Sakayyah 5

 


📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇


                     *SAKAYYAH*

                            _Page 5_


                               *NA*

            *AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


                *FREE PAGE*


    *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE, 1K NE KACAL ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276.*



Zare Ido Hajja Nana tayi cikin faɗa da fushi tace.

“Ke! Ke!! Ke!!!.Faɗimatu ki kiyayi kanki dani fa zan tsige Miki fuka-fukinki!”.


Ita kuwa khausar fuska ta haɗe Idanunta tsaye akan Hajja Nana tace.

“Nifa ba tsuntsuwa bace da zaki tsige min fuka-fuki, ai gaskiyane tsakani da Allah da Annabi mahaifiyata zata tafi kinsa ankawo ni aise ki kirani muyi sallama na musu Allah ya tsare”.

Ta ƙare mgnar tare da juyawa ta kalli Dija tace.

“Fisabillilhi ba haka ya kamata ba Dija?”.


Dija kuwa tuni ta sunkuyar da kanta yayin da jikinta ya shiga ɓari tsananin tsoro ya bayyana afuskarta sanin halin Hajja Nana babu wanda ya isa tana magana yana mayar mata da martani!.


Cikin rawan jiki da tsoro daya bayyana amuryanta  tace.

“Khausar kidena kar ki sake bata amsa ki bata haƙuri”.

Tana ida maganar ta tsugunna gaban Hajja Nana tace.

“Goggo Hajja Waɗɗu munyal”.


Hajja Nana kuwa kwaffa tayi kana tace.

“Aaaa Dija matsa kusa da ita inzo na same ta ai ke ba ruwanki”.

Ita kuwa khausar batare da tsoro ba tace.

“Toh kizo mana kawai dan mutum ya faɗi gaskiya don dai ba'a son gaskiya da zaman lafiya ai yakata dai akirani muyi sallama da Momyna tunda dai ansa an kawoni wataƙila ma sai nayi sati biyu ko uku bangan taba aida se akirani muyi sallama ince agaida mutanen gida sannan nayi musu fatan isa gida lafiya”.


Ita kuwa Hajja Nana afusace tace.

“To idan kece zaki kaisu gida lafiya kada Allah yasa ki kaisu shegiyar yarinya mara ji Ɓee Usmanu La'ilaha illallahu ohoho gabtarel”.


Tuni Baffa Jauro da Baffa Sadu suka shigo idanun su akan yayar tasu suka ce.

“Lafiya Addah Hajja?”.

Kai ta girgiza tare da nuna Khausar dake cika tana ba tsarewa tace.

“Ɓeee Usmanu,Nikam ban taɓa ganin fitsararriyar yarinya kamar 'yar Usmanu ba”.

Itade Khausar na jingine jikin bango tana tura ƙaramin bakinta dake ƙarawa fuskarta kyau.


Kallon ta Hajja Nana tayi cikin harara  tace.

“Nikam Usamanu na Kam ba haka yake ba, haka zalika Mahaifiyarki ko surukata ce bazan mata ƙazafi ba macece mao mutunci amma ke kam waya fitsare miki Ido? Kodan zama tsakiyan Mayun gidan kune yasa kika zama haka!?”.


Khausar dake jingine da bango ta ɗago kanta kana ta wara manyan Idanunta masu kyau da tsari tace.

“Nikam de kar kice min Mayya idan su Mayu ne toni ba Mayya bace idan kince ni Mayyace sede idan awajenki na gada!”.


Baffa Jauro da Baffa Sadu suka dubi juna alokaci ɗaya cikin ƙasa da murya yanda Hajja Nana ba zata jiba Baffa Jauro yace.

“Lalle akwai rigima anan? Addah Hajja ba abata amsa idan tayi magana amma ga 'yar Usmanu daga zuwa tana bata amsa gatse-gatse jika kenan mafi akasari duk zafin mutum jikoki bazasuji tsoronka sosai ba”.

Murmushi Sadu yayi yana jinjina kai.


Baffa Jauro kuwa kan Khausar ya ɗan buga yace.

“Kay Hausajo kidena mu ba'a rashin kunya agarin nan!”.

Ita kuwa khausar inda ya ɗan bugeta tasa hannu ta riƙe tana sosawa duk da cewa bawai zafi ya mata ba ta tura ƙaramin bakinta tace.

“To ai muma ba rashin kunya bane wannan kam”.

Dan ƙolo ya mata yace.

“Dije jata ku tafi”.

Kai Dije ta gyaɗa wacce se alokacin ta samu kuzarin miƙewa tace.

“Khausar kizo mu tafi“, Sannan taja hannunta suka fita.

Suna fita Khausar kuwa hannunta dake cikin na Dije ta janye tace.

“Yanzu ina zamuje?”.


Murmushi Dije ta sakar mata tace.

Rafi zamuje”.

Murmushi mai sanyi Khausar ta sakar mata wanda ke ƙarawa fuskarta kyau tace.

“Toh mu tafi”.

Dan sosai weather garin yake abin burgewa da sha'awa.


Cikin nutsuwa suka nufi Rafin suna hira.

 Da sauri Dije ta riƙon hannun Khausar tare da   nunawa mata gefen damansu, masu wasa da birine ke tafiya kana yaran rugagen dake gefe dasu na biye dashi, bisa alamun yanzu kuma rugarsu zasu shiga.

 wani ƙaton Biri yake ta kolongoiso yara nata ja da baya.

 Cike da nishaɗi Khausar tace.

“Muje muma mu gani”.

Kai Dije ta gyaɗa mata , kana suka nufi wajen me wasa da Biri suna ganin yanda Birin ke duk abinda aka sashi.


Cike da farin ciki Khausar ta kalli mai wasa da Birin tana ƙara kusawa cikin yara matan tace.

“Mai Biri yanzu duk abinda na sashi zai min?”.

Kai mai wasa da Birin ya jinjina yace.

“Idan kuma baki yarda ba ki gwada ki gani”.

Kusa da Birin Khausar ta matsa tana murmushi tace.

