Sakayya 13

 


📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇


                 *SAKAYYAH*

                    _Page 13_

      

                              _NA_

              *AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama, ba haƙƙin kowa akanki. Littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin littafin inda zan rinƙa posting. 



*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*


_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._



               

      🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,



Khausar kuwa cikin tsare Hajja Nana da ido ta riƙe ƙugu tare da cewa.

“Gaskiya nikam bana son irin wannan mulkin mallakar naki”.

Da sauri Mommy ta ɗaga mata hannu fuskarta babu walwala ta kalli Khausar kana tace.

“Kifita, daga nan Khausar!”.

Lokaci daya fara'ar data shigo da shi ya gushe  ɓacin rai ya mamaye mata zuciya juyawa tayi ta fice daga Bedroom ɗin Mommy ta nufi nata tana shiga Bedroom ɗin ta jiyo  Muryan Asma'u afalo.

Kai tsaye Bedroom ɗin Khausar Asma'u ta shiga tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Atare Dije da Khausar suka amsa da.

“Wa'alaikum Salam”.

Asma'u naganin fuskar Khausar ta ware Ido kana tace.

“Ya dai mutuniyar naga fuskarki haka?”.

Wani abu mai masifar ɗaci Khausar ta haɗiye Idanunta akan Asma'u dake tsaye ta gyara zamanta tare da faɗin.

“Babu komai ƙara so ki zauna”.


Zama Asma'u tayi tare da tsare Khausar da ido ganin yanayin damuwa atare da ita.

Kallon Dije Khausar tayi sai kuma ta juya ta kalli Asma'u tare da faɗin.

“Wannan Itace Dije”.

Murmushi Asma'u tayi Idanunta akan Dije ta ajiye Handbag din dake hannunta kana tace.

“Sannunki”.

Murmushi Dije tayi tare da faɗin.

“Yawwa”.


Juyawa Asma'u tayi tare da kallon Khausar kana tace.

“Khausar wacece ban ganeta ba”.

Muskutawa Khausar tayi tare da gyara zamanta kana tace.

“Dije ce wacce nake baki labarin ta a Jauro Yaya”.

Jinjina kai Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ohh Ayyah na tuna ta itace tazo ita da Hajja Nana suka zone?”.


Khausar kuwa kai ta gyaɗa mata kana tace.

 “Eh"

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Ai lallai dai kam kice muna da manyan baƙi Dije amma zamu daɗe ko?”.

 Kai ta girgiza tare da yin murmushi kana tace.

“A'a yau zamu koma ”.

Ware ido Asma'u tayi tare da faɗin.

“A'a yau zaku koma kuma?”.

Sai kuma Asma'u ta juya ta kalli Dije kana tace.

“Shaf-shaf haka?”.

Ita dai Khausar na gefe ta jingina bayanta da jikin gado Idanunta alumshe tana tunanin maganar Hajja Nana.

Kai Dije ta gyaɗa tare da faɗin.

“Eh ai da Yaya Aliyu muka zo”.

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ayyah ai kam munji daɗin ganinki”.


Asma'u kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar wacce ta tsirawa waje ɗaya Idanu cike da kulawa Asma'u ta dafa kafaɗar ta kana tace.

“Wai Meye ne kike ta haɗa rai!?”.

Iska mai zafi ta furzar tare da kallon Asma'u fuskarta babu walwala ta saki Ajiyar zuciya kana tace.

“Kina ji wata magana da wannan tsohuwar tazo dashi wai batun Aurena!kuji min tsohuwar nan da wani iyayi ta bari Iyayena suyi magana akai na mana ita kuma kaka wake maganarta!?”.


Asma'u kuwa Dariya mai sauti tayi tare da cewa.

“Iyeeee kice zamu sha bidiri!”.

Dije tayi murmushi kana tace.

“Barta dai kuma ma kinga mijin data samun ne kyakkyawa fa?”.

Baki Khausar ta kuma taɓewa tare da wurga musu Harara kana tace.

