Min Qalb 46-50

 


MQ 46/47_*

Yau kwananta uku da dawowa batareda ta sanarda kowa dalilin dawowarta ba tadai ce musu hutu tasamu me Dan tsayi shiyasa tazo Dan haka Babu Wanda yasa ko kawo tunanin komai cikin ransa gameda zuwan ko tsakaninta da mijinta sai suka hau shaanin gabansu aka bude majalisar me zaman kanta gidan kawu tasu maman junior Dan har wasu abubuwan gyare gyare suka Fara Shirin Fara harhadawa Amatun na gyaran jiki Dana cikin jiki musamman ma iyami da dama batai gyaran yarta ba lokacin da akai auren Dan haka yanzu zata gyara abarta.


MAHMOUD ZABEERA kuwa tunda yaji daga bakin kawu tana gida taredasu sai hankalinsa yadan kwanta  Amma duk da hakan a matse yake daya dawo Nigeria din tun kafin kowa yasan halinda suke ciki Dan shi kunyama zaiji ace matarsa ta tafiyarta  Yana yawon neman komawarta ko Modibbo saiyace ba MAHMOUD ZABEERA din dasuka sani bane gashi kamar zuwan nasa Kai tsaye bazai samu ba sbd wani urgent work Kuma daya taso Masa Wanda dole saiyaje Dan haka zarah kawai zata taho Nigeria shi zai wuce inda zaije daga Nan daga can zai wuto Nigeria din.


Yau kwananta bakwai da zuwa zaune suke suna fira itada anty salamatu da iyami Dan yau Yan firar tasu duk basanan sunfita anguwa Dan haka yau gidan tsit ba hayaniya sai su kadai USI ma yadawo asibiti da wuri yau Yana dakinsa baccin gajiya yakeyi sbd a asibitin ya kwana yau.


Sallamar umme sukaji Muhammad na bayanta tafe cikin gudu hannunsa riqeda Ben10 soldier dinsa dayafi so cikin kayan wasansa Yana Kiran sunan anty salamatu yana shigowa yaga mummynsa a zaune da gudu yayi kanta Yana cewa''


Mumma mumma.


Rungumesa tayi tana cewa''


My Muhammad has become a superman ji wannan gudu fuiiiiii.


Dariya yayi Yana Jin dadin Superman data kirasa Yana sake hayewa jikinta yace"


Mumma where is my Daddy?

Inason ganinsa i miss him""yafada Yana leqa bayanta da kallon koina Yana son ganin baban nasa.


Murmushi tayi tana zaunar dashi gefenta tace"


Muhammad look"tafada tana nuna Masa su iyami tace"


Baka gaida grandma ba da antyty dinka"cewar anty salamatu.


Gurin iyami ya nufa Yana miqa Mata biscuits din daya Ciro aljihunsa wanda yakawo Mata yace"


Kaka iyami ga biscuits da umme ta siyomin ki ajewa kawu.


Dariya dmtayi tana jawosa jikinta suna sake gaisawa da umme data zauna tana amsa gaisuwar Amatu data salamatu tana cewa''


Amatu wato muda muka matsu dason ganinki gamu munzo Muhammad ya isheni Wai babansa yakeson akaisa gurinsa shine nace Bari muzo dai idan yaganki qila ya rage fitinar neman uban.

Murmushi kawai tayi batareda tace komaiba saita kamo wani zancen suka fada wani zancen Bayan anty salamatu takawowa ummen ruwa da brabiskon dasukai Wanda ummen na sonsa sosai musamman yanda iyami keyinsa yayi wani irin laushi.


Sai dare umme ta tafi tabar Muhammad dayace gurin mamansa zai zauna.

Washe gari kwananta Tara kenan da zuwa suka shirya itada anty salamatu suka fita da motar USI daya bar musu Wanda duk yanda taso taja motar kasawa tayi sbd yanda ta koya tuqi a Greece daban da tuqin nan din Dan haka Dole tabar anty salamatu da USI ya koyawa tuqi sbd fita da iyami ko lalurar gida idan antashi Dan yakan bar musu mota ya tafi asibiti musamman idan acan zai kwana.


Family house dinsu maman basiru sukaje barkar haihuwar da qanwar maman basirun tayi shiyasama kwana biyu basa zaman fira sun Dan jima acan kafin suka baro suka nufi kasuwa siyayyar takalman iyami data Basu saqon anaso sun qare daga Nan gurin bada dinki suka Amatu tabada dinkuna sai yamma sosai suka dawo gida Dan haka suna komawa sallah kawai sukai sukaci abinci Amatu ta kwanta Dan matuqar gajiye take.


Washe gari tana buqatan gyara kanta daya Fara damunta suka shirya zuwa blue fox itada anty salamatu Dan haka guraren 12 suke fice bayan sunfara biyawa sun ajiye Muhammad a zabeera taje ta gaidasu Andi dasukai mamakin Jin zato hutu Ashe Amma sanin ba ayi maganar tarewarta ba yasa suka barta takomawarta gidansu inda ta sauka saidai Kam tunda har tazo Dole ayi maganar tarewarta ta tare sbd daga yanzu idan tazo ta sauka a gidan mijinta dama tuntuni anyi gyaran sashen marigayi Dr khalil  an rushe komai ansauya tsarin gurin gababaki daya Kuma sai akai qatuwar katanga aka zagayayesu cikin qaramin gate me kyau tareda sashen zarah sai harabarsu ta zama daya me girman sosai.


Daga zabeera blue fox din suka wuce suna Isa Allah ya hadata da manager kuwa ai Nan ya tsaya kallonta cikin girmamawa da sauri ya qaraso Yana cewa''


Ran Amaryar zabeera ya dade yau an tuna baya kenan.


Dariya taso Yi ta gimtse tana kallon gurin da aka sauyawa tsari me kyau fiyeda da ga girma da fadada gurin da akayi ya sauya matuqar Dan yanzu ma tun a gate Saida tickets ake shigowa ga uban securities tana jinjina kai tace"


Manager komai na blue Fox yasamu sauyi Banda Kai kana Nan yanda kake  har halayen.


Dariya yayi Yana cewa''


Allah ya taimaki Amatun zabeera ai mu Babu wani sauyi daya fiyemin blue fox musamman yanzu datake zaman mijinki Dan kuwa ya jima ya siyeta gabaki dayanta Kuma nasan idan Allah ya yadda sbd ke ne tunda kowa yasan har yanzu kina qaunar blue fox dinnan shine yayi Mana dukkanin wannan gyare gyaren Takoma kamar turai yanzu hadda sashen geaming da sports munada aciki haka Kuma komai namu anqara fadadashi daga restaurant din har spa din dasauransu.


Girgiza Kai tayi tana kallonsa tace"


Ga antyna dai ku gaisa sbd Naga ko ganinta bakayiba sbd dadin labari.

Da sauri ya kalli anty salamatu dake sanye cikin riga da skirt na red embellished atampa da gyalenta red shima sai tsawonta me tsari ya fito cikin dinkin riga da skirt din ya washe dukkanin haqoransa da fara'a yace"


Sannu da zuwa blue fox Ina Miki barka da zuwa sirikar me gidanmu.


You'll never change manager" Amatu tafada tana yin gaba Yana biye dasu Yana musu bayanin yanda tsare tsaren gurin yake ayanzu da kansa yaje jiki na mazari ya karbo musu tickets na komai da zasuyi yakawo musu a kebantaccen gurin da sai oga zabeera din yazo da kansa shikadai ke zama acan suka Fara cin snacks kafin suka nufi spa Dan komaima yimata zaayi.

Da gyaran Kai aka Fara musu kafin da aka gama aka koma gyaran qafafuwa daganan aka koma gyaran jiki.


Basu baro blue fox ba sai magrib suna isowa gida itace tafara fitowa tana juyowa sai Jin Muhammad tayi a jikinta ya Fado Yana mata "oyoyo mummah"


Da mamaki take kallonsa suka nufo cikin gida tana cewa''


Waye ya dawo da Kai?bakace Kuma gurin umme kakeso ba sbd ka ringa wahalarda mutane zaka ringa saka masu kaika da dawo dakai yawo.


Daddy yazo Dani...


Kallonsa tayi da sauri tana kallon bakinsa daya furta dadyn tace"


Dadynka Kuma?


Eh dady ne yadawo yau yazo Dani yace muzo mutafi da mummah.


Kallon inda yake kalla tayi numfashinta nason sauya fita ta hanyar qara sauri tana dannewa ta kalli gurin tagansa zaune Kan kujerun harabar gidan tareda kawu 

Kawu sai zuba yake Masa Amma shi idanuwansa na kanta ya zuba Mata su cikin yanayi da kasalar da ganinta ya sakar Masa idanuwansa na bayyanarwa sbd wani lumshewa dasukeson Yi Amma Basu lumshe din ba.


Bugawa ZUCIYARTA ke Naman Yi sbd wani irin kyau da sheqi tareda qwarjinin da Allah ya horewa wannan bawa nasa MAHMOUD DAHEER ZABEERA ta dauke idonta ahankali tareda juyawa ta shige ciki batareda tabari kawu ya gansu ba Dan yanzu zai Fara kawo Mata zantukan tazo ga mijinta.


Suna shiga daki tashige ta tube saidatai wanka kafin tayi sallar magrib da yanzu aka gama ta sanya doguwar riga mara nauyi me kamar boubou ta fito tana tambayar abinci ta nufi kicin ta dauko zobon da iyami keyi tana sawa a fridge sbd baqi dakuma kawu dakeson ruwa me kala ta fito tana Shan zobon saiga USI yashigo yace taje palon kawu yana namanta.


Can ya wuce Kai tsaye sbd ta daina Jin hayaniyar Muhammad tasan sun tafi ne tunda dare yafara Yi takumasan babansa bai Bari ana fitar dare dashi.

Tana shiga da Muhammad din tafara cin karo kwance yayi bacci jikin kawu  tana ganin hakan saita daure fuskarta taqi kallon dayan gefen Dan taji ajikinta MD ne agurin.


Kallon kawu tayi muryarta na daidaituwa cikin nutsuwa tace"


Kawu likita yace kana kirana.


Eh mijinki ne gashinan zaune yazo tun dazu bakwanan yanata zaman jira.

Miqewa kawun yayi daukeda Muhammad ya fice yakaiwa iyami dakinta ya fita zuwa gurin abokanan hirarsu ta dare a qofar masallaci.


Kawun na fita ta nufi qofar fita itama batareda ta kalli inda yake ba ko qofar Bata qarasa isaba taji yariqo hannunta tareda dawo da ita baya har bayanta na gugar qirjinsa ya bude baki da muryarsa me taushi yace"


Why?

Meyasa Zaki taho a irin yanayin da kike ciki Kuma ki dauki fushi Bayan nine yakamata na dauki fushin tunda kin baro batareda sanina ba.


Juyowa tayi ta kallesa ahankali kafin ta zame hannuwansa cikin nata daya riqe ta wuce tabarshi tsaye Yana kallonta.


