Abokin Aikina Book 1 Page 8


 LAMBA TA TAKWAS.*    

       Har cikin harabar ma'aikatar ya shigar da ni, bayan ya ɗan tsaya na gaisa da maigadin wurin. Saboda zaman shi dattijo kuma yarena waton Hausa Fulani, hakan ya sa a duk lokacin da ya gan ni yake ba ni girma sosai ni ma ina ganin mutuncin shi a idona.

     Mai adaidaita na biya kuɗin shi sannan na rataya jakata a kafaɗa, taku na fara yi cikin taƙama irin wanda nake jin sauyin tafiyar a jikina.

     Gaisawa na fara yi da mutane kamar yadda na saba cikin sakin fuska da babu yabo balle fallasa. Kai-tsaye ofishina na nufa ina baza ƙamshin da ya janyo mini kallo a wurin mutane. Domin ina hankalce da ɗaiɗaikun da suke bi na da kallo ta gefen idona. Murmushi na yi mai bayyana jerarrun haƙorana farare tas da ke cikin ɗan ƙaramin bakina, saboda tsintar kaina da na yi a cikin mayalwacin farinciki.


    'Da alamu kwalliya za ta biya kuɗin sabulu'.


     Zancen da na yi a zucina kenan, bayan na buɗe ofishina na shiga. Zama na yi a kan kujera bakina ya ƙi rufuwa saboda ina ji a jikina zan yi bankwana da damuwar Mukhtar, matuƙar haƙa ta ta cim ma ruwa.

      Zamana ba da jimawa ba wani ɗaya daga cikin ma'aikatanmu ya shigo yana faɗin. Akwai waɗanda suke jiran zuwan ki tun ɗazu, amma Oga ya ce ki je yana son ganin ki yanzun nan kafin ki fara ganin su. 

     "Ok" Kawai na faɗa cikin tsare gida ya fice, saboda abu ne wanda kowa ya sani ba na sakin jiki da kowa cikin ma'aikatar idan aka cire Amina. Ita ma sai da na gama tantance halinta sannan na fara sabawa da ita a farkon zuwana. 

       Turare na fito da shi na ɗan goga a hannu sannan na shafe a jikina, nan take ƙamshin ya ƙara kama ni na nufi offis ɗin MD kai-tsaye. Zuciyata a sake kuma cike da zumuɗin yin ido biyu da shi, duk da ina ji a raina babu kyautuwa a cikin abin da nake ƙoƙarin yi. Amma na kasa hana wa zuciyata muradinta.

      

      Ƙofar na tura a hankali bakina ɗauke da siririyar sallamar da harshena ya karye a lokaci ɗaya yayin furzo ta. Kan shi a duƙe yana ta rubuce-rubuce a cikin wasu files, ya ɗago babu shiri tare da jefa idanuwan shi a kan fuskata. Kallo ya fara bi na da shi amma ban san me ya tuna ba ya ɗauke kan shi daga kaina cikin sauri,  mayar da idanuwan shi ya yi a kan files ɗin yana ci gaba da rubutun shi.  

        Shiru ya ɗan ratsa tsakani ina tsaye cikin sanyi jiki, sannan na yi ƙarfin halin furta masa, "Barka da safiya". Daga duƙen ya amsa mini da,

  "Barka dai! Ya ƙarfin jikin?" 


    Ina wasa da yatsun hannuna na ce "Alhmdulillah!" Bai sake cewa komai ba ya fara tattara files ɗin wuri ɗaya sannan ya miƙo mini, kan shi a duƙe ya ce "Akwai mutanen da suke jiran ki, file ɗinsu ne duk wanda ya bayar da kuɗin sai ki cike masa idan kin gama ki dawo mini da su". 

       Karɓa kawai na yi ina ƙoƙarin juyawa, sai dai kafin na yi wani dogon motsi na tsinkayo muryar shi cikin kunnuwana a sarƙe yana cewa, "Ki daina amfani da turare mai ƙarfi idan za ki zo offis". 

       Daga haka bai sake cewa komai ba ya janyo wasu takardun yana rubutu, nan take ƙirjina ya buga jikina ya fara rawa cikin saurin murya na ce "In Sha Allah zan kiyaye".

     Ina gama faɗar hakan na fice cikin sauri, saboda har cikin raina na ji kunyar abin kuma na ji daɗin kulawar da ya yi a kan hakan. Duk da bai yaba turaren a zahiri ba, amma Hausawa sun ce,


 'Tankawa yabawa ne'.


       Cike da tsantsar farinciki na fara aikin da ya saka ni, domin har wani ƙarfi na samu da kuzarin yin aikin cikin nishaɗi. Kuɗin haraji na shiga karɓa ina haɗa kansu bayan na cike takardun shaidar an biya.

    Ban samu kaina ba har sha biyun rana, sannan na tattara kuɗin da files ɗin na nufi ofishin shi. Sai dai ko da na shiga da sallamata a baki dole na yi turus, saboda ban hango shi a kan kujerar shi ba kamar yadda na tsammata. Nufar teburin shi na yi da nufin ajiye masa takardun da kuɗin na juya, sai ga muryar shi na ji tana tashi a cikin toilet ɗin da ke Offishin kamar yana faɗa. 