“Toni ina ruwana dashi?,

Ni bana so kada ma ayimin wannan maganar tsakani da Allah shi yafara Auren yayata fa Asma'u”.

Da sauri Asma'u ta ɗago kanta tare da cewa.

“Addarki kuma?, Dama ba kece ƴar farin Mommy ba?”.

Jinjina mata kai Dije tayi tare da cewa.

“Eh ba ita bace ƴar fari Akwai Addarta Nenne Amma ta rasu kuma itama Yayanta Aliyu aka aura mata sunyi aure da shekara biyu ta samu ciki tazo wajen haihuwa ta rasu!”.

Asma'u ta jinjina kai tare da cewa.

“Allah sarki Allah ya gafarta mata,.

Ohh Ashe shiyasa Mommy bata kunyar kiran sunanki nida duk atunanina kece ƴar fari har nace Mommy ƴar zamani ce bata ɓoye sunan ki”.


Kai Khausar ta girgiza kana tace.

“A'a ba nice ƴar fari ba ni ta biyu ce”.

Murmushi Asma'u tayi tare da faɗin.

“Ohhh lalle kam kice zamu sha biki”.

Khausar kuwa fuska ta tsuke kana tace.

“Zaku sha bikin waye?”.

Dariya Asma'u tayi tare da cewa.

“Bikin ki mana”.

Cikin haɗe rai Khausar  kai ta girgiza tare da faɗin.

“Asma'u kiyi min fatan alkhairi mana, kina jin tsohuwar nan da shiririta da shirme wai ko bayan sallah za ayi ko menene oho?”.

Dije kam kai ta girgiza tare da cewa.

“Bafa cewa tayi bayan sallah ba ita dai alissafinta ki gama karatunki sai anyi idan yaso in kinaso kici gaba da karatunki sai Yaya Ali ya saki ki cigaba dayi a Adamawa bayan sallan baɗi take nufi”.


Fuska Khausar ta ya mutse kana tace.

“Aima Allah ya kiyaye abar mutum yayi karatunsa mai zurfi mana sannan ai mutum nada tsarin rayuwarsu da kuma yanda yake so ya kasance haka kawai sai atakura min”.

Dariya Asma'u tayi tare da cewa.

“Mu dai kar ki mana baƙin ciki ki hana mu shan biki”.

Harara Khausar ta maka mata kana tace.

“Ai sai kuyi shagalin ku kuka ɗai”.

Dije na dariya ta dubi Khausar kana tace.

“Yo ina zamuyi shagali ba Amarya ai dan ke za'ayi”.

Baki Khausar ta taɓe kana tace.

“Ai lalle dai kam”.


Mommy ce tashiga ɗakin bakinta ɗauke da sallama kallon Asma'u tayi kana tace.

“A'a Asma'u kece yaushe kika zo”.

Asma'u kuwa zamewa tayi daga kan gadon tare da cewa.

“Ban daɗe da zuwa ba Mommy Ina yini?”.

Mommy ta amsa da.

“Lafiya lau alhamdulillah yasu Umminki?”.

Miƙewa Asma'u tayi tare da zama agefen gadon kana tace.

“Tace agaisheki”.

Masha Allah Mommy ta faɗa tare da maida kallonta kan Dije kana tace.

“Dije kizo Hajja Nana na kiranki wai zaki rakata gidan Aminiyarta”.

Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.

Miƙewa Dije tayi tare da kallon Khausar kana tace.

“Khausar mu tafi mana”.

Fuska Khausar taya mutse kana tace.

“A'a kuje kawai Allah ya kiyaye hanya ni bazan jeba, muyita faɗa da ita a gidan  mutane muna raba hali agidan mutane duk inda mukaje sai ansan mu”.

Murmushi Dije tayi tare da faɗin.

“Toh shikenan mun tafi”.

Sannan ta fice kai tsaye ɗakin Mommy ta wuce sannan ta samu Hajja Nana atsaye.

Hajja Nana na kallonta tace.

