Namijin Zuma 7


 SAADATU BINTU ABDULLAHI (Writer of kyautar Allah)

Free page6

Jin muryarta ya haifar masa dajin Wani irin sanyi me sanyaya ruwan jiki, ya sauke ajiyar zuciya 2tyms a jere ya lumshe Ido ya sake budewa kana yace. "mommy bani da lafiya wallahi..." Ya fadi a shhagwabe kmr me

Shirin fashewa  mata da kuka. Ya saba mata shagwaba Amma wannan Karan  Se taji abun ya mata gatsal kmr bata saba ji ba. "Subhanallahi Meya sameka?"  Ta fadi cikin sanyin murya sabanin farko data daga wayar. "Wani Abu nakeji mara dadih a jikina da zuciyata..." Ya fadi Yana mejin Sanyi a jikinsa kaso Dari na abinda ke damunsa ya ragu zuwa tamanin  sbda muryarta kawai dayaji, shide be tabajin abinda yakeji ba a kanta kamar na yau,ada inyaji muryarta ba haka yakeji ba.  "Kamar me babyna? Banason abinda ze dameka pls,, Ba munyi magana dakai ba a kan kan ka denasa damuwa a ranka Dan Allah kayi Adduarh itace maganin komi na rayuwar duniya, haba Jarumina!" Ta fadi tana mejin yanayi mara dadih a jikinta sbda ko a muryarsa ta tabbatar da Wani Abu na damunsa Amma setasha ko damuwarsa da na'eema ce. 'ajiyar zuciya kawai Aeezad ke saukewa yana me sauraronta kawai shi kadai yasan meke damunsa, shide yasan ba dmwar na'eema bace a wannan karon kuma besan meke damunsa ba. "kaji babyna !'' ta fadi jin yayi shiru sede ajiyar zuciyarsa kawai take juyowa ta cikin wayar. "Naji mommy insha Allahu zanyi Addu'ah kema kiyi min pls ....''  ya fadi cikin sanyi. Nabeelah ta jinjina tabbas yasa damuwa a ransa sbda muryarsa ta nuna alamar nadama a ciki duk yayi sanyi shida bakinsa be mutuwa  Amma yau murus take jinsa, ko maganar batsa babu a bakinsa. "Zanyi maka kaji na mamansa..Amma se kayimin promise zaka denasa damuwar komi a ranka Dan Allah ka dinga sanyayawa a kan komi hkri fa maganin zaman duniya ne ..." ta karashe cikin muryar rarrashi da kwantar da hankali. "Thank you,,, proud of you ..."  "Nima ina alfahari dakai na mamanshi...Ka kwanta kayi bacci kaga time ya tafi dare yayi sosai ko baka koma kanon bane?" "No na koma..." "Okay Allah ya bada sa'ah ya tsareminkai gabas da yamma kudu da Arewa..." "Amin ya Allah mommyna..."  "Seda safe ka kwanta zuwa 3 or 2 katashi kayi sallar ka gayawa ubangiji damuwarka nima zan tayaka Kai kukanka , Allah shike mgnin damuwowinmu..." Aeezad ya kara sauke ajiyar zuciya yace "Insha Allahu nagode mommyna sweet dreams.." ya karashe badan ransa naso ba, haka kawai ya tsinci kansa da rashin San ta ajiye wayar. "Nagode babyna bye..." Ba tare data jira cewarsa ba ta katse wayar,. Bayan ta katse wayar ya kasa cire  wayar daga kunnensa  seda wayar tayi 5mnt a kunnensa yana mejin muryarta na masa gizo, ya cire wayar daga  kunnensa ya kure  Screen din wayar da Ido, ya shafa creen din wayar   ta kawo haske, picture dinta ne kan lock screen dinsa, tana zaune a farfajiyar hutawar gidansu, sanye take  da doguwar  rigar atamfa tasha daurin ture kaga tsiya yayin datai murmushi har wushiryarta ta bayyana, ba karamin kyau tayi ba, sumar goshinta ta kwanta luf-luf. Wani irin murmushi ne ya subuce masa yayin dayake kallon picture din nata  kamar Yana gabanta haka yakeji a zuciya da kwanjinsa.     "Kinada kyau na matsifa mommy!" Ya fadi yana me kara kureta da idanuwa, be taba sanin tanada kyaun daya wuce lissafinsa ba se yau. Bude wayarsa yayi yashiga gallery dinsa ya fara duba picture dinta da yaketa mata ba tare data sani ba, kaf wayoyinsa itace take cika masa gallery kuma duk photos din da yake mata ba tare da saninta yakeyi ba,  itace a kaf lock screen and home screen na kaf wayoyinsa,  sunyi fada da na'eema yafi a kirga a kan hakan tayi tayi ya cire yaki cirewa,  har hajiya mommy seda na'eema ta gayama,  hajiya mommy ta kira Aeezad Ta tambayesa meyasa zesa kaskantacciya a screen dinsa..." Aeezad yayi mata banza, Nan ta rufesa da bala'i da matsifa tace dole seya cire kaf pictures din nabeelah a wayoyinsa, cikin Mulki Aeezad yace " am sorry hajiya mommy Wallahi bazan cire ba, ai kowa abinda yakeso shi yakeyi... Kuma in zaku lura ai a matsayin uwa mommy take a gurina..." Sam hajiya mommy bazata iya jaa da Aeezad ba Dan haka ta kyalesa kawai  ita  kanta Tsoronsa takeji wasu lokutan sometimes data gansa se taji zuciyarta na yawaita faduwa kwarjini yake mata, dole sede ta bawa na'eema hakuri a kan hakan. Dadin karawar abinda ya kara dasa musu kiyayyar Nabeelah a ransu kenan saboda ganin yadda Aeezad ya bata muhimmancin fin komi na rayuwarsa.  Seda ya Kai 2:am Yana duba picture dinta haka kawai kallonta kesa masa nishadi,. Mikewa yayi ya nufa toilet ya dauro alwala ya fito ya fara jero sallolin dare Yana me Adduah Allah ya yaye masa abinda ke damunsa , danyafi tunanin boyeyyen ciwo yakeyi Wanda shi kansa besan Kona menene ba. Har seda yayi sallarh asubahi kana ya kwanta bacci ya barawo ya figesa, bashi ya tashi ba se 9:am, ya shirya ya tafi office 11:am. A office dinma yau kmr jiya se tunani tunani  kawai yakeyi , ya kirata a waya yaci saah ta dauka bugu daya,, wuni sukayi suna waya, har ya bar office din, a voice dinsa nabeelah ta fara fuskantar kamar ya soma chanzawa, nutsuwar dole ta fara shigarsa. 



*Katsina state*

Zaune suke a falon hajiya mommy  kusan su biyar, hajiya mommy se kawayenta manyan mata su uku manyan mata ne kamar Hajiya mommy,  Dayar ce karama wato na'eema . Duk kaninsu sunada kiba sosai, ba kamar ma ita karamar cikinsu, dukda a zaune take hakan be hanani gano itadin gajera bace, sede fara ce sol, bata da kyau kwata-kwata ga kananun Ido,  gashi duk tayi kiba tako ina, irinsu ne akewa lakani da badan fari ba se bola.  Zaune suke sun Sa table a tsakiya Wanda ke cike da kayayyakin motsa baki se sanyin AC da AC kawai keta ratsasu tako ina masu Aiki nata hidima dasu, sauran ukun duk Aminan hajiya mommy ne na bugawa a jarida, kallo daya zaka musu kasan sunci sun tada Kai, tinda hajiya mommy ta Auri Alhaji sunusi Ta dena kawance da talakawa sede  Yan gayu masu kudi kawai. Hajiya mommy dake zaune kan kujerar 1ctr tana facing na'eema dake zaune da wayarta kirar iPhone 13promax a hannu tana  kallon  TikTok. "Ke tinda Allah yadawo dake lafiya ya kamata ki koma dakin mijinki Ko zuwa gobe ne..." na'eema dake kallon wayarta ta dawo da dubanta kan Hajiya mommy dake maganar ta tabe baki cikin mamaki tace "Ai benan mommy Na tambayi me gadi ta waya ya gayamin ya koma kano ai.. kuma ma ko Yana Nan gaskiya bazan koma yanzu ba. " Hajiya mommy ta amshe da "Dole ki koma saboda kinsan de mijinki ba hankali ne dashi ba, na fuskanci ya fara kosawa gaskiya, danma Allah ya rufamin Asiri uban a tafin hannuna yake .."  