Qofar data fice yabi da kallo Yana Dan rintse idonsa ya sauke numfashi Yana komawa zaune dama yasan Amatu bazata sauko acikin sauqi ba.

Hakanan ya fito ya wuce batareda kowama yasaniba Yana Isa gida ko abincin dare daqyar yaci sbd kada Zarah daya lura kamar itama tafara iya Magana akan Abu tayi Magana bazai iya daukar wani stress Bayan Wanda yake daukaba yanzu aikin dayayi a Sudan duk tsawon kwanakin baiwani bada hankali yayi Abinda yakaisa ba sbd har lokacin komai Kiran dazaiyiwa Amatu baya samunta,

Wanka yayi ya kwanta kawai dama akwai gajiya a taredashi sbd yau din ya dawo.


Washe gari ma taso fita Amma iyami ta hanata sbd cewar mijinta na gari ba Maganar yawo yanzu Dan haka Dole ta zauna gida tana kallo su Anty salamatu hadda iyamin suka tafi gurin sunan qanwar maman basiru suka barta.


Tana zaune Palo tana kallo sama sama bayan la'asar har bacci ya Dan Fara daukarta taji qamshin imperial majesty na shiga hancinta kobata juyoba tasan shine zai shigo palon ta tashi zata shige daki tun bai qarasa shigowaba tana kaiwa tsakiyar palon Yana shigowa da sallamar cikin sauti me taushi ya tsaya gabanta Yana kallon fuskarta dake daure tam sai yaji jikinsa yayi sanyi ya rasa kalmar furtawa ya riqo hannunta cikin nasa idanuwansa na kanta a gajiye da wannan fitinar yace"


Wannan shirun naki is killing me 

Kiyi mgn Koda zakiyi fada ne I'm ready Zan dauka infact I won't say a word indai har Zaki sauko.


Bata kallesaba ta kwace hannunta a hankali kafin tace"


Zan kwanta Kuma bakowa a gidan nikadai ce.


Tunda yadawo gida zarah ta rasa gane kansa abun duniya ya isheta ga cikinta nada damuwa an hanata sakawa Rai damuwa Amma wlh bazata iya rashin damuwarba sbd Abinda take gani shi ake Kira da asalin damuwar,

Yau satinsa guda cif da dawowa Amma yarasa gane Kan Amatun tun abin na iya tsakaninsu har gidansu Amatun dai kowa yasan Abinda yake faruwa kawu dayaji hadda 6arin ciki tayi sai baiji dadin yanda MAHMOUD din yabari tadawo ba ita kadai cikin yanayi irin wannan Amma zamansa uba saiya ringa bin Amatun da rarrashi har gwara iyami na Dan Mata zafi wani lokacin Amma duk da hakan shidai MAHMOUD baiga sauqi ba saima yakoma ya hurawa su Andi wutar batun tarewar Amatun Wanda yabar Andi cikin mamakinsa dakuma tunanin shima wato lokacin gyaransa yayi a hannun Amatu sai suka aikawa kawu yace zai Basu ranar tarewa idan yayi mgn da Amatu.

Jin hakan sai tension dinsa yafara bayyana ga aikinsa Dan duk wasu ayyukansa da meetings dinsa na watan kusan duka yayi postponing dinsu sbd kwanakin Yana samun matasalar saurare a bangaren aikin shiyasa ya tsayar.


Batareda tsayawa neman bayanin kowaba yasa aka Zo aka zubawa sashen sabbin royal furnitures masu kyau da tsari saidai har lokacin Amatu takasa tsayawa dashi ko Magana suyi tun Yana daukar Muhammad Yana zuwa dashi harya Bari kada ya kwashi sanyi da yawa 


Zaune yake Yana duba wayarsa hankalinsa gabaki daya baya Kan wayar Yana wani gurin..

Fitowa tayi daga dakinta cikin Dan adonta na riga da skirt na atampar data Dan fitar da qaramin cikinta daya Fara Dan turowa ta kallesa tana nazarinsa tsawon lokaci kafin ta sauke numfashi ta nufi kicin ta bude fridge ta dauko Masa lemondrink da cup ta Dora Kan tray ta dawo takawo gabansa ta ajiye tareda zama gefensa ahankali tana budewa ta zuba Masa ta miqa Masa ahankali tareda Kiran sunansa cikin sanyin murya.


Waiwayo yayi ya kalleta tareda kallon kwalliyar jikinta datai Masa ya karbi drink din Yana qaqalo sahirtaccen murmushi ahankali yace"


Thank you and you look great.


Kurbawa yayi ya ajiye Yana kashe wayarsa gabaki daya ya ajiye ya qara daukar drink din yanasha harya shanye ya ajiye cup din yasake Dan juyowa ya kalleta Yakuma cewa''


Thank you"Yana maida kallonsa kan TV Yana kallon news.


Jinjina Masa Kai tayi tareda fuskantarsa gabaki tana jinjina qarfin Rai irin na MAHMOUD din dayake dannewa da boyewar abindake ransa kamar yanda ya Saba boye al'amura saidai yanxu wannan damuwar ta dabance Dan itadake taredashi tana iya hango damuwa ataredashi.


Numfashi takuma saukewa akaro na biyu kafin ta Kai hannunta ta Dora Kan nasa ya juyo ya kalleta da idanuwansa dasukai laushi sbd rashin isashen bacci ta bude baki ahankali tace"


I'm really sorry MD sbd tun farko daban Bari ta tahoba da duk haka bai faruba,

Laifina ne na yarda Kuma Inshallah idan munhadu Zan fahimtar da ita hakan but for now idan akwai ta inda Zan taimakawa alamarin let me know please..


Shiru yayi idanuwansa a rufe na mintuna kafin ya budesu ahankali ya juyo ya kalleta na mintuna Yana NAZARIN yanayinta ya bude baki yace"


She respects you fiyeda komai sbd tanajin nauyinki fiyeda komai because of the old relationship that you two shared Wanda deep down haryanxu tana Miki kallon yayarta.


Kallonsa take da dukkanin girman idanuwanta bugun zuciyarta na sauyawa sbd Fara tammahar inda zancensa keson dosa muryarta na rawa tace"


To ta Yaya hakan zai.....


Ki tayani fahimtar da ita Abinda nakeson tagane please.


Saura qiris zuciyarta ta buga daga cikin qirjinta ta da Abinda ya fada din,

Wani dishi dishi take neman Fara gani sbd bugawar da zuciyarta keyi da sauri,

Wani irin zafi yafara taso Mata tun daga cikin qasan zuciyarta Yana mamaye zuciyar Tata take taji tsanarsa nason darsuwa a zuciyarta akaro na farko a rayuwarta Amma ta yakice hakan tareda kallonsa cikin Ido ta bude baki Kai tsaye tace"


For the first time yau MAHMOUD ZABEERA ka farkar Dani daga wani babban kuskuren danake ciki,

Miqewa tsaye tayi ta kallesa cikin muryar dake bayyanarda jarumtarta tace"


Zuciya ce a kirqina ba dutse ba dan haka inaga ko dan Abinda yake cikina na cancanci wata karramawar Amma duk da hakan tunda ka buqata Zanyi mgn da ita Amma bisaga sharadin idan Bata dawoba Nima nagama zaman gadin gangar jikinka sbd inason ayau kasan sonka zuciyata ya Kama bawai zuciyar ya cinye ba.


Zaiyi mgn tabar gurin batareda ta tsaya sauraronsa ba ta nufi dakinta ta shige tareda rufowa ta Isa bakin gado ta zauna tana son fashewa da kuka Amma Abinda takeji yafi qarfin kukan  sai kawai ta miqe ta zari doguwar hijab da keys din motarta ta fice tanajin idan Bata bar gidanba komai zai iya faruwa.


Tana Isa gidansu Kai tsaye dakin ummanta ta wuce ta zube Kan gado sai alokacin wani gigitaccen kuka ya 6arke Mata me ciwo.


Umman data fito toilet taganta tana kukan sai kawai ta barta tayi me isarta kafin tabar gefenta Takoma Kan kujerar dakin ta zauna tana kallonta tace"


Wannan kukan dakikeyi ki Dena zarah sbd Abinda yake taredake Wanda baya buqatan irin wannan tashin hankalin tunda kinfi kowa sanin yanda cikin baida qwari.


Tashi zaune tayi tana share hawayenta ta zare hijabin jikinta ta dago ta kalli umman dake Mata kallon jiran jin dalilin wannan kukan.


Bude baki tayi ta korowa umman bayanin komai zata Dora da wata maganar umman ta daga Mata hannu cikin takaicin ZARAn da cewa''


Zarah kinada matsala babba idan har Baki dawo hayyacinki ba,

Shi so da zaman aure duk ba hauka bane,

Ta Yaya Zaki maida kanki doluwar qarshe akan gudun zuciyar namiji,

Shin meye amfanin rayuwar aurenda babu fahimtar tunani ko Babu so ana zaman aure me Dadi idan kowa yasan mutunci da darajar kansa data abokin zamansa,

Matsalarki zarah itace kin kasa bawa kanki darajarda shima abokin zaman naki zai baki,

MAHMOUD ya zaune dake cikin girmamawa da mutuntawa tsawon shekaru masu tsayi batareda ya taba complain ko nuna muzantawa garekiba duk da kece Kika kasa kawo sauyi da shaquwa acikin auren naku sbd kece mace kinada hanyoyi da damarmaki da Zaki sauya MAHMOUD tun  kafin wata tashigo rayuwarku Amma Kika kasa yanzu abin yazo a biyu na farko koki yarda ko karki yarda MAHMOUD son mararsa AMATULLAH yake so me tsanani musamman tunda yanzu gatanan tana bude Masa hanyoyin sanin zamantakewar aure sannan akwai fadanda ko sunyi abunsu na tsakanin ma'aurata ba huruminkineba Shiga gashinan yanzu kin qare zuwa bikon kishiya Wanda idan dai baki koyi sanin darajar kankiba data Kama kanki akan Abinda Babu ruwanki har ruwan wanka kina Kan hanyar daukarwa kishiya Dan haka kada kiga laifin mijinki laifinkine

Da Zaki farka ki nuna Masa kinsan darajar kanki data aurenki da zamanki matarsa tsaf zakiga yazo yazauna daku anbawa kowacce haqqinta anzauna lafiya.

Bance kinyi baya ba sbd wannan halindakike ciki Allah na gani Kuma Yana sane wlh zakiga irin tanadin sakamon da Kika samu agaba Amma gskia zarah ki farka Babu Wanda zai qwaceki a cikin wannan yanayin sai kanki da kanki Zaki qwaci kanki ki tashi kije bikon naki dakika daure kanki da zakiyi Danni bana cikin wannan mutuwar zuciyar.


Mutuwa jikinta yayi ta miqe ta wanko fuskarta tadawo ta dauki keys ta fice batace qala ba ta shiga mota ta nufi gidansu Amatu.

Tana Isa tayi parking ta fito tana daidaita kanta da nutsuwarta ta nufi ciki ta Isa qofar Palo tashiga da sallama 

Su iyami dake zaune palon duk suka juyo suna kallonta

Saiga Amatu ta fito daga kicin daukeda indomie data dafo tana ganinta itama ta tsaya cak tana kallonta.