“Yauwa yaya salon mugun Malami yake idan zai daki ɗalibansa?”.

Da sauri ta ware idanunta ganin.

Birin ya wani ja baya tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya ɓata fuska tare da harɗe sawunsa sai kuma ya ɗauki wani sanda ya riƙe yana nuna Khausar da Dije.


Hannu Khausar tasa ta dafa kafaɗar Dije tare da tintsirewa da dariya mai cike da sautin shauƙi yayin da ɗaya hannun kuma ta ɗaura saman shafefen cikinta tana mai cigaba da dariyar.

Domin kuwa babu wanda ya faɗo mata arai lokacin da Birin ke gwadawa face Moddibo duk da kasancewarsa ba mutum ne mai Fara'a ba amma duk sanda zaisa a zaneta a makarantar Islamiyya seya sake tamke  fuskarsa..

Dariya sosai takeyi wanda da yawa cikin yaran tayata sukeyi.


Ganin bata da niyyar daina dariyar ne yasa Dije jan hannunta cikin dariya tace.

“Khausar Mu tafi,Dariyar me kuma kike haka!?”.


Tsagaita Dariyar Khausar tayi sai kuma lokaci ɗaya jikinta yayi sanyi tuna wa da tayi Moddibo zai iya jira duk lokacin da tawo ya yanke mata hukunci ahankali tace.

“Kawai na tuna da wani  Malamin mune”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Allah sarki shike zaneki kena”.

Kai ta jujjuya tare da cewa.

“Wancan da shegen madarar ƙasaita sawa yake a zaneni dai yana nan jiki kamar auduga ai shi dukan ma aikine a wurinsa”.

Murmushi Dija tayi tare da cewa.

“Da Goggo Hajja zataji haka sai ta sa mishi al'barka”.

Baki ta tura ba tare da tace komai ba sukaci gaba da tafiya.


Suna shiga Rafin idanun Khausar ya sauƙa akan Bishiyoyin Piya,  Caɓɓulle, Mangoro, Ayaba, Gwanda, Gwaba, Lemo,  da sauran kayan itatuwa duk sun yiwa wajen ƙawanya.

Sake wara Ido Khausar tayi ganin bishiyoyin Inabi guda uku a jere,

Cikin farin ciki ta dubi Dije tace.

“Harda Inabi Laha'Ila Ha'illalhu Masha Allah zan kuwa ci”.

Ta ida maganar tare da nufar jikin Bishiyar zata hau.


Saurin riƙe hannunta Dije tayi tace.

“Kada ki hau Khausar Baffa Liman ya hanamu yace ba shida amfani 'ya'ya mata su riƙa hawa bishiya ba tarbiyya bace mai kyau”.

Ita kuwa khausar janye hannunta dake cikin na Dije tayi tace.

“Ke rabu dashi da ƙa'idojinsa hawa za muyi mu cire abinmu, ai kuma ba har can sama zamu hauba”. 

Langwaɓar da kai Dije tayi kafin tayi magana suka hango wani farin saurayi kyakkyawa daga ɗaya gefen.

Hannu Dije ta ɗaga masa da faɗim.

“Yawwa Sadik dan Allah zoka cire mana Inabi wai zata ci”.


Ƙara sowa Sadik yayi idanunsa akan Khausar yace.

“Dije wannan yarinyar wa kika samo?”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Yarinyar Marigayi Baffa Usmanu cefa yaron Goggo Hajja”.


Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa yace.

“Allah sarki itace wacce take Birni ko?”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Eh itace”.

Ita dai Khausar ba tace komai ba.

Raɓar bishiyar yayi ya ciro musu Inabi kana ya koma bishiyar Ayaba shima ya ciro yasa musu aƙaramin kwandon dake hannunsa irin na saƙar kaba na gargajiya miƙawa Dije yayi.

Sai asannan Khausar tace.

“Mungode”.

Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba,

 suka fara tafiya cikin rafin akai-akai Khausar ke lumshe idanunta tana wasa da yatsun hannunta sosai weather garin ya mata daɗi.

Juyowa tayi ta kalli Dije tare da cewa.

“Garinku yayi min daɗi”.

Cikin sauri Sadik yace.

“Garinmu de kin cire kanki ne a ciki? Ko kin manta nanne tushenki kuma asalinki nanfa cibiyarki take abinne”.

Dariya tayi kafin tace.

“Hmmm Shiyasa ma naji daɗin garin inba haka bama masifar wannan tsohuwar yasa bana sha'awar zuwa garin nan”.

Zare ido Sadik yayi yace.

“Wacece masifaffiyar!?”.


Asanyaye Dije za tace.

“Wai Goggo Hajja take cewa masifaffiya”.

Sake zare ido Sadik yayi se kuma yace.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”,Ya dubi Dije yace.

“Meye sunanta ma kika ce?”.

“Khausar”

Dija tace.

Ya maida kallonsa kan Khausar da hankalinta yabi shuke-shuken da kallo yace.

“Khausar kiyi Istigfari”.


Khausar kuwa kallon mamaki tayi masa kafin tace.

“Saɓon Allah nayi da zanyi Istigfari?”.


Habarsa ya riƙe  still Fuskarsa ɗauke da Mamaki yace.

“Goggo Hajjan kike cewa Masifaffiya”.

Baki ta taɓe tace.

“Yo ba masifaffiyar bace daga zuwa na fa kawai takama yimin bala'i”.


Kai ya jinjina kafin yace.

“Toh kar ki sake wallahi in Goggo Hajja taji abinfa baze miki daɗi ba”.

Cikin sanyin murya Dije tace.

“Allah de ya kyauta anma wannan baƙunta ai akwai kallo aciki”.

Ba wanda ya sake magana har suka fito daga cikin Rafin.

Gani tayi Sadik ya ɗauki wani babban kwando da sunyi ta fiya kaɗan sai ratsa cikin ciyawa ya buɗe ya ɗibi ƙwan Zabbi ya saka acikin kwando.


“Me kakeyi haka?”.