“Wuce ki kira su Aliyu mu tafi”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan ta fice.

Mommy kuwa Jakar data haɗa wa Hajja Nana tsaraba ta ɗauka sannan ta fice.

A coumpund ɗin ta samu Yaya Aliyu da Yaya Abba tsaye jikin mota cike da girmamawa da kuma ladabi Ya Aliyu ya kalli Mommy tare da cewa.

“Toh Mommy mun gode Allah ya saka da alkhairi Allah yabar zumunci”.

Murmushi Mommy tayi tare da cewa.

“Amin, Allah ya tsare muku hanya”.

Hajja Nana ta amsa da.

“Ameen”.

Tare da buɗe bayan motar tashiga Dije ta zauna agefenta Yaya Aliyu na gefen mai zaman banza Yah Abba kuwa shike Driving suka fice daga gidan.

Sai da Mommy taga fitar su sannan ta koma cikin gida.


Yaya Abba kuwa kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa.

 Hajja Nana nayi masa kwatance har suka isa gida suna shiga gidan.

Cikin sauri Yaya Ali ya lumshe Idanunsa kana yace.

“Masha Allah wlh Ina son garin Gembulan nan saboda yana da kyawun tsari dan yafi Adamawa kyawun tsari da komai akwai yanayin sanyi da daɗi”.

Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.

“Aikam sosai ma”.

Yaya Ali ya juya tare da kallon Hajja Nana kana yace.

“Hajja Nana wannan kuma gidan  wacece ɗinkin ne?”.


Murmushi Hajja Nana tayi alokacin da take sauƙa amotar ta kalli Ali kana tace.

“Ƙawata ce tare mukaje da ita aikin hajji na farko na biyu ma tare muka je sannan ko daga baya muna yawan zuwa   Umarah tare da ita”.

Murmushi Yaya Ali yayi tare da cewa.

“Ai dai lalle kam kice gidan Aminiyar kice?”.


Dariya Hajja Nana tayi tare da cewa.

“A'a sosai ma kam”.

Dai-dai lokacin da suka isa ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da farfajiyar tsakar gidan Innayi.

Innayi dake zaune ta hango Hajja Nana da baƙi abayanta,

Cike da fara'a ta miƙe da sauri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi mai cike da jin daɗi ta matso kusa da Hajja Nana kana tace.

“Aaaa Lalle marhaba Hajjaju Makkatun Masha Allah Hajiya Nana mutanen Makka lale marhaba ku iso”.

Ta faɗa tare da juyawa ta shiga ɗaki tare da ɗaukan lallausan Chanis capet ta shimfiɗa musu.


Sai kuma ta fito cike da farin cikin daya kasa ɓoyuwa afuskarta kallon Yaya Ali tayi tare da cewa.

“Wannan shine  Mijin namu na Adamawa da kike bamu labarin?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana murmushi kana tace.

“Eh”.

Innayi ta juya ta kalli Hajja Nana kana tace.

“Ku shiga”.

Sannan ta kalli Yaya Abba da Yaya Ali kana tace.

“Ku ƙara so”.

Ta faɗa tare da ficewa Innayi ta nufi sashen Moddibo tare da cewa.

“Moddibo, Moddibo ga baƙi munyi”

Shi kuwa Moddibo atare suka miƙe da M Jameel suka fito.

Ɗan sake fuska Moddibo yayi kana yace.

“Sannunku da zuwa ku iso”.

ya faɗa tare da matsa musu.


M Jameel na ganin Yaya Abba ya miƙa masa hannu fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.

“Ha'a Abba kaine?”.

Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.

“Ni ne dai”.

M Jameel yayi dariya kana yace.

“Sannu ku da zuwa”.


Yaya Abba na bin bayansu yace.

“Laaa Jameel nan gidan kune?”.

M Jameel yayi Murmushi tare da shafa sajensa ya kalli Yaya Abba tare da faɗin.

“Eh gidan mune!”

Murmushi Yaya Abba yayi da faɗin.

