Daudar Gora Book 2 page 78


 Chapter 78


.....…..Bayan idar da sallar magrib dunbin al'ummar dake cikin masarautar ruman suka shaida daurin auren Zayyan ibn Abbas Jumna. Da amaryarsa Ammarah bint Abdul-majeed Aliy Qutb, akan sadaki mai darajar gaske, inda Kaka ya zama waliyyin ango, Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majee

d Aliy Qutb ya zama waliyyin amarya. Ba mutanen daular ruman bane kawai suka girgiza, masarautar ce gaba dayanta ta girgiza da wanna al'amari na bazata. Duk da ana cikin dunbin jimami na abubuwan da suka faru a kotu yau, babu wanda yay zato ko tsammanin faruwar abinda ya farun kamar haka ba. A take sabon topic ya sake barkewa a saman wanda dama aka yini anayi har

a cikin hadimai…





**




Tun bayan sallar la'asar da suka shigo da su Kaka bata koma ba tana a sashen nasa. Dan sanda zasu fita domin gabatar da sallar magrib har zata bisu itama Malikat Haseenat ta dakatar da ita. Kasancewar sallar magrib da ake kira ita da shi babu wanda yacema dan uwansa komai. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke a bayan fitarsa sallar, sai kuma ta shiga wanka dan a karo na farko tun bayan samuwar cikinta yau ne take jin zazzabi a jikinta. Doguwar riga mara nauyi kawai ta saka ta tada salla, bayan ta idar ta zauna komai na dawo mata daki-daki kamar wani shirin film. Kuka sosai tayi fiye da wanda tayi a dazun, a haka kunnenta ya tsinkayi shelanta sake aura auren mahaifanta guda biyu da kaddara ta hada. Kuka ta sake rushewa da shi har kanta na mata ciwo batare da tasan dalilinsa ba. Shin farin ciki ne ko sabon rudani, da kyar tai sallar isha'"i ta zame akan abin sallar ta kwanta.....


   Tana kwance a wajen cikin yar takurewar sanyin zazzabin da take ji ya shigo dakin da sallamar nan tasa ciki-ciki. Bata motsa ba har ya karaso gabanta, jin tsaiwarsa a kusa da ita ya sata bude idanun a hankali ta sauke kansa. Kallon juna suke kamar yau suka fara ganin kansu, kafin itama ta fara janye nata idanun ta mike a hankali. Ganin yanda take dan layi na wandda jiri ke kwasa ya sashi mika mata lallausan farin hannunsa sol mai dauke da dogayen farata. Nata ta daura a hankali cikin nasa, ya dagata gaba dayanta ta mike tsaye a gabansa. Yanda yake binta da kallo kamar sabuwar halitta ya sake raunana mata zuciya, sai kawai ta sakar masa wani shagwabebben kuka da fadawa jikinsa ta kankamesa. Bashi da zabin da ya wuce amsarta hannu biyu shima ya kara matseta a jikin nasa yana mai lumshe idanunsa dake cike da so da kaunarta. Kuka take sosai dake sake sukar zuciyarsa, sai dai baice mata uffan ba har kusan tsahon mintuna uku suna tsayen. Sai da yaji ya daina jin dumin hawayenta dake sauka masa a kan kirji ta koma sauke ajiyar zuciya sannan ya dagota. Mayafin da tai rolling ya warware, yaja hanunta a hankali ya zauna a bakin gado ita kuma ya daurata a saman cinyarsa.

 

"Shi kukan baya isa ne".


 Ya fada a fisge fuskarta a cikin tafukan hannunsa. Fuskar ta sake kwabewa zata saki wani sabon kukan ya girgiza mata kai da fadin, "Please bana son gani kuma, kin cika shagwaba fa". Shaaa hawayen suka zubo dan ta kasa rikesu, sai kuma ta turo masa baki gaba. Murmushi yayi a zuciyarsa, tare da matso fuskarta dab da tashi ya tura yatsunsa cikin gashin kanta ya zare ribbon din data dauke gashin a tsakkiya ya shiga yamutsa mata shi yana goga mata hancinsa kan nata, lips din ta sake dan turowa, shiko ya samu damar hadesa da nashi kirif. Iya kokari yayi na ganin ya tsaya iya hakan, sai dai zuciyarsa gaba daya taki bashi hadin kai. Sai kawai ya zarce da abinda gangar jikinsa ke tsananin bukata da kwadayi, da ga haka labarin ya canja da salo mai matukar nauyi dake kara tabbatar musu yanda suka narke a so da kaunar juna mai tsananin gaske. 