Khausar ta tambayesa tana kallon wajen da ciyayi masu kyau da tsari suka lulluɓe wajen.

Murmushi yayi yace.

“Ƙwan Zabbi nake tattarawa”.

Cikin lumshe ido tace.

“Ohhhh lalle kam Masha Allah abamu naci”.

 Murmushi yayi tare da faɗin.

“Toh babu damuwa”.

Haka suka riƙa tafiya suna hira jefi-jefi sun kusa fita daga cikin Rafin ne Khausar ta jiyo hayaniya na tashi kamar kasuwa anata surutu da dariya jujjuya wa tashiga yi amma bata ga inda sautin surutun ke tashi ba.Ta dubi Sadik da Dije tace.

“mene nake tajin hayaniya da surutun nan kam a cikin daji?”.

Sadik ne yace.

“Mutanen Bishiyar ƙare zancen kane”.

Da sauri ta sake duban sa tare da  cewa.

“Bishiyar ƙare zancen ka?,Wai mene ma'anar Bishiyar ƙare zan cenka?”.


Dije ce tace.

“Ai mu garin nan bamu da service, Service ɗinmu waje ɗaya ne inde mutum yana so yaje yayi waya seya je ya hau bishiyar ƙare zencen ka anan ne ake samun network idan kina wajen zaki iya kira sannan za'a iya kiranki kina sauƙa daga bishiyar ko kuma kina Matsawa daga wajen bishiyar toh shikenan Service ya yanke ba zaki samu kiyi magana ba kuma shima sai in layin MTN ne ko Zain”.


Cike da Mamaki Khausar tace.

“Ikon Allah wannan wani irin ruga ne?. Dama ashe har yanzu akwai irin wuraren nan daya rage aduniya?”.

Murmushi Dije tayi tace.

“Sosai ma”.

Ahankali Khausar ta ɗaga kanta nan ta hango manyan tsaunika da bishiyoyi Kallonta ta mayar kan Dije tace.

“Haba ko wannan manyan tsaunuka da bishiyoyin ai sa tare muku service da network”.


Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Lalle kam da alama shi ya tare”.

Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace.

“Muje inga wajen”.

Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da rassan bishiya masu taren yawa  saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru.

Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya.


Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace.

“Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?".

Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace.

“Baban nawa ne tsoho?”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”.


Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace.

“Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da sauran Jaurorin garirruwa”.


Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.

“Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”.

Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka sauƙa akan wata tsohuwa dake waya.

Ta maida kallonta kan Dije tace.

“Wannan kuma fa?”.


Dije tace.

“Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”.

Kallonta Khausar ta sake yi tace.

“Ƙawar Masifa de zaki ce”.

Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace.

“Ki bari fa”.

Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace.

“Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”.


Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar.

Dije kuwa  tayi murmushi tace.

“ 'Yar Baffa Usmanu ne”.


Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo.

Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace.

“Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”.


Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace.

“Kinga wannan?”.

Kai Khausar ta gyaɗa.

Dije tace.

“Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Ayyah Allah Sarki yayi kyau".

Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.

“Hi Sister how are you?”.

Ta mayar masa da martanin Murmushin tace.

“Am fine how's everyone?”.

“Fine Long time?".

“Thank God”.

Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace.

“Kuyi magana da yaren da zanji”.


Murmushi Khausar tayi tace.

“Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”.

“Toh”.

Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace.

“Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”.

Murmushi yayi yace.

“Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”.

Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin ko wannensu da alama akwai inda  ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin  waje-jen...

Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace.

“Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”.

Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!.

Ashagwaɓe tace.

“Wayyo na tuba ka sake”.

Sake mata hannun yayi yana dariya yace.

“Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari ba'ason wahala”.


Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace.

“Dije”.

“Na'am Baba”.

Yace.

“Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi  tsar Nono tare”.


Kai Dije ta gyaɗa kana tace.

“Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”.

Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace.

“Nide inda wuya bazan yiba”.

Dije tace.

“Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi.

Kai ta gyaɗa tace.

“Toh shikenan ba damuwa zanje”.


Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace.

“Ki tafi dashi".

 Sannan ya juya ya cigaba da tafiya.

“Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace.

“Kaifa baza ka bimu bane”.

Girgiza Kai yayi yace.

“A'a ban ƙarasa ɗiba ba”.


Kai ta gyaɗa tace.

“Toh inde kazo ka kawo min nawa”.

“Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi.


Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye.

Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace.

“Waye”.

Cike da ladabi Dije tace.

“Dije ce".

Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa.

“Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”.

Ƙasa da murya Dije tayi tace.

“Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”.


Khausar kuwa baki ta taɓe tace.

“Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”.


Daga ciki Hajja Nana tace.

“Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”.


Dije tace.

“Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”.

Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi.

“Toh shikenan”.

Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice.

Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take.

Suna isa suka ajiye Ƙwoyin.

Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace.

“Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”.


Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba  alamar hasken wutar lantarki ta dubi Khausar tace.

“Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tace.

“Eh babu amma ana tada Generator”.

Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!.

Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace.

“Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata rana zakiga garin”.

Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu.


Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi.

 A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace.

“Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”.


Kallon ta Khausar tayi tace.

“Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi alwala”.


Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace.

“Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi ruwan zafi”.


Bakinta ta tura amma ba tace komaiba.

Dije ce tace.

“Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”.


Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.

“Toh shikenan”

Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga.


Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”.

Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa.

“Lafiya Khausar meye faru?”.


Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa  takasa furta komai numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta.

“Kuliya”.

Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana.


Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja.

Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi.


Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar.


Daga can waje Hajja Nana ke cewa.

“Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”.


Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa.


A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa.

“Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa.

Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita,

Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n

Ya Allah na tuba ka yafe min”.

Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi.


Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije.

Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace.

“Lafiya”.

Asanyaye Dije tace.

“Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo 

Hajjs ce take haka”.


Cike da tausayinta Goggo Nanne tace.

“Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da hankalinki ki nutsu kinji?”.


Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta.

Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta.

Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace.

“Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”.

Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta.

Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace.

 “Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita kuma wannan ga tsoron kuliya”.


