Abokin Aikina Book 1 Page 24


 *ASHIRIN DA HUƊU.*


         _Miƙewa ya yi ya shige toilet, a gurguje ya yi wanka ya shirya. Ina nan inda ya bar ni kwance ko motsin kirki na kasa yi, saboda tsabar takaici da baƙincikin da ya turnuƙe mini zuciya. Wurina ya zo yana faman murmushi ya sauke mini kiss a goshi, sannan ya nufi hanyar fita yana faɗin,_

        "Ni zan tafi Makaranta, zan aiko da cefane." 

          _Murmushin yaƙe na yi masa ya fice yana yi wa Ummu Salma bye-bye, wadda ke ta wutsil-wutsil da ƙafafuwa tana tsotson hannu. Shiru na yi ina tunanin abin a raina, a ƙarshe na miƙe  babu kuzari na tsarkake jikina ina jera tsakin haushin wanka ba tare da na mori komai ba._

      

****

_Haka rayuwa ta ci gaba tafiya kullum abin yana damuna a zuciya, ga shi ina jin kunyar sanar da shi meke damuna balle na yi masa bayanin abin da yake yi mini ba na jin daɗin shi. Saboda kunya da kuma nauyin ta yadda zan fito masa da abin da ke zuciyata, amma a raina kullum muka haɗa shimfiɗa sai na ji kamar na kuwata don haushi da takaici. Saboda ko kaɗan bai damu da nemar mini gamsuwa ba, da ya tsiyayar da ruwansa cikin minti biyu, uku zuwa biyar ya gama. Kuma babu wata wasar kirki da yake yi mini balle na ɗan rage zafin abin da ke damuna, ga shi da yawan buƙatuwa a lokacin kai-da-kai yake nema na kuma da buƙatarsa ta biya shi kenan._ 

       _Haka ma dangane da kayan ɗakina babu wani tarnaƙin da ya fuskanta,  saboda na bi na toshe duk wata ƙofar da za a ganin laifin Mukhtar. Domin da labarin canjin kayana ya je kunnen Umma, ta kira ni tana faɗan me ya sa aka canza mini kayan ɗaki ba tare da na sanar da ita ba. Na ce da ita ta yi haƙuri saboda ba na so ta yi mini faɗa shi ya sa ban sanar da ita ba, maganata ba ƙaramin ɓata wa Umma rai ta yi ba. Saboda faɗan da na ce ina gudu ta yi mini shi ta balbale ni da shi tamkar ta kamo ni cikin wayar ta yi ta jigba. Ban da haƙurin da nake jera mata babu abin da nake yi a lokacin, saboda jikina ya yi sanyi musamman da ta nuna don ba ta isa da ni ba ne shi ya sa ban yi sanar da ita ba._

       _Ranar da ta zo ta ganar wa idanuwanta kayan, da ɓacin rai ta fice gidan tare da yi mini kashedi a kan; Duk lalurar da ta taso mini a gaba kada na neme ta. Saboda na sanar da ita wata lalura ce ta sa na sayar da kayan dole ba don na so b, ta tambaye ni to me na yi da kuɗin. Na fara kame-kame haushi ya sa ta kwaɗa mini mari tare da nuna ni da hannu ta ce,_

      "Daga yau ki zamo uwar kanki da uban kanki, domin na zare hannuna a cikin duk wata buƙatar da za ta taso miki a gaba. Tun da har kina iya sayar da kayanki ina cikin gari ba tare da kin sanar da ni ba. Ke ko ba na garin nan idan kina mini kallon daraja ba za ki rasa ɗaga waya ki kira ni ba. Don haka yanzu na yarda kin ishe kanki, ki je ki yi duk abin da kike so babu hannuna babu ƙafata, balle abin da zai fito daga aljihuna."

       _Na yi kuka sosai ranar, saboda fushin da ta yi da ni, ya fi komai tsaya mini a zuciya. Amma duk da hakan bai sa na ji haushin Mukhtar dangane da abin da ya yi mini ba, saboda na gamsu da abin da ya sanar da ni don a lokacin ma har ya fara zuwa makarantar. Kuma na sa a raina idan ya zamo wani abu ta sanadin karatun ita ma za ta ji daɗi, a lokacin zan sanar da ita yadda kayan suka yi na san za ta ji daɗi, kuma za ta yaba mini a kan rufin asirin da mijina ya samu ta sanadina._


      _Akwai wata matashiyar budurwa mai suna Jamila, wadda ke cikin unguwar kuma muke maƙotaka da gidansu. Tana shigowa sosai gidan saboda ƙaunar Ummu Salma da take yi, kullum tana hannunta na yi ta aikina tana yi mata wasa ko ta goya ta. Wani lokaci kuma har aikin gidan tana taya ni don ba ta da ƙiuya ko kaɗan, hakan ya sa na saki jikina da ita sosai tamkar ƙanwata uwa ɗaya uba ɗaya. Ba na baƙincikin ba ta komai daga na ci har wanda za ta je da shi gida bayan na amfanin rayuwa._

     _Matsalar da na fara fuskanta dangane da zaman da take yi da ni; Yawan damuwa da lamurranta da Mukhtar yake yi, ita ma idan ya zo gidan idanuwanta a kan shi ko ƙyaftawa ba ta yi. Sai ta ga ina haɗe rai sannan za ta shiga taitayinta._

      _Ba na manta watarana yana tsaka da cin shinkafa da wake, ya shiga zuzuta yajin yana faɗin,_

        "A gaskiya wannan yajin ya yi mini daɗi, ke kika daka shi kuwa?"

