zan yi ba gaskiya sai dai duk abun da zai faru ya faru, miƙewa Ummi tayi itama tana faɗin "ranka ya daɗe idan kun gama zaman ka kira malam mai rukiyya yazo ya musu dan ga dukkan alamu aljana che ta auri ƴa'ƴan nan, a sukwane suka juyo gaba ɗayan su suna kallon Ummi, ɗaure fuska tayi kafin ta juya ta fice daga palon, kallan Aunty amarya Abba yayi tun bai yi magana ba ta miƙe ta fita tana ɓata rai dan taso jin me Abba zai che musu wani amsa zai basu, "Maryam salma mardiya kutashi ku bamu waje,chewar Abba yayi maganar yana kallon su, jiki ba kwari suka miƙe suka fita. 

Palon ya rage daga Aunty farida, DON Khalid Yusuf Aryan Aiman Ahmad Umar haihar da kuma Fahad 

Dawo da kallansa Abba yayi kansu DON ko'wannen su sai faman ɗaure fuska yake sai wani chi chijewa suke, ɗan gyaran murya Abba yayi kafin yafara Magana "ke farida na barki ne saboda bakin ku ɗaya dasu ke che sirrin su basu taɓayin wani abu batare da kin sani ba dan haka ku saurareni, "ni bazan tilas ta muku kuyi Aure ba, wani dauyayyar ajiya zuchiya DON Aryan Fahad, suka sauke a tare, har da ɗan sakin fuska, ganin hakan yasa Abba murmushi yachi gaba da chewa "bazan takura muku kuyi abun da baku so ba, saboda farin cikin ku nake bukata, amma dai burina shine naga kunyi aure kun haifamin jikoki shine babba burina a duniya kuma farinchiki na, ni ina san farin chikin ku ban sani ba ko kuma kunason nawa, ban sani ba ko zaku iya chika min burina tun ina raye, ɗan dakatawa Abba yayi yana satar kallon fuskokin su,a ransa yana faɗin nina haifeku ai baku kuka haifeni ba a chikin ruwan sanyi zanyi maganin ku,  nan take fuskar DON da Aryan ya sauya sosai dan sun gano tarko Abba ke neman yima'su da kalaman sa, Fahad kuwa sai murna yake Abba bazai yimasu dole suyi aure ba, shiru Aiman yayi ya ɗora hannu a gemun sa yana kallon kasa yana nazarin magan ganun Abba, Khalid da Yusuf kuwa ɓata rai sukayi sosai dan su gaskiya Aure suke so kuma suna da matan da zasu aura, amma DON da Aryan suna neman watsa musu farin chiki, Aunty farida kuwa jikinta ne yayi sanyi sosai jin kalaman Abba, tabbas Abba na da gaskiya yakama suyi aure amma banso Abba yabi musu ta wan nan sigar ba da an bi a hankali an bisu da addu'a inshaa Allah komai zai tafi dai dai

Ganin sunyi shiru kowan nan su yatafi tunani yasa Abba chewa, "nifa ban takura'wa kowa daga chikin kuba, burina da kuma farinchiki na kawai na faɗa muku, kuma ban che dole sai kun chika min burina ba koma me ni zan zama mai chika muku burin,kuma mai saku farin chiki a ko da yaushe, kuje ku zauna kunitsu kuyi tunani yana kai karshen maganar yamike ya shige betroom ɗin sa, 

chikin fushi da ɓachin rai DON ya furta "never Abba aure fa, wlh I cannot do it I cannot do it gaskiya bazan iya chika maka wan nan burin nakaba, a fusache ya miƙe ya bar palon, da sauri Aryan ya miƙe zai bi bayan sa "ina zakaje Aryan Aunty farida ta tambaya, "Aunty farida baki ganin ɗan uwana yana chikin ɓachin rai ne ai bazan iya zama ba, yana kai karshen maganar batare daya jira amsar taba ya fiche da sauri, a fusache Aiman ma ya mike yaja tsaki yana faɗin "nima dai ba zan iya chika'wa Abba wan nan burin na shi ba sai dai in ku zaku iya bani da lokachin mace yanzu, yana kai karshen maganar ya juya da, sauri ya nufi hanyar fita dan bai dan Aunty farida ta.  dakatar da shi

Girgiza kai Khalid yayi kafin yache  "gaskiya a wan nan gaɓar ya kamata mu chika wa Abba burinsa, domin duk wani abun da mukeso yana mana yanzu ki duba Aunty babba saboda bama son mulkin nan, Abba ya hakura da bamu mulkin duk dan muyi farin chiki, tun muna yara har muka girma har izuwa yanzu bamu taɓa chewa Abba muna bukatar abu kuma yaki yi mana ba, to meyasa mu kuma zamu rinƙa kin abun da yake so, yache zai bamu mulki munki ya hakura yanzu kuma kin fa ji auren mu shine kaɗai burin daya rage masa a duniya da yake san mu chika masa,to why bazamu chika masa burin sa ba.  ɗan daka tawa Khalid yayi da magana yana mai da numfashi "Kana da gaskiya Khalid amma a hankali Ya kamata abi abun tun da kaga dukkan ku ba soyayya kuka taɓayiba babu wata alaka da ta taɓa haɗaku da wata mace idan ba mu yan uwan ku na gida ba, SO kaga abune mawuyache lokachi ɗaya a che zaayi muku maganar aure garama kai dasu Yusuf da sauki, amma kafini sanin halin DON da Aryan, basu san wani abu wai shi soyayya ba, bai da che amusu zuwa ɗaya haka ba a hankali za'a shawo kansu, yanzu dai zanje in same'su dan musan abunyi tana kai karshen maganar ta miƙe tanufi hanyar fita, shiru Khalid yayi yana tunani, miƙewa Fahad ma yayi yabi bayan Aunty farida, haidar da umar ma suƙa miƙe suka fita suka nufi ɓan garensu palon ya rage Khalid Ahmad Yusuf.

*💫STAR LADY💫*


          👑UK Writers👑


*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*



Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣5️⃣*


........Ɗago ido Khalid yayi yana kallon su Ahmad san nan yafara Magana "yanzu menen mafita, Khalid bai gama rufe baki ba, Ahmad ma yamiƙe yabi bayan su Aiman, dawo da kallan sa kan yusuf dake zaune Khalid yayi san nan yace "Yusuf mene mafita ni fa gaskiya ina son Zahra sosai wlh ina san muyi Aure kuma gaskiya time yayi daya kamata a che munyi auren idan fa muka biyewa su DON baza mu taɓa yin aure ba awan nan rayuwar, dan su babu Aure a tunanin su kwata kwata, 
dogon numfashi Yusuf yaja kafin ya fara Magana "yaya Khalid ni kai na ina matikar son my baby wlh, duk da yarin yache sosai amma ina san muyi aure taje ta karisa girma a gidana amma bansa ya abun zai kasan cheba kanafa jin abun da yaya prince ke faɗe, wai har abada shida Aure kuma ni nasan mawuya chin abune a shawo kan sa ya yarda yayi Aure, "dole fa Yusuf musan abunyi Khalid ya faɗa yana kokarin miƙewa "jirani muje mana chewar Yusuf ya karisa maganar tare da miƙewa shiam, suka jera atare suka fice daga palon kowa yayi ɓangaren sa 

Abangaren DON kuwa yana fita palon Abba ɓangaren sa yanufa chikin sauri, yana shiga ɗaki ya zauna a bakin katafaren gado sa, ya dafe kai dan ji yake kansa na sara masa,kamar zai faɗi kasa, tunani ya shigayi, ni gaskiya Abba bai min adalchi ba tayaya zai wani haɗani dawani abu wai shi Aure, dole ma nazo nabar kasar nan, tun kafin Abba ya sake kawo wata maganar. 

Awan nan yanayi Aryan ya shigo ya same'sa, gefen sa ya zauna saman gadon yasa hannu ya dafa kafaɗarsa cikin cool voice yafara Magana "calm down my blood kafasan idan ka shiga damuwa nima dole nashiga damuwa, kuma ni nasan ba kasan ka ganni chikin damuwa ko, ɗago green eyes nashi yayi yana sauke su kan face ɗin Aryan,  har sai da Aryan ya tsorata ganin yadda idon nashi suka sauya sunyi jaaa sosai ga jijiyoyin kan nan nashi duk sun tashi duk da sanyi A.c dake ɗakin hakan bai hana DON zufa ba, chikin wata iriyar voice mai sauti yace "why, why Aryan why Abba zai nemi ya chazamin kai why yake neman kassarani, "calm down my blood ya isa haka kayi shiru pls Aryan ya faɗa tare da dora hannun sa saman ɗan karamin bakin DON ya rufe masa, yana kokarin sake magana Aunty farida tashigo da sallama, zame hannunsa Aryan yayi daga kan dan bakin DON yana kallonta

Karisowa chikin ɗakin tayi ta zauna a bakin gadon ta ɗayan gefen su kasa DON a tsakiya ita da Aryan a nitse tafara magana "nasan abun da Abba ya faɗa bazai muku daɗi ba amma hakan kar ya dame ku kuyi hakuri, ni nasan Abba ba zai so ya ɓata muku rai ba koma me zanyi magana dashi idan ya huche, yanzu dai banaso wani abu ya dame ku dan kunsan idan kuka shiga damuwa dole nima hankali na ya tashi kuma zan shiga damuwa, ɗan dakata wa tayi da magana tana mai da numfashi, buɗe ɗan karamin bakin'sa Aryan yayi zai yi magana kenan sukaji sallamar Abba, da mamaki suke bin kofar ɗakin da kallon, 

ƙarisowa chikin ɗakin Abba yayi, mikewa sukayi gaba ɗayan su, suna kallon Abba kai tsaye DON ya nufa yaje ya rungume sa, shiru Aryan da Aunty farida sukayi suna bin Abba da DON da kallo, tunani  Aunty farida ta shiga yi  anya bawani abun Abba ya shirya musu ba, bata gama tunanin nata ba taji Abba yana faɗin "bana son ɓachin ran ku ƴa'ƴana kune farin chiki na, yanzu dai ke farida jeki haɗa masa complex ki kawo mana muna sha muna hira 

......ita dai Aunty farida gaskiya bata yar da da neman sulhun da Abba yazo yi ba, dan tafi kowa sanin halinsa yanzu wata kila wani idea ne tazo masa shiyasa zai musu wayo ta haka, jiki ba kwari tana ta tunani har ta fiche daga ɗakin, 

Sakin DON Abba yayi ya haye kan katafaren gadon DON ya zauna yana ta murmushi, haye gadon Aryan da DON ma su kayi suka saka Abba a tsakiya, "Abba ya kamata mu koma bakin aikin mufa Aryan ya faɗa yana kallan Abba, murmushi Abba yayi kafin yache "ku rubuta musu later akan za kuyi wani aiki a nan na tsawon wata uku dan gaskiya ina san kasan chewa da ku a'wayan nan watannin, 

.....DON yace  "Abba a matsayi na BGS (Brigadier General Safras) ba sai na rubuta wani later ba, Aryan da Yusuf kuma dama a'wajena zasu tambayi permission na hutun, tun da kana bukatar mu kasan che da kai na wata uku su rubuto min later zan sa musu hannu, murmushi Abba yayi sosai kafin ya rungumi DON yana faɗin ilove U my Son, "ilove too my love my pleasure my only Boss, farinchiki kamar Aryan ya nitse kasa dan daɗi, ganin yadda Abba da DON suke zuba wa juna kalan kauna, "eyeee lallai Abba wato haka abun yake ko? chewar Aunty farida dake tsaye a bakin kofar shigowa ɗakin tana ta murnushi hannunta ɗauke da babban trey mai ɗauke da cup 4 na complex, sakin Abba DON yayi ya juyo yana faɗin "Aunty babba kin fa iya sa ido, kariso tayi chikin ɗakin ta ajiye trey ɗin saman table ɗin tsakiyar ɗakin ta zauna saman sofa tana murnushi

A tare suka sauko daga gadon suka nufo ta, kowa ya zauna a saman nashi sofan suna fiskantar juna, Aunty farida zata mike ta ɗauko musu complex ɗin Aryan ya rigata yana faɗin "bari na hutar dake Aunty babba, ɗaukan trey ɗin yayi ya fara miƙawa Abba, ya ɗauki cup ɗaya san nan ya miƙawa Aunty farida itama ta ɗauka, ko da yazo mikawa BGS wani harara BGS ya wurga masa kafin yace "au nine karshe ko "hannu ɗaya Aryan yasa yaja dogon hanchin BGS har sai da yace wash mugu kawai, dariya Abba yayi yana faɗin "daman Aryan kai kake jan hanchin BGS koh shiyasa naga hanchin nashi kullun tana ƙara tsawo Sosai, taɓe baki Aunty farida tayi tana kallon Abba, da mamaki wato ma idan ana jan hanchi kara tsawo yake koh? Tab ai da  kuwa hakane lilin baba shine mutun na farko da zai fara bawa ummi rahab tana ja masa dan hanchin nasa yayi tsawo 

.....Wani naushi BGS ya kai wa Aryan a kumatu sai dai ina kauchewa Aryan yayi yana ɗan murnushi, bai bari hannun BGS ya sauƙa a jikin sa ba, "wai zaka ɗauki complex ɗin nan ne ko kuma na ajiye, ɗaure fuska BGS yayi kafin yace "bazan sha ba, "oh my lovely bro pls ka sha idan baka sha ba nima bazan sha ba kuma wlh inasan sha amma dole zan haku in dai baka sha ba, ɗan sake fuska kaɗan BGS yayi kafin yasa hannu ya ɗauko cup ɗin yana faɗin "zan sha ne kawai saboda kana son sha kuma bani da wani burin daya wuche inga kasamu abun da kake so, matsowa Aryan yayi ya man nawa BGS kiss, a goshi kafin yace "ina kaunar ka kamar raina my blood, "Hmmmm faɗa ɓatawa my bro ai kaunar da nake maka ba zai faɗu ba

... Abba dai ido kawai ya zuba musu a chikin zuchiyar shi yana gode wa Allah da ya haɗa masa kan ƴa'ƴansa suke matukar kaunar ju nan su haka,

 "Abba na, gobe idan Allah ya kaimu in mun gama raka Ahmad fada, zan bi jirgin yamma na koma, chewar Aunty farida "Allah ya kaimu bai lovely daughter, shiru su kayi suna shan complex nasu chikin ni shaɗi , 

zubur Aryan ya mike kamar wadda akawa allura yana faɗin "Abba sai da safe da mamaki BGS da Aunty farida ke kallansa, Abba kuwa sai murnushi yake chikin ransa yana faɗin, Allah kasa na chinma abun da nake hari afili kuwa sai yace  "to my Son yaka mata daman ka ajiye complex nan haka kaje kasha coffee mai zafi, a'sukwane Aryan ya dawo da kallansa kan Abba yana mamakin ya akayi Abba yasan abun da zaije yayi, kashe masa ido ɗaya Abba yayi yana murmushi yace  "to ka tafi mana me kuma ka tsaya kana kallan mu, jiki ba kwari Aryan ya juya ya ajiye cup ɗin complex ɗin dake hannunsa a saman table yanufi hanyar fita, yana jiyo muryan Aunty farida na faɗin "wai meke damun Aryan ne muna zaune muna hira kawai kache sai da safe, bayan ga wayan nan manya manyan idon nan naka ba alamar barchi a chikin su, fichewa yayi da sauri dan karma Aunty farida  ta jefo masa wani tambayar, 

a hankali BGS ya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi ya furta "kila ya gaji da hiran ne, da sauri Abba ya chan za musu topic ɗin hirar dan karsu tsawai'ta magana a kan Aryan, yasan BGS ba karamin kwakwalwa bane da shi yanzun nan zai iya gane komai "My daughter ya kamata kema kije ki kwanta kinga yanxu almost 10, "to my lovely Abba tana faɗin hakan ta mike ta ajiye Cup ɗin hannun ta saman trey,  san nan ta ɗauki trey ɗin ta juyo ta ansa cup ɗin hannun BGS dana hannun Abba ta ɗora kan trey ta ɗauka tayi waje,

Dawo da kallansa Abba yayi kan BGS san nan yafara Magana "kasan me nake so da kai my Son "aa Abba "abun dana ke so da kai dan Allah ka dai na korar yarinyar nan idan na ai'kota wajen ka, kuma ka dai na yi mata tsawa kaji my lovely Son ya karisa maganar chikin sigar rarrashi, ɗaure fuska sosai BGS yayi kafin yace "Abba ni pls ka daina aiko min su ɗaki, wlh dan ma a'baya kache kar na kara bugun tane Allah da ɗazun da tashigo sai na ɓallata, ka rinka aiko Fahad ko ka kirani awaya mana Abba haba, ya karisa maganar kamar zai yi kuka, "to shike nan zan daina aiko ta tun da baka son,

... hakan yayi maka? mikewa BGS yayi yaje ya rungumi Abba yana faɗin "shiyasa nake son ka my Abba murmushi Abba yayi yasa hannu yana ɗan bubbuga bayan BGS kamar karamin yaro yana faɗin "nima ai ina matikar kaunar ku sosai duk wani abun da zai saku farinchiki shina ke so, "Abba muma mu ma matikar son farinchikin ka ai yayi maganar yana raba jikin sa dana Abba, miƙewa Abba yayi yana faɗin lokachin barchi yayi good night my lovely son, "good night Abba na BGS ya bashi amsa yana nufar, kaban mirrow, Abba kuma ya fice daga ɗakin yanufi part nashi, jallabiyar jikin sa, BGS ya chire ya nufi toilet dan yin wanka.

Abangaren Aryan kuwa yana fitowa daga part na BGS kai tsaye, part nashi ya nufa da sauri yana shiga betroom ɗin diyana na fitowa ta kawo masa coffee ta ajiye zata fita, karo sukayi kanta ya bugi faffaɗar kirjinsa ta fame chiwon nata wani ihu azaba ta saki tayi baya zata faɗi, da sauri ya rikota, nan take jini ya fara zuba daga goshin nata, rungumeta yayi sosai ajikin sa da kyar ya iya furta "sorry kiyi shiru, "yaya Aryan zafi ya kemin sosai "na sani nasan zai miki zafi amma ki daure ki daina kuka kinji muje na duba miki, ya karisa maganar tare da raba jikin su, ya kama hannun ta suka koma chikin ɗakin saman sofa ya zaunar da ita, ya zauna gefen ta ya zuba mata ash eyes nashi yana kallan yadda hawaye wani ke bin wani a kunchinta calmly ya fara magana "ba na che ki dai na kukan nan ba, turo ɗan karamin bakin nan nata tayi "to zafifa yake min, hannu yasa yana goge mata hawayen yana faɗin "to ki daure kinji bana son kukan naki ne ko kaɗan yana damun na idan ki nayi, ba kiga yadda ki kayi tsara kwalliyar ki ba ko so kike ya ɓachi "a'a bana son ya ɓachi "to kiyi shiru kinji, gyaɗa masa kai kawai tayi, shi kuma ya mike ya ɗauko A box,ya dawo kusa da ita ya zauna

A hankali ya fara gyara mata chiwon nata, sai was Allah na take faɗi shi kuma yana che mata sorry, har ya kammala san nan ya miƙe ya mayar da Box ɗin ya koma gefen katafaren gadon sa ya zauna, 

...ɗaure fuska yayi sosai yana kallonta "ke wai bana che kada ki sake kwalliya da daddare ba, baki da lfy ma amma sai kin zana waɗan nan abubuwa a ɗan karamin face nakin nan ko? turo ɗan karamin bakin nan nata tayi kamar biro kafin tace "kayi hakuri bazan sake ba "kullun haka ki ke chewa ba zaki sake ba amma sake... Bai karisa maganar ba ash eyes nashi ya sauƙa a kan kayan jikinta, 

wasu shaggun riga da wando ne, Black jeans ne ya matseta sossi santala santalan chin yoyin nan nata kamar zasu fasa wando, sai yar figaggiyar T-shirt pink colour itama ta matseta kana ganin shap na breast nata sosai daman gasu nan masha Allah tula tula dasu,  ga kanta ba ɗan kwali ta saki wan nan bakin lallausan gashin nan nata har baya,sai shekin gashin ke yi, ta zubo wani ɗan kaɗan ɗin gashi ta gaban goshin ta, tayi make up nata iya make up,ga wani shegun high heel pink da ta sa a kafar ta, mamaki ne ma yaka mashi wai wa ya koyawa yarinyar nan duk irin waɗan nan abubuwa, nan take yaji ransa ya bachi sosai chikin tsawa yace "ke kina da hankali kuwa haka daman ki ka fito,kika keto gaba ɗaya part part na gidan nan har ki ka zo nan ko? chikin tsoro ta ɗago dan jin yadda yayi maganar, ba karamin raza tayi ba data kalli yadda fiskarsa ta sauya lokachi guda, asukwane ta miƙe zata gudu, 

Taku ɗaya yayi ya tamki kugunta ta baya, tsabar raza da tayine bata san, lokachin da ta fasa ihu ba, asukwane yasa hannu ya toshe mata baki, chikin tsawa ya furta "kimin shiru,shiru tayi jikinta har bari yake  .  zame hannunsa yayi daga bakinta ya juyo da ita suna fuskantar juna, nan take kuma sai yaji ɓachin ran nasa duk ya kau sosai yake kallon face, nata a ranshe yana faɗin "yarinya sai kyau kamar ita tayi kanta komai tayi kyau yake mata,

Ganin yayi shirune yasa diyana ɗago blue eyes nata karaf suka sauƙa chikin nashi,  murya na rawa lips nata sai kerma suke saboda tsoro kamar mai jin sanyi tafara magana "yaya Aryan kayi hakuri wlh ba laifi na bane Aunty farida da che tache... Bata karisa maganar ba sakama kon fisgota da yayi ta faɗa faffaɗar kirjin sa, dan ba zai iya jure kallan yadda lips nata ke motsawa ba,mutuwar tsaye diyana tayi dan gaba ɗaya ji tayi kamar baa duniya take ba, ran kwafar da kansa yayi sai tin kunnen'ta chikin wata iriyar kasalalliyar murya ya fara magana kasa kasa "karki sake saka irin waɗan nan kayan kinji ko? idan ma kina so sakawa kisa a iya ɗaki kawai idan zaki fita waje kisa hijabi kinji ban son na kara ganin ki haka.

