The Sexy Boss 6

 


*F*



*Littafin THE SEXY BOSS na kuɗi ne ban yarda ki karanta mun ba tare da kin biyani haƙƙi na ba... Regular group ₦300...Vip group₦500... Special ₦1000 via 6037312299 Mohammed Aisha keystone bank ko kuma ki tura katin MTN ta wannan number

08081202932 Idan VTU transfer zakiyi ki tura kai tsaye ta wannan number 09061466409*



Eh har nan Wurin zanyi mawa Allura.! Saurin kallon sa Umaima tayi ganin yanda Yake maganan da gaskiyar sa babu wasa ,sai shafan Wurin yake kaman mai Son jin wani Abu sabo . A'a nidai Ban taɓa jin hakan ba , wallahi ko a labarai , ya za'a yi kamun allura anan? Dama na daɗe da jin labaran wasu mutane masu cire sassan jikin ɗan Adam da Ransu ,to sai dai idan kaima kana ciki . Kuka ta saki masa wanda dariya ya kusa kuɓce masa ,don yanzu idan tana kukan dariya ma take bashi . Maida dariyar nasa yayi yana kallon ta tare da sauraren me kuma zata cigaba da cewa " Jan majina tayi tana cewa " Wallahi ka tuna da ALLAH ,idan ka cuceni Ni baiwar sace ,ALLAH zai saka mun , duk wani mulki da ƙarfin da kake dashi bai kai gana ALLAH ba shine wanda ya halicce mu nida kai duka . Kuma a wata rana dole zamu koma garesa komai mu ka aikata yana kallon mu ,mai ƙyau ko mai muni . Shiru yayi ya kasa kauda hannun sa daga Durin nata ,kuma ya kasa sarrafa komai na jikin nata , sakamakon maganganun nasa yasakar gwiwa ,ji yayi jikin sa yayi sanyi.  Kusan minti uku yana jin shashsheƙar ta , ke wannan kukan fa na meye? Yayi maganan kaman bashi ɗin ne yasata kukan ba. Cigaba Umaima tayi da kukan ta ,don ta fuskanci Umair shahararren ɗan duniya kamin ta kuma tsinkayar Muryar sa yana cewa " Duk akan Allura kike kuka? Ko ku kuwa tunanin ki ba'a allura a nan ? Yayi maganan yana matsa Famin Virgina ɗin ta da yayi mata , saurin rintse ido tayi tana faɗin Ashhh". It's ohk ". Yayi maganan yana cire hannun sa daga wurin , kamin ya cigaba da cewa " Waya ce Maki baa Allura Anan wurin , ranan da kika haife mana baby to Ni da kaina zan ɗinka ki... wani irin fiddo da ido Umaima tayi na mamakin rainin wayon da yake mata , wato bazai barta ta koma gida ba sai ta haifa masa yaro . Amma  yanxu magani zaki sha kinji Matana". 


Ji yayi ta sakin masa wani irin kuka da bai san dalilin zuwan shi ba , Cikin kuka take faɗin " Don ALLAH ka maida Ni gidan mu , wallahi ni yarinya ce bazan iya haihuwa ba ,mutuwa zanyi kashe Ni xakayi . Amma kuma kike da Wanda zaki Aura? . Saurin kallon sa tayi kamin tayi magana ne yace " bafa wani ya faɗa mun ke da bakin ki kika faɗa . Ki cire wa kanki Son Auren kowa , Ni zaki aura ai mugun baki kika yi mun wanda babu wanda ya taɓa mun irin shi , don haka dake zan zauna har sai maganan taki ta tabbata shahararrar mara kunya . Yayi maganan yana ɗaga hannu kaman zai sauke yatsun sa a kuncin ta . Rintse ido tayi da ƙarfi don ta sadakar da marin ta zaiyi . Tashi muje ki gasa jikin ki , ki taho kici Abinci. A hankali ta fara ƙoƙarin miƙewa ,amma ta kasa ganin haka yasa shi ɗaukar ta cak yana nufar privacy da ita tare da cewa " Ki saki jikin ki daren yau ma irin haka zan ƙara Maki. 


***


Ganin Hajiya Turai da wannan yammaci yasa Ammie Maryam cike da mamaki saurin muskutawa tana faɗin " Lale maraba Barka da saukar baƙin dare. Fareesa ce ke bin bayan Hajiya Turai yayin da Surayya dake tare da Ammie Maryam ta nufe Hajiya Turai da gudu tana hugging ɗin ta tare da faɗin " Oyoyo Mummy . Murmushi Hajiya Turai tayi tana shafa kan Surayya kamin tace " Ke wato kin guje ni ko? , A'a Mummy Dama ina shirya zuwa a satin nan . Hummmm to ai shikenan ina nan ina baza idanu . Dariya Surayya tayi tana komawa mazaunin ta kusa Da Ammie tana zama. Fareesa ita ma na nufo Ammie Tare da gaishe ta . Muryar Hajiya Turai ne ya katse su tana cewa " Eh Ammien Umair kin ganni da wannan daren, nima wani labari ne ya tadani zaune tsaye da ya riskoni ,sai ina ganin Abun kamar ƙarya ce da sharrin da Al'umma suka saba . Kamin Hajiya Turai ta numfasa ne Ammie tace " Akan Umair ko?. Ƙwarai kuwa. Ai na sani dama kullum a haka ake . Meke faruwa Hajiya?. 


