Sakayyah 4

 


📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇



                     *SAKAYYAH*

                          _Page 4_


                               *NA*

             *AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

               *Free page*


*KADA DAI KU MANTA WANNAN FREE PAGE NE, KI KI BIYA KI KARANTA CIKIB AMINCI BA HAƘƘIN WANI GABA GAREKI SAKAYYAH 1k ne kacal ƴar uwa. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* 



*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken  GARKUWAR MA'AURATA*


NI DAI AYSHA Ɗiyar ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaici, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.


Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki. 

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!? 

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu. 

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki? 

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ji zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan set ɗin 10k ne kacal wlh koda sanyin mahaifane in sha Allah zakiji saukin.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya. 


Akwai ɗaya bangaren wato *KAMSHI* 

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, kana da kulaccar sirri sayan na gari maida kuɗi gida, banda harkar karanta yayin gyara Hajia.


Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.


🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA

     *(GARKUWAR MA'AURATA)*



Tana dirowa hannunta dake dungule da Appel  suka sauƙa kan ƙafarsa.

Yayinda yatsun hannunta dake ɗauke da zoban azurfa na kusa da da ƙaramin yatsa da kuma ƙaramin suka sauƙa akan  faratun yatsun sa,

atake yatsun hannunta suka bada sautin ƙash! yayin da shi ma Moddibo yatsun ƙafansa suka bada sautin ƙas-ƙas!, Idanshi ya rumtse da sauri, sabida wani irin masifaffen zogi da yaji ya ratsa sa cikin sauri ya tsugunna da niyyan matsasu tuni ɗanƙwalin ta ya zame yalwataccen sumar kanta baƙi daya sauƙa zuwa kafarɗarta ya zubo yana fitar da wani sihirtaccen ƙamshi...


Khausar kuwa jin zafin daya ratsa ƙafarta data malkoɗe ne  yasa ta furta.

“Wayyyo Allah ƙafata!”. ta faɗa da ƙarfi  tare da ɗago kanta yayin da yalwataccen sumar kanta ya rufe mata fuska da sauri tasa hannu ta janye ta ɗago kanta.

 Idanunta ne suka sauƙa akan Moddibo dake durƙushe, cikin ruɗewa da tsanananin tsoronsa ta  ɗauki ɗan kwalinta kana ta miƙe da gudu tana cewa.


“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n dan Allah kayi haƙuri wallahi Allah bansani ba”.

Ta faɗa tana ƙoƙarin fita daga gate ɗin.


Asma'u kuwa fitowarta daga gate ɗin da zai sadaka da cikin farfajiyar  Innayi kenan ta hango Khausar na shirin fita babu ɗan kwali akanta.

Cikin Sassarfa tabi bayanta tana faɗin.

“Khausar! Khausar!! Khausar!!!”.

ta kira sunanta har sau uku Kafin ta sake cewa.

“Dan Allah kada ki fita ahaka Khausar ki tsaya”.


Moddibo kuwa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyinsa ya kira sunanta da faɗin.

“Asma'u”.

Saidai akwai alamun ɓacin rai acikin sautin Muryansa.


Atsorace Asma'u ta juya Idanunta cike da tsoro tace.

“Na'am Yah Moddibo”.

 Tsayuwarsa ya gyara  tare da lumshe idanunsa masu ƙwarjini da haiba kana ya buɗe su ya dubi Asma'u da har yanzu take tsaye da tsoro a idanunta yace.

“Meyesa zaki ɗauko Biri ki kawo mana gida!?”.

Ya ƙare mgnar da bin Khausar da ido wacce tuni ta kai bakin gate.


Asma'u kuwa saurin ɗagowa tayi ta dubesa jin ya kira Khausar da Biri saidai bata yarda sun haɗa ido ba.

Shi kuwa cike da takaici

ya cigaba da cewa.

“Koda wasa kada ki sake zuwa da wannan yarinyar gidan nan, tunda ita bata da hankali da kuma nutsuwa da kamun kai”.

Ya ƙarashe mgnar yana mai lumshe idanunsa dake cike da ƙwarjini har zuwa sannan yatsun ƙafar na masa rawa tamkar alokacin ta buga masa yatsunsa.


Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe ganin tuni Khausar ta fice kanta a ƙasa tace.

“Dan Allah kayi haƙuri Insha Allah hakan bazai sake faruwa ba”.

Moddibo kuwa baice da ita Komai ba saima lumshe idanunsa da yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yaci gaba da yi.


Ita kuwa Asma'u jin baice komai ba yasa ta juya cikin sassarfa ta nufi gate dan bin bayan Khausar...


M Jameel dake zaune cikin falon Moddibo kuwa wanda ya tsirawa window idanu yana ganin duk abinda ya faru ya saki lallausan murmushi tare da miƙewa yana gyara zaman Farin t-shirt da blue jeans dake jikinsa kana ya sanya hannu ya buɗe ƙofan falon ya fito fuskarsa ɗauke da ƙayataccen murmushi cikin yanayin sa na ƙaunar Amininsa  yace.

“Ba sa ido ba?,ka fita sabgar yarinya ka ƙi yanzu inba sa'a ba kasa taji ciwo dan naga lokacin da take gudu tana ɗin gishi”.

Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi tare da zab gawa M Jameel Harara cikin yanayin nutsuwarsa daya zame masa jiki yace.

“Dama karyewa tayi da shi yafi yarinya bataji bata da hankali ko kaɗan”.


Da gudu Asma'u ke bin Khausar tana cewa.

“Khausar ki jira ni mana”.

Ƙin tanka mata Khausar tayi tana cigaba da sassarfa yayin da ko wani gaɓa na jikinta ke rawa kana tana cigaba da ɗaure gashinta daya baje kasancewar unguwa ce da babu hayaniyar mutane yayin da take yarfe hannunta dake masifar zugi kana tana me ɗingisa ƙafarta.

Ganin da gaske Khausar ba zata tsaya ba yasa Asma'u ta ƙara gudunta har ta isa inda take tana sauƙe numfashi saboda gudun da tayi tace.

“Ayyah Khausar ki tsaya mana ga hijabinki saka”.

Hannunta tasa ta amshi hijabin nata tare da zirashi a jikinta kana taci gaba da tafi.

“Ayyah Khausar ki tsaya mana”.

Asma'u ta kuma faɗa tare da shan gabanta,

a raunane  tace.


“Bazan tsaya ba Asma'u meyesa zaki min haka Asma'u? banyi tsammanin zaki yimin haka ba gidansu Moddibo kika kawoni mutumin da kin san baya ko son ganina.

 Gashi yanzu kinsa na buga masa yatsuna masu zobe aƙafa naji masa ciwo,yanzu bansan  wani irin hukunci zai ɗauka akaina ba”.


Tsoron Khausar ɗaya kada Moddibo yace zai zaneta duk irin rashin ji da ƙiriniyarta tana matuƙar tsoron bulala kana tasan duk hukuncin da Moddibo zai ɗauka bazai wuce yasa Malam Bello ya zaneta idan taje Hadda.


Cikin sanyin murya Asma'u tace.

“Ayyah Khausar kiyi haƙuri, amman kuma ai da kinji mgnata da haka bai faruba. kece bakya ji sannan ba kyaso ataɓa lafiyar jikinki”.

Kallonta Khausar tayi da Idanunta dake cike da tsoro da kuma fargaba tace.

“Meyesa zaki ce haka Asma'u kawai naga Appel da inabin ne ya ban sha'awa shiyasa na cira”.


Kai Asma'u ta girgiza tace.

“Inabi Khausar? na tabbata duk wannan abubuwan da kika gani akwai su a gidanku ku fiye ma da hakan”.


Sake Marerece fuska Khausar tayi tace.

“Na ganine ya bani sha'awa laifi ne dan na cire!?”.

Murmushi Asma'u tayi ganin har zuwa lokacin Atsorace Khausar take sai kuma tace.

“Kema dai baki jira kanki ba daga zuwa gidan mutane sai ki fara cire musu abu batare da neman izini ba”.


Ita kuwa khausar jin abinda Asma'u tace yasa ta watsa mata Harara cike da tsiwa tace 

“Tun da kinsan gidan masu baƙin hali zaki je Meyesa zaki ɗaukeni ki kaini?, Kisa aranki daga yau babu inda zan sake rakaki tunda haka kikayi min”.


Wara ido Asma'u tayi sai kuma ta langwaɓar da kai tace.

“Kiyi haƙuri Khausar bansan haka zai faru ba ni kawai da niyyar mu gaida Innayi nace ki raka ni amma kada kice baza ki sake raka niba na tuba”.

 

Kallonta kawai Khausar tayi amma ba tace komai ba, sake langwaɓar da kai Asma'u tayi cike da tausayinta tace.

“Ki zauna awancan dakalin se inja miki ƙafar!”


Kai Khausar ta girgiza tana rintse Idanunta tace.

“Basai kin ja minba kawai sama mana adedeta mu hau”.

Kai Asma'u ta jinjina tare da riƙe hannunta suka ɗan tsaya bakin titi cikin sa'a tsayuwar su babu daɗewa suka samu adedeta hawa sukayi tare da yimasa kwatancen inda ze kaisu...


Aƙofar gida me Adedeta ya sauƙe su bayan sun isa Asma'u ce ta ciro kuɗi ta basa kana ta riƙe hannun Khausar suka nufi gate Khausar ce tasa hannu ta tura gate ɗin cikin rashin sani suka buge juna da Samira Sani wacce ke ƙoƙarin fita Amina na biye da ita.


Saurin ɗago kai Khausar tayi jin Samira Sani na cewa.

Ke 'yar uban waye da zaki haɗa kafaɗa dani shin dame kike taƙama!?”.

Kamar Khausar za tace wani abu sai kuma ta fasa taja siririn tsaki tare da jan hannu Asma'u suka bar wajen tana me cigaba da ɗingisa ƙafarta.

Ƙwafa Samira Sani tayi cikin kumfar baki tare da tsanan Khausar aranta tace da Amina.

“Wallahi na tsani wannan shegiyar yarinyar me kama da sadaka yalla Idan ban sabautata ba bazan taɓa samun nutsuwa ba!”.