Dakin yay shiru sai fitar sanyin na'ura tana lafe a jikinsa cikin muryarta da ta disashe take fadin, "Komai kamar a mafarki ko? Ji nake kamar idan na farka zanga ba haka bane ba Maleek. Har yanzu gaba dayan zuciyata taki yarda da komai dari bisa dari".


Murmushi yayi mai sanyi da sake gyara mata kwanciya a jikin nasa, hannunsa kam na'a kan cikinta. Lumsassun idanunsa ya bude a kan kyakykyawar fuskarta da hatta dan kumbura saboda kukan da ta sha a yinin yau. Motsa lips dinsa yay a hankali ya furta "Rayuwar ma gaba dayanta tamkar mafarkice Niger. Yanda muke kwantawa mu tashi da wucewar gobenmu haka kwanakin kaddarar rayuwarmu ke shudewa da abubuwan da suka gabacemu. A duk abinda kikaga ya far a yau tabbataccene da tabbatar rubutun alkalamin kaddara. Wata hikimace kuma da ga hikimomin UBANGIJI. a randa na fara hacuwa dake komai ya cigaba da maimaitamn kansa tamkar mafarkina. Da ga cikin duk abinda ya faru har kina tunanin akwai abinda zai iya gagara da ga tarkar UBANGIJI? 


   "Murmushi ta danyi mai sanyi a karo na farko tare da dagowa tana kallon kyakykyawar fuskarsa. "UBANGIJI gagara misalin masu misali ne ai, duk abinda ya zartar haka yake babu kokwanto ko shamaki a cikinsa. Kai dabanne a cikin daban MIJINA RAYUWATA" tai maganar da dan ja masa hanci. Murmushi yayi mai Kayatarwa da dungure mata kai. Ya ce, "Ai kin fini zama daban. Mai mama biyu, yayu biyu, kakanni biyu, gida biyu, kefa hatta duniyarki biyu ce My sohaa".


   Dariya ta kyalkyale da shi kamar ba yanzu ta gama rusar kuka ba. Ta kankamesa da fadin, "Idan na hada da taka duniyar ma uku garan FARIN CIKINA".


  "Oh oh, yarinyar nan fa naga alamar kin fetsare". Yay maganar yana dagota. Gashin da ke a gemunsa ta kamo da yatsunta tana wasa da shi, cikin shagwabe fuska ta ce, "To ai duk karatunka ne, su Ummu ma shaidane ba haka suka baka ni ba, ni da ko kallon mutane bana iyayi cikin ido..."


   "K din dai dana sani?".


Ya fada cikin katseta da dan waro idanunsa waje. Fari ta masa tana murmushi cikin dage gira sama da fadin, "Kaima ai shaidane, saliha dani aka kawo maka ga hakuri ga shiru-shiru"., Mizai yi inba dariya ba, sai da yay mai isarsa tana kallonsa cike da jin dadi sannan ya dungure mata kai. "Wai ke din nan ce mai shiru-shiru, bayan randa na fara ganinki da rashin kunyarki nai karin kummalo. Lallai an cuci masu shiru-shiru kuwa indai aka sakaku. Ke Fitinanniyar nan. Ranar fa harda fadin wai ko Shahan-shan ne sai kin sashi ya tsaya dole. Kai yarinyar nan ke abar toro ce".


   Dariya ta kyakykyale da shi, sai kuma ta shiga boye fuskarta dan sai yanzu abinda tai din yake bata kunaya ma. Kanta a boyen ta ce, "Wai dan ALLAH ranar bakaji kamar kasa a tsireni ba?".


   "Ke dai kika tsiremun zuciya ban shirya ba. Danni kadai nasan dauriyar da nayi ban fallasa abinda ke a raina ba tun a wajen".


   Dariyarta mai tada masa tsigar jiki tayi da fadin, "Nima fa kadan birgeni a ranar, dan kamshinka ya tafi dani matuka da wadan nan fararen idanun masu kyalli kamar madara. Kawai dai ranar haushin kowa nakeji ne sai na samu na sauke akan yaranka. Wai kuwa suna ina ma?".


