Saran Boye 76


 No. 75


.............Su Jay dai sun wuce abuja, amma  duk da su Addah na a asibiti suna a ƙarƙashin kulawar hukuma ne. Bayan wucewar su Jay shi ma Omar da Yoohan suka wuce da yamma. Ya bar Nu'aymah anan kano saboda Umm bata da lafiya. Har yanzu ta kasa fida daga ruɗanin data shiga. Ga jininta yaƙi sauka yanda ya kamata.

Ita kanta hajjo jininta ya hau sosai. Sai dai ita Alhmdllh bai kai na Umm da komai yazo mata a yanda bata zata ba. Bama Umm kaɗai ba hatta da ƴan uwan Umm dana Addar wannan al'amari yay masifar rikita tunaninsu da basu tsoro. Anatama Addah ALLAH wadarai da wannan hali nata. Su Hajarah kam sunyi kuka har sun rasa hawayen zubarwa. Musamman Kubrah da dama ba daɗin zaman gidan mijin take jiba. Fitinar yau daban ta gobe daban.

      Yanda gidan dai yay wani iri daga shigowa zaga fahimci akwai matsala. Baba malam salla kawai ke fiddashi. Da an idar yake dawowa gida. Komansa ya tsaya cak. Dan duk da daurewar da yakeyi a bala'in gigice ya ke da al'amarin. Bai taɓa ƙawowa a ransa cikin ƴan uwansa za'a samu mai wannan tunaninba akan dukiya dauɗar duniya. Yayi kuka bana wasaba a ɓoye, har ji yake gaba ɗaya ƙasar ta fita masa a arai.


___________★★


        Su Yoohan na isa Abuja suka iske sabon tashin hankali. Dan sun iske gidansu zagaye da jami'an tsaro. Da ƙyar ma aka barsu suka shiga saboda sanin Yoohan ɗansa ne. Cikin tashin hankali Yoohan ya ƙarasa falon inda ya tarar da ƙannensa duka da mama debora a hagitse. Suna ganinsa kuwa duk suka taso kansa a guje suna rusar kuka. Su duka rungumeshi sukayi har mama debora da Gebrail dake gudunsa a da.

     Kallonsu kawai Yoohan keyi cike da tsoro, maganama ya kasa yi. Sai da Umar yay dauriyar cewa, “Granny wai mike faruwa hakane? Ku sanar mana Please. Gida zagaye da ƴan sanda. Gaku kuma cikin tashin hankali. Ina su papa suke ne?”.

        Cikin matsanancin kuka joy tace, “Sun gudu Brother Richard”.

       “Sun gudu kamarya? Ban ganeba nikam Joy?”.

      Sakin Yoohan duk sukayi, mama debora ta kama hannunsa ta zaunar a kusa da ita. Shima Umar ɗin ya zauna. Sauran yaranma duk zama sukayi bisa umarnin mama debora. Tana sharar hawaye ta fara musu bayani.

         “John munata kiran wayarka tun jiya ai amma mun kasa samunka. daren shekaran jiya kusan ƙarfe goma na dare wani mutum ya shigo gidan nan a kiɗime jikinsa jina-jina saboda harbi da akai masa. Lokacin duk munyi barci, kururuwarsa ta sakamu tashi batare da mun shirya ba duk muka fita compound. Tun a yanda mahaifinku ya ambaci sunansa a kiɗime na fahimci ya sanshi. Dan gaba ɗaya ya ruɗe shi da Chioma da guards ɗinsu. Shine ya sakamu komawa ciki akan dole batare da munji mike tafe da wannan mutumi dake a cikin jini ba. Muna falo tsaitsaye mun kasa komawa ciki mu kwanta sai ga shi sun shigo. Duk ɗakunansu suka shiga batare da sunce mana komaiba. Sai kuma suka sake fitowa a rikice. Mahaifinku ya rungumeni yana faɗin, karna damu na masu addu'a kawai, ga ATM card ɗinsa nan duk abinda muke buƙata Gebrail zai dinga ciro mana kuɗi. Daga haka suka fice zuwa garden. Ban taɓa sanin akwai wata hanyar fita gidannan ta garden ba sai a ranar. Dan sai bayan wucewarsu da kusan mintuna talatin ƴan sanda suka shigo anguwarnan sunata harbe-harbe. wasu suka shigo nan gidan suna nemansu harda guards ɗinkun nan. Sai lokacin mukasan guduwa sukayi harsu Solomon. Amma an kama guards uku a cikinsu. Su kuma ba'asan inda sukeba har yanzun”.

       Wata irin masifaffiyar zufa ce ke ketoma Yoohan ta ko ina, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un yaketa faman maimaitawa. Shi kansa Umar zancen yay masifar rikita tunaninsa. Batare da Yoohan yace komaiba ya kama hannun Umar suka haye sama. Duk binsu sukai da kallon mamakin mizaiyi?. Bai saki hannun Umar ba sai da suka shiga sashensa can cikin ɗakin motsa jikinsa. Inda tanan yana iya hango duka ƴan sandan dake a compound ɗin gidan da anguwar ma.

          Cikin matsanancin fushi ya yarfar da hannun Umar sannan ya tsatstsare sa da jajayen idanunsa. Muryarsa da tsananin kaushi da fushi yace, “Umar mi kuke ɓoye min kai da Matata akan iyayena?. kar kaimin ƙarya, dan ba ita nake buƙataba a yanzu na roƙe ka”.