Tsaki Amina taja tana kallon Samira tace.

“Allah ne kaɗai yasan irin abinda zan mata”.


Kafin su ƙarasa shiga falon Khausar ta janye hannunta dake cikin na Asma'u kana ta gyara tsayuwar tare da dai-dai ta tafiyarta tana me rintse Idanunta sam bataso Momy ta fahimci abinda ya sameta.

Asma'u kuwa kallon ta tayi cike da tausayinta amma batace komai ba Ƙofan falon suka tura 

suka shiga tare da haɗa baki wajen cewa.


“Assalamu Alaikum”.

Momy dake zaune kan kujera ta ɗaura ɗaya kan ɗaya ce ta faɗaɗa Murmushin fuskarta tace.

“Wa'alaikum salam har kun dawo?”.

Zama suka yi daga gefen ƙafarta aƙasan chanis capet Asma'u tace.

“Eh Momy”.


“Masha Allah ya jikin Innayin?”.

Cewar Mommy.

Khausar na ƙoƙarin miƙewa tace.

“Da sauƙi Momy” Sannan ta nufi Bedroom ɗin ta da sauri Asma'u ta miƙe tabi bayanta.


Bakinta ɗauke da sallama tashiga ɗakin nata kana tayi saurin ɗin gisa ƙafarta se kuma ta kwanta agefen  gadonta dake shimfiɗe da white bedsheet tana sakin ajiyar zuciya akai-akai alamar har yanzu akwai tsoro atare da ita.

Zama Asma'u tayi agefenta ganin yanda ƙafan Khausar ke rawa yasa tace.

“Bari na ɗebo ruwan ɗumi na matsa miki”.

Kai Khausar ta girgiza da faɗin.

“A'a ga can man zafi agaban mirrow ki ɗauka min na shafa”.


Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta ɗauko man zafin ta ɓude kana ta kama ƙafar Khausar tana mulka mata.

Khausar kuwa rintse Idanunta tayi tanajin zafin man na ratsa jikinta  yayin da aƙasan zuciyarta tsakanin tsoro da firgicin hukuncin da Moddibo ze ɗauka akan tane.

Asma'u kuwa hira ta riƙa yiwa  Khausar na ɗebe kewa kana daga bisani ta miƙe ganin yamma tayi seda ta biya ta kichen ta sake yiwa Momy Sallama kana ta tafi.


Khausar kuwa yanayin zogin da ƙafarta da kuma hannunta ke mata yasa bayan  tafiyar Asma'u ba jimawa bacci ya ɗauke ta...


Ita kuwa Momy ganin har maghariba tayi bata jiyo motsin Khausar kuma bata nemi Raudat suyi salla ba  se abin ya bata mamaki bayan ta idar da Sallah ta fito daga Bedroom ɗinta Kai tsaye Bedroom ɗin Khausar ta nufa,

 bakinta ɗauke da sallama ganin Khausar na bacci yasa ta ƙarasa bakin gadon tare da taɓa fuskarta da hannunta dake da damshin ruwa ruwa tana kiran sunanta da faɗin.


“Khausar! Khausar!! Khausar tashi kiyi Sallah maghariba tayi”.

 Momy ke faɗa tana me sake shafa fuskarta da hannunta dake da damshin ruwa.

jin muryan Momy da kuma damshin hannunta da take shafa fuskarta yasa ta buɗe Idanunta ahankali tace.

“Na tashi Momy”.

Juyawa Momy tayi ta fita ita kuwa khausar miƙewa tayi tare da furta.

“Alhamdulillah”,Jin babu ciwo da Zugin da ƙafar ke mata se kuma hannun data ji ya sake baki ɗaya tamkar ba ajikinta yake ba.


Ta lumshe lumsassun idanunta kana ta miƙe ta nufi toilet tana me furta.

“Allahumma Inni Auzubika Minal khubsi wal khaba'is”.

Kana tashiga cikin toilet ɗin da komai ke akimtse yana fitar da wani irin ƙamshi Anutse tashiga yin alwalan har ta ida kana ta fito bayan ta furta.

“Gufra naka”.

 Bayan ta gabatar da Salla tayi adduo'i ta miƙe tare da naɗe darduman se kuma ta juya ta fice tana me buɗe hannunta da rufewa koda ze dawo dai-dai...


Zaune ta samu Momy kan kujera hannunta riƙe da hisnul Muslim tana Azkharul Masa,Yayin da Raudat ke gefenta daga ƙasa tana bin bakinta zama Khausar tayi daga gefen Raudat kanta aƙasa tace.

“Momy gobe zan tafi JAURO YAYAH”.

Da mamaki Momy ta zuba mata ido jin mgnar a bakatatam cike da mmki tace.

“Zaki tafi Jauro yaya kuma Khausar?”.

Ataƙaice Khausar tace.

“Eh”.

tana mai cigaba da jan yatsun hannunta.


Momy ta sake duban ta da mamaki akaro na biyu tace.

