Abokin Aikina Book 1 Page 35

 


TALATIN DA BIYAR .*


        "Lafiya!? Me ya same ki!?" 

      Abin da na fara faɗa kenan a hargitse tun kafin na isa inda take. Tana gani na da ta tarye ni da gudu ta faɗa jikina, tare da

rushewa da wani sabon kukan ya sa jikina kyarma.

      Domin ko ni rabon da na saka hannu na dake ta har na manta, saboda tana ƙoƙarin barin abin da duk ta san ba na so,  balle ta yin abin da zan dake ta a kansa. Haidar ne kawai yake shan duka a wurina, don ko Iman miskilancinta kawai yake sa na dake ta idan na saka ta aiki tana jan jiki.

      Jikina na ɓanɓare ta ina faɗin, "Faɗa mini me ya faru?" Cikin shesshekar kuka ta ce, "Abbanmu ya dake ni"


     "Me kika yi masa?" 


 Ƙirjina yana bugawa na yi maganar saboda sabon ɓacin ran da ya ziyarci zuciyata. 

      "Girki na zo zan ɗora amarya ta ce ba zan ɗora shi ba, ni kuma ganin kin ce na yi kafin ki dawo ya sa na ci gaba da yi. Ban san ya aka yi ba ina tsaka da kwasar abincin na ji muryar Abbanmu yana ta zagi na. Shi ne ya same ni a kitchen ɗin yana ta dukana, kuma ya ɗauke abincin duka ya ce ba za mu ci ba tun da amarya ta yi girki shi kowa zai ci."

 

     "To fa! Abin har ya kai can?" 

       "Har ya wuce ma! Kuma wallahi matuƙar kika sa ta raina Barcy sai na ci uwarta a cikin gidan nan."

      Zancen Mukhtar kenan a sama yana ba ni amsar tambayar da na yi wa kaina cike da mamaki. Na saki hannun Ummu Salma na tarye shi gaba da gaba na ce,

      "Sai dai ka ci ubansu waton kai kenan! Don wallahi daga kai har wannan ƙanjamammar amaryar holoƙon da kake tinƙaho da ita; kun yi kaɗan ku ci zarafin yarana ba bisa haƙƙinsu ba. Abinci da ta dafa kuma ni na ba ta umurnin dafawa, saboda ba zan sake zama wata ballagaza tana hora mu da yunwa ba."

      "Ke kika ba ta umurni Barcy kuma ta hana ta, saboda tun kafin su dawo gidan ta yi girki. Kuma shi za a ci dole don tuni na kyautar da wanda ta dafa."

     Baki a sake nake bin fuskarsa da kallo saboda mamakin zancensa na 'ke kika saka ta Barcy ta hana'.

      "Waton ita Barcyn ce za ta dinga ba mu umurnin abin da za mu yi a gidan da wanda za mu bari?"

      "E! Saboda ni ce amarya kuma har yanzu ina cikin kwanakin girkina. Ki bari idan girkin ya dawo hannunki ki yi duk abin da kike so babu ruwana. Amma yanzu kam babu wanda zai ɗora girki a cikin gidan nan bayan wanda na dafa."

      Martanin Barira kenan tana girgizar jiki tare da riƙe ƙugu. Ta so ba ni dariya amma na fuske na ce,

     "Sannu shafaffiya da mai jikar sarauniyar Ingila 'yar gidan Sarki Macciɗo. To na rantse da Allah zan yi bikin watan cin ubanki a cikin gidan nan. Ko ki fita sabga ta da yarana; ko na nuna miki na fi ki sanin makamar iskanci da rashin mutunci. Abincinki kuma wallahi daga ni har yaran ba za mu sake jiransa ba, ke da cin abinci ya kawo gidan ki buɗe ciki ki yi ta zubawa, nawa kaso da na yarana duka mun bar miki. idan kin ƙoshi ki miƙa saura gidanku don na san suna da buƙata."


   Baki a sake take kallona tare da cizon yatsa tana faɗin,

 "Kai kai kai!"

     Kansa na juya ina faɗin,

 "Kai kuma mijin ta ce! Namijin ho-ti-ho! Ɗankwali ya ja hula! To ka sanar da ita babu kwanakin girkin kowa a kaina. Idan ma akwai duka na bar mata don haka ku sake wa 'ya'yana mara su ji daɗin fitsari. Kuma daga yau abincinmu daban za mu dinga girkawa, idan ka ji tsoron Allah ka ba mu namu haƙƙin. Domin ka rage wa kanka guzurin mugun bugun da Mala'iku za su yi maka a ranar lahira. Idan kuma ka bijire kamar yadda ka yi a baya, ina maka albishir za ka girbi duk abin da ka shuka khairan ko sharran. Na zare hannuna a cikin sha'anin girkin matarka, ni ma daga yau babu ruwanta da duk abin da za mu ci ko mu sha, a cikin gidan nan ni da yarana. Saboda ba za mu zauna tana gasa mana aya a hannu ba saboda abinci."

    " Ina ƙare faɗar hakan na yi gaba zan shige ɗakina, sannan na yi saurin juyowa ina faɗin, 

       "Gass nawa ne, ni na saya da kuɗina, repelling ma ni nake yi ba wani yake yi mini ba. Daga yau kada a sake taɓa mini kaya ko da ɗora ruwan zafi ne!"


     "Wallahi ni kuma ba zan yi girki da itace ba!"


     Abin da Barira ta yi hanzarin faɗi kenan tana murguɗa baki. Saboda Ummu Salma ta faɗa mini ita ce ta nuna mata yadda ake amfani da shi. Lokacin da take girkin tana 'yan waƙe-waƙen farinciki, lokacin da wata ta kira ta a waya baki a sake take faɗin,

     'Ke yarinya na wuce nan! Sabod Allah ya kawo ni gidan arziƙi, inda ba zan sha wahalar hura wutar ice ba. Gass cooker Hajiya shi nake girki da shi yanzu haka har na kusa gamawa... Ja can yarinya! Allah dai ya ba ku irin tawa kawai, don ni na tako arziƙi na wuce da sanin ku ƙananun ƙwari.'


    Tuno labarin na yi murmushi mai sauti sannan na ce da ita, "Wannan kuma mijinki za ki faɗawa ba ni ba!"


      "To ni ko idan dai da ice zan dinga girki, sai dai kada kowa ya ci abinci a gidan nan, daga ni har shi wallahi."


     "Kanku ake ji!"


Kafaɗa na ɗaga, sannan na juya na shige ɗaki yarana suka biyo bayana, Haidar na kalla raina a ɓace saboda yadda ya zama kalar tausayi. kuma na sani ba komai ba ne face yunwa don ko kaɗan bai da haƙurin ci.

     Jakata na ajiye da sauri na nufi kitchen ɗin, dole na yi tsaye ina wassafa abin da zan yi a lokacin. Saboda komai na kayan abinci an kwashe babu komai na sarrafawa, kuma na san ina da sauran Indomie da kayan tea waɗanda ni na saya da kuɗina, ba waɗanda Mukhtar ya kawo ba a daren da aka kawo Barira. 

     Amma duka an haɗa an kwashe domin a nuna mini iyakata. Na fito kitchen ɗin cikin ƙoluwar ɓacin rai na ƙwala wa Haidar kira, umurni na ba shi ya je gidan Maman Taufiƙ ya ce, na ce ta zuba musu abinci su ci shi da Iman.

     Sannan na koma ɗaki na ɗauki kuɗi na fice tamkar wata zararriya, saboda tsananin ɓacin ran da nake ciki. Adaidaitasahu na hau kai-tsaye ta ajiye ni shagon da nake siyayya, na ɗauki duk abin da muke da buƙata tsakanin abin kari da na girki har da rabin buhun shinkafa.

      ATM ɗina na bayar ya zuƙe kuɗin da ke ciki tas, sannan sauran da ya biyo ni na ce da shi mu tara ƙarshen wata. Don a lokacin kwanaki ne kawai suka rage a yi albashi. 

       Cikin Napep aka loda mini kayan na nufi gida. Inda na taras da Mukhtar yana ta bala'i har da kumfan baki, a kan na je roƙon abinci a wani gida bayan ga wanda Barira ta dafa.

     Ƙanzil ban ce da shi ba, illa yaran da na tambaya sun ci abincin suka ce da ni sun ci har sun ƙoshi. Sanyin daɗi na ji ya tsirga mini sosai a raina, saboda ganin kular da ta zubo musu abincin na tabbatar da zai wadace su.

      Tuwon garin masara na fara yi sannan na kaɗa miyar kuka, saboda ban da kuɗin nemo cefanen wata miyar bayan kukar da nake da ita.

      Duk da babu ƙiren nama ko kifi ta yi daɗi sosai, don ta sha daddawa da waken da na kwankwatsa cikin kayan yaji, wanda nake amfani da shi a wasu lokutan, a watsa a matsayin naman miya. 

Ban samu damar yin sallar Zuhur ba sai da aka yi kiran Asr, saboda ina gudun na bar girkin Mukhtar ko Barcynsa su yi mini ganganci.

     Abincin na kwashe duka a kula na kawo ɗakina har miyar, na ce da yaran su ƙara abincin kafin su tafi makaranta. Ummu Salma da Iman suka ce da ni sun ƙoshi, suka fara shirin makaranta Haidar kawai ya ce bai ƙoshi ba, na zuba masa sannan na yi arwala na yi sallah. 

      Ruwa na fara watsawa sannan na fito cikin sauri, saboda surutun da Ummu Salma take yi wa Haidar a kan ya ja sun yi latti. Don huɗu da rabi har ta gota saɓanin dokar makarantar da ake zuwa ƙarshe uku da rabi.

       Gani na ya sa suka fice shi ma ya bi su da gudu yana faɗin su tsaya masa. Ina tsaka da shafa mai a jikina Mukhtar ya faɗo ɗakin kamar an jefo shi yana faɗin,


       "Wai ke wace irin mace ce da ba ki ƙulla alheri sai sharri!?"


       "Koya na yi a wurinka!"


Na faɗa kaina tsaye ina ci gaba da shafa mai, ba tare da na kai idanuwana inda yake ba. 

       "Ni duk abuna, ban taɓa hana sunnar ma'aiki ba! Ke kuma ƙiri-ƙiri kina ƙoƙarin hana abin da Allah ya halasta. Don kin ga yarinya tana jin maganarki shi ne kika hure mata kunne a kan abin da take so. To ta Allah ba taki ba wallahi! Don aure ne ko kin ƙi idan Allah ya nufa za ki ji kunya."

       "Shi kuma wannan soki-burutsun daga ina ya fito? Da kake tayar da jijiyoyin wuya kamar wani zautacce!"

      

     "Da komai ma za ki iya siffanta ni da shi don ba yau kika fara ba, amma auren Sajida da Malam Aminu kamar an yi an gama ne! Ki so ko kada ki so duk ɗaya don babu haɗin dangin iya ke da ita balle na Baba. Saboda tun kafin ya je wurinta sai da ya fara yi mini zancen, kuma Ni na ba shi lambarta da hannuna saboda na gamsu da haɗinsu. Don haka kin yi kaɗan ki hana sunnar ma'aiki a kan wani guntun dalilinki na banza."

      "Wannan kuma ku ta shafa babu ni a ciki. Amma duk wanda ya ƙi ji ba zai ƙi gani ba."


   Zancen da na gama faɗa kenan ina saka kayana, saboda mamakin yadda aka yi maganar ta fito. Da kuma wanda ya faɗa masa ni ce na hana Sajida kula Baban Taufiƙ.


     "Don girman Allah ki ce da ita idan aka kai Sajida kada ta bar ta da rai ta kashe ta tun a daren farko!"

      Maganar da ya faɗa kenan a fusace yana nuna ni da hannu tamkar ya tsokale mini ido. 

      "Ohon muku! Ko a jikina, don babu ni a cikin kashin balle na kwasa." Na yi maganar tare da ɗora haƙarƙarina a kan gado. Saboda jikina ko'ina ciwo yake yi mini duk da wankan da na yi.


     "Na dai faɗa miki daga yau ki zare hannunki a cikin auren nan!"

       "Ummhh! Kanka ake ji!" 