       "Jamila ce ta daka. Kuma yadda nake dakan yajin kullum haka na sa ta yi mini."


       "To gaskiya ta samo shi da kyau."


       _Ban sake cewa da shi komai ba, duk da ban ji daɗin yabon da ya yi ba. Amma ban kawo komai a raina ba, sai da na nutsa nazari sannan na tuna ai ya shigo ya taras da ita tana dakan yajin, to kuma me ya sa ya tambaye ni bayan ya san ita ce ta daka. Haka kawai na tsinci kaina da ce masa,_


      "Yanzu shi dakan yaji har wani abu ne mai girman da za a yi ta zuzutawa haka?"


       "Allah ya ba ki haƙuri! Daɗin shi da na ji ne shi ya sa na yaba."


       "To ba na son yabon tun da ba a yi maka dole sai ka yi ba, idan kuma ita kake so ka jinjina ma to ka bari idan ta zo gidan ka yi mata godiya. Ko kuma ka same ta gidansu idan abin ya dame ka."


      "Can kika nufa kuma? To ni kin ga fita ta Allah ya huci zuciyarki!" 


     _Ya fice ya bar ni ina aika wa robar yajin harara tamkar shi ne nake kallo. Tun daga lokacin na hana ta taya ni duk wani aikin da ya shafi girki ko abin da za a ci. Sai dai ta kula mini da Ummu Salma ko shara da wanke-wanke, amma na katange ta da yin abin da Mukhtar zai yaba saboda masifar kishin shi da nake yi. Wanda in da ina da iko a lokacin, kallon wata ma ba zai yi ba balle ya hango kyawunta, don ko waya na ji yana yi cikin siririyar murya sai na ji haushi da kishi ya kama ni, kuma sai na zargi da wata yake yi. Wani lokaci ma har kiran waɗanda suka yi wayar yake yi domin na ji gaskiya a bakinsu, musamman idan ya yi ta rantsuwar ba da wata yake ba na ƙi yarda._ 

      _Akwai watarana da na ji yana waya cikin toilet yana kashe murya, na je jikin toilet ɗin na lafe ina sauraron hirar da yake yi da wata. Raina a ɓace na dinga dukan ƙofar ina faɗin sai na kashe ko wace ce yake waya da ita cikin ɗakina. Hankalin shi a tashe ya fito yana ta rantsuwar babu macen da yake waya da ita. Idan kuma ban yarda ba sai ya kira mini wanda suke wayar na ji da kunnena. Ban ce da shi komai ba sai hucin da nake yi riƙe da ƙugu ina aika masa harara, ina sauraron ringing ɗin da wayar take yi saboda ya saka ta hands free domin na ji komai._


"Hello! Don Allah da kai na gama waya yanzu ko ba da kai ba?"


"Da ni, me ya faru ne?"


"Madam ce daga jin ina waya ta fara zargin da wata nake waya."


"To idan ma da wata kake yi ai ba haramun ba ne! Don kai mijin mace huɗu ne kuma kana da ikon ka yi abin da kake s..."


      _Haushin da ya turnuƙe ni ya sa na wafce wayar na buga ta ƙasa, sannan na durƙushe ƙasa ina kuka cikin ɗaga murya. Wayar shi kawai ya tattara ya fice yana surutan faɗin sai zargi ya kashe ni, tun da bai isa ya yi waya ba sai na ce da wata yake yi._

       _A irin wannan lokacin ne aka yi ƙaramar sallah, ni da kaina na ba shi shawarar ya yi wa Jamila ɗinkin sallah. Saboda yadda take ƙoƙarin rainon Ummu Salma ba ƙaramin jin ta nake yi a raina ba. Amma ya fitittike a kan shi bai da kuɗi ba zai yi ba, na ciyo bashin zane biyu na kai aka ɗinka wa Jamila na ba ta tana ta jin daɗi. Godiya ta yi mini sosai tare da addu'o'i iri-iri gare ni, cikinsu kuwa har da zama ni kaɗai a gidan Mukhtar iya rayuwa. Sosai na ji daɗin addu'o'inta ina ta wasar baki saboda ganin ta gama mallaka mini komai a rayuwa, tun da ta yi mini fatan zama da Mukhtar ni kaɗai babu kishiya._

      _Da dare Mahaifiyar Jamila ta zo fuska faram-faram na tarbe ta cikin fara'a muka gaisa. Ta ce da ni yana nan na ce da ita ba ya nan, zama ta gyara tana wasar baki ta ce,_

      "Don Allah idan ya zo ki yi masa godiya, mun ga abin arziƙi mun gode sosai Allah ya ƙara buɗi."