      Yanda ya ƙare maganar muryarsa na rawa kamar zaiyi kuka da haɗe hannayensa waje guda kuma sai zuciyar Umar ta ƙara raunana. Hannayen ya riƙe duka a cikin nasa ya sauke. “Yoohan anzo gaɓar da basai ka roƙeniba zan sanar maka. Sai dai inason ka fahimceni Please. Nima bani da wani zaɓin daya wuce hakan”.

     Komai Yoohan bai ceba, saima cire rigarsa da yayi ya hau wani machine ɗin motsa jiki ya fara da sauri-sauri. Huci Omar ya sauke tare da fara bama Yoohan labari. Tun daga abinda ya fara ji akan kashe Nu'aymah da papa ya bama Dr Mateo kwangila har zuwa ɓoyayyun harƙalloli daya fahimci papa nayi a ɓoye. Kamar safarar miyagun ƙwayoyi da cocaine. Safarar makamai, satar yara yana tarasu a wani gida acan ƙauyensu........

       Ihunsu Mama debora daya cika gidanne ya saka Yoohan dan Umar fita da gudu zuwa ƙasa.

     Cike da firgici da tsoro Yoohan da Umar ke kallon Little bee da tawagar jami'an hukumarsu. Ta haɗe fuska matuƙa, babuma alamar tasansu. A fusace Yoohan yace, “Lafiya kuwa?”.

      Uffan Little bee batace masa ba. Sai ma i'd card ɗinta kawai ta nuna masa. Sannan ta ɗora da faɗin, “Muna buƙatar shiga ɗakin Mr Goshpower domin yin bincike”.

     Magana Yoohan zai sakeyi Umar ya girgiza masa kai alamar karya ce komai. Hannayensa duka biyu ya tura cikin aljihun wandansa ya koma jikin bango ya jingina saboda jiwa dake neman yaddashi a ƙasa.

      Da Gebrail sukai amfani ta hanyar ɗora masa bindiga akai. Tuni fitsari ya jiƙe gaban wandonsa kuwa. Babuko kwana-kwana wajen kaisu har sashen papa. Tun a falo suka fara bincikensu. Yoohan baiyi niyar binsu ba, amma sai Omar ya kama hannunsa suka shiga. Basu sami komai a falon ba sai cctv dake a ɓoye. dan haka suka wuce cikin bedroom. Akan idon su Yoohan akaima ɗakin dalla-dalla. Ta hanyar tsabar ƙwarewar aiki su little suka gano ɓoyayyar drawer ɗin nan ta sirri dake a jikin bango. Sai dai kuma garƙame take da security, gashi kuma basu sani ba. An gwada password kala-kala baiyiba. Daga ƙarshe suka yanke shawarar yin amfani da na'urar fasa ƙarfe ko wane irine. Ta wannan hanyar aka fasa wajen. Sosai Yoohan ya firgita da ganin kalolin bindigu, da harsasai kala-kala. Sai tarin hodar ibilis da ƙwayoyin shaye-shaye masu matuƙar haɗari. 

      Kasa daurewa Yoohan yayi, sai da ya furzar da wani zazzafan hucin da sai da kowa ya juyo ya kallesa. An ƙara bibbincika ɗakin sosai kafin su kwashe duka kayan da suka samu ɗin sannan suka sakko ƙasa inda su mama debora keta faman kuka. Ganin makaman kuma ya sake rikitasu fiye da farko.

         Koda suka fito sai suka shiga bincike gaba ɗaya lungu da saƙo na gidan, su dai su Yoohan suna binsu ne kawai da idanu. Sai da suka tabbatar da basu sake samun komaiba sannan suka tattara waɗanda suka samu ɗin zuwa mota. Sun buƙaci tafiya da wasu a cikinsu zuwa asalin ƙauyen su Yoohan ɗin, zakuma su cigaba da riƙesu har sai papa da madam Chioma sun bayayana kansu. 

      A take falon ya sake ruɗewa da kukan su mama debora. Ganin yanda suke neman fita hayyacinsu Yoohan ya ce zai bisu kawai shi da Gebrail. Kuka harda kururuwa Gebrail ya fashe da shi. Abun zat-tausayi zad-dariya. Haka su Mama debora naji na gani aka wuce da Gebrail daketa kwasar kuka da Yoohan.

       Yoohan bai sake fahimtar al'amarin mahaifin nasu babba bane sai da suka iso airport, anan ma wasu jami'an suka tarar da alama jiran isowarsu sukeyi. Babu wani tsayawa ya akai ya za'ai aka shiga da su jirgi. Gebrail na nane da Yoohan cikin tashin hankali. Koda suka isa canma sun iske wasu jami'an tare da helicopters biyu. Nanma babu ɓata lokaci suka shiga zuwa can ƙauyensu. A canma sun iske garin a ruɗe sosai, dan uban batakashi akeyi tsakanin jami'an tsaro da yaran su papa. Gaba ɗaya ƙauyen a harmutse yake, dole aka bar su Yoohan a helicopter ɗin su little kawai suka firfita suma da nasu bindugun. Sai a yanzu ne fuskar Yoohan ta nuna tsantsar ruɗani. Gaba ɗaya komansa ya sare akan wannan al'amari. Lallai da alama mahaifin nasu ya jima cikin wannan mummunar harkar batare da su sun sani ba. Haba no wander yake ganin mahaukatan kuɗi basa gajiya da shiga accaunt ɗin papa. Sannan sam bayajin fargaba ko ciwon fitar da kuɗi wajen musu hidima ta bajinta.