Tana sakin ajiyar zuciya tace.

“Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”.


Murmushi Goggo Nanne tayi tace.

“Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”.

Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka shiga da Dije cikin ɗakin duhu.

Araunane Khausar tace.

“Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”.


Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace.

“ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”.

Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske,

Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a.

Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace.

“Ina kuma zaki je?”.


Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace.

“Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”.

“A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.

“Eh akwai”.

“Ok to kibari sai munyi Azkhar”.

“Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i suka Idar...


             GEMBILA

Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu da network bare ta kira taji muryanta.

Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy.

Murmushi Mommy tayi tace.

“Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”.

Kai ya girgiza yace.

“Momy wallahi yau gidan nan ba daɗi da Addah Khausi bata nan”.

Murmushi Momy tayi cike da ƙaunar 'ya'yan nata da kuma yanda suke nunawa juna kulawa tace.

“Yau kuma?,Ko da yake dama haka kuke bakwa shiri sannan bakwa san rabuwa da juna”.


Fuska ya Marerece kafin yace.

“Allah yau gidan babu daɗi yau tunda gari Ya waye babu wanda yace min Haiydar kar kayi kaza, Haiydar zo in aikeka, Haiydar bakaji, Haiydar karenani,  Haiydar kada fa kaci komai wurinsu Umma, Haiydar ban girme ka bane kam wai da in na saka abu bazakayi ba, Yau duk babu wanda ya faɗa min haka nayi missing ɗinta! Sosai wlh Momy Ina son Adda Khausi”.

Murmushi mai cike da shauƙi Momy tayi  tare da zuba musu ido.


Raudat da shigowarta kenan ta Shagwaɓe fuska tace.

“Wallahi nima nayi kewarta Mommy yaukam tare zamu kwana ko?”.

Janyo hannunta Momy tayi tace.

“Autanah ba dole ba yau In kwana dake tunda Addah Khausar bata nan”.


Haiydar ne ya sake kallon Momy cikin yanayin kewar 'yar uwarsa yace.

“Momy dan Allah ki kira kice ta dawo munyi missing ɗin ta”.

Ramadan da Raudat suma sukayi saurin cewa.

“Please Momy ki kira”.

Kai Momy ta girgiza tace.

“Basu da network sai dai idan sunje wajen bishiyar ƙare magarka sun kira”.

Ramadan yace.

“Toh yanzu Mommy Gobe wa zai Miki shara?,da wanke-wanke da kuma gyaran falo?”.


Murmushi Momy tayi tana shafa kansa tace.

“Zanyi ƙoƙari nayi da kaina”.

Zare Ido Ramadan yayi yace.

“To wallahi Momy aɗauko Miki Addah Khausi yafi Miki gidan babu daɗi idan bata nan”.

Murmushi tayi tace.

“Toh”,Da haka hiran yazo ƙarshe Haiydar ya miƙe kana ya ɗauki Ramadan suka tafi ɗakinsu wanda zai ka fita falon Momy ƙofar nasu na jere da ƙofar falonta,

 ita kuma Raudat gadon ta hau ta kwanta gefen Momyn.


Acan ɓangaren su Moddibo kuwa.

Zaune yake Atsarerren falonsa da yagaji da tsaruwa kana yana fitar da sihirtaccen ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa.

 Yayin da M Jameel ke kwance akan 3sitter da waya maƙale akunnensa, Anutse Moddibo ya juya ya zuba masa Idanunsa tare tsarasa da su, still wayan yake Amsawa ɗauke kansa yayi ya cigaba da operating system ɗin sa kana ahankali ya sake maida Kallonsa kan M Jameel still wayar ne maƙale akunnensa.


Cikin ga jiyawa da wayar da yake yi Moddibo ya zuba masa idanunsa tare da motsa laɓɓansa da suka sake yin pinch kana suka tattare saboda tsananin sanyi da akeyi yace.

“Wai kai da wa kake yin wayar?”.


Gyaɗa masa kai M Jameel yayi tare da juya hannunsa alamar ya kusa gamawa.

Ganin haka yasa Moddibo maida hankalinsa kan system ɗin sa yana cigaba da duba muhimman saƙonnin da suke shigo masa.

Wayarsa dake gefen Centre table ne yayi ƙara hannu yasa ya ɗaga nan yaga sunan Abba na yawo a screen ɗin wato Abban M Jameel.

Cikin han zari yayi picking call ɗin kana yace.

“Assalamu alaikum Abba Barka da dare”.

Daga ɓangaren Abba yace.

“Barka dai Moddibo ya gida ya kuma ɗalibai?”.

“Lafiya lau Alhamdulillah Abba”.


“Masha Allah kana tare da Hassan ɗinna ka ne?”.


Murmushi Moddibo yayi wanda ke sake fitar da ainihin kyawun fuskarsa yace.

“Eh Abba muna tare waya yake tun ɗazu nayi zaton ma da kai yake yin wayar”.

Abba yace.

“Aina kira wayarsa naji Line busy shiyasa nace bari na kira ka naga dare yayi bai dawo ba za'a rufe ƙofar gida”.


Murmushi Moddibo yayi yace.

“Ayyah Abba yau kam abarshi mu kwana tare gashi naga alamun Agajiye yake bacci ma yake ji”.


Kai Abba ya gyaɗa yace.

“Toh shikenan Moddibo ayi bacci lafiya Allah ya tashe mu lafiya amma gobe da safe kuzo ina son ganin ku”.


Kai Moddibo ya gyaɗa cike da mutuntaka yace.

“Toh insha Allah Abbah”.

Kana ya katse kiran.


kallon M Jameel yayi sai kuma ya ajiye System dake kan ƙafarsa ya miƙe ya isa inda M Jameel yake yasa hannu ya cire wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin sai yaga number ba suna saidai aƙasan Number ansa Bahrain wato ƙasan Bahrain.


Kallon M Jameel yayi yace.

“Ooo kaida Jalaludeen ne dama?”.

Kai M Jameel ya gyaɗa yace.

