Mawahib 9-10


 💗MAWAHIB💗

       (Hot luv) 

Writing By Amnah El Yaqoub

9&10

Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin Samun Audio Novel's👇🏻

https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels





Captain Aryan yaci gaba da fadin "please kadena min maganar ta"


Ashraf yace"dole inyi ma maganar ta kuwa, saboda Ina sonta, najira kadawo ne infara yima maganar,banason kai tsaye in yiwa su Daddy maganar, kaima kuma kadawo kace kana sonta"


Captain Aryan dayake kwance cikin wani irin fargici ya tashi zaune yace"inso wa? ni...? Inrasa wazan aura sai wannan abar?"


Cikin zafin rai Ashraf yace"yauka fara? sau nawa Ina nemo yarinyar dazan aura kana cewa kaima ita kakeso? ban'isa inyi sabuwar Baby ba, kaima saika sota, 'yanbiyu mata masu kama daya kakeso insamo mana? shiyasa nafara fad'ama maganar,kar inje infad'awa su Daddy inason Mawahib kaima ka dage kace kai sai ita..., inkasan kana sonta to tun wuri inyi shiru da maganar"


Cikin taqaici Captain Aryan yace"kaga Ashraf,dan Allah idan zakayi zancen 'yanmata, toka dena saka yarinyar nan aciki, idan zaka so kowacce irin yarinya tonima zan'iya sonta,saboda jinin mu ahad'e yake,zan'iya son dukkan 'yanmatanka,amma banda ita..."(🙆🏻‍♀️)


Ashraf yayi shiru yana qarewa dan'uwan nasa kallo, tunda yacewa Mawahib qwaila yake tantama aransa anya Aryan yana cikin hankalin sa kuwa?kokuma de ya makance? 

Ahankali yasaki ajiyar zuciya yace"kagama?" 


Kai tsaye Captain yace"ban gamaba,inaso kasani batada abubuwan dazaija hankali na har'insota,bazan ta6a sontaba har abada,nawuce ajinta,bata cikin tsarina,bata Isa takama qafar irin matar dazan aura ba, sannan kaima Ina gargadinka,karka bari Momy taji maganar nan ,kuma abinda ya shafeni kaima yariga ya shafeka,bana qaunar ta,saboda haka dole kaima karabu da'ita tunda bana sonta...."


Ashraf yace"saboda

kaine kakawo ni duniyar ko? to saina aureta,inyaso ka mutu" 


Cikin sauri Captain Aryan yace"saide kaika mutu,kuma baka Isa ka auretaba INDE INA RAYE"



Ashraf yace"tosaika hana mugani"


Yafadi hakan tareda sakin tsaki, ya dauke fillonsa yamaida shi qafafun Aryan,ma'ana sukai kaida qafa. 


Kusan minti biyar dukansu sukai shiru babu wanda yasake yin magana, sai can Captain Aryan shima yasaki tsaki yadauke fillonsa yadawo dashi  kusadana Ashraf.(😂)



Ashraf yana jinsa yayi shiru ya qyaleshi,Captain yaji shiru Ashraf bai kula shi ba duk da yadawo da fillonsa wajansa,a hankali yace"Ashraf..."


Ashraf yayi shiru yaqyaleshi, yasake sakin dan qaramin tsaki yace"Ashraf katashi kayi Addu'ah"


Babu musu Ashraf yatashi yafara Addu'ah,saida yagama addu'ar sannan ya kalli Captain Aryan yace"kai kayi addu'ar ne?"


shima Captain Aryan yanajin Ashraf din yayi shiru yarabu dashi(😂)

Ashraf yasan sarai yana jinsa,sai yayi murmushi kawai yad'ora hannunsa akan lallausar sumar Aryan din batare daya qara magana ba,yanajin lokacin da Aryan din yafara bacci, amma shi bai fara bacci ba yana tunanin yanda zai 6ullowa iyayensu akan maganar aurensa da Mawahib,har wajan qarfe biyu nadare yana tunanin mafita,yanajin yanda Captain Aryan yaketa juye-juye kamar akwai abinda yake damunsa,ahankali ya rufe idonsa har bacci yayi nasarar daukar sa. 