Anty salamatu ce tayi saurin miqewa tana cewa''


Zarah kece da yamman Nan sannu da zuwa.

Iyami ma cewa take"

Qaraso ki zauna zarah kinji sannu da zuwa fitar yamma.


Murmushin qarfin hali tasaki tana qarasowa ta zauna tana kallon Amatu dake kallonta tana Mata sannu da zuwa itama.


Murmushi tasaki tana cewa''


Amatu idonki kenan.


Indomin ta ajiye tana murmushi tace"


Anty zarah kedai karkice komai nakira wayarki Allah harso biyu bana samu.


Zobo anty salamatu takawo Mata suna qara gaisawa zarah tace"


Iyami wannan 'yar Taki zaneta zamu farayi sbd tashin jinta yanzu kiduba kiga yanda takasa aje fushin datakeyi damu shiyasa nazo da kaina nabata hkr tunda taqi sauraron mijinta to gani nazo Dan yau bazan fita gidan nanba saida ita.


Kallonta Amatu tayi cikeda mamaki tace"


Anty zarah.


Tsit antyn tayi sbd tsawon lokaci sai yau takirata anty zarah complete.


Juyowa tayi ta kalleta zuciyarta na rauni da damuwar datake ciki Amma tana daurewa kada ta gasa ta bude baki zatayi mgn sukaji sallamarsa dukkaninsu suka juya.


Iyami na ganinsa gaisawa kawai sukayi ta miqe ta bar gurin hakama anty salamatu.

Kallonsa zarah tayi harya qaraso gabanta baice komaiba ya kamata hannunta ya miqar da ita yace"


Let's go.


Kallonsa tayi da idanuwanta dake son cikowa ya sakar Mata murmushin dake nuna banhaqurinsa Yana girgiza Mata Kai yace"


Ita tariga ta taho gidansu ke dakike taredani bazan Bari ki barni ba,

Bazaki bawa kowa hkr ba sbd selfishness ba.


Wani irin sanyin Dadine yake kwaranya cikin zuciyarta haryana bayyanuwa Kan fuskarta tasaki wani yalwataccen murmushi tana girgiza Kai tace tunda nazo zankoma da ita idan har da akwai mutunci da ganin girma a tsakaninmu.


Gyaran muryar kawu sukaji daga bayansu suka juya Banda Amatu da abun duniya ke neman shawa Kai.

Palonsa suka nufa aka zazzauna Nan ya rufe Ido duk su dukan yayi musu fada tareda sanarwa da kowa laifinsa Kuma ya buga rantsuwar yau Amatun a gidanta zata kwana da daddare iyami da salamatu zasu kawota.


Godiyar da MAHMOUD din yaringa yiwa kawun yasa su iyami Jin wani iri sbd zarah din.

Bayan tafiyarsu Amatu Tasha kuka harta gaji iyami ta kalleta tana cewa''


Amatu kiji tsoron Allah kobaki zauna da mijinki lfy Dan Allah ba Kya zauna dashi lafiya kodan baiwar Allan Nan tasamu nutsuwa gidan aurenta,

Karki manta shifa aure hkr ne cikinsa kusan gabaki daya,

Bakiyi rayuwar zaman aureba da Khalil ya rasu sai yanxune zakiyi rayuwa Kuma wlh duk Kika dagawa MAHMOUD hankali har hakan yasa aka Shiga haqqin zarah Allah bazai barki ba,

Matar Nan koba komai wlh duk Wanda yasameta abokiyar zama ya huta a rayuwa sbd matardake danne kishin Mijinta Dan kawai a zauna lfy ai itace abarso da tattali Banda shi so yake wani dabam,

Dan haka Amatu Dan Allah ki dauke Ido ki koyi hakuri Kuma ki zauna da Matarnan tsakani da Allah kamar yanda kuke ada ni wlh tausayi take bani Kuma Ina tsananin ganin girmanta.

Itadai Amatun Banda hawaye Babu Abinda takeyi sbd hukuncin da kawu ya yanke akanta ta wani bangaren Kuma yanzunema zasu Fara tsara zaman auren dakuma kishin tunda yanxune za'a hadesu araba musu kwanan aure da komaima.


Daki Takoma anty salamatu na hada Mata sauran kayan Sha da iyamin ke hada Mata kullum tun ranarda aka Fara maganar tarewarta.


Har dare Basu Gama Shiri ba sai Bayan ishai tayi wanka ta shirya cikin wata farar lafaya da wani lace me taushi aka bita da turaruka masu sanyin qamshi suka fito bayan kawu yaqara tashi nasihar.

Andi ne dakansa ya aiko drivern dayazo daukarsu suka nufo zabeera inda ake jiran isowarsu.

##Mamuh#*_MQ 48_*


*_THE FLAVORLAND BY ACEEY_*

Ina ma’abotan son ingataccen yaji, Different Flavors that complements each other, Yajin da ke daidaituwa da duk sinadaran abinci na al’adance da zamanance, Muna muka albishir da sanardaku cewa nesa tazo kusa domin @the_flavorland by Aceey yakawomuku duk nau’ukan yajinda kuke iya buqata Saboda yajin ya hada da:

Daddawa Yaji, Waton yajin daudawa

Garlic Yaji, waton yajin tafarnuwa da kuma

Beef Yaji, wato yajin Nama kuma me hade da nama

Domin ayukkanku da yau da kullum wanda ya hada da:

Dahuwar abinci/nau’uka na miyoyi DA

Gashe gashe da soye soye kamar su

Kaza

Kifi

Nama

Doya

Dankalin turawa/hausa

Awara

Danwake

Gurasa

Kwado da dai sauransu....

Ba Mu tsaya anan ba——

The_flavorland ya hada da kayan tande tande da lashe lashe da suka hada da

Hoppers wato Fara

Milky candies wato alawar madara da kuma

Milky balls wato Gullisuwa da de sauran abunda rai ke buqata...

Zaku iya tuntubar mu a kafofin sada zumunta kamar haka

IG: @the_flavorland

Whatsapp:08104673847

Sending Some treats your way.... l


Let us satisfy your cravings:

We Deliver anywhere and everywhere.

*******



*********

Suna Isa zabeera Kai tsaye motar data daukota sashen Andi aka nufa dasu sbd har Modibbo da umme na can dashi kansa MAHMOUD din Wanda ranar yakoma MD ZABEERA dinsa sak miskilanci da izzarsa sun motsa ko wayoyinsa duk akashe ma suke Abu daya kawai yakeji atare dashi shine nutsuwar zuciya data ruhi harma data gangar jikinsa Wanda yagama tabbarwa da kansa cewa tabbas Amatu tarigada tazama wani babban bangare an zuciya,jiki da rayuwarsa tunda haryakejin wannan nutsuwar me sanyin Dadi tattare da dawowarta garesa.


Suna shigowa akansa idonta yafara sauka ta dauke Kai Yana sunkuyarwa ta zauna daga qasa gefen umme dake kallonta fuskarta na bayyanarda farin ciki da murmushi.


Da MAHMOUD din Andi yafara nasiha akan haqqoqan Mata dake Kan mijinta dakuma ire iren halayen .ata da Dole namiji saiyayi hkr dasu sbd rauninta dakuma rashin zurfin tunani  da Rashi haquri irin na wasu matan kafin yadawo Kan Amatu da nasihar zama da miji da girman haqqoqinsa akanta da girmansa dayafi na kowa akanta yanzu yaqara da nasihar adalci tsakanin mataye biyu dakuma haqurin zama da abokin zama Dana rayuwa kafin daganan Andi yayiwa Amatun kyautar aure ta sabuwar mota fil sak irinta zarah datake hawa banbancin kalane kawai dayace Tata Ash ce ta zarah farace.


Godiya sosai sukayi suka fito umme na riqeda hannun ta saka Mata wani acikin hannun dayake rufe cikin qaramar kwalbar roba suna shiga mota tace"


Shanye kiban roba.


Kallon ummen tayi tana sake kallon abun ta Dan 6ata fuska zatai mgn tace"


Bansan Jin komai hanzarta kishanye kiban.


Marairaice fuska tayi tana kallon abun.

Anty salamatu dake sit din gaba ta juyo ta kwace kwalbar ta bude tareda Dora Mata abaki tana cewa''


Dallah shanye da abin dadine da yanzu kinfara maganar qari to wannan dadinsa saikin fi kowa.....


Rufe Mata baki Amatun tayi da sauri tana zaro Ido kunyar umme kamar ta nitse ta saci kallonta tace"


Haba anty salamatu nidai karki fara zancenki Dan Allah.


Itama anty salamatu kunya taji sbd mantawa tayi da umme da iyami dasuke taredasu sbd sun Saba zantukansu na banza dasu maman junior shiyasa.


Shanyewa tayi ta miqawa umme kwalbar daidai isowarsu qofar part dinta motar har qofar palonta ta faka suka fito umme na riqeda hannunta tana fada maganganu qasa qasa na rikita miji wainda sukafi qarfin duk rawar Kan Amatun kunya kamar ta qwace hannunta ta zura da gudu Amma ummen ba ruwanta fada Mata takeyi har suka shiga suka zauna palon tana sake zayyano Mata zantuka masu qarfi wainda wasune suka samu damar shiga kanta wasu kuwa nauyinsu yasa suna kasa shigewa Kan nata.


Turaruka ummen ta fitar cikin jakar hannunta ta fesawa Amatun ko Ina jikin masu wani irin sanyin qamshi dagaji tasan bazasu wuce ouds ba masu tsananin tsada take qamshinta ya qaru tana fitarda wani qamshi me ni'imtaccen sanyin dadi suka Fara qoqarin tafiya anty salamatu tace"


Zarah ko lafiya Naga banganta ba na dauka ma zamu sameta anan gashi har zamu tafi.

Umme tace'


Eh Kam gashi dai Nima duk yau banganta ba Nima nai zatan zamu sameta anan din tana jiran isowarmu.


Iyami data miqe tsaye tana gyara zaman mayafinta yace"


Mezaisa zarah tazo ta zauna anan tana jiranmu karku manta bafa kamar da bane yanzu ana Magana akan Amatu tazama matar mijintane Dole wani abun zata Kama kanta ba kamar da ba da Amatun take matsayin qanwarta yanzu kishiyarta ce Dole akwai radadi ko yayane aranta.


Tsit Amatu tayi tana saurarensu sbd duk lokacinda akai Mata tunin kishiya saitaji kamar hankalinta nason tashi saidai girma da nauyin anty zarah da haryanxu take gani da ji atareda ita yana danne kishin datakeji shiyasa take sauke zafin kishinta agun MAHMOUD sbd bazata iya kallon fuskar anty zarah tayi fitinar kishi da ita ba duk zafin kishinsa kuwa sbd Abu daya data fahimta takuma lurarwa kanta MAHMOUD da kansa zai iya kiranta butulu akan zarah idan bata nutsu ta iya zama acikinsu ba yanzu Kam akwai aiki agabansu su dukan na iya zama da juna.