“Eh shi ya hana ince da kai dashi nake waya”.


Murmushi M Jameel yayi yace.

“Yayi kyau”.

Jalaludeen abokinsa ne tare sukayi karatu a Jami'atul Madina asalin Balarabe Bahrain ne...


Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yace.

“Abba ya kira yace baka koma ba har dare yayi sai nace zamu kwana tare yace gobe yana son ganinmu”.

Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.

“Allah ya kaimu”.

“Ameen”.

Moddibo ya amsa tare da kallon M Jameel yace.

Bacci na keji zanje nayi wanka”.

Zare Ido M Jameel yayi yana kallon Moddibo yace.

“Wallahi inba cikin kashi na faɗa yanzu ba ba zanyi wanka ba yanda ake tsuga wannan sanyi agarin nan.


Kai Moddibo ya girgiza ba tare da yace komai ba ya wuce Bedroom.

wanka yayi da ruwa mai ɗumi, kana yayi shirin bacci.


Washe gari, da safe bayan sun dawo daga masallaci sashen Innayi suka nufa lokacin da suka shiga tana zaune kan darduma tana lazimi   M Jameel ya zauna kusa da ita tare da riƙo tafin hannunta yace.

“Barka da safiya tsohuwa mai ran ƙarfe!”.


Murmushin fuskarta ta faɗaɗa tare da damƙe hannunsa dake cikin nata tace.

“Jameel Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku”.

Ya amsa da.

”Ameen Innayi”.

Shi kuwa Moddibo kusa da ita ya matsa ya ɗaura kansa akafaɗarta yana mai lumshe idanunsa ahankali yace.

“Barka da safiya Innayi”.

Hannunta tasa ta shafa fuskarsa tare da cewa.

“Fatan ka tashi lafiya ya ƙoƙari?”.

Ya amsa da. “Alhamdulillah” sai kuma ya miƙe tare da kallon M Jameel da still hannunsa ke cikin na Innayi yace.

“Mu je ko”.

Bai jira cewarsa ba ya fice daga sashen nata kana ya nufi nasa yana shiga kai tsaye Bedroom ya wuce ya cire naɗin Hiramin dake wuyan sa da kuma jallabiyar.

Kai  ya shiga bathroom Masha Allah Komai na cikin toilet wanka ya fesa kana ya fito bakinsa ɗauke da addu'a

“Gufra naka”.Alokacin daya ziro ƙafarsa ta dama zuwa cikin Bedroom ɗin ya fito M Jameel kuwa jin ƙamshin sabulun wankan da kuma tularensa yasa ya ɗago kai sai kuma ya miƙe ya shiga toilet ɗin.

Shi kuwa Moddibo zama yayi agaban dressing mirrow ya shafa mayukan sa tare da taje yalwataccen sumarsa kana ya miƙe ya buɗe durowarsa

 Masha Allah kayane aciki masu uban yawa fannin jallabiya da ban fannin yaduka da ban haka zalika fannin ƙananun kaya daban duk da cewa bai fiye amfani dasu ba yana tsaye awajen har M Jameel ya fito daga wanka bai ɗauki komai ba.


Murmushi m Jameel yayi tare da nufar jikin durowar yana cewa.

“Nasan koda zaka kwana nan ba zaka taɓa cire kayan da zamu sanya ba kai de inba jallabiya ba baka ganewa ko wani irin kaya”.

Moddibo kuwa murmushi yayi Aransa yana jinjinawa M Jameel yanda yake iya fahimtar komai nasa koda kuwa ƙwaƙa-ƙwaran motsi yayi yasan me yake nufi...


M Jameel kuwa Wani boyel Sky blue mai gidan dara-dara ya ciro musu tare da boxer da kuma singlet Fari ƙal.

Kallon Moddibo yayi tare da miƙa masa.

Murmushi Moddibo yayi tare da karɓa yana kallon kayan amma bai ce komai ba sai ya juya ya kimtsa.

 Masha Allah wani irin kyau na musamman Moddibo yayi acikin kayan kalar shigar sai ta kasance tamkar kalar sararin samaniya  ƙirjinsa na ƙiran jarumtaka ya bayyana acikin rigar kana yalwataccen sumar kansa ya kwanta luf yana sheƙi,Anutse ya juya wajen M Jameel dake miƙo masa takalmi da hula kalar sky blue Masha Allah m Jameel ma sosai Yayi kyau acikin kayan sai suka kasance tamkar tagwaye masu tsananin ƙaunar junansu.


Atare suka fice sashen Innayi suka nufa tun daga farfajiyar tsakar gidan Moddibo ya lumshe idanunsa yana jinjinawa tsaftar Kakar tasa har sanda suka isa ƙofanta inda sanyayyan ƙamshi turaren wuta ke tashi.

Ganinsu atare yasa ta sakar musu da murmushi atare suka shiga ɗakin suka zauna.

Ta dubesu cikin ƙaunarsu tace.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Allah yasanya farin ciki acikin rayuwarku Ubangiji ya tsareku da dukkan sharrin mai sharri”.


Cikin jin daɗin addu'ar da take musu ako yaushe suka amsa da.

“Ameen Innayi”.

Innayi kuwa miƙewa tayi ta haɗo musu tea mai zafin gaske saboda sanyin da akeyi sosai amsa sukayi.

A hankali Modibbo ya ɗan zuƙan tea ɗin ahankali har ya Ida shanyewa zuwa lokacin tuni M Jameel ya shanye nasa.

Yana ƙoƙarin ajiye Mug ɗin yaga M Jameel ya tsaresa da ido Harara Moddibo ya watsa masa shikuma saiya sakar masa da murmushi.


Kallon Innayi Moddibo yayi yace.

“Zamu je gaida Abba”.

Jinjina kai Innayi tayi tace.

“Idan kunje ku gaishe min dashi”.

Moddibo na miƙewa yace.

“Zaiji insha Allah”.

Sannan suka fice.