Cikin dare Captain Aryan yafarka dawani irin ciwon mara,tun yana daurewa harya fara ciza lallausan lips dinsa, ga esi yanayi adakin amma Captain Aryan sai gumi yake had'awa,ahankali ya runtse idonsa yana tuna shawarar da likita yabashi akan wannan ciwon cikin nasa yakamata ace yanemi mace yayi aure hakanne zai kawo qarshan jinyar,ahankali yatashi zai dauko maganinsa yaji bazai Iya miqewa ba.


Cikin sauri yafara tashin Ashraf, yace"Ash,tashi!!"


Cikin bacci Ashraf yabude idonsa a hankali,ganin Captain Aryan a zaune sai had'a gumi yake hakan yasa yatashi cikin sauri, yadora hannunsa a kafadar Captain din sannan yace"meyake damunka?"


Saida ya cija lips dinsa sannan yace"magani na,bani maganina"


Cikin sauri Ashraf yasauko daga gadon,yabude yar qaramar jakar da Captain din yazo da'ita ya dudduba sannan yaga maganin,wutar dake gefen gadon su ya kunna saida ya karanta yaga maganin menene, sannan yabashi,yaje fridge ya dauko masa gorar ruwa, cikin sauri Captain Aryan ya 6alli maganin yasaka a bakinsa, sannan yakafa gorar ruwan a bakinsa saida ya shanye shi tas, sannan yafara maida numfashi ahankali.


Ashraf ya dafashi yace"Aryan...,nayima magana kadena shan maganin nan,gara kazauna haka idan kayi mafarki shikkenan zakaji sauqin abinda yake damunka"


Captain Aryan da kansa yake sunkuye yad'ago ya kalli Ashraf yace"kullum zan zauna kenan banida aiki sai mafarki? ni bazanyi asarar abuna ba,na matata ne...."(🙈🙊)

Yaqarasa maganar cikin sigar shagwa6a kamar ba Soja ba


Dariya takama Ashraf,amma dayake yasan halin dan'uwan nasa akan wannan dariyar yanzu saiya fara yimasa masifa, saiya danne dariyarsa yayi murmushi yace"tokayi aure"


Cikin shagwa6a yace"niba wacce nakeso"


Ashraf yace"Okay...mugunta ce tasa kake rabani da 'yanmata na kenan ko? kai baka auraba niban aura ba"


Captain Aryan baice dashi uffan ba,yaja fillonsa ya rungume tareda runtse idonsa yana numfashi sama-sama har baccin wahala yadaukeshi. 


Ashraf yana zaune yana kallonsa saida yaga yayi bacci sannan shima ya kwanta agefensa yayi bacci.


Dasafe bayan sungama buga ball dakinsu suka dawo kowa yayi wanka,gaba dayansu suna daure da farin towel a qugunsu sai wani d'an qarami guda d'aya kowa yana goge sumar kansa, Ashraf yad'auki wayarsa ya dokawa Mawahib Kira, a lokacin tana zaune tanashan tea tagama gyaran part dinsu kenan, har zuwa lokacin Mamy bata tashi ba kasancewar yau weekend ne bata tashi da wuri, mamaki ya kamata,kiran Yaya Ashraf da wannan safiyar lafiya? gaba daya sai taji tsoron daga wayar kartaje tunanin Nabiha yazama gaskiya idan kiranta yayi domin yafada mata yana sonta mezatace masa? haka ta kasa daukan wayar harta katse, daga nasa 6angaren yasake kira akaro na biyu,sai a lokacin ta dauka cikin ladabi tace"yaya Ashraf barka da safiya"


Saida yasaki wani murmushi najin dadi sannan yace"yawwa Mawahib idan kingama abinda kike please kizo ki gyara mana dakin nan..."