    Kallo dai iya kallo su Yoohan sun yisa. Daga ƙarshe su Little bee suka sami nasarar cafke gaba ɗaya yaran papa da su Uncle Godwin da aka ritsa a garin tun jiya. wasu sun sami raunika, wasu ko ma an kashesu. A cikin su little ma wasu sun sami raunuka.

      Daga haka aka fasa ƙaton gidan da su papa ke ajiye yaran da suka sato ciki. ‘Hazbunallah’. Yarane mata da kananu, sai wasu baƙaƙen ƙartan bayi da kallonsu kawai ya ishi mutum amai, wasu da tsohon ciki, wasu cikin ƙananu ne, wasu kuma suna a tsaka tsaki. Sai jariran da aka haifa da har an gama cinikinsu ga masu buƙatarsu.

        Tsabar tashin hankali little sai da tayi kuka ita da sauran ƴan uwanta jami'ai mata. A take Dawood yay kiran Jay ya tabbatar masa al'amarinfa babbane gaskiya. Ga ƴan jarida sunyi caa suna neman bayanai. Kamar yanda I.G na ƴan sanda ya kasance a wajen dole Jay ma ya taho ƙauyen da tawagarsa su Hafeez. Hakama gwamnan jihar dole ya shigo ƙauyen, dan kuwa kowa yasan da taimakon su papa ya hau mulki. Dan papa nada matuƙar ƙarfi cikin jahar tasu musamman daya kasance yana riƙe da muƙamin shugaba (Pastor).

      Dole aka kawo manya-manyan motocin guda uku aka kwashe kaf mutanen dake gidan zuwa can babban birnin jihar. Su Dawood kuma suka shiga yima gidan filla-filla da bincike ta ko ina. daga haka suka sake kwasar jiki zuwa ainahin family house ɗin su Yoohan ɗin da suke zama idan sunzo garin. Ananma an samu abubuwa da dama, harda ɗakin sirri dake danƙare da Computers da suke gudanar da ayyukansu na yima mutane kutse, da zuba uwar sata a asusun bankuna dana mutane. A takaice dai papa shugabane mai zaman kansa na ƴan Yahoo.

      Tuni zuciyar Yoohan ta gama bushewa tayi tauri akan wannan al'amarin. Binsu kawai yake da kallo tamkar mai kallon film a television. Shi ba zuwa ƙauyen yakeba sosai saboda karatun daya tafi ƙasashen ƙetare yayi. Bayan ya kammala kuma aikinsa baya bari sa samun nutsuwar irin waɗan nan ziyarce-ziyarcen. Idan ka gansa a ƙauyen sai lokacin Christmas da hutun ƙarshen shekara. Wannan kam a ko ina yake a duniya dolene sai yazo bisa sharaɗin papa. koda baizo Christmas ba zaizo a kwanakin ƙarshen shekara yayi new year. To mafi yawancin lokaci ma sai dai ya samesu anan. Bai taɓa damuwa da sanin sarrin duka gidanba. Iyakacinsa ɗakinsa da garden. Sai ko compound. Yawo ma a ƙauyen sai idan su Osin na tare da shine yake fitarsa. Amma shi kaɗai baya zuwa ko ina. Yafi buƙatar yay zamansa a gida.


      Tone-tone dai kam an yisu a ranar game da sirrikan papa masu ban mamaki da tsoro. Hakan yasa su Jay fahimtar riƙe su Yoohan bazai taɓa saka Papa kawo kansa hannun hukumaba. Dan haka suka sallamesu su koma gida kawai. Dan aikine babba wannan ya wuce wasan yara. Shi dai Gebrail yaji daɗin barinsu da akayi. Yoohan kam gaba ɗaya kansama ba aiki yakeba a wannan lokacin. Dan brain ɗinsa ta toshe.

         Tun a wannan daren ƴan jarida da masu alhakin faɗin albarkacin baki suka fara kayayatu. Inda ƙungiyar catholic tai azamar fara fitowa ta banbanta tafiyarta data goshpower. Sun tabbatarma duniya bada yawunsu ko saninsu yake aikata duk wannan al'amarin ba. Hakama gwamnan jiharsu da manyan ƴan siyasa sun fito sun nisanta kansu da papan kai tsaye.

     Tofa abin magana ya samu lallai da gaske. Dan ƙasar tuni ta ɗauka tare da kafafen yaɗa labarai na televisions da redios. Yanar gizo dama duk wata kafar maida yanda akayi. Videos ɗin da wasu a cikin ƴan ƙauyen sukai ƙarfin halin ɗauka tuni ya fara yawo a yanar gizo. Yayinda ƴan jaridu suka fara tabbatar da cewar mafi yawan yaran da aka samu a gidan nasu papa yarane da aka sata daga arewacin ƙasar. Ƙalilanne a cikinsu suka fito daga kudanci. Tofa magana ta girma.