“Anma babu yanda banyi dake ba jiya kan cewa kishirya yau kutafi tunda mutanen garinsu na zuwa sallan jumma'a sosai ku tafi tare, kika ce ba zaki tafi dasu ba kuna hadda, sannan kun kusa zuwa ƙarshen surar idan kika tafi karatun ki ze koma baya sannan na yarda na barki kan cewa se sati me zuwa yanzu kuma kice zaki tafi gobe”.


Murmushi ta ƙaƙalo tare  da faɗin.

“A'a Momy babu damuwa munyi magana da Asma'u tace koda awaya zan iya ƙarawa da kaina batare da anwuce Ni ba”.

Dubanta Momy tayi tare da cewa.

“Kin tabbata Khausar har cikin ranki kikeson zuwa Jauro Yaya!?”.


Kai ta gyaɗa tace.

“Eh”.

Aranta kuwa cewa tayi ba gwara masifar wancan tsohuwar ba dan ko yaya bazan tsaya ta dake niba amma wannan mutumin ya riƙa tsareka da firgitattun idanunsa masu saka tsoro da fargaba, baya ga haka in banyi sa'a ba duka na zai sa ayi banyi masa lefi bama idan yasamu sarari sawa yake  aci zalina  bare kuma nayi masa laifi...


Muryan Momy dake cewa.

“Toh shikenan nima nafi so ki tafi Kinga idan hutun ku ya ƙare sannan anƙarasa muku gyaran makaranta seki dawo”.

Ya dawo da ita daga duniyar data lula.


Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Shikenan Momy”, Sannan ta miƙe ta shiga Bedroom ɗin ta.

Momy kuwa Hisnul Muslim ta ɗauka ta cigaba da Azkhar yayin da Raudat ta miƙe tabi bayan Khausar.


Ita kuwa khausar na shiga ɗaki ta hau kan stoll ta janyo trolley ɗin ta sannan tashiga haɗa kaya Raudat dake kallonta tace.

”Dani Zaki tafi Addah Khausi?”.

Girgiza mata kai Khausar tayi alamar a'a.


Kuka Raudat ta fashe dashi tana cewa.

“Ni zan biki”.

Zama Khausar tayi ta riƙe hannunta tare da langwaɓar da kai tace.

“Raudat garin bashi da daɗi fa, ga tsohuwar garin ta fiye masifa, kana yi mata kuskure kaɗan zata  zane Mutum”.

Jin haka yasa Raudat ta girgiza kai tace.

“Nide ba zanje ba idan haka ne”.


Aɓangaren Momy kuwa bayan tashiga turakar Lamiɗo sunyi shirin kwanciya ta dubesa fuskarta ɗauke da murmushi me sanyi tace.

“Uhum wai ɗazu Khausar ke cemin idan Allah yakaimu gobe tana son zuwa Rugar Jauro Yaya”.

Zamanshi ya gyara tare da  faɗaɗa Murmushin dake fuskarsa kana yace.

“Allah ya kaimu hakan nada kyau idan yaso tunda gobe weekend ne zamuje dukan mu kema sai ku gaisa tunda kinyi shekaru baki jeba”.

Kai ta jinjina kafin tace.

“Kai naji dadi Allah ya kaimu”.

Amin yace kana sukaci gaba da hirarsu.


Washe gari Ya kama asabar da wuri Khausar ta tashi ta gyara ɗakinta  sannan ta nufi ɗakin Momy ta gyara kana ta share har zuwa falo da kuma duk sashen saida ta gyara ko wani lungu da saƙo.

Bayan ta gama ta dawo ta shiga kichen ta zuba musu Breakfast soyayyan cheaps da tea  ita da Raudat ke ciki.

Bayan sun kammala ta miƙe tana ƙoƙarin tattare wajen Momy tashigo Idanunta akan Khausar.


fuska ta ɗan tsuke tare da faɗin.

“Maza kije yanzu Aunty Jamila tayi Miki kitso”.

Aunty Jamila matar ƙani Lamiɗo ne sannan Momy tasan inba tayiwa Khausar dagaske to baza taje ba domin bata ƙaunar kitso.


Ganin fuskar Momy babu walwala yasa Khausar gyaɗa kai tare da shiga Bedroom ta ɗauko dogon hijabinta fari Nevy blue daya sha ninkin guga ta ɗaura akan riga da wandon dake jikinta kana ta fice ta nufi gidan Aunty Jamila tana zumɓura baki da kuma kifiya da kum a hannunta.


Bakinta ɗauke da sallama tashiga gidan, Aunty Jamila dake zaune ta amsa Sallamar tana faɗaɗa fara'ar dake fuskarta tace.

“A'a Khausar kece?, sannu da zuwa”.

Sake fuska Khausar ta ɗanyi tace.

“Eh nice Aunty wai kitso nazo kiyi min zanje Jauro Yaya”.

Murmushi Aunty Jamila tayi tare da cewa

“Masha Allah kice zakije ziyara?”.

Kai Khausar ta gyaɗa tana murmushi.

Cikin sakin fuska Aunty Jamila tace.

“Allah Ya kaiku lafiya".


“Amin ya rabbil izzati”.

Cewar Khausar.

“Kinga kuwa kinyi sa'a duk na gama aiyuka na”.

Da sauri tace.