“Masha Allah”.

sannan suka shiga falon din wanda tuni Ya Ali da Moddibo suka shiga.


Innayi dake tsaye ta juya tare da cewa.

“Moddibo zoka kawo musu abin taɓa wa”.

Daga ciki Moddibo ya miƙe kana yace.

“Toh Innayi”.

Sannan ya fice tare da bin bayanta.

Juyawa Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake biye da ita kana tace.

“Kashiga daga ciki ka gaida ƙawata Hajja Nana dana ke ce maka munje aikin Hajji na farko dana  biyu kuma yawanci Umarah ma tare muke zuwa ɗakin mu ɗaya tun da take zuwa gidan nan bata taɓa samunkaba,

Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Na'am”.Ya ida maganar tare da shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama Idanunsa ya sauƙa akan tsohuwar da yaje ya yamata ta'aziyya a Jauro Yaya.

Cike da nutsuwa da kuma ladabi ya zauna daga gefenta kana yasa hannu ya shafa sajensa cikin yanayin rashin walwalarsa yayi ƙasa da kansa tare da cewa.

“Sannun da zuwa”,Ya gaisheta batare daya nuna ya ganeta ba.


Hajja Nana kuwa Kallonsa tayi kana tace.

“A'a kamar nasan wannan fuskarta fa, kwanaki kamar kunje da wani abokin Malam Liman mai suna Malam Arɗo ko?”.

Kai Moddibo ya jinjina still Kansa a ƙasa kana yace.

“Eh”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Ayyah sannun ka ashe dai Jikana ne Allah yayiwa rayuwarka albarka Allah yabaka zuri'a ɗayyiban”.

Still Kansa A ƙasa ya shafa kwantaccen sumar  kansa mai sheƙi da yalƙi kana yace.

“Ameen Ngd”.

Ya ida maganar  a taƙaice tare da miƙewa ya fice.

 Tiren da Innayi ta haɗa Gasassun Zabbi da  M jameel yasa ta gasa musu, shinkafa da miyar dage-dage da yaji naman kaza sai Akwashi dake ɗauke da ƴaƴan itatuwa ta miƙawa Moddibo amsa yayi kana ya nufi sashen sa dashi.


Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga tare da ajiye Tiren akan center table dake tsakiyar falon kana ya maida kallonsa kan M Jameel dake ta hiran Yaushe gamo da Yaya Abba kai ya girgiza tare da cewa.

“J miƙo musu ruwa acikin fridge ka barsu haka gashi har na dawo baka kawo musu komai ba”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Wallahi muna ta hiran yaushe gamo da Abba nasan sa mun taɓa haɗuwa dashi a Adamawa”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kushin kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Ayyah ashe kunsan juna”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa alamar Eh.

Ya Ali kuwa hankalin sa ya mayar kan wayarsa yana latsawa.


Acan ɗakin Innayi kuwa zama Innayi tayu tare da kallon Hajja Nana kana tace.

“Yanzu ma kinzo wajen jikar tamu ce?”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.

“Eh wallahi".

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Shine baki zomin da ita ba”.

Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.

“Barta ba shiri muke da ita ba fitsararriya ce yanzu ma nazo ne akan batun aurenta da yayan ta amma na lura ma kamar batason abin ko yayane ohon mata kinsan ƴaƴan yanzu da tsaurin ido su suke zaɓawa kansu maza yanzu ma na barta tana can tana kumbure kumburen baki”.

Murmushi Dije da ke kurɓan tes tayi aranta tace Dramer Hajja Nana da Khausar bai ƙarewa.


Innayi kuwa murmushi tayi kana tace.

“Ayyah ai da tazo na ganta kice mu shirya akwai shan biki?”.

Dariya Hajja Nana tayi kana tace.

“Ai dai kam Insha Allah akwai shan biki dan biki yana nan yana tafe”.

Innayi kuwa kai ta gyaɗa kana tace.

“Lallai abu yayi kyau amma dai zamu kwana”.

Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.

“A'a yanzu ma zamu tafi dan mun sallami can kam da zan tafi da jikar tawa ma to sai mahaifiyata take ce min bata da lafiya don haka na barta saboda tana taimakawa mahaifiyar tan da ɗan aikace-aikacen yau da kullum”.


Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.

“Ayyah Allah yabata lafiya.

Yaushe zamu koma Umarah bana zaki je na Ramadan?”.

Hajja Nana kuwa kai ta jinjina kana tace.

“Eh Insha Allahu zanje in Allah ya yarda amman ta Adamawa zan tashi kefa zakije kuwa?”.

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Nima zanje in Allah ya yarda amman kin san ni ta nan Jaligo zan tashi”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.

“Abu yayi kyau Ubangiji Allah yasanya alkhairi Allah ya bamu sa'a”.


Innayi ta amsa da.

“Ameen”,kana ta cigaba da cewa.

 “Nima zamu tafi da jikina da kuma abokinsa tare za muje”.

Dariya Hajja Nana tayi kana tace.

“A'a abu yayi kyau to sai mun haɗu acan ɗin”.

Hiran yaushe gamu suka cigaba dayi yayin da Dije ke gefe tana yagar Gashesh-shen Zabbi da nonon shanu mai ɗumi.


Acan falon Moddibo kuwa bayan sun gama gaisawa Yaya Abba da Yaya Ali suka sha fruit din kana suka ci gashshen Naman  dake fitar da ƙamshi tare da ruwan Tea mai zafi.

M Jameel ya kalli Yaya Abba daya koma ya zauna tare da rufe Warmers din Cike da kulawa ya sake Kallonsa kana yace.

“Abba ya bakuci abincin ba”.

Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.

“Wallahi aƙoshe muke yanzu ma dan kar kuce munƙi cin komai ne amma Alhamdulillah”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Toh shikenan”.

Miƙewa sukayi Atare jin Innayi na cewa.

“Moddibo kufita Hajja Nana zasu wuce”.

Da to Moddibo ya amsa kana suka fita cike da kulawa M Jameel da Moddibo suka kalli yaya Abba da yaya Ali atare suka haɗa baki wajen faɗin.

“Toh mun gode da ziyara Allah yabar zumunci”.

Yaya Ali ya amsa da.

“Ameen”.

Sannan Yaya Abba yashiga mazaunin Driver Yaya Ali kuma ya zauna gefen mai zaman Banza yayin da Hajja Nana da Dije suka zauna abaya M Jameel ya miƙa kansa ta window tare da ajiye wa Hajja Nana kuɗi akan cinyarta tare da cewa.

“Allah ya tsare”.

Murmushi tayi kana tace.

“Allah ya muku albarka nagode”.

Motar Yaya Abba yaja suka fice saida motar ta fita layinsu kafin Innayi, Moddibo,da kuma M Jameel suka koma cikin gida.


Cikin awa biyu Hajja Nana suka isa Jauro Yaya Washe gari Da safe yaya Ali ya koma Adamawa dashi da Abba suka tafi.


A ɓangaren Khausar kuwa tunda daga ranan da Hajja Nana tayi mata maganar aure ta watsar da maganar kasancewar Momynta bata sake yi mata maganar ba ita ma bata sake tada maganar ba hakan yasa bata ɗauki maganar da muhimmanci ba ita kuwa Mommy tasa aranta tun daga Ramadan ya kawo kai ta samu dama ta yanda zata roƙowa ƴar ta al'khairi idan har Aliyu al'khairi ne agareta Allah ya tabbatar mata da al'khairi idan kuma ba al'khairi bane Allah ya zaɓa mata mafi al'khairi shima kuma Allah ya musanya masa da mafi al'khairi.


Yau ya rage azumi saura kwana biyu da hantsi Mommy na zaune afalo taji Sallamar sabon mai gadinsu da aka kawo kallon Khausar dake riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar tayi sai kuma ta maida kallonta ga Haiydar dake danna wayarta ta gyara zamanta tare da cewa.