Bayan tafiyarsu iyami kasa tashi tayi daga Inda take zaune tashiga tunani daban daban akan rayuwarta da Kuma ranar farko da aka Fara kawota cikin part dinnan amatsayin matar KHALIL DAHEER ZABEERA yanzu Kuma gashi ankuma kawota amatsayin matar Dan uwansa MAHMOUD DAHEER ZABEERA,

Duk da ansauya sashen gabaki daya Babu inda zaka iya gane shine wancan din Amma dai memories diinsa suna cikin zuciyarta.

Hawayene suka ciko idanuwanta suna qoqarin gangarowa taji bude qofa 

Bata dagoba Amma qamshin daya shiga cikin hancinta da motsinsa da baya qarfi yasa ta fahimci waye yashigo ta rufe idanuwanta ta bude ahankali batareda ta dago ta kallesa ba saima sake lumshe idanuwanta datai.


Qarasowa yayi cikin nutsuwarsa da kamalarsa ya zauna kusada ita sosai qamshinta ya Shiga hancinsa yanl dago fararen idanuwansa dasuka Gama gabalaituwa a sonta ya zuba Mata tareda riqo hannuwanta ya sarqe da nasa ya sauke ajiyar zuciya wadda itama ta sauke tata a boye cikin cikinta.

Kasa Magana yayi sbd bayajin yin maganar ya kwantarda kansa Kan kafadarta Yana sake sarqe hannuwansu ya lumshe idanuwansa sukai shiru ahakan sai numfashi da qamshin juna dasuke shaqa nutsuwa na shigarsu duk da Babu Wanda yafito yagfada Amma numfashinsu dake fita ya bayyanarda hakan.

Sun jima ahakan Babu wani motsi Saida yagama samun dukkanin nutsuwar daya rasa kafin ya sauke numfashi tareda dagowa ya kalli fuskarta suka hada idanu ta sauke nata tana qoqarin rufesu ya Kai hannu ya juyo da fuskar tata Yana kallon halittar da ita kadai ke iya rikita MD ZABEERA baisan lokacinda ya saki wani irin murmushi ba yana kallon bakinta daya iya fidda Magana ta arziki data tsiya.

Fuskarsa yakai dab da tata Yana kallon cikin idonta yabawa bakinta light kiss Yana sake sakin murmushi cikin taushin muryar data sanyata dago idanuwanta cikin rashin yadda ta zuba Masa yace"


I can't live without you Mrs MD ZABEERA so kada ki sake tunanin barina sbd komai zakiyi bazaki iya barin rayuwa Dani ba.


Miqewa yayi tsaye hannunta cikin nasa har lokacin ya miqar da ita Yana cewa''


Let's have dinner zarah is waiting.


Ba musu tabiyosa suka fito hannunsa na riqe da nata itama saiyi takeyi tana kallonsa duk da tasan so yake azauna lfy Amma dai mamakinsa bai daina kamata ba sbd ganin yanda ya sauya din dama ita batada niyar zama da miji Babu shaquwa Babu Wasa da dariya Babu hayaniya Babu muguwan wasan gudu gudu idan ma takama to Ina dadin rayuwar auren take tanason morewa sauran kuruciyarta a tareda mijin aurenta Dan haka Babu wani daga mulki sai oda a Shirin zamanta dashi.


Suna shiga anty zarah na fitowa daga bedroom dinta cikin adon riga da skirt na lace maroon tayi Yar simple makeup ga qaramin cikinta daya Dan fito tayi kyau itama sai qamshi take saidai suna qarasa shigowa qamshin dake fita cikin Amatun saita ji ta daina Jin natan ta qurawa Amatun idanuwanta dake son raunana da irin dacewa da kyan dasukai tareda juna ta kalli hannuwansu dake sarqe tafara Kiran sunayen Allah tana kore shedan daga zuciyarta ta saki murmushi tana kallonsu tace"


Sannu da zuwa Amatu.


Murmushi Amatun ta saki tana kallonsa da shima ita yake kallo tace"


Thank you anty.


Kallon MD din zarah tayi tana dauke idonta daga Kan hannunsa dake riqe Dana Amatu tace"


Dinner is ready fa.


Dining suka nufa su dukkansu suka zauna zarah ce ke zaune kusada MAHMOUD din sukaci abinci itadai Amatu drink kawai Tasha sai spoon biyu datai ta miqe tace ta qoshi.


Shima ba wata yunwa yakeji ba Amma ya zauna yaci abincin sosai tareda zarah haryana yaba abincin sosai sbd Fara sanin halin Mata dayayi ya fahimci sunfi son ko yaushe ka nuna musu yabawa da kulawa.

Aikuwa hakan ya faranta ran zarah musamman daya nuna Jin dadin abincin a fili saitaji damuwarta ta ragu sosai suka baro dining din itama Yana riqeda hannunta suka iso ya zaunar da ita Kan kujera ya zauna gefenta Yana kallon Amatu data matsu tawuce yafara musu bayani da nasiha tareda roqon Dan Allah a zauna lfy plus respecting juna duk da yasan suna ganin qimar junansu sosai kafin ya sanar dasu 2days ne kwanan daga haka aka tashi Amatu tafara wucewarta shikuma zarah yabi Dan sake lallasarta Abinda Baya faruwa a zamansu mamakinsa da Jin dadin hakan ya sanyaya zuciyarta sosai harta cemasa yatafi gurin Amatu tana jiransa.

Bedroom dinsa ya nufa yashiga wanka Yana fitowa Saida ya tsaya wata waya kafin ya fice.


Bedroom 'dinda ta tabbatarda shine nata tashiga data dawo daga sashen na zarah ta ajiye wayarta ka bedside drawer ta warware lafayarta ta nade takai wardrobe

tana budewa ta tsaya kallo cikin mamakin ganin Kaya a shaqe maqil da hadda wainda aka dinka da wainda ba'a dinkq ba ga qananun Kaya da jallabiyas ire iren wainda yasan tana sanyawa.

Murmushi ne yaso subuce Mata data Kai hannunta Kan tarin qananun kayan dake jere Wanda taga bumshorts ne sukafi yawa abin data lura yafiso kenen wato shigarta zata fiddo cinyoyinta duka a waje.


Rungumeta taji anyi tayi saurin juyowa sbd bataji motsin shigowarsa ba,

Kallon fuskarsatayi cikin basarwa ta zame daga jikin nasa ta jefa lafayar ta rufe wardrobe din ta bar gurin ta nufi toilet ta jima ciki Babu Abinda zatayi tana saqa da warwara kafin dai ta wanke hannuwanta tayi alwala kawai ta fito tana goge fuskarta da qaramin towel sai ganin lafayarta tayi ya miqo mata Yana cewa''


Ki mayar inason nizan cire miki inason sake ganinki cikinta you look innocent acikinta.

Batareda ta kallesaba ta karba ta nufi gaban mirror tana nadawa ya zauna Kan sofa Yana kallonta hannuwansa nade da qirjinsa.


Tana gamawa ta juyo ta kallesata ta gefen Ido ya taso Yana murmushi ya Kama hannunta suka nufi bedroom dinsa suna shiga wani sanyin qamshi ya doki hancinta sbd kalar turarukansa ba Arabians bane nasa designers Eglh perfumes yake amfani dasu,

As she expected komai na dakin fari ne da milk sbd sune colours dinsa.

Daddumar sallah ya Ciro itama milk color ce ya shimfada Yana kallonta yace"


Kinyi alwala right?


Saida ta dauke Kai kafin tabude Baki daqyar tace"

Yes.


Yanda taketa daure Masa din Yana sake burgesane Bata saniba sbd shi fushin ma nata Yana Masa kallon wani sabon feeling.

Sallah sukayi ta nafila rakaa biyu kafin ya juyo ya riqo hannuwanta duka biyun Yana kallon fuskarta ahankali ya furta"


Sorry.


Qin juyowa tayi ta kallesa ta zame hannuwanta zata miqe ya matse hannun Kai tsaye yace"


I love you..


Cak ta tsaya daga qwace hannun dazatayi zuciyarta ta Fara tsananta bugu takasa motsawa hakama takasa juyowa ta kallesa.


Ya lumshe idanuwansa yasake budewa ya Dora akan hannuwanta dayake riqe dasu cikin murya me taushi yasake cewa''


I love you AMATULLAH K SALEH and I am saying sorry so please wannan fushin yakamata ya sauka please.


Juyowa tayi tana kallon fuskarsa zuciyarta na qarasa bugawa da qarfi ta kasa yadda da Abinda taji idan MAHMOUD ZABEERA dinda tasani ne yake furtasu saidai zumudin zuciya dakeson kamata gudun bada kanta yasa ta miqe ahankali tana zare hannuwanta ya dawo da ita jikinsa ta hanyar fixgota ta Fado qirjinsa ya Bata kyakkyawar runguma Yana fada Mata Magana cikin kunnenta data sanyata saurin zaro Ido waje tana kallonsa takaici da muguwar kunya suka dabaibayeta batasan lokacinda ta Fara mintsinansa ba ta bude baki Dole tana cewa''


Wlh ni sharri ne wannan kakemin, Allah bazan yaddaba....


Dariya yakeyi Mara sauti da hayaniya wadda yaune karonta ba farko ganin dariyarsa ba murmushi ba.

Ganin ta kunnu sosai da Abinda ya fada din yasashi miqewa Yana Sosa inda ta mintsinesa Yana cewa''


Zaki fasamin fatane da wannan mintsinin naki..

Biyosa tayi tana sake kunnuwa har lokacin kunyar zancen bai saketa ba ta nufesa tana cewa''


Saika janye wannan sharrin dakamin bazan yadda ba..

Tana isowa gurinsa ya riqe hannuwan tareda shigar da ita jikinsa ya Kai fuskarsa Kai tsaye ya hade da Tata ya hade bakinsa da nata yana Bata wani ni'imtaccen kiss daya kashe jikinta harya warware Mata lifayar jikinta Bata saniba Saida ya cirata gabaki daya zuwa Kan qaton gadonsa Yana rage musu hasken dakin ta makunnin gefen gadonsa.

##Mamuh#*_MQ 49_*




*_THE FLAVORLAND BY ACEEY_*

Ina ma’abotan son ingataccen yaji, Different Flavors that complements each other, Yajin da ke daidaituwa da duk sinadaran abinci na al’adance da zamanance, Muna muka albishir da sanardaku cewa nesa tazo kusa domin @the_flavorland by Aceey yakawomuku duk nau’ukan yajinda kuke iya buqata Saboda yajin ya hada da:

Daddawa Yaji, Waton yajin daudawa

Garlic Yaji, waton yajin tafarnuwa da kuma

Beef Yaji, wato yajin Nama kuma me hade da nama

Domin ayukkanku da yau da kullum wanda ya hada da:

Dahuwar abinci/nau’uka na miyoyi DA

Gashe gashe da soye soye kamar su

Kaza

Kifi

Nama

Doya

Dankalin turawa/hausa

Awara

Danwake

Gurasa

Kwado da dai sauransu....

Ba Mu tsaya anan ba——

The_flavorland ya hada da kayan tande tande da lashe lashe da suka hada da

Hoppers wato Fara

Milky candies wato alawar madara da kuma

Milky balls wato Gullisuwa da de sauran abunda rai ke buqata...

Zaku iya tuntubar mu a kafofin sada zumunta kamar haka

IG: @the_flavorland

Whatsapp:08104673847

Sending Some treats your way.... l


Let us satisfy your cravings:

We Deliver anywhere and everywhere.




************

Ahankali ta bude idanuwanta dake cikeda nauyin baccin dabai Gama isarta ba sbd sai Bayan sallar asuba ne tasamesa tana Gama budesu da kyakkyawar fuskarsa tafara cin karo daf da tata numfashinsu na sarquwa cikin na juna,ta kalli idanuwansa dake lumshe ta gangaro da idanuwanta Kan lips dinsa wani gajeran murmushin samun nutsuwa ya subuto Mata ta motsa hannuwanta dake sarqe cikin nasa taji yasake matsesu ta maida kallonta Kan fuskarsa da mamakin da alama idanuwansa biyu kenan?

Hancinsa taji akan nata ya hade fuskarsu ya Dora mata ta Kai idanuwanta Kan idonsa daidai Yana budesu cikin kasalar baccin dabai Gama sakinsa ba ta dauke idanuwanta ahankali daga nasa zata sake zamewa yasake qin Bata damar motsawa.


Ahankali ta bude bakinta dake daidai kunnensa cikin qaramin sautin daya qarasa kashe jikinsa da saukar Masa da kasalar tace"


Yunwa.


Daqyar ya iya bude idanuwansa dasukai laushi da yanayin yanda dumin numfashin bakinta ke shiga cikin kunnensa ta maganar datai Masa.

A kasalance ya saketa ta tashi zaune ta sauka daga Kan gadon ta nufi toilet ta Shiga.

Wanka tayo tana fitowa daureda towel brown ta nufi closet dinsa ta dauko wani sabon towel din qarami Tana sake goge kanta ta nufi gaban mirror Yana duba dryer Amma Babu a dakin ta waiwaya ta kallesa taga idanuwansa qyam akanta Yana binta dasu kamar wani mayen qarfe saita fasa tambayarsa sbd ganin hadda miskilancinsa daya hanasa tashi bare Magana sai binta yake da idanuwa ta nufi qofa ta fice zuwa bedroom dinta sbd akwai acan taganta jiya gaban mirror.


Tana Isa dakin ta zauna gaban madubin ta jonata ta kunna ta hau busarda gashin tana kallon fuskarta dake wani irin blushing da qyalli ta cikin madubi,

Tana gamawa ta gyara Kan ta daure ta shafa Neutrogena oil sai bodymist dasu spray ta qara da humra me sanyin qamshi ta miqe takoma jikin wardrobe ta bude Bata wani tsaya zabe ba ta dauko wani plain drylace peach ta saka riga da skirt ne saita fito Palo tana qoqarin nufar kicin akai Knocking ta nufi qofar ta bude,

Cikin sa'a kuwa abinci ne anty zarah ta aiko musu Dan haka saita fasa aikin ta ajiye a dining ta Kama hanyar zuwa tadoshi aka Kuma knocking taje ta bude wani abincin ne daga umme itama ta karba duk ta hada ta ajiye a dining tana juyowa da nufin zuwa tadosa saigashi yafito shirye tsaf cikin wani milk yadi me tsananin taushin daya bayyanarda tsadarsa fili ya nufota Yana kallon kwalliyarta tareda nuna yabawarsa a fili Yana Mata kallon qasa qasa daya sanyata Jin kunya me tsanani sbd kallon ya qunshi yagama da saninta cikinta da wajenta ga sauke Kai daga kallonsa tana juyawa ya riqota ya dawo da ita gefensa suka nufi dining din Yana kallonta qasa qasa da wani irin murmushi harsai data gaji cikin muryar shagwaba tace"


Dady Allah zantashi na tafi.


Qaramar Daria Mara sauti ko kadan yadan saki Yana sauya kallonsa daga kanta yace"


Ok sorry sorry na daina Zo Nan lemme feed you.


Akan cinyarsa taci abincin tana bashi Yana Bata sai sake kashe Masa jiki takeyi da rashin zamanta guri daya ajikinsa daqyar dai aka gama cin abincin ya dauketa suka koma daki tana wani zille zillen daya qarasa juyar dashi daga MD ZABEERA.



Qarfe goma sha daya harda kusan rabi suka fito tana riqeda hannunsa ta sauya wasu kayan sbd wani wankan datayi tayi simple makeup da wani irin hot red lipstick daya zauna daram Kan lips dinta dayaketa saukar hankalinsa Amma Dole ya dauke Kai suna shiga palon zarah ya saki hannunta ya nufi sama inda hafsatu tace musu tana can yatafi yabarta tana kallon hannunta daya saki domin zuwa ga wata wani rashin Jin Dadi ya taso ya rufe zuciyarta ta zauna Kan kujerun dake palon Ahankali tana Kiran sunayen Allah tareda kore shedan daga cikin Kai da tunaninta taji motsin saukowarsu ta daga Kai tana kallonsu hannuwansa duka biyun riqeda zarah din suna saukowa yanajin kamar ya daukota gaba dayanta ya sauko da ita sbd ganin yanda take tafiyar sbd tace Masa da ciwon qafafu ta kwana.


Har Kan kujerar yakaita ta zauna Rana kallonsa cikin farin cikin kulawarsa gareta tace"


Thank you MD.


Murmushi me sanyi ya sakar Mata Yana zama kusada ita yace"


Akwai godiya tsakanin miji da Mata ne?


Dariya tayi tana kallon Amatu dake qaqalo murmushi tace"


Amatu Yana tambaya tayani bashi amsa sbd zaifi ganewama idan Kika fada Masa Dan Naga yafi gane yarenki.


Maganar ta daki zuciyarsu daga Amatun har shi Musamman shi ya tsura Mata idanuwansa yanajin wani irin yanayi me nauyi na rashin Jin Dadi wato tariga da ta amincewa kanta yafi son Amatu kokuwa yafi daukar Amatun da mahimmanci akanta ko me?


Amatu ma Jin tayi nauyi da rashin Jin Dadi ya dabaibayeta take sbd maganar antyn Magana ce data fito dauke da raunin da zuciyarta ke ciki batareda tasani saitakejin sabon mutuncin antyn na sake shigarta koba komai haryanxu anty mutum ce me tsananin mutunci da ganin qimar Dan Adam duk wannan auren na bazata da akaiwa mijinta da qanwar data ke yiwa kallon uwa daya uba daya bai canzata zuwa wata daban hakama vai sauya kyawawan halayenta ba.


Kallonta tayi taga cikin Yar dariya tai maganar bakin gskiyarta batasan tayi mgnar da wata manufa Abinda yake gskia ta fada Dan haka sai itama ta qirqiro murmushi cikin batar da zancen tace"


Anty baya buqatan amsa yasan akwai godiya tsakani ma'aurata musamam ma keda kikeji da Rabin ranki godiya bakomai bace.

Dariya anty zarah tayi tareda kallon Amatun tana jinjina sunan Wanda rabonta dataji tun zamansu asibiti jinyar Muhammad.


Yanason fita Amma sbd yakira Dr Fatima yasa ya jira harsaida tazo ta duba zarah din ta tabbar Masa da bakomai bane duk cikin laulayin cikine sai nauyi da cikin zai Fara shiyasa Dan haka bayan fitar Dr Fatima fita yayi shima ita Kuma Amatun ta Dan jima kafin ta tafi sbd qafafun anty zarah din ciwo sukai Mata sosai Sai data Dan tattausa Mata su tasamu tayi bacci kafin ta fito Takoma tayi sallah ta kwanta tanajin bacci.


Da daddare Takoma tasake dubo anty zarah din duk da ba wani Abu dake Mata ciwo kawai qafafun ne acan tabarosa tadawo Saida antyn tayi bacci yadawo sukai wanka suka kwanta.

Washe gari zai bar sashenta yakoma na anty zarah Dan haka tun safen bai fita ko Ina ba suna Palo suna shiririta ita ala Dole saiya lallasheta yasata bacci kafin yatafi haka dai suka shiririce har sallar magriba tayi ya tafi.


Zarah duk yanda tayi tunani da Shirin dauriyar abubuwan dazataita gani tareda daukarwa kanta alqawarin dangana tayi Shirin zaman hkr sai abin yazo Mata a baibai yabarta da mamaki sbd MD sauya Mata yayi daga MD ZABEERA zuwa asalin miji,

Ya sauya ta bangarori dabam dabam,

Babban mamakinta ayanxu shine zaman gida daya koya sosai yake zama agida wani lokacin Yana yini guda cikin zabeera bai fita ba Yana tareda iyalinsa ga yawan fara'a daya samu kansa aciki Abu daya datake maimaitawa shine Bata taba Tunanin ummanta datace Mata wata kishiryar kamar alheri ce sbd tana gyara maka mijin daka jima Yana wahalarda rayuwar aurenku hakama wasu yancin naki wata kishiyar itake kwato muku keda yayanki gurin miji ta hanyar sauyasa,

Tabbas ta yadda da hakan,

Akwai Abinda bazaka iyaba arayuwar zamantakewarka da mijinka sbd ka kashe zuciyarka Dan haka kodai duk wadda za'a auro kingama cutarta sbd kin sabawa mijin da yin shiru akan haqqinki Dan haka itama bawani dadinsa zataji ba kokuma kisamu wadda zata sauya mijin kisamu rayuwar dabaki samuba abaya,

Kishiya ko wace iri kasamu ta gari ko akasinta tasan da akwai ciwo Amma dai duk da hakan tana jinjinawa Amatu sbd ta taimaketa tanan Dan ita dai daza'a barta saidai suyi rayuwarsu sugama ayadda suka Fara bazata iya yiwa MD hayaniya ko yunqurin sauyashiba sbd yafison rayuwar kadaicinsa kamar tafi Masa nutsuwa takega shiyasa batason shige Masa sosai.

 Abu dayane data lura dashi shine wen ever Amatu is around idanuwansa akanta suke sbd bazai iya Hana zuciyarsa Abinda takeso ba saidai Bata damuba sbd itama aduk lokacinda take kusa to hannuwansa bazasu iya zamaba sai acikin nata Koda Amatun na kusa Wanda hakan ya tabbatar Mata da tanada nata bangaren me mahimmanci a rayuwarsa.