“Aunty Jamila manya fa zakiyi shida ko takwas”.

Murmushi Aunty Jamila tayi.

Kana ta miƙe ta shiga ɗaƙi tare da kwantar da yaronta kana ta fito,

Akan kujeran roba Khausar ta zauna ita kuma ta tsaya ta fara yi mata kitson suna cikin kitson ne suka jiyo Sallamar Gimbiya Dadu.

Anutse Aunty Jamila ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Sannu da zuwa Mama”.

Asaman laɓɓa Gimbiya Dadu ta Amsawa Aunty Jamila baki ɗaya nutsuwarta da hankalinta suna kan Khausar.

Miƙewa Aunty Jamila tayi tashiga ɗaki dan ɗaukowa Gimbiya Dadu Darduman zama.


Ita kuwa khausar ahankali ta ɗago kanta caraf Idanunta suka sauƙa akan Gimbiya Dadu data tsareta da ido ita kuwa khausar cikin hanzari tayi ƙasa da idanunta tana mai karanto duk wata addu'ar da tazo bakinta kamar minti ɗaya Khausar ta sake ɗago kanta akaro na uku still Idanun Gimbiya Dadu na kanta.


Ita kuwa khausar kasa jurewa tayi ta tsayar da Idanunta akan Gimbiya Dadu  cikin dakiya tace.

“Wai dan Allah Gimbiya Dadu Meyesa kike kallona haka?”.

Wani murmushi mai cike da ma'anoni Gimbiya Dadu tayi tare da cewa.

“Uhum yaro man kaza,

ai tunda kika bar cikin Awaki 'yan uwanki kika dawo cikin Kuraye ai dole akalleki! In kalleki in kuma”.

 jin abinda Gimbiya Dadu tace yasa ta miƙe cikin rawan jiki da alamar tsoro aƙwayar Idanunta ta sanya hijabinta ta fita batare data jira Aunty Jamila ta fito ta ƙarasa yi mata kitson ba...


Sauri-sauri gudu-gudu take tafiya har ta isa  bakin gate dinsu da sassarfa ta shigo coumpund ɗin su har yanzu jikinta be daina ɓari ba tana gyara zaman hijabin kanta Momy ta fito,Kallonta Momy tayi tare da cewa.

“Har angama kitson ne".

Ka ta gyaɗa mata ba tare da tace komai ba.

“Dama yanzu zan aika Haiydar ya kira ki kizo mu tafi”.

Murmushin karfin hali ts ƙirƙira kana tace.

“Eh mun gama”.


Wuce ta Momy tayi taje tashiga gaban mota Ita kuwa khausar kallon Raudat, Ramadan, da kuma Haiydar dake tsaye tayi tare da ɗaga musu hannu suma hannu suka ɗaga mata ahankali ta juya ta nufi wajen motar tana isa tasa hannu ta buɗe tashiga gidan baya Haiydar da Ramadan na cigaba da ɗaga mata hannun.

Babban gate mai gadin ya buɗe musu kana Lamiɗo  ya cilla hancin motarsa.

Khausar kuwa jingina bayanta ajikin motar tayi tare da lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da mugun sauri abu biyu ne suka yiwa zuciyarta ƙawanya na farko hukuncin da Moddibo zai ɗauka akanta na biyu kalaman Gimbiya Dadu wanda suke ƙara tabbatar mata da zantuka dake yawo a gari cewa matar nan mayyace...


Anutse Momy ta dubi Moddibo dake sharara gudu akan Lafiyayyan titin nasu tace.

“Abban Haiydar gudun nan baiyi yawa ba”.

Kanshi ya ɗan jujjuya mata,

Ita kuwa cikin sanyi tace.

“Gsky dai ka rage gudun kamar yayi yawa”.

Juyowa yayi ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.

“Lokaci na tafiya kinga yanzu goma tayi gwara mu isa da wuri kada rana tayi mana mu samu mu juyo da wuri”.

Kai ta gyaɗa  kafin tace.

“Amma duk da haka arage gudun".


Tattausan murmushin ya sakar mata  tare da gyaɗa kai...


Sunyi tafiya mai tsawo kafin suka fara hango garin Atake suka fara tabbatar da sanyin da ake acikin Gembila wasa ne.

Domin tun kafin su shiga garin suka hango tamkar hayaƙi ke tashi saboda masifaffen sanyin da ake tsugawa acikin Jauro yaya suna shiga cikin garin suka fara ratsa  bishiyoyi masu korayen ganye suna rangaji tare da fitar da sanyayyan Iska kasancewar hantsi ne duk makiyaya sun tafi  se kuma,

 'yan dalo da aka ɗaɗɗaure masu kyan launi ga kuma kukan tsuntsaye dana zabbi da ke tashi suna ajiye ƙwai.


Suna shiga tsakiyar Rugar Jauro,

 kai tsaye ƙofar gidan dake kusa da babbar fadan Rugar suka nufa anan sukayi parking motar tare da fitowa.


Wasu dattawa dake zaune aƙofan masallacin dake kusa da babbar fadan suka taso baki ɗaya idanun su akan Khausar data fito daga mota tana gyara zaman hijabinta suna faɗin.