....da kyar ta iya ɗago kanta daga kirjin nashi dan ta samu iskan da zata yi numfashi kasan chewar ya matseta sosai,bata iya wani numfashi da kyau, a hankali ta buɗe ɗan ƙaramin bakin ta muryar har rawa yake tafara magana "to yaya Aryan ai Aunty farida che tache na rinka sawa idan zan... Bai bari ta karisa ba ta ɗora ya tsan sa a saman lallausan lips nata yana girgiza kai kafin yace "a'a koda Aunty farida ta sake chewa ki saka kiche mata na hana ki kinji? kuma ai ita Aunty farida gobe ma zata koma ni dai kar na sake ganin ki da irin wan nan kayan bana so, to kawai tace masa tana numfashi da kyar saboda matse ta da yayi, 

Shiru sukayi dukkan su shi yana kallanta ita kuma tana kallon kirjinsa, Almost 5mnt a haka, san nan diyana ta ɗago blue eyes nata slowly ta sauke su kan face nashi, karaf suka sauka chikin ash eyes nashi, dan kuwa ita yake kallo, da sauri tayi kasa da kanta dan bazata iya kallan chikin idon sa ba, "yaya Aryan na gaji da tsayuwa wlh jinake kamar zan faɗi "to ni kuma ban gajiba, da sauri ta ɗago blue eyes nata tana kallonsa ganin yadda ta ɗago ne yasa yashiga tunanin me ya faɗa ne, dan shi kwata kwata bai ma san me ya faɗa ba, sauko da ash eyes nashi yayi kan ɗan karamin bakin ta, yana kallan lallausan lips nata, da sauri ya sake ta yana furta a'uzubillahi minasshe ɗanin rajim, a chikin zuchiyar sa "ke wuche ki tafi ɗaki dare yayi kuma karki sake fitowa da irin kayan nan, yana kai karshen maganar ya juya yanufi toilet da sauri wai danma kar ya sake kallonta, 

Kwas kwas kwas diyana ta juya jiki ba kwari ta nufi waje, 

Aryan kuwa wanka yayi ya fito a gurguje ya shirya cikin kayan barchi riga da dogon wando masu kyau da tsada farare tas masu laushi, ganin dare yayi sosai yasa shi hayewa katafaren gadon sa batare da yashi coffee ɗin ba  ja blanket yayi zuwa chikin sa ya sage gudun A.c ya lumshe ido ba jimawa barchi yayi awon gaba dashi

 



*💫STAR LADY💫*


          💖The Talent Troupe Writer's 💖




*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star Lady*



Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣6️⃣*


Misalin karfe 7 na safe Ammi na zaune a bakin katafaren gadon ta sanye take da wata ɗankareriyar lace baki mai zanen flower manya manya ajiki jaa, ɗinkin bubu gawn, ta sanya wani dan kareren sarkan gold a wuya ka wasu manya manyan abun hannu masu kyau da tsada a hannunta, sai kamshi take zubawa,kamar anyi ɓarin turare ajikinta

 da sallama ɗauke a bakin sa BGS ya shigo, kauda kai gefe Ammi tayi tana amsa sallamar, ganin hakan yasa BGS ya kariso chikin ɗakin da sauri a gaban ta ya zauna saman lallausan karpet na alfarma dake shinfiɗe a ɗakin, chikin sanyi murya ya fara magana "ina kwana Ammi, kara ɗaure fuska sosai Ammi tayi kasa kasa ta amsa masa da lfy, kwantar da kansa yayi kan chinyar ta ya riko hannunta cikin ladabi da girmamawa yafara Magana "kiyi hakuri Ammi na, kinji nasan nayi laifi dayawa amma pls ki daina fushi dani kinji, kin fa san idan ki na fushi da ni, ina cikin fushin Ubangiji kuma kome nasa a gaba bazan yi nasara ba pls my Ammi for give me, ɗan daka tawa yayi yana sauraron yaji me zata che

..... Hannu Ammi tasa ta fara shafa lallausan gashin kansa kafin tace "ni ba fushi nake da kai ba kuma ba zan iya fushi da kai ba saboda na san idan iyaye suna fushi da ƴa'ƴansu, wache bala'i mai girma suke jawa ƴaƴan nasu, kawai dai abun da ka keyi ne baya da chewa, "zan daina Ammi na duk wani abun da baki so ki faɗa min zan dai na "kayi alkawari "na miki alkawari Ammi na keche fa farin chikina lokachin da bana kasar nan kin ta ɓa ganin nayi 2 hours ban kira ki ba, kome aikin da nake sai na daka tar na kira ki koda na 5mnt ne, saboda kawai inji ya kike, "eh hakane na sani kuma kana da gaskiya 

.... yanzu dai abu biyu ne kake yi a gidan nan yake ɓatamin rai, kuma nake son ka daina yi, da sauri BGS  ya ɗago kai yana kallan ta, murnushi kaɗan Ammi ta sakar masa, shima wani cool murmushi wan da bai ta ɓayi ba ya sake har sai da dimple nashi ta lotsa, chigaba da magana Ammi tayi "ina son ka rage tsawar da ka kewa su hiyana abun yana damuna kaga marayune ba uwa ba uba pls ku jasu ajiki dan ku mantar da su marai chin nasu, kannen kane kai yaka mata kafi kowa sakar musu fuska da jansu ajiki,

..ɗaure fuska BGS yayi,bai che komai ba yayi shiru yana tunani, yanzu dai sulhu nazo nema wajen Ammi bai kamata nayi wani abun da zai sake ɓata mata rai ba gaskiya bari dai na bita a yadda take so for now, in yaso daga baya na koma normal, ɗan murmushi gefen fuska ya saki a hankali ya motsa ɗan karamin bakin nan nashi ya furta "daga shi sai mai kuma Ammi, ajiyar zuchiya Ammi ta sauƙe kafin tace "sai batun kannen ka su Umar, inajin ɓachin rai idan suka gaishe ka baka amsa ba, sai kache wasu abokan gaba, ai ko bazaka amsa gaisuwar mutane a waje ba to fa ya zama dole ka rinƙa amsa na kannen ka "to shike Ammi na i will try my best kinji daɗi " kwarai kuwa naji daɗi  "Thank God, my Ammi haka nake so in ga kina chikin farin chiki, zame hannunta Ammi tayi daga gashin kan nashi tana faɗin "nima ina son naka farinchikin ai, yanzu dai katashi kaje ka shirya kuje ku raka Ahmad fada "a'a Ammi ni bazan je ba "what Ammi ta faɗa tana kara waro fararen idon ta "baka isa ba ka tashi kuma Allah idan ban ganka a fada ba.. bai bari ta karisa maganar ba yace "a'a my Ammi yanzu ma zanje na shirya yayi maganar yana miƙewa, san nan yanufi waje 

Nauyayyar ajiyar zuchiya Ammi ta sauƙe, a fili ta fara magana, Alhadulillah Allah na godema da ka bani ɗa mai kauna ta mai jin tausayi na mai gudun ɓachin rai na, ya Allah ka tai makeni nima na rinƙa faran ta masa kamar yadda yake min ya Allah ka nunamin ranar da zaiyi Aure, bana son na chigaba da ta kura masa a kan batun Aure, yana min biyayya iya gorgidon iyawar sa yana son farinchiki na, bai kamata ni kuma ya dage wajen sashi abun da baya so ba zan rinƙa taya shi da addu'a har Allah ya karkato da hankalin sa kan Auren, karisa hayewa saman gadon tayi ta kwanta da kyau ya lumshe ido tana ta tunani

Misalin karfe 9:30 gaba ɗaya family sun haɗu a faɗa sun sha kwalliya sosai Abba na zaune kan kujerar mulkin su Ammi suna gefe gefensa, ga wata ha ɗaddɗiyar gujera a gefen na Abba ba kowa a kan gujerar, su Aryan suna kujerun dake jere gefe guda kujerun su Aunty farida na fuskantar nasu Aryan, ga manya manya baki kamar su sarkin zaria sarkin gombe sarkin yola da dai sauran su, 

Miƙe Wa Abba yayi daga kan kujerar da yake zaune, yayi tattaki izu tsakiyar fada san nan ya fara magana "kai Ahmad tashi ka hau kujerar mulkin ka, jiki ba kwari Ahmad ya mike ya nufi kujerar, yana zama su wajiri suka miƙe suka nufoshi, nan take suka ɗauko farin kyalle suka fara naɗa masa rawani a kai, shidai kamar zai yi kuka haka aka naɗa masa rawanin sarautar,bayan su waziri sun gama na ɗawa Ahmad rawanin ne, Abba yace "salati goma ga annabi yayi maganar yana nufar gujerar kusa da Ahmad, 

...zama Abba yayi san nan su kafara yiwa annabi salata bayan sun gama salati, Abba ya ɗago ido yana kallan BGS "Safras ka rufe mana da addu'a, BGS bayasan yin magana ko kaɗan amma yana gudun ya sake ɓatawa Ammi rai Allah badan Ammi na wajen nan ba da ba zanyi addu'ar nan ba, slowly ya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi, da wani zazzakar Muryar sa ya fara zuba addu'oe, gaba ɗaya palon sunyi shiru suna sauraron'sa slowly hiyana ta ɗago blue eyes nata ta sauke su a kan shi chikin ranta tana faɗin "wow dama haka yake da voice mai daɗi? shi yasa baya magana dan kar murinƙa ji hmmm sosai take kalansa, har ya kai karshen Addu'ar yana kai karshe ya mike da sauri ya fice daga fada

sai sauri yake yana taku irin na jaruman maza, yazo dai dai zai shiga ɓangaren kamar daga sama yaji murya daga bayan sa tana faɗin "baka jiba, batare daya juyaba yayi shigewar sa, kai tsaye betroom nashi ya nufa yana shiga ya nufi katafaren gadon sa, ya haye ya kwanta ya lumshe ido yana jan tsaki

A hankalin ta turo kofar ɗakin ta shigo kwas, kwas, kwas, take takawa  har gaban gadon nashi ta zo, kashe murya tayi tafara magana "haba mana shine ina maka magana a waje ka shareni, kasan wacece ni? nifa yar Autan sarkin zaria che pls kyakkyawa katashi mana muyi magana wlh ni bana barin abu a rai na da abu ya burgeni nake faɗe, wlh ka tafi da ni tun da kafara addu'a a fada nake kallon ka, kuma SON ka nake da dukkan zuchiyata, ko motsi BGS bai yiba bare tasa ran zai yi magana "haba mana kyakkyawa nasan ba kayi barchi... Bata kai karshen maganar ba taga BGS ya mike batayi auneba taji saukar wani gigitatchiyar ma haukachiyar mari,a kan kunchinta wani ihun azaba ta saki

.. a fusache ya zaro belt daga ma zaunin sa ya fara zuba mata ta ko ina a jikin ta, ihu take kamar ranta zai fita,shiko ko ajikinsa rai ambachi yake zabga mata belt ɗin,  data ga dai BGS zai iya kashe ta ba wan da yaji ihun data ke bare yazo ya taimaka mata yasa ta miƙe da kyar tanufi hanyar fita, damko atachimen ɗin datayi chikon gashi da shi yayi ya daga ta da kai, yayi wurgi da ita gefe hakan yayi dai dai da shigowar Aryan ɗakin, a fusache BGS ya sake nufar ta, ko motsi batayi da alama ta suma chigaba da bugunta yayi

Da gudu Aryan ya karisa chikin ɗakin ya sa hannu biyu ya damko damsen BGS yana faɗin "haba blood kisa zakayi ne, chikin tsawa BGS yace "sakeni Aryan nache kasake ni "bazan sake ka ba BGS bazan sake ka ba nache, ida kuma nima zaka haɗa har dani ka bugane to Bismillah, a fusache BGS ya ya kwache hannunsa daga rikon da Aryan ya masa ya fice daga ɗakin sai huchi yake,  bin yarinyar da kallon Aryan yayi a ranshi yana faɗin ko wacece wan nan kuma ko me ya haɗa su, wayar sa ya chiro daga aljihun wandon jeans dake jikin sa ya fara kiran layin Aunty farida, 

....Bugu ɗaya Aunty farida ta ɗaga tare da faɗin "hello bro "Aunty farida kizo ɗakin BGS ki ɗauki wata yarinya "wata yarinya kuma? Aryan "eh nima yanzu shigowa na ka nan, na samu yana bugun wata yarinya gashi da alama ta suma "Allah dai yasa ba diyana ko hiyana bace "aa Aunty babba basu bane wan nan ma ba yar gidan nan bache "to ke nan a chikin baƙin nan ne, me tamasa zai bugi yar mutane, "to nima dai ban sani ba idan kinzo kya tambaye shi yana gama faɗin hakan ya katse kiran, ya juya ya fice daga ɗakin

Misalin karfe 2 na rana gaba ɗaya family Abba sun haɗu a babban palon Abba dan chin abinchin rana ban da ƴanma tan Ammi sune kaɗai basa nan sai BGS wadda daman ba tare suke chin abinchi da shi ba, "kin san me Safras ya aikata yau kuwa? Chewar Abba yayi maganar yana kallan Ammi "aa me kuma yayi chewar Ammi "hmmm yar sarkin zaria ya kama ya rinƙa bugu yanzu haka tana asibiti wlh bakiga yadda mahaifinta ya bata rai ba da kyar na bashi hakuri "kai wan nan yaro to me ya haɗa su Ammi ta tambaya tana kokarin ajiye spoon ɗin hannunta, da sauri Aunty Farida tace "aa baruwan DON ita taje ɗakin sa ta same sa ai, shiru sukayi dan Abba ya gane dalilin daya sa BGS ya bugi yarinyar


wai ina yan mata nane chewar Abba "suna ɗaki kasan diyana sarkin kwalliya che tana chan wai sai ta gama kwalliya, zata zo chin abinchin, su hiyana kuma suna jiranta chewar Ammi, murmushi Abba yayi kafin yace "ai tana da gaskiya gara ta rinƙa kwalliya sosai dan ta samu miji da wuri na aurar dasu, a sukwane Aryan ya ɗago ash eyes nashi karaf, idon nasa,  ya sauka chikin na Abba dan kuwa shi Abba ke kallo mayar da kansa yayi ya sun kuyar ya ajiye spoon ɗin dake hannun sa ya ɗauki wayar sa ya fara latsawa, 

...... Aure kuma Abba Aunty farida ta tambaya da mamaki, "eh mana my daughter yanzu su diyana basu kai Aure bane, ai da diyana hiyana Zahra sun kai Aure kuma nan ba da jimawa ba zan musu,  wani dogon tsaki Aryan yaja wadda yasa gaba ɗaya mutanen palo suka ɗago suna kallon sa "Aryan lfy Ummi ta tambaya tana kallan sa daga sama har kasa, rai a ɓace yace "lfy Ummi, kau da fuska Abba yayi daga kallon Aryan ya chigaba da chewa "ita kam diyana ma ai tana da masoya ga yaya bellon ta, na Yola ga kuma malamin makarantar su duk da naji anche an karya masa kafa, baya tafi to in dai diyana na son shi zan fiddashi kasar india amasa aiki, "oh my god Aryan yafaɗa chikin tsawa yana dafe kai, wadda sai da gaba ɗaya jama'ar palon suka tsorata, "Aryan kana lfy kuwa Aunty farida ta tambaya da mamaki a fiskar ta, ban za yayi dasu ko sannu bai cheba, Abba kuwa chewa yayi "kai ku kyalesa mana tun da ba ya son magana, mikewa Aunty farida tayi daga nata kujerar tana faɗin "aa Abba wan nan irin tsawa haka ba lfy ba ta karisa maganar tana karisawa wajen da Aryan ke zaune, hannu tasa tana shafa kansa kafin tace "me nenen bro, ɗago ash eyes nashi yayi wadda suka sauya sukayi jaa ya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi zai yi magana ke nan, sai sukaji yar siririyar muryan diyana tana doko sallama tun daga bakin kofar palon

Mai da kallon su gaba ɗaya mutanen palon su kayi izuwa bakin kofar palon, anko su kayi gaba ɗayan su chiki jalla biya pink colour Zahra hiyana lamrat amrat duk sun yafa mayafin rigar amma ban da diyana, ita kam ta tasaki wan nan bakin lallausan dogon gashin nan nata har gadon baya, a nitse suka kariso chikin palon kowan nan su na zauna a kujera table ɗin,

Wow my daughter kinyi kyau sosai chewar Abba yayi maganar yana kallan diyana, dan ita kaɗai che a chikin su tayi kwalliya, "laaaa Abba kasan me ranan ma yaya yusuf yace nayi kyau haka yaya Aryan ma da na kai masa coffee yace nayi kyau dana ɗan kwali, asukwane matasan gidan suka juyo da kallan su kan Aryan, 

ɗaure fuska sosai Aryan yayi kamar bai taɓa dariya ba ya chigaba da latsa wayar sa,  ita kuwa diyaba ko ajikin ta sai murmushi take tana bawa Abba lbr, ganin Aryan ya ɓata rai sosai ne yasa Yusuf yace "eh mana my sister ai dole kowa yace kina da kyau, to ke ba sis ɗin mu bace idan bamu yabe ki ba, waza mu yaba, wani murmushi diyana ta saki tana faɗin "Allah yaya Yusuf idan nayi kwalli ina kyau? "kai sosai ma kuwa may sis ai duk gidan nan kin fi kowa kyau kuma kin fi kowa... Bai karisa maganar ba saka makon wani mugun kallon da Aryan ya wurga masa, irin kallon nan na ina ruwan ka da ita idan ma tafi kowa kyau, shiru Yusuf yayi a chikin zuchiya yana tunani kai yaya Aryan akoi bala'e kishi to kai kaki bayyana soyayyarka san nan kuma idan wani na ya bonta ko ya raɓe ta  ka hukun tashi, yanzu da kake harara'ta ni ina ruwana ai ban che ina son taba kawai yabon ta nake ni da nake da mai baby . Juyawa Aunty farida tayi ta koma wajen zaman ta ta zauna, shiru palon yayi sai karar spoon kawai zaka ji  

"Yauwa yaya Aryan wan nan jakar da ka bani nan taki buɗuwa, kullun nache zan kawo ka buɗe min sai na rinƙa mantawa, chewar diyana tayi maganar tana kallon Aryan, tab aiko gaba ɗaya palon sun zuba musu ido suna jiran amsar da zai bata, ɗago ash eyes nashi yayi ya sauke su kan face nata sai murnushi take nan take kuma sai yaji wani sanyi na ratsa zu chiyar sa, calmly ya fara magana "eh nina kulle jakar zan buɗe miki amma ba yanzu ba, tirkashi Aunty amarya ji take kamar ta tashi ta shake diyana dan bakin chiki Amma tana tsoron Abba

Ayya yaya Aryan ka buɗemin kaji, kaga su Aunty Zahra duk sun sa nasu tsara bar kuma wlh kayan nasu yamin kyau nima ina son saka nawa ta karisa maganar kamar zata yi kuka, zuba mata ash eyes nashi yayi sosai, ya kasa kawar da kallon sa daga gare ta, Abba dai ajiye spoon nashi yayi ya zubawa Romeo and Juliet ido kawai yana kallan su, Khalid Yusuf Aunty farida sai murnushi suke suna murna, Aunty amarya Aunty Maryam kuwa kamar zasu mutu dan bakin chiki, Ammi da Ummi kam ko ajikin su abin chin su kawai suke chi basu ma lura da Abun da ke faruwa ba, Fahad ma abinchin sa yake chi ko ajikin sa bai ma san suna yi ba  haidar Umar sai satar kallan yaya Aryan suke suna mamaki, tsoro suke kar ya kama su suna kallon sa, Aunty salma Aunty mardiya wayoyin su suke latsawa han kalin su baya kan jamar palon

Da kyar ya iya saita voice nashi kasa kasa kamar mai raɗa yace "an jima ki kawo min jakar na buɗe miki yana gama faɗin hakan ya miƙe da sauri ya bar palon, dawo da kallon ta Aunty farida tayi kan Abba, ta kashe masa ido ɗaya wani cool murmushi Abba ya sake mata a hankali ya motsa lips nashi, yayi ta alama da mun fara nasara, gyaɗa masa kai kawai Aunty farida tayi san nan ta chigaba da chin abin chinta.

Misalin karfe 3 :30 na rana gaba ɗaya ƴanmatan Ammi suna zaune a karamin palon sama na ɓangaren Ammi hiyana na riƙe da Alkur'ani mai girma tana karatu, diyana na buga game a wayar Zahra lamrat da amrat suna kallo Film a makeken Tv dake makale a bango, Zahra riƙe da littafin husnul Muslim tana karatu addu'oe, hankalin su yayi nisa a kan abubuwar da suke,

.... da sallama Yusuf ya shigo palon da sauri suka ɗago suna kallon sa, da gudu lamrat ta miƙe ta nufe'sa hannu ya buɗe mata ta faɗa kan faffaɗar kirjinsa ya mai da hannun sa ya rufe yana faɗin "my baby nayi kewar ki, cikin shogoɓa tace "nima nayi kewar ka yaya Yusuf, hannu yasa yana shafa kanta a hankali yana faɗin "my baby ina san gashin nan naki kyau yake min, lamrat zata yi magana yayi sauri raba jikinta da nashi kasan chewar yaji alamun tafiya ta bayanzu kamar mutun zai shigo palon, riko hannun ta yayi suka karisa chikin palon suka zauna saman sofa mai zaman mutun 3, 

da sallama Khalid ya shigo palon shima da gudu Zahra ta miƙe tanufe sa,  har zata rungume sa sai kuma ta dakata, kallanta yake itama tana kallon sa "sannu da zuwa yaya Khalid ta faɗa tana sun kuyar da kai  "Auta yau kam babu oyoyo ne ya tambaya yana ɗago haɓatar da hannun'sa, chikin shagwaɓa tace "Ammi che tace wai kai zan Aura kuma na daina yi maka oyoyo sai bayan Aure, wani nauyayyar ajiyar zuchiya Khalid ya sauke tare da faɗin "da gaske Auta Ammi ta faɗa miki ni zaki Aura, gyaɗa masa kai Zahra tayi alamar eh,  gyara tsayuwar sa yayi kafin yace "to kina sona, juyawa Zahra tayi zata gudu yayi sauri riko hannunta sai lokachin idon'sa ya sauka kan Yusuf dake zaune ya zuba musu ido, diyana kam bata ma san sunayi ba game nata kawai take bugawa hiyana ma kanta na kan qur'ani karatun ta kawai take

Harara Khalid ya wugawa Yusuf zai yi magana ke nan haidar ya shigo da gudu yana faɗin Ammi, Ammi ina kike yaya Ahmad ya mut....✍️


💖The Talent Troupe Writer's 💖

1 Duk Karfin Izzata 
2 Gidan Aunty
3 Jini Ɗaya
4 Sarki Sameer
5 Kafita Zakka 
 
Kar kubari abaku lbr love Story's 

*💫STAR LADY💫*27

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
                     ⬇️
               *Star Lady*
Star lady


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣7️⃣*



......Ammi, Ammi ina kike yaya Ahmad ya mutu, a sukwane Yusuf ya miƙe yana faɗin "kai haidar ka dawo cikin hankalin ka, wani Ahmad ɗin? "wlh yaya Yusuf ina chikin hankalina yanzun nan muna zaune dashi a fada kawai ya fara tari, jini na fito kafin kache me ya faɗi, ai tun haidar bai kai karshen maganar ba Khalid ya saki hannu Zahra ya juya har suna karo da Yusuf wajen fita da gudu, Haidar kuwa ya nufi betroom ɗin Ammi,  mikewa diyana hiyana zahra lamrat amrat sukayi suka bi bayan su Yusuf, tare Ammi da haidar suka fito suma suka nufi fada

Koda su Ammi suka isa fada gaba ɗaya family sun haɗu awajen suna tsaye chirko chirko da kaga fiskokin su kaga alamun tashin hankali musamman Khalid da Aiman na su tashin hankali  banne,  


BGS daune a tsakiyar fada ya ɗora kan yaya Ahmad kan chinyar sa yana zura hannun sa chikin rigan Ahmad, Abba Aryan Fahad Umar suna tsaye a kansu, Aiman da Khalid kam sun ma kasa kariso wa wajen saboda tashin hankali daga baya suka tsaya

, shiru gaba ɗaya su kayi suna sun zubawa BGS ido suna sauraron suji me zai che 

.. Almost 5mnt san nan BGS ya ɗago green eyes nashi da suka sauya launi izuwa jaa sosai chikin wata iriyar voice mai kama da mara lfy ya furta "bai mutu ba  suma yayi,ku bani ruwa mai sanyi sosai  gaba ɗaya fada ta ɗauƙa da alhamdulliah san nan Khalid ya juya da sauri ya nufi katuwar freij dake cikin fadan ya ɗauko ruwa mai sanyi ya dawo ya miƙawa BGS, tsabar tashin hankali har ya manta ma ana buɗe robar ruwa..