“Haidar jeka duba lafiya Namadi ke Sallama”.

Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.

“Toh Mommy”.

Sannan ya miƙe ya fita.

Kallon Namadi dake tsaye yayi kana yace.

“Lafiya kuwa”.

Kai Namadi ya gyaɗa tare da faɗin.

“Kayane Alhaji ya aiko dasu Azo ashiga dashi ciki”.

“Ok kashigo dasu”. Ya faɗa tare da juyawa ya koma ciki.


Kallon Mommy Haiydar yayi kana yace.

“Kayan azumine Abbah ya aiko dasu shine Namadi zai shigo dasu”.

Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.

“Ok”.

Da Sallama Namadi yashigo kansa ɗauke da buhun shin kafa ya ajiye a store kana ya koma ya ɗauko na ɗanyen shinka yakai, sannan ya kuma kimawa ya rinƙa shigo da catton ɗin indomie, Catoon ɗin Spaghetti, Cotton ɗin Macoroni, Couscous, Buhun fulawa, Buhun niƙeƙƙen garin gero na kunu, buhun wake, buhun sugar Corn Flakes, Madara, Patoto, Doya Crate din ƙwoyi Jarkan mai Jarkan man ja haka ya riƙa shigowa da tarkacen kayan buƙata na Ramadan.


 Kamar yanda ya kawo sashen su Khausar haka ya kai sashen Hajiya Bunayya.


Yayinda hakan take a kowani gida haka magidanta suka riƙa shiga da kayan azumi domin shiryawa wannan wata mai falala.


Acan ɓangaren gidansu Moddibo kuwa shida M Jameel amota Moddibo ke driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza sai kuma wani yaro daga baya mai suna Iro wanda ke musu aika hong sukayi aƙofar gidansu Moddibo kana suka shiga cikin gidan bayan Iro ya fita ya buɗe musu.

Innayi na zaune atsakar gida akan kujera ƴar tsugunno taji ƙaran mota na shiga cikin harabar gidan aranta tace yau lafiya Moddibo ke shigowa da mota har cikin gidan.

Moddibo kuwa  kusa da Innayi yayi Parking motar tare da buɗe Murfin motar ya zira ƙafarsa ɗaya awaje ɗaya kuma na ciki M Jameel da Sadik kuma suka fita kusa da Innayi M Jameel ya zauna shi kuwa Sadik Boot ɗin motar ya buɗe tare da fito da buhun far n gero,  Buhun wake, Buhun shinkafa ɗanye da gumi, Catoon ɗin indomie, Catoon, Spaghetti, Bushesh-shen kifi crate ɗin ƙwoyi, Gongwanaye mayen madara da Vournvita buhun, Sugar kwalin Lipton sai kuma naman rago da aka gyara gaba ɗaya ga kuma na shanu ga kifaye duk Sadik yasa su a fridge


Kallon Moddibo Innayi tayi sai kuma ta maida kallonta kan M Jameel dake kusa da ita tayi tare da cewa.

“Lalle kayan Azumi sun saƙƙo ga Azumi sai ƙaratowa yake yau saura kwana biyu ko uku”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Ai dai kam Innayi azumi yazo”.

Ya ida maganar tare dasa hannu acikin aljihunsa ya ciro Bandir ɗin kuɗi kimanin dubu ɗari ya miƙawa Innayi tare da faɗin.

“Innayi gashi babu yanda banyi da Moddibo ba yabarni in saya miki kayan Azumi amma dake ɗan baƙin haline baya so in samu lada yaƙi furrr yace komai shi zai siya gashi wannan ki riƙe kiyi yadda kika ga dama dasu”.


Kallon kuɗin Innayi tare da Girgiza kai kana tace.

“Ayyah Jameel am bana son wannan shungullan yanzu ni kuma me zanyi da wannan kuɗin kabar su Jameel am ni ba ɓuƙatar su nake ba”.