Suna fita suka nufi inda mota ke ajiye M Jameel ne ya buɗe gefen Driver ya shiga yayin da Moddibo ya shiga mazaunin mai zaman banza ahankali M Jameel yayiwa motar key  suna isa gate ɗin Moddibo ya fita ya buɗe musu gate sannan M Jameel ya cinna hancin motar yafita saida Moddibo ya sake rufe gate ɗin kafin ya koma cikin motar M Jameel ya tayar suka bar unguwar.


Anutse M Jameel ya dubi Moddibo da idanunsa ke lumshe yace.

“Anma aikin makarantar nan zai yi kyau domin masu aikin sun san makamar aikinsu”.

Shi kuwa Moddibo kai ya gyaɗa da faɗin.

“Sosai Insha Allah”.

Tafiyar Mintuna Kaɗan sukayi suka isa gidansu M Jameel Hon yayi mai gadin ya taho da sauri ya buɗe musu tamfatsetsen gate din.


Wow  Masha Allah babban gida ne wanda yake ɗauke da Sashe huɗu sai kuma BQ da kuma wajen ajiye motoci kamar takwas zuwa goma sai ɗakin mai gadi cikin gidan akwai shuke-shuke saida basu da yawa sosai bayan sunyi parking sun fito ajere suke cikin tafiyar nutsuwarsu da tazame musu jiki kai tsaye sashen mahaifin  M Jameel ya nufa dasu.


Adai-dai ƙofar da zai sa dasu da falon Mahaifin M Jameel suka haɗu da Hajiya Karima kallon Jameel tayi  kana ta kawar da kanta wani irin tsuke fuska tayi ganin Moddibo abayan M Jameel.

Cike da ladabi M Jameel yace.

“Ina kwana Aunty Karima”.

Fuska ta sake tace.

“Lafiya lau ɗana ya gida ya kuma ƙoƙari??”.

“Alhsmsulillah ya amsa”.

Yana mai shafa sajensa

Shi kuwa Moddibo cikin tsuke fuska alamun ba wargi ataƙaice yace.

“Ina kwana”.

 

Wani irin kallo ta watsa masa kafin tace.

“Kaska raɓi mai jini anzo kenan?”.

Shiru Moddibo yayi tare da kauda kansa kamar bai jitaba.

Sai ma Murmushi da yayi tare da kallon gefen dama inda Aunty Larai Amaryar Aunty Karima ke tare da ce mata.

“Yau barka dai”.yayi mgnar yana mai tsare fuskarsa da ido alamun yana nazartar ta,

Ita kuwa Aunty Larai cikin sakin fuska tace.

“A'a to Moddibo ya kuka tsaya nan ku shigo daga ciki man Jameel”.

Ta ƙare mgnar tana kallon Jameel tare da juyawa ta nufi cikin falon Daddyn Jameel din.

Cikin jin yanayin ɓacin ran da kalaman Aunty Karima suka sa mishi yace.

“Gamu nan shigowa Aunty Larai”.

Ya kare mgnar tare da 

ɓata fuska cikin rashin jin daɗin abinda ta yiwa amininsa yace.

“Aunty!Aunty!!, Meyesa!!?, Meyesa!!!?”.


Cikin taune lips inta dubesa tace.

“Jameel gaskiya ne ai, amma ba zaka gane ba, ba zaka yarda ba  sabida ya fika wayo.

Kawai dai ya zama dole in faɗa maka”.

Shiru M Jameel yayi tare da juyawa wajen Moddibo wanda har zuwa lokacin yake tsaye hannunsa M Jameel ya riƙe yace.

“Dan Allah kayi haƙuri inda sabo yaci kasaba da halin Aunty na roƙeƙa Kayi haƙuri mushiga daga ciki”.

Murmushi Moddibo ya sakar masa ahankali ya furta.

“Bakomai me zatayi ya dameni sam babushi tunda tana son aminina”. Yayi mgnar da iya gskyarsakan

 suka shiga cikin falon.


Ita kuwa Aunty Karima  tsaki taja tare da barin wajen tana maijin tsanar Moddibo.


Zaune suka samu Alh  Bashir Mafindi Shahararren mai kuɗi daya sharahara aƙasa da kuma faɗin Afirca baki ɗaya mutum mai tsananin tausayin al'umma da jin ƙai.


Hannu ya buɗe musu cikin nutsuwarsu suka ƙarasa Moddibo ya nufi gefen damansa yayin da M Jameel ya nufi gefen hagunsa ya rungumesu tare da buga kafaɗar su.

Cike da so yace.

‘Yan ta gwayena Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku ina jin dadin ganinku atare kunyi kyau tamkar matasan Larabawa Allah Ubangiji ya nuna min aurenku”.

Moddibo kuwa murmushi yayi shikam sai ya zo wajen Abban Jameel ake masa maganar aure sai yaji abin banbara ƙwai duk da yasa ba duk lokacin da yazo wajen Abba saiya masa Maganar amman kullum a baƙuwa yake jin kalmar a cikin kunnuwansa.


Cike da ladabi da kuma girmamawa suka gaishesa cike da ƙaunarsu ya amsa da.

 “Lafiya”.

Kana ya tambaye su ya ɗalibai?.

Suka haɗa baki wajen faɗin.

“Lafiya lau Alhamdulillih”.


Zama Abba yayi bisa kujera.

Kana su kuma suka zauna a ƙasa bisa tattausan carpet ɗin, cikin kula Abba ya  ɗan sunkuyo ya kalli  M Jameel  kana yace.

“Yanzu kaga damuna ta kusa sauƙo za'a fara shuke-shuke to inason bana zan shuka Auduga mai yawa saboda ina son zan habaƙa  Company dake Marrocco muna buƙatar Auduga mai yawa domin mun samu haɗin guwar da wani ɗan Saudia wurin sufurin Sallayoyi da zannuwan gadaje da kuma Abayoyin na mata”.


Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh Abba hakan yayi Allah ya sanya alkhairi”.

Shima Moddibo yayi Murmushi da faɗin.

“Allah yabada sa'a”.

Cikin jin dadi Abban yace.