 

      _Sakato na yi ina dariyar yaƙe, saboda mamakin godiyar da take yi masa bayan ni na yi wa Jamila ɗinki ba shi ba. Na kasa shanye mamakina iya ni na ce mata,_


     "Ai ni na yi wa Jamila ɗinki ba shi ba."


      "E, na sani kuma mun gode sosai, amma idan ya zo don Allah ki yi masa godiya ki ce mun gode sosai Allah ya saka da alheri."


     _Murmushin yaƙe kawai na bi ta da shi tare da faɗin "To" Saboda raina bai yi mini daɗi ba ko kaɗan. Musamman da na fahimci akwai abin da take ɓoye mini wanda ba ta so na sani._

       _Da ya dawo na sanar da shi saƙon Mamar Jamila, baki kawai ya washe yana sosa ƙeya. Amma bayan hakan bai ce da ni komai ba balle na gano inda zaurancen su ya sa gaba. Na kasa danne zuciyata har sai da na ce da shi,_

       "Aikin me ka yi musu da har suke gode maka?"


      "Aiki kuma?"


          "E, don na san banza ba ta kai zomo kasuwa. Kuma babu yadda za a yi su yi maka godiya ba tare da ka yi musu wani abu ba."

        "To ki je ki tambaye su ki ji tun da abin ya dame ki."

  

       _Daga haka ya yi kwanciyar shi bai sake cewa da ni komai ba, duk da faɗan da nake yi masa a saman kai tamkar na dake ki. Saboda na rasa me zan yi na ji daɗi a raina, domin zuciyata ta kasa cire mini tunanin abin da ya ba su ban sani ba. Da ƙyar na saita kaina daga haukar kishin da nake yi masa_

       _Tun daga lokacin na fara jan jikina da Jamila, duk da ita ba ta nuna mini komai na baƙin hali idan aka cire kallon ƙurullar da take yi wa Mukhtar.  Ko shi da ta gano take-taken shan ƙamshin da nake yi mata ta rage a gabana, amma idan Mukhtar yana falo ta dinga sintiri kenan tana bi ta ƙofar ɗakin tana dawowa. Musamman a lokacin da Ummu Salma ta fara rigima, haka za ta yi ta yawo da ita tsakiyar gidan tana yi mata kurrrr! A cikin kunnuwa har ta yi shiru._


***

     _Zamanmu da Jamila ya miƙe har zuwa lokacin da Ummu Salma ta iya tafiya. Duk da kafin lokacin wani babban al'amari ya faru da ni, wanda har yanzun nan da nake ba da labari ban daina jin zafin abin cikin raina ba. Saboda Ummu Salma tana da wata bakwai na samu wani ciki, Mukhtar ya fito fili ya nuna mini ba ya son haihuwar cikin. Sannan ya yi ta ɗora ni a kan hanyar da za a salwantar da cikin ina jin tsoro, duk da ni kaina ba na son cikin saboda wahalar da nake sha, ga Ummu Salma ta fara ciwo kullum jikinta zafi rau ga afkin kukan da take hana ni shaƙat da shi. Dalilin hakan ya sa na ji ina son rabuwa da cikin kamar yadda Mukhtar yake ɗora ni a hanyar. Wani ɗan'uwansa ya nemo mai aiki asibiti, ya zo da shi har ɗakina na yi masa bayanin watannin cikin, sannan da halin da nake ciki dangane da wahalar da yake ba mu ni da Ummu Salma. Tare suka fice yana cewa da ni na kwantar da hankalina in Sha Allah za mu samu lafiya._

       _Da dare suka dawo tare da shi ya kawo mini wata ƙwayar magani ya ce na saka a jikina. Tare da yi mini bayanin cikin zai zube kafin safiya saboda ko wata uku bai rufa ba. Sai dai da a ce na san abin da zai biyo baya, da na fi son na haife cikin da azaba, takaici, fargaba da baƙincikin da na ƙumsa tsakiyar daren zuwa safiya._

       _Kamar yadda ya faɗa mini haka na aikata, lafiya lau na kwanta bacci har ina tunanin ko dai cikin ba zai zube ba. Kwatsam tsakiyar dare ina tsaka da bacci na ji kamar an saka wuƙa an yanki marata, babu shiri na farka a firgice dafe da ƙuguna da nake ji tamkar zai rabe gida biyu. Kafin bayana ya karɓa da luguden bala'in zafin da nake ji tamkar a raba ni da ƙugun na huta. Na fara buge-bugen hannuwa ina ƙwala masa kira ya tashi a firgice yana tambayar me ya faru. Na cije leɓe tare da baki saboda azabar da nake ji ba zan iya kwatantawa ba, sannu ya fara jera mini ba tare da na iya amsawa ba. Kwanciyar shi ya koma yana ta kallona bai koma baccin ba, saboda azabar da nake ji ta kai ƙololuwar da na kwashe tsawon lokaci ina fama. Cikin ikon Allah ina zaune tