Daudar Gora Book 2 page 50

 


DAUDAR GORA...II

Chapter: 50


Zaune take kan gado tun bayan idar da sallar magrib da Jasrah ta taimaka mata tayi kafin ta wuce. Idanunta tsaye suke kyam a waje

guda alamar tayi matukar zurfi a tunani, dan sam hankalinta ma baya a cikin duniyar mutane,

ya tafi ga yanda zata shawo kan uwa ne kwai da kuma gusar da Iffah datai kane-kane a cikin

rayuwar danta, dan tasan abinda uwa ta fada babu fashi bazasu taba canja sharadinsu ba inhar bata karasa cika alkawransu ba. Ita mai bada labari ce akan bijirewar da surikinsu

(Tajwar Abdul-majeed) yay da abinda ya biyo bayan hakan, dan har yanzu hukuncin uwa na biye da su daki-daki wanda shine ma

makasudin komai akan kanta yanzu haka da tushen faruwar komai akanta. Tun dazun gaba

daya hankalinta a tashe yake. Tana ta kokarin kiranyen uwa amma babu alamar zata ziyarceta,wannan shine mafi zama kololuwar tashin

hankalinta a yanzu. Motsi da kamshinsa ya sata dago manyan idanunta farare tas da a yanzu

launinsu gaba daya ya koma jazur har baka iya gane bakin ma da kyau. Duk da fushin da take

da shi bai hanata jin sanyi da ganinsa ba a cikin ranta, dan da gaske shine abu mafi kololuwar

soyuwa a gareta a kaf abinda take ganin ta mallaka a diniva KAfesa tai dA kallo rike da so da kauna, sai dai tana kokarin dannewa a zahirance. Wani irin harbawa zuciyar Iffah da girarta ta dama sukayi a lokaci guda, tai saurin ja ta tsaya da kokarin son janye hannunta da ke a cikin nasa. Amma sai yaki sakinta har sai da suka isa gaban Malikat Bushirat da sai yanzu ta lura da Iffah da ke faman boyewa a bayansa

Hannunta ya jawo a hankali ta dawo gabansa idanunsa akan Malikat din dake wani irin

kallonsa. Sassanyan murmushi ya saki kadan dai-dai yana sakin hanun Iffah'r da kaiwa duke

ya kamo na Malikat Bushirat ya saka na Iffah ciki sannan ya ja da baya zuwa bakin gado ya zauna

abinsa tamkar baiga kallon da Ammien tasa ke masa ba. A wani zafi Malikat Bushirat ta yarfar

da hannun Iffah'r tana watsa mata mummunan kallo. Iffah da kanta ke wani irin yamutsawa tun

shigar hanunta cikin na Malikat Bushirat din ta bude idanunta da suka kada jajur. Amma sai taki

kallon kowa a cikinsu tama risinar da kanta da fadin "Ammie ina yini?".


       "Mi wannan tazo yimun nan?".

Ta fada ranta a matukar bace tana maida kallonta ga Tajwar Eshaan maimakon amsa war da Iffah tai mata. Shiru kamar ba Adi ba, ran Malikat Bushirat ya kara sos matuka, duk da sanin halinsa ne dama hakan. Sai da ya mula dan kansa sannan ya dubeta yana dan guntun murmushin daya sake harzuka Ammien tasa. A hankali ya motsa lips dinsa yana lumshe idanu da budewa. "Ammie! Munzo mu baki hakuri ne, ta kuma dubaki.



        "Hakuri? To nace mata ina bukatarsa ne.Saiful-malik ka fita idanafa ko. Ka fita idona karka bari akan yarinyar nan mu samu matsala da kai. Ita bata kai matsayin da zata zama kO abin kallona ma balle har a saurari wani abu daga bakinta. K! Tashi ki fitar min anan, karna sake ganinki a cikin idanuna, inba hakaba sai kinyi nadamar sake maimaita wanna kuskuren.


      "Ammie.



Da sauri ta daga masa hannu, "Na fada maka bana bukatar jin komai daga gareka, kuma ina

akan bakana na sai ka saketa. Inba haka ba Eshaan zan baka mamaki da ga nan zuwa safiyar gobe in har baka janye garkuwar daga bama yarinyar nan ba tare da takardar saki

uku.