__________★★


        Baba malam ne ya fara cin karo da wannan babban al'amari a labaran ƙarfe goma na dare da yake kallo. Sai ga Nu'aymah data shigo kawo masa shayin da rabi ta dafa masa dan baya iya cin abinci sosai itama ta ganema idanunta.

     Da ga ita har baba malam ɗin kasa magana sukai, sai tv da suka zubama idanu da tsananin mamaki da al'ajabi. Ganin tayi tsaye ta kasa zama baba malam yace ta zauna saboda ba ita kaɗai bace. Zama tai a kujera jikinta har rawa yake saboda ganin yanda aketa bata kashin ruwan harsasai a ƙauyen su papa da aka nuna. Idonta bai ganar mata Yoohan ba sai lokacin da akaje family house ɗinsu. Anan kuma Umm ma ta fito ta samesu. Duk da batajin ƙarfin jikinta itama saita zauna zaman kallo.

       Can sai ga Hajjo a rikice itama ta shigo tana ƙwalama baba malam kira. Sai da Rabi ta sanar mata yana falonsa sannan ta nufo nan. Tunkan ta shigo ta fara faɗin, “Ɗan malam kaga kuwa tsiyatakun da aka tono yau na surikinka?”. Tana ida shigowa taga suma abinda suke kallo kenan ta shiga tafa hannu da jera salati. A kusa da Nu'aymah ta zauna suka cigaba da kallon tare.

       Kafin kace mi sai ga kiraye-kirayen waya sun fara shigoma Baba malam a wayoyi. Yasan kwanan zancen, dan haka yaƙi ɗaga wayar kowa. Kansama gaba ɗaya sai ya ƙara ɗaukar zafi. duk da yasan papa riƙaƙen ɗan harƙalla ne baiyi xaton al'amarin ya kai haka girma ba. Dan yasan papa ne shekaru ashirin da takwas da suka shuɗe a jami'ar ƙasar France, lokacin yana haɗa degree ɗinsa na biyu a can. Shima papan yazo ne wani course na wata tara. Tunda yazo makarantar a tantirinsa yazo dama. Dan karatunma asha ruwan tsuntsaye yake masa. Duk wasu abokan banza zaka samu papa da su, dan adalilin takurama wata yarinya mai suna Sadiya ƴar ƙasar Niger da papan yayi akan dole sai tayi soyayya da shine ya zama sanadiyyar sanin juna da sukai da baba malam ɗin. Kasancewar baba malam shine shugaban mss na makarantar a lokacin duk da ba wani ƙarfi ne dasu ba sai yay tsaye a kan lamarin papa da Sadiya. yayma papa gargaɗi sosai akan ya fita harkar yarinya ya barta tai karatunta. Idan ba hakaba kuma zai ɗauki mataki a kansa. A lokacin papa baice komaiba sai dariya da suka shiga sheƙawa shi da yaransa suna busama baba malam hayaƙin taba da suke sha. Baba malam dai ya ja musu gargaɗi ya kama gabansa. Ba'a rufa wata ɗaya da wannan al'amari ba tsakanin papa da baba malam sai baba malam yaga wai papa  ya zama Pastor. Harma yana kula da church ɗin cikin jami'ar. Abin ya ɗaure kan baba malam sosai, dan ya fahimci lallai da biyu goshpower ya samo wannan muƙamin.

      Baba malam dai baice komaiba, dan sunama haɗa kwanaki sama da takwas basu haɗuba kasancewar kowa da sabgar gabansa. Sai dai tunda Goshpower ya zama Pastor a cikin jami'ar ƴar tsama mai ƙarfi ta shiga tsakaninsa da baba malam. a kuma lokacin akaima Sadiya fyaɗe tare da kasheta. Wannan al'amari yayi masifar girgiza baba malam dama sauran musulmai da suke a jami'ar. Dan kowa yasan goshpower ne zai iya aikata hakan ga sadiya. Su baba malam sun kai ƙararsa ga hukumar makaranta, an kuma amshi ƙorafinsu a zahiri, amma babu alamar za'a ɗauki wani mataki. Hakanne ya harzuƙa zuciyar baba malam yaje ya samu Pastor goshpower da kausasan maganganu. Amma abin mamaki ko ɗar papa baiyiba. Hasalima da bakinsa ya sake jaddadama baba malam cewar shine yayma Sadiya fyaɗe ya kuma kasheta. Tunda taƙi yarda ta bashi kanta da arziƙi shiyyasa ya ƙwata da ƙarfi dan yana ƙwaɗayinta sosai. Kasheta kuma da yayi yayine dan yaga mi baba malam ɗin ya isa yayi?.

       Baba malam akwai zuciya, hakan yasa a take ya fara dukan goshpower da iya ƙarfinsa. Kafin kace mi makaranta ta ruɗe da ihun ɗaliban dake ta wajen da abin ke faruwa. Kowa yayi mamakin yanda baba malam ke dukan goshpower. Dan babu wanda yay tsammanin zaiyi wannan ƙarfin. Musamman da ake ganinsa shiru-shiru baida kwaramniya sam a cikin ɗalibai. Hasalima ko ƙwaƙwaran aboki baida shi. Jina jina baba malam yayma papa a wannan lokacin, dan da ƙyar security ɗin makaranta suka amshi goshpower a hannun baba malam. Harma wasu na tsammani da zaton papa ya mutu.

