Gidan Aro 16

 


*16*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*

Suna ficewa daga lungun Alhaji Isyaku ya mik’a ma Aminu hannu saka tafa yana sakin muguwar dariya. 


“Kai Aminu naji dad’in yanda ka masu barazana, na tabbata yanzu basuda yanda zasuyi face su amince dani.”


Aminu ya dafe kud’ad’ensa yana k’irgasu yake fad’in “Toh kai d’in ai bana wasa bane Alhaji. Na gode K’warai. Idan kanaso na koma gobe ma zan koma na kuma masu barazana.” 


Alhaji Iskyaku ya kuma aza babbar riga yana sakin dariya “Aminu Aminu.. Ai bayan abinda ya faru yanzu dole zasu amince dani dan idan ba haka ba basuda mahalli, kaga basuda sauran zab’in da ya wuce su amince dani.” 


Suka kuma k’ek’yata dariya Aminu na kuma godiya, nan yai sallama da Alhaji Isyaku ya wuce.


**


Tinda Inne ta tura k’ofar d’akin gaban Ajidde ke yankewa, batasan mai zata gani cikin d’akin ba amma kam zuciyarta ya tsananta bugawa. Bugun zuciyarta ya k’aru sanda Ta hango matar dake kwance saman gado idanunta a lumshe. Sumarta da yake tamkar na Indians ya rufe b’angaren fuskarta. Fuskar nata yayi fayau irinta marassa lafiya. Dan koda gani ba wata fara bace can tsananin Jinya  ne ya sanya fuskar nata yin fari. Saidai ga dukkan alamu tanada Yalwan suma irin mai tsananin tsantsin nan.. Ajidde taci gaba da takowa a hankali tana jin zuciyarta na wani irin fuzga tana duban matar. Kyallu tasha kwantar da majinyata a gidanta tana masu magani da rawan Bori wanda akasari mutuwa suke amma ko kusa bata tab’a karo da matar da ganinta ya mugun raunana zuciyarta irin wannan matar ba. Taci gaba da takowa zuwa gadon da matar ke kwance bisa.


Inne na hankalce da ita har ta k’araso.

Ganin ta zubawa Aunty Nuratu idanu Ta kasa janye idanunta yasa Inne gyaran murya ta soma fad’in “Shekaru goma sha biyar kenan tana kwance haka. An gwada magunguna da dama, anje k’asashe da dama amma babu wani abinda yake canzawa haka za’a hak’ura a dawo da Ita.. Mun yanke shawarin dawowa gida ko Allah zaisa a dace.”


Ajidde tasa hannu Ta share hawayen da taji na ziraro mata.


Inne ta kuma dubanta tace “Ban tambayeki ba. Ya sunanki.?”


Ajidde ta d’ago tana duban Inne “Suanana Ajidde.”


“Ajidde.” Inne ta nanata, sai kuma ta saki murmushi tace “Ina fata maganinki ya mana aiki Ajidde.. Ina fata Ubangiji yasa mu dace da maganinki.. Allah ya nufa maganin Nuratu na cikin tafin hannunki.” 


Ajidde Ta d’ago manyan idanunta da suke farare k’al masu gauraye da hawaye tana duban Inne dasu. Bata iya furta komai ba Sai duk’awa da tai gaban gadon tana k’ok’arin bud’e jakan maganinta.


“Amm Hajiya ko zan d’an sami k’aramar kwano.?” Ajidde ta tambaya tana duban Inne.


Murmushi Inne Ta sakar mata Tace “Ki kirani da Inne kinji koh..”


Ajidde ta maida mata martanin murmushin tana mai jinjina kai tace “Toh Inne..”


Inne ta kuma murmusawa kafin ta bud’e murya tana kiran Hindu. 

Hindu ta shigo cikeda risinawa tana fad’in “Gani Inne.”


“Kije ki kawo mata kwano k’arama.”


“Toh Inne.” Hindu ta amsa tana mai ficewa.