Wani irin lallausan murmushi Iffah ta sakikamar ba'a kanta ake dambarwar ba. Ta dago a hankali ta dubi Malikat Bushirat, sai kuma ta maida kan Tajwar Eshaan. Hada ido sukai, ta sakar masa wani murmushin da yafi Nafarko neman wargaza masa lissafi. "Mutuwa da rayuwa gaskiya ne *_Sultan_*, kamar yanda kaddara da jarabawa suke abokan rayuwar kowane dan adam. Ammie tayi gaskiya, ban cancanci GARKUWA da ga gareka ba, sannan kuma igiyar aurenka bata dace da cigaba da zama kan mace irina ba. Nima a yau na fahimci komai, na gano komai, babu abinda ya rage kuma, tabbas babu. Ka bani dama zan bata hakuri da kaina, zan kuma fahimtar da ita yanda zata fahimci komai dan nasan yanzun ma bayin kanta bane masu zuga ne.Kallonta kawai yake a narke da jin kaunarta na kara ratsashi. Wayonta yana rinjayar duk wani karfin ikonsa a zahirance. Ya fahimci tana son ya basu wajene. Sai ko ya mike a hankali yana kai waya kunnensa kamar wanda ke shirin

kiran wani.


          Wani irin shegen murmushi Iffah ta sake saki idanunta akan Malikat Bushirat da ke jin kamar ta hadiyi zuciya ta mutu. Itace wanna yarinyar zata nunama danta da ke matsayin Shahan-shan tacika mace a garesa. Iffah dake danne dariya ta wani kashe mata ido daya da kada mata yatsun hannunta biyu akan fuska. "Hy my Mather in-law ya da suman zaune haka tun ba'a fara wasan ba. Kin damu kanki da saki-saki kinmanta danki sarki ne, bai isa sakin n Ahaka kawai bai sai da hujja mai karfi? Oh!! Kina son a sakeni saboda na zame miki kadangaren bakin tulu ko? Ayya!! Ayya!! Mather in-law kinyi sakaci ai, kinyi sakaci tunda har kika bari Fhareedah bint Zayyan ta kasance daya da ga cikin Zawjata-almilk. Kinyi sakaci tunda har danki ya zama a tsakkiyar tafin hannuna. Kinyi sakaci tunda har kika yarda hanunki ya taba jikina a karo na farko yau ma karo na biyu kika sake. My Hamäh idon Iffah bude yake tun a randa ta shigo wannan masarautar, sannan biye nake da takun kowa hatta ke kanki. Dan haka nice zan baki mamaki kafin safiyar goben da kika shardanta masa idan baki bi a hankali ba ba kece zaki bada mamakin ba. Bara na bude miki zancen a bayyane, naba danki gubar dafin macizai a cikin madara badan ya mutu ba, sai dan na kusanta da shi. Dan wannan hanyar ce kawai zata bani damar zama a sashensa din-din, saboda na tabbatar duk wadda ta kasance tana aikata ko yana aikata barnar da kisan matansa da ma duk wani mugu mai boayyen nufi a kansa bazai barni ba zai yi yunkurin ganin ya kashe ni tun a cikin kurkukun, shiko bazai bari ba zai bani kariya dan dole-dole yana son sanin dawa mukai aikin ai. Kinji na farko kenan"ta kare maganar da dage mata gira. Sai kuma ta juya idanunta masu rikita lissafin Malikat Bushirat da har yanzu basu gama sabewa ba


       "'Na biyu tun a randa aka kawoni gidan nan wika zama suspect dina na farko. Dan nagano matsanancin tashin hankali a cikin idanunki

lokacin da naki shan madarar da kika saka a bani. Kinji na biyu in-law. Na uku randa nake kwance asibiti dalilin rigar da aka sanya mun akwai kallon da kikai mun da ya saka na ajiyeshi a kyakykyawar ma'adana. Na hudu randa kuka zaunar dani akan kunaso na koa sashen Eshaan da zama danna gano muku wai shike

kashe matansa ko wanine. kai jama'a" ta fada tana kyalkyalewa da siririyar dariya. "Wihy

kinada basira in-law. Kin iya makirci da in har mutum bai san ainhinki ba sai ki gama halakashi

bai sani ba. A ranar na fahimci abubuwa da yawa a cikin kalamanki, kawai kina boye kanki

ne cikin rudanin bayin ALLAH. Uhhm kin dan birgeni fa. Randa Eshaan yasha gubar dana

bashi shirunki ba yana nufin baki da abin fada bane, ni nasan kinfi kowa zama a kololuwar

bala'i dan naga haka a cikin idanunki. Randa kika bashi umarnin ya sakeni na gano abinda ke bakiyi tunanin zan gano ba a cikin kwayoyin

idanunki da taba jikina da hanunki yayi. Hhhhhh Iffahr nan da kike gani batta a inda kika ganta batta, tafi karfin zama yar wasan kura, ni din hazabibiya ce fiye da yanda kike tunani