“Audiii Barka da zuwa kece?”.

ɗaya daga cikin dattijon ne ya taso wanda ya kasance shine Jauron garin ya riƙe hannun Khausar.

Fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.

”Addah, Addah, Addah, kizo ga Khausar”.

 sauran ma bin bayansu sukayi zuwa cikin gidan suna masuyiwa Momy da Lamido Barka da zuwa.


Biyu daga cikine suka ce da Momy da kuma Lamiɗo.

“Sannunku da zuwa ya kuka tsaya ku shigo daga ciki”.

Kai Momy ta gyaɗa kana suka yi musu godiya bisa jagoranci suka nufi cikin gidan.

Jauro kuwa yana riƙe da hannun Khausar yana mata wasa da faɗin.

“Iyeee girman falo ji jiki kamar auduga,

bakisan riƙe sandar kiwo ba sannan baki san ta tsar nono ba girman burodi wayon shayi kawai”.


Ita kuwa khausar hannu ta wara da faɗin.

“Ban iya ba kam”.

 Murmushi yayi kana yace.

“Zamu koya muki ai”.

 maƙale kafaɗa tayi tace.

“Bana so ba kace min girman bread wayon tea ba”.

Murmushi yay i tare da cewa.

“To girman fura da nono”.

Akuma dai-dai lokacin suka shiga ɗakin tsohuwar wanda yake ginin gargajiya shatin kobo.


Suna shiga Jauro yace. “Addah ga 'yar Usman tazo”.

Ya mutse fuska Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar tace.

“Shegiyar kaya me wuyar ɗauka se yau kika ga damar zuwa??”.

Murmushi Jauro yayi still hannunsa na cikin na Khausar yace.

“Tazo da mahaifiyarta da kuma Mahaifinta”.

Wani kallo Hajja Nana ta masa tare da cewa.

“Kai Jauro ka gyara kalamanka,

 badai mahaifinta ba mahaifin riƙo  dai ko?  ka manta mahaifinta da kai aka binnesa shekaru goma sha biyar da suka wuce?”.

Kai ya jinjina alamar hakane amma bece komai ba ita kuwa miƙewa tayi ta ɗauko taburma ta shimfida tare da ɗauko darduman kilisa ta shimfiɗa.


 A kuma lokacin Momy da Lamiɗo suka shigo cikin sakin fuska tashiga yi musu lale marhaba.

zama Momy da Lamiɗo sukayi akan shimfiɗar data musu kana ita kuma ta zauna awajen zamanta na farko yayin da duka ƙannenta maza suka zauna daga bayanta se ta zamto tamkar sarauniya acikinsu ko wannensu fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.

“Addah yau kam ga Khausar tazo”.

Haka yasa ta juyu.

Ta dubi Khausar da alamun farin cikin ganinta afuskarta saidai yanayin zafinta bazai sa ka fahimta ba.

Ta dubi Khausar da tayi kicin-kicin da fuska tace.

“Menene kike wani kumbura fuska? gwara ma ki saki ranki fa”.


Zumɓura baki Khausar tayi saidai ba tace komaiba.

Hajja Nana kuwa sake kallon Khausar tayi akaro na barkatai tace.

“Ki tashi ki kawo ma baƙi abin taɓawa”.


 Lumshe idanu tayi kafin tace.

“Nice zan kawo abin taɓa wa?,Nima ai baƙuwa ce akawo mana dai”.

 

“Ina magana kina magana!?”.

Hajja Nana ta fadi a faɗace.

Cikin tura baki tace.

“Ai gaskiyane”.

Danƙolo Momy ta yiwa Khausar hakan yasa ta tsuke bakinta.

Ɗaya daga cikin ƙannen Hajja Nana wanda ya kasance shine ƙaramin su (Autah)ya miƙe da faɗin.

“To bari na kawo musu”.

Sannan ya shige uwar ɗakan Hajja Nana ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe da Akwashi ya ajiye agabansu sannan ya koma ya ɗauko goran zuma kana ya koma ya sake ɗauko wani Akwashin.


Hajja Nana ta dubi Momy tare da cewa.

“Ayyah wallahi ban san da zuwanku ba”.

Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai inata gwada kiran layin ki baya shiga”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Kinsan Rugar tamu bamu da network se kaje bishiyar ƙare zancenka  in kaje bishiyar ma seka hau sama ni kuma ban cika son zuwa ba da girmana Inje in hau bishiya na faɗo”.


Khausar kuwa taɓe baki tayi tace.

“Hmmm ba network kuma har sai anje wani bishiya?”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata ta cigaba da cewa.

“Wallahi bansan da zuwan kuba dana shirya muku abin taɓa wa”.

Murmushi Momy tayi batace Komai ba.

Akwashin da aka shigo dashi ne Autansu Hajja Nana ta buɗe Nono ne me zafi yana tururi ga kuma goran zuma dake gefe ɗayan kuma daya buɗe ɗumamen danɗerun zabbi ne suna tururi.

Sauran mazan dake kewaye da Hajja Nana ce suka shiga Gaisawa dasu Lamiɗo.