Cewar hajiya mommy.  Kaf kawayen hajiya mommy suka kwashe da dariya Hadi da hada baki gun cewar "Da kyau ta gurina ai bakya wasa..." hajiya mommy tayi Wani farr da Ido tace "ina zan tsaya wasa,,, ai kaf gidannan d'anne ya zamar min. Kadangaran bakin tulu....ita kuma wannan wawiyar tasha nono ta zubar Sam ta kasa maidasa kmr masa a tandaa." Hajiya mommy ta karashe mgnrta tana kallon na'eema.  Hajiya naja'atu babbar Aminiyar hajiya rafi'ah ta amshe da "ta yaya zata maidasa kamar masa kullum kina kan aikata kasashen waje sarin kaya?"  Na'eema ta  amshe da "Gaya mata  dai mama.. " cikin tsiwa tayi maganar daman bata da alamar kunya ko a Ido.. "A gayawa uwar ubanki me dattin talauci..." Hajiya mommy ta amshe da kundumoma na'eema manyan ashariya. Na'eema ta hade Rai tana kunkunai. "In ban aikaki kasashen wajen saro kayayyakin ba ubanki dake kabari zan aika ya saromin shigiya kawai!  Yar bura uba, Nan dattin talauci ne ya kashe ubanki! shegiya Dan uban ubanki tashi ki barmin falona kuma gobennan ki shirya ki koma gidanki ,in mijinki yadawo ya taddaki gidansa,karki jamin yazo ya gayawa ubansa, tin uban be tafuka Wani Abu yazo ya tafuka a kansa, tinda azabar sonshi yakeyi kamar hauka.." cike dajin haushi da bakin ciki na'eema ta tashi ta bar falon ta cika fam ta batse, a rayuwarta ta tsani yarfi kuma mommy ta matsifar iya disga mutum a cikin friends dinta, ita kuma na'eema ga rashin kunya,ba tattausa harshe ko a kan uwa ne, a rayuwarta tana kaunar tafiye tafiyennan da takeyi , ko Dan pictures datakeyi tana nunawa duniya ta faso gari, uwa uba kuma tana facaka da kudi, ga yawon bude Ido tanayi tana ganin Yan Gayu  da masu kudade.  Hajiya wasila tace "wannan Karan kin matsawa yarinyarnan a kan seta koma gidan mijinta, bayan ke takema Amfani,saboda Allah fa yarinyar nan na Kokari ..." hajiya mommy tace "Eh nasani hajiya Amma ni tsorona kada yaronnan ya gaji ya gayawa mahaifinsa kinga de ko be mgna wata rana se yayi magana, ni shine kawai problem dina... " "Karki taba damuwa tinda kin riga kinsan hannunki..."cewar  Hajiya najmu. Duk suka kyalkyake da dariya, hajiya nana ta nisa cikin nutsuwa domin duk tafisu nutsuwa da ilmi ita Dr ce, tace "Kawata gaskiya be kamata ace yarinyar Nan tayi wannan kibar ba Tari guda, alhalin ko haihuwar farko batayi ba,duba fa yadda tayi kiba duk gashi tafimu kiba, ke kanki uwarta tayi hudunki, mazan yanzu fa bawani So sukeyi mace tayi kiba ba, Nan da Nan seta narke inta cika kibarnan,.." Hajiya naja'atu ta amshe da "Ah Dr nana batta ta narka kibarta, yadda kowa ya kalleta zesan tana auran me kudi kuma babban soja Masu fada aji a Nigeria .."  hajiya wasila ta amshe da "Wallahi kuwa a batta ta barbaza kibarta ...yooo taci tayi hani'an, uba kudi d'a kudi kaf  dangi bana tsifa, a batta ta narka kibarta yadda zata kara bayyana a hajjajunta, Muma da kika ganmu Hana hajiya dande iya jikin kenan, Amma kiba  ai kwarjini ce...."  "Wannan de magana taku ce kune masu diya..."cewar hajiya rafi'ah, duk kaninsu duk suka murmusa ..  hajiya nana ta rausayar da Kai tace "gaskiya de ni a ganina ya kamata ta rage,, kinga ita yarinya ce mu kuma mun manyanta a garemu kiba take kwarjini,ita Kam na'eema ai kunga yanzu take tashe, gashi Mijin nata shima yaro ne,gudun kada yaga wata yayi sha'awah mazann na yanzu se A hnkli daga haka se su jajibo maganar Aur..."  "Aaahhhhhh kullll hajiya kulll da maganar Aurennan,, ke kinga alamar ni Rafi'ah ina raye za  ayima diyata kishiya? Yooo ni Nan na da nake tsofai-tsofai Dani ma a Kanta ba Amin kishiya ba se ita datake yarinya danya a kaina... Allah kyauta, ya kade zancen kishiya,, ni wallahi wallahi a kan ama diyata kishiya kwara ni Amin kishiyari!'' rafi'ah ta fadi tana huci Kai kace kishiyar akayo mata ynzu. kaf  kawayen nata seda suka juyo suka kalleta jin furucin datai na karshe. "Kinsan me kikace kuwa Aminiyata?'' cewar hajiya naja'atu baki sake. Hajiya rafi'ah dake girgizar kafafuwa cikin isa da takama da duniya tace "ina sane wallahi hajjaju. Sanin kankune a duniyar Nan kaf dinta na'eema kawai na mallaka a matsayin diyata, wlhi San da nake mata ko kaina ban masa wannan San, Sam banason abinda ze tabamin ita, kinga kuwa da ace an mata kishiya kwara ace ni akayima ita, nasan yadda zanyi da ita, itafa ga yarinta ga rashin wayau, uwa uba ba halinmu Daya da ita ba, ni ina iya kisan rayuka da yawa a kan mijina...Sam babu digon imani a zuciyata musammanma a kan kishiya,,kinga ita kuma na'eema akwai digon imani a zuciyarta bazata iya kashe kishiyarta ba,, ni Kam wlhi wlhi hajiya in akamin kishiya ko ban kasheta da makirci ba zan kasheta da hannayena, sede a wayi gari ta mutu, Kuna a rasa ta yaya ta mutu...wlhi duk abinda zan Aikatawa kishiyar da Akamin zan Aikata mafiynsa a kan kishiyar da Akama diyata,,''  kaf sukayi tsit suna nazarin kalaman  Hajiya rafi'ah, Hajiya naja'atu tayi tsit Sam batasan kawarta tayi nisa ta wuce tunaninta har haka ba.  tabbas kmr yadda tace Sam bata da digon imani.  "Allah ma ya kyauta..." Cewar  Hajiya naja'atu,  datai mgnr Hadi da sauke ajiyar zuciyar da ita kadai tasan kona Menene. Kaf suka amshe da Amin  hajiya nana ta zarce dacewa  "Ai duk me tsautsayin data shigo muku a matsayin kishiya tini sunanta R.I.P...." "ai kwara Matacciyar da aka ga gawarta ta fita gata..." cewar Rafi'ah datai maganar zuciya da murya babu alamar imani dai-dai da kwayar zarra. "hmmmmm Allah de ya nisanta me tsautsayi..." cewar hajiya wasila suka amshe da Amin. "Hajiya mu gama muyi sallar la'asar se muje ki kaimu sabon shago muga didimar Arziki Musa albarka..." Cewar naja'atu, daman  shago rafi'ah ta bude shine sukaxo gani dasa Albarka. Nan aka  chanza Hira zuwa hirar sabon shagon hajiya  Rafi'ahWadda liyafa keta kankama.  