   "Wai ke Fatima har yaushe za ki yi hankali ne? Yanzu abincin da zan ci ma kin kasa tashi ki girka sannan ki zo da zancen fita? To babu inda za ki je, kuma na dawo na tarad da ba kya gidan sai kin gane kin yi wauta, mitsssss! Aikin banza kawai. Mace har ma mace amma ta kasa sanin yadda ake tattalin miji. Sai baƙin yawon masifa daga wannan biki sai wancan..."


     Da sauri na ajiye masa takardun da kuɗin na nufi hanyar ficewa offis ɗin, saboda na ji takun shi alamun zai fitowa kuma ba na so ya same ni. Har na riƙe handle ɗin ƙofar da nufin ficewa a ƙoƙarina na son arcewa kafin ya fito. Cikin sauri na juyo jikina yana rawa na yi jarumtar ɓoye tsoro kada ya bayyane a kan fuskata, saboda ba na so ya zargi na yi masa laɓe domin na ji wani abu daga cikin sirrin shi. 

     A take ya musa tunanina ta hanyar faɗar, "Karɓi waɗannan ki haɗa list ɗin wuri ɗaya. Amma ki bar su a hannunki har zuwa gobe, don na san ba lalle ne ki kammala su a yau ba".


    Karɓar takardun na yi na fice, zuciyata a cunkushe na nufi offis ɗina. Saboda muryar da na ji ya yi amfani da ita wurin yi mini maganar ƙumshe take da damuwa. Haka kawai na ji ina jin haushin matar shi a raina, domin ganin Allah ya ba ta dama amma tana wasa da ita cikin izgilanci. 

     Shiga ta offis ke da wuya na hango Amina zaune a kan kujerar baƙi ta yi tagumi. Murmushi na yi babu shiri maimakon na ji tausayin halin da na gan ta, kuma na san tana ciki. Amma sai na ji dariya ta zo mini, saboda kallon da nake yi mata har yanzu ba ta san komai a cikin ƙalubalen aure ba, idan na auna shekarun aurenta da ta sanar da ni, da shekarun aurena da kuma matsalolin da nake ciki. Waɗanda nake hangen ko rabin kwatar ba ta kai ba balle ta kamo ƙafata.


   Zama na yi tare da faɗin "Wash Allah!" Ta ɗago da kanta tana kallo na hawaye kwance a kan fuskarta. Mamaki ya so kama ni saboda tunanin me ya saka ta kuka a lokacin...

      "Ina cikin tashin hankali Zaituna. Wallahi zuciyata gaf take da bugawa matuƙar Mama ba ta canza tsarin da ta yi ba.."

 Zancen da ta tarye ni da shi kenan cikin rawar murya hawaye suna kwarara a kan fuskarta. Kafin ni ma na tari hanzarinta da cewa "Haba Amina! Har zuwa yaushe ne za ki saba wa zuciyarki shanye damuwa a kan halin Mama...?" 

      "Wannan karon daban yake da sauran abubuwan da take yi mini. Ta ya za a ce ta ɗauki kwanana ta bai wa kishiyata? Na rantse da Allah ba zan iya jurar ganin wannan kayan baƙincikin ba. Na fi so na je gidanmu da dai a ce na zuba ido Sanusi ya kwana ɗakin Sadiya".


    Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi, sannan na kira sunanta cikin sanyin murya na ce "Amina! Idan na tambaye ki za ki ba ni amsa?"

"Me zai hana idan na sani?". Ta ba ni amsa a gatsali kuma ta da dawo mini da tambayar kaina. 


"Don me Mama ta nemi yi miki haka.."

"Saboda ta ƙuntata rayuwata ta ɓata mini rai. Idan ma mutuwa zan yi na je na yi ita babu ruwanta". 

 Ta ƙare maganar cikin kuka wanda ya ƙara tona asirin ƙunar da zuciyarta take yi. Gajeren murmushi na yi sannan na ce,

       "Kin san da hakan kuma kike ta wahalar da kanki a banza? A tunanina tun da har kin gano da gayya ta yi don ta ɓata miki rai. To ya dace ke ma ki ci maganin abin ki nuna mata hakan bai dame ki ba..."


      "Ta ya zan iya jure wannan cin kashin Zaituna? A gaban idona ya kwana ɗakin Sadiya kuma a ranar kwanana a ce ba zan damu ba? Wace irin juriya ce zan yi a kan dokarta? Bayan ita ta saka ƙafa ta yi fatali da faɗar Allah Manzonsa, ta halasta haram ta haramta halas. Sai dai ana so na yi juriyar zuwan mala'ikan ɗaukar rai, domin ya zo ya karɓi raina cikin gaggawa na huta da wannan rayuwar baƙincikin ba.  To ni wallahi ba zan iya ganin wannan kayan takaicin ba gidanmu zan je..." 