Cikin ladabi tace"to Yaya"


Daga nan yakashe wayar yad'auki mai zai fara shafawa, Captain ya

kalle shi yace"yanzu kai bakaji kunya ba?kasa yarinya agaba kana wani kashe murya saika ce kasamu wata babbar mace,wannan abun kunya har'ina "(😖) 


Ashraf yayi murmushi yace"kaine kake ganinta amatsayin yarinya,amma Mawahib tanada abinda wata babbar ma batadashi,ka nemi mace kayi aure kaqi, ka dameni da juye-juye cikin dare dashan magani, kawai ka lalla6ani inbarma Mawahib,ninasan abinda nagani, kaima kuma idan ka qarewa yarinyar kallo zakasan akwai kayan alatu"


Captain Aryan yasaki wani irin tsaki,cikin 6acin rai yace"Ash...nifa yarinyar nan batada wani abu wanda zangani har inji sha'awarta"


Ashraf yabi Captain Aryan da kallon mamaki,to kodai saboda rashin zuwansa gida akai-akai shiyasa baisan yaya Mawahib din take ba? girgiza kansa yayi, da alama dan'uwan nasa baisan yarinyar ba.


Captain Aryan yace"kuma a'irin wannan yanayin nawa kwanaki wani me magani yakai office dinmu, a lokacin inajin kasala,bana yin gym kamar yanda nasaba"


Ashraf ya zauna abakin gadon nasu yaci gaba da shafa mai a jikinsa,shikuma Captain Aryan yana goge jikinsa da dan qaramin towel din hannunsa,cikin aji kamar bayaso yaci gaba da fadin"naji me maganin yana cewa da maiqo da zaqi da kasala duk maganin yana yi,to nima inajin kasala, sainayi tunanin nima irin nasu ne,nakar6a nasha,inashan maganin nan daga nan labari yafara sauyawa,nakifa kaina qasan table sai hada gumi nake,na riqe mara,da farko nafara jurewa, danaga abun bana qare bane ahaukace naje wajan mai magani najashi gefe,nafada masa abinda nakeji,shine yacemin ai yayi tunanin inada aure, maganin masu aure ne, yaje yanemo min wani abu kamar goro, nide ban tsaya na tantance menene ba nafara ci,shine naji dama dama..."


Ashraf ya kwashe da dariya,yace"tokaima kawai daga ganin suna shan magani kaima saika sha?"


Adede lokacin Mawahib tazo kofar dakin nasu,a lokacin Captain Aryan baibawa Ashraf amsa ba, ita Kuma Jin shiru tayi tunanin basa cikin dakin,ahankali tatura qofar dakin ta shigo, gabanta ne yafadi ganin murd'ad'd'an jikinsa abaiyane,cikinsa har wani hawa-hawa yake alamun yana motsa jiki,ga faffadan qirjinsa wani irin gashi mai laushi ya kwanta,bata ta6a ganin namiji hakaba,gaba daya saita diririce jikinta yadauki rawa taqame awajan, adede lokacin Captain Aryan wanda bai lurada zuwan Mawahib dakinba,yasaki wata irin dariya wadda tunda Mawahib take, bata ta6a ganin yayi dariya haka ba,cikin dariya yacewa Ashraf "ta'inda ake hawa batanan ake sauka ba?,inacin abinda yabani najini nadawo Normal,daga ranar ban sake cewa zansha ba"


Suka saki dariya gaba dayansu,yajuya zai goge kunnansa na hannun dama, karkatawar da zaiyi yaganta a tsaye idonta yayi tsuru-tsuru, lokaci daya annurin fuskarsa ya sauya,ya wullar da towel din dake hannunsa,cikin 6acin rai yadaka mata wata irin tsawa yace"stupid girl....mekikeyi anan!!!?"


tun kafin yagama rufe bakinsa Mawahib tajuya da gudu tabar wajan,yanda yaga uban Hips dinta suna kad'awa saboda gudun datake hakanne yasake 6ata masa rai, 'yar qanqanuwar yarinya hartasan tayi ciko...(😱)


Ashraf ya ajiye manda yake shafa wa yataso yaduba baiga kowa ba,cikin damuwa yace"miye haka Aryan? Mawahib ce tazo kakoreta ko?"


Cikin 6acin rai yace"tayaya yarinya zatazo taganni ahaka ta rainani?" 


Ashraf yace"nina kirata tazo tagyara mana dakinfa"


"ta barshi,kaima idan bazaka gyaraba kabarshi" 



Ashraf yace"kaine qarami,kaine zaka gyara"


Aryan yace"minti nawa kabani?"