Ajidde tai zuru tana jiran taga ko Inne zata fice amma bata fice ba, dik addu’an da take cikin zuciyarta matar ta fice daga d’akin domin ta gudanar da abinda Kyallu ta turota tayi amma tak’i ficewa. Har Hindu ta k’araso da k’aramar kwano ta mik’a ma Ajidde. Ajidde ta amsa tana mata godiya. Har lokacin dai Inne na zaune saman kujera mai kallon gadon Aunty Nuratun Ita kaw Ajidde tana zaune gaban gadon tana k’ok’ari ciro had’in maganin.. Wani ruwa cikin gora irin wanda ake fafewan nan ta ciro.. A hankali ta soma zuba ruwan cikin kwanon.. Saida ta ida zubawa kafin ta ciro had’in maganin tana tina bayanan yanda ake had’a maganin daki daki.. Tana ida had’a maganin ta rik’e cikin hannuwanta guda biyu tana duban matar dake kwance, hannayenta sai rawa suke, zuciyarta na wani irin tsinkewa.

‘Ke Ajidde kiyi k’ok’arin saita kanki idan ba so kike asirinki ya tonu ba.’ Ta fad’i haka cikin zuciyarta.

Ta d’an juyo ta dubi Inne wacce itama Ajidden take duba “Inn Inne nace Ko za’a d’an tallafa mun kanta zan bata magani."


Dai dai lokacin Mu’azzam yai sallama ya shigo, kayan training ne jikinsa, ga dukkan alamu daga morning jugging ya fito.


A tare Inne da Ajidde suka dubi mai sallaman. Zuciyar Ajidde yai wani irin yankewa, k’iris ya rage bata tintsirar da ruwan maganin dake rik’e cikin hannunta ba, dikda ba da wannan shigar ta gansa ba fuskarsa bai b’ace mata ba, tana tuno sanda ya nunata da bindiga daga yanda yake a saman bishiya. 


Gaisawa Mu’azzam yake da Inne amma Ajidde bata janye idanunta daga dubansa ba. Har saida Inne tace “Yauwa Modibbo na tinda ka shigo sai ka taimaka mata ta bawa Nuratu maganinta dama zan kira Hindu ne tinda ni banida k’arfin d’agata amma tinda ka shigo sai ka taimaka mata.” 


Mu’azzam ya juyo yana duban yarinyar da zata bawa mahaifiyarsa magani, K’uri yai mata yana so ya d’ago a ina yasan fuskar tata.. Taso ta masa kamanni da fuskar da ya sani amma ya kasa tuna ina yasan fuskar. Haka kurum yanayinta yai masa Zubi dana criminals abinka da wanda ya saba cin karo da masu laifi.. Shi bama wannan ba mamaki yake Wai wannan k’aramar yarinyar ce zata bawa Maminsa magani..? Jiyo muryar Inne da yai tana fad’in ya tallafo kan mahaifiyarsa a bata magani kar lokaci ya k’ure ya dawo dashi daga duniyar tinanin da ya tafi. A hankali yake takowa har ya iso kusan Ajidde.. Ajidde dai sai kauda fuskarta take alamun bataso mutumin nan ya ganeta.

Idanunsa naga Ajidde yake k’ok’arin tallafo kan mahaifiyarsa. Dik iya tinaninsa dan ya tina a ina yasan wannan fuskar ya kasa.


Maidoda dubansa ga mahaifiyarsa yai yana k’ok’arin d’ago kanta. Ajidde sai rawa hannunta yake tana k’ok’arin kai kwanon kusan bakin Aunty Nuratu.


“Dakata.!” Ya fad’i yana duban ruwan maganin da yake bak’ik’irin.


Cak Ajidde ta tsaya zuciyarta naci gaba da tsinkewa.


“Wannan ruwan za’a bata.?” Ya tambaya yana kuma duban ruwan.


Inne tai karaf tace “Maganin kenan za’a bata. Kasan had’e had’e ne.”


“But Inne wannan zai iya cutar da lafiyarta dan bamusan da mai da mai aka had’a ba.. Sannan wannan yarinyar itace mai maganin dama.?”


Inne ta sauk’e ajiyan zuciya tace “Banda abinka Modibbo jinjiri ma ai sai ya baka magani kuma a dace idan Allah ya nufa. Karka damu da yanayin wanda zai baka magani kawai kai add’uan dacewa.. Mudai fatanmu shine Allah yasa a dace.”