      

        Maganar da katse ni da ita kenan cikin matsanancin fushi na zahiri da ya tona asirin zaman shi a kan fuskarta. Da kai wa ƙololuwar ɓacin ran da ya fito har a cikin lafuzzan bakinta. A fusace ta miƙe ta ja jakarta da nufin ficewa, sanin idan ta fita a irin wannan halin da take ciki komai za ta iya aikatawa. Na yi hanzarin miƙewa na sha gabanta sannan na rufe offis ɗin da key na zare. Ƙasa ta durƙushe tana gunjin kuka mara sauti, na yi saurin isa inda take cikin tausayawa na fara rarrashinta. 

     Ganin da gaske take ba za ta iya juriya a kan shanye damuwarta ba. Na miƙe cikin tsananin ɓacin rai tare da rugume  hannuwana a ƙirji, cikin wata kausasshiyar murya na ce  "Da a ce zan iya, da na sanar da ke labarina. Wanda nake da tabbacin ya linka naki baƙinciki sau goma, wataƙila ki gano ba ke kaɗai ce igiyar aure take wahalarwa ba. Domin ina da tabbacin taki matsala tamkar shafin mai take idan kika ji tarihina".


    Sai da ta rage sautin kukanta sannan ta ce, "Kina nufin ke ɗin nan da nake gani kin taɓa shiga matsalar aure a baya kafin yanzu?"

     "Yanzu haka ina cikin matsalar, kuma har yanzu ban shaƙi iskan 'yanci ba". 


Kallon mamaki ta bi ni da shi kafin ta sake cewa, "Kina da damuwa amma ban taɓa gani a kan fuskarki ba? Kina da damuwa amma ba ki taɓa nuna alamun hakan ko a cikin furucinki ba? Kina da damuwar da ta fi tawa kuma kika iya haɗiye ta cikin cikinki, ba tare da kin yi aman jinin fitar da baƙincikinki a fili kin huta ba? Ta ya zan gamsu da hakan bayan ni na kasa shanye rabin kwatar damuwar da kika ce kina da ita? Kaico Zaituna, ni na kasa farinciki balle wanda zai linka ni fuskantar matsalar a rayuwar aure?"


    Murmushi na yi mata sannan na fara safa da marwa a tsakiyar offis ɗin, kaina a duƙe hannuwana a baya ina furzar da iska mai zafi daga bakina. Saboda tuno majaujwar tashin hankalin da ta yi ta juyawa da ni a baya har zuwa yanzu. 

    Hawayen da suka fara gangara a kan fuskata na share da gefen hannuna, sannan na yi jarumtar ba ta amsa a gajarce.

      "Ta hanyar sanar da ke labarina" 

Ban jira cewarta ba na fara jero mata  tambayoyina kamar haka;  

       "Kin taɓa kama mijinki yana hulɗa da matar aure?"

     "Mijinki ya taɓa faɗa wa duniya kin ce sai kin kashe shi?"

      "Mijinki ya taɓa damfarar Iyayenki?"

        "Mijinki ya taɓa yi wa 'yar aikinki ciki?"

       "Mijinki ya taɓa neman auren ƙawayenki na ƙud-da-ƙud waɗanda kuka tashi tun kuna ƙurciya?"

       "Mijinki ya taɓa bai wa ɗanki matsayin da ya yi kamanceceniya da zama kishiyarki?"

       "Mijinki ya taɓa sayar miki da kayan ɗaki? Ko ya taɓa satar miki kuɗi ko wani abin amfani?"

       "Mijinki ya taɓa fallasa ki a bisa ƙazafi cikin dangin shi da naki bayan 'yan'uwa da abokan arziƙi masu ganin girmanki?"

        "Mijinki ya taɓa zuwa wurin mutanen da kike jin kunya aron kuɗi ko roƙo?"

       "Mijinki ya taɓa yi miki ƙazafin kina tare da wasu mazan waje a gaban 'ya'yanki?"

       "Kin taɓa neman haƙƙinki wurin mijinki bai sauke ba?"

         "Kin taɓa shekara huɗu ba tare da mijinki ya kasance ki ba...?"


      "Dakata Zaituna. Kada ki sanar da ni cewa duk waɗannan abubuwan da ke suka faru?" Hanzarin katse ni ta yi saboda mamakin maganganun da ta ji suna fita bakina. Kafin na ba ta amsa cikin muryar kukan da ya kasa tsaya mini, saboda ta sa na fama mikin baƙinckin da ya daskare mini zuciya. 


      "Tabbas da ni waɗannan abubuwan duka suka faru, har ma da sauran wasu tambayoyin da kika katse ni ban samu sararin furzowa ba..." 

      "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Ke kam wace irin zuciya ce da ke haka mai shanye baƙƙan ciki manyan kashi kashi irin haka? Ni ko zan so na ji waɗannan abubu ɗaya bayan ɗaya, don na san tabbas akwai karatun da zan kwashe a cikin tarihin rayuwarki. Kuma zan ɗauki darussa a ciki ko don na magance matsalar da ta addabe ni. Cabɗijam! Ashe daman akwai wadda ta fi ni shiga matsala a rayuwar gidan aure?"






Akwai Amina. Domin kuwa kafin a je ko'ina ga Zaituna nan a kusa da ke🥲


No comments

Powered by Blogger.