A bangaren Na'eema tanashiga dakinta tayi dealing number din Aminiyarta daya tal khadija, a Egypt dataje sarin kaya suka hadu da khadija rafi'u , suka kulla kawance gashi yanzu har sunyi 3yrs tare,. bugu daya khadija ta dauka. "Hajjaju da kanta uwar gidan Alhaji Aeezad,, yaushe kika dawo kasar?'' cewar khadija daga cikin wayar. Na'eema ta tabe baki tace "Jiya nadawo khadyn buba..." "Meyafaru Naji kamar bakya mood ?'' cewar khadija data fahimci na'eema bata mood a yanayin yadda ta amsa ta, da ace tana mood da yadda ta mata kirarinnan kyalkyalewa da dariya zatayi. Kmr na'eema na jira taja Wani dogon tsaki me shaddah da kisrah,kana tace "wallahi mommy ce ta bani mugun haushi...wai yau ni mommy kecewa in tattara in koma gidan Aeezad daga dawowata ko  hutawa banyi ba, salon ya dawo ya maidani kamar dafaffen food me maggi..." Khadija ta kwashe da wata uwar dariya sbda karshen mgnr na'eema. "Yanzu meye abin dariya a Nan ?'' na'eema ta fadi a kule. Khadija ta tsagaita daga dariyarta tana fadin "am sorry kawai kece kk bani dariya da kikace wai ya maidaki kamar food...wlhi kawata rashin juriyarki tayi yawa, ke kawai matsalarki sex in namiji nasan sex in baki jure masa a hakan wlhi komi zaki masa bakya burgesa...." Na'eema ta amshe da "shi wannan ko gindin zan wanke in basa ya hada da gabansa su zama daya bazan burgesa ba wallahi,yadda kikasan mommy haka yake Sam ba ayi masa gwaninta., Kmr yadda de kikaga   mommy ga yarfin tsiya,.."  khady tace "Ohhh Wani na Nema Wani na gudu,, ni kinga wallahi Rabon da Alhajibuba yayi sex Dani yafi 2yrs shifa a rayuwarsa inde kudi na shigo masa ba ruwansa da maganar sex dinsa dani, kingade aurena dashi 4yrs tsaf zan iya kirga sau nawa ya kusanceni daga lokacin zuwa yanzu, kullum se yacemin beda lafiya shi yayi ayyuka ya gaji, gashi ko romances be iya ba, in Yana taba nonuwa ke kyace yaki akeyi ,kamar ze tsinkeminsu daga jikina, nifa da akan yayi wasa Dani kwara na hakura na fawwalawa ubangijina, na kallo sex video na hkra..tin abun na damuna har na hakura, ina Nan zan samarwa kaina solution danni ba dutse bace du-du-du shekaruna ashirin da uku, tinda mukayi Aure ko bari ban taba yiba,, to in takaice miki tinda yake kwanciya Dani a fari, be taba kaimin karo ba har in kawo sede inyi wasa da kaina in kawo Byn ya gama sex Dani...ganinan ba alamar ciki ,shi Alhaji inde da kudi to mgna ta kare a garesa, kudinsa sunfi masa iyalinsa daraja..."  na'eema ta ciza yatsa tace "inama ace shine Aeezad..." "inama ace ni Aeezad dinne mijina..." Khady ta fadi a ranta domin mgnr bata faduwa a fili, ta jima tana mafarkai da dama a kan Aeezad mijin kawarta, taso ace daman a talaka ya fito da kudi ko nawa ne seta dinga biyansa domin ya dinga cinta, Amma Kash seya fito ame kudi ta yadda bata isa ta tunkari gabansa  Kai tsare ba balle da wannan maganar. A zahiri Khadija tace "Hmmm ki bari kawai Na'eema Allah baya ba me wuka nama..." da wata manufa khady tayi mgnr Amma sam na'eema bata ankare ba, tace "Tabbas da nice ke yadda kike watayawannan ai danaji dadih dako tunanin Namiji bazan