...Ansan ruwan Aryan yayi da sauri ya buɗe bakin roban san nan ya mikawa BGS, hannu BGS ya mika wa Aryan alamun ya zuba masa ruwan, zaba masa kaɗan Aryan yayi a hannun nashi, a hankali BGS ya shafawa Ahmad ruwa a fuska 

wani atishawa mai karfi gaske Ahmad yayi, ya fara tari da karfi karfi kamar makogoran sa zai fashe yana kokarin miƙewa, da sauri BGS ya rikosa yana faɗin "kubani ruwan, a hanzar che  Aryan ya miƙa masa roban gaba ɗaya, ansa yayi  ya ka fawa Ahmad a baki amma ina Ahmad yaki sha sai kokarin mikewa yake, gaba ɗaya ya sauya lokachi guda ya rame ya fita hayyachi sa,

Da karfi Ahmad ya fisge jikin sa daga na BGS zai mikewa, a'sukwane BGS ya tamke sa ya mai dashi ya zaunar gaba ɗaya fada hankalin su ya tashi ganin halin da Ahmad ke chiki

faɗa ne ya kaure tsakani  BGS da Ahmad dan Ahmad ya dage sai ya tashi, shi kuma BGS ya hana shi,da BGS ya ga dai Ahmad ba zai sarrafu ta lalama ba sai ya mike, yasa karfi ya danne Ahmad a kasa ya haɗa hannayen sa dukka biyi ya taka da kafa ɗaya ya damki gashin kan sa ya ɗago da fiskar'sa ya kafa masa robar ruwan mai sanyi a baki, dan ruwan zata tai maka masa sabo da tarin da yake, 

ba shiri Ahmad ya fara haɗiye ruwan, dan dole,  kawar da kai Ammi da Ummi su kayi daga kallon Ahmad suna kwalla,  da gudu Aunty mardiya ta juya ta bar fada tana kuka, bazata iya kallon halin da Ahmad ke chiki ba, kuka Aunty salma keyi sosai rungumeta Aunty farida tayi tana ɗan bubbuga bayan ta alamar rarrashi,ita ma dai Aunty farida hawaye take,  shi kansa Khalid daure wa yake amma ji yake kamar zai yi kuka, sosai hiyana ke kuka kamar ranta zai fita daman ita sarkin tausayine, haidar Umar duk kwalla suke, Fahad ma idon sa ya chika tab da kwalla amma basu zubo ba,  Abba kuwa idon sa ta sauya tayi jaa sosai, ga tashin hankali nan karara a bayyane a kan fuskar sa,  Aiman kam ba'a magana dan yafi kowa shiga damuwa saboda tare suke komai da Ahmad ko Aryan da suke yan biyu bai shaku dashi kamar yadda ya shaku da Ahmad ba

Ganin yadda BGS ya taka hannun Ahmad yayi yawane dan har hannun nashi sun chanza izuwa jaa sun fara kunbura abunku da farar fata, yasa Aryan ɗukawa kasa yasa  hannun'sa  ya dan bubbuga kafar BGS alamar ya sassauta takun da yawa hannun, chire kafar sa yayi gaba ɗaya tare da chire roban ruwan daga bakin Ahmad din,  ya zuba masa ido, 

shiru Ahmad ya kwanta a kasan kamar mai tunani,wani abu hannu Aryan yasa ya ɗan tattaɓa kuma tunsa yana kiran su nan sa, shiru Ahmad bai amsaba kuma idon sa a buɗe ya na  kallon su, ganin hakan yasa BGS mikewa tsaye sosai ya ɗauki Ahmad ɗin ya saɓashi a kafadar sa ya fiche dashi, daga fadan  gaba ɗaya family suka bi bayan su 

Kai tsaye ɗakin da suke jin yar duk wan da bai da lfy a gidan ne, dan in dai ba sun koma London ba, to ba wan da ake kai wa asibiti su suke duba kowa na gidan, dan babu abun da babu na jinyar ma jinyata a ɗakin

akan katafaren gadon da aka tanada dan marasa lfy BGS  ya kwantar da Ahmad, har lokachin idon sa biyu yana bin su da kallo amma ya kasa magana, kayan aiki BGS ya ɗauko ya fara duba shi, 

almost 30mnt BGS na kan Ahmad yana ɗuba shi,

Slowly ya juyo ya kalli su Abba da su kayi chirko chirko suna jiran suji meke damun Ahmad "Abba ni fa banga wani abun da yake damun Ahmad ba, nayi iya bin chike na banga komai ba . Amma Aiman Aryan kuma kuzo ku gwada mugani, ya karisa maganar yana kallon Aiman da Aryan dake tsaye waje guda,  da kyar Aiman ya iya buɗe baki yace "bazan iya ba bazan iya ganin Ahmad chikin chiwo ba shiyasa na kasa karisawa inda yake, gaba ɗaya mutanen ɗakin sun tausaya wa Aiman dan kowa yasan duk inda kaga Aiman to fa Ahmad na wajen tare suke komai .

a hankali Aryan ya tako izuwa wajen gadon Ahmad, ya karbi na urorin dake hannun BGS ya fara nashi gwaje gwajen, shima almost 30mnt ya ɗauka san nan ya juyo a hankali yana kallon su Abba har bai san haɗa ido dasu "Aryan ka gano wani abu ne Abba ya tambaya a ruɗe, girgiza kai kawai Aryan yayi alamar a'a, dan ya kasa magana, jin hakan yasa Aiman juyawa da sauri ya bar ɗakin 

shiru gaba ɗayansu su kayi kowa da abun da yake tunani almost 1h, san nan BGS ya juya ya ɗauki alluran barchi ya yiwa Ahmad, yana zare alluran ya ajiye ya fita dakin da sauri dan ji yake kamar zuchiyar sa zata fashe, dan yana matikar kaunar yan uwansa mu samman Aryan Aunty farida Khalid Aiman Ahmad Yusuf Son da yake musu na da ban ne "Abba muje mu kyalesa alluran barchi aka masa mu barshi ya huta chewar Aryan yana gama faɗin hakan ya nufi waje shima, gaba dayan su suka bi bayan Aryan su ma

YOLA


Dawani matsanan chin ihu buba ya farka daga doguwar sumar daya faɗa, har sai da ya tsorata su inna dake zaune awajen kowa ya miƙe zai gudu, ban da yaya bello dake zaune ko motsi bai yiba, zubur buba ya miƙe yana ko karin fita waje,  da sauri malam yace "ku riƙe sa 

 a guje inna habiba da innar bubu su kayi waje saboda tsoro, yaya bello ne yayi ta maza ya riko buba sai kokarin fiskage buba keyi, malam daya ga abun tayi yawa sai ya che da yaya Bello "a ɗaure sa da igiya domin kuwa tun lokachin da kuka kawo sa na fahimchi ya bugu a kai sosai kuma hakan ya taɓa masa ƙwaƙwalwa gaskiya, yanzu dai sai dai a barshi a ɗaure ana masa magani idan da rabon samun sauki to Allah ya sauwaka, idan ku kache zaku sa kesa to ina tabbatar muku bola bola zai fara bi, wasu hawayen masu zafi na tausayin ɗan uwan sa yaya Bello ke yi,  haka nan ya nufi wajen da malam ke ɗaure mahaukata ya sa karfi ya danne buba ya ɗaure sa, a zuchiyarsa yana tunanin "duk abun da ya faru da kai buba kai kaja ma kan ka, da kan ka, ka kun tatawa marayu, bayin Allah basu jiba basu gani ba basu maka komai ba ka takurawa rayuwar su ka addabe su ai daman alhakin su bazai taba barin ku ba,

Sosai ya ɗaure buba, sai ihu buban ke yi yana surutai, miƙewa malam yayi ya nufo su hannun sa riƙe da kwarya mai ɗauke da magani, "kai bello riƙemin kanshi mu bashi maganin nan zata tai maka masa chewar malam, da kyar suka iya ɗurawa buba maganin san nan yaya bello ya sake sa ya fito daga bukkar, a bakin kofa ya samu inna habiba da innar bubu sai sare ido suke "kai bello ya ake chiki? innar buba ta tambaya tana ɗan leƙa ɗakin, haushi kamar yaya Bello ya shaƙeta ta mutu ya keji wai ɗan da kika haifa a chikin ki,  ki ke gudu dan ya kamu da wata laluran ba duk ku kuka ɗorasa a kan gurɓatattiyar hanya ba

 banza yaya Bello yayi dasu bai tanka suba dan haushi, chikin tsiwa inna habiba tace "kai mara kunya, mara albarka ba da kai  muke  magana ba ne da zaka mana shiru, zaka faɗa mana ya jikin bubane ko sai na kwakkwaɗa maka mar

rabawa ta gefen su yaya bello yayi ya wuche ba tare da yace da su komai ba, wani dogon salati inna habiba tayi tana faɗin "a lallai bello ka girma to ko zaka yiwa innar bubu rashin kunya ai ni ba zaka min ba ko? tun da ni kanwar uban ne, shi dai yaya bello tafiyar sa yayi yana jin inna na surutai amma ko ajikin sa yanufi hanyar gonarsa chikin zuchiyar sa yana tunanin diyana "ya take shin chiwon nata ya warke ne Allah sarki bayin Allah, ɗayan ban garen zuchiyar sa kuwa tunano masa irin kyan da diyana tayi yake, tayi wani fresh da ita daman diyana ba baya ba wajen son kwalliya wow ga kyanta ya kara fitowa, sosai yake tunanin ta oh ni Bello Allah ka bani diyana a'matsayin mata aure, da sauri kuma ya kawar da tunanin damun diyana a matsayin mata dan yasan yanzu kam tafi karfin sa

Zama yayi chikin gonar tashi sai tunani yake yama rasa meke masa daɗi


Kano

gaba ɗaya family Abba suna zaune a babban palon sa sunyi jugum jugum daka gansu kaga alamar tashin hankali a kan fiskokin su

 "my daughter jirgin ku fa karfe 4:30 zai tashi yanzu kuma 4 tayi ya kamata ki tafi chewar Abba yayi maganar yana kallon Aunty farida "aa Abba ba zan iya tafiya ba sai naga yadda zata kasan che zan jira farka warsa, mugani "aa my daughter ya kamata ki koma tun da akoi waya zamu kira ki idan ya farka koma me ake chiki zaki ji  "Abba Allah bazan iya tafiya na bar ɗan uwana a haka ba wlh Abba idan na tafi nasan zuchiya ta zata iya bugawa pls my Abba ka bari dai zuwa gobe, ta karisa maganar kamar zata fashe da kuka "to shike nan my daughter Allah ya kaimu Allah yasa idan ya farka ya dawo dai dai, gaba ɗaya palon suka amsa da amin, shiru palon yayi bakajin komai sai shesshekar kukan hiyana dan ita ta kasa yin shiru, tana da tausayi sosai, bare ma idan ta tuno lokachin da BGS ya haɗe hannun yaya Ahmad ya take a kasa sai ta sake rushe wa da kuka 

......alama Ammi ta mata da hannu akan tazo da sauri ta miƙe ta nufi Ammi riko hannunta Ammi tayi ta zaunar da ita saman sofar da suke zaune ita da BGS,  hiyana da BGS su ka sa Ammi a tsakiya kwantar da hiyana Ammi tayi kan chinyar ta tana ɗan bubbuga bayan ta kasa kasa tafara magana "kiyi shiru hiyana kukan ya isa haka kinji zai samu lfy ki masa addu'a,

 jin Ammi na magana  kasa kasa ne yasa BGS ɗan wai gowa ganin yadda Ammi ta kwantar da hiyana a kan kafar tane, yasa shi sauri kawai da kai yana jan tsaki a zuchiyarsa yana faɗin "nikam ban san ya Ammi take san mai da yaran nan ba, yanzu wan nan abun zata wani kwantar da ita a kan kafar ta, gaskiya ni dole ma yaran nan su bar gidan nan ko kuma ni na koma gida na Abj dan bazan iya kallan abun haushi ba "BGS time ɗin farka wan Ahmad yayi fa chewar Aryan

Gaba ɗayan su, suka mike da sauri suka fito suka nufi ɗakin da Ahmad ke kwanche, 


Koda suka shiga already Ahmad ya farka, idon sa  a buɗe dan ya kai 5mnt da farkawa, da sauri BGS da Aryan suka kariso bakin gadon, hannun Ahmad BGS ya rike kasa kasa ya kira su nan shi "Ahmad,  shiru bai amsa ba kuma dai idon sa a buɗe, kariso wa wajen gadon Aiman yayi cikin dashewar murya ya fara magana "Ahmad pls wake up ba zan iya juran ganin ka a haka ba, wlh idan baka tashi ba zuchiya ta zata iya bugawa pls my blood, kuka Aiman yake kamar karamin yaro yana Magana, ko motsi Ahmad bai yi ba kuma dai still many manya fararen idon nan nashi a buɗe, jijjiga shi Aiman ya farayi da karfi karfi yana faɗin "Ahmad pls wake up,  ko motsi Ahmad bayyi ba ganin Aiman zai iya illata Ahmad  yadda yake jijjiga shin nan yasa BGS riƙe hannun sa yana girgiza masa alamar ya dai na jijjiga shin, rungume BGS Aiman yayi chikin kuka yace "why, why, chiwon bata kama Ni ba takama Ahmad pls kuche chiwon ya dawo jiki na ya kyale min dan uwa na,ganin Aiman fa ya fita hayyachin surutai kawai yake hakan yasa.

....BGS juyowa ya kalli Aryan,ba tare da yayi magana ba,  chikin sauri Aryan ya juya ya ɗauko allura ya haɗa ba tare da Aiman ya Ankara ba Aryan ya tsira masa alluran nan take yayi shiru difff kamar an ɗauke wuta sai kuma ya sake wa BGS dukkan jikin sa alamun yayi barchi, ɗaukan sa BGS yayi chak ya saɓa sa a kafaɗa ya nufi waje da shi 

Hannu Aryan yasa ya ɗago Ahmad daga kwanchiyar da yake ya zaunar dashi ya sa masa fillo a bayan da ya jingina shi da jikin bango yana kallon face nashi, ban da ido ba abun da ke iya motsi a jikin Ahmad, juyawa Khalid yayi ya bar ɗakin dan zuchiyar sa ta gama karaya dab yake da fashewa da kuka 

Aunty salma Aunty farida Aunty Mardiya hiyana sun fi kowa kuka a ɗakin shi kan shi Abba daure wa kawai yake, jiyake kamar yayi kukan shima ko zai samu sassauchi a zuchiyarsa, Ammi da Ummi sai sharan kwalla suke Aunty amarya kam bata wani damu sosai ba, dan ko kwallin hawaye bata yiba, sosai Aunty Maryam ma ta shiga damuwa dan itama har chikin zuchiyar ta tana son yan uwan ta, su hiyana ne dai bata so, Fahad ma daurewa kawai yake amma shima idon sa ta chika tab da kwalla, Haidar Umar sai kwalla suma suƙe dan gaba ɗaya ƴaƴan  Abba suna matikar kau nar junan su, shiru Yusuf ya zauna dan shi tsabar tashin hankali ko hawayen ya gagara fita

"Hauwa'u ki tattara su gaba ɗaya ku tafi kowa ta tafi ban garen ta kuyi shiru kukan ya isa haka, addu'a zaku masa chewar Abba yayi maganar yana kallon Ummi, jiki ba kwari dukka matan suka fita ya rage mazan

da sallam BGS ya dawo ɗakin kusa da Abba yaje ya zauna suka zubawa Ahmad ido shima dai Ahmad ɗin su yake kallon kamar zai yi magana amma ya kasa, cikin tsawa BGS yace "kai ku mana shiru yayi maganar yana kallon haidar da Umar, nan take suka goge kwallan idon su suka nitsu,

.....Dawo da kallan sa kan Abba BGS yayi kafin yace "Abba yanzu menen abun yi dogon numfashi Abba yaja kafin yafara magana "ina ganin mu fitar da shi waje kawai mu kai shi Us ko UK ko india tun da suna da kwararrun likitochi  "aa Abba dan uwana ya fi karfin yaje wata gasa jinya sai dai ita kasar tazo ta same sa a nan, likitan wani kasa kake son yazo ya du bashi, zanyi waya koma wani irin likitane kake so gobe zai zo, "to ka kira likita daga India dan sunfi kwararrun likitochi chan "ok kawai BGS ya faɗa san nan ya mike ya nufi waje, mikewa Abba ma yayi yana faɗin "Aryan ka kwantar da Ahmad muje ko mu kwalesa ya huta, yana gama faɗin hakan ya nufi waje, juyawa Yusuf da Fahad su kayi suka bi bayan Abba haidar da Umar suka rufa musu baya 

a hankali Aryan ya mai da Ahmad ya kwantar, san nan ya shafa kansa yace "Allah ya baka lfy my bro,  abun mamaki  gani Aryan yayi Ahmad ya lumshe ido a hankali ya buɗe alamar ya ji daɗin addu'ar da Aryan ya masa

.... A sukwane Aryan yace "Ahmad daman kana jin mu, lumsha ido Ahmad ya sake yi san nan ya buɗe alamar eh ina jin ku, a ruɗe Aryan ya zauna gefen sa ya riko hannun sa yana faɗin zaka iya buɗe bakin ka juya ido Ahmad yayi alamar a'a, "ok to shike nan bama sai ka buɗe baki ba tun da kana jin duk abun da nake faɗe,  idan eh haka ne sai ka lumshe min ido idan kuma ba haka bane ka ɗaga min ido sama kaji,? Lumsha ido Ahmad yayi ya buɗe alamar yaji "akoi in da yake maka chiwo ne a jikin ka?  ɗaga ido sama Ahmad yayi alamr aa "zaka chi abin chi? nan ma ɗaga ido sama yayi alamar a'a bazai chiba, wasu zafafan hawaye ne suka fara bin kunchin Aryan, wai yau Ahmad ne ke magana da ido kai duniya abun tsoro, ɗaga ido sama Ahmad yayi alamar Aryan yayi shiru ya dai na kwalla, fika kai Aryan yayi kan goshin Ahmad ya chigaba da kwallar sa, hawayen sa na zuba kan fiskar Ahmad, 
Sai da Aryan yayi kukan sa mai isar sa sannan ya ɗago yana bin Ahmad da kallo,

...hawaye kwanche a chikin idon Ahmad ɗin ga wasu na bin gefe gefen idon sa alamar dai shima kukan yake, girgiza kai Aryan ya shiga yi yana faɗin "No bro No bai kamata kayi kuka ba kaga baka da lfy lunshe ido Ahmad yayi alamar yaji, hannu Aryan yasa ya goge masa hawayen, san nan ya miƙe ya koma saman sofa daƙe chikin ɗakin ya zauna yana kallan Ahmad, shiru sukayi dukkan su har bar chi ya ɗauki Ahmad, ganin yayi barchi ne yasa Aryan mikewa ya fiche daga ɗakin daman ya zauna ne dan bai san ya bar Ahmad shi kaɗai. 


Misalin karfe 9 na dare zaune Aryan yake a bakin katafaren gadon sa yana latsa waya, sanye yake chikin kayan barchi riga da dogon wando Sky Blue masu kyau da tsada, yayi nisa chikin abun da yake a wayar tasa, yaji wani fitinannen kamshin perfume ta kai mai karo a hanchi kan ya ɗago kai, sai yaji tafiya kwas,kwas,kwas, ai bai ma san san da ya saki wani cool murmushi ba tun bata karisa shigowa ɗaƙin ba, 

ba ko sallama diyana ta shigo hannun ta ɗaya rike da cup mai ɗauke da coffee, ɗayan hannun nata kuma rike da jakar da ya bata amatsayin tsaraba,  from head to toe yake kallan ta, 

Sanye take chikin wata dan ƙareriyar lace Blue colour da ratsin fari, ɗinkin riga da sket kayan sun zauna a jikin ta sosai, yau ba ta yi make up sosai ba iya powder ta shafa sai man baki, tayi kyau kamar ita tayi kanta, ga ɗaurin dan ɗaurin ɗan kwali ture kaga tsiya da ta yi,  yau kam ta rufe kan nata, gawani high heel fari da tasa a kafar ta sai wani fitinannen kamshin turaren humra dake tashi a jikin ta  zubawa, a hankali take takawa tana wani rausaya ta kariso chikin ɗakin

.....gaban shi tazo ta duka har lokachin bai dai na kallan ta ba, yama kasa ɗauke idon sa daga kanta  "ina wuni yaya Aryan, wani dogon numfashi ya ja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuchiya, kasa amsa gaisuwar nata ma yayi, jin bai amsa ba yasa ta ɗago kai a hankali, karaf blue eyes nata ya sauka chikin ash eyes nashi da sauri tayi kasa da kanta, 

"yaya Aryan dan Allah ka ansa mana wlh chinyata na min zafi kayan sun matseni sosai ta karisa maganar kamar zatayi kuka,  slowly yasa hannun ya ansa cup ɗin ita kuma ta miƙe, tana faɗin yaya Aryan ga jakar ka buɗe min ta karisa maganar tare da miƙa masa jakar, batare da ya ansa ba yasa ɗayan hannun sa  ya mata nuni da kan drawar gefen gadon alamar ta zauna, ba musu ta zauna ta ajiye jakar a kasa a gefenta

"Bana hanaki kwalliya da daddare ba, yayi maganar yana ɗaure fuska turo dan karamin bakin nan nata tayi a shagwaɓe tace "to ai Aunty farida che tache nayi kwalliya nazo na kawo maka coffee, shiru yayi bai sake magana ba ya ɗago da cup ɗin sai tin ɗan bakin nasa ya fara sha coffee ɗin yana kallan ta,  juyo da kallanta itama tayi kan sa, kallo ɗaya ta masa ta ɗauke idon ta kasan chewar yana kallon ta 

"yaya Aryan me yasa kayi kuka kuma meyasa naga ka rame, a'sukwane ya chire cup ɗin  daga bakin sa ya kara waro manya manyan ashe eyes nashi yana kallan ta, batare da ta kallesa ba ta chigaba da magana "ko ɗazun fa da yaya Ahmad ya fara rashin lfy kowa a palon yayi kuka har da ni, nima nayi amma kai da wan nan mai kama da hiyana da kuma Abba ba kuyi kuka ba to yanzu kuma.....ba shiri ta ja birki bata karisa maganar ba saka makon hannun da Aryan yasa ya rufe mata baki, ɗago ido tayi tana kallansa zaro mata manya manyan ashe eyes nashi yayi ya ɗaure fuska sosai da kakkausar murya yafara magana

Waya koya miki kallon maza? zaro blue eyes nata tayi sosai har sai da Aryan ya zame hannun sa daga bakin ta ba shiri, dan ganin idon nata yayi data zarosu waje kamar ta kara musu haske ne har wani kyalli suke, zuba wa kwayar idon ta ash eyes nashi yayi sosai yana kallan su abun ma mamaki ya bashi, ganin haka yasa diyana ta turo ɗan karamin bakin nan nata tafara magana "ni bana kallan maza ni ba maza bama har mata dukka bana kallon su.

    a fusache Aryan ya miƙe, ganin ya miƙe yasa itama ta miƙe da sauri "Ke ni zaki chewa baki kallon maza, baya baya ta fara jaa tana girgiza kai chikin tsoro, binta yafara yi  har suka kure bango matse ta yayi sosai da jikin bangon, a tsorache tace "Allah yaya Aryan ni bana kallon kowa ma "baki kallon kowa ya akayi ki kasan gaba ɗaya mutanen dake palo lokachin da Ahmad ya faɗi sunyi kuka? ya akayi ki ka san nayi kuka? Ya akayi ki ka san na rame? "Allah yaya Aryan Saboda kana da mahimmanci ne awaje na shiyasa na sani kuma ai kaga kullun ina kawo maka coffee, kuma ai idan nazo kullun ina kallon ka sau ɗaya,  shiru yayi har chikin ranshi ya ji daɗin amsar da ta bashi na chewa yana da mahimmanci awajen ta, "me yasa nake da ma himmanchi awajen ki? yayi maganar yana ƙara matsowa kusa da ita sosai "ai saboda yanzu ka dai na yimin tsawa kuma kana sona baka buguna ka kawo min tsara ba kuma ranar kache nayi kyau, tunani ya shiga yi sosai anya yarinyar nan mutun che kuwa yar karama da ita sai ƙwaƙwalwa yanzu duk waɗan nan abubuwan bata manta da suba ko wama ya faɗa mata ma'anar mahimmanci oho, ganin yayi shiru ne yasa tace "yaya Aryan Allah ni bana kallon kowa pls kayi hakuri kaji, "ok promise me that ba zaki rinƙa kallon kowa ba, da sauri ta ɗago a dai dai goshin ta bakin sa ya sauƙa saboda yayi kusa da ita sosai, wani irin shock yaji daga tsakiyar kansa har izuwa tafin kafar sa da sauri ya ɗan ja da baya, ita kam ko ajikinta bata ma san yayi kissed na goshin ta ba ..