Ashraf ya harare shi yace"au Allah? to ko zamuje a tambayi Momy?" 


Cikin sauri Aryan yace"muje"


Kamar wani abun arziqi zasuyi haka suka shirya cikin sauri kai tsaye suka nufi part din Hajiya Kilishi,suna shiga Ashraf yace"Momy"


Shima Aryan din yace"Momy"


Tasan duk lokacin dasuke mata irin wannan kira to musu sukeyi a tsakanin su,cikin sanin abunda ya kawosu Hajiya kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,shekaru ko? nasani, dan Allah kurabu dani zuwa yanzu yaci ace kun daina wannan musun"


Alqali dayake zaune yanashan tea yakallesu yayi murmushi,wankan shadda su kayi mai launin light blue,banda shine ya haifesu to zaiyi wahala ya banbance su saboda hatta agogonsu iri daya ne, hular dake kansu ma iri dayace,koda yaushe yana alfahri da 'ya'yansa,tsugunnawa sukai suka gaida shi, sannan Hajiya kilishi tafara hada musu tea din suma, Ashraf yanacin sultan Chips din dake gabansa yana turawa Mawahib text naban haquri,sannan yasake roqarta akan taje tagyara musu dakin itada Nabiha, Mawahib tana ganin text din ta fadawa Mamy, sannan taje tasamu Nabiha, suka nufi dakin su Yaya Ashraf din,suna zuwa suka fara gyara dakin,duk wani kaya dasuka ganshi babu ninki suka ninkesu, suka adana musu shi,saida suka wanke har toilet din komai yayi tsaf, a lokacin aka kira wayar Nabiha, ta amsa wayar tafita, Mawahib kuma ta dauki air freshener tana fesawa a dakin,tabude fridge din dakin tasake gyara lemuka da ruwan dasuke ciki,glass cup din dasuke kan fridge din suma tasake gogesu tana gyara musu zama, adede lokacin suka shigo dakin duka su biyun,Aryan yana ganinta ya daure fuska yanuna mata hanyar fita daga dakin, cikin tsawa yace"get out...."


Tsawar da yayi matane yasa ta tsorata batasan lokacin data saki cup din hannunta ba, nan take yafashe,bai damu da yanayin datake ciki na tsorata ba yasake daka mata tsawa yace"zoki fice nace"


cikin 6acin rai shima Ashraf yace"Mawahib karki fita"


Cikin sauri Captain Aryan ya'iyo kanta gadan-gadan,cikin sauri  tayi gudu ta6uya a bayan Yaya Ashraf,ganin Captain Aryan yana tattare hannun rigar sa hakan yasa Ashraf yasaka hannu zai kareta,Mawahib kuwa tana ganin Yaya Ashraf ya tareta tayi qasa tarage tsawon ta, tafice da gudu daga dakin.


Cikin 6acin rai Ashraf yace"wai dan Allah menene damuwar kane da yarinyar nan? Aaka kawai yarinya tana walwalarta harka tsorata ta kasa tafita babu nutsuwa"


Captain Aryan yana jinsa ya shareshi, Ashraf yaci gaba da fadin "meta tsare ma? haka kawai kasaka yar mutane agaba bakada buri wanda yafi ka zalunceta?"


Cikin 6acin rai Captain Aryan yace"wai Ashraf saboda wannan abar kakemin masifa?kanamin masifa saboda ita kamar wanda ka haifeni?"


Lokaci daya jikin Ashraf din yayi sanyi,koda suke fadansu saide akan abinda ya shafesu,amma basa fada saboda wani, bazaka ta6a Jin kansuba inde akan wani ne,saide akan abinda ya shafesu su biyu,to yanzu kuma ga Mawahib tana nema tashiga tsakani, cikin damuwa yasaka hannunsa yadafe goshinsa(🤦🏻‍♂️)


Sannan ya kalli Captain Aryan yace"meyasa naga kamar kana cikin damuwa ne?,meyake damunka?"