ba balle gabansa..." khady tayi humming kawai, ita ba bakuwar kudi bace, na'eema ce bakuwar kudi, iyayenta asalin masu kudi ne na fitar hankali kuma dattawa ne, mahaifinta shiya hadata da mijin da take aure, Alhaji buba shiya ganta yace yanaso Aminin mahaifinta ne, ya taba aure yanada yarinya Daya mahaifiyarta ta rasu tin yarinyar na 15yrs yarinyar sa'arh Khady ce yanzu haka tana kasar waje karatu, tinda khady ta Auri Alhaji buba bata samu abinda takeso ba a tattare dashi , ita Kuma gata jarababbiya tanada tsananin bukatuwa da d'ana miji.   Haka take zaman hakuri da Alhaji buba saboda bata da yadda zatayi ,ba halin taje gidansu mahaifinta baze barta ba , domin shi babban mutum ne ga dattako bawai irin mutanen  Nan bane da basu da girma sena rigunan jikinsu. "Yanzu yazanyi kawata? Wlhi Sam banasan komawa gidan Aeezad ynzu..." Cewar na'eema da abun ke damunta tinda Mommy tace ta koma gidan mijinta tashiga dimauta. "Toh in baki koma ba meye amfanin Auren? Kinga kawata wlhi mijinki nada hkri inba shiba a zamanin Nan ba wanda ze jure yawon da kikeyi zuwa kasa-kasa ba izinin mijinki...kowa yaji ai yasan ba izininsa kk tafiye tafiye, ina kirge fa tinda  akayi Aurenki 1month kkyi a dakin mijinki kika cigaba da  barin kasa-kasa sarowa mommy kaya, mijinki fa  babban mutum ne kowa yasan ba a San ranshi ba,ynzu kuma ki dawo kina kyashin komawa meye problem dinki ne kawata? Sex kou?..'' na'eema ta amshe da ''After that shegen sa Aikin tsiya,  kullum sena gyara masa room 2tyms, ga wankin toilet bayan uban gajiyar dayake taramin, dasafe inta masa aikace Aikace, ko maids dinafa baya fari su tinkaro part dinsa balle insasu gyara masa dakinsa..." Baki khady  ta saki  tace "gaskiya kawata kin cika San jiki, yanzu kawai wadannan sune problems dinki? Ke da maids kkeso su dinga gyara bed din da kuka kwanta?'' na'eema ta amshe da "Ehh mana kajiki ke kuma, ni  me Aikinsa ce dazanta masa whla,,shifa Sam beso yaga kin zauna, ga shegiyar tsaftar tsiya a haka komi kkyi baki iya masa ba, ke kanki a kazanta yake kallonki..."   "Tabdijan...yanzu inYa cire  boxes dinsa wake wanke masa'?" "Waze wanke masafa khady? Shike wanke  kayansa da kansa, ko nawa panties din ban wanke ba se nasa...tinda baze iya bawa maids Ko yasa a matching ai sede yasha whlrsa shi kadai,ke namiji fa kome kika masa  baya gani kwara ma karkiyi..."  khady tace "Hmmm Allah kyauta..." A zuciyarta tana hasaso inama ace itace ke Auren yaro karami me danyar kaciya tabbas dayasha lailaya, seta kara danyatasa tass, itafa dama za a dawo mata da baya da babu abinda zesa ta AUREN Alhaji buba NAMIJIN KUNAMA, bashi da dadih se azabar zafin harbi. "Gobe zanzo in kawo miki kayan gyara ki gyara jikinki kafin ki koma ko zaki samu sauki a bangaren sex din .." cewar khady.  Badan na'eema taso ba tace "Okay se goben nagode best friend..." Daga haka sukayi sallahma.  





Wannan book din na kudi ne, gamesan Namijn zuma da Namijin duniya se biya 1500, in kuma days kkeso zaki biya 1k 0542703718 Saadatu Abdullahi gT bank🐝🐝🐝🐝🐝🐝🐝🐝🐝🐝

No comments

Powered by Blogger.