Ya jinjina kai a hankali yana mai maidoda dubansa ga ruwan maganin.


Idanun Ajidde naga hannayen Mu’azzam da ya tallafi mahaifiyarsa wanda suke fresh dasu. Ta kasa janye idanu daga duban yatsun hannunsa da suke dogaye tamkar dai yanda yake da tsayi... Tsaban kallon yatsun hannayensa da take k’iris ya rage bata d’urawa Mamy magani a hanci ba. Mu’azzam yai caraf ya rik’e hannun nata wanda ke k’ok’arin Kai magani hancin mahaifiyarsa.. Jin hannunsa saman nata ya sanyata d’agowa a zabure tana dubansa zuciyarta na wani irin yankewa.


Shiko yasha mur sosai yake dubanta “Concentrate.. Ki kula..” Ya fad’i fuska babu walwala.


Ajidde ta jinjina masa kai amma jin bai sakar mata hannu ba ya sanyata kai idanunta ga hannayen nasu.. Sai sannan shima ya dubi yanda take kallo. A hankali ya sakar mata hanunta kafin ya kuma tallafe kan Mamy sosai..

Wane irin nannauyan ajiyan zuciya Ajidde ta sauk’e kafin ta soma k’ok’arin bawa Mamy maganin, a daidai sanda ta kawo maganin dai dai saitin bakinta tana jin sanda Mu’azzam ya furta Basmala a hankali. Batasan dalili ba amma taji wani irin natsuwa na sauk’o mata a lokacin da yake ambaton Allah.


A haka Ajidde ke bata maganin, rabi na shiga bakinta rabi na zubowa jikinta. Inne ta taso ta gyara mata napkin d’in dake d’aure wuyanta har saida Ajidde ta ida bata ruwan maganin kafin Mu’azzam ya maida kanta ya kwantar, ya dafa goshinta da gumi ke tsartsafowa tin sanda aka soma bata maganin. A hankali ya share mata zufan yana mai kuma gyara mata kwanciyar. Ya jima yana duban fuskar mahaifiyar tasa yayinda Ajidde ke k’ok’arin tattare kayyaykinta.


“Allah baki lafiya Maami.” Ya fad’i yana maida mata sumarta cikin hulan da aka rufa mata.


Ajidde samun kanta tai tana mai furta “Ameen.”


Yai saurin dubanta dan yaji Ameen d’in data ce, ya soma k’ok’arin tino yanda yasan irin muryar amma nan ma shiru bai iya tuna komai ba. Ganin zai bawa kansa wahala babu dalili ya sanyasa mik’ewa yana duba agogon dake d’aure hannunsa na hagu. 


“Abinci fah ko sai zuwa anjima.?” Inne ta tambayesa cikeda kulawa.


“No sai zuwa anjima Inne, zanyi wanka yanzu dai.” Yana ida fad’in haka ya nufi k’ofa.


Inne ta jinjina kai tace a fito lafiya.


Ajidde kaw alla alla take ta gama abinda take ta fice daga gidan kafin wannan mutumin ya kamata dan ta lura sam bai d’auko kamanninta ba. Ta murmusa cikin zuciyarta tana fad’in ta Ina zai d’auko kamanninta bayan yau d’in gaba d’aya ta canza yanayi, yau d’in jan powder ta shafa Wanda ya k’ara ma bak’in fuskarta haske sannan bata cika kwalliya ba kad’an tayi kuma harda hijabi Ta saka ba kaman wancan ranan ba, gaba d’aya dai ta sauya yanayi yanda ba lallai a ganeta ba. Canza yanayi da kamanni dik na cikin d’abi’ar Ajidde tinda dama damfaran mutane Kyallu ke sanyata yi, mai Sana’a irin nata dole yanada dabaru na b’adda yanayi daban daban.. Ta kuma murmusawa tana fad’i cikin zuciyarta Wo ni Ajidde gaskiya na iya shashashantar da mutane tinda na shashantar da wannan k’aton.. Muryar Inne ta sinkayo tana fad’in “Ajidde idan kin gama da maganin nata sai kici abinci ko.. Hindu zata baki abinci.”


Ajidde ta girgiza kai tace “A’a Inne na gode, sauri nake akwai yanda zanje na kai magani.”


Inne tace “A’a ai kuwa dole zakici abinci dan ba’a zuwa gidan nan a fita ba’aci komai ba kinji koh.. Jirani a nan Ina zuwa.”


Ajidde ta jinjina kai tana murmusawa. Inne tana fita Ajidde ta mik’e tana k’are ma d’akin kallo.. Ya zama dole ta nemi abinda zata d’auka takaima Kyallu.. Saidai sam idanunta basu gane mata wani abinda zata d’auka ba. Sannan bata jin zata iya satar ma Kyallu wani abu a d’akin majinyaciya irin wannan.. Yanzu ya zatayi.? Bata isa ta koma ma Kyallu hannu banza ba dan Ta tabbata muddin ta koma mata haka a d’akin awakai zata kwana. Tana tsaka da tinanin ta hangi k’ofar d’akin a bud’e a hankali cikin sand’a ta fito daga d’akin. Doguwar corridor ta hanga da ya mik’e zuwa b’angaren hagu, ga wasu k’ofofin kana iya hangowa. Cikin sand’a Ajidde ta soma bin wad’annan k’ofofin.. Tana tafe ta hangi wata kaman bata ida rufuwa kirif ba. Ta Washe baki tana fad’i a hankali “Sa’arki tazo Ajidde.” Cikin sand’a ta isa jikin k’ofar tana turata a hankali. D’akin tas tas Sai k’amshin ‘yan gayun da take shak’a kaman dai yanda tace a cikin zuciyarta. Ta lumshe idanu tana shak’an k’amshin. “Kaji k’amshin Turawa.” Ta fad’i tana gyad’a kai. Ga kuma zuban ruwa tana jiyo daga wani wajen amma batasan daga ina bane. Kar dai ma ana kallanta.? Ta tambayi kanta cikin zuciyarta. Kafin takai ga nemo amsar tambayarta ta hangi wannan bak’ar jakan Ta mutumin nan data so masa sata dan sam bazata mance jakan ba, sannan shine mutumin da ya taimaka mata suka bama matar nan magani. Ajidde ta Washe baki tana fad’in “Jaka jin nace sai na sata ma Inna Kyallu abinda ke cikinki.. Watau yauma saida kika biyoni. Toh Bari dai muga Meye a cikinki.” Tana ida fad’in haka ta k’araso kusan jakan tana mamakin yau a bud’e ta sami jakan. Saidai k’arasowarta jikin jakan kenan taji an turo k’ofar d’akin an shigo. 


Cak Ajidde ta tsaya ba tareda ta iya juyowa ba, jikinta sai rawa yake. Ta nemi layar zana da kyallu ta bata ta rasa. Tana cikin dibi dibin ta sinkayo muryar mutumin da ya shigo d’akin yana fad’in “Who are you.? What are you doing in here.?”


A slow motion Ajidde ke juyowa. Musaddiq ya ware idanu yana duban yanda ta zaro k’wayar idanunta, dikda babu janbaki da jagiran data zana wancan lokaci tsaf ya ganeta dan bazai mance wannan k’wayar idanun nata masu tsananin haske da kyau  ba “You again.?” Ya furta yana nunata. 


Daidai lokacin aka soma tab’a k’ofar bathroom alamun mutumin dake ciki  zai fito.


Ajidde ta rikice ta rasa wanne zatai dan tuni Mu’azzam ya fito d’aureda towel, rufin asirin Allah hannunsa na rik’e da k’aramar yana goge fuskarsa zuwa sumarsa sam bai an kare ba balle ya gane da mutane cikin d’akin.


Cikin azama Musaddiq ya finciko hannun Ajidde da ta saki baki da hanci tana duban Mu’azzam ya turata cikin wardrobe.


K’aran rufe wardrobe Mu’azzam yaji ya d’ago fuskarsa yana duban Musaddiq dake tsaye wajen cikin wani irin yanayi na daburcewa.