Mamana. A yau kuwa shigar hanuna cikin naki ya sake tabbatar min da ke ce, ke ce Malikat Bushirat da ke hallaka matan danki da kika haifa da cikinki. Mi kike bukata ne? Minene a rankine? Minene burinki ne? Mi kike son zama ne?Bayan duka ALLAH ya baki?. Ki fada min, nikuma na miki alkawarin taimakonki bazan kuma tona asirinki ba ko dan daraja da mutunci dakimar danki, dan bazan bar ZUCIYAR MIJINA ta buga ba a dalilin son zuciyarki. K uwa ce garesa,kuma ina kallonki da wannan kimar ne har yanzu saboda mutuncinsa Ammie. Sai dai bazan iya yafe miki jinin yan uwana guda biyu ba. Kar kiyi sakaci da wannan damar, in ba haka ba ki sani da ga yau wannan lokacin na yaki ne, tabbas na

yakine.


         Tabbas Malikat Bushirat a sume take, sumar da kunne na ji ido na gani amma gangar jiki bata motsawa. Suma irin na mamaki da tsantsar tashin hankali. Dan babu abinda ake iya gani sai wutar masifar da ke ci a tsakkiyar idanunta dake kallon Iffah. Iffah da tuni ta fahimci haka murmushi ta sakar mata da buga hanunta na dama dake dunkule a tsakkiyar na haggu taialamar yanka wuya a saitin wuyanta tana kashe

ido da cije lips.



      Wani irin mikewar zabura tayi kamar wadda aka dawoma da dukkan karfinta dai-dai da dawowar Tajwar Eshaan akin. Fashewa Iffah tai da kuka da durkushewa gaban Malikat Bushirat da ta mike tsaye a zafafe. Ta riko duka kafafunta tana kukan da fadin, "Ammie nasan zaki fadukkan bayani na, kuma zakimun adalci a cikin dukkan abinda ya farun nan. Nima ba laifina bane tirsasani sukayi da mun barazanar karar da ahalina dama ku musamman ke da kike mahaifiya ga adalin shugabanmu. Ni kuma a shirmena idan na bashin za'ai saurin kaisa ga likita kafin ma dafin macizan yay tasiri. Ki yafe min Ammie nayi kuskure da wauta ki yafe min…

        

           Gaba daya Malikat Bushirat sai ta sake mutuwar tsaye. Eh lallai yau taga masifa, anya yarinyar nan mutum ce kuwa? Shikam mai gayya da aikin yay wata irin tsaiwar da ko bai fito fili yace komai ba Malikat Bushirat da kanta ta hango abinda ta hango a cikin idanunsa da ke tsaye kyam akan Iffah da ke a gurfane gabanta.Tabbas idan tai wani abu a yanzu akwai matsala,zakuma tayi kuskuren da yafi na yarda da shigowar yarinyar nan masarautar nan. Hadiye abinda yay mata tsaye a makoshi tai da kyar, ta rankwafa ta kamo kafadun Iffah ta mikar da ita tsaye. (Ya ALLAH hawaye fa share-share a fuskar Iffah kamar gasket). Bata da zabin daya wuce rungumeta itama tana matsar kwallan karya ta shiga fadin. "Ban san haka bane Ibnati miyasa kika ki fahimtar da ni da ban miki irin wannan mummunan zaton ba ai. Kiyi hakuri ki gafarceni"……….✍️




_Wannan yarinya ta zama abin toro gaskiya

😂. Ahe haka take 🥱


🥱Ni wannan ya ta Babiy kodai sunada sarauta ne a kauyen Jumna bamu da labari. Wannan hayen izza na dauran kai gaskiya 😂


No comments

Powered by Blogger.