....Yaya Aryan Allah nama alkawarin ba zan kalli kowa ba, batare da yayi magana ba ya wuche ya koma bakin katafaren gadon sa ya zauna, san nan yace "dawo ki zauna muyi magan, a hankali ta tako izuwa kan drawer da ta tashi ta zauna "kin san me nake so dake "aa tafaɗa tana girgiza kai "daga yai idan munje chin abinchi a palo kai bama palo ba ko ina ne,  kar na sake jin kinyi magana da kowa,sai dai idan an tambaye ki abu, kuma idan an tambaye iya abun da aka tambaya iya shi zaki amsa karki kuskura ki ɗaura wani abu kinji, to kawai tace, ɗaukan coffee nashi da ya ajiye yayi ya chigaba da sha 

"yaya Aryan ayya bani wayar ka na buga game, batare da yayi magana ba ya ɗauki wayar ya chire pin ɗin ya miƙa mata, ansa tayi tafara latse latse "ayya yaya Aryan to ai ni banga game ɗin ba "shiga play store ki ɗauko dan ni kam bani da game, da murna a fiskar ta tace to   
Aryan a tunanin sa diyana batasan kan waya ba shiyasa ma bai damu ba ya miƙa mata wayar

"Laaaa yaya Aryan daman hoton mun nan yana nan, a sukwane Aryan ya ɗago ya ansa wayar yana kallon screen ɗin "ke ya akayi ki ka ga hoton nan? yayi maganar yana mai do da idon sa kan face nata, shiru ta danyi kafin tace "kawai naga an rubuta KGA ne a jikin App ɗin shine na shiga "to ai akoi pin awajen ya akayi ki kasan pin ɗin?, "nima fa wlh ban sani ba kawai ni dai hannuna ya daddanna wayar ne shine naga ya buɗe, kara waro ido waje yayi a zuchiyar'sa yana tunani yanzu *kam zargin na ya fara tabbata koda diyana mutun che to tabbas tana da aljanu a kai* "yaya Aryan ka bani wayar mana na ɗauko game ɗin, pita chikin App ɗin yayi ya chanza pin ɗin san nan ya mika mata wayar 

Game har uku ta ɗauko daga play store, super killer mario subway, subway ta shiga ta fara bugawa,  tani nisa chikin buga game ɗin da take, sai taji an fisge wayar da sauri ta bi hannun sa zata kwache wayar dan ita tama manta a dakin yaya Aryan take ita duk tunanin ta tana ɗaki kuma Zahra che ta fisge wayar, tafiya tayi gaba ɗaya ta faɗa kan faffaɗar kirjinsa, dukkan su suka zube kan gadon, kallon face nata sosai Aryan ke yi ita kuma ta runtse ido tana mai da numfashi

      wani irin bakon yanayi Aryan yaji gaba ɗaya jikin sa ya mutu, har wani sanyi yake ji  kamar mai zazzaɓi, da kyar ya iya juyawa da ita a kan kirjinsa,  ya mai da ta kan gadon ya mata runfa da faffadar kirjinsa yana kallon face ɗin ta, sosai taƙara runtse ido tana jiran taji saukar mari, chikin wata iriyar kasa lalliyar murya yace "ke me yasa kika faɗomin jiki? Lips nata sai kerma yake tace "wlh yaya Aryan na manta ne na ɗauka Zahra che ta anshe wayar shiyasa na bi hannun... Bai bari ta karisa maganar ba ya rufe mata baki da hannun 
     sa sauko da kansa yayi ya haɗe goshin su waje guda han chin su na gogan na juna, yayi shiru yana mai da numfashi.

...ko motsin kirki ya kasa saboda wata kasala da ta saukan masa lokachi guda almost 10mnt suna kwanche haka sai da yaji diyana na kokarin suma ne ya ɗago kai da sauri yana kallon ta,  da kyar take numfashi saboda danneta da yayi wan nan ma iya rabin jikin sa ne kawai a kanta, da kyar ya iya miƙewa ya koma gefe ya jingina da jikin kayin gadon ya ɗaga kai sama ya lumshe ido, ita kam diyana ta kasa mikewa dan har lokachin numfashi ta bai dawo dai dai ba

Sauko da kai yayi Slowly ya ware idon sa a kanta tana kwnache tana kallan sama chikin da shewar murya yace "tashi ki kawo jakar naki na buɗe miki ki tafi ɗaki dare yayi, da kyar ta iya mikewa itama ta ɗauko jakar ta miƙa masa ansa yayi yana faɗin "to jeki dressing room na kije wajen ajiye agogo zaki ga wani ɗan karamin a kwati awajen na gold ki ɗauko ki kawo min, a hankali ta nufi dressing room ɗin 

After some mnt

Ta fito rike da wani ɗan karamin a kwati mai kyau sai ɗaukan ido yake tazo ta mika masa,  ansa yana faɗin "to zauna yayi maganar yana nuna mata gefen sa a bakin gadon, zama tayi tana kallan yatsun kafar ta, buɗe ɗan karamin akwatin yayi ya chiro wasu key guda biyu, ya ajiye ɗaya a gefensa yasa ɗayan kuma ya buɗe jakar 

"ɗago to ki kalli abun da ke chikin jakar da kika damu abuɗe maki,  ya karisa maganar yana kallan face ɗinta,  da sauri ta juyo,  idon ta na sauka kan jakar ta mike zubur tasa hannu a baki tana faɗin yaya Aryan.....✍️✍️



💖The Talent Troupe Writer's 💖

1 Duk Karfin Izzata 
2 Gidan Aunty
3 Jini Ɗaya
4 Sarki Sameer
5 Kafita Zakka 
 
Kar kubari abaku lbr love Story's 


More comments like an share



     
💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣8️⃣*


.....da sauri takoma kusa da shi ta zauna "yaya Aryan yanzu wan nan kayan dukka nawane har da kayan make up ɗin, gyaɗa mata kai kawai yayi batare da yayi magana ba, hannu tasa tafara watsa kayan "yaya Aryan to ai baka buɗe ɗayan gefen jakar ba, tayi maganar tana nuna masa ɗayan zip ɗin da ke kulle "zan buɗe miki shi amma ba yanzu ba kuma karki sake chewa na buɗe maki, irin kayan su Zahra ki kache ki ke so to gashi nan shi kuma ɗayan gefen idan lokachi yayi da kai na zan buɗe maki, kinji ko? gyaɗa masa kai kawai tayi alamar taji "ok to kwashe kayan kije ɗaki kinga dare yayi kuma karki kuskura ki bawa wani jakar nan kije ki ɓoyeta, in lokachi yayi zan ansa sai na buɗe maki, "to yaya Aryan dan allah ka dan faɗamin menene a chiki, ɗago ido yayi yana kallanta yayin da itama shi take kallo, ji yayi harshen sa ba zai iya yimata musu ba, "sako ne a chiki ya faɗa yana mai do da kallan'sa kan jakar  "to dan Allah yaya Aryan ni ka buɗe min mana in gani, ta karisa maganar kamar zata yi kuka, "oh my god ke dai wan nan yarinya to shike nan tun da hakan ki ke so, rufe idon ki..

...da murna tasa hannu ta rufe idon ta, tana ta murnushi, ɗaukan ɗayan key ɗin da ya ajiye a gefen sa yayi, yasa ya buɗe jakar, ɗago ido yayi dan yaga shin da gaske ne ta tufe idon ko dai tana kallon sa, dan yasan halin ta  
ganin ta rufe idon ta da gaske ne yasa yayi saurin buɗe jakar ya chire wani kana Box da akayi selling nasu guda 2 ya ɓoye ta bayan sa, san nan ya ɗago ya zuba mata ash eyes na shin nan Sosai yake kallan face nata, ta rufe ido sai murnushi take 

Sauko da idon sa yayi kan wuyar ta, a zuchiyarsa yana faɗin, wan nan yarinya akoi dogon wuya ga wuyar nata a chike, ba ƙaramin kyau wuyar nata ya masa ba jiyake kamar ya sa hannu ya shafa ko zai rage raɗaɗin da zuchiyar sa ke masa a duk lokachin da yake kallon ta, sosai ya kura wa wuyar nata ido, ita kam diyana bata ma san meke faruwa ba sai murmushi take tana jiran yace ta buɗe ido, 

 slowly ya sauko da manya manyan ashe eyes nasan nan zuwa kan kirjinta, kara waro idon nashi waje yayi yana kallon kirjin nata sosai,  chikin zuchiyar sa yana faɗin, i think yarinyar nan ba zata wuche 15 years ba to ya akayi take da manya manya boobs haka, kodai ta wuche hakan ne "ke shekarar ki nawa, batare da ta buɗe ido ba tace "na kusa chika 16 shiru yaɗan yi still dai kallonta yake 

"Yaya Aryan nayi kyau ne yasa kake tambaya ta shekaru na, ai bai san lokachin da murmushi ta kub che mana ba, ita dai bata da wata matsala burinta kawai ache tayi kyau, "yaya Aryan to ba kache komai ba "eh mana my sister kinyi kyau sosai da sosai kuwa kuma ai ke daman kyakkyawa che tun asali, wani haɗadɗen murmushi ta saki, 

Manuniyar yatsan hannun sa,  yasa chikin ramin da dimple nata ya lotsa saboda murmushi da take yana faɗin "nafi son wan nan a gaba ɗaya face naki, "laaaa yaya Aryan to zan baka kyauta, murnushin gefen fuska ya ɗan saki kafin yace "ok to ngd

"yaya Aryan in buɗe ido na? "Eh buɗe, da sauri ta waro idon ta a kan face nashi wani cool murmushi ya sarkar mata wadda shi kan shi bai san yayi ba "yaya Aryan ka buɗe jakar tayi maganar tana mai do da kallon ta kan jakar "eh na buɗe gashi nan da sauri tasa hannu ta fitar da wani ɗan ƙaramin Box mai shagen kyau gwaldin colour sai kyalli yake

Yaya Aryan taya ake buɗe wan nan Box ɗin?, ansan Box ɗin yayi daga hannunta ya buɗe mata san nan ya mika mata,  wani dagareren abun hannun gold ne a chiki mai matikar kyau da tsada an masa kwalliya da duwasu farare masu kyalli ajikin sai ɗaukan ido yake,  anyi rubutu da larabchi a jikin  "yaya Aryan me aka rubuta a nan tayi maganar tana nuna masa rubutun Arabic ɗin, kallan rubutun yayi, kafin yace "sunanki ne ajiki, shiru ta ɗanyi kafin ta sake chewa 

"laaaa yaya Aryan daman kasan sunana, shiru yayi batare da ya sake chewa komai ba "yaya Aryan menene manar Kga ɗin nan ne? naga skoi shi a wayar ka kuma gashi ma an rubuta a jikin abun hannu na "ke nima ban sani ba kwashe kayan nan ki tafi ɗaki dare nayi mayar da abun hannun nan chikin Box nashi ki mai dashi cikin jaka ki bani na kulle jakar "ayya yaya Aryan ke nan ba zan saka abun hannun ba "eh ba zaki saka yanzu ba sai gaba, na bakine ma kawai dan zamu koma London kar na manta na tafi dashi kuma yanzu dan kin dame Ni na buɗe maki ne shiyasa na buɗe "to yaya bari nagama kallon abun dake chiki,shiru yayi ya zuba mata ido kawai yana kallonta

       Ajiye abun hannun tayi a gefe tafara fitar da sauran kayan dake chiki "Wow ta faɗa lokachin da tafitar da wani dankareriyar sarkan gold fito dashi tayi daga cikin gidan sa, sai kyalli yake yana ɗaukar ido 
karawa tayi a wuyar ta, tana faɗin "yaya Aryan dan Allah ka saka min sai kamin hoto tun da  kache ba yanzu zanyi amfani da su ba "ni ban iya saka sarkan mata ba, tsuke fuska tayi ta turo baki kafin tace "to yaya Aryan in kai wa Aunty farida ta ɗaura min, wani dogon numfashi yaja tare da sauke ajiyar zuchiya kafin yace "a'a nunamin yadda ake sawa sai na samiki kuma banche ki faɗawa kowa abun dake cikin jakar nan ba, Allah awan nan karo idan ki ka faɗawa wani sai na miki duka, "Allah yaya Aryan ba zan faɗa ba "ok  to nunamin yadda ake ɗaura wa na ɗaura miki, chiro sarkar tayi daga karawar da tayi a wuyar tafara nuna masa yadda zai sa mata

Ansa yayi yana faɗin "ok to juya na sa miki, juyawa tayi shi kuma ya ɗauko wayar sa ya kunnan video recorder, ya ajiye wayar sai tin su, a hankali ya ɗago hannun sa ya sako mata sarkan ta gaba ya kewayo da hannun sa ya baya yana ko karin ɗaura mata, 

wani irin shock yaji lokachin 
da hannun sa ya taɓa lallau san fatar wuyar ta a'sukwane ya saki sarkan ya faɗa chikin rigar ta ta gaba, da sauri ta juyo tana kallon sa shi ma kallonta yake "yaya Aryan ya kuma ka sake sarkan, da kyar ya iya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi yace "ke ni ban iya ɗaura wa ba, shagwaɓe fuska tayi ta turo baki tana faɗin "kai yaya Aryan nafa nuna maka yadda akeyi dan allah ka ɗaura min, 

dafe kai yayi a zuchiyar'sa yana faɗin, oh my god ni Aryan na shiga uku wan nan yarinyar tana neman ta bugamin kai ni ban san meyasa ma yanzu bana iya daka nata tsawa ba ban san meyasa bana iya mata faɗa ba oh god

Ganin yayi shiru ne yasa tasa hannu ta ɗan bubbuga hannun sa tana faɗin "dan Allah yaya Aryan to ka ɗaura min mana "juyo ta gaba na ɗaura miki sai ki mai dashi ta baya, da sauri ta juyo suna fiskantar juna, tana murmushi "to ina sarkan take yayi maganar yana kallon face nata, hannunta ta ɗago tana kokarin turawa chikin rigar ta dan ta chiro sarkan amma ina rigar ta matse ta sosai, ido kawai Aryan ya zuba mata yana jiran ya ga yadda zata fito da sarkan, 

Abun mamaki sai yaga ta juya masa baya tana faɗin "yaya Aryan zugemin zip ɗin nan ƙasa, bari na fito da sarkan, mamakine ya ƙara bayyana karara akan face nashi yayi shiru yama kasa magana "yaya Aryan dan Allah ka zugemin mana "ke ni ban iya ba ya faɗa yana kawar da kai gefe "to yaya Aryan yadda ake jan na wando haka shima wan nan zaka ja, oh Allah, ya furta kafin yasa hannu a hankali ya zuge mata zip ɗin kasa ba tare da ya kalle ta ba, 

yayi tunanin kafin ta juyo gareshi zata chiro sarkan sai yaga akasin hakan dan kuwa yana zuge mata zip ɗin ta juyo kuma gashi ta zura hannunta a chikin rigar ta wuyar hakan yasa rigar tayi kasa gaba ɗaya rabi da kwatan boobs nata awaje, 

A'sukwane ya kau da kansa daga kallon ta, ita kam ko ajikinta, tunani ya shigayi wan nan shine kaɗan daga illolin rayuwa batare da uwa ba yanzu nasan da agaban ma haifiyar'ta ta taso wlh ba zata yi hakan ba amma In Sha Allah zanyi kokarin naga ya koya mata wasu abubuwan kafin mu koma,  katse masa tunani tayi da chewa "yaya Aryan to mayar min da zip ɗin na chiro sarkan, dawo da kallon sa yayi kanta ta juya masa baya tana jiran ya mai da mata zip ɗin, mamaki ne ya kama shi lokachin da yaga bayan ta tunani ya shigayi *kai anya yarinyar nan bata fi 16 years ba kuwa? ai ni duk ganin da nake mata na ɗauka tana sa bra shiyasa kirjinta suke chika riga sosai, ashe bata sawa, kai yarinya 16 years da manya manyan breast haka wow gaskiyane abun yayi*jin Aryan yayi shiru ne yasa diyana ta ɗan waigo tana faɗin "yaya Aryan ka zugemin mana, "ok kawai yace tare da sa hannu ya zuje mata zip ɗin sama, yana zugewa ta juyo da sauri ta miƙa masa sarkan tana faɗin "gashi nan, ansa yayi ya san ya sarkan ta bayan wuyar ta ya dawo da hannunsa ta gaba ya ɗaura mata da sauri ya zame hannun sa daga jikinta yana kallon face nata...

.....ɗago blue eyes nata tayi tana kallon face nashi "yayi mani kyau yaya Aryan? ta Tambaya tana murmushi "ai daman dan ke akayi dole zai miki kyau duk duniya babu mai irin shi ke kaɗai Company su kayiwa "yaya Aryan kaga fa shima a jikin shi an rubuta Kga, kuma ga sunana ɗin a gefe, " ke dai juyo  na miki hoton  ba ruwan ki da abun da aka rubuta ya karisa maganar tare da ɗauko wayar sa, mamakine ya kama shi lokachin da ya kawo wayar dai dai face nashi "tab ni fa nama manta da ina yi mana video, saving na video yayi san nan ya fita da sauri sauri ya ɗauke ta pic kala 5 san nan yace "kwashe kayan ki maida su chikin jakar dare yayi yanzu Almost 11  yi sauri ki wuche ɗaki


Tattara kayan tayi gaba ɗaya ta mai da zata rufe jakar yayi saurin chewa "bani na rufe kuma ki rufe idon ki, ba musu ta rufe idon ta ɗauko wayan nan Box guda biyu da ya boye a bayan sa yayi, ya mai dasu chikin jakar ya sa key ya rufe zip ɗin gefen ya bar mata na ɗayan gefen wadda ke ɗauke da kaya irin nasu Zahra "to buɗe idon ki,  ki ɗauka ki tafi ɗaki kije kiyi barchi, "to kawai tace san nan ta buɗe ido ta ɗauki jakar ta miƙe tana faɗin "sai da safe yaya Aryan, ba tare da ya amsa mata ba ya miƙe ya kwanta yana kallonta har ta fiche, ajiyar zuchiya ya sauke san nan ya lumshe ido

Da Sallama diyana ta shigo dakin su gaba ɗaya su zahra sunyi barchi wajen drawar kayan su ta nufa ta ajiye jakar hannunta sannan ta chire kayan jikinta tasa na barchi ta haye gado ta ɗauko remote ta gara gudun A.c taja blanket zuwa dai dai wuyar ta ta lumshe blue eyes nata


YOLA 

Da baya baya inna ta shiga wajen bokan nata saman jar kyallen da suka saba zama ta zauna tana faɗin "barka da wan nan lokachin malam "haba habiba ya zaki zauna a nan kishiga chiki mana ina zuwa chewar bokan, da murna inna ta miƙe ta shige ɗan kewayayen wajen, tafara chire kayan jikinta tana gamawa ta haye kan yar katifar chiyawar sa ta kwanta, 

Tana kwanchiya shima ya shigo tsirara ba komai ajikin sa, sai murmushi mugunta yake ya haye kanta ya fara aiki, sosai ya nemeta gaba da baya yauma kamar kullun tare suka sheƙe ayar tasu yana yi tana tayasa, 

Bayan sun kammala ne ya miƙe ya fito wajen tsafin nasa ya saka kayan sa ya zauna kan dutsen daya saba zama 

itama inna ta miƙe ta mai da kayan jikinta ta fito, zaune ta same'sa akan dutsen 
Zama itama tayi kan jar kyallen da suke zama tace "malam ya batun aikin wani dariya mara daɗin ji yayi kafin yace "komai na tafiya dai dai ki kwantar da hankalin ki san nan kuma, ina so ki san ba keka ɗai kike bibiyar rayuwar yaran nan ba akoi wasu, kuma dukkan wayan da ke bibiyar su ba wan da zai iya kunche tsarin jikin su sai Ni. 

.....Ni kaɗai zan iya kunche wa kuma saura kaɗan nagama, ina gama wa zan musu mummunar aiki, wani murmushi inna ta saki kafin tace "yauwa malam ngd sosai, zan iya tafiya? Aa yau baza mu kwana ba ke nan, kinfa san zanyi kewar ki sosai idan kika tafi "to shike nan na fasa tafiya ai nima ba'a son raina nake tafiyar ba zan shiga daga chiki amma na kwanta "a'a habiba ba dai kwanchiya ba ki dai shiga ina zuwa ayi na biyu " to kayi sauri ka shigo nima a matse nake "au daman bai sheki bane? Shine kuma baki fada min ba yayi maganar yana mikewa, muje na baki sai kin koshi in dai wan nan ne ya karisa maganar yana zaro ayabar sa daga chikin wando, hannu inna tasa ta kama ayabar tana dan matsa ta "a'a habiba ba a nan ba mana mushiga daga chiki dan kar nayi baki, "ai malam abun ne ba sauki bana gajiya da tsosar ta

 "nima ai habiba bana gajiya da tsosar min da kike ban ki ache ko wani lokachi tana bakin kiba "to shike nan tun yanzu ka kulle kofa karma wasu su zo sai mushiga chiki daga nan har dare inyi ta tsosa ma "kai habiba iya tsotsa kawai bazan chi ki ba ke nan kike nufi "aa Malam china kam ai ya zama dole ko sau ɗari kake so ma yau kayi na shirya "yauwa yar gari yanzu naji batu bari na rufo kofar,sake masa ayabar inna tayi ya juya ya nufi bakin kogon ya rufo yar kofar zanan ya dawo ya rungumi inna suka shige chiki 


Kano

Babban Dr yazo daga kasar india gaba ɗaya family Abba suna zaune a ɗakin da Ahmad yake sunyi shiru suna jiran suji me Dr Ram zai che 

20mnt Dr Ram ya ɗauka yana duba Ahmad san nan ya ɗago fararen idon sa ya fara  magana chikin harshen turanci "nayi duk wani bin chiken da ya da che nayi amma ni banga wani chuta dake damun sa ba, lfy kalau yake "haba Dr taya zaka che hakan, ya zaka che mana ba abun dake damun sa bayan, gashi nan baya magana baya chin abinchi baya shan ruwa ko motsi bayayi chewar Abba ya karisa maganar chikin bachin rai, hannu Aryan ya ɗora kan kafaɗar Abba yana faɗin "Sorry Abba pls calm down mubi a hankali amma dai dole akoi abun dake damun Ahmad, shidai Bgs ko magana ya kasa yi ya dafe kansa da hannu ya sunkuyar da kan kasa.

chikin tsawa Aiman yace "kai Dr ko ka dubo mana meke damun ɗan uwana wlh ko na ɓaɓɓalla ka a chikin ɗakin nan "haba Aiman ya zaka che masa haka ai bai kamata ba chewar Aunty Maryam, wani mugun kallo ya mata kafin yace "ke idan na sake ina magana kika sa min baki wlh zai na sharara miki mari, gaba ɗaya ido jama'ar ɗakin ya dawo kan Aiman.