Anasa bangaren kuwa yasamu kwanciyar hankalinda baitaba samuba a rayuwarsa tun bayan rasuwar mahaifiyarsa tabarsa,

Yasamu nutsuwar zuciya da rayuwa,

Yasamu kwanciyar hankali data ruhi,

Rayuwa cikin iyalin dakake matuqar so suke sonka tareda baka nutsuwa shine asalin Abinda baisaniba sai yanzu,

Amatu ce takawo sauyi arayuwarsa da zuciyarsa Amma Kuma zarah ce abar jinjinawa kwanciyar hankali da nutsuwar rayuwar dasuke sbd itace ta   dauki komai da salama da dangana tareda sawa kanta nutsuwa batareda damuwa ko tashin hankali ba azaman Wanda yasa ake zaune kalau,

Da Bata bada wannan gudunmawarba da duk yanda suka Kai ga tsananin son juna shida Amatu bazasu samu wannan kwanciyar hankalinba da nutsuwar zaman lafiya.

Nuratu tazama tamkar aminiyarta yanzu sbd kusan kullum gurinta ma take yini hardai ranarda anty salamatu tazo gidan yini sukeyi fira USI ma da tintini yarinyar ta fice Masa arai sbd kusan itace silar komai tun Yana shareta har suka Fara sabawa sbd Amatu dakuma yaganta Dr salman dayake babban abokin shawarar USI dabaida amintaccen Dan uwa irinsa da hakan dai suka Fara sabo da ita sosai.



Satinta hudu da tarewa tafara Shirin komawa sbd school karatunsu yadauki zafi Dole zata koma Dan haka duk sukabi suka wani sukukuce musamman ita dazata Koma ita kadai ko Muhammad gurin umme zaiyi zamansa daqyar ma dadynsa yabari Dan acan yaso sanyashi school Amma ummen ta toqa hakama shima Muhammad din yafison gurin ummen yanzu sbd tana sakaltashi da yawa gashi Kuma yaga Yana ganin dadynsa anan.


Ita kanta anty zarah zatai kewar Amatun sbd sunyi sabon sabo duk da har abada zasu taba komawa yanda suke Ada ba Amma ko yanzu sunyi sabon shaquwarsu suna tsananin mutunta juna da gujewa Shiga haqqin juna.


A gidansu ta yini Daren ranarda zata koma canma Saida tayiwa su iyami kukan barin gida kafin yazo da daddare ya dauketa suka koma gida.

Washe gari Saida tayiwa kusan kowa dake cikin zabeera bankwana kafin suka wuce USI ne dakansa yakaisu airport suka wuce yadawo.


Sbd son cire Mata damuwar data sanyawa ranta yasa Basu koma Greece ba direct suka nufa US.

Wata irin rayuwar Jin Dadi da sakewa sukai a US tamkar turawan qasar Dan sai alokacin tasake sanin asalin waye MAHMOUD ZABEERA sbd wani bangarensa data gani na dabam wato Dan rayuwa.

Duk yanda zatai rayuwa bazata manta wainnan kwanakin dasukai a US ba sbd ya shayar da ita soyayyarda har abada bazata barta ba,

Ya sanyawa zuciyarta wani sabon maganadisun sonsa da qaunarsa.


Kwanansu takwas suka tattara suka nufi gida saidai Kuma kamar karsu dawo tunda suka dawo tafara zuwa school kwana biyu shikenan ciwon zazzabin dare ya sanyota gaba sunyi yawon asibitin hardai aka tabbatar musu da ciki ne Dan haka ba wani magani haka suketa fama duk wani aikinsa ya ajiyesu jinyar matarsa yake cikeda kulawa da tsananin qauna.


Ganin harya share kusan wata daya da rabi yasa ta daure ta bawa kanta qwarin ta nuna Masa ta warke sarai kafin yafara maganar komawa sbd tarin ayyuka da Kiran dayaketa faman Sha dazai tafi ita dakanta takaisa airport suka fito motar ya kamo hannunta ya matso da ita cikinsa Yana kallonta da fararen idanuwansa dake bayyana newarta tun kafin ya tafi ya bude baki ahankali Yana shafo cikinta cikin laushin murya yace"


I will miss you wife.


Dan dago qafarta tayi sbd yafita tsayi takai bakinta Kan nasa ta Dora ahankali ta zura Harshenta tabashi wani irin kiss tana kallon cikin idanuwansa tace"


I will miss you More.


Rungumeta yayi tareda sauke ajiyar zuciya Yana shafa Bayanta yace"


I love you.


Qanqamesa tayi kalmarsa na sake kashe jikinta.

Sun jima ahakan kafin lokacin tafiyarsu yayi yabata kiss a goshi ya wuce tana kallonsa harya shige ta juya jiki amace ta shiga mota tabar airport din tana Jin kewarsa kamar tabisa. 

##Mamuh#*_MQ 50_*



https://youtu.be/1VyZ6f1GTWg

Please subscribe to our YouTube channel 👆👆👆




Tana komawa gida kwantawa tayi tun anan Palo tana waya da anty salamatu akan maganar zuwan datakeson tayi suna gamawa anan palon bacci ya dauketa.

Bacci me nauyi tayi sai kusan yamma ta farka ta tashi zaune tana Dan dafe kanta dayayi Mata nauyi sbd baccin datai dakuma Dan ciwon dayake Mata.

Miqewa tayi ta nufi daki Kai tsaye toilet ta wuce tayo wanka dan jikinta yasaki tayo alwala tafito ta sanya riga da wando me Fadi ta sanya dogon hijab tahau dadduma ta tayarda sallah.

Bayan tagama sallar kicin taje ta hado tea da biscuits tazo ta zauna Tasha tana kallon agogo tasan zuwa yanzu ya Isa sauka Amma bazata kiraba zata Bari idan yahuta yasamu lokaci zai kirata.



Washe gari da wuri ta wuce school sbd akwai asibitin dazasuje daga school din,

Tunda safe shine ya tayarda ita daga bacci suketa waya Saida zata Shiga wanka suka aje tana Shirin fitowa yasake kiranta harta Isa school suna waya har Anty zarah yabata suka gaisa tayi Mata ya jiki daga Nan daqyar tasamu yayi hanging wayar ta maida hankali Kan Abinda yakawota,


Sai yamma likis ta dawo gida amatuqar gajiye Dan haka ko abinci Bata tsaya Ci ba wanka tayi ta kwanta baccin gajiya da daddare data tashi bayan tayi komai tasake komawa ta kwanta suna waya ta rikice Masa akan sai anturo Mata anty salamatu wlh bazata iya rayuwa ita kadaiba.

Dole ya amince wa buqatarta yaje yasamu kawu da kansa yayi Masa roqon zuwan anty salamatun wannan karon hadda iyami ya roqa taje tadubota tunda batada lafiya zataji dadin ganinta sosai.


Kawun bedai cemasa ya amince da zuwan iyaminba tukuna Amma dai ita salamatun zataje itama bazata jimaba sbd maganar neman aurenta da Andi ya nemawa alhaji qarami Wanda yake autansu Modibbo basason doguwar bidia kamar a taqaice suke son ayi auren.


Da kansa yasa akawa anty salamatun shirye shiryen tafiya sbd kusan shima a matse yake dataje din yasamu me kula Masa da Amatun Dan gabaki daya hankalinsa ba'a natse yakeba Jin yake kamar yaje da kansa yayi jinyar abarsa Amma Kuma ayanzu zarah dake kusan haihuwa tafi buqatarsa shiyasa ma duk wasu tafiye tafiyensa ya rage saita haihu sbd Bata kulawar datake buqata.


Duk yanda yaso anty salamatu ta Isa cikin kwanaki qalilan bai yiyuba sai bayan sati biyu da maganar ta tafi tareda USI dazaiyi 6month program acan aikuwa Nan suka dasa sabuwar rayuwa a Greece hakan kuwa ba qaramin nutsuwa yabawa MD din ba Dan dama shineya tsayawa USI akan zuwa Greece din yin program dinsa acan infact ma shine yadauki nauyin komai sbd kawai Amatun tasamu Yan uwanta atareda ita hakan ne kawai zai bashi cikakkiyar nutsuwa sbd yanayin datake ciki.


Zaman USI agarin tareda zuwan anty salamatu ya kawarda duk wata damuwarta da rage Mata kewarsa sosai Dan haka saita kwantarda hankalinta take karatunta cikin kwanciyar hankali da bada himma musamman yanzu da cikinta yafara girma Dan kusan wata hudu cikin na biyar kenan ita Kuma zarah ayanzu tana gab da shiga cikin watan haihuwarta shiyasa Koda yazo gurinsu bai wani dadeba yakoma yasake barinta cikin sabuwar kewarsa Dan har wata qaramar tafiya sukai dayazo din.


Zaune suke apalo tana duba wasu textbook na school anty salamatu Kuma tana yanka Mata gwaibar data siyo daga wani superstore ahanayarta ta dawowa school suna Dan fira sama sama sbd Rabin hankalinta nakan books din wayarta tayi ringing tun daga Kan kalar ringtone din tasan waye me Kiran ta Kai hannu ta dauki wayar tana sake wata qaramar ajiyar zuciyar son mijin nata ta daga cikin kasalalliyar murya tace"


AMATULLAH's husband..


Duk da Yana cikin wani yanayi na damuwa Saida yadan murmusa hartaji sautin murmushin ta cikin wayar ahankali tace"


Barka da yamma.


Barka wife,

Hw are you and my baby?

Ya anty salamatu hope duk Kuna lafiya?


Yes lafiyanmu kalau it's just that we're missing you badly.


Numfashi ya sauke Wanda yasata Dan gyara zama tana ajiye books din jikinta cikin sauti me nutsuwa tace"


Lafiya kuwa? You sound worried.


Dafe goshinsa yayi cikin yanayi na damuwa yace"


Zarah na asibiti tun safe she can't deliver by her self itama aiki za'a yi Mata.


Faduwa gabanta yayi cikin tsoro da damuwar itama zatazo wajen ga tausayin anty zarah din sai jikinta yayi sanyi da rawar murya tace"


Yanxu tun cikin dare anty zarah take cikin wannan halin Amma baka fadaminba dady sai yanxu?

Wlh na tausaya Mata yanxu kenan suna ZABEERA specialist?


Yes yau sukeson ayi aikin sbd qarfinta harya qare nagaji da ganinta cikin wannan halin.


Kwantar da murya tayi cikin tausayawa anty zarah din da tausayinsa shi kansa sbd tana iya Jin irin damuwar dayake ciki a muryarsa tafara qoqarin kwantar Masa da hankali tana sake bashi qwarin gwiwa akan Allah yasa ayi aikin lafiya akuma dace.


Bayan sungama waya tana fadawa anty salamatu tana lalubo numbern umman zarah din ta Danna kiranta,

Tana dauka ta gaidata cikin ladabi ta Dora da cewa''


Umma Ashe anty zarah haihuwar tazo wlh bansaniba sai yanzu dady yake fadamin tun safe Kuna asibiti.


Amatu antynki Kam tanajin jiki kitayata da addua Allah yarabasu da bbyn lafiya.


Inshallah Allah lafiya kalau zasu rabu 

Allah yasa ayi aikin cikin sa'a 

Nasan bazata iya mgn yanzu ba Ina Mata sannu zuwa anjima zansake Kira naji Inshallah.


Shikenan Amatu angode Allah yayi albarka.


Amin umma ngd sai anjima.