M Jameel kuwa zama ya gyara tare da fuskantar Innayi da kyau kana cikin wata raunan'niyar Murya ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Tunda muke tare daku tsawon shekaru Innayi daga ke har Moddibo ban taɓa ɗaukar abu in baku ku karɓa ba, duk abinda na baku sai kun mayar min dashi baya, ban sani ba wataƙil shi Moddibo yana ɗaukar Maganar Aunty Karima keyi amatsayin matakin ƙin karɓan abu awajena”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da jingina kansa da Murfin motar yana sauraron abinda aminsa ke faɗa.

Ita kuwa Innayi idanu ta zuba masa tana nazarin kalamansa.


M Jameel ya cigaba da cewa.

“Abinda Moddibo bai saniba koya karɓi abu awajena ko karya karɓa ita gani take komai na rayuwarsa Ni nake masa dan haka gwara ma ya karɓa idan yaso ta tuhumesa da tushe”.

Ya furzar da iska mai zafi kana ya cigaba da cewa.

“Kema kuma Innayi ina ganin maganar mutane kike ɗauka da suke cewa Babana ke daukar ɗawainiyar ku amma ni nasan ba haka bane. Allah ne kaɗai ya barwa kansa sanin yanda kuke rayuwarku duk da aminantakar dake tsakani na da Moddibo har yau ɗin nan bansan taya kuke mu'amala da rayuwarku ba bansan ta yanda kuke samun abinda kuke biyan buƙatar rayuwarku ba kama daga karatun Moddibo kab babu aƙaramar makaranta zuwa hidimar fitanmu Makarantar waje ina sane ina kuma tunawa Naira biyar kun ƙi karɓan tallafi awajen Babana ku keyin komai abinda yasa mutanen gari suke ɗaukar haka suna lura da Moddibo ba wani sana'a yake ba sannan ana mamakin irin buƙatun da kuke yafi ƙarfin samun ku ko kuma tattalin ku Innayi!”.


Dariya mara sauti Innayi tayi tare da jinjina kai kana ta tsaida idanunta akan Moddibo daya dafe kansa sai kuma ta kalli M Jameel daya dafe kansa tayi murmushi tare da cewa.

“Abun aduhu ne Jamilu barshi kawai babu ɓuƙatar sai ansani,  shi kansa Moddibo bai san komai akan al'amuran rayuwar nan ba bare ya gaya maka”.

Moddibo kuwa Sanyayyar Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon M Jameel ya buɗe masa hannunsa alamar kaji dai  nima bansan komai ba a cikin abubuwan da kake son sani.

Sai kuma Moddibo ya numfasa tare da lumshe Idanunsa kana cikin sanyin murya mai cike da rauni ya kalli Innayi tare da cewa.

“Kagani ni kaina ban san komai  ba kama daga lokacin dana ke karatu.

 Ni dai nasan tana min komai idan nayi magana sai tace gadon Iyayena da suka bar min ne, bansan inda ta ɓoye kuɗin ba na girma ma yanzu ta bani gadona ahannuna taƙi ko gani take har yanzu ban kai ba oho.

Kai kuma kana tuhumata kamar acikin aminantakar mu akwai abinda nake ɓoye maka, bayan kuma J ka sani babu wani shamaƙi tsakaninmu”.

Ya ƙarisa mgnar tare da

runtse idanunsa a take kuma ya  buɗe su akan M Jameel da shima shi yake kallo, a hankali ya furzar da iska mai sanyi tare da cewa.

“J ba'ayi wani abu na duniya da ni Aliyu zan iya ɓoye maka ba, aminantakar mu ta wuce babin in ɓoye maka wani abu”.

Jinjina kai M Jameel yayi yana kallon amininsa cike da tausayawa.


Innayi kuwa murmushi tayi tare da jinjina kai amma ba tace komaiba ba.

Moddibo kuwa kallon Innayi yayi kana yace.

