Abokin Aikina Book 1 Page 7

 


LAMBA TA BAKWAI.*


        Raina a ɓace na fito falo saboda sautin maganar shi da nake ji a sama, yana bayanin rikicin da muka yi da shi. Wanda nake da tabbacin waya ce yake yi kuma Ummata ce yake faɗa wa. Bakin ƙofar shi na nufa saboda baƙincikin makircin da na ji yana yi a cikin

wayar, don bayan abin da ya haɗa mu har da ƙarin gishiri da mai, yana ta ƙoƙarin dole sai ya ɗora mini laifukan da ya saba ya wanke kan shi. Saboda komai na yi a wurin shi laifi ne shi kaɗai ne mai yin daidai.

     "Wallahi Umma har yanzu suna tare, a kan shi yau babu abin da ba ta faɗa mini ba. Babban baƙincikina mutane har sun fara yamaɗiɗi da ita a cikin unguwar nan saboda tarayyar da take yi da shi..."

       "Hakiƙa duk mai irin halinka a rayuwa ba ƙaramar asara ya yi ba wallahi. Ina takaicin zama wuri ɗaya da kai, ina da-na-sanin auren da na yi maka tsawon shekaru. Haka ma ina tausaya wa yarana da na yi zaɓen tumun dare wurin zaɓar musu uba kamar ka..." Abin da na faɗa kenan a bakin ƙofar ɗakin shi, cikin ɗaga murya bakina yana kumfa, domin ya tabbatar da na ji abin da yake faɗa. 

     "Ai kin saba faɗa ba tun yau ba, don haka yanzu ko kin maimaita ba abin mamaki ba ne..." Na katse shi cikin hanzari ina faɗin, 

      "Tir! Da rayuwarka Mukhtar! Ka ji haushi iya haushi a kan rayuwar azuzancin da kake yi. Idan burinka haɗa ni da mahaifiyata ne, to ka je ka ci gaba ga gani idan Allah zai bar ka..."


      Ƙarar da wayata take yi cikin sautin kiɗan da na saka mai daɗi, hakan ya tabbatar mini da Umma ce take kira na. Ban bi ta kan wayar ba na ci gaba da aika masa baƙaƙen maganganu yana mayar mini da raddi cikin rainin hankali, domin duk na faɗa sai ya mayar mini ɗaga can cikin ɗakin shi. 

        Shigowar yara aguje bai sa na daina abin da nake yi ba, saboda na riga da na zo wuya. Kamar yadda har lokacin wayata take ta ɓurarin neman agaji. Kallo kawai yaran suka bi ni da shi bayan kowanensu ya sha jinin jikin shi, domin in da sabo sun saba gani amma sun kasa cire damuwar hakan a ransu. Saboda su na koma kan kujerar falo na zauna ina sauke numfashi, Haidar ya zo ya zauna kusa da ni yana riƙe mini hannu cikin nuna kulawa. Ummu Salma ta yi ɗaki da sauri ta ɗauko wayar ta kawo mini, Iman ta rakuɓe tana kallona tana sharar ƙwalla. 


     "Mukhtar ƙarya yake yi Umma, kuma ƙazafin da ya saba ne ya sake yi mini..." Na faɗa raina a ɓace ba tare da na jira cewarta ba. 

       "To me ya haɗa ki da mutumin har ya ba ki waya?" 

     Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce "Waya ce aka rarraba a ma'aikatar kowa aka ba shi ba ni kaɗai aka bai wa ba. Shi ne fa daga ganin ta ya fara jifa ta da ƙazafin da ya saba, tun da ni babu ranar da zan yi abin kirki kullum sai ya kawo ƙara ta. Saboda ganin yake yi ya fi ni iya faɗar zance, da daɗin bakin ƙarya domin kawai ya sa ki ga laifina.."

     Na katse maganar saboda kukan da ya zo mini. Umma ta yi shiru na ɗan lokaci sannan ta ce, "Daina kuka ba na son jin kukan nan raina ƙara ɓaci yake yi. Ki yi haƙuri zan fahimtar da shi domin ya daina tunanin da yake yi a ran shi..."

      "Na gaji da zama da Mukhtar Umma, na kai matuƙar ƙololuwa a kan zaman nan da nake yi.." Ƙit! Ta kashe wayar, saboda abin da ta tsana kenan a ranta ta ji ire-iren waɗannan maganganun suna fita daga bakina. 

      Kuka na ci gaba da yi Haidar yana goge mini hawaye cikin fuskar tausayi. Ummu Salma da Iman suka shiga sharɓar kukan su ma, kafin Ummu Salma ta miƙe cikin ɓacin rai ta shige ɗakinsu.


   Na kai kallona ga Iman cikin muryar kuka na ce "Tashi ki cire kayan Makarantarki. In dai wannan ƙaddararren uban naku ne, kuna da aiki idan kuka ce za ku dinga kuka a kan mugun halin shi. Kai ma ta shi ka je ku cire kayan ka fito ka yi shirin zuwa masallaci".