Aje wayar tayi tana kasa cigaba da karatun ta shiga damuwa da tunani tasake Kiran MD din takuma kwantar Masa da hankali.


Haka Takoma sukuku tunda sukai Magana takasa sukuni sbd hadda tsoro tsoron zuwan tata haihuwar yake sake shigarta takasa zama sai kiransu takeyi akai akai tana tambaya har lokacinda aka shiga aikin da zarah Amatun kiransa takeyi tana Kiran umman zarah din harsaida umman tace Mata"


Amatu ki kwantarda hankalinki tunda kema bake kadaiceba kada ki daga hankalinki wata matsalar ta taso Kuma ku rabawa mijinku hankali Kashi biyu.


Ana fitowa sallar magriba aka fito da lafiyayyan jaririn zarah cikin qoshin lfy sai kuka yakeyi cikin qoshin lfy aka wuce dashi sukai duk aune unen dasuke buqata kafin aka shiryasa cikin fararen overall masu kauri nurse ta fito dashi fuskarta daukeda murmushi ta nufo inda MAHMOUD yake tareda mahaifinsa Modibbo daya iso asibitin alokacin tareda umme da Haj maryam.


Modibbo aka miqawashi ya karbesa cikin farin cikin ganin jikinsa 'da na farko ga MAHMOUD dinsa.

Addua yayiwa jaririn kafin ya miqawa MAHMOUD da idanuwansa suke Kan fuskar yaron Wanda tunda nurse tafito dashi kafin yashigo hannunsa zuciyarsa tagama cika da soyayyar 'dansa.

Zarah tabasa farin cikin rayuwarsa,

Ada baidamu da samun 'dan kansaba Amma tun Bayan haihuwar Muhammad zuciyarsa ta cika dason Tara zuriar me yawa kodan ya Gina tashi zuriar sbd fita rayuwar kadaici.


Addua yayiwa yaron tareda Masa huduba yakirasa da sunan Muhammad DAHEER Modibbo.

Godiya Modibbon yayi cikin Jin dadin takwaran da akai Masa.

Nan kowa yafara karban yaron ana Yaba kyawunsa da kamannin babansa daya Dan dauko.


Saida aka gama murnan samun Modibbo aka koma murnar samun nasarar aikin da akayi umman zarah kuwa farin cikinta a bayyane yake ganin yanda kowa ke murnar haihuwar 'yarta.


Babban tashin hankalin dasuka shiga na samun mugun labari daga bakin likitoci shine ba lallai zarah din tasake haihuwa ba sbd rashin qwarin mahaifarta data fashe kafin Cs din.

Hankalin ummanta yatashi sosai hakama da duk Wanda yake gurin Saida jikinsu yayi sanyi Amma ganin MAHMOUD dakansa ya dauki qaddarar ya dauki juriya yasa kowa ya hkr suka buge da tarairayar zarah wadda tayi kukan wannan mugun labarin MAHMOUD na aikin lallashinta cikin nuna Mata tsananin damuwarsa Dole qarshe ta dangana tabarwa Allah akan hakan shine qila mafi alkhairi.


Amatu data sake Kira kusan karo na biyar kenan bayan haihuwar sai yanzu tasamu damar Magana da anty zarah din Tai Mata barka tana sake Mata sannu daga Nan suka Dan gaggaisa da jamaar dake asibitin ta kashe wayarta.


Kallon babynta takeyi idanuwanta na cikowa da hawayen farin ciki Dana damuwa taji an zauna gefenta tareda zagayeta da hannunsa har ita har Modibbon Yana kallon Modibbo dake baccinsa cikin nutsuwa ya shafa fuskarsa tareda maido kallonsa Kan fuskarta Yana riqo hannunta cikin kulawa da nutsuwa yace"


Zarah ki daina damuwa akan Abinda ba Allah ne yafadaba,

Banson Baki empty hopes Amma Dan ance bazaki sake haihuwa ba ba lallai bazaki sake haihuwar ba sbd ba fadan Allah bane ki dauki qaddara ki rungumeta Allah nason bayinsa masu yadda da qaddara.


Dago jajayen idanuwanta dake tsiyayar ruwan hawaye tayi ta kallesa cikin tunani daban daban Wanda ya kunshi irin hope din data hangowa kanta na samun soyayyarsa ta hanyar Tara zuria me albarka dashi sbd gano burinsa da qaunarsa tason Tara Yara.


Kamar yasan Abinda take Tunani ta ganin irin kallon datake Masa ya rungumeta ahankali tareda shafa Bayanta cikin murya me taushi yace"


Zarah yanzu ke ba matata ce kawaiba ke uwar 'yayana ce,

Ayanzu kin riga kinzama wani sashe na rayuwata da zuciyata,

Samun haihuwa a tsakani wani alamarine me girma Dan kuwa kinriga kinzama tamkar jagoran zuriar dazan Tara a gaba ko ba naki yayanba,

A da ke zarah ce matar MAHMOUD yanzu Kuma ke zarah ce matar MAHMOUD uwargidansa Kuma uwar Dan haka ki cire kowane irin tsoro ne kikasa acikin ranki sbd mi MAHMOUD DAHEER ZABEERA Ina baki tabbacin mutuwace kawai zata cireki daga rayuwata.


Wani irin kuka tasaki tana sake qanqamesa zuciyarta na cika da farin ciki da nutsuwar zancensa....


Ahaka ummanta tashigo tagansu Dadi yasake kamata ta karba Modibbon ta fita dashi sbd su iyami dasu maman junior dasukazo ganinsa.



Kwanansu shida a asibitin aka sallamesu suka dawo gida inda kowa keta zuwa barka da farko gida taso komawa MAHMOUD din yace tazauna a gidanta bayason zuwanta ko Ina.


Amatu kullum tana kiransu Jin takeyi kamar tazo Amma Babu dama Dole saidai take ganinsu ta hotuna shikansa MAHMOUD din bataga alamar zai barta tabiyo hanyar zuwaba sbd ko school yanzu ya hanata tuqi da kanta anty salamatu ke kaita wani lokacin Kuma USI idan yanada time kenan sbd akusa da street dinsu yakama apartment yake zaune.

Ranar data Fara Masa maganar tanason zuwa Kai tsaye yace"


No,Babu inda Zan iya Bari kije until you deliver.


Dama tasan haka zai fada Dan haka Bata wani damuba ta bar zancen ta maida hankali Kan rainon cikinta da karatunta ta bangare daya ga MAHMOUD din dayanzu wani soyayya yakeji kodan itama lokacin haihuwarta ya matso ne Amma sam yanzu ko barinta bayayi ta sarara akan Kiran wayarsa.


Bayan sunan Modibbo da sati uku yayi daidai da Gama exams dinsu tana gida kwana biyu Babu inda take fita ga nauyin cikinta ya dameta ma gabaki daya.


Zaune take ita kadaice agidan anty salamatu sunfita da USI siyayyar wasu daga cikin kayansa na lefe dayake siya tun anan sbd Shi da Nuratu sungama daidaicewa tsakaninsu yana dawowa yakeson ayi idan son samunsanema to ahade aurensu danasu anty salamatu sbd dagashi har nuratun kamar zasu cinye juna sbd soyayya shiyasa itama yanzu nuratun kamar ta hadiye Amatu sbd qauna Dan sai yanzu take qara sanin mahimmanci Amatu agurin USI da irin tsananin qaunar junansu dake tsakaninsu.


Kallon wani tv program na likitoci takeyi a CWTv hankalinta rabi nakan waya sbd tun safe take kiran wayarsa Bata shiga Kuma shima tun Daren jiyan raban daya kirata.


Sake Danna kiransa tayi akaro ba adadi still Bata shiga tana qoqarin sake Kira taji ana qoqarin bude qofarsu ta shigowa ta juyo tana kallon qofar da waya a hannunta sukai Ido biyu itada shi ta Dan zaro Ido tana kallonsa tareda miqewa tsaye komai nata na bayyanarda mamakin ganinsa shikuwa kallonta yakeyi cikin kewa da soyayyarta ya tsaida kallonsa Kan cikinta dayayi girma cikin wata free doguwar rigar masu ciki data saka wadda batakai qasa ba sbd kada ta takurata ya ware Mata hannu Yana kallon fuskarta daukeda boyayyan murmushi da gudun dabatasan zata iyaba tayo kansa ta fada jikinsa ya rungumeta Yana Dan dagata sama cikin farin ciki da murna tace"


I love this surprise of urs Husband.


Sauketa yayi tareda Kama hannunta suka qarasa shigowa taso karban luggage dinsa ya hanata suka nufi dakinsa tafara gyarawa Yana tayata suka gyara dakin duk da Babu Abinda yayi 'yar qurace kawai.

Wanka yashiga ta fita zuwa kicin hada Masa abincin dazaici.

Cikin farin ciki tafara dafa Masa pasta da carrots sai beef meat ta hado Masa Kan tray takawo Masa har bedroom dinsa yaci tana zaune tanata tambayarsu Modibbo Wanda kamar ubansu daya da Muhammad sbd suna dibar kamanni.

Yana gamawa ta kwashe kayan ta maida ta dawo ta zauna Kan cinyarsa tana sake tambayarsa meyasa be fada Mata zaizoba.


Fuskarsa ya Dora kan tata Yana sauke ajiyar zuciya a boye yana kallon cikin idanuwanta da itama shi take kallo ya Dora hannuwansa Kan cinyoyinta Yana shafawa cikin malalacin sauti yace"


Sbd inason ganin farin cikin bazata a kyakkyawan fuskan matana.


Murmushin Jin Dadi tasaki tana sake shigewa jikinsa ahankali tana qara cukuikuyesa qasa qasa da murya tace"


Ko acikin barci MAHMOUD ZABEERA yazomin farin cikina bayyananne ne bare ganinka a zahiri so lovely husband zuwan bazatanka ya tafi da zuciyan AMATULLAH K.


sake matsota yayi cikin jikinsa Yana shaqar qamshin jikinta ya shaqi numfashinta dake sauka Kan fuskarsa sbd matsuwar dasukai da juna ya Dora bakinsa Kan nata Yafara kissing dinta Yana zame hannuwansa zuwa wuyan rigarta.


Koda anty salamatu suka dawo da daddare guraren 9 Bata tareda wata gajiya sosai sbd sun Dan bibbiya guraren hutawa sun shaqata bataga Amatun ba a apalo ta shige da kayan zuwa dakin Amatun inda sauran kayan lefen suke Nan na Bata ganta ba sai tayi tunanin toilet Dan haka dakinta Takoma ta fada toilet itama tayo alwala tazo ta tayarda sallah.


Jin shiru shiru ba motsin Amatu yasata fitowa tana zuwa kicin ta duba ko tana can,

Ganin anyi sabon girki a kicin din yasata bubbudewa tana dubawa tafito  Palo ta nufa dining tana ganin plates da kayan da akai amfani dasu ta fahimci oga kwata kwata ya taho kenan ta fito kicin tana kallon hanyar zuwa dakinsa tasake tabbatarda shi dinne yazo ta wucewa daki tana cewa''

Naji dadin zuwanka nasamu yanzu nabi usi next week idan zaije gida.