“Ameen. Yauwa sai kuma noma shinkafa da zamuyi mai yawa da alkama, dan Company kayan masarufin dake Ɓadamaya yana  buƙatar ninkin abinda yake sarrafa a shekara, domin samun haɗin guiwa da shi'ar ƙasar Niger”.

Kai suka jinjina alamun gamsuwa kana cikin kula Abban yace.

“Na sani kuma na fahimta, cewa akan su Asma'u ne ka nacewa karantarwa da kai da amininka. To Alhamdulillah na baku dama, amman ku sani suna gama secondary School, dole ku bar karantar wannan Moddibo ina buƙar taimakonku a Company's ɗin tunda Allah yayi kun karanci Business ɗin nan kafin ma ku tafi Jami'atul Madina.

Babana yanzu girma ya cinmini abubuwa sunayi min yawa dole ina bukatar tai makonku”.

Ya kare mgnar yana dafa kaɗan Jameel.

Cikin sanyi Jameel ya ɗago kansa ya kalli mahaifin nasa kana cikin sashi farin ciki yace.

“Allah ya kaimu lokacin Daddy in Sha Allah zanyi maka dukkan abinda kake so, muddin ina raye”.

Cikin jin dadi yace.

“Kaifa Moddibo baƙace komai ba?”.

Murmushi gefen baki yayi tare da cewa.

“Daddy duk inda J yake to in sha Allah ina nan”.

Cike da jin daɗin Alh Bashir 

Mafindi ya shafa kansu tare da cewa.

“Allah yayi muku al'barka".

Cike da jin daɗin sukace. “Amin Ya Allah Allah ya ƙara nisan kwana da lfy”.


“Amin Ya Allah”.

 Abba ya amsa tare da nuna musu dinning area da hannunsa, inda Aunty Larai ke shirya dinning ɗin tama mai murmushin jin tattaunawarsu.

Sai kuma ya kalli Moddibo kana yace.

“Bismillah kuje kuyi Breakfast”.

Moddibo kuwa kai ya girgiza a hankali yace.

“Daddy na ƙoshi”.

 

Kallonsa Daddy yayi cikin kulawa yace.

“Meyesa haka ne Moddibo gsky ni bana son yadda kake  in kazo gidan nan kaci abinci sai kaƙi ci”.

M Jameel ne ya amshi zancen da cewa.

“Rabu dashi Daddy in baici ba sai muyi masa ɗure”.

Murmushi Daddg yayi tare da faɗin.

“Aikam".

Moddibo kuwa harara ya wurgawa M Jameel.


Adam ƙanin  M Jameel yaron Aunty Karima  ne   yashigo ganin M Jameel yasa ya faɗaɗa Murmushin sa yace.

“Yaya Jameel Ina kwana?”.

Cikin murmushi M Jameel ya mayar masa da.

“Lafiya lai alhamdulillah Adam ya school”.

Adam kuwa kallon tsana ya watsawa Moddibo ba tare daya gaishe saba dan gani suke yana amfani da M Jameel ne wajen cin dukiyar mahaifinsu ko kaɗan M Jameel baiji daɗin abinda Adam yayi wa Moddibo ba, haka yasa ya haɗawa yaron fuska.


Acan Rugar Jauro yaya kuwa Washe gari.

Bayan Khausar sunyi Sallar asbah tare da Azkharul sabah ɗakin Goggo Nanne suka shiga ita da Dije suka gaisheta,

Ta amsa fuska asake Idanunta akan Khausar tace.

“Ya kwanar baƙunta da kuma tsoron kuliya?”.

Murmushi Khausar tayi tana wasa da yatsun hannunta har yanzu Atsorace take idan akwai abinda tafi tsoro acikin dabbobin duniya to kuliya ce da ƙadaggare.

Dije ce ta miƙe tace.

“Mun tafi gidan Hajja Nana”.

“Toh adawo lafiya".

Miƙewa sukayi suka fita ahanya Khausar ta dubi Dije cikin sanyin murya tace.

“Idan munje Kar mu daɗe tsoron gidan nake".


Kai Dije ta gyaɗa suka cigaba da tafiya bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga Hajja Nana dake hakimce akan kujeranta ta amsa Khausar kuwa kusa da ƙafafun Hajja Nana ta zauna tace.

“Ina kwana Hajja Nana”.

Ta dubeta fuska asake ta amsa tana jin ƙaunar ta aranta.

Dije ma gaisheta tayi ta amsa fuska asake.

Miƙewa Khausar tayi tace.

“Mu tafi”.

Kallonta Hajja Nana tayi tace.

“Ki zauna mutanen garin zasu zo gaisheni zan gabatar dasu awajenki”.


Khausar kuwa narai-narai da idanu tayi har cikin ranta take tsoron gidan Hajja Nana Allah ya sani tana masifar tsorob kuliya, jiki asaɓule ta zauna tare da riƙe Dije suka zauna tare.


Suna zaune Baffa Jauro yazo cike da girmamawa da kuma ladabi yace.

“Addah Hajja ina kwana”.

“Lafiya ta amsa”,tare da kallon Khausar dake takure tace.

“wannan shine ƙanina dake bina”

Murmushi Khausar tayi tare da gyaɗa kai tace.

“Baffa ina kwana”.

Dariya yayi yace.

“Lafiya Audiii ya fargaban kuliya!?”.

Baki ta ɗan tura  amma batace Komai.

Can sai ga Goggo Nanne

Kusa da Khausar ta zauna tace.

“Addah Nana ina kwana”.

Ta amsa da lafiya tare da kallon Khausar tace.

“Wannan itace matar Jauro wacce kuka kwana agidanta sunanta Nanne ita ce kuma takwaran marigayi yayarki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tana sake damƙe hannun Dije dake cikin nata.


Can sai ga Garga yazo idanun sa akan Khausar ya mata murmushi hannunta ya riƙe yace.

“Addah Nana ina kwana ya kwanan baƙuwa?”.

Hajja Nana kuwa taɓe baki tayi tace.