Muskutawa Hajja Nana tayi tare da gyara zamanta ta kalli Lamiɗo dake zaune ya tanƙwashe ƙafafunsa tace.

Wa'annan daka ke kallo duka ƙannena ne mu goma ne acikin mahaifiyarmu gaba ɗayansu Mazane ni Kaɗai ce mace kuma nice 'yar Fari.


Jinjina kai Lamiɗo yayi yana sauraronta da duka nutsuwarsa duk da yasa abinda take faɗa kishin. tunda ba yaune zuwansa na firkoba.

Ita ko Hajja Nana nuna wanda ke gefenta tayi tare da cewa.

“Ga mai bina Jauro, Sannan kuma sai Sadu, Sannan se Abubakar, Sai kuma Garga, sannan sai Aliyu liman, Sannan kuma sai Dumau ,Sai Salmanu, Sannan kuma Isa sai kuma Umaru”.

Lamiɗo kuwa kallon su yake yana sake tabbatar da abinda ta faɗa saboda kamannin dake tsakanin su.


Hajja Nana tayi murmushi tace.

“Duk ƙanne nane sannan kuma duk da matansu”.

Ta nuna Jauro tace.

 “Matan sa biyu,Garga ma Matansa biyu, Sannan Sadu ma matansa biyu, sai kuma Liman shima Matansa biyu”.

Ta sake nuna Jauro, Sadu, Garga, da kuma Liman tace.

Jauro da Sadu 'ya'yansu maza biyu sunyi aure kuma 'ya'yan Liman da Garga suka Aura ma'ana Auran dangi sukayi”.

Lamiɗo kuwa murmushi yayi alamar yana fahimtar abinda take faɗa masa.


Ita kuwa Hajja Nana  cigaba tayi da  cewa.

“Duk garinmu babu bare mu ya mune, sannan kuma babu maye mu garinmu atsarkake yake kushigo hankalin ku kwance ku fita lafiya,

Salamun Ƙaulan Min rabbil Raheem”.


Momy kuwa sunkuyar da kai ƙasa tayi Saboda tasan ana zargin Mahaifiyar Lamiɗo da Maita.

 Shima Lamiɗo sun kuyar da kansa ƙasa yayi dan yasan zargin da ake yiwa Mahaifiyar sa kenan kasancewar sa mutum me haƙuri da kuma dattako saiya ɗago kansa fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Masha Allah yayi kyau zuri'a tayi albarka Allah yaƙara rufa asiri”.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Ameen ya Allah”.


Domin Hajja Nana 'yar takife ce bata tsoro inma tsoron wani abu ake itace ke isar dashi.

Miƙewa Sauran sukayi suna kallon Lamiɗo suka ce bari mu barku kuci abinci sannan suka fice.


Itama Hajja Nana miƙewa tayi tace.

“Khausar zo mu shiga ciki kici naki”.

Girgizi kai Khausar tayi tace.

“A'a zanci anan”.

Ta juyi ta dubi Khausar da kyau tace.

“Kizo mu tafi nace”.


Shi kuwa Lamiɗo cike da ladabi yace.

“Da kin barta munci anan ɗin babu matsala”.

Juyawa Hajja Nana tayi kafin tace.

“Toh shikenan”.


Miƙewa Khausar tayi tabi bayanta ta karɓo ƙananan akwashi aka zuba mata sannan suma suka zuba,Yanayin sanyin da ake tsugawa agarin yasa mazauna garin ke bukatar abu me ɗumi,Suna cin zabbin suna ɗaurawa da Nono me ɗumi bayan sun gama Khausar ta miƙe ta tattara akushin ta mayar.

Ganin ta mayar ne yasa Hajja Nana fitowa suka zauna.

 Atake sega yara suna ta shigowa a jere a jere angama abincin rana suna kawowa duk gida Jen garin Hajja Nana tana da kwanonta acan suna kawo mata abinci domin ita bata girki abinci safe ne kawai bata Yarda akawo mata ita take dafa wanda zata ci,Duk ƙannenta taran nan sai ankawo kwanuka tara an ajiye mata ga kuma na 'ya'yansu da sukayi Aure tana da ƙore goma sha uku.

Ga yaran garin ƙanana kyawawa dasu farare soll kamar irin yaran ƙauyen larabawa.

Lamiɗo da kansa da yaga yaran na shigowa sun basa sha'awa,Ko wacce idan tashigo zata ce.

“Goggo Hajja! Goggo Hajja!! Aɗonna”.

Ƙannenta da Addah Nana suke kiranta 'Ya'yan  ƙannenta kuma Goggo Goggo Hajja idan kuma jikoki zasuce mata Hajja Nana.

Duk Wacce ta kawo mata abinci zata ce nice,daga gidan Sadu,Nice daga gidan Garga,saboda yawansu kowa ke gabatar da kansa.

Duk wanda yazo ya ajiye zata ce.

“Angode masu nomawa Allah ya basu ƙarfi da lafiyar nomawa masu girkawa ma Allah yabasu ƙarfin girkawa”.


Sannan ga yanayin tsarin yaran garin babu alamar ƙazanta ajikinsu ko wanne tsaf dashi ga kuma tarbiyya duk wanda suka zo sai sun tsugunna sun gaida Lamiɗo da Momy da fulatanci kasancewar basu iya Hausa Sosai ba.