     Kwana biyu da yin wannan rikici abin mamaki sai ga takardar sallama baba malam ya samu daga hukumar makaranta. Babu wanda yay kiransu ya zauna dasu domin neman ba'asin yanda akayi? Musulman ɗalibai dake makarantar hankalinsu ya tashi akan wannan rashin adalci da akaima baba malam. Amma sai shi baba malam ɗin ko a jikinsa. Dan dama koda basu koresaba yayi alƙawarin bazai ƙarasa karatunsa a wnann makarantarba, tunda har za'a iya kashe rai suƙi nutsuwa suyi ƙwaƙwƙwara bincike akai su gano mai laifi su yanke masa hukunci. Tunda baba malam ya baro jami'ar France bai sake haɗuwa da goshpower ba sai a sanadin Yoohan. Wannan shine dalilin da yasa yay matuƙar mamaki akan papa bai isa haihuwar Yoohan ɗin ba sam. Sai dai kamar da Yoohan ke ɗanyi dashi ya sakashi yin shiru da tunanin ko acan wajen yima ƴaƴan jama'a fyaɗen ya samosa. Sai dai zuciyarsa sam bata yarda da wannan tunaninba. Musamman da yaga yanda Yoohan ke da ƙyawawan halayya abin koyi. Sai gashi a hankali ya fara fahintar akwai wani ɓoyayyen al'amari dake a tsakkiyar papa da Yoohan, daga hakane ya fara burin saka ido aka lamarin papa ta hanyar Nu'aymah da wasu ɓoyayyun hanyoyi nasa. To binciken nasa bai gama kaiwa inda yaso ɗinba Jay yazo masa da tambayoyi akan Yoohan ɗin shima. sai dai shirin nasu akan binciken papa ɗin bai ƙarasa kaiwa can ɗinba gashi ɓoyayyun halayen papan sun fito a idon duniya. 


        Tun a dare Nu'aymah ta shiga neman Yoohan amma ta gagara samunsa sam. Sai washe gari tana idar da sallar asuba ta kuma gwadawa anan ta samesa. Hankalinta ya tashi dajin muryarsa. Ta tabbatar masa ita dai zatazo abujan tunda taji kamar baida lafiya. Amma sai ya lallasheta akan tai haƙuri ta cigaba da zama a kano dan gidansu bazai zaunu a garetaba yanzu kodan halin da take ciki. Bazai yuwu taita ganin tashin hankaliba. Jin yanda yaketa lallashin natane yasa taɗanjin sassauci. Daga haka ta kira Umar dan ta ɗan ƙarajin bayanai. Shine ya tabbatar mata da karta damu Yoohan ɗin yana cikin ƙoshin lafiya damuwar abinda ya faruce kawai. Hakan kuma dolene a garesa tunda al'amarin yazo masa a bazata. 


     Baba malam ma ya kira Yoohan yay masa nasiha da kwantar masa da hankali, tare da faɗa masa yayta addu'a a ransa ALLAH zai sauƙaƙa musu waɗanan jarabawoyi da suka samesu a kusan lokaci guda.


★★★★


       Jami'an tsaro sun cigaba da neman papa, tare da zaƙulo dukkanin abokan harƙallarsa ta ƙarƙashin ƙasa. Harma waɗanda suke a ƙasashen ƙetare. Yayinda zancen yara da ake zargin mafi yawansu ƴan arewacin ƙadar ne ya tabbata. Wasu tun suna yara aka satosu, wasu ko suna a manyansu. An saida wasu ga masu buƙata. Wasu kuwa ana kaisu wasu ƙasashen ƙetare batare da sauran sunsan mi suke yi acan ba.

    Yarinyar da aka tattauna da ita tace, shekararta tara kenan a hannunsu. An satota ne a jihar Jigawa bisa hanyarta ta dawowa daga makarantar islamiyya a wani yammaci ranar litinin. Tana kuka tace, “Wani abu suka shaƙamin, wanda yasa ban sake sanin ina kaina ya keba sai a wannan gidan da kuka ganni a ciki. A randa na dawo hayyacina abinci kawai aka bani naci wani ƙato ya haikemin yaymini fyaɗe. Naga tashin hankalin rayuwa kala-kala a wannan tsakani, dan saida ta kasance kullum sai mutumin nan yayi amfani dani. Bai barniba sai da aka tabbatar da na samu ciki sannan. Sai a lokacin na fahimci ashe duk macen dake gidan hakane ke faruwa da ita. Waɗanan gardawa zasuyita amfani da ke ne har sai ka samu ciki. Ka gama wahalar rainon cikin a randa ka haihu a ranar za'a ɗauke yaron, watama ko ganin fuskar ɗan nata batayi. Kina haihuwa da sati biyu waɗan nan maza zasu koma yi miki fyaɗe har sai kin sake samun wani ciki”.

    Kuka ya sarƙeta ta kasa ci gaba. Sai da tayi sosai wasuma a jami'an tsaron na tayata, harma da ƴan jaridar dake ɗaukar rahoton. Da ƙyar ta cigaba da faɗin, “A shekara tara dana samu ni yanzu haka haihuwata takwas, dan duk shekara ƙa'idane sai ka haihu, a yanzu hakama satina baifi shida dayin wata haihuwarba. Bana tantama kuma ƙila na ƙara samun wanu cikin ma”.

