Najma 5-6

 


👄👄👄👄👄👄

      *NAJMA*

💋💋💋💋💋💋

By maman noorul hudah


This page naku ne masoyan asali da Banda ku ba da Banda niyyar Fara novel yanzu,thanks for always loving me....anty haddy,anty Aisha dahiru,da dai sauransu I appreciate you guys 


🅿️5️⃣❤️6️⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim


            Tace"toh miye dan ance su sake kissa nace suyi ai bani na hadasu ba tun farko bare a had'a ni da shaidani kallon na zoyi in samu ladan gudun da nayi shine za a wani so a zageni


Ya rigada yasan halinta ba kunya ne da ita ba ya kalli delu yace"deluwa jeki gida in ba so kike a Miki duka ba "

Da Ido tayiwa deluwa alaman da karta tafi Kuma ya gani saiya girgiza Kai yayi tafiyarsa Yana Mata addu'ar Allah ya shirya 


Cikin d'aga murya tace"Amin ai addu'a kayi "tana ganin yayi Nissa ta dibi kasa ta cika a hanun ta ta dunkunle taje gaban deluwa da sadiya dake Harare haranre juna tace"in kun San kun  Isa  ba tsoro kuke ba ki d'auki wanan ta hagun ta matsifa ne ta damar ta balai


      Dukkaninsu suka d'aki hanunta 


      Ta buge kirjin deluwa da ta sadiya tace"in kun Isa ku Rama a jikin junanku  


   Deluwa ce ta Fara kaiwa sadiya Mari tuni dambe ya kacame tsakaninsu,uwani ta koma gefe ta natsu tana kallonsu dambe yayi dambe har zanin deluwa ya kwance ,itako sadiya rigarta ta yage nononta da ba  wasu girman ne dasu ba Suka bayyana 


    Ganin suna son su raba kansu Dan sun gaji yasa uwani sakin Waka tana cewa ku casu arna ku casu, ku casu ba me raba ku


    Cikin daga murya tace"  ke deluwa karki barta cire Mata hakora,kema sadiya karki barta sai kin fidda  rainin "


       Har Kan hanya suka hau Dan Jin maganar uwani suke Kamar na  uwarsu 


    Wata tsadadiyar motace ta danno Kai horn ake Kamar za a kurmatasu ganin sun saki juna uwani tace"karfa ku damu da masu motar nan kuyi kamar Baku San dasu ba ku cigaba da damben ku 


     Cakume  juna Sukayi suna son  cigaba dukda sun gaji 


      Bude driver side akayi kafarsa dake sanye da tsadeden halfshoe baka data karbi fatar jikinsa kasancewarsa fari tas,jikinsa sanye  da coffee shadda da hula me coffee baground sai milk zare da akayi aiki dashi sai kamshi yake 


    Fitowa yayi ya zuba musu Ido tare da ciren bakin glass din da ya karbi fuskarsa 


        Jinjina rainin wayau Yan kauye yake


    Dan satar kallonshi uwani tayi kafin tace"ko wanene ya nimi Hana wanan fadar Allah ya tsine Masa albarka,Kuma sai ya ci Mai garinsu ko wanene shi 


   Shafa Kai yayi ya zuba Mata Ido duk sai ya ganta a fige ma'ana dai kana kallonta ka gan cikkakiyar Yar kauye Mara kunya 


     Kwafa tayi dan har ga Allah haushinsa take ji dan cak su deluwa Suka tsaya da dambe tayi ta tsaki sai a yanzu Suka ji kunya kasancewarsu ba Kaya ita Kuma sadiya sai Kare kirjinta take 


Ganin inda tayi kicin kicin da fuska tana kunkuni 


  Sai ta bashi dariya ya karaso ya d'auki zanin delu ya Bata ta d'aura da alamu taji jiki Daman kiris take jira sai ta fashe da kuka 


        Baki sake cikin zigi uwani tace"delu Wai kuka zakiyiwa sadiyar nan ah lallah raini bazai fita tsakanin ku,wawiyya bazaki Kai Mata bugu ba ki nuna kema shegiyar Darin ce 


    Zuba Mata Ido yayi ganin irin kallon da yake Mata yasa ta Kau da Kai tace


Maman Nur

No comments

Powered by Blogger.