“Yanzu kuma hidimar da nake kai kan ka kasan inda nake samu tunda muna aiki kuma ana biyan mu sannan kuma. Ni kaina wataran saidai inga tayi min abu misali yanzu mota dai ni bansa araina ba kafin in ankara har ta saya anyi komai kafin ma mu dawo”.

Numfashi ya sauke  kana ya cigaba da cewa.

“Babu yanda banyi da ita ta faɗa min ba idan ma a kuɗin gado nane tunda na girma ta bani abuna zan iya sarrafawa”.

Hararansa Innayi tayi kana tace.

“Anƙi abaka”.

Shiru M Jameel da Moddibo kai ya jinjina ba tare da tace komai ba sai tsirawa Innayi ido da sukayi.

Miƙewa M Jameel yayi yace.

“Bari mu tafi Innayi”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Allah ya tsare”

Suka amsa da.

Amin

Shi kuwa Moddibo Kallon Innayi  yayi kana yace.

“Innayi har yanzu yarinyar nan bata zoba?"

Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa.

“Dama wannan shekarar Ummin Asma'u tace in bari zata turo min Asma'u dan ƴaƴan ƙabilun in sun zo gaba ɗaya lalata sukeyi sannan basajin magana to Asma'u zata zo ta tayani”.

Cikin kula ya kalli  Innayi  kana yace.

“Innayi anya Asma'u zata iya ayyukan da suna da yawa fa kinga akwai abincin da za'a dinga fitarwa na masallaci”.

Jinjina kai Innayi tayi kana tace.

“Zamu iya ai naga Asma'u tana da kuzari kuma nima da kuzarina da kuma lafiyata zan iya”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Toh Allah ya temaka”.

Ta amsa da.

“Ameen”,Kana tace.

“Ai girkin ma na iya tsawon kwana goma sha biyar ne zamuyi”.

Kai M Jameel ya Jinjina kana yace.

”Eh haka ne Innayi”.

Sallama suka mata sannan M Jameel ya Miƙe.

Dama already Moddibo na cikin motar yaja suka tafi.


Kai tsaye kasuwa Moddibo ya sake nufa Kallonsa M Jameel yayi kana yace.

“Mai zamu kuma yi a kasuwa?".

Ba tare da Moddibo ya juya ya kallesa ba ya lumshe idanunsa kana yace.

“Idan muka je za kaga ni”.

Shiru M Jameel yayi har suka isa kasuwar kamar yanda Moddibo yayiwa Innayi siyayya haka ya sake sayan wasu Kallonsa M Jameel yayi tare da cewa.

“Wannan kayan na waye haka?”.

Anutse Moddibo yace.

“Ina ruwanka”.

Daga haka yaja motar suka fita kai tsaye hanyar gidan Ummi ya nufa.

Da sauri M Jameel ya juya ya kallesa kana yace.

“Ai baka isa ba Ummi ba zata karba ba ai kai ma idan zan kaiwa Innayi abu hana wa kakeyi”.

Moddibo kuwa baki ya taɓe kana yace.

“Ai ba Umminka kai ka ɗai bane harda ni dan haka kabarni in  samu lada”.

Murmushi M Jameel yayi Amma baice komaiba.



Koda suka isa aka shigar da kaya, M Jameel yayi wa Ummu bayanin yadda sukayi.

Ita kam Ummi sai ta riƙa sakin murmushi bayan ta gama jin jawabin M Jameel sai kuma ta kalli uban kayan da aka shigo dasu ta juya ta kalli Moddibo daya tanƙwashe ƙafafunsa tare da sunkuyar da kansa ƙasa tayi murmushi fuskarta ɗauke da murmushi cike da ƙaunarsu ta saki ajiyar zuciya kana tace.

“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Ubangiji Allah ya baku ƴaƴan da zasuyi muku biyayya fiye da yanda kuke mana”.

Atare suka amsa da.

“Ameen”, Bayan sun sake taɓa hira suka miƙe tare da yimata sallama suka tafi...!








                        By

      *GARKUWAR MARUBUTA*

No comments

Powered by Blogger.