“Ga tanan matsoraciya saboda kuliya taƙi kwana anan".


Murmushi Garga yayi yace.

“Audii ki zama jaruma Mahaifinki fa ba rago bane babban jarumi ne”.

Murmushi tayi amma  batace Komai ba.

Hajja Nanan ce tace.

“Wannan shine Garga shike bin Jauro.

Can sai ga wata mata tazo itama ta gaida Hajja Nana.


Hajja Nana ta dubeta tace.

Wannan itace Dijarro matar Garga”.

Cikin sanyin murya Khausar ta gaisheta,

Cikin sakin fuska Dijjaro ta amsa.

Ba daɗewa saiga Liman yazo sanye cikin Alkyabba kansa naɗe da hirami kusa da ƙafafun Hajja Nana ya zaune cike da ladabi da kuma dattako yace.

“Addah Hajja ina kwana”.


Ta amsa da.

“Lafiya”.Sannan ta dubi Khausar tace.

Wannan shine Aliyu Limamin garin nan Uwarmu ɗaya Ubanmu ɗaya mutum ne mai tarin Ilimin addini”.

Cike da ladabi Khausar tace.

“Ina kwana”.

“Lafiya lau ya kwanan baƙunta?”.

Ta amsa da

“Alhamdulillah”.


Bayan tafiyarsa sai ga matansa biyu Rabi da Loddo,Kai kawai Khausar ke gyaɗawa.

Ita de Khausar ta kasa sakewa,Ahaka suka riƙa  zuwa duk wanda yazo Hajja Nana zata gabatar wa da Khausar shi.

Can saiga Yaya Abba yazo Hajja Nana tace.

“Wannan shine Abba ɗan ƙanina ne liman shi aka tura karatu birni yana karatun arnanci irin wanda kike yi”.


Abba kuwa ƙasa da kai yayi yana murmushi.

Ita kuwa khausar kallon Hajja Nana tayi tace.

“Wai waya ce Miki karatun Arnanci mukeyi?”.

Hannu Yaya Abba ya ɗaya mata alamar tayi shiru!.


Khausar kuwa ta wani juya masa manyan Idanunta tace.

“Taya ba karatun Arnanci mukeyi ba tace karatun Arnanci mukeyi ko ance mata acoci muke zuwa karatun?”.


Kallonta Abba yayi cikin harshen turanci yace. 

“Please Khausar Enough, Don't sey anything again”.

Zare Ido Hajja Nana tayi tace.

“Abbah zagina kayi ka juya yare zaka zageni da yaren Arna!??”.

Kai Yaya Abba ya girgiza yace.

“Wallahi ba zaginki nayi ba Goggo Hajja na isa in zageki?,Ai Babana ma bai isa ya zageki ba bareni”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Oooo”.


khausar kuwa murmushi tayi tace.

“Hajja Nana zamu tafi!".

Kai ta gyaɗa alamar toh kasancewar duk sun gama zuwa, Sai kuma ta kalli Dije tace.

“Ki ɗauke ta ki zagaya da ita gidajen kowa ki gabatar da ita”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan suka miƙe suka tafi kamar yanda Hajja Nana ta faɗa haka Dije ta riƙe zagayawa da Khausar duk gida jen ƙannen Hajja Nana da kuma 'yan uwa aƙarshe suka shiga gida Umar Autansu Hajja Nana...


Abakin ƙofa suka samu Baffa Umaru kallo ɗaya zaka masa kasan jarumin namiji ne mai cike da haiba da kuma ƙwarjini.

Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.

“Girman biredi wayon shayi”.

Murmushi tayi tace.

“Ni dai ba girman biredi bace”.


Yana dariya yace.

“Shekaranki nawa?".

Tayi murmushi da faɗin.

“Sha takwas".

Ya wara ido yace.

“A'a, ai babanki ma da kaɗan yafi haka”.

Ɓata fuska tayi tace.

Meyesa kuma zaka sa Babana?banaso shi kam baya rasu ba abarshi ya huta mana”.


Murmushi  mai cike da ciwo yayi tare da janyo hannunta ya ajiye ta gefensa kana a yace.

“Ai nima Babanki mutumi nane Shiyasa duk maganata nake kawo sunansa saboda banaso amanta dashi.

Ni sa'an sane tare muka taso mukayi wasan ƙasa banaso amance shi ina so ko yaushe arika kiran sunan sa ana masa addu'a”.


Khausar kuwa murmushi tayi tace.

“Nagode sosai Allah ya saka da alkhairi”.

“Ameen”,Ya amsa sannan ya kamata hannunta suka shiga cikin gida.

Da fara'a matarsa mai suna Adama ta yi musu sannu da zuwa sannan ta shimfiɗa musu abin zama bayan sun zauna ta kawo musu ɗumamen tuwon shinkafa da miyar taushe sai kuma madaran shanu mai zafi.


Kallon Umaru Khausar tayi tace.

“Har matarka ta gama abinci?”.

Kai ya gyaɗa ita kuma matarsa murmushi tayi kana tace.

“Eh saboda shi jarumi ne  baya son zama da yunwa kinsan shine garkuwan rugan nan”.

Wara Ido Khausar tayi tana dariya tace.

“Ba wani Garkuwa kawai de kina kurara sane”.


Murmushi  Adama tayi tace.

“Shikenan duk lokacin da Arnan maƙota suka kawo farmaki zakisan shine garkuwan rugan nan".

Murmushi sukayi Dukansu sannan ya fice Khausar da Dije suka wanke hannu suka fara cin abincin bayan sun gama ne suka tafi.


Kai tsaye Ruga suka nufa  suna isa Rugar aka ɗaurewa Khausar shanu sannan Dije ta shafa mata man shanu ayatsu saboda yayi santsi tsugunnawa tayi aka ɗaura mata ƙwayar ya akan cinyarta kana cikin azama ta kai tatsuniya kan bakin n......!







*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*


_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._



               

      🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,



                          By

     *GARKUWAR MARUBUTA*

No comments

Powered by Blogger.