"Aiman hauka kake ne Maryam ba yar ka ba che chewar Aunty farida "ke Aunty farida ban yi da ke ba kema, wlh ko ku faɗa min me ke damun dan uwana ko ran kowa ya ɓache, zaro ido waje Abba yayi dan jin maganganun fa Aiman ke yi a fusache  ya mike ya ɗaga hannu zai mari Aiman ɗin, da sauri Bgs ya miƙe ya riƙe hannun Abban da kyar ya iya buɗe baki yace "Abba kayi hakuri ku yiwa Aiman uzuri wlh duk wan nan maganganun da yake baya chikin hayyachi sa bai ma san yana yi ba, Aryan ya ɗora da chewa "Abba kafi kowa sanin shakuwar dake tsakin Aiman da Ahmad, ko ni da aka haife mu tare bai shaku dani kamar yadda ya shaku da Ahmad ba  to ya kamata mu masa uzuri duk abun da zai che kar wanda ya sake tan kashi a chikin ɗakin nan.

Jiki ba kwari Abba ya koma ya zauna dan shi kanshi ya tausaya wa Aiman sosai dan yasan irin shakuwar da su kayi da Ahmad ɗin,

 wani dogon tsaki Aiman yaja chikin tsawa yace "kai wai ba zaka faɗa mana meke damun ɗan uwan mu ba ya karisa maganar yana kallon Dr Ram da idon nan nashi da suka rine su kayi jaa kamar wan da ya sha wani abun, jiki na rawa Dr yace "iya gaskiyan na faɗa muku wlh ba abun da ke damun ɗan uwan ku, a fusache Aiman yayi kansa da nufin ya bugesa, da sauri Aryan ya tare sa, nan fa kokawa ta kaure tsaka nin su da sauri su Ammi gaba ɗayan su matan suka fiche daga ɗakib, dan basu son ganin tashin hankali kan tashin hankali.

      sosai Aryan ya riƙe Aiman, sai naushi Aiman ke kai wa Aryan a baya amma Aryan yaki sakin sa kuma a halin da Aiman ke chiki Aryan ba zai iya bugun saba ko ya masa wani abun, da gudu Yusuf ya kariso wajen ya rike hannun Aiman dukkan biyu dan ya dakata daga bugun Aryan da yake, allura barchi Bgs ya ɗauko ya shammachi Aiman ya masa,  kan kache me barchi ya ɗauke sa wani ajiyar zuchiya Aryan ya sauƙe kafin yace "kamashi Yusuf ka kai shi ɗaki pls "haba yaya Aryan ina ni ina iya ɗaga Aiman yaya nane fa ko ka mantane "to kai ba soja bane? Chewar Abba "aa Abba ai duk da ni sojane ba zan iya ɗaga Aiman ba yafi jiki da zauyi fa tab a'a ya karisa maganar yana zaro ido, tsaki Aryan yaja san nan ya saɓi Aiman a kafaɗar sa yayi waje da shi

Dr yanzu da kache ba wani abun da ke damun sa to me yasa baya magana? Abba ya tambaya yana mai do da kallon sa kan Dr "kwarai ba abun da ke damun sa idan da akoi ai da kun gani a jikin Tv chan lokachin da na sa na ura a jikin sa, shiru sukayi kowa da abun da yake tunani, mikewa Dr Ram yayi yana faɗin "na wuche dan jirgin yamma zan bi, ba wan da ya amsa masa a chikin su dan dukkan su yanzu basu da bakin magana, fichewa Dr Ram yayi ya daga ɗakin

Abba yanzu mene abun yi kuma Bgs ya tambaya yana juyo da kallonsa izu kan Abba "musake kiran wani likitan daga wata kasan kuma muji me zai che "to kawai Bgs yace san nan ya miƙe ya fita bin bayan sa Khalid da Yusuf su kayi, Haidar da Umar ma a tare suka fice, suka bar Abba shi kaɗai 

almost 10 mnt Abba na zaune shiru Ahmad kuma yana ta shararan barchin sa, jiki ba kwari Abba ma ya miƙe ya fito ya nufi ɗakin sa 



                  💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'💖

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
     👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
       by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
       by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
      by(xeemat....love)

*4, JINI DAYA*
      by(mrs bbk)

*5,YA FITA ZAKKA*
       by(mum Sayyid)
            
*💫STAR LADY💫*29

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣9️⃣*


Zaune yamma tan Ammi suke a palon sama na ɓangaren Ammi, suna ta hira hiyana na duba takar dun ta na boko diyana na kallon awayar Zahra amrat na karatun qur'ani, Zahra da lamrat suna kallo a makeken Tv dake manne a bango,
                         da sallama yaya Khalid ya shigo palon, har suna haɗe baki wajen amsa masa sallamar kariso wa chiki yayi ya zauna saman sofa mai zaman mutun 1 murya kasa kasa hiyana tace "ina wuni yaya Khalid ya mai jiki, kakalo murmushi dole yayi kafin ya amsa mata da "lfy sister ya shirye shiryen koma wa makaranta ina fatan kungama shiri, hiyana zatayi magana Zahra ta rigata "ina wuni yaya Khalid, dawo da kallan sa kan Zahra yayi kafin ya amsa da "lfy sis love ykk, sunkuyar da kai kasa Zahra tayi dan jin sunan da ya kirata yau ta tashi daga Auta ta koma sis love.

Yaya Khalid ya mai jiki chewar diyana "jiki da sauki sister ya aikin kai coffee, sai lokachin diyana ta ɗauke blue eyes nata daga kan wayar Zahra ta mai da kallonta izu kan yaya Khalid "hmmm ai inayi ku jiyama na kai masa kuma.. bata karisa maganar ba tayi shiru kasan chewar ta tuna abun da yaya Aryan yace mata akan idan ta kuskura ta faɗa wa wani abun da baa tambaye taba to sai ya ɓallata,

 ganin tayi shiru ta kasa karisa maganar yasa yaya Khalid ɗan sakin murnushin kaɗan dan yasan Aryan ne ya mata gargaɗi kuma hakan ba karamin daɗi ya masa ba dan diyana tana sakin layi dayawa

"To ku shirya fa gobe zaku koma school kunji daman abun da nazo faɗa muku kenan yana kai karshen maganar ya miƙa ya nufi hanyar fita, har suna haɗe baki wajen chewa to, 

Abangaren Ahmad kuwa

Zaune Aryan yake a gefen gadon da Ahmad ke kwanche yana kallon face nashi "bro zaka chi wani abune, ɗaga ido sama Ahmad yayi alamar a'a "why bro, why ba zaka chi abinchi ba tunfa jiya da rana baka chi komai ba haba, ɗaga ido sama Ahmad ya kuma yi alamar aa ba zai Chi komai ba, Aryan zai sake magana sai ga Bgs ya shigo tare da wani likita 
        zama Bgs yayi kusa da Aryan Dr kuma ya fara kokarin sakawa Ahmad ruwa dan ta taimaka masa tun da baya chin komai, 

"Yallaboi ko dai zaku gwada maganin gida ne tun da na asibiti yaki chewar Dr yayi Maganar dai dai lokachin da yake ɗaure hannun Ahmad dan neman jijiya, 
wani dogon tsaki Bgs yaja kafin yace "Allah ya kyauta abawa ɗan uwana wan nan dattin, zan nemo kwararrun likitochi daga kasa da ban da ban suzo su du bamin shi, "Allah ya baka hakuri sir, Chewar Dr ya karisa maganar dai dai lokachin da ya gama sawa Ahmad ruwan, ya tattara kayan aikin sa ya nufi waje

Kallon Bgs Aryan kafin yace "bro wai yanzu menene abun yi, shiri Bgs ya ɗan yi kafin yace "ban yi tunani a kai ba amma muje zuwa anjima dole musan abun yi ya karisa maganar yana mikewa, mikewa Aryan ma yayi suka fita tare

Misalin karfe 2 na rana gaba ɗaya family sun haɗu a palo dan chin abinchin rana ban da Bgs Aiman Fahad da kuma Ahmad, shiru palon ba abun da zakaji sai karan spoons

"My daughter ya kama ki koma gidan ki yau kinji, chewar Abba yayi maganar yana kallon Aunty farida, Mardiya salma Maryam dukka ku shirya kuma kuwuche gidan mazajen ku, "Abba daman gobe in Allah ya kai mu zan koma nariga na faɗawa dady'n  junior ma chewar Aunty farida, chikin dashe war murya wadda da kaji kasan tasha kuka har ta koshi Aunty salma tace "Abba pls ka barni na kara koda 2dys ne sai mugani y jikin Ahmad ɗin zai kasanche "a'a Salma ban yar da ba gobe idan Allah y kaimu kafin karfe 1 kowache ta koma gidan mijin ta, wai ma idan kuka zauna kara masa lfy zakuyi ne? Akoi waya duk abun da ake chiki zan sanar daku ai addu'a kawai yanzu ya ke bukata awajen ku bawai kubar gidan mazajen ku, kuzo ku zauna kusa da shiba,
Har suna haɗa baki wajen chewa to Abba Allah ya bashi lfy, gaba ɗaya palon suka amsa da amin
                      shiru palon ya sakeyi ba mai magana kowa kawai tsakuran abin chin yake dan kamar magani suke jin abinchin ba dan daɗi suke chiba sai dan kar yinwa ta musu illatasu, 

"My daughter kayan nan sun miki kyau Chewar Abba yayi maganar yana kallon diyana, daman kamar jira take tafara surutu "Abba ai yaya Aryan ne ya bani ji, daman tare ya kawo mana da su Zahra shine ya kulle nawa chikin jaka, sai jiya ya buɗe min kuma Abba kaga wata dan kareriyar sar...bata karisar da maganar ba tayi shiru kasan chewar ta tuna yaya Aryan yace idan ta faɗawa wani sai daketa, jin bata karisar da maganar ba yasa Aryan sauke wata nauyayyar Ajiyar zuchiya wadda yasa Abba ɗagowa ya kallesa, kuma sai yanzu ya fahimci dalilin da yasa diyana ta dakata da maganar bata karisa ba.

 saboda jin baki irin na Abba sai yace

"My daughter ya kika dakata da maganar, a sukwane Aryan ya ɗago yana kallon Abba, harara wasa Abba ya wurga masa, da sauri ya mai da kai kasa yana ɗan murnushi dan ya gano abun da Abba ke shirin yi, "babu komai Abba kawai dai na manta me zan faɗane diyana ta faɗa tana satar kallon yaya Aryan, 

mamakine ya kama Abba daman ya tambaye tane dan yaji shin diyana tayi hankali ne ko kuma dai da saura, abun da ya bashi mamaki kuma shine yau diyana che da karya abun da bata taɓayi ba tab lallai na yar da yanzu kam diyana na Son Aryan daman zargi kawai nake Amma bari dai na sake gwada su.

"My daughter ina malamin makaranta kun nan daya taɓa chewa yana Son kin nan?
Ɗaure fuska diyana tayi ta ɓata rai ta turo baki ta fara magana "to ai ni Abba bana son shi soja nake so kuma ai ni tun ranan ma ban sake ganin sa ba wata kila ma ya bar makarantar, kila kuma mutuwa yayi waya sanin masa, gaba ɗaya mutanen palon sai da sukayi mamakin ɗaure fuskantar da diyana tayi har shi kanshi Aryan dan tun da suke da ita basu taɓa ganin ta ɗaure fuska ko ta ɓata rai ba ita ko dukan ta akayi tana gama kuka zata koma dariya

"My diyana menene abun ɗaure fuska kuma? Ai ba wan da zai miki dole mijin da ki ke so shi zamu baki chewar Aunty farida "to ai Aunty farida ni bama wan da nake So sai yaya Khalid a sukwane gaba ɗaya jama'ar palon suka ɗago ido suna kallon ta musamman ma Aryan da atake idon nasa suka sauya zuwa jaa saboda kishi, itakam diyana bata ma san sunayi ba ta chigaba da magana "yaya Khalid yaya Yusuf yaya Aryan yaya Bello Aunty Zahra Aunty mardiya Aunty salma Abba Ammi Ummi Aunty amarya hiyana lamrat da amrat da ke Aunty farida sai Bappa na da Inna ta, ku kaɗai kawai nake so aduniya, wani ajiyar zuchiya Aryan ya saki, ya duƙar da kai ya ɗauki wayar sa dake gefen hannunsa kan table ɗin, yashiga latsawa

"Hiyana karfe 3 dai dai ki dama fura ki ka womin fada Chewar Abba yana magana faɗin hakan ya miƙe ya nufi waje, 
      Nmiƙewa Aryan Khalid Yusuf sukayi a tare suka fice daga palon, "haidar muje mu duba jikin yaya Ahmad ko Chewar Umar "eh ya kamata kam ya kai karshen maganar tare ta mikewa, mikewa haidar ɗin ma yayi suka nufi waje, a tare Aunty Salma da Aunty mardiya ma suka miƙe suka fice daga palon, Aunty maryam Aunty amarya suma tare suna mike suka fita, Ummi da Ammi kuwa betroom ɗin Abba suka miƙe suka shiga, palon ya rage daga aunty Farida sai su diyana.

"My diyana daga yau idan kinje ɗakin yaya Aryan karki sake daɗewa kina jina koh? Chewar Aunty farida, "to Aunty farida ai shi yake chewa in zauna muyi magana ta karisa maganar tana turo ɗan karamin bakin nan nata 

"eh ko yache ki zauna kiche kina jin barchi sosai,  jiya fa har karfe 10 ina ɗakin ku ina jiran dawo warki, amma baki da wo ba, kamar zanzo na kiraki sai kuma nache bari na bari da safe sai na miki faɗa, "to Aunty farida ba ke ki kache idan naje ɗakin na rinƙa koya masa surutu ba tun da baya magana kuma kinche ni bazai bugeni ba ko na masa surutun  "eh daaa ni nache hakan amma yanzu na fasa saboda idan namiji da mace suka keɓe to na ukun su sheɗan ne,duk da zan iya shedar kanne na a ko ina, amma dai daga yau kina kai masa coffee ɗin ki dawo kinji, "to Aunty farida kawai na daiii na kai masa coffee ɗin mana tun da hakane "aa karki dai na kai masa ki chigaba da kai wa kinji amma dai da kin kai sai ki dawo, "to kawai diyana tace tare da miƙewa ta nufi hanyar fita "kutashi muje Zahra, chewar Aunty farida, gaba ɗayan su, suka mikewa a tare suka nufi waje,


Karfe 3:5

Da sallama hiyana ta shigo fada hannun ta riƙe da kyakkyawar kwarya  ta rufe shi da pai pai,  ta sanya zumbulele hijabi har kasa ajikin ta fari tas, fiskar ta sai kyalli take bawani make up da tayi asalin kayan tane kawai,ga ɗan bakin nan nata pink sosai kamar tasa jambaki, geranta kuwa kamar tayi caving, idan mutun yaga hiyana zai rantse da Allah tayi make up, amma haka fuskar ta yake,halittar Allah ne duk da kwayar idon ta Blue ne amma idon nata farine tas manya manya kamar ball, kuma idan ta kalleka kache tasa kwalli amma ba ta saba haka idon yake gata da bakin kwanche cin gashi mai tsantsi a gaban goshinta ga wani baki haɗadɗen saje a kwanche a gefen kumatun ta dogon siririn hanchin nan nata kuwa baa magana har baka yake, duk lokachin da tayi murmushi sai wani haɗaɗɗen dimple irin na Bgs ya lotsa, ga hakoranta farare tas sai wani ɗan siririn wushirya a tsakiyan hakoranta na sama

  a hankali take takawa kamar mahauniya, gaban kujerar Abba taje ta duƙa kasa ta, dukar da kai chikin ladabi da girmama wa tace "barka da hutawa Abba, wani murmushi Abba ya saki dan shi har chikin ran shi yana kaunar hiyana sosai akoi ta da ladabi da girmama na gaba da ita ga sanyin hali bata son hayaniya son addini ga sun katun boko da arabic dukka,

Da fara'a Abba ya amsa mata, san nan ta juyo kasa kasa ta kallin in da Bgs ke zaune tace "ina wuni yaya prince, bai amsa ba kuma bai ko kalli in da take ba saima latsa wayar sa da yake,chikin kwanchiyar hankali 
            Hiyana bata damu da rashin amsa gaisuwar nata da Bgs yayi ba,  dan in da sabo sun saba da halin sa, "Abba ga furan ta faɗa tare da ɗago kai ta miƙawa Abba kwaryan dake hannun ta, 
Ansa Abba yayi zai yi magana Bgs ya mike yana faɗin "Abba zanje ɗaki sai da daddare, "aa Safras dawo ka zauna ai ban sallame kaba,  ba don yaso ba hakan ba ya koma ya zauna dan ba yadda zai yi  da Abba ne kuma ba zai iya yiwa Abban musu ba
                     dawo da kallon sa Abba yayi kan hiyana dake duƙe kanta na kallon kasa

"My daughter jeki kawo wa yayan ki nashi furan kinji, to kawai hiyana tace san nan ta miƙe da sauri ta nufi waje 

"Abba nifa bazan sha wan nan abin ba Chewar Bgs ɗin ya faɗa yana yamutsa fuska kamar wadda yaga kashi,  "Allah sai ka sha, na dai faɗama ni ba santin furar bane ya jani har nabi Ammin ku Yola na kasa samun kwanchiyar hankali sai da na Aure ta, kuma ita ta koyamin sha dan nima da bana sha ɗin, "to Abba ai kai kache ba ni ba ni kam bana so kyama yake bani "koma me yake baka Allah sai ka sha na dai faɗama ka, kasani ma ko daga sha.... Sai kuma Abba yayi shiru bai karisa maganar ba, dan yasan in ya karisa to wlh ko ya zai yi Bgs ba zai sha furar ba,  shi daman Bgs ba wani sauraron maganar Abba yake ba kasan chewar yasa blooth a kunne ɗaya, 

Da sallama hiyana ta dawo fada hannun ta riƙe da kwayar nono da ta damawa Bgs, har gaban sa tazo ta duƙa chikin ladabi da girmamawa tace "yaya prince gashi nan, wani dogon tsaki yaja chikin tsawa yace "dole sai na ansa ne bazaki ajiye a kasa ba, 

"mikomin nan my daughter Abba ya faɗa yana miƙa mata ɗayan hannunsa joyowa tayi wajen Abba a hankali ta miƙa masa kwaryan muryan ta har rawa yeke saboda tsoro tace "Abba zan iya tafiya, "aa my daughter zoki zauna a kujeran nan kema muyi hiran dake yayi maganar yana nuna mata kujerar kusa da shi da ido.
Ba musu ta miƙe ta koma saman kujerar ta zauna ta sunkuyar da kanta kasa, 

miƙawa Bgs kwayar nono Abba yayi yana faɗin "ansa kasha idan nima bazaka ansa a hannuna ba sai naji, rai a bace Bgs yasa hannu ya ansa kwaryar,batare daya kalli Abban ba,   
              ajiye wayar sa a gefe yayi,   yasa hannu yachire pai pai da aka rufe kwaryar, kara ɓata fuska yayi lokachin da green eyes nashi yayi arba da damammiyar nono, 
 yaji fura ga kwakwa da dabino,amma duk da haka Bgs sai ɓata fuska yake, a hankali ya ɗauki ludayin ya ɗebi nono ya kai baki sa sai wani tsuke hanchi yake wai dan kar yaji warin nonon. 

....Duk abun da ya keyi Abba na kallonsa,  a chikin zuchiya sa yana faɗin ai yau sai kasha nonon nan.

a sukwane Bgs yayi wurgi da kwaryar nono ya miƙe da sauri kafin ya kai bakin kofar fada ma ya fara kwarara amai,dukawa yayi kasa,kawai ya chigaba da Aman, 

 da sauri hiyana ta mike jiki na bari a zuchiyar ta tana faɗin, nashiga uku wayyo Allah yanzu shike nan na sashi yin amai nasan sai ya hukun tani.

Ajiye kwaryar nono dake hannun sa Abba yayi ya miƙe ya nufi Bgs dake duƙe yana ta kwarara amai kamar zai amayar da kayan chikinsa, dafa kafaɗarsa Abba yayi ta baya yana faɗin "sorry, my Son,
     sosai bgs yayi amai dan sai da idon sa suka sauya sukayi jaa saboda wahala "my daughter bani ruwa a freij Chewar Abba, chikin tsawa Bgs yace "bana so Abba banson duk wani abu da yaran nan zasu taɓa da hannun su, kyamar su nake ji Abba shiyasa nache maka ni bazan sha ba, shiru Abba ya ɗan yi kafin yace "to me tama ka da kake kyamar ta, "Abba ta taɓa zubamin jin... Sai kuma ya dakata yana yamutsa fuska "ok kawai Abba yace san nan ya wuche ya ɗauko masa ruwan da kansa ya kawo masa
 
Chikin tsawa Bgs ya kuma chewa Abba kace ta bar ɗakin nan ban son ganin ta, tun Abba bai yi magana ba hiyana ta fita da gudu tana kuka, shiru Abba yayi yana tunanin me yasa Bgs ya tsani hiyana haka har zai che baya son ganin ta

Kuskure baki Bgs yayi san nan ya miƙe ya nufi hanyar fita, ido kawai Abba ya zuba masa har ya fice daga fadan, Ajiyar zuchiya mai nauyi Abba ya sauke kafin yace "Allah ya shiryamin Safar ai ko me ta maka bai kamata ka tsane ta haka ba, yarinya bai war Allah, marainiya, bani da wani burin da ya wuche a che yau ka auri mace irinta shiyasa nake kokarin haɗa ku, Amma tun da hakan bazata yiwuba dole na samo maka wata matar dan tun da kafara furta ka tsaneta nasan da iya gaskiyar ka ka tsane ta, kuma idan nache zan haɗaku tofa ni da kaina zan kashe maraini yar Allah, Ya Allah ka sassautawa Safras wan nan zuchiyar tasa,  yana kai karshen maganar ya juya ya koma kan kujeran sa, ya zauna, ya ɗauko waya ya kira masu aiki akan suzo su goge amai da Bgs yayi da kuma nonon da ya zubar, 


Ƙarfe 9:10 pm agogon Nigeria ta buga


Taku take ɗai, ɗai, kamar wata mahauniya, sanye take da wata haɗaɗɗiyar doguwar riga abaya pink colour, ta yafa mayafin rigar a kanta, yau dai batayi kwalliya ba, mai kawai ta shafa sai ɗan man baki da tasa a bakinta,fuskan ta sai kyalli take, tasa high heel pink tana rike da ɗan karamin plate mai ɗauke da cup, san nan ta rufe cup ɗin ma da wani ɗan ƙaramin plate mai shegen kyau, ta nufi part ɗin Aryan 

ko sallama babu ta faɗa chikin palon kasa kai tsaye ta haye sama stair ɗin ta shige palon sama nan ma ba ko sallama ta shige, kai tsaye betroom ɗin sa ta shege, babu kowa a chiki, table ɗin tsakiyar ɗakin ta nufa ta ajiye cup ɗin, ta juya da sauri dan gargaɗin da Aunty farida ta mata akan karta daɗe.

