Bakon Lamari 1


 BAƘON LAMARI...!*🌹

     { Eternal love }


           *NA*

AUTAR MANYA


Bisimillahir Rahmanir Rahim


                     *001*


Lumshe Manyan idanunshi yayi yana shafo gemun shi a hankali yana jin sautin kukan ta yana tashi ta cikin wayar dake kare a saman kunnen shi.


Magana take masa wadda tsabar yadda take masa kuka, ya hana muryarta fitowa.


"Yaya dan Allah kazo kano, ina cikin matsala babu wanda zai fuskance ni sama da kai yaya, duk yadda kake tunanin matsala ta tawuce nan Yaya ka taimaka mini"


Shuru yayi mata tamkar bada shi take magana ba, sai da yaga dama dan kanshi sannan yace.


"Amatu! ki haƙuri da rayuwa kowa sai da ya fuskanci matsaloli kafin ya kai inda yake son kaiwa a rayuwa, Pls kada ki ƙara kirana kinga ke Matar aure ce"


Ƙit! ya katse wayar yana mai fesar da zazzafan Huci ta cikin bakin shi.


Miƙewa tsaye yayi tare da yada wayar yana mai shiga cikin bedroom ɗinshi, Dogone sosai mai suffar ƙarfafan maza kasancewar sa Soja wanda yasha gwagwar mayar training duk wata halittar ƙarfi ta buɗe ajikinsa, fari ne tas mai manyan idanuwa tare da dogon hanci ga wani gemu daya aje wanda ya bawa kyawun fuskar shi damar ƙara bayyana daga saman goshin sa kuma ƙaton tabon abin sallah ne wanda har wani ƙurzunu, ƙurzunu yayi yay girma sosai, saman kanshi kwa ƙwalƙwal ne bai bar suma ko ɗaya ba, bashi da yawan sakin fuska bare ka saka ran ganin dariyar shi, ya mallaki hankalin kanshi dan a tsarin shekarunsa na haihuwa zai kai shekaru talatin da takwas ( 38 ).


wanka yayi tare da shiryawa cikin uniform ɗinsu na sojoji army green, ya fita waje tare da rufe ƙofar shi ya nufi filin dake cikin barrack ɗin wanda anan suke horar da ƙananun sojoji yadda zasu yi dabarun yaƙi.


Bai yarda ya saka tunanin ta ko kukanta cikin ran shiba haka ya mayar da hankalin shi wajan aikin dake gaban shi.


*KANO*


Ta yada wayar tana mai rufe bakinta sabida tsabar kukan dake ƙara tawo mata.

A fili take furta.

"Ameerah kin cuce ni da kika samon Numbern Yaya kika ce, na kira shi nina san Koda yana da mafita baze min komai ba, Nina san Yaya baze taɓa taimakona ba a rayuwa, Zan cigaba da addu'a Allah ya kawon mafita acikin lamurana"


Ta faɗi tana mai kifewa a saman haɗaɗɗan carfet ɗin dake falon.


Tsawar da aka daka mata tasa ta ɗago da sauri nan da nan jikinta ya soma rawa sabida haɗa idanun da sukai da mijinta IMRAN!


"Bani wayar hannun ki, Uban wa kika kira macuciya shaiɗaniya?"

Jikinta yana rawa ta miƙa masa wayar sabida tsabar yadda take jin tsoron shi Ko muryar shi taji firgita take yi.


Hannun imran har karkarwa yake sabida zumuɗin yaga wata kira idanun shi ya sauka akan Numbern da tayi saved da Sunan Yayanmu.


Ya cilla wayar ta daki Tv stand sannan ya wani kwashe da dariya wadda har ta saka yana dafe cikinsa.


"Kar dai Har yanzu Zuciyarki bata haƙura da maitar son AHMAD ALI Ba? to kima jini da kyau Ahmad yayi miki nisa duk da yana Ɗan uwanki jininki yayanki Amman a yanzu yayi miki nisan da har abada bazaki kamo shiba"


A gigice Amatullah ta ɗago idanunta fal hawaye bakin ta har rawa yake wajan furta masa.


"Tir da irin munanan kalaman ka Imran Allah ya kiyashe ni yin soyayyah da Aure na aka, Inma ƙazamar zuciyarka tana raya maka hakan maza ka kawar wallahil Azim Ni Amatullah Shu'aib Makama! ban taɓa jin son Yayah Ahmad cikin zuciyata ba.........


Bai jira ta ƙarashe maganar tata ba ya janyota ya haɗeta da bango ya shaƙe mata wuya yana faman zare idanu kamar mai taɓin kwakwalwa.


"Nine zan miki ƙarya in ba son shiba mai ya kaiki ki masa waya dan ubanki ƴar matsiyata"

Yakai maganar yana tofa mata yawu a fuskarta, Hannu ta sanya ta dafe Wuyanta tana kakarin Amai sam bata damu da yawun sa ba, face Kokawar da take numfashinta ya dawo.


Zubewa tai saman kujera tana hawaye hannunta har lokacin yana wuyanta.


Ya koma da baya ya zauna saman kujerar dake kallonta, Yana mai laluba aljihunshi wiwi ɗauri guda ya ɗauko ya kunna ta yana sha nan da nan hayaƙinta da warinta suka cika mata ɗaki ƙoƙarin yin amai take yaƙi bata dama sabida matsawar da yayi gabanta yana watsa mata hayaƙin yana lumshe mata idanunshi da sukai fici fici suka koma jajir babu ko kyawun gani.


Bakinta fal da yawun data kasa haɗiya sabida Warin wiwin daya tokare mata maƙoshi.

"Imran ka matsa kada nai maka amai ajikinka wai kai wani irin azzalumi ne in Allah ya yarda sai Allah yayi maka abin da yafi wanda ka min dan shi adalin sarki ne baya zalunci kuma ya hana a zaluntar"

Ta faɗa tana miƙewa daga wajan.


Aguje! ya taɗota da ƙafa ta faɗo kanshi ya daidaici daidai goshinta ya kashe wiwin ta saki ƙarar zafi! ya saki dariya tare da kama laɓɓanta yaja yawun data Aje a bakin suka sube a ƙasa ya saki dariya tare da kai bakin sa saman nata ya cafki harshenta yana tsotsa yana fesa Warin wiwin daya sha ta cikin bakinta.


Tashin hankali ya sa numfashinta ɗaukewa cak ta samƙame masa ajikinsa amman hakan bai saka ya sarara da shan bakinta ba, har sai da yaji ya gamsu dan kanshi sannan ya tureta ta faɗi ya miƙe tsaye ya soma janta a ƙasa har ya kaita cikin bethroom ya kunna mata famfon ruwan zafi a saman kanta.


Da sauri ta miƙe tana sakin marayan kuka! Sautin tafin shi taji akanta yana dariya harda riƙe ciki.


"An gaya miki barno gabas take? ni zaki kawowa bariki har na raɓe ki, ki sume min, To ai yanzu kinji ruwan zafi kin miƙe munafuka mai kalar ragon ruwa"

Kifewa tai a wajan tana kuka! wanda kafin ta ɗago ya soma jan rigarta yana rabata da kayan jikinta, tsirara yayi mata haihuwar uwarta kafin shima ya soma fidda nashi tsiraicin wanda ya sanya Amatullahi tai saurin rintse idanunta.


Kafin da sauri kuma ta buɗe su tana ja da baya tana girgiza masa kai tana yarfe hannunta.


A buƙace yake ƙara goga gaban shi da mazaunanta, Yana ƙoƙarin nemanta ta baya, wa'iyazubillahi hasbinallahu wani'imal wakil ɗabi'ar dabobi kenan.


Wata ƙara ta saki tare da rarumar glass ɗin window daya fashe ya faɗo ta saita shi a hargitse kamar mahaukaciya tana cewa.


"Wallahi Imran da haihuwar irinku gwara ɓarin ku, danai luwaɗi gwara na kashe kaina kuma kaima na kashe ka, Munafikin Allah ka fice ka bani wuri"

Ta faɗa tana nufo shi da glass ɗin dake hannunta.


Dariya ya soma yana nuna abarshi da hannu.

"Bazaki gane shauƙin ta, ta baya ba har sai kin zama ƴar hannu na ƙara baki lokaci koki aminta dani ko kicigaba da karɓar Baƙar azaba da masifa acikin gidana wadda sakarkarun mahaifanki gidadawa basu isa sun kuɓutar dake ba"


Ya faɗa yana mai tureta ya fita.


Ta faɗa saman glass ɗin windo wanda ya bawa kanta damar fashewa nan da nan jini ya wanke mata fuska wanda ya bata damar tafiya suman wucin gadi numfashinta ya ɗauke tsaf..............

*Duk abin da yayi jinkiri to tabbas alheri ne na jima ina ƙoƙarin haɗa labarin nan amman Allah bai bani iko ba, sai yau Allah ya kinsa mini labarin Amatullah wanda zai taɓa makaranta ƙwarai da gaske domin na taɓo inda kewa al'ummah ciwo,Salon na daban ne Ku daure ku bi ku yi sharhi akan shi ƙofa tana buɗe domin ganawa da Autar manya 09022260850*





*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami  ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah  ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*

*Ina masu kananan nono?*

*Ina masu yaye?*

*Ina yammata da ake shirin aure?*

*Ina matan gida masuson gyara?*

*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*

*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*

*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE  muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko  uwargida  ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*


BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE  @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679

IG Bintus-spa-nd-more..

No comments

Powered by Blogger.