  Murmushi kawai yayi baice komai ba, sai da ya mula da kansa sannan ya magantu. "Uhm ashe nayi babban kamu tun a ranar faro amma aka tsiwaceni tas. Ke ta dabbance yar kanwata. Su Azaan suna nan abinsu, ma'aikata ne a gidan jaridata ta AFRICAN EYE. Inda kika so zuwa ki tone mun asiri da min zigidir a bainar nasi ALLAH ya taimakeni".


 "Shine ka tareni ko? Ashe dai kanajin tsorona?".


  "Kai sosai ma kuwa. Mra Eshaan ko bakin nan naki da baya gajiya da magana ai yasa aji tsoronki."


  Harara ta dan masa tana tura bakin, sai kuma kamar wadda aka tunatar ta ce, "Wai dama dan ALLAH gidan jaridar Africa eye naka ne?".


  Kai ya gyada mata idanunsa a lumshe ya ce, "Shine burina na farko dana cika bayan kammala karatuna".


  "Uhm Masha ALLAH, shiyyasa akema manyan duniya tone-tone ba ragi babu ragowa kuma komai

bai faru ba. Amma gaskiya kayi kokari. Nima wannan

shine burina"


  "Ki dauka kin cikashi insha ALLAHU My Sohaa, Kina haifomin babyna makaranta zaki koma, insha ALLAHU arena bazai tauye miki cikar duka burikanki ba. Zan tsaya miki da tsayawar UBANGIJI har sai kin cika duk burin da ALLAH ya rubuto a cikin kaddarar rayuwarki na alkairi".


   Wani irin rungumesa tai da fashewa da kuka. Hannu biyu ya amsheta yana murmushi. Gain kukan na gaske ne aka sauya masa salon lallashi kamar ba yanzu aka fito a komar ba. Da alama dai Iffah'r mu ta haddace karatun gwarzon nata har sun zama dai-dai,🚴










        Hankalin Jasrah ba karamin tashi yay ba da yanayin data samu yar uwarta. Rasama abinda ya dace tayi tai, a rikice tai kiran number likitan Malikat Bushirat din. Cikin kankanin lokaci kuwa sai gashi. Shima hankalinsa ya tashi, dan shi abinda ma zuciyarsa ke raya masa da ban da wanda ke a hakika. Zai zauna bin ba'asi Jasrah ta katsesa da fadin, "Yanzu ba lokacin sanin miya faru bane. Ceto rayuwarta shine mafita first".

  

"Hakane"


   Ya fada cikin gamsuwa. Da taimakonsa suka maidata saman gado, babu bata lokaci ya shiga aikinsa, ya samu nasarar tsaida jinin, tare da ceto numfashinta da tuni yabar gangar jikinta. A tare suka saki ajiyar zuciya bayan daidaiton komai. Jasrah ta dubesa cikin roko ta ce, "Doctor Please wanna al'amarin ya tsaya da ga ni sai kai dan ALLAH. Dan yana da kyau mu fara sanin abinda ya faru da ga bakinta karmu tashi hankalin mutane. Musamman ma Shahan-shan abubuwan zasu masa yawa. Ga wanna rikicin da yake ciki ga kuma wannan. Shima mutum ne kamar kowa yana bukatar sassauci".


   "Gaskiya ne ranki ya dade. Insha ALLAHU baki da matsala. Dan aikina ne wannan. Ki dai kasance a kusa da ita dan zata iya farkawa a firgice kasancewar daga suma muka maidata barci, Sannan gaskiya ya kamata kusan abinda ke damunta Kinga wanna fa shine karo na biyu, zata iya samun matsala idan haka ya cigaba da faruwa. Dan yanzu haka da kyar na samu bugun zuciyarta ya daidaita, ga jininta ya hau matuka sai tana samun kulawa lafiyarta zai samu daidaiton da muke bukata".


   "Insha ALLAHU Doctor za'a kiyaye".


  "ALLAH ya tabbatar, zuwa safiya zan kawo magunguna ko kuma zuwa anjima kadan"


   "Okay inaga ka kawo anjima din zai fi".


   "Shike nan bara naje sai na dawo"….✍️


No comments

Powered by Blogger.