Washe gari tana kwance cikin jikinsa tana bacci cikin nutsuwa sbd irin kyakkyawar rungumar da yayi Mata suna bacci cikin baccin tafara Jin kamar ciwo ciwon Mara na damunta Wanda yasata bude idanuwanta tana sake saurarawa Abinda takejin saitaji da gaske ciwon yake ta yunqura zata tashi zaune yabude idanuwansa Yana kallonta ta yunqura ta tashi zaune ya tashi shima Yana riqota yace"


Lafiya kuwa?


Kallonsa tayi da sauri tana dafe qasan cikinta a Dan tsorace tace''


Ina ganin labour ne..... kasa qarasawa tayi cikin tsananin azaba da firgici tace"


Hospital hospital hospital take me" duk arude take maganar a jujjuye batareda tasaniba 

Ganin hakan ya sauko gadon ya nufi wardrobe ya dauko shirt da wando yasaka cikin sauri tareda dawowa ya dauko Mata riga kamata ya sanya Mata suka fito tana sake dafe cikinta cikin azaba tana Kiran sunan Allah Dana MAHMOUD din cikin ciwo.


Jin dogon salati da qarfi yasa anty salamatu fitowa daidai qarasowarsu tsakiyar palon a Dan rude ta kallesu tana maida kallonta Kan Amatun daketa faman salati ba qaqqautawa cikin mamaki tace"


Subhanallah haihuwar ce ko me?

Lafiya kuwa?


Muje asibiti"kawai ya iya furtawa anty salamatun Yana nufar qofa da matarsa.

A gigice suka Isa asibiti musamman da ciwon ya taso Mata gabaki daya suna Isa ruwan haihuwa na fashewa akai labor room da ita.


Zama yayi Kan kujerun jira Yana kashe wayarsa sbd baya buqatan ko hayaniyar ringing waya.

Suna zaune saiga USI shima ya iso Nan suka Fara zaman jigum jigum cikin zullumi da fargaba,

Wannan zaman jiran dayakeyi yau yana daya daga cikin ranakun tsananinsa na rayuwa sbd gabaki daya Jin yake kamar nutsuwarsa zata bar jikinsa Amma haka dai yake zaune shiru kamar ba Wanda ke cikin tension ba.


USI da anty salamatu ne ke samun damar waya da Yan gida sunajin yaya kota haihune?

Zaman awa uku sukayi cikin ta hudu kafin Allah yabata ikon haihuwar baby girl lafiyayya da ita saidai ba qatuwa bace sosai sai kuka takeyi aka shiryata aka miqowa familynta ita ya karbeta Yana kallonta cikin wata irin nutsatsiyar sonta da qaunarta ya shafa Dan qaramin kumatunta Yana Mata adduoi da murmushi akan fuskarsa yace"


De symbol of my love FADIMATU ZARAH MAHMOUD ZABEERA.


Aikuwa cikin farin ciki anty salamatu itama ta karbi babyn tana kallon fuskarta cikeda murna tace"


MAHMOUD wannan 'ya da yayunta take Kama.

Murmushi kawai yasaki zuciyarsa na sake wanzuwa da farin ciki sai alokacin ya bude wayarsa da atake Kira suka Fara shigowa ya fice Yana amsawa.


Yana dawowa ya tararda anfito da Amatun ankaita dakin hutawa ya shigo Yana aika Mata da wani irin kallon samun nutsuwa ya qarasa bakin gadonta ya zauna tareda Dan rungumota yabata kiss agoshi yace"


Thank you.


Murmushi tasaki tana Dan harararsa tace"


Bazan qaraba daga wannan.


Dariya maganar tabawa anty salamatu takuwa ringa qyaqyata dariyarta shikuma wani guntun murmushi ya sake Yana sake kissing hannunta dake cikin nasa batareda yace komaiba.


Acan Nigeria kuwa cikin both families din haihuwar ta Isa kunnen kowa akaita Sanya alkhairi da yiwa FADIMATU ZARAH adduar Allah ya raya Akan sunna,

Zarah da akaiwa takwara kuwa rasa abin cewa tayi sbd farin ciki shiyasa ma tace zatazo taga takwara da kanta.


Kwananta daya a asibitin suka sallamota suka dawo gida Nan anty salamatu tayita hidima dasu ganin suna hutu Kuma gashi umme da zarah hadda Nuratu since zasuzo yasa ya yanke shawarar su dawo gida bayan ko 30days ne saita dawo.


Kwana biyar da haihuwar suka dawo Nigeria Nan aka kacame da sabuwar murnar zuwansu 'yan barka suka Fara sintiti musamman aminanta su maman junior da kullum saisun Zo iyami ma kwana biyu ta jera tana zuwa Saida akai suna tukuna suka samu sauqin baqi sai alokacin tafara samun kanta.


Yau satinsu uku da zuwa tuni tafara Shirin komawa musamman ganin yanda ogan yafara shishige Mata tanason Takoma tasamu matakin dauka kafin wani abun yasake Shiga sbd taga alamar son dawowa bakin aiki yake.


Ana gobe zata koma tafito palonta zuwa sashen anty zarah saigasu taci karo dasu sunfito itada MAHMOUD din Yana daukeda Modibbo hannunsa daya Kuma Yana riqedana ZARAn sunci ado cikin traditional attire sai murmushi suke ta qaraso suka hade tana murmushi ta gaida anty zarah tana cewa''


Fita zakuyi?


Eh Amma ba dadewa zanyi ba gurin umma zai ajeni.


Ok to adawo lfy Ina gaida umman bansamu nazo nayi Mata bankwana ba.


Kallonsa tayi shima tana sauya kalar murmushinta zuwa na neman mgn tace"


Take care.


Fuskar fadimah ya shafa Yana gyada Kai.

Suna wucewa Takoma ciki taqarasa sauran parking din da bataiba.


Washe gari anty zarah ce takaisu airport suka wuce dagacan ta wuce gidansu gurin ummah.


Bayan dawowarsu Greece da sati biyu yakoma bayan sun dauki me aiki da Nanny hakan saiya taimaka Mata sosai sbd samun damar maida hankali ga karatunta.


Rayuwa ahankali tafara sauri fadimah tayi wayo sosai tana cikin final exams dinta ta fahimci tanada wani cikin hankalinta yatashi sbd fadimah Bata Isa yayeba Dan haka taso cire cikin saigashi kamar Wanda aka fadawa yayi Mata zuwan bazata cikin sa'a kuwa kafin yatafi Saida yasanda zaman cikin Wanda yasama ya daga komawarsa yaqara kwanaki Saida tagama exams dinta akai duk wata hidimar daza'a yi ta karbi takardunta suka dawo Nigeria sbd shagulgulan bikinsu USI da aka Fara Wanda aka hade danasu anty salamatu Dan haka biki sosai akeyi a zabeera Koda ta iso ta fada cikin hidimar gadan gadan sbd dama amatse ake ta iso sbd wasu abubuwan da akeson gudanarwa Wanda suke buqatar kasantuwarta bikin USInta guda dakuma antynta anty salamatu.


Ranar asabar aka gama bikin amare kowacce ta tare gidanta

Anty salamatu zabeera ita Kuma Nuratu cikin sabon qaton sabon gidanta da USI ya Gina musu Wanda zasu zauna tareda iyayensa.


Ana kammala bikin ta yaye fadimah wadda anty zarah ce ta hadasu ya yaye tareda Modibbo takwashesu suka koma gurin umma tace sunyi yayen acan.


Ganin zarah batanan dazaiyi tafiya saitace zata bisa takuwa shirya tabisa suka tafi sudan.


Satinsu biyu suka dawo anty zarah ta karba miji daganan zaman ya Dore ahaka cikin kwanciyar hankali ba hayaniya sbd kowacce ta shafawa kanta lafiya sbd fitinar wani lokacin Hana komaima takeyi a tsaya guri daya akasa gaba akasa baya.


Lokacin haihuwarta nayi ta haifi baby boy aka saka Masa sunan kawu suna kiransa ABBA bayan haihuwarta da wata shida anty salamatu ta haihu a hannunta a asibitinsu wadda MAHMOUD yasake sauya Mata tsari da girma tafara aiki tun bayan haihuwar ABBA shiyasa itacema ta karba haihuwar antu salamatun data samu BBY girl itama bayan sunan anty salamatu da sati biyu Nuratu ta haihu itama a hannunta tasamu Me sunan kawu DR USMAN K SALEH yasawa babyn.


Fadimah a hannun anty zarah take Dan haka ita ABBA ne kawai agabanta  Muhammad ma tuni yafara zama saurayi Yana gurin Rabin ransa umme  wadda takejinsa fiyeda sauran 'yayanta Dan haka Babu me tabasa.

Shima ABBA Yana Isa yaye iyami ce tayi yayensa Nan MD yasata gaba akan sabon baby yakeso tanajin yafara fadar haka taso daga hankalinta Saida anty zarah Tai Mata waazin damace Allah yabata tayi haihuwar ta huta tunda gashi ita tanaso Allah be Bata ba.



Kallonsa tayi lokacinda tafito daga toilet daureda qaramin towel da ko Gama rufeta baiyiba ta qaraso inda yake zaune Yana aiki da laptop ta zauna Kan cinyarsa tana tanayi kamar zata saki towel din ta marairaice murya tace"


Positive.


Dagowa yayi Yana kallonta da fararen idanuwansa Yana Mata kallon are you serious?


Daga Masa Kai tayi yayi saurin rungumeta Yana zura hannu cikin towel dinta Yana cewa'' 


Thank you love.

##Mamuh#



ALHAMDULILLAH.


Da yardar Allah anan mukazo qarshen wanann littafin namu me suna MIN QALB wato DAGA ZUCIYA,


IDAN NAYI MANTUWAR WANI ABUN DABAN QARASA FADABA A LABARIN KUMIN UZURI KU DAUKESA AMATSAYIN AJIZANZI IRIN NA DAN ADAM.


INA ROQON ALLAH YABAMU IKON AMFANI DA ABIN ALKHAIRIN DAYAKE CIKI SABANINSA KUMA ALLAH YA MANTAR DAMU YAKUMA YAFE MANA,


AKWAI WAINDA TUN BAAZO QARSHE BA SUNA MAGANAR DANGINSU AMATU DA USI,

ANSAN KOWA BA DAGA SAMA YAFADO DUNIYA BA AMMA KADA KU MANTA AKWAI MARAYUNDA ADUNIYA HARSU BARTA BASUSAN ASALINSUBA BARE DANGINSU,

AKWAI WAINDA SUKE RAYUWA BATAREDA SUNSAN ASALINSUBA KO INDA SUKA FITO AMMA SAI ALLAH YABASU IKON GINA TASU RAYUWAR SU GINA ZURIAR KANSU DAN HAKA KU SANYA SU AMATU AKAN MASU IRIN WANNAN QADDARAR SBD A DUNIYA BAKOMAI KAKE SAMUBA.


ALLAH YA GAFARTAMANA

AMIN.


No comments

Powered by Blogger.