Babban Goro 3

 


Episode___3


Cikin wani irin ɓacin rai Minal ta zaburo masa 

“Who do you fucking think you are da zaka saka kazamin hannunka ka mare ni?” 

 Saif kamar jira yayi cikinta da matsifa 

“Quiet silly little stupid girl taya zaki rik'a fadawa Mahaifiyarki waɗannnan kalaman bakisan darajar iyaye ba ko or maybe baki da hankali” 

Da karfi tace 

“Nayi ni ba mahaukaciya bace nayi saboda ina da damar yin haka get the hell out of here here” 

Zai sake magana Dr. Salamatu ta rik'e mashi hannu 

“Ka barta tayi duk abinda take so tana da damar yin duk abinda take so” 

Cike da mamaki Saif ya kalleta 

“Kinsan abinda kike faɗa kuwa yarki ce fa ke kika haifeta ba ita ta haife ki ba ko dai kin manta ne?” 

“Please Saif let her b thanks for the Concern” 

Taɓe baki yayi ya janye hannunshi daga rik'on da tayi mishi ya juya ya fice, 

    Yana fita Dr. Salamatu ta nufo Minal tana bata hak'uri

 “I am so sorry dear i.. -” 

Hannun Minal ta ɗaga mata hakan yasa ta kasa k'arasa maganar... 

“You too Mom please just go” 

Yatsanta ta shiga murzawa “Please Minal ki fahimceni mana banyi hakan dan na cutar da rayuwar ki ba nima bada son raina hakan ya faru ba inason ki kwantar da hankalinki nayi miki bayanin komai”

Hannu Minal ta kai ta danna wata yar karamar ɗanja ja dake gefen gadonta, nan take ɗakin ya ɗauki k'ara cikin mintunan da basu fi 3 ba likitoci suka shigo tare da nurses, 

Dafe kai Minal tayi tana kallonsu 

“Dan Allah ku fitar dani daga nan bana son ganinta” 

 Da sauri wata daga cikin likitocin wadda nake zaton bahaushiya ce ta kalli Dr. Salamatu,

“Dan Allah Hajiya ki ɗan bata guri for now tana muna bukatar natsuwar ta” 

Kai kawai Dr. Salamatu ta ɗaga ta juya ta fice tana hawaye, 

   Tana fitowa wata daga cikin matan dake tare da ita ta dafata tana tambayar lafiyar Minal, 

Kasa magana tayi saboda kukan da ya ci karfinta, nan suka shiga tambayarta ko lafiya duk hankalinsu ya tashi, 

sai da tayi mai isarta sannan ta share hawaye ta ta ɗauki Jakarta tana faɗin

 “Babu komai Minal kuma taji sauki” 

Tana kaiwa nan ta nufi hanyar fita su kuma suka rufa mata baya, 


         A k'ofar Emergency suka tararda Saif tsaye kamar mai jiran fitowarsu, Tsayawa Dr. Salamatu tayi dai-daishi sannan ta kalli matan dake tare da ita tace “Kuje gurin mota”

 Ba musu suka nufi gurin motar 

Sai da suka fice sannan ta kalli Saif zatayi magana ya rigata 

“I'm sorry to ask you miyasa yarki ta tsaneki kuma tayi kokarin kashe kanta?” 

Wani dogon numfashi taja tare haɗiye wasu yawu da karfi 

“Kace wai Mr President na gode sosai da kulawarshi kuma kace taji sauki ina mika mashi gaisuwar ban girma” 

Bata tsaya jiran abunda zai sake cewa ba tayi tafiyar ta 

   Ajiyar zuciya ya sauke ya ɗaga kafaɗunshi,

_Toh wai miye na damuwa da sanin dalilin koma minene ai can su suka sani nidai nayi abinda ya kawo ni_

A zuci yayi wannan maganar yasa hannayenshi aljihu ya fice. 



                         MINAL.... 

Sai da suka tabbatar da hankalinta ya kwanta sannan suka fice suka bar mata wata nurse guda ɗaya, tana haɗa mata tea, 

   “Please brought borrow me your phone” 

Ta tambaya tana matsar gurin da akayi mata karin ruwa, 

Juyowa nurse ɗin tayi ta kalleta tana murmushi tace “OK but you should drink this tea first” 

 Ta k'arasa maganar tare da mika mata tea ɗin, ba musu ta karɓa ta kai baki, sai da ta shanye shi kaf sannan ta dire kofin tana shafe bakinta,

     Hannu naga nurse ɗin tasa ciki aljihu ta ciro wayar ta mika mata, da sauri ta karɓa tana mata godiya "Thank you” 

Murmushi Nurse ɗin tayi “Your welcome” 

Sannan ta juya ta fice, 

  Wasu numbers Minal tasa guda goma sha ɗaya sannan ta danna calling.

Ringing tayi har ta katse ba'a ɗauka ba nan ta sake bugawa, 

“Com-on pink the call pink the call” 

Abinda take faɗa Kenan tana yarfar da hannu, 

Sai da ta kusa katsewa sannan aka ɗauka cikin rawar murya ta soma magana 

“Hello Deen ina asibiti yanzu haka” 

Shiru tayi can kuma tace 

“I need to see you Deen urgent” 

Banji mi aka ce mata ba na dai ji tace 

“Ok” 

Ta kashe wayar, 

Ido ta tsurawa tana shafa gashin kanta,


27 MINUTES LATER.... 

Aka turo kofar ɗakin aka shigo

 “Deen” 

Abinda wadda ya shigo kenan ya faɗa yana kokarin maida kofar, 

 Ganin tana unkurin saukowa yasa shi yin saurin k'arasa kusa da ita ya zauna saman godon suka rike hannayen juna, 

       Nan da nan idonta suka kawo ruwa nan ya ware hannunshi na dama ya shafa gefen fuskarta 

“Kinyi unkurin kashe kanki Deen why kinsan da kin mutun kin mutu kafira kenan kuma ba zaki sake ganin kowa ba.?”

   Hawaye ne suka zubo mata “Bansa abinda zanyi ba na tsani rayuwata ne...”

Fashewa tayi da kuka mai karfi har lips ďinta na rawa, 

    Rumgume ta yayi yana faɗin

 “I love you Deen faɗa min mi yasa kikayi unkurin kashe kanki?” 

“Not now Deen bana son maganar a yanzu zan faɗa maka wani lokacin” 

  Kanta ya shafa “Kenan as you wish” 

Shiru ne ya biyo baya babu wadda ya sake cewa wani abu har na tsayon lokaci, 

    Can ta ɗago kai ta kalleshi “Deen bana son zama Kasar nan duk jin nake ta ishe ni zan iya aikata komai idan ina ciki bana son kusanci da Mummy” 

“Kina son barin kasar ne?”

“Yes kuma yau yau ɗin nan Please kuma bana son kowa ya sani” 

  “Ok but not today dan kinga yanzu ko fitarki cikin asibitin nan aiki ne dole sai na samu abokina yayi min hanya kuma yanzu ba lalle bane a samu jirgi ba, but i promise you da safe zaki bar kasar nan” 

Kai ta ɗaga mishi “Ok in the early kuma bana son Mummy ta sani just between us please”

Fuskarta ya rik'a da hannayensa biyu,

“Anything for our friendship do you want me to a company you?”

  “No me along”

Ta bashi amsa tana kokarin kwantar da kanta saman jikinta,

No comments

Powered by Blogger.