“Hey are you with someone.? Ina wanka kaman naji murya..” Mu’azzam yace yana k’arasowa.


Musaddiq da gaba d’aya yake a rikice sabida Ajidde dake b’oye cikin wardrobe saurin girgiza kai yai yace “Me. A’a no.. Yanzu shigowarta.. Mu’azzam you need to come, wani mutumi ne naga ya dirk’o ta Katanga shine nazo kiranka.. You need to hurry kafin ya b’ace mana..”


Yanda duk yake a birkice yasa Mu’azzam zuba masa idanu yana karantarsa “Musaddiq will you calm down please..”


“Wane irin calm down kake magana. Inace maka b’arawo ne kaman naga ya shigo kana ce min calm down.. I know you’re a Corp shisa nazo wajenka direct.. Please you need to hurry..” Ya k’arashe yana mai janyo Mu’azzam d’in suka nufi k’ofa.


“Wait Musaddiq.. I need to get dressed first.” Mu’azzam ya dakatar dashi da fad’in haka.


Sai sannan Musaddiq ya tina towel ne jikin Mu’azzam d’in.


Mu’azzam ya d’an girgiza kai yana k’ok’arin nufan wardrobe.  

‘Oh shitt.. He can’t see her in there.’ Musaddiq ya fad’i cikin zuciyarsa. Kafin Mu’azzam d’in ya bud’e wardrobe d’in wanda tuni Ajidde dake dubansa ta d’an tsakanin da bai ida rufuwa ba ta sadak’ar kawai ya kamata dan har toshe bakinta tai ta rintse idanunta tana jiran mai afkuwa ya afku. Kwatsam Musaddiq ya k’araso ya damk’o hannunsa ya hanasa bud’e wardrobe d’in lokaci guda yake fad’in “Dan Allah kazo muje kar ya gudu.. Zo ka gansa ta window..” Ya k’arasa da Mu’azzam jikin window yana yaye curtains yake nuna masa “Look look duba tacan ka gani..”


Girgiza kai Mu’azzam yai cikeda k’osawa yace “Musaddiq I can’t see anything..”


“Ok wait muje wajen ka gani..”


Ya d’an fuzar da fuci hannayensa saman kunkumi “Bani jallabiyata cikin wardrobe I just hang it there.”


Cikin sauri Musaddiq ya jinjina kai yayinda Mu’azzam d’in ya d’an girgiza kai yana mai fuzar da fuci.


Musaddiq na bud’e wardrobe d’in sukai ido hud’u da Ajidde da k’iris ya rage bata saki fitsari ba dan tsoro.. Ya aika mata mugun kallo kafin ya zaro jallabiyar dake lank’aye jikin hanger. Ya maida wardrobe d’in ya rufe kafin ya kawo wa Mu’azzam jallabiyar ya zira. Lokaci guda Mu’azzam d’in ya nufi waje ba tareda ya kuma bi takan Musaddiq ba.. Mu’azzam na ficewa ya dawo ya bud’e Ajidde yace “Kina jina kar ki sake ya ganki dan idan ya kamaki kashinki ya bushe.” Cikin sauri Ajidde da tuni Ta had’a gumi take jinjina kai alamun taji. Sauri sauri ta fice ta nufi d’akin Aunty Nurah tana sauk’e nannuyan ajiyan zuciya.


Tana shiga ta tadda Hindu ta kawo mata abin kari. Hindu ta dubeta tace “Ina kika fito ga abin kari na kawo miki tuntuni..”


Murmushin yak’e Ajidde tai tace “Oh wllhi makewayi na fita inata nema ai.”


Hindu ta murmusa tace “Banda abinki Ajidde ai da tambaya kikayi muje na kaiki.”


Ajidde tai saurin girgiza kai tace “A’a ki barshi kawai ai yanzu ma zan tafi bana so nayi rana.”


Hindu Ta d’an tab’e baki tace “Toh shikenan.. Abincin fah..?”


Ajidde ta juya taga kayan dad’in da aka kawo mata. Sai kuma ta dubi Hindu tana wage baki alamun tanaso taci.

Hindu ta murmusa tace “Ki zauna kici abincinki kafin ki tafi..”


Aiko Hindu na ficewa Ajidde ta shiga yagan pepper soup d’in kaza tana turawa bakinta, hannu bibbiyu takeci kaman wanda za’a k’wace.. K’arshe bud’e jakarta tai tana tura sauran ciki. Kaman wacce ta tina wani abu sai kuma ta d’ago tana duban matar nan majinyaciya. A hankali ta k’arasa kanta ta tsaya gabanta “Na gode kinji. Ba don ke ba da bazan shigo gidan nan har naci dad’i irin haka ba.” Ta k’arashe tana wage baki. Lokaci guda ta mutsuke hannayenta jikinta ta sab’i Jakarta ta nufo k’ofa.

Sauri sauri ta fice tana lek’e tamkar maras gaskiya.


Koda Mu’azzam ya fice baiga alamun kowa ba baiga alamun komai ba gajeren tsaki yai yana girgiza kai yasan bazai wuce shak’iyancin Musaddiq bane suka motsa. Ya yanke shawarin tuntub’ar securities ko sunga wani abu suspicious.  Har zai nufa gate Musaddiq ya k’araso yana d’an haki alamun yayi gudu. 


Mu’azzam ya  dubesa yace “Are you sure kaga wani ya shigo.”


Sosa kansa yake yana duban Mu’azzam d’in “I think it’s just my imagination.” 


Kafesa da idanu Mu’azzam d’in yai yana karantarsa “Are you alright.?”


“Of course.. I’m absolutely fine, Inspector.”


Jinjina kai Mu’azzam yai yace “Lets go and ask the security men Ko sunga mutumin da ka gani..”


“No no no.. Nace maka Ina tunanin imagination d’ina ne.. Babu kowa.” Yai maganar yana d’an ciza lab’e bakinsa kad’an irinta masu laifi.


Takowa Mu’azzam yake zuwa gabansa yana mai tsaresa da idanu 

“Wait. Are you sure you’re not on drugs.?” Mu’azzam ya tambaya yana duban Musaddiq d’in.


“Kasan na daina tin ba yau ba.. kuma bazan k’ara komawa ruwa ba in sha Allah. Dik da ban maka alk’awari ba amma nace In sha Allah.”


Jinjina kai Mu’azzam yai yana mai kuma karantarsa ba tareda yace komai ba.


Daidai nan Jume ya k’araso suka gaisa da Mu’azzam kafin ya dubi Musaddiq yace ana nemansa a wajen aiki. A tare Musaddiq da Jume suka wuce yayinda Mu’azzam ya nufo cikin gida yana jin dad’in yanda Rayuwar d’an uwan nasa ya Inganta a gidan gonar cikin ikon Allah.


Can Ajidde ta hangosa zai shige, gabanta yai wani irin fad’uwa dan ba komai Ta tina ba sai ganinsa da tai d’aure da towel. Tai saurin rintse idanunta ga k’amshin wardrobe d’insa da ya kama illahirin jikinta. Koda ta rintse idanun ma shi take hangowa. Ta kuma bud’esu tana furta “Wayyo Ajidde shige shigen ki ya kaiki kika gano sa a haka.” Jikinta ta shiga shinshinawa tanajin k’amshin wardrobe d’insa da ya kasa barin jikinta. 

Muryar data sinkaya daga bayanta ya sanyata juyowa babu shiri.


Musaddiq ne ke tsaye bayanta ya tsareta da idanu. Ta ganesa shine mutumin da ya taimaketa ya sanyata cikin wardrobe. Kan kace mai ta duk’a saman gwiwoyinta ta d’ago hannu tana rok’onsa ya rufa mata asiri.


“Kin ganeni..?”


Tambayar da ya mata kenan.


Tai K’uri tana dubansa, sai kuma tai saurin girgiza kai alamun a’a


Yashin dake wajen ya d’iba cikin hannunsa ya kakkab’e had’ida shafa sauran saman fuskarsa. Take fuskarsa tai hazon k’ura.


Ajidde na zaro idanu waje tace “Kuran tashe.!”  Sai kuma ta soma dariya tana nunasa.




No comments

Powered by Blogger.