Ɗaya daga ciki data zone ta ajiye kwanon Idanunta akan Khausar tace.

“Goggo Hajja Khausar naa” .

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Eh”.

Murmushi yarinyar tayi ta matso kusa da Khausar tace.

“Sunana Dija”.

Murmushi Khausar tayi tace.

“Yayi kyau Dija”.

Dija ta kuma murmushi tace.

“Kullum Goggo Hajja na bamu labarin ki rabonki da nan tun kina ƙarama yanzu ya kai shekara shidafa ake cewa”.

Kai Khausar ta jinjina da faɗin.

“Eh”.

Hannunta Dija ta riƙe tace.

“Kizo muje gidanmu ku gaisa da Mamana”.

Ta ƙare mgnar tare da jan hannu Khausar suka fice...


Kiran sallan Azahar yasa Lamiɗo ya miƙe ya tafi masallaci tare da Ƙannen Hajja Nana ita kuma Momy tayi alwala tare da gabatar da sallah bayan sun idar da Sallah Hajiya Aysha ta ɓude jakan da tazo dashi ta fito da turaman zannuwa da Sabulai ta miƙawa Hajja Nana.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Hadda ɗawainiya haka?,To angode Allah yayi albarka”.


“Ameen”, Momy ta amsa kafin tace.

“Hajja ga Khausar nan na kawo tayi hutu amma mako uku  ne hutun nasu”.

Murmushi Hajja Nana tayi tace.

“Toh Nagode”.

Ita ko Momy tana gyara mayafinta tace.

“Sati uku  ne hutun nasu”.


Faska Hajja Nana ta tsuke tare da cewa.

“Sai kin sake Jaddada min ne?”.

Da sauri Momy ta girgiza mata kai.

Cikin isa tace.

“Toh sai sanda naga dama zata dawo kinyi naki saura nawa”.

Ƙasa da kai Momy tayi tare da faɗin.

“Shikenan Hajja duk yanda kikace yayi mukan zamu tafi”.


Miƙewa Hajja Nana tayi tace.

“Bari akira muku Khausar kuyi sallama”.

Cike da ladabi Momy tace.

“A'a Hajja base ankira taba”.

Dan tasan muddin aka kirata sai tayi kuka kafin su rabu.

Sallama suka sake yi musu kafin suka fice suka tafi...


Acan Gembila kuwa Washe gari.

Asabar Moddibo ya shirya kamar ko yaushe cikin Jallabiya Sky blue Kansa sanye da hula da kuma hirami cikin nutsuwarsa kamar ko yaushe ya shiga cikin makarantar yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi da hannu kawai yake amsa gaisuwar da ɗaliban haddar ke masa kai tsaye Ajin haddarsu Khausar ya nufa yayin da Aransa yayi ƙudurin sawa Malam Bello ya casa masa ita saboda gaba ta kiyaye domin ya lura ganganci da sakalci ke damunta.

Cikin rashin sa'a yana shiga ajin ya samu bata nan.

 Asma'u ya kira.

Cike da ladabi ta fito tare da tsugunnawa agabansa tace.

“Gani Yah Moddibo”.


 Tsayuwar sa ya gyara cikin yanayin sanyin Muryansa yace.

“Ina wannan Birin?”.

Asma'u kuwa kanta aƙasa tace.

“Nima yau da nazo ban ganta ba sai nake tambayar Amina ina take shine tace wai taje garin Kakanninta”.

Ƙwafa yayi yace.

“Shikenan yayi kyau”.

Kana ya juya ya bar waje....


Acan mota kuwa Momy ta dubi mijinta tace.

“Kayi hakuri da Hajja Nana yanayin tsufa ne”.

Murmushi yayi still Idanunsa ahanya yace.

“Ai bakomai ba gamu da Gimbiya Dadu ba ai haka take”.


Acan Rugar Jauro yaya kuwa bayan Khausar ta dawo gida ta tar da Momy ta sun tafi ta tsare Hajja Nana da ido tace.

“Meyesa ba ki kirani ba kafin su tafi?”.


Salati Hajja Nana ta sanya tace.

“Tuhuma ta kikeyi? Ko kuma me?”.

baki ta cinna sama tare da cewa.

“Ai gaskiyane abinda ya dace na faɗa”.

Salati Hajja Nana ta sanya tare da faɗin.

“Ohhh ni Shatu Allah ya nuna min 'yar Usmanu yarinya kamar ruwan aski sai rashin ta ido”.

Ta ƙare mgnar tana kallon Khausar dake tsaye fuska akumbure cikin tsawa tace.

“Bari kiji in faɗa miki ni agarin nan idan nayi magana kamar yankan wuƙa yake babu me bani Amsa ko musu ko jayayya dani!”.

Ita kuwa Khausar wani irin juya Ido sama tayi tare kana tace.

“Uhummm to gwara ma ki sani.

Idan maganarki yankan wuƙa ne to kin samu me yankan rez”......!




Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA



                           By

       *GARKUWAR MARUBUTA*

No comments

Powered by Blogger.