Dai dai zata fita taji an buɗe kofar toile ɗin, da sauri ta wai go karaf idon ta suka sauka kanshi ɗaure yake da towel a kugun sa.

     ga jikin sa a jike da alama wanka yayi, wani kara ta saki ganin yadda kiran jikin sa yake afili,  kafin yaya Aryan ya juyo tayi waje, da gudu, a sukwane ya bi bayan ta, 

saboda high heel dake kafarta bazai bari tayi wani gudu sosai ba, a dai dai zata fita palon sama ya damko kugunta ta baya, sama ya ɗaga ta da hannu ɗaya ya juya da ita cikin ɗakin, ihu diyana keyi, tana faɗin "yau kam na shiga uku yaya Aryan dan Allah kayi hakuri wlh na rantse maka bansa zaka fito ba kaya bane da bazan gan ka ba kuma ai ni, ban ganka sosai ba, shidai ko sannu bai che mata ba saman katafaren gadon sa yayi kurgi da ita san nan ya koma ya rufe kofar ɗakin ya zare makullin ya nufi dressing room nashi,

 shiru diyana ta kwanta tana kallon sama kasa kasa ta fara magana "yau kuma aljanun mugun tan yaya Aryan ne ya dawo ko?, to ni me ma na masa shiru ta ɗanyi kamar mai tunani sai kuma ta chigaba da magana "kai lallai yaya Aryan ashe haka hannun shin nan yake kato kamar chinyar lamrat, kut lallai yana da nama sosai amma kuma shine yake saka riga ya ɓoye  wlh in ni ne shi bazan ɓoye ba ai hannu mai nama sosai ɗin yafi kyan gani,  bari ya fito idan bai dake ni ba zan che masa ya faɗamin me yake chine hannunsa tayi nama dayawa haka nima inrinƙa chi ko nawa zaiyi, jin motsin shine yasa ta miƙe zaune tana zare ido

Fito wa yayi sanye chikin kayan barchi mai kyau da tsada gaban morrow ya tsaya yana gyara gashin kansa, Almost 10mnt ya ɗauka a gaban mirrow san nan ya juya ya nufi saman sofa ya zauna, duk abun da yake diyana na kallonsa ta wutsiyar ido amma bata bari ya kamata tana kallon sa ba duk da chewa shi ɗin ma duk abun da yake idon sa na kanta.

A hankali ta zuro kafafunta kasa san nan ta sauko daga gadon ta nufi inda yake, gaban sofar da yake zaune,tazoe ta sugun na, Murya na rawa tace "yaya Aryan dan Allah kayi hakuri kaji, 
     "laifin me ki ka min da kike bani hakuri, da sauri ta ɗago kai, "laaaaa yaya Aryan da gaske ban maka laifi ba, kallonta kawai yake dan yanzu tama dai na bashi mamaki, "yaya Aryan in tafi ɗaki ta Tambaya tana kallon face nashi yayin da shima ita yake kallo "a'a tashi ki kawomin coffee din kizo ki zauna muyi hira "aa yaya Aryan Aunty farida tace na daina daɗe wa a dakin ka "me yasa zaki dai na dadewa a dakin nawa, dariya diyana tayi kafin tace "Aunty farida tace idan namijin da mace suka keɓe to wai na ukun su sheɗan ne, a sukwane ne Aryan ya kara waro idon sa waje yana kallonta,  ganin ita ko ajikin tane ma yasa yace "ok to dauko coffee din ki kawomin sai kizo ki buga game kaɗan da wayata kafin ki koma ɗakin na ku, da sauri ta nufi table din tana murna ta ɗauko masa coffee ta kawo masa, ya ansa ya mika mata wayar sa shi kuma, gefensa ta koma ta zauna tana latsa wayar.

"Yaya Aryan kasan me, batare da tajira amsar sa ba ta chigaba da magana, Allah ko kwanan nan ina tunanin yaya bello sosai ina kewar sa

, wani tarine ya sarke sa coffee din ta haura masa kai sosai yake tarin,  asukwane ya ajiye cup ɗin coffee ɗin ya dafe kansa da hannu ɗaya yana tari,
                 da sauri diyana ta ajiye wayar ta nufi freij ta ɗauko masa ruwa, ta dawo ta mika masa, bai ansa ruwan ba sai yasa hannu ya damko wuyar ta ya fisko ta da karfi ta faɗa kan faffadar kirjinsa, sosai yake tari ya kasa magana, ita kuwa da sauri ta ɗago kai daga kirjin nashi, jin yadda yake tari, chikin tsoro tace "yaya Aryan ka sakeni in ɗauko maka ruwa dan Allah, da kyar ya iya faɗin "babu ruwan ki da ni ki bari tarin ya kashe ni "dan Allah yaya Aryan kayi hakuri Allah bana son ganin ka kana tarin kaji pls, ta karisa maganar kamar zatayi kuka, "aa ba ruwan ki dani nache maki koh "hannu diyana tasa ta toshe masa baki tana girgiza tana faɗin "dan Allah yaya Aryan ka daina faɗin haka mana wlh akoi ruwana da kai kuma har da tsaki na, hannunta ya chire daga bakin sa, chikin dashewar murya saboda tarin da yayi, yace "tashi min ajiki kuma ki fitamin a ɗaki karki sake zuwa, yayi maganar in a serious matter, "yaya Aryan me na maka to?  "Ban sani ba ki tashi ki fita nace, yayi maganar da ɗan karfi

Nan take diyana tafara hawaye tana faɗin "yaya Aryan to dan allah ka faɗamin me nayi maka da kache kar na kara kawo maka coffee, kuma ai nasan kana son coffee din, wani irn raɗaɗi yaji a zuchiyar sa saboda kukan da take, slowly yasa hannu ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna runtse ido tayi ganin yadda yake kallonta, calmly ya fara magana "me yasa kike kuka kuma?, Chikin shesshekar kuka tace "to ba kai ne ba kaki ka faɗamin me na maka, "ya isa to kiyi shiru baki min ko mai ba kinji, da sauri ta buɗe idonta tana kokarin tashi daga jikin nashi kara firgota yayi ta dawo kirjinsa har sai da  kanta ya bugi gemunsa.

...ɗago kai tayi suna fiskantar juna pink lips nata har kerma suke, zata yi magana, yayi sauri ɗora yatsan sa a kan lips nata yana girgiza Mata kai, sauko da kansa yayi ya haɗe fuskokin su yana kallonta,Wani irin farin chiki da nitsuwa ya keji tana ratsa zuchiyar sa, 
             lunshe ido tayi dan ba zata iya haɗa ido da shiba, goga hanchin sa ya fara yi a jikin nata hanchin, kasa kasa yace " menene tsakanin ki da Bello?, da sauri ta buɗe ido tana faɗin "yaya na ne kuma shine idan Inna ta hana mu abin chi yake zuwa ya karɓo mana wajen Adda hasana, 

"shike nan alakar dake tsakanin ku, "eh shike nan "to amma me yasa ki ka che kina kewar shi? "To ai yaya Aryan kaga yana da kirkine kuma idan na samu kuɗi zan saya masa mota da gida dan shima ya dawo birni, "to idan Abba yace zai Aura miki shifa? dariya diyana tayi kafin tace "nifa idan ba soja ba to bazan yi aure ba soja kawai bake so.

Wani dogon nunfashi Aryan ya ja tare da sauke ajiyar zuchiya kafin ya sake ta "tashi ki tafi ɗaki to tun da Aunty farida tace karki daɗe, da sauri ta miƙe har tana kokarin faɗuwa,key din ɗakin ya miƙa mata, 
        Ansa tayi,  ta nufi bakin kofar tasa key ɗin ta buɗe kofar ta fice da sauri, miƙewa shima yayi ya nufi kan katafaren gadon sa ya kwanta ya lumshe ido yana mai da numfashi, 

Washe gari misalin 9 na safe zaune suke a palon Abba kamar yadda suka saba dan yin breakfast. 

Ammi  ta dubi diyana tace "ke diyana jeki ɗauki abinchin babban yayan ku a kichin ki kai masa, a sukwane Aryan ya ɗago dan yasan halin diyana yana son ya hanata zuwa sai dai kuma bai san surutan Aunty amarya dan yasan yana hana diyana zuwa sai Aunty amarya ta sa shi a gaba da tambaya, meke tsakanin su.

Da sauri diyana ta mike Abba na kokarin ya dakatar da ita amma ina har ta fice, kichin ta nufa ta ɗauki abinchin nashi already an gama shirya masa fitowa tayi ta nufi part nashi.

Bb ko Sallama ta faɗa palon babu kowa kai tsaye ta haye stair ɗin ta shiga palon saman nan ma babu kowa kofar da ta gani chikin palon ta nufa ba ko sallama ta shiga,

 tsaye yake gaban mirrow yana gyara gashin kansa sanye yake chikin Black jeans da t-shirt blue, bakarin kyau kayan suka masa ba,kamar dan shi akayi su,   jin an buɗe kofar ɗakin yasa ya zubawa kofar green eyes nashi ta chikin mirrow, ganin diyana che yasa ya ɗaure fuskar nan kamar wani zaki ya kau da kallonsa daga kanta

 "Kai mai kama da hiyana ga abinchin ka nan anche na kawo maka, a sukwane Bgs ya juya dan jin sunar da ta kirashi kuma har da che masa kai, chikin tsawa yace "get out, diyana ko tsoro tsawar ma bata jiba ta ɗan ja tsaki kafin tace "dan ka samu ma na kawo maka abinchi wlh ba dan Ammi ba bazan.... Bata karisa maganar ba kamar wata walkiya ta gefar da kwandon abinchin tayi waje a guje, da gudun gaske Bgs yabi bayan ta sai huchi yake

To masu karatu sai mun haɗu ranar Monday idan Allah ya kai mu,  ina masoyan diyana? tofa yau masoyiyar ku ta taɓo gidan rina ato ku tanaji ruwan zafi gasa mata jiki idan ma ta saura da ranta kenan


                  💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'💖

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
     👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
       by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
       by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
      by(xeemat....love)

*4, JINI DAYA*
      by(mrs bbk)





More comments an like pls
 


*💫STAR LADY💫*30

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 3️⃣0️⃣*


Gudu take kamar zata tashi sama har tsallake stari uku take ta tana na huɗu batare da ta sani ba, a dai dai tsakiyar palon kasa tayi karo da Aryan baya baya tayi zata faɗi, yayi sauri rikota yana faɗin "ai daman na san za'ayi hakan shiyasa na biyo bayan ki me ke faruwa? Bai gama rufe baki ha yaga Bgs na saukowa a guje sai wani huchi yake, a sukwane ya saki diyana yace "ki kudu sister kar ki tsaya ko ina sai bayan Abba, ai diyana bata jira taji me Aryan zai cheba dan yana sakin ta ta kwasa a ɗari tayi waje.

Azuchiye Bgs ya sauko ya nufi hanyar fita da sauri Aryan yasha gaban sa yana faɗin haba bro lfy? Hannu yasa ya hankaɗe Aryan gefe ya nufi kofar fita, A zafafe Aryan ya saƙe tare masa gaba, chikin tsawa Bgs yace "Aryan ka bani hanya tun ban illataka ba "haba Bgs pls kayi hakuri mu koma chiki, wani naushi Bgs ya kai wa, Aryan a fiska, da sauri Aryan ya tare yana faɗin "aa bro ba dai yanzu ba gaskiya, a zuchiye Bgs yasa ɗayan hannu sa ya damki wuyar Aryan ya ɗa gashi sama yayi wurgi dashi gefe guda, ya juya ya nufi hanyar fita da gudu Haidar da Umar daƙe tsaye a bakin kofar palon wadda kusan tare daman suka shigo da Aryan, suka juya suka bar part ɗin gaba ɗaya.
                        Tattaro dukka sauran karfin sa Aryan yayi ya miƙe ya saƙe tarewa Bgs gaba, "Aryan zan illata wlh idan baka barni na bugi yarinyar nan ba "haka na keso  daman kafara illatani kafin ka illata ta, dun kule hannu Bgs yayi ya sake kai wa Aryan bugu a firji wadda sai da yasa Aryan tan gal tan gal kamar zai faɗi, amma abun ku da soja, chikin zafin nama ya kame jikinsa chikin bachin rai ya kaiwa Bgs duka a wuya da karfi, a fusache Bgs ya ɗaga sama yayi wurgi dashi a tsakiyar palon chikin zafin nama ya nufi hanyar fita..

...har ya kai bakin kofar palon zai fita sai kuma ya ja birki da sauri ya juyo, gani ko motsi Aryan ba yayine yasa Bgs kariso wa wajen daya ke kwanche da sauri, 
                         Duƙawa yayi yasa hannun sa a dai dai sai tin kofar hanchin Aryan yana faɗin "my blood kar kamin hakan, hannu Aryan yasa ya chapko hannun Bgs tare da waro ash eyes nashi kan face ɗin Bgs ɗin, dogon tsaki Bgs yana kafin yace "me hakan ɗin? " To ai bani da wani zaɓi na da katar da kai ne sai hakan ɗin, miƙewa Bgs yayi san man ya ɗuƙa ya ɗauki Aryan chak ya saɓasa a kafaɗar sa yanufi stair ɗin dashi 
         "Amma Aryan baka kyau ta min ba "me kuma na maka? " Da ka hanani bugun yarinyar nan mana "au to kai daman so kake na barka kayita bugun yaya mutane, kuma kasan idan kache zaka bugi yarinyar nan a yadda kake chikin fushin nan, tofa zaka iya kasheta "to ta mutu mana menene amfanin ta daman? ai  inaga wlh watara na idan ban kashe enamiece nawa ba kai zaka mutu a shiga faɗar da ba ruwan ka, tsaki Aryan yaza dai dai lokachin Bgs ke kwatar dashi kan katafaren gadon sa
      
"Wlh Bgs baka da kirki ko kaɗan yanzu gashi ga bugi yar sarki Zaria tana asibiti,  jiya naje hospital ɗin dan naga ya jikin nata saboda baban ta ya ɗau zafi dayawa, kar yaga ko ɗaya daga chikin mu bai jeba ya duba taba, Allah ya rinyar nan ko motsi batayi kamar ba rai a jikinta amma a hakan kuma yau kake so na barka kasake bugun wata ko?

 "au wai dan babanta har wani zafi ya ɗauka ke nan to ya baku sanar dani ba dan shima na hukuntashi, waro ido waje Aryan yayi kafin yace "zaka iya zuwa ai yanzu ma sai ka hukun tashi, ni dalla ka bani ruwa nasha hai, Aryan ya karisa maganar chikin ɓachin rai 

"Wlh Aryan ba dan ina kaunar ka ba Allah da yau inaga sai dai a kwashi gawarka ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya nufi freij, " zaka iya ajiye kaunar a gefe ai sai ka kashe nin Aryan ya faɗa chikin fushi,  Bgs ba tare daya sake chewa komai ba ya ɗauko ruwa kawai ya dawo kan gado ya ɓalle bakin robar ya ɗago kan Aryan ya kafa masa robar a baki, sosai Aryan ya sha ruwan har sai da ya kusa shanyewa, sannan Bgs ya chire roban daga bakin shi yana faɗin "ya isa haka shan ruwan, Aryan yace "to ba kai ka min wani wawan naushi a kirji ba ai dole nasha ruwa "kaɗan ma kagani ai wlh ka chigaba da shiga faɗan da ba ruwan ka watarana sai dai a kwasheka zuwa hospital.

murmushi kaɗan Aryan yayi san nan ya yunkura ya miƙe zaune, a hankali y zuro kafarsa kasa ya miƙe tsaye "ina zakaje bro? Bgs ya tambaya yana kallon face ɗin sa, "fada zanje wajen Abba mana, "why ba zaka tsaya a nan ba "no akoi maganar da zamuyi ne mai mahimmanci "ok let's go together, ya kai karshen maganar tare da miƙewa, atare suka fito

Dai dai wajen part na Ammi  sukachi karo da su Zahra sun fito daga palon Abba.
        Ganin Bgs da yaya Aryan yasa diyana ta fasa ihu ta watsa a guje ta shige ɓangaren Ammi,  da gudu hiyana tabi bayan ta,  su Zahra ma ba'a barsu abaya ba da gudu suka wache suka bi bayan su hiyana.

"Bgs gaskiya baka kyauta wa yanzu dan Allah dubi yadda yaran nan suke ihu da suka ganka kamar sunga dodo, wani dogon tsaki Bgs yaja kafin yace "bana son haka Aryan ka daina kawomin maganan yaran nan, "ai gaskiya na faɗa maka bro menene anfanin kasa su suna jin tsoronka, shiru Bgs yayi bai sake magana ba har suka karisa chikin fada

Misalin karfe 11 :20 Aryan ya fito daga fada ya nufi part nashi dan ya je yayi wanka yazo dai dai part na Ummi sai yaji haidar da Umar suna hira tsayuwa yayi da kyau ya kasa kunne yana jin su, 

"Umar ai wlh ko baka faɗaba kowa yasan Son yarinyar nan yaya Aryan yake, bakaga yadda yake kallonta ba idan mun haɗu wajen chin abinchi, 

"kai haidar kai kallo kawai ka gani ka dubafa yau saboda ita yaya Aryan yayi faɗa da yaya prince, ai mugu mugun Son ta yake, wani dariya Umar yayi kafin yace "tab aiko zamuga ya, yaya prince zai yi idan yaji lbr yaya Aryan ya faɗa soyayya dariya suka kwashe a tare har da riƙe chiki, 

A fusache Aryan ya juya ya fasa shiga part nashi ya nufi part ɗin Ammi sai wani huchi yake, chikin ransa yana faɗin soyayya ni wai aa never wlh har abada. 

da sallama yashiga palon bb kowa kai tsaye betroom ɗi ta ya nufa, a bakin kofa ya tsaya yayi sallama, Ammi na daga chiki ta amsa masa tare da bashi izinin shigowa, shiga yayi ya zauna saman manya manya throw pillow dake tsakiyar ɗakin
          "Aryan lfy kuwa naga ranka a ɓache haka, "Ammi so nake yarinyar nan ta bar gidan nan "wace yarinyar kuma? "Wan nan yarinya dake kawomin coffee "au diyana? "eh ita ban son sake ganin ta gaskiya, yana kaiwa nan ya miƙe ya fita rai a ɓace, miƙewa Ammi tayi itama ta ɗauki alkyabban ta ta sanya ta fito ta nufi fada

Da sallama ta shiga ta karisa wajen Abba ta zauna saman kujera tana masa sannu da hutawa "Aisha lfy naga kamar ranki a ɓache? Abba ya tambaya yana kallon face nata, Ammi bata ɓata lokachi ba  wajen sanar da Abba abun da Aryan ya faɗi

 a tunanin ta Abba zai ɓata rai sai kuma taga yana murmushi ya ɗauko wayar sa dake gefensa yafara kiran layin Aunty farida,
                      Bugu ɗaya Aunty farida ta ɗaga tare da faɗi "hello Abba na "my daughter ki zo fada yanzun nan ki sameni, yana gama faɗin hakan ya katse kiran, 

baifi minti 5 sai ga Aunty farida ta shigo da Sallama har kasa ta duƙa chikin girmamawa ta gaida Abba da Ammi, da fara'a dukkansu suka amsa, "zauna my daughter muyi magana chewar Abba
                      Miƙewa Aunty farida tayi ta kowa saman kujera ta zauna ta zubawa Abba ido tana sauraron taji mai zai che "so nake yanzu ba sai anjima ba ki ɗauki diyana ku koma Maiduguri da ita, kuma karki kuskura ki sanar da wani tana wajen ki koda Aryan ne ko zai miki tambaya dubu idan ki ka kuskura ki ka sanar da shi to ban yafeba. Sai da Abba ya daka ta da magana sannan Ammi ta fara magana

Ranka yadaɗe me yasa zaka che hakan? "Aa Aisha ku kyaleni tun da har Aryan bai ji kunyar idon ki ba yazo yace baya son ganin yar ɗan uwanki to wlh sai nayi maganin sa, "tayaya zakayi maganain sa to? Ai naga shi yace bai son ganin ta to kaga idan ta tafi ai sai yafi kowa murna da hakan "Aisha ke nan yanzu kina nufin bakisan chewa Aryan na Son diyana ba, to idan ma baki sani ba yau kin sani,  kuma So bana wasa yake mata ba "amma yana Son ta kuma yace baya son ganin ta a gidan nan? 

"Kedai ba ruwanki kuyi abun da nache muku wlh duk wadda tasake ta faɗi inda diyana take to sai na ɓata muku, kutashi kuje, my daughter yanzun nan ku tafi kuma karki bari kowa yaga kin fita da diyana, "to kawai Aunty farida tace sannan ta miƙe tanan murna sosai dan ambata diyana atare suka fito fada da Ammi

Yola

Ihu take tana faɗin nashiga uku na ku kawo min agaji zan mutu, da gudu yaya bello ya fito daga chikin gonar sa ya nufi gonar bappan su dan daga nan yake jiyo ihun, 

"Subhanallah innar buba lfy? Chikin ihu da kuka innar bubu tace "Bello mutuwa zanyi na shiga uku kumurchin machijine ya sareni a kafa, chikin sauri bello ya kai kallonsa kan kafar nata, gaba ɗaya kafar ta kunbura sundum, girgiza kai Bello yayi yana faɗin "shike nan dafin yagama shiga jikin ki wlh ko kinsha magani yanzu ba lallai ki chigaba da takawa da kafar ki ba, dan dafin ta riga ta illata namar kafar taki

"Bello ka taimake ni mutuwa zanyi wayyo Allah, da gudu yaya bello ya juya ya koma chikin gonarsa ya tsinko wasu ganye ya nufi rafi ya wanke su tas, san nan ya ɗauko wani ɗan kwarya, ya dawo wajen innar buba, murje ganyen bello ya shigayi chikin kwaryar sai da ta fitar da ruwa san san nan ya bawa innar buba, ruwan akan tasha ganyen kuma ya manna mata awajen chizon machijin.

Tana shan maganin ta fara amai, amai sosai ta amayar da dafin machijin, amma kafar ta kuma har yanzu a kunbure yake gashi yayi wani green dashi,  ɗaukan kwaryar yaya Bello yayi ya koma rafin ya ɗebo mata ruwa ya dawo ya bata tasha, san nan ya ɗauke ta chak ya saɓata a kafaɗar sa ya nufi hanyar gida

Da sallama ya shiga gidan hasana na tuƙa tuwo ganin yaya Bello ɗauke da innar buba a kafaɗar sane yasa hasana miƙewa da sauri ta ɗauko ta barma mai kyau daga ɗakin ta ta shin fiɗa a tsakar gidan.