     Suka miƙe tare da jan jakar islamiyarsu suka yi ɗakinsu. Na daɗe zaune a wurin ina karanta wasiƙar jakin da na saba, a kan wace hanya zan rabu da wannan baƙin zaman da nake yi. Sai dai duk hanyar da na zura kai cikinta sai na hango tarnaƙin da ke gabana idan na ce ita zan kama.

      'Ni shi kenan a haka zan ƙare rayuwata da mijin da ba zai share mini hanyar shiga aljanna ba?' 

      Tambayar da na jefi kaina da ita kenan wadda ban da cikakkiyar amsarta, kiran sallar magrib ya sa na miƙe na yi ɗaki. Ina kan sallaya har aka yi isha, sannan na miƙe na fito falo na zauna, ɗauke da wayata ina chat su Ummu Salma suna kallo. Jiki na saki a cikinsu muka ci abinci tare na sha magani kamar ba ni da damuwar komai, domin Allah ya saka ni cikin mutanen da damuwa ba ta zauna mini a zuciya duk girmanta. Daga na yi masifata na gama shi kenan nake jin komai ya wuce a wurina, amma duk lokacin da ban samu damar furzar da abin da ke bakina ba, abin ya fi tsaya mini a zuciya har ya haifar mini da damuwa. 

     Mun ja lokaci a falon har suka yi bacci. Sai da na tayar da su suka shiga ɗakinsu, sannan na tofe su addu'o'i na rufe musu ƙofa na nufi ɗakina. 

    

        MD na hango online bayan na kwanta na sake buɗe datata, saboda Gb WhatsApp ne gare ni duk wanda ke online sai ya nuno mini yana nan. Haka kawai na tsinci murmushi a kan fuskata, domin har cikin raina na ji daɗin ganin shi ko da ba za mu yi magana ba. Na shiga duba status ɗin mutane idan na fita wannan na faɗa wancan har na isa ga na MD. Shiru na yi ina nazarin maganganun da na ga ya rubuta a status ɗin shi, domin kai-tsaye na alaƙanta rubutun da ni. 

    'Mu yi haƙuri da yanayinmu na yau idan bai yi daɗi ba. Domin komai wucewa yake yi kamar ba a yi ba. Babu abin da yake tabbatacce idan ba wanda Allah ya tsara ba! Ubangiji ya kawo mana farincikinmu a kusa da mu'. 

     Ajiyar zuciya na sauke, tare da goge ruwan hawayen da ya ziraro mini a gefen fuska. Saboda ina ji a raina kamar ya shiga zuciyata ya hango abin ke cikinta. Ina ji kamar ya haska wani madubin da ke hango masa hoton abin da ke damuna. 

     "Tabbas!" 

Comment ɗin da na yi masa kenan a jikin status ɗin. Babu jimawa ya buɗe saƙon tare da fara typing a lokaci ɗaya. Kasaƙe na yi ina jiran ganin me zai ce, saboda sanyin da jikina ya yi a lokacin ɗaya bayan na fito daga akwatin sirrin shi.

     'Barka da dare!'

    "Barka dai sir!"

Maganar shi da amsata kenan bayan na ɗan ja lokaci kafin na buɗe saƙon, gudun ya gano zumuɗin da nake yi da ganin maganar shi. 

 "Ba ki yi bacci ba ashe?"

"I, yanzu dai zan shige"

     Na ba shi amsa daidai da tambayar shi, kafin ya sake jefo mini wata tambayar na amsa masa. 

  "Ya jikinki?"

"Alhmadullilah! Na ji sauƙi sosai."

"Allah ya ƙara lafiya"

"Amin Ya Rahman!"


Shiru ya ratsa tsakanin maganganun. Har na bar akwatin sirrin shi na koma status ina kallo sai ga wani saƙon ya jefo mini, wanda na hango abin da ya ce tun a saman sanarwar da ake yi mini ta shigowar saƙon.

   "Yaushe za ki koma aiki?" 

   Ɗan jim na yi kafin na ba shi amsa da cewa, "Laraba in Sha Allah!"

"Allah ya kai mu". Ita ce amsar da ya ba ni kafin ya sauka. A gaban idona ya sauka online ba tare da ya jira mun yi sallama ba, haka kawai na tsinci zuciyata da ɓacin rai, saboda rashin jin daɗin hakan a raina. Shiru kawai na yi ina tunanin me ya sa bai jira mun yi sallama ba, a ƙarshe ni ma kashe wayar na yi na gyara kwanciya. Da tunanin shi na kwana a raina, tare da guntayen mafarkan da na yi da shi a cikin baccina. Waɗanda ba zan iya kawo ya ya na yi su ba, amma dai tabbas na gan shi a cikin mafarkina kuma a yanayi mai daɗi. 


    Abu kamar wasa wunin ranar zungur MD yana maƙale a zuciyata, domin ko na so kawar da tunanin shi sai ya dawo mini sabo. Ta kai minti ɗaya biyu sai na buɗe data domin kawai na yi katarin hango shi online, sai dai abin haushi tun daga saukar da ya yi bai sake hawa ba sai dare. A galabaice na ga daren saboda matsuwar ganin shi da na yi.