       Ai Yoohan baima san sanda ya fashe da kuka ba, dan tunda yake a rayuwarsa bai taɓa cin karo da makamancin tashin hankali irin wannan ba. Sai gashi wai mahaifinsa shine tushen aikatawa. Abin takaicima harda sanin Momynsa. No wander ta mitsike idonta ta nema yin tarayya da shi duk da shiɗin ɗanta ne. A yanda yakejin zuciyarsa game da waɗannan yaran koshi ya ga Papa da Momy sai ya ɗaukesu ya damƙama hukuma ya rantse da ALLAH kuwa.


_________


      A kano ma dai su Abban Abdallah na cigaba da kasancewa a hannun kulawar likita. Duk da dai jikin nasa kam dai babu ƙyan gani dan gaskiya yanajin jiki, dan har yanzu baya iya gane kowa dake a kansa. Addah ma dai jikin nata wataran yayi sauƙi wataran yayi tsamari. Duk da tsiyatakun da suka tafkama baba malam kuma bai gaza wajen fidda kuɗaɗen da ake kula da lafiyarsuba. Sannan shiketa tausar ƴaƴansu da zantuka masu taushi, tare da ƙoƙarin ganin wannan al'amari ya zama sirri a tsakaninsu batare da sauran jama'ar gari sunsan tushensu ba.

     Abban Mustapha dai ya riga ya saki Addah, sai baba malam ya hanashi faɗa mata ita da ƴaƴanta, sunbar maganar a tsakaninsu su manyan har sai ta samu lafiya kamar yanda baba malam ya roƙa mata alfarma. Dan yanzu bai kamata a haɗa mata zafi goma da ashirinba musamman daya kasance tayi nadamar kurakuranta. Halin datake ciki kaɗai ya isheta tashin hankali mai tsanani ai.

       Aikoda gaske tashin hankalin da Abban Abdallah da Addah ke ciki ko shi kaɗai kam ya ishesu. Dan suna cikin tsananin azabar ciwo da magauta. Duk taurin zuciyarka ka gansu dole ka tausaya musu kuwa.


     Haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa. Su Adda ba faman jiyya a asibiti, jami'an tsaro na neman su papa ruwa a jallo. Masu maida yanda akayi na cigaba da tattaunawa da ƙara gishiri da magi akan al'amarin. Yayinda ƙungiyar kiristoci ma ta fito ta nuna cewar bata goyon bayan papa sam, sannan bata tare da shi. Hakama Pastors nata sharhi akan papan da tabbatarma duniya wamnan ba halin kirsata na ƙwarai bane aka samu papa da shi, dama suma ba ƙaramin matsi suke fuskanta daga garesaba ta ƙarƙashin ƙasa.


     Duk wannan cece kuce da ake famanyi suna shiga kunne papa a maɓoyarsa shi da mike, Anthony, Joshua da Solomon, sai madam Chioma. Abinda yasa aka gaza samunsu shine ajiye duk wani layin wayarsu da sukayi, dama duk abinda zaisa a iya bibiyarsu. Godwin da sauran ne ke a hannun hukuma. Duk wahalar da sukesha kuma sunƙi faɗar ina za'a samu su papa saboda basu saniba suma.


    Haka dai kwanaki suka cigaba da shuɗawa har Yoohan ya bar ƙasar saboda aikinsa, Nu'aymah ta cigaba da zama anan Nigeria bisa shawarar da baba malam ya bama Yoohan ɗin. Dan rashin kama su papa ba ƙaramin haɗari baneba. Musamman daya kasance Nu'aymah tana ɗaya daga cikin mutanen da a yanzu haka suke a cikin mummunan ƙudirinsa ita da baba malam ɗin. Yoohan kuwa yaji wannan shawarar duk da baiso yin nisa da iyalinsaba. Itama kuma Nu'aymah taji daɗin haka duk da kewar mujinta na tare da ita. A haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa cikin rahamar UBANGIJI da jin ƙansa.

       Cikin Nu'aymah ya shiga watan haihuwa, aiko su Umm nashan raki sosai da taɓara, Hajjo taita mata dariya da kiranta ragguwa. Yoohan kansa yanashan nasa shagwaɓan ta waya. Inko yazo ƙasar kuka rurus take tasasa a gaba tanayi wai itadai ta gaji wlhy a cire mata cikin nan. Takan bashi tausayi da dariya, sai dai bayayin dariyar sai yayta lallashinta da nuna nata tayi haƙuri saura ƙiris ai.

       Ai ko zuwan ƙarshe da yayi yay kusan sati ɗaya sannan ya koma, kamar jira Aymah keyi ya wuce washe gari ta tashi da naƙuda. Wayyo zo kaga raki wajen masu haihuwa. Yoohan har ALLAH ya isa sai da yasha a wannan ranar😂, takuma rantse bazata sake yarda da wani cikiba dan wannan haihuwa daga ita bazata sake ba. Tun hajjo dake tare da ita a asibiti itada Mama amaryar Abba Musbahu na danne dariyarsu har suka kasa saida sukayi. Baiwar ALLAH tako sha wahala sosai, har dai ALLAH ya sauketa lafiya ta sunkuto jaririnta dake ta faman canyara uban kuka.

        Su Dr Aysha sun gyarata tsaf da bata dukkan kulawa kodan darajar mijin aurenta da iyayenta. Shima yaro aka gyara shi tsaf sannan aka fiddoma su Hajjo shi. Kowa sai ambaton masha ALLAHU yakeyi a baki da zuciya. Yayinda Hajjo ta saka Ahmad ya kira mata Yoohan wai itace zatai masa albishir. Aiko ita dince tai masa dan ya dai gane hausar tata saboda Alhmdllh zuwa yanzun harshensa na ƙara faɗawa. Rikicewa yay gaba ɗaya, dan yasan dai hajjo bazata faɗa masa Nu'aymah ta haihu ba danta zolayesa. Sai kawai ya durƙusa yay sujidar godiya ga ALLAH. Duk da a ransa yaji babu daɗi da sai da ya taho ta haihu. Sauƙinsa ma zai tafi hutun ƙarshen shekarane daman dan al'umar Christians nata shirin bikin Christmas.


         Zuwa dare aka sallami su Nu'aymah da ɗan jinjirinta bayan an tabbatar da ingancin lafiyarsu, kai tsaye sashen hajjo aka nufa da Nu'aymah, duk da ita dai a ranta taso zama ne wajen Umm ɗinta. Kafin su kwanta Yoohan ya kirata a waya a karo na kusan huɗu kenan. Dama tuni hotunan ɗansa sun gama cika masa wayarsa. Ganin jaririn nan Abdallah har hawaye sai da yayi, dan da yanzu ɗansane fa Nu'aymahrsa ta haifa masa. Sai dai ƙaddara ta riga fata labarin ya canja daga yanda ya fara.  

         Video call sukayi mai tsaho ita da Yoohan, tana rungume da ɗansu da sai a yanzune ta samu damar zaman masa kallon sosai. Yayinda ran Yoohan ke cike taf da tarin farin cikin ganinta da yaron a jiki, tayi ƙyau sosai ta kuma dace da uwa. Musamman da ƙibar ciki ta sata komawa wata babbat mace. Bai barta ba har sai da ya ga tana hamma. Yasan babu abinda tafi buƙata a yanzu kamar barcin, dan lokacin da cikin ya shiga watan haihuwa bata iya barci sosai. Wani lokacinma kwana take a zaune, sai da rana takan ɗanyi ta rage nauyin ido.

       Washe gari ƴan uwa da abokan arziƙi suka fara isowa gidan ganin ɗan jinjiri. Yayinda tun a farar safiya ta amsa kiran ƴan Abuja su Mama debora, dan har yanzu suna nan a gidan su Yoohan ɗin tare da jami'an tsaro. Tun jiya kuma Yoohan ya sanar musu da haihuwar Nu'aymah harma ya tura musu hoton jariri. Sunso kira tun da daren yace suyi haƙuri sai da safe. Aiko gari na wayewa saiga shigowar kiransu ta hanyar video call.

    Nu'aymah tasha mamaki matuƙa ganin wai harda Joy da Gebrail cikin ƴan murnan haihuwarta. Sun mafi kowa zaƙewar cewar zasuzo kano. Taji daɗin hakan har cikin ranta, dan koba komai dai ba'a canjama tuwo suna. Dole su wannan ɗan nata zai kalla matsayin dangin mahaifinsa. Sune kuma adonsa a cikin al'umma.

       Baba malam shine ya tauna dabino ya bama jin jiri bayan yayi kiran Yoohan ya tambayesa akan yayi masa huɗuba kokuwa zaizo da wuri yayma yaronsa da kansa. Maganar ta bashi kunya sosai sosai. shi ko bama ɗansaba koshi kansa ai Baba malan ya isa da shi. Cikin jin nauyi yace, “Uncle dan ALLAH ka daina neman izinina aka. dukkan abinda ya dace da shi. Kai masa dan kaima ubane a garesa ai. Suna kuma asa masa sunanka, dan ina fatan ya zama mai gadon ɗabi'u da ƙyawawan halayenka da tarin ilimi”.

      Baba malam yaji daɗi sosai da wannan girmamawa. dan haka yayma yaro huɗuba da suna Muhammad Soorajidden. Sai dai ya bar hakan a ransa sai ranar suna idan ALLAH ya kaimu. Ya dai sanarma Umm da hajjo kawai.

         A washe garin data haihu da kwana biyu aka maido su Abban Abdallah gida daga asibiti. Dan baba malam dai da kansa ya roƙa Jay akan a bar maganar zuwa kotun ɗin nan a barsu suji da ciwukan dake tare da su. Badan Jay yaso ba ya yarda da buƙatar ta baba malam aka rufe case ɗin ma gaba ɗaya daga can ofishinsu.  jikin Abban Abdallah yayi sauƙi, sai dai kuma fa akwai matsaloli sosai, dan sakamakon karayar da yayi a kafaɗu wuyansa baya iya zama sam, gashi kansa ya bugu ƙwaƙwalwar sa ta samu matsala daga ciki, matsala irin waddama tafi ta Nu'aymah muni. Baya gane wasu abubuwan yanzu tamkar ƙaramin yaro, ko dubashi kaje yi sai dai ya dinga kallonka kamar wani soko.

      Addah ma dai al'amari ya tsananta a gareta, duk ta rame ta lalace tayi baƙi. Har yanzu da tayi tari kuma sai kaga jini duk da dai ya ragu ba kamar da canba.

     Alƙawarin ALLAH ya cika ta ɗauki gudan jinin Yoohan da Nu'aymah a hannunta. Tai dariya tai kuka abin tausayi. Abban Abdallah kuwa koda aka kai masa jaririn kallonsa kawai ya dingayi amma babu bakin magana, hasalima ba wani fahinta yayi da ƙyau ba sai da Monyn Abdallah tai masa bayani, dan suna nan kano sunma dawo gaba ɗaya. Cikin karkacewar baki ya nuna Nu'aymah ya nuna jaririn yana magana yawu na dilalowa. Yace, “Mamana. Ɗanta?”. 

    Kai Momy ta jinjina masa. Hakan ya sakashi yin murmushi mai ciwo sai ga hawaye na zirara masa da gudu. Sosai hakanma da yayi ya bama kowa mamaki, dan baya magana balle nuna fahimtar mutane.

      Ranar dai ansha sabon kuka a gidan, dan komai sabo ya dawo a zukatansu. Sai da baba malam ya sake musu nasiha sannan suka samu nutsuwar zukata. 


       Ƴan Abuja basu sami isowa kano ba sai kwana huɗu da haihuwar Nu'aymah. Ba ƙaramin shan mamakin ganin da gidan da Aymah ta fito sukayi ba, sun sake tabbatar da lallai itaɗin jinin babban gidace. Dan duk da kasancewarsu ba ƙabila ɗayaba, ga abinda mahaifinsu ya aikata daya jawo musu baƙin jini a waje. mutanensu acan anan sai ake nuna musu mutuntawa da girmamawa. Hakan ba ƙaramin sakasu jin kunyar Nu'aymah yayi ba. Mama debora harda kukanta kuwa. Dan batai zaton dangin Aymah zasu amsheau da hannu biyu kamar haka ba kodan cin kashin da taima ƴarsu..

         Washe gari ana gobe suna shima Yoohan ya iso tare da Juliet ɗin Umar da baby Ayisha. Kai tsaye nan kano suka nufo dama. Inda Yoohan yay masauki a hotel da Omar ke jiransu. Juliet dai zuwa dare aka kaita gidansu Nu'aymah. Sunyi farin cikin ganin juna sosai, Juliet nata mamakin Nu'aymah da ɗa. itako dariya ta dingayi tana rungume da Ayisha ɗinta. 

     Su kansu Omar da Yoohan kallonta kawai suke. Daga baya Umar da Juliet suka basu guri. Tasowa Yoohan yayi yazo ya rungumeta yana sake godema ALLAH ɗan jaririnsa na jikinsa.

      Tai dariya da faɗin, “Silly boy duk ka wani rikice kai ka zama Baba ko?”.

     Dariya sukayi a tare cike da jin daɗi da farin ciki. Yoohan ya sumbaci goshin yaron da faɗin. “ALLAH ya raya Sheikh to be insha ALLAH”.

     Murmushi kawai Aymah tayi da faɗin amin.


*_RANAR SUNA_*


         Washe gari aka raɗama yaro sunansa Muhammad Soorajidden a masalaci. Tare da doguwar addu'a a garesa. Kowa yaji daɗin wannan suna musamman Nu'aymah da taji kamar ta haɗiye Yoohan dan farin ciki. Dan babu yanda batai da shi ya faɗa mata sunan jiya ba yaƙi. Kusan ƙarfe goma na safe kuma sai ga tarin alkairi daga Yoohan. Duk wani al'ada na hausawa a bikin suna sai da yayisa bisa shawarar Ahmad da Hamza manager.

      Kowa kam ya yaba ƙoƙarin sa, baba malam ma ya dinga faɗa hidimar tayi yawa.

       Amaryar jego tasha ƙyau harta gaji. hakama ɗan jinjiri Deen. Da yamma akasha walima a ƙofar gidan. wadda tai sanadin karyar da zukatan su Gebrail da su mama debora da suka fahimci Yoohan ɗinsu ya zama musulmi, basu nuna ƙyamar hakanba ko a ransu, saima yanda tsarin yake gudana da ɗabi'un musulman yasa Momy Destiny kasa yin shiru har sai da ta yaba. Dan har ranta abubuwan sun birgeta gaskiya.

     Bayan tashi da ga walima ƙarfe takwas na dare kuma wani tashin hankali ya biyo baya. Dan sama da ƙasa an nema ɗan jariri Deen an rasa. Kafin kace mi gidan ya hargitse. A take Nu'aymah ta sume musu sai da aka zuba mata ruwa. Yoohan na cikin ɗimuwa shima aka ƙwamushesa. Faruwar hakan a gaban mutane ya sa Omar da Ahmad da Omar ɗin su Nu'aymah, da Abdallah da Naseer binsu a mota. Yayinda Nu'aymah ta faɗa miotar batare da kowa ya fargaba sai da sukai nisa.

    A yau tai niyyar nunama Yoohan hoton papa da wadda suke zargin itace mahaifiyarsa. Sai gashi kuma abinda basuyi zatoba ya auku...........✍


‘Hummm mikuke tunani masu karati😱🏃?’.

No comments

Powered by Blogger.