A hankali yaya Bello ya kwantar da innar buba a kan ta burman, san nan ya dubi hasana yace "kiyi sauri ki kammala abinchin ki zuba mata, to kawai hasa tace Sannan ta miƙe ta koma wajen girkin nata, innar buba kuwa sai hawaye take saboda azabar da kafarta ke mata, 

*💫STAR LADY💫*

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 3️⃣1️⃣*

Aunty Amarya che zaune a bakin gadon ta tana waya da hajj sadiya 

"To yanzu hajj sadiya ya ki kayi dashi ne nifa wlh na matsu, banson ganin yaran nan a gidan nan, daga ɗayan bangaren hajj sadiya tace "haba hajj  hajara sai kace yau muka fara aiki da gagarabadau, ki kwantar da hankalin mana yanzu zan miki bayani ai tun da ki kaga na kiraki kam kema kinsan akoi bayani "to hajj sadiya ki faɗamin da wuri mana dan na matsune naji ai

"Jiya naje wajen sa, yana faɗamin chewa Aiki na tafiya yadda ya kamata, dan yache ma akoi wani shu umin malamin da basu san daga ina yake ba yana taimaka musu sosai, shima yana bibiyar rayuwar yaran ne, ahalin da akechiki yanzu yama kusa kunche tsarin dake jikin yaran saura kaɗan, amma fa yace ita babban wlh ba wanda ya isa ya mata wani abu asiri ba zai kamata ba, aljanu ma bazasu iya shiga jikin taba, dan tana karatun qur'ani tana askar, bata wasa da sallah kuma tana sallan dare gashi bata shiga harkan kowa, yaso shiga jikin ta last month da tana period ma amma sai dai kas bai yi nasara ba, domin duk da tana period, tana askar, kuma tana zama da alwala,ba ta yadda zaiyi ya shiga jikinta,  su kuma sauran nan da two weeks, malin Chan in ya gama kunche tsarin jikin nasu, yana gama kunchewa shikuma gagarabadau zai ɗaura nashi aikin a kansu
            Dogon numfashi Aunty Amarya taja kafin tace "to shikenan Allah ya kaimu "amin Hajj Hajara karki damu ke dai ki kara hakuri saura kaɗan yauwa baki bani lbr sabon sarkin ku ba ya ake chiki? " Hmmm ke dai hajj sadiya bari wani sarki wlh ranan da ya fara hawa kujerar mulkin nan tun ranar ya fara rashin lfy baya magana baya motsi, sai dai numfashin sa kawai da zakiji shine zai tabbatar miki da bai mutuba abun gwanin ban tausayi, 
               Wani shewa hajj sadiya tayi ta chikin wayar kafin tace "ai albishir ya kamata kimin hajj Hajara kiche aikin gagarabadau yayi kyau,
 zubur Aunty amarya ta mike muryar ta har rawa yake wajen faɗin "hajj sadiya kenan ke kikayi wa Ahmad wan nan abun? ke nan daman ba chiwon Allah da annabi bane ya kamashi? tsaki Hajj sadiya taja kafin tace.

Kamar ya ni na masa, ke dai kika masa ba niba, dafe kirji Aunty amarya tayi ta zaro ido tana faɗin "ni kuma hajj sadiya a yaushe na masa hakan, "Hajj Hajara wai lfy ki?, watoma kin manta aikin da kika sani naje na sa gagarabadau ya miki akan, idan ba mijin ki ko ƴaƴan ki ba, ba wanda zai karɓi mulkin nan duk kuma wan da yayi kuskuren hawa mulkin tofa mutuwa zakiyi 

Girgiza kai Aunty amarya ta shigayi tana faɗin "aa hajj sadiya ni dai gaskiya banche a kashe kowa ba ni dai to a kunche aikin nan dan wlh bakiga yadda Ahmad ya koma bane Allah ko ke kika ganshi sai kin masa kwalla,ni su Ahmad basumin komai ba,su diyana ne bana so, su nakesan a haukata min, amma ban da su Ahmad
    Wani dogon tsaki Hajj sadiya ta kuma ja kafin tace "amma hajj Hajara bansan baki da wayau ba sai yau wlh ki na tunanin idan da uwar su che ta samu damar da ki ka samu a kan ƴaƴan ki, zata raga musu ne? wlh bazata ragawa kowa ba, ke kowa da kika gani aduniyar nan kanshi kawai ya sani wlh sai dai in bai samu dama bane sai ya rinƙa nuna chewa shi na Allah ne, da zarar ya samu dama to a nan zaki gane asalin mugun halinsa, ki tsaya ke dai kiche kinajin tausayin su kina ji kina gani, Aisha zata mamaye komai na gidan in bakiyi Sa'a bama wlh sarki na mutuwa yar wanke wanke Aisha zaki zama, dan haka zaɓi yarage gareki. 
 
Dogon numfashi Aunty amarya taja tare da sauƙe ajiyar zuchiya kafin tafara magana "eh hajj sadiya kina da gaskiya wlh,dan yanzu ma mai martaba yafi jin maganar Aisha fiye da na kowa a duniyar nan, da Zarar Aisha tace ga abun da takeso wlh zakiga jikin sa har rawa yake wajen biya mata bukatun ta, kin dai san halinsa idan yayi magana baya chanzawa to wlh Aisha tana sa shi ya sauya magana.
 
"Yauwa hajj Hajara kin gane abun da nakeson ki gane kenan yanzu dai bari mugana dasu diyana sai mu koma kan farida muna gamawa da ita sai muyi maganin Aisha itama, wani murmushi Aunty amarya tasaki kafin tafara magana "yauwa kawata shiyasa nake son ki ai, amma yanzu ya zamuyi da maganar zulaihat? tunda kinga ita ya kamata Safras ya aura
       "Eh karki damu yanzu zulaihat ɗin ma bata nan wlh wai tabi saurayin ta party a Dubai, zasu dawo nan da tsakiyar wata mai shiga, inaga abun da za'ayi, idan ta dawo kasar sai ta  dawo wajenki  da zama har musamu shi Safras ɗin ya fara Son ta ni kuma zanyi nawa kokarin wajen malamai na dan naga an chusa masa Son ta sosai

"Haba hajj sadiya ya za'ayi ki barta tabi saurayi, yanzu tana zuwa yawon nan ne kuma kike tunanin Safras zai sota to wlh tun wuri ki hanata in ba haka ba tofa duk in da zaki shiga Safras dai ba zai sota tana yawon banza ba   "Karki damu hajj Hajara idan ta dawo ai shike nan zata dawo wajen kine da zama, gashi kinga gidan ku ba'a fita sai masu zuwa school, suma kai su ake,  a dawo dasu, kinga ba halinta fita taje yawon ko ? 

"Eh hakane kam to shike nan sai munyi waya zan turomiki 500k ki karawa malamai ɗin naki amin aiki masu kyau da zafi, "to kawai hajj sadiya tace daga haka sukayi sallama, Aunty amarya ta ajiye wayar sama drawer gefen gadonta ta karisa hayewa gadon gaba ɗaya ta kwanta, ta lunshe ido

 
Aryan

Zaune yake a bakin katafaren gadon sa sanye da kayan barchi riga da dogon wando masu laushi farare tas,yan shara shara marasa nauyi,   ya dukar da kan sa kasa, gaba ɗaya gashin kan nan nashi a hargitse ya kwanto masa har kan fuska, ya zuba uban ta gumi, sai wani irn huchi yake kamar wadda aka batawa rai wayar sa dake kan gadon ya ɗauko ya kunna hasken screen ɗin, ya duba time 10:30pm chire password na wayar yayi ya shiga chikin contact nashi, yayi dealling num ɗin Zahra, wayar tana ta ringing har ta kusa katsewa san nan Zahra ta ɗaga.
                        Chikin muryan barchi tace "hello yaya Aryan, ina wuni
Bai amsa mata gaisuwar sai yace "ki chewa yarinyar nan ta kawomin coffee
"Yaya Aryan ai bata nan, "what? Bata nan ina kuma taje a daren nan? yayi maganar chikin tsawa
"Ammi  ta mai da ta kauye, zubur ya miƙe yana faɗin "what? kauye kuma to da izinin wa za'a fita da ita gidan nan, nache a kai min ita wani waje ne? 
Ita dai Zahra tsoro ne ya kamata jin yadda yaya Aryan ke magana chikin tsawa, muryar ta har rawa yake tace, "kayi hakuri yaya Aryan, 

a fusache ya nufi kofar fita batare da ya sake che da zahra komai ba, kuma bai katse kiran ba,dan yama manta waya yake, idon sa ya rufe,
 har ya kai bakin ƙofa zai fita sai kuma ya dakata ya ɗago wayar sa dake hannunsa, ya katse kiran Zahra san nan ya duba time 10:38 " dare yayi bai kamata naje part na Ammi yanzu ba, 
Chike da ɓachin rai ya juya ya koma kan katafaren gadon sa ya kwmata ya lumshe ido kamar mai barchi, Almost 5mnt

Sai kuma ya miƙe zubur ya zauna chikin tsawa yace "kauye kuma aa ina hakan ba zai yuwuba wlh,  wai shin nama bada izinin ta fita gidan nan ne? wlh duk ma wanda ya fita da ita daga gidan nan sai na hukun tashi, akan wani dalili? 

Zuro kafarsa kasa yayi kafin ya miƙe gaba ɗaya yanufi hanya fita yana faɗin "wlh Ammi dole na tasheki a daren nan, dan in ji ina kika kai yarinyar nan ba zan iya hakuri gari ya waye ba, 
Taku yake irin na jaraman maza ji kake dif dif dif idan yana taka kasa, sauri yake sosai kamar zai tashi sama, 

Da sallama ya shigo babban palon Ammi na kasa, chikin sauri ya haye sama, kai tsaye betroom na Ammi ya nufa, a bakin kofa ya tsaya tare da ɗan buga kofar yana faɗin Assalamu alaikum.

Ammi dake kwanche kan katafaren gadon  jin muryan Aryan yasa ta miƙe zaune da mamaki a face nata, ta amsa masa sallamar

San nan ta sauko daga gadon ta nufi drawer kayan ta ta ɗauko hijabi ta sanya a jikinta, ta dawo bakin gadon ta ta zauna tana faɗin "shigo mana Aryan.

A hankali ya turo kofar ya shigo, tsayuwa yayi a bakin kofar ya ɗan jingina da jikin kofar, yana kallon Ammi dan ya kasa ko magana saboda azaban raɗaɗin da zuchiyar sa ke masa

"Aryan lfy baka yi barchi ba? Da kyar ya iya buɗe baki ya fara magana "Ammi pls tell me ina kika kai yarinyar nan
          Ɗaure fuska sosai Ammi tayi kafin tace "kauyen su mana na mai data 
"Kauye kuma Ammi to akan me? Akan wani dalili? Kuma taya zaki mai data kauye ba tare da izinina ba, tirkashi Ammi dai baki ta sake tana ganin ikon Allah, ganin Ammi tayi shiru bata bashi Amsa ba yasa yace "wai ma tayaya zaki ɗauke ta bada izinina ba? Kuma wani driver nema ya fita da ita daga gidan nan wlh yau sai ya karɓi hukunchi, in a serious matter yayi maganar, 
                     "Kaga Aryan wlh ka fita min a ɗaki bansan iya shege fa,  kai da kanka kazo nan da safe kache baka son ganin yarinyar nan a gidan nan yanzu kuma na mai data gidan baban ta san nan kache, ya za'ayi a mai data ba da izinin ka ba to sannu,nache sannu,

Waro ash eyes nashi yayi waje sosai kafin yace " Ammi yaushe nache bana son ganin ta kuma, ni fa aa inaga dai mantuwa ki kayi Ammi, 

cheke da jin haushi Ammi tace
"Karya dai zakache na maka ba mantuwa ba, girgiza kai ya shigayi yana faɗin "nashiga uku karya kuma Ammi aa wlh ban haka Ni nake nufiba kawai abunne yake bani mamaki da ki kache, Ni nache bana son ganinta.

"To idan ka gama mamakin naka sai katafi ɗaki ka kwanta ai dan dare yayi, 

shiru yayi kamar mai tunani almost 10 mnt yana tsaye ya kasa koda motsi, 
      sosai ya bawa Ammi tausayi dan bata taɓa ganin Aryan a irin wan nan yanayi ba sausauta murya tayi tace "Aryan kaje ka kwanta kaji dare yayi, ɗan firgigit yayi alamar tunani yaƙe, ɗago ash eyes nashi yayi ya sauƙe su kan Ammi, bakaramin tsorata Ammi tayiba ganin yadda idon sa suka sauya sukayi jaaa sosai, ya kasa magana ma a hankali ya juya ya fice daga ɗakin

Dafe kai Ammi tayi tana faɗin "wai duk wannan abun na menene mai yasa mai martaba zai wa yaran nan haka ni ai tunani na burin shi kenan yaga sun fara son mace har ya samu ya musu aure to Amma me yasa yanzu kuma zai wa Aryan haka, ni gaskiya bazan iya ganin Aryan a chikin irin wan nan halinba dole musan abunyi,  yau kawai da bai ganta ba jibi yadda ya dawo, hmm

jiki ba kwari ta chire hijabin jikin ta ta mai da drawer san nan ta dawo ta kashe wutar ɗakin ta haye gadonta ta takwanta

Aryan kuwa saboda bakin chiki da ɓachin rai dakyar ya iya kai kanshi ɗaki, dan gaba ɗaya idon sa sun rufe baya gani, addu'a kawai yake Allah ya gaimu gobe, yayi wa garin Yola diran asuba yana shiga ɗaki ya haye katafaren gadon sa ya kwanta, sai juyi yake ya kasa barchi 
sai ya lumshe ido kamar mai barchi idan ya tuna diyana na kauye kuma wata kilama yanzu tana tare da wanchan wawan Bello sai ya sake ware manya manyan ashe eyes nashi, da suka sauya yanzu suka koma jaaa sosai saboda tsananin kishi da ɓachin rai, 

Da kyar ya iya laluɓo wayar sa ya kunna hasken screen ɗin, ya shiga Kga App yayi playing na hoto nan diyana ya fara binsu ɗaya bayan ɗaya yana kallo, nan take murnushin ta bayyana a kan kyakkyawar fuskar sa, abu ɗaya kawai yake tunawa kuma yake jin sautin a kunnensa wan nan zazzakar muryar tata idan tana faɗin Yaya Aryan, wow gaskiya yau nayi missed sexy voice naki sis, sosai yake ta kallon hotunan yana murnushin har ya kai kan video da ya musu shekaran jiya da zai saka mata sarƙa, 

playing na video yayi ya fara kallo yana murnushin, zuba mata ido yayi sosai yana kallon yadda ta zura hannu a riga tana kokarin chiro sarkan, bai ankaraba kawai sai yaka boobs nasa a waje daman shekaran jiya ya kawar da kansa bai san taya ta fitar da sarkan ba, ashe wayar sa ta ɗau komai, a sukwane ya chire video ya fita daga App ɗin san nan ya kashe wayar ma gaba ɗaya, ya ajiyeta a saman drawer gefen gadon, shiru yayi kamar mai tunani har barchi ɓarawo ta ɗauke sa batare da ya saniba.

Maiduguri

Aunty farida che kwamche kan katafaren gadonta ta tada kai da chikin yar dadyn junior, suna yar hirarsu yana shafa kyakkyawa kuma lallausan bakin gashin kanta
      My farida magana mai muhimmanci nake son muyi dake fa amma kinzauna kinata zubamin shagoɓa 

Aunty farida tace "Kai baby Allah kana da neman rigima to yanzu kafaɗi maganar mana ina jinka ae, 
  "Watoma nine nake da rigima ko? "Eh mana Allah my baby kafini iya rigima,
Kwafa dady'n junior yayi yana faɗin zamu haɗune yanzu dai magana mai muhimmanci nake son muyi bari mugama maganar zakiyi bayani "to shike nan na ji yanzu dai faɗamin me ka ke so muyi magana a kai
    "Yauwa my farida to bani hankalin ki nan, nitsuwa Aunty farida tayi ta zuba masa ido tana kallonsa

"Wan nan yarinyar da kika zo da ita wlh ta shiga raina sosai dan Allah idan ba damuwa ki faɗawa Abba, ya taimaka ya bawa Auta bakura Auren ta, 

    zubur Aunty  farida ta miƙe zaune,tana kallon face ɗin shi taga dai da gaske yake "aa my farida lfy kika miƙe haka ko dai yarinyar matar Aure che? To ai ko matar Aure chema bai kamata kiyi irin wan nan miƙewarba, 
      "Dady'n junior diyana fa Abba ya riga da ya mata miji wlh, dan da zamu taho har mun shiga mota zamu tafi, Abba yasake bina har chikin motar yamin kashedin kada na kuskura na bar diyana ta kula wani namijin, domin ya mata miji a ɗaya daga chikin kanne na Amma bansan wanene daga chikin su ba, dan Abba'n bai faɗamin wanene ya bawa diyanar ba
  
Dogon numfashi dady'n junior yaja kafin yace "to shike nan, nima dai kafin na tambaya nayi tunanin hakan domin abun da mamaki ache yarinya kyakkyawa kamar wannan tafito daga gidan ku, dake chike da zaratan samarin nan, ache ba'a mata miji a chikin su ba abun,  abun dubawa ne, 
Aunty farida zatayi magana sai sukaji alamar motsi a palon kasa, kallon dady'n junior tayi shima ita yake kallo, a tare suka sauko daga gadon da sauri suka nufi waje

Suna saukowa palon kasa turus suka tsaya, suna kallonta da mamaki, Aunty farida tace "my diyana me kikeyi a nan ? Meyasa kika fito daga ɗakin? Shiru diyana bata basu amsa ba tana zaune  saman sofa tana kallon kasa ta buga uban tagumi, 
juyowa Aunty farida tayi ta kalli dady'n junior, shima ita yake kallo, sake dawo da kallonta tayi kan diyana dake zaune ko motsi batayi, a hankali Aunty farida ta taka zuwa kusa da diyana tasa hannu ta ɗan taɓata tare da kiran sunan ta a hankali,
        Firgigit diyana tayi tare da miƙewa, zuba mata ido Aunty farida tayi kafin tace "my diyana lfy kike zaune a nan? Tunanin me kikeyi haka kuma?
 Tsuke fuska diyana tayi ta turo baki ta fara magana

"Aunty farida wlh na kasa barchine, kuma ina jin ajikina kamar yaya Aryan bai da lfy san nan kuma Allah idan na rufe idona sai in rinƙa ganin yaya Aryan yana faɗin, bakin ki kawomin coffee ba yau to munɓata, Allah Aunty farida ina son ganin yaya Aryan, kewar shi nake

Tirkashi turus Aunty farida tayi tama rasa me zatachewa Diyana, domin iya gaskiya diyana tafaɗa dan bata karya, amma bansan meyasa Abba zai yankewa yaran nan irin wan nan ɗanyen hukunchin ba gashi diyana ta kasa barchi, kuma ina da tabbachin shima Aryan ɗin yana chikin damuwa.

 ganin Aunty farida tayi shiru alamar ta tafi duniyar tunani ne yasa dady'n junior ya dubi diyana yace 
"jeki ɗaki ki  kwanta ko da safe da kaina zan kai ki wajen yaya Aryan kuma ki daina tunanin ko bai da lfy, lafiyan sa kalau sharrin sheɗan ne yasa kike ganin kamar bai da lfy, kije kiyi addu'a ki kwanta kinji, to kawai diyana tace san nan ta nufi ɗakin ta, 

Hannun Aunty farida dady'n junior ya kama suka nufi stair ɗin suka koma ɗaki, 
     "My farida wai meke faruwane?, ko dai Aryan shine mijin da Abba yayi wa diyana 
  "Dady'n junior wlh nima abun yafara ɗauremin kai, nan dai Aunty farida ta shiga bashi lbr duk wani abun da ta sani dan gane da yaya Aryan da diyana, ta karisa maganar dai dai lokachin da suƙe hawa kan gadon su, 

"Kinsan me my farida, batare daya jira amsar taba ya chigaba da chewe "Abba yana da gaskiya domin kinga dukkan kannen namu basu taɓa soyayya ba hasalima basu ɗauki mace da daraja ba, ganin ta suke kamar abun banza, wlh a irin wan nan yanayin da suke chiki idan aka ɗauki mace aka basu to ta shiga uku domin basusan darajar taba zasu wahalar da ita sosai, yanzu dai ki dubi yadda Aryan ke masifar son yarinyar nan batare da yasan Son nata yake ba amma duk dahaka daga ɗan magana dasu Umar sukayi, ya fusata har yaje ya samu Ammi ido da ido yace bayason ganin diyana kinga a nan ma rashin sanin darajar mace ya bayyana karara, a tare dashi, wlh gwara da Abba ya masa hakan, kuma ku barshi sai ya gasu sosai sai yasan mace fa halittace mai daraja wadda kowani ɗa namiji ke son kasan chewa da ita, ku kyalesa sai ya furata da bakin sa chewar yana Son ta, in ba hakaba ko an musu aure ran da su Umar suka sake mai maita abun da sukayi shima sake mai maita abun da yayi zai yi. da katawa yayi da maganar yana mai da numfashi,

"Kana da gaskiya dady'n junior wlh rashin sanin darajar macece har yasa Aryan ya iya tinkarar Ammi ya faɗa mata hakan, to amma abun tausayin a nan shine ita diyana yanzu dai da kunnen ka kaji halin da take chiki, tana son Aryan sosai Amma itama batasan chewa Son nashi takeba, saboda kaga ita yarinya che kuma gashi ba wani ilimin ke gareta ba ita ko kallon film batayi sai dai buga game kawai, ta iya

"Hakane my farida dolene diyana ta zama abun tausayi amma ke zaki jata a jiki domin ki rinƙa rage mata, kewar nashi kada ki bari ta rinƙa zama ita kaɗan, gobe idan Allah ya kaimu zan saya mata sabuwar waya mai kyau sai kisa Sim naki a chiki, ki mata download game's dayawa, idan kin gama ki chire Sim ɗin, san nan kema kiyi taka tsantsan da wayar ki dan kinsan gaba ɗaya kannen ki basa iya yin wuni ɗaya batare da sun kira ki ba, kada ki kuskura ki sakawa diyana Sim card a wayar ta, domin a yadda kika bani lbr na fahimci yariyar akoi kwakwalwa sosai, dan haka sai kinyi taka tsantsan da ita sosai 

"To shike nan dady'n junior zanyi duk yadda kace Saboda nima ina kaunar diyana sosai kamar yadda nake kaunar Aryan, bazan so taje gidan mijin da bai san darajar ta ba, zanyi iya bakin kokarina wajen ganin, na bata kulawa na chanza mata abubuwa da dama

"Good my farida hakan yayi to yanzu dai mu kwanta muyi barchi kinga dare yayi ma karisa maganar gobe idan Allah ya kaimu,

 atare suka kwanta ta shige chikin kirjin sa ta lafe shi kuma yana shafa bayan ta har barchi ya ɗauke su.

Kano

Tun misalin karfe 6 su hiyana suka gama shirin zuwa school, yaya Khalid kawai suke jira yazo ya ɗauke su.

sai misalin karfe 7:30 yaya Khalid yazo ya tasa su a gaba suka fito harabar gidan suka nufi parking space, yau da kanshi ya tuƙa su a family car, 

Gudu yake shararawa da motar sosai akan shin fiɗaɗɗiyar  hanyar school nasun, chikin kan kanin lokaci suka isa makarantar,kai tsaye parking space na ya nufa yana kashe motar, ya fito a gurguje ya yana faɗin "kufito ku tafi class dan kun kusa makara, yana gama faɗin hakan ya nufi office na HM na makarantar, domin naje ya biya musu kuɗin makaranra. 