Cikin damuwa Captain Aryan yace"no,babu abinda yake damuna,kawai de banajin dadin yanda yarinyar nan take nema tashiga tsakanina dakai,kadena son abinda nakeso saboda ita,banajin dadin zaman,gara in tafi "


Cikin sauri Ashraf yace" babu inda zakaje"


sannan yakama hannunsa suka zauna abakin gado,ya Kalle shi yace"inajin wani iri wannan zuwan naka Aryan,may be idan katafi sainayi rashin lafiya kamar yanda nasaba,kokuma kai kayi"


Captain Aryan yace"kadena tunanin komai,babu abinda zai faru insha Allah,bani kad'ai nazo ba,akwai yaran dasuke tare dani,yakamata inkoma next time idan nazo nikad'ai saina huta sosai"


Cikin sanyin jiki Ashraf yace"to Allah yasa,yau ba muje wajan Anty Mamy ba"


Captain Aryan ya yatsina fuskar sa yace"inason ganin Anty Ma-my, but banason ganin wannan yarinyar..."


Ashraf yalumshe idonsa ya bude tareda girgiza kansa baice komai ba. 


Haka suka wuni a daki babu inda suka fita,saide suje sallah sudawo,Captain Aryan baya gajiya da zance inde tareda Ashraf ne,suyi fada su shirya kansu da kansu babu wanda yajisu. 


Da daddare suna kwance sunyi shirin bacci Captain Aryan yadauki wayarsa yakamo wani hadadden gida gari guda kamar ba'a qasar yake ba,yabawa Ashraf wayar yace"Ash kaga aikin gidan nan har sun gamashi,ansaka komai aciki,wannan komawar da zanyi a cikinsa zan sauka,matata ma nasa sun saka mata komai da komai kawai clothes ne babu,shima dan bansan size dinta bane danayi mata order ansaka mata kafin tashigo gidan, but....naso ace tareda ita zamu fara shiga"


Ashraf ya kalli photunan gidan yace"Wow...,gaskiya yayi kyau,banbancin sa da nawa na nan garin kadanne,naka farin fenti nawa brown,to amma kayi auren mana saika tafi da matarka kushiga tare tunda haka kakeso"


Captain Aryan ya girgiza kansa kawai sannan ya basar da zancen alamun bayaso,yace"nima kayan ciki har windows din duka brown ne,yayi kyau sosai,inaso wannan shekarar gaba daya yan gidannan sutafi aikin hajji,daga nan kawai saika taho muje muyi zamanmu a gidan muhuta kafin su dawo" 


Cikin farinciki Ashraf yace"babu damuwa Allah yakaimu,sannan bazaka samu lada kai kadai ba,kai kabiyawa su Daddy nikuma su Momy,sannan gaskiya ni bazan tare agidana yanzu ba,saina jira na auri Mawahib tukunna,sai mu koma tare rana daya,duk wasu yan'uwa zan basu sati daya sugama zuwa ganin amarya, daga nan kuma zan rufe gidan in fara amarci na hankali na kwance"


Cikin yatsina fuska Captain Aryan yace"mekace? kayi aure kuma kana kallon amaryar har tsawon sati daya?kayi aure bakayi komai ba a wannan ranar saika ce wani kidahumi?"


Ashraf yace"menene yakawo maganar kidahumi kuma Aryan?,kana nufin kai bazaka Iya jiran sati daya ba kenan? kaide matarka taga ta kanta wallahi,zan fadawa Daddy yayima aure" 


Cikin rashin damuwa Captain Aryan yace"gaskiya kam,because nide babu wasa,cikin kwana biyu ma zan'iya  yimata ciki"


Ashraf yanajin haka yakai masa dukan wasa,yariqe kunnansa yace"bakajin magana Aryan"


Dahaka sukai addu'ah suka kwanta cikin farinciki. 


Washegari yahada kayansa tsaf zaikoma bakin aikinsa,jikin Ashraf duk yayi sanyi,kokadan bayason tafiyar Aryan din baisan meyasaba,saida sukayi sallama da Hajiya Kilishi,bayan ya ajiye mata wasu manyan kudade a gabanta, sannan sukaje yayiwa Mama Sadiya sallama,itama ya ajiye mata kudi masu yawa akan kujera, sannan suka d'unguma suka tafi part din Mamy.



Suna shiga part din Mamy suka tarar da'ita tareda wata baquwa, babbar mace ce sosai tana zaune akan kujera da wayarta a hannunta tana dannawa, Cikin farinciki Mamy tace"Captain har tafiyar tatashi?"


Captain Aryan yayi murmushi ya kalli  agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa,yace"Anty Ma-my barka da safiya"


Ta amsa masa cikin girmamawa tareda shige wa dan qaramin kitchen din dake falon ta. 


 Ashraf ya kalli babbar matar dake zaune afalo yace"ina kwana"


Cikin walwala tadago kanta tace"lafiya kalau yagida"


Kafin Ashraf yabata amsa shima Captain Aryan cikin sauri ya rissina yace mata "Barka da safiya"


Ta kalleshi tace"masha Allah,yawwa sannunku"


Adede lokacin Mamy tafuto daga kitchen hannunta daukeda leda,tabawa Captain Aryan tace"ga dambun kaza"



Ya kalli ledar hannunta cikin shagwa6a yace"haba Anty Ma-my, gaskiya ni bazan tafi dashi a leda ba,saikace wani marar gata,Allah nide saide ki sauya min,haba Anty Ma-my kina d'an girmama ni mana,amma haka abu aleda?"

ya qarasa maganar cikin shagwa6a kamar zai fashe da kuka.


Mamy tace"naqi,bazan sauya maba, kaje kayi aure sai matarka ta dinga saka maka a flask"


Captain Aryan yayi shiru yana kallon wannan leda,duk girmansa Anty Mamy bazata sake girmama shi tazuba masa a qayataccen food flask ba?bai Isa yayi magana ba komai sai tace yaje yayi aure(😔) 


Ashraf yayi murmushi yazuba musu ido yana kallon wannan drama tasu, adede lokacin Mawahib tafuto daga dakinta tana sanye cikin riga da siket 'yan kanti, amma tasaka mayafi a jikinta, ganinsu yaya Captain a falon yasa taja ta tsaya daga nan bakin qofar d'akinta. 


Ashraf yana ganin futowar ta yamaida kallonsa gareta,yazuba mata manyan idonsa yana kallonta cikeda so. 



Qawar Mamy dake zaune agefe tana ganin abinda yake faruwa tayi dariya tace"Maryam wannan kamar yaran nan naki dakika yayesu ko?"


Cikin sauri Captain Aryan yajuya yana sake kallon matar, tunda yaji tana maganar lokacin da Anty Mamy ta yayesu yasan cewa tabbas babbar mace ce,kuma tasan yarintar su,yagama qarewa matar kallo kenan yajuyo zai maida kallonsa wajan Mamy anan idonsa yasauka akan Mawahib,sai akayi dace idonsa ya sauka cikin nata qwayar idon,lokaci daya bugun zuciyar su yasauya,cikin sauri kowa ya janye idonsa.


Mamy tayi murmushi tace"Sister Hadiza sune wallahi, gasunan duk sun girma"


Babbar matar da aka kira da Sister Hadiza tace"ikon Allah,kinga duk sun girma sun taroki kamar wasu qannanki, waye kwa me tsoron ruwan zafi acikinsu lokacin da aka musu kaciya?"(🙊🙈😂🙆🏻‍♀️)


Mawahib ta dago kanta da sauri ta kalli Sister Hadiza.


Cikin sauri Captain Aryan ya runtse idonsa, saboda yasan akansa ake maganar, shitake tambaya, yatuna Mawahib fa tana cikin falon nan,shikkenan matar nan tagama dashi,ta kunyata shi agaban wannan yarinyar, cikin sauri yafuto daga falon da ledar dambun kazansa a hannu yanaji kamar ya nutse awajan dan kunya(😂)


Ashraf yayi dariya shima yabi bayansa












(Sister Hadiza baki kyauta mana ba🤣   asauka lafiya captain 🙏🏻)





Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼


Zaki turo 500 ta wannan account din


0164549488

Amina muhammad

GTbank


Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034


Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034








Amnah El Yaqoub✍🏻

No comments

Powered by Blogger.