       Cikin sa'a bayan Isha ina hawa na hango shi, farincikin da ya lulluɓe ni ya sa na kasa ɗauke idanuwana daga kan lambar shi. Sannan tunatarwar da ake ta yi mini ta MD online ta ƙara rura wutar murna ta. Haka kawai na tsinci kaina da shiga Gallery na ɗauko hotona da nake ji da shi na ɗora a status, duk da hakan ba halina ba ne ɗora hoto a status. Amma zuciyata ta ƙawatu da saka shi cikin ɗoki da zumuɗi, mintuna a tsakani da ɗora shi na shiga duba saƙunan da ke ta shigo mini har lokacin tsakanin groups da private. 

     "Ma Sha Allah!"

Ita ce kalmar da ya yi mini comment da ita a jikin hoton. Murmushi na yi a raina ina faɗin 'Dama ta samu' Sannan na yi reply da "Na gode Sir"


    Shiru bai sake cewa da ni komai ba bayan ya duba saƙon, kawai sai na ji ina sha'awar gaishe shi. 

"Ina wuni?" Ita ce tambayar da na yi masa ƙirjina yana bugawa, saboda har raina ina jin kaina tamkar wata mara gaskiya.


 "Lafiya lau ya ƙarfin jikin?"

"Alhmdulillah!"


Daga haka kamar ba zai sake ce mini komai ba, sai na hango ya sake cewa, "Gobe sai offis ko?"

      Cike da jin daɗi na amsa da, "In Sha Allah!" 


     "Your welcome!"


Yana gama faɗar hakan ya sauka, na yi reply da "Thanks!" Amma har sha biyun dare ta wuce bai dawo online ba balle ya ga godiyar da na yi masa, na ji matuƙar haushin hakan, a raina na ce,

     'Wai shi bai san babu kyau ana tsaka da magana a sauka ba a sanar ba?' 

 Tsaki kawai na yi saboda ya ɓata mini rai ba kaɗan ba, sai da na nutsa cikin tunani na hango rashin yi wa kai adalcin da nake ƙoƙarin yi. Sai kuma na dawo faɗin, "To ma ni ina ruwana da shi wai? Ummh!" Shiru na yi kawai ina ta bai wa kaina laifi, a kan damuwa da wanda bai dace na damu da shi ba, har bacci ya yi awon gaba da ni. A cikin baccin ma na yi ta ganin fuskar shi yana mini murmushi. 


     Safiyar Laraba na tashi cikin kuzari da ƙarfin jiki, saboda magungunan da na sha sun taimaka mini wurin rage mini ciwon da nake yi. Sannan a gefe ɗaya kewar ofishina da ɗokin ganin MD ya saka ni gaba, saboda ina ji a raina tamkar wannan ne karo na farko da zan fara zuwa wurin aiki. 

      Kwalliya na yi sosai cikin shiga mai fisgar zuciya, sannan na feshe jikina da turaruka masu ƙamshin daɗi. Jakata na saƙala a kafaɗa, sannan na saka yarana gaba muka fito gidan suna ta yaba kyawun da na yi musu a ido. Inda Haidar yake wasar baki ya ce, 

     "Kin yi kyau sosai Mama. Ko wurin biki za ki je idan kika dawo aiki?" 

    Murmushi kawai na yi masa sannan na ce, "Kai na yi wa kwalliyar nan duka domin ka ji daɗi Yarona" Haidar ya yi tsalle yana faɗin "Gobe ki yi wata Mama, zan siyo miki yalo da kuɗin tarata". 


Ummu Salma ta maka masa harara tana faɗin, "Daina murna yaro ba don kai kaɗai aka yi ba har da mu". Yana yi mata yelum muka shiga adaidaita sahu, Iman ta riƙo hannuna tana murmushi ta ce "Kin yi kyau Mama" Cike da jin daɗi a zuciyata na rungume su duka ina faɗin, 


"Na gode yarana! Ubangiji ya yi wa rayuwarku albarka, kuma ya ƙara shirya mini ku..." Nan take muryata ta fara rawa saboda ƙwallar da ta cika idanuwana.

 

"Amin" suka ce, sannan  suka dinga yi mini surutu kala-kala, tare da ba ni labarin bulalar da za a yi wa 'yan latti a makantarsu, har muka je bakin gate ɗinsu aka ajiye su. Kuɗi na ƙara musu domin su dawo gida saman abin hawa, kada su biyo sayyada kamar yadda suke yi kullum. Godiya suka yi mini dukansu suna mini bye-bye har suka shige, sannan mai adaidaitan ya juya da ni zuwa ma'aikatarmu. Inda nake ji a raina tamkar wannan ne zuwan farko da na fara yi a wurin aikin nawa. Saboda sauyin da na samu tsakanin wancan zuwan da nake yi da wanda zan yi a yanzu. 





Shin me zai faru a gaba a kan wannan canjin na Zaituna?🥲 Ni dai ba za a ji mutuwar Sarki bakina ba🏃🏻‍♀️


No comments

Powered by Blogger.