Nisawa Hajiya Turai tayi tana gyara zama tare da labarta nawa Ammie duk abun da taji daga Bakin Ru'aifa ƴar leƙar asirin ta .  Sauke numfashi Ammie tayi kana tace " Ina tunanin wannan Shirmen mutane ne kawai , babu yanda za'a yi ɗana yayi Aure ba tare da sani na ba ,haka kema ba tare da sanin ki ba Hajiya , amma ina tunanin wani Abu dabam ,ina zuwa . Hannun ta Ammie takai tana ɗaukar wayar ta dake a gyefen ta . A hankali tafara latsawa tana karawa a kunnen ta . Kiran Umair tayi dai dai lokacin da yake bamawa Umaima Exercise tana hawa stairs ɗin falon da sauka ,don ya bata abinci tasha magani a yanxu so yake ƙafafuwan nata su saki .  Ganin ta tsaya tana maida numfashi don ta kai ta kawo yafi sau goma , yanzu ita ba ƙafan bane ya ke a riƙe ,zafin hawa da saukar ya dameta . Tsayawa tayi tana matso ƙwallah a zuciyar ta tana furta mugu azzalumi . Gani yayi bakin ta na motsi wanda tabbas yasan ƙunƙuni take wannan yasa shi hayewa stairs na uku yana facing ɗin fuskar ta . Cikin sauri ta juya ƙasa zata cigaba ,jin hannun sa tayi ya riƙo nata hannun . Cak ta tsaya zuciyar ta na bugawa dam³ . Juyowan da yayi da ita ne taji jikin ta na gogar nashi tana fuskantar shi , ƙirjinta da nashi suna gab da shafan juna , saurin kallon dogon rigar ta na English wears tayi , kana tayi baya cikin sauri tana cewa " Cigaba fa zanyi. Hannun sa yakai yana rungumo ta jikin shi tare da shafa bayan ta , kawai jin kansa yayi da yi mata hakan ba tare da ya san dalilin sa ba. Umaima zaki Aure Ni??. Wani girrrr yaji , wannan yasa shi saurin raba jikin shi da nata jin Kirar da ya shigo masa . Ɗaukar phone ɗin nasa yayi ba tare da ya kara a kunnen sa ba ,don ya ɗauke da maɗaukar magana a kunnen sa . Ammie Barka da dare . 



Yowa Umair ya kake ya ayyukan? Alhmdllh Ammie. Daddy ya dawo ne?. A'a kasan yana gidan Hajiya Turai . Ohk " . Yayi maganan tare da barin wancen . Umair wani labari naji , Wai ance kayi Aure har da mata bamu sani ba. Shiru yayi cike da miskilanci n sa , kun san dama wa'annan muskilallun idan kuka ga sunyi shiru ,to zurfin tunanin da suke yi fi na mai yawan zuba kaman jarida. Ammie me ya faru wa ya faɗa maki?. Kai tsaye Ammie ta faɗa masa Hajiya Turai ce... Wani Murmushi yayi yana tunanin wato Ru'aifa ta hannun Hajiya Turai ta tazo wurin sa . Ohk Ammie that's not real ,ba gaskiya bace , Amma soon zai zama gaskiya ,ina so zan Auri wannan yarinyar da kika kawo mun a matsayin cleaner . Ohk wannan shine gaskiyar al'amarin eh Ammie . Yayi maganan kan sa tsaye . Kana kusa Da Umaima n ka bata mu gaisa . 



Wani irin bugawa ƙirjin Hajiya Turai yayi da take gyefe , wato da gaske ne kenan, abun da take fadi a zuciyar ta kenan. Kallon Umaima yayi da ta faɗa duniyar tunanin Umma da gida , ji tayi ya sunkuyo yana haɗa bakin ta da nashi tare da manna mata wani irin Kissing , cikin sauri ta ɗago tana kallon shi , ɗan haɗe gira yayi na Arrogant Yana ɗaure fuska kaman bashi yayi mata kiss ɗin. Ammie zata yi magana dake . Yayi maganan yana katsewa . Can kuma sai ya kara kirar Ammie tare da manna mata a kunnen ta . Riƙe ko Ni zan riƙe maki ,tun da ina Son kiyi magana da Ammie na".

No comments

Powered by Blogger.