 Data ta na kunna ina duba saƙonni har ya gama bambamin da yake yi ya fice. Zuciyata cike da tunanin abin da ya janyo maganar har aka saka ni ciki. Don na san Sajida ba za ta faɗi yadda muka yi da ita  ba.

     Kasa haƙura na yi har sai da na kira ta a waya, raina babu daɗi na ce da ita,

      "Ya kuka yi da Baban Taufiƙ?"

 'Wallahi Aunty na faɗa masa gaskiya. Kuma ya aminta da zancen har mun yi sallama da shi a kan ya janye. Me ya faru halan?'


      "Mukhtar ne ya zo yana wasu surutan da ban san ina ya jiyo su ba, wai na hure miki kunne komai na ƙi idan Allah ya nufa zan ji kunya."


     'Gaske na ji suna waya da Mama tana ta faɗa. Ashe zancen ne yake faɗa mata. To wallahi wannan munafukar matar tasa ce ta faɗa masa yadda muka yi ni da ke. Saboda lokacin da muke yin maganar tana falon har ta yi waƙa.'


      "Eeeee! Tabbas ita ce! Domin kuwa biri ya yi kama da mutum!"


     'Ki bar ta kawai Aunty! Zan zo har gidan na ci uban shegiya. Ba ta san daman can haushin ta nake ji ba.'


     "Ki ƙyale ta kawai da ni take zancen! Da sannu sai na koya mata hankali a cikin gidan nan."


        'Ke da wa kike waya? Idan mai hure miki kunnen ce ki faɗa mata na ce; ta Allah ba tata ba wallahi...Ni dai Mama don Allah ki san me kike faɗa haka kawa....'


     Tsinke kiran kawai na yi tare da sauke ajiyar zuciya, saboda zancen Yaya Maimuna ba ƙaramin ƙona mini rai ya yi ba. Duk da daman can na san tana adawa da ni tun lokacin da na tuɓure, a kan ba na son zama da Mukhtar sai ya sake ni. Tun daga lokacin ko gaishe ta na yi sai ta nuna mini zallar ƙiyayyar da take yi mini. Bayan zagi da cin zarafin da take yi mini a bayan idona suna dawo mini. 


      Kwance nake kan gadon ina ta juya abin cikin raina, tare da rikicin da za a yi muddin Maman Taufiƙ ta san da labarin. Har su Ummu Salma suka dawo ban tashi daga kwanciyar ba, ba su jima da shigowa ba aka yi kiran sallar magrib. 

     Saboda punishment ɗin da aka ba su makaranta a kan lattin da suka yi. Iman sai ajiyar zuciya take yi saboda tambon bulolin da suka sha sun fito raɗau a tsintsiyar hannunta.

      Da ƙyar na shawo kanta ta daina kukan, don daman can ita raguwa ce. Ko kaɗan aka taɓa lafiyar jikinta sai ta yi raki balle an saka bulala an dake ta.


     Sai da muka yi sallah dukanmu, sannan muka zauna zaman cin abinci ni da su a cikin ɗakin. Bayan sallar Isha muka koma falo muna kallo, Barira ma tana ta wayoyinta da mutane tana shewa. Bayan zagin da take kamfatowa iri-iri tana sauke wa ƙawayenta.


     "Ke shegiya! Gobe ki zo akwai sabuwar chepter...Sosai ma ke dai ki zo kawai akwai labarai...Yawwa 'yar gari ki zo da kayan duka mu ɗan kora an kwana biyu ba a haɗu ba."


     Maganganunta sun saka jikina sanyi, saboda tunanin yarana da za su dawo ba na gidan. Kai-tsaye wata sabuwar idea ta zo mini, na yanke hukuncin tura su wurin Ummata goben. Gudun na taras da tashin hankalin da ya fi na yau, kuma ba zan juri rainin hankalin kowa ba a kan yarana.

      Matsayar da na kai kenan wadda kuma na kwana da ita a cikin raina. Da kayansu na fita na miƙa wa Najib tare da yi masa kwatancen gidan Kawu Sale, sannan muka rabu da zummar idan aka tashi ya kai su gidan. Zuciyata wasai saboda ganin na kashe gobarar da take ƙoƙarin tashi ta ƙone zuciyata da ta yarana. 


No comments

Powered by Blogger.