Abangaren su hiyana kuwa yaya Khalid na tafiya suma ko wace ta kama hanyar class nasu, amma kallo ɗaya zaka yiwa hiyana kasan tana cikin matsanan chiyar damuwa ga blue eyes natan nan duk sun kunbura da alama tasha kuka, dan dai ita ba mai yawan kallon mutane bane kullun kanta na kasa shiyasa mutun ba zai gane kunburin da idon nata sukayiba, tazo dai dai zata shiga class nasu, taji daga bayan ta an che "ke zonan chikin tsiwa, da sauri ta juyo, ganin....✍️✍️

More comments an share
 






 💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'💖

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
     👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
       by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
       by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
      by(xeemat....love)

*4, JINI DAYA*
      by(mrs bbk)





More comments an like pls
 

*💫STAR LADY💫*32

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

    💖Story And Written💖
                     ⬇️
               *Star lady*


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 3️⃣2️⃣*

Da sauri ta juyo ganin jabir ne yasa ta ƙara ɗaure fuska sosai, ta sunkuyar da kanta kasa, "my hiyana me ya same ki kikayi kuka? Chewar jabir Ya yi maganar yana matsowa kusa da ita, ɗan ja da baya kaɗan tayi kasa kasa tace "ina kwana, batare da ya amsa gaisuwar nata ba ya sake mai mai ta mata tambayar daya mata da farko  "me yasa meki ki kayi kuka? waya taɓamin ke?
    
Chikin sanyin murya tace "ni ba wanda ya taɓani kawai nayi kuka ne saboda an mai da kanwata garinmu, 
   "Eyya to sorry kinji kije class idan an tashi break kizo muyi hira dan ina missing naki sosai, ko dai ke baki missing na ne? Ya karisa maganar yana ɗan dukar da kai yana leka fuskan ta dayake ta sunkuyar da kan kasa, shiru tayi bata sake che masa komai ba, ganin bata da niyar magana ne yasa yace "to kije class ɗin idan antashi sai kizo na kawo miki tsaraba
     Bata jira ya karisa maganar shiba ta shige class nasu da sauri, binta yayi da kallo har ta shige sannan ya juya ya nufi nasu class ɗin

Sosai Bgs yake sauri kamar zai tashi sama taku yake irin na sadaukin yaki, yazo dai dai zai shiga ɓangaren Aryan, yajiyo muryan Abba daga bayan sa yana faɗin "jirani mushiga tare, batare da ya juyoba ya tsaya har Abba ya kariso, wajen a tare suka jera zuwa chikin part ɗin, 

"Menene ya hana Aryan zuwa sallar asuba Abba ya tambaya yayi maganar dai dai lokachin da zasu haura stair case ɗin chikin palon Aryan, 
   
"Abba wlh nima ban saniba abun da nazo tambayar sa kenan, shiru Abba yayi bai sake chewa komai ba, har suka karisa betroom ɗin, da sallama suka shiga a tare

Kwanche yake saman katafaren gadon sa,yana sharara barchin,  da mamaki Abba ya juyo ya kalli Bgs wadda shima Abba yake kallo.. 

....Karisawa bakin gadon sukayi a tare zama Abba yayi a gefen gadon shi kuma Bgs ya haye saman gadon ya ɗan jayye bargon da Aryan ya lulluɓu, zuba masa ido Bgs yayi sosai kamar mai karantar wani abu a kan face nashi 

"Abba da alama ɗan uwana bai yi barchi jiya da daddare ba koda kuma yayi to kaɗan ne, ka duba time fa yanzu Almost 8:5am amma yana barchi ko sallar asuba bai yiba, anya Aryan yana da lfy kuwa?  Dogon numfashi Abba yaja kafin yace "kila akoi abun da ya tsare sa ya hana shi barchi da wurine.
 
Guntun tsaki Bgs yaja sannan yasa hannu yana ɗan bubbuga hannun Aryan, 
  "Aa Safras ka barshi mana yayi barchin sa chewar Abba "aa Abba ya tashi dai kofa sallar asuba bai yiba ya tashi idan yayi Sallah sai ya koma barchin, shiru Abba yayi bai sake Magana ba, bubbuga Aryan Bgs yake yana kiran sunan sa "my blood, my blood

Da kyar Aryan ya iya waro ash eyes nashi nan, sun chanza sunyi jaa saboda barchi chikin muryan barchi yace "Bgs lfy? Ɗaure fuska Bgs yayi kafin yace "zaka tashi kaje kayi sallar asuba ne ko dai sai na maka 1bloo 7 die, 

Wani sallar asuban kuma? I Already nayi sallar ton asuba ɗin, yayi maganar yana kokarin miƙewa zaune, da kyar ya iya miƙewa zaune, da sauri yasa hannu ya dafe kansa dan ji yake kamar kan nashi zata faɗi kasa ga wani azaban chiwo da take masa, sai sara masa kan keyi kamar zai fashe, 

Ganin Aryan ya dafe kai ne yasa Bgs saurin kai hannunsa saman goshin Aryan ɗin yana faɗin "my blood lfy? Menne? Kai ɗinne ke maka chiwo? Karisa hayewa gadon Abba ma yayi ya sa hannun'sa ya riko kan Aryan yana faɗin 

"Aryan meke damun kane? ɗago jajayen idon sa  yayi yana binsu da kallo ganin yadda suka ruɗene yasa ya ɗan kakalo murmushi gefen fuska, da kyar ya iya motsa lallausan red lips nashi ya furta "bb komai, a tare Bgs da Abba suka chire hannun su daga saman goshin nasa, 

Aryan me yasa baka je masallaci da asuba ba? Chewar Abba yayi maganar yana sauƙa daga gadon, "Abba makara nayi wlh, lokachin da natashi already an gama Sallah "me yasamu wayar ka? na kiraka da asuba ai a kashe, Bgs ya tambaya yana kallon face nashi, 
       "Eh Ni na kashe wayar jiya da daddare, to akan idan nazo barchi zan kunna sai na manta

Shiru Bgs ya ɗan yi kafin ya chiro wayar sa daga aljihu wandon sa, ya kunna hasken screen ɗin ya chire password ya shiga contact nashi, layin Fahad ya fara kira ringing ɗaya Fahad ya ɗaga

"Hello big bro, ina kwana,  "lfy Fahad, baki buɗe Abba da yaya Aryan ke kallon Bgs tunani Abba yake wai daman Bgs ya iya amsa gaisuwa tab lallai Fahad yarone mai Sa'a ya chire tuta a gidan nan, kaiii 

Yaya Aryan ma tunani yake anya na taɓajin Bgs yana amsa gaisuwar wani ko wata kuwa? Yayi iya tunanin sa duk bai tunano in da Bgs ya taɓa ansa gaisuwa ba kwata kwata, ko awajen Aiki  yaran mu zasu gaishe sa sai dai ya ɗaga musu hannu ko kuma ya musu alamar yaji da ido, ashe daman yasan yadda ake amsa gaisuwar kenan? Lallai yaya prince sai dai nace Allah ya shirya min kai.

"Fahad ka kawomin coffee mai zafi ka haɗo da hot milk, ina ɗakin Aryan yana gama faɗin hakan ya katse kiran. 

      ..dawo da green eyes nashi yayi kan Aryan dake zaune ya zuba masa nashi Ash eyes ɗin shima yana kallon sa
         "Aryan lfy kake kallo na haka? Kawar da kallon sa gefe Aryan yayi zai yi magana sai Abba ya rigashi da chewa "ba dole ya kalleka ba daman ka iya amsa gaisuwa? Dawo da kallon sa Bgs yayi kan face ɗin Abba yace "na iya Abba  "au ka iya shine idan aka gaida ka baka amsawa "wlh Abba bawai da gangan nake kin amsawa ba,  kawai ni ban son magana ne Allah harchena nauyi ya kemin idan zanyi magana 

"Ba shakka Safras nima shaida ne ba tun yanzu ba haka aka haifeka baka son yawan magana amma dai karinƙa daurewa kana Amsa gaisuwar yan uwan ka, shiru yayi bai sake chiwa komai ba

A hankali Aryan ya zuro kafar sa kasa kafin ya sauko daga gadon, jiki ba kwari ya miƙe ya nufi toilet, wani irin jirine ta kwashesa batare da ya shirya ba kawai sai dai yajisa a faffadar kirjin Bgs, kara waro ash eyes nashi waje yayi, yana kallon face ɗin Bgs yayin da shima Bgs ɗin shi yake kallo

"Aryan baka da lfy ne? Abba ya tambaya yana karasowa wajen su, da kyar ya iya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi yace "aa Abba lfy na kalau kawai kai nane ke ɗan min chiwo sai jiri da nake gani, ɗan duƙawa Bgs yayi batare da yayi Magana ba ya saɓi Aryan a kafadar sa ya nufi toilet ɗin dashi, 

komawa gefen gadon Abba yayi ya zauna yana tunani " lallai Aryan ai ka makara ita soyayya baa nuna mata jaruntar, ai san da zaka kawo kanka ma ba wan da ya sani, Ni kuma inshaa Allah sai na koyamaka sanin darajar mace sai kasan chewa mace halittace mai daraja Abba yayi nisa chikin tunanin sa, bai maga shigowar Fahad ba sai dai yaga mutun yana ƙoƙarin hawa gado yana faɗin
         "Abba ina kwana, murnushi Abba ya sakarwa Fahad kafin yace "lfy ka tashi lfy, fuskar nan a ɗaure kamar bai taɓa dariya ba, da kaga  Fahad ba sai an faɗa maka chewa kanin Bgs bane, zaka gane domin komai nasu iri ɗaya, kaman nin su ɗaya irin yadda Bgs ke haɗe fuska haka shima Fahad ke yi, rashin son maganar su ma irin ɗaya komai dai na Fahad sak na Bgs, dan yanzu ma da Abba yace katashi lfy Fahad, bai amsa ba sai ma kara ɗaure fuska da yayi ya zaro wayarsa yana latsawa, Abba kam ko ajikinsa dan gaba ɗaya ƴa'ƴan sa ba wanda bai san halin su ba, 
         Hannun su riƙe chikin na juna Bgs da Aryan suka fito daga toilet ɗin, da alama brush Aryan yayi, saman gadon suka haye,  Bgs yace "Fahad ina coffee ɗin, Fahad ba tare da yayi magana ba ya sauko daga gadon ya nufi table ɗin tsakiyar ɗakin ya ɗauko kwakkyawar plate mai ɗauke da haɗaɗɗun cups guda 5 kowani cup an rufeshi da ɗan karamin plate mai kyau, bakin gadon ya dawo ya tsaya yana faɗin  "gashi nan, ɗago green eyes nashi Bgs yayi yana kallon Fahad, da mamaki yace
     "Fahad coffee da hot milk kawai nace ka kawomin ya naga cups har guda biyar?

"Eh to ai naji kache kana ɗakin yaya Aryan ne shiyasa na haɗo muku kai da shi ni kuma na haɗawa kai na black tea dan nima na taya ku sha, kaga cups 2 naka 2 na yaya Aryan, ɗaya'n nan kuma nawa, girgiza kai Bgs yayi yana faɗin "to ai daman Aryan nace ka haɗawa coffee ba Ni ba Ni kataɓa ganina inashan coffee ne? Kaje ka ajiye a saman table ɗin, bari mu sauko, juyawa Fahad yayi ya maida plate ɗin saman table sannan ya zauna saman sofa mai zaman mutun 1, yanan jiransu
   Miƙewa Abba yayi yana faɗin sai kun fito fada sannan ya nufi hanyar fita, Aryan ne kawai ya amsa wa Abba da to 

A tare suka sauko daga gadon suka nufi Fahad dake zaune saman sofa yana latsa waya.

A saman sofa mai zaman mutun 3 suka zauna da sauri Fahad ya miƙe ya ɗauko cup mai ɗauke da coffee ya miƙawa Aryan, sannan ya ɗauko cup mai ɗauke da hot milk ya miƙawa Bgs shi kuma ya ɗauki black tea ɗin sa ya koma ya zauna, shiru sukayi  

A hankali Bgs ke ɗan korɓan hot milk ɗin haka zalika Fahad yana latsa waya yana ɗan kurban Black tea, Aryan kuwa ya riƙe cup ɗin ya kasa kai wa bakin sa yayi shiru kamar mai tunani

"Aryan me kake tunani? Meke damunka? Bgs ya jefo masa tambaya, ajiyar zuchiya ya sauƙe kafin yace "babu komai my blood bana jin sha coffee ɗin ne bakina ba ɗan ɗano

ajiye cup ɗin hannun sa Bgs yayi sannan ya juyo da kyau yana kallon Aryan "Aryan wai nikam yaushe kadawo ragon namiji  ne? Waro manya manyan ashe eyes nashi waje Aryan yayi a sukwane ya juyo da kyau shima yana kallon Bgs, da mamaki "rago ya mai mai ta kalmar chike da jin haushin dan gantashi da kalmar da Bgs yayi, nan take kuma yaji wani karsashi yazo masa, ji yayi duk wata damuwa ta gudu domin ba abun da ya tsana arayuwa iri amasa kallon ya gaza ko kuma yana da rauni ko dai ache masa rago.
      Ganin yayi shirune yasa Bgs yace "me ya sauya kane Aryan? da alama fa yanzu kafara zama... da sauri Aryan ya sa hannu ya rufe masa baki bai bari ya karisa maganar ba domi ba zai iya jin taba, zuba masa green eyes nashi kawai Bgs yayi yana kallon face ɗin sa 

A hankali Aryan ya zame hannun'sa daga bakin Bgs san nan ya ɗauki cup ɗin coffee sa ya fara sha, juyawa Bgs ma yayi ya ɗauki  hot milk nashi ya chigaba da kurɓa a hankali, shiru sukayi ba wanda ya sake magana

YOLA

da sallama Inna habiba ta shiga gidan su buba, da kyar take iya jan kafarta, har ta karisa tsakar gida, inna yaya Bello da innar buba suna zaune saman tabarma guda, inna yaya Bello tana shafawa innar buba magani a kafarta daya kumbura sosai yayi wani green kamar ya ruɓe, 

Saman ta barman Inna habiba taje ta zauna "sannun ki da zuwa habiba Chewar Innan yaya Bello, wani harara inna ta wurgawa inna yaya Bello, tana faɗin "to ai ba wajenki na zoba munafuka sai ki tashi ki bamu waje, ajiye robar maganin hannun ta innar yaya Bello tayi tana kokarin miƙewa, 

Da sauri innar buba ta riƙe hannun ta tana faɗin "aa innar bello dalla kiyi zaman ki, ki rabu da habiba, bata da hankali ne, waro ido waje inna tayi chikin tsawa tace "ke larai ni zaki chewa bani da hankali eh, au yanzu da wannan munafukar kika haɗa kai,kenan? "habiba ki daina zagin min yar uwa wlh idan ba haka ba zamusa yaranmu su miki duka tsiya, 

Wani dariya Inna tayi har da shewa kafin tace yanzu ne kika san dachewa ita yar uwarki che ko? to wlh idan baki dawo chikin hankalin ki ba Allah sai na tona asirin duk abu da kika aikata wa yaron ta Bello, dariya Innar buba tayi  kafin tace 
     "Ki tona mana, dan Allah habiba ki tona ni bani da wata damuwa idan kin tona saboda nasan bello da innar sa, zuchiyar su ba irin na dabbobi bane wlh duk kauyen nan babu mutanen kirki kamarsu ki duba duk kuntatawa rayuwansu da nayi hakan bai hanasu taimako na lokachin dana shiga halin mutuwa ko rayuwaba, alhamdulillah kuma ni nasamu na roki gafarar su kuma sun ya femin, ke ma wlh idan dai baki tuba ba to karshen ki ba zaiyi kyau ba, ko da yake ko kin tubama dole sai kin karɓi azaba da hukunchi, domin Allah baya yafe hakkin wani bawan, sai dai idan bawan shiya yafe maki da kansa, to kuma aina zaki ga bappa ki roƙi gafarar sa ina zakiga su hiyana da mahaifiyar su, duk babu wlh habiba kekam kinshiga uku

A fusache inna ta miƙe ta ɗaga hannu zata zabgawa innar buba mari, chikin tsawa Bello dake tsaye a bayan su tun ɗazun yace "wlh kina marin ta  sai na shemeki da sandar nan, a tsorache inna ta juyo da sauri dan tasan Bello akoi shi da zuchiya sosai kuma idan yace zaiyi abu tofa zai yi ne "zo ki fita mana a gida Bello ya faɗa yana nuna mata hanyar fita da hannun sa, ba musu ta kama hanya fita tana jan kafa a hankali hankali har ta fice daga gidan

Karisawa yaya Bello yayi wajen su inna ya zauna gefen innarsa yana faɗin "innar buba kinsha maganin ki kuwa? "eh bello nasha ni dai ba abun da zanche muku sai dai in muku fatan alkhairin kuna da kyakkyawar zuchiya
      "Ki daina faɗin haka Inna ai duk abun da muka miki yiwa kaine kuma ai Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya faɗa chewa idan kana tare da mutun yana aikata abun da ba dai dai ba to karka kyamachesa karka gujesa ko da ka masa wa'azi bai jiba karka damu ka jashi a jiki kana masa alkhairin a hankali kana nuna masa abun da ya keyi ba mai kyau bane sannan kana binsa da addu'a, sai kiga Allah ya shirya shi ya chanza hali ya dai na, ba wai idan kaga mutun yana abun da bai dache ba sai kaje ka zauna kana zaginsa kana tsine masa a chikin mutane ba, yanzu ba gashi da muka jaki ajiki bamu je wajen kowa mun zage kiba bamuyi gulmar ki da kowa ba bagashi Allah da ikonsa ya shirya mana ke ba, kin gane gaskiya 
     
   Ajiyar zuchiya Innar buba ta sauke kafin tace "hakane Bello zancheka gaskiyane to Allah dai yasa itama habiba ta gane Allah ɗaya ne, a tare innar yaya Bello da yaya Bello suka haɗa baki wajen chewa Amin, 
Miƙewa innar yaya Bello tayi tana faɗin bari naje na ɗora mana girkin safe dan yau naga kamar hasana batajin daɗi, 
miƙewa yaya Bello ma yayi ya nufi ɗakin sa dan ya duba jikin matar tashi, suka bar innar buba ita kaɗai, 

Maiduguri

Da gudu junior ya fito daga ɗakin su diyana na biye dashi a baya tana faɗin "wlh idan na kama ka zakayi bayani da harchen larabchi, kai tsaye ɗakin Aunty farida suka nufa, 

Aunty farida na kwamche saman katafaren gadon tana shararan barchinta chikin kwanchiyar hankali, kamar daga sama taji diran mutane a kanta, a sukwane ta farka ta miƙe zaune, ganin Aunty farida ta miƙe zaune ne yasa junior ya faɗa jikin ta yana faɗin "na ɓuya ai, dafe kai Aunty farida tayi tace "my diyana zonan ki zauna, ba musu diyana ta zauna kusa da ita ta zuba mata ido

"My diyana kina jina, gyaɗa mata kai diyana tayi alamar eh chigaba da magana Aunty farida tayi,  "my diyana yanzu fa kin girma bai kamata kina wasan guje guje ba kinji ko? Gyaɗa mata kai diyana tayi alamar taji, "good yanzu dai kutashi kuje palo ku fara breakfast ina zuwa, bari nayi wanka "Aunty farida yaushe zaki mai dani gida? Diyana ta tambaya 
"My diyana ki saurareni da kyau kiji me zan faɗa miki, gida ba yanzu zaki koma ba, anjima dady'n junior zai dauke ki kuje yamiki registration a school nasu junior, ki fara zuwa school kinaji na ko? Turo baki diyana tayi kamar zatayi kuka tace "Aunty farida nikam ina son komawa gida Allah, ina son ganin yaya Aryan dasu Ammi, 

       "My Diyana yaya Aryan fa ya koma London, dan haka ki daina tunanin sa gida kuma zamuje nan da wata 3 kinji yanzu dai kuje Aunty jummai ta zuba muku abinchi kuyi breakfast ina zuwa, 
  
Jiki ba kwari diyana ta miƙe ta riko hannu junior suka fito daga ɗakin, ajiyar zuchiya Aunty farida ta sauke kafin tace "gaskiya ina da aiki babba kafin na sauya ki my diyana, dan ba abun da kika sani sai shirme da wasa 
     A hankali ta zuro kafar ta kasa sannan ta miƙe ta nufi toilet
     

KANO 

Misalin karfe 3:10 dankareriyar family ka dake ɗauko su hiyana daga school che ta kutso kai ta chika katafaren gate ɗin gidan, kai tsaye parking space driver ya nufa, tun bai gama gashe motar ba hiyana ta buɗe kofar ta fito da sauri ta nufi part ɗin Ammi, 
Da sallama ta shigo palon betroom ɗin Ammi ta wuche kai tsaye, da sallama ɗauke a bakinta ta shiga

Ammi na zaune a bakin gadon ta, tana riƙe da littafin addu'oe, gaban ta hiyaba tazo ta tsugunna ta sunkuyar da kai kasa
 da wanna zazzakar kuma sanyayyar muryan nata tace "barka da rana Ammi, 

"Hiyana lfy bakije kin chire uniform ba eh? Ammi ta tambaya tana ɗago haɓar hiyana da hannun ta, "Ammi daman nazo in roke ki ne dan Allah ni ki mai dani kauye sai ki dawo da diyana nan, kinji ni zan iya jure duk wata wahala, kuma zan iya hakuri da halin inna da buba, na san diyana bazata iya hakuri ba kome buba ya mata zata che zata rama kuma wlh Ammi dukan mutu buba yake mata tsoro nakeji kar su kasheta shiya gara ni ki kai ni chan sai ki dawo da diyana nan.

tsabar tausayi Ammi batasan lokachin da kwalla ya chika mata ido ba har yana kokarin zubowa, gaskiya hiyana mutunche, wadda samun irinta a duniyar yanzu akoi wahala ya Allah kasa ta zama matar ɗaya daga chikin ƴaƴana

"Ki kwantar da hankalin hiyana kinji, diyana bata kauye, tana chan wajen wata kawata hajj fatima dake zaune a saudia, ammafa karki faɗawa kowa kinji ko an tambaye ki, kiche tana kauye 

ɗago blue eyes nata tayi ta ɗan saki murmushi har sai da dimple nata ya bayya, tace "to Ammi bazan faɗaba "yauwa my hiyana koke fa kinga yadda kika kara kyau da kikayi murmushi nan kuwa? To yanzu dai ki tashi kije ki chire uniform kiyi wanka kuzo kuchi abinchi, karki kara saka wata damuwa a ranki, "to kawai hiyana tace sanna ta mike da murnar ta har sauri take tanufi kofar fita

Tana tura kofar zata fita shi kuma yana shigowa karo sukayi kanta ya bugi  faffaɗar kirjinsa nan kasan chewar ya fita tsawo sosai,  waro blue eyes nata tayi nan take tafara ganin jiri, baya baya tayi tana kokarin faɗuwa..



 💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'💖

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
     👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
       by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
       by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
      by(xeemat....love)

*4, JINI DAYA*
      by(mrs bbk)





More comments an like pls
 





No comments

Powered by Blogger.