Idon Naira 6

 *_ID


ON NAIRA_*

_Arewabooks@Mamuhgee_

_ZAFAFA BIYAR 2023_


6


_ASSALAMU ALAIKUM JAMA’AR KWARAI.. JAMA’AR AMANA… JAMA’AR ZAFAFA… MASOYA KUMA MABIYA MASU ALHERIN SAYAN ZAFAFA A KODA YAUSHE BA GAJIYAWA…GODIA MAI TARIN DIMBIN ALBARKA DA FATAN ALKHAIRI AGARE KU.._


_KUNSAN DUK INDA ABUBUWAN ARZUKA SUKE MUNA SHIGA MU KURDA MU NEMO MUKU SU DOMIN JIN DADIN KU..🥰💕SABODA KU DIN NA GABAN GOSHINAN MU NE._


_TAMKAR KO DA YAUSHE.. YAU MA MUNZO MUKU DA WATA TSARABAR.. TSARABAR DUNIYAR KAYAN KITCHEN, DECORATIONS DA SAURAN SU… KU MARMATSO KU JI…_


*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*


_KUN GANI KO? TO INA AMAREN? INA UWAYEN GIDAH INA YAMMATAN DA KE SHIRYE SHIRYEN SHIGA DAGA CIKI? INDA ZAKU JE KU KANKARO MUTUNCI KU DANDALO ARZIKI NA KECE RAINI.. INDA ZAKU WUCE RENI DA GANIN KASKANCI..INA MAZAN DA KE BURIN FARANTAWA MATAN SU DA ‘YAYAN SU DA KANNEN SU? _


_MAAB LUXURY HOME: RIGIJI GABJIN KENAN! WOHOHO WANI KAYA SAI AMALE KAN DAUKA.. MAAB LUXURY HOME : ALJANNAR KAYAN KITCHEN KENAN, INDE AKACE KAT TOH KARSHEN MAGANA TA KARE KENAN.. MAAB LUXURY HOME ; A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY KITCHEN UTENSILS, HOME DECORATIONS AND MUCH MORE_


_ADIRESHIN MU: MUNA KAN TITIN AHMADU BELLO WAY, KANO STATE. ZAKUGA TAMBARIN DA MAAB LUXURY HOME.._


_DAN SAUKAKA MAKU FITA ZUWA SHAGON MU. ZAKU IYA ORDER AKAWO MUKU DUKKANIN INDA KUKE A FADIN NIJERIYA DA KETARE. _


_INSTAGRAM: @maabluxuryhome._


_FACEBOOK: @maabluxuryhome._


_KO KU NEME MU TA LAMBAR TARHON MU: 08034631010_


_KYAU! INGANCI! RAHUSA! ADADE ANA AMFANI DA SHI SAI KAYAN: MAAB LUXURY HOME_


_100% TESTED AND TRUSTED😍☑️_

______


*********

Kokarin janta ajikinsu Alh Asad yafara sbd tasake dasu kaman Yan uwanta Kuma kamar iyayenta musamman Haj maryamah din wadda ita kadaice tata hakama matuqar Basu fara sabuwa da junaba har kauna tashigo ciki tabbas duk ranarda Zainab din tayi aure zumunci da alaqar yankewa zaiyi kwata kwata har gwara yanzu da akwai Aqeel a tsakiya Wanda ya tabbatarda ko sunyi rabuwar aqalar bazata taba rabuwa Dan kuwa Shi agurinsa su biyun iyayensa Babu abinda zaisa ya zaba daya yabar daya idan ya girma.


Duk yanda Alh Asad din yaso ganin sun fara rabar Hadi da Yar sabo da juna hakan bai samuba saima shi data Dan fara sabuwa dashi Tana qara ganin tsananin girmansa Tunda shike janta ajiki da kulawa da kokarin kyautatawa.


Maryamah na lure Amma tayi kaman Bata San meyake faruwaba sbd tasan abinda Alh Asad din yeke tunani bamai yiyuwa bane lokaci daya 

Idanma zai yiyu din kenan Dan kuwa sun riga sunyiwa juna wata nisa da tazara Mai girma da bazasu taba sabawa ko shakuwa da kaunar junaba lokaci 

Dan haka ta tattara ta sake maida hankali kan aikinta tareda kokarin mantar da shi zancen kwata kwata ta hayar kulawa da tarairayarsa,...ta manta da tarairayar 'dan data Haifa Wanda takasa tsayawa ta tarairaya.


Babban mummanan lamarin daya samesu shine rasuwar Alh Asad kwatsam ba tsammani.


Tafiyar kwanaki biyar ce ta kamasa zuwa daya daga cikin manyan kamfunins na shinkafa dake Lagos,


Ranar dazai tafi har Rana Yana tareda Dansa Aqeel a palonsa Yana jansa da fira cikin tsananin kauna da kulawa har saida Zainab takawo Masa abincin Rana ta jera a kan dining yaci tareda Aqeel din kafin ya kirata tazo ta tafi da Aqeel din shikuma ya wuce tareda Maryamah data dawo Dan kaisa airport din da kanta.


Bayan tafiyarsa Hakanan daga ita har Aqeel suka koma sanyi sanyi dasu karshe dai shi Aqeel din harsaida ya kwanta zazzabi Mai karfi na kwana biyu kafin yasamu sauki a ranarda Alh Asad din yacika kwanaki biyar cif da tafiya ya dawo Amma saiya sauka Maiduguri sukai wani daurin aure daga can motacin Sauran Aminansa  dasuke tareda securities ya biyo zuwa dawowa gida a hanya suka samu mummanan accident din daya dauki rayuwarsa.



Zainab da ke riƙe da AQEEL sun iso cikin falon ne daidai da lokacin da Maryamah ta zube a ƙasa da waya a  hannunta batareda tagama sauraron bayaninda Alh Yusuf qanin Mahaifiyaru Alh Asad yake Mata ba Dan kuwa zancensa na farko tuni ya nauke numfashinta daga fitowa ta zube qasa a some.


Da wani irin gudu Zainab ta isa gareta tana jijjigata da hannu ɗaya, ɗaya hannun Kuma ta kasa sakin Aqeel dayake kallon mahaifiyarsa jikinsa a matuqar mace Dan kuwa har lokacin lafiyar Bata Gama dawo masaba.



Zainab ganin lamarin ya girmama yasata tashi da gudu ta dauko ruwa a fridge tadawo Tana tsoro da shakkar zubawa Antyn tata Amma Kuma batada zabi sbd Maryamah din kamar bama wani sauran Rai a jikinta Dan haka jiki na rawa ta zuba Mata ruwan.


 Wani tunani ne ya haska cikin kan Zainab na cewa ko Umma ne aka bugo waya ta rasu?

 Mummanan faɗuwa kirjinta yayi take ta sake shiga firgicin dayafi na farko sbd idan umma ta rasu ita shikenan batada Wanda zai tsaya Mata a rayuwa Koda kuwa Babu so Babu kulawa kamar umma.


Ba shiri ta sakewa Maryamah ragowar ruwan da ke hannunta Tana kallonta hannuwanta na rawa batama San tafara tambayar Maryamah din waye ya rasu ba.


Babban masifar data sake rikita Zainab shine rashin farfadowar maryamah Dan haka suka kwasheta hankali tashe sai asibiti.


A asibitinma saida suka dauki lokaci kafin ta farfado cikin tsananin kuka da tashiin hankali Mai ban tausayi,


Zainab sai alokacin tasan waye ya rasu take itama jikinta ya sake daukan rawa da firgici sbd Bata kawo mutuwar a kansaba....


Innalillahi Wainnah IlayhirRaju'un..."


 Shine abinda tahau maimaitawa tanajin tashin hankalinta na qaruwa da tausayin Aqeel daya zama maraya kamar ita duk da shi yanada sauran gatansa sosai.


Washe gari har aka gama haɗa gawar MUHAMMAD ASADULLAH bisa jagorancin ƴan uwansa da suka samu isowa tare da abokan arziƙinsa Maryamah na can gadon asibiti ita da umma data taso tun jiya ta iso gabanin asubar yau 

Zainab Kuma Dole Takoma gida sbd gidan a hannunta yake matuqar masu gidan basa Nan gakuma Aqeel da zazzabinsa ya dawo Wanda kowa ya tabbatarda na rashin mahaifinsa ne da yayi.


An Gama komai maryamah da ake jira suka dawo daga asibiti ko tafiya da kanta Bata iyayi riqe ake da ita sbd mummanan jiri dake dibarta ga wata irin firgicewa datai a kwana dayan Dan kuwa bakinta Kansa ya bushe ko yawu daqyar take iya nemowa a bakinta ta hadiye.


Dawowarta kuka ya dawo sabo acikin gidan dake cike sosai da mutane Yan uwan Asadullah din na nesa da kusa duk sun halarto cikin baqin ciki da alhinin wannan mummanan rashin daya samesu.


An yi masa sallah an kuma kaisa gidansa na gaskiya ya samu ɗinbin mutane da kyakkyawar sheda daga gurin mutane musamman malaman addini sunata yabonsa sbd mutum ne Mai tsananin son Addininsa.


Maryamah kuwa dai tana cikin matsanancin hali na ɗimuwa da firgicin babban rashin nagartaccen miji kuma uban ɗanta ƙwaya ɗaya jal 


Addu'a kawai ake mata tana sha ana tofa mata sbd lamarin ya tabata sosai Dan kuwa daga baya har asibiti ake tunanin fara kaita idan ba harda kanta rasuwar ta taba ba.



 Zainab kuwa wani babban al'amarine ya risketa na zaman karban gaisuwar Dan kuwa kusan a tsaitsaye tagama figewa tas Takoma kamar Yar qaramar fatalwa sbd wahala da nata tashin hankalin na rasuwar Wanda shine takewa kallon gatanta a gaba Amma shima ta rasashi Dan haka kukanma kasawa tayi sbd nauyi da dacin da zuciyarta take dabaibaye dashi koina,


Abincin datake dafawa na zaman yafi qarfin duk wani kokari da iya wahalarta Dan kuwa duk masu taimakawa gurin aikin ba wani aikin arziki sukeyiba kusan duk itace qarfin aikin aikuwa take cikin kwanaki qalilan ta fice hayyacinta 

Ga kula da Aqeel Wanda shima jikin yakeji Kuma yaqi aminta da kowa ya kula dashi sai ita Dan haka duk tabi ta qarasa haukacewa gwanin tausayi.


Haka aka gama kwanakin zaman karban gaisuwar har rasuwar tayi sati biyar kusan koyaushe basa rasa Yan zuwa gaisuwar.


Kwanakin da suka biyo bayan rasuwar Alh Asad sun kasance kwanaki mafiya ƙunci da soya zuciya a wajen Maryamah da ma duk wani me ƙaunarta don ta yi kwanakin ne cikin tsananin ruɗani da ficewar hayyaci sabida bada wasa ba soyayyar mijinta ta gama rarike zuciyarta baki ɗaya gashi Aqeel danta datake kallon Asad acikin Sam yakasa rabarta kokuma kaunarta yanda yake kaunar wadda renonsa kawai takeyi duk sai tasake susucewa Takoma kamar wata bebiya ko yawan magana bataso kullum shiru take batason hayaniya.



*********


A hankali kwanaki sukai ta shurawa suna bada watanni cikin aminci da yardar Ubangiji Maryamah ta gama takaba

A hankali aka fara tattara duk wasu kadarori da marigayin ya mallaka kama daga kan kamfanoni da gidaje zuwa zunzurutun kuɗaɗe da ya tara aka raba gadonsa Wanda kusan 'dansa Aqeel shine da mafi yawan gadonsa sai mahaifiyar Alh Asad din da matarsa maryamah sai ya kasance kusan komai na tarin dukiyarsa Mai yawa a hannun maryamah yaje Dan kuwa itama sai dataji tsoron dukiyar da 'dan ya gada harma da nata Jason


 Hakan ya sanya wasu daga cikin ƴan uwansa suka fara jin haushin Maryamah din musammam dasuka nuna zasu karba Aqeel din su rikesa Tunda ita Cameroon zata koma gurin mahaifiyarta...



Babban rikici tayi da Yan uwan nasa akan 'danta Aqeel Wanda qarshe ta yanke shawarar Babu inda zata tafi  zata zauna ta tarbiyantar da 'dan takuma kula da dukiyarsa.


Da wannan aka kashe zancen Wanda kusan har kotu ake Dan kawai suna son karbe yaron.


Sun saka Mata ido sosai tareda sharadin idan ta almubanzarar da dukiyarsa da tarbiyarsa zasu karbesa har abada bazasu Bata Shiba.


 

Wannan rigimar itace babban qalubalen daya fara samun rayuwar maryamah Wanda kusan tashin hankalinta sabo yadawo Dan kuwa tasan badan Allah sukeson karban Aqeel dinba su rabata dashi sai Dan kawai su cinye dukiyar da mijinta yayi wahalar Tarawa iyalinsa karshe 'danta yayi wulaqantacciyar rayuwa.



Wannan qalubalen shine yafara juya rayuwar maryamah datayi alqawari tareda sadaukar da kanta gurin tsare haqqinta Dana 'danta Dan kuwa bazata Bari 'danta yayi wulaqantacciyar rayuwaba indai har Allah yabarta da ranta da lafiyarta da ikonsa insha Allah zatayi yaqi ta kare haqqinsu. 




*****Ahankali Maryamah tafara yawon duk garuruwa da inda dukiyarsu take Tana duddubawa da kanta sai personal assistant dinta da aka kawo Mata Dan kuwa dukiya ake magana a manyan gurare...


Tun lamarin na zuwar Mata da sauki har kanta yafara neman bugawa sbd Takoma ko sati hudu Bata iyayi a gidanta kullum Tana hanya a mota ko a jirgi musamman Lagos Wanda kusan can cibiyar kasuwancin Alh Asad din yake sbd acan yayi karatu Kuma yayi rayuwa.


Duk yanda take tsananin so da kaunar  'danta Aqeel haka tanaji Tana gani ta hakura tabarwa Zainab shi Dan kuwa Shi Kansa Bata ganin kaunarta a idonsa irin yanda yakewa Zainab...


Zainab itace tasan ciwonsa,.

Itace tasan lafiyarsa,

Itace tasan damuwa da quncinsa,

Itace tasan wankansa da kashinsa da fitsari tun Yana jaririnsa har zuwa lokacin,


Dararraku marasa adadi Zainab ce take kwana zaune Tana fama da kukansa da ciwonsa,


Tunda aka haifesa Zainab ta rasa barcinta na dare da lokacinta sai nasa,


Batayi aureba bare tasan Yaya daukar cikin yake Amma takai stage dinda zata daki kirji ta sanar cewa daukar cikin da haihuwa ne kawai bataiba Amma Babu abinda kowace uwa zata nuna Mata akan rainon 'da tun Yana zaninsa har girmansa.


Tayi bautar mahaifiyar maryamah,

Tayi ta maryamah da mijinta

Yanzuma gashi tanayin ta 'danta Wanda shi tasa bautar ta yarda ta sadaukar da rayuwarta agurin wahalta Masa har tsufanta sbd tsananin son datakewa Aqeel din jinsa takeyi tamkar 'dan data Haifa jininta.


Ba Aqeel kawai maryamah tabarwa Zainab ba hatta gidanta Dan kuwa kusan komai a hannun Zainab yake na kula da komai Amma a fannin wahala sbd kusan wani nauyi ne dayafi qarfinta aka Dora Mata.


Bata taba saurayi ko wani Wanda zai ganta yayi shaawar aurenta ko soyayya da ita sbd Bata wani fita tamkar a prison take Idan ta fita ko dai wani aikin wahalar aka aiketa taje tayi.


Aqeel karatunsa yafara nisa Dan kuwa  yagama primary js 1 zaije,


Zainab kuwa tuni tafara wuce tsarin 'yan Mata budurwai sbd shekarunta dasuke gaba da baya ba Amma Babu wani cigaban dayazo Mata koda na barin bautane saima abubuwan dake sake cabewa rayuwarta Dan yanzu maryamah Sam Bata zama tayi dedicating rayuwarta itama gurin aikinta Dan kuwa  yanzu tazama babbar mace Haj MARYAMAH ADAM ASADULLAH.


Aqeel bai taba Jin kaunar Mamin tasa (Zainab) ta ragu a ransaba duk girman dayakeyi.


Kullum shaquwa da kaunarta yake qatawa tareda dibbin tausayinta,


Tun baiyi girmaba lokuta da Dama idan yaga yada take figewa Tana fita hayyacinta agurin aikin wahalar gidan kullum alqawarinsa akanta shine"


"Mami idan na girma nayi Miki Alqawarin zan daukeki daga Nan na Gina Miki babban gida da mota da komaima da kikeso"


Murmushi kawai takeyi Mai ciwo aduk lokacinda ya fada Mata Hakan sbd batasan me kaddararsu ta tanadar musu a gaba ba Amma Zataso hakan ace Aqeel dinta ya girma suna tare,taga aurensa da 'yayansa Dan ba lallai ita tanada nata rabon 'yayanba da zataga nasu auren da yayan.


 


Haj maryamah Bata taba zaunawa ta duba wautar datakewa kanta da rayuwarsu itada 'danta ba,


Takasa zaunawa taja yaronta ajiki,

Ta kaunacesa,

Ta rungumesa tayi fira dashi,

Taji Yaya rayuwarsa take..


Shin meyasa ba shaquwa da kauna tsakaninsa da ita tabarwa Zainab komai nasa Wanda hakan yasa Zainab tamaye gurbin uwa agaresa batareda dukkaninsu sun Ankara da hakan ba.



Kwata kwata Hankalinta a kwance ya ke akan ɗan ta AQEEL din don zuwa yanzu ta gama yarda cewa duk duniya Babu Wanda zai iya so da kaunarsa da kulawa dashi sai Zainab

Wanda su Zainab da 'danta Aqeel din har mantawa sukeyi da Bayan junansu sunada wasu 'yan uwan ko mahaifiyar.

##MAMUH#

#FAMILY#SISTERS#LOVE#ROMANCE

#AMAL IDON NERA# HAJ ZAINAB IDON NERA.




*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*🔥

Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*🔥

Billyn Abdul


*IDON NERA*🔥

Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*🔥

Safiya huguma


*KI KULANI*🔥

Miss xoxo


Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171

Maryam sani

Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*Thanks for choosing us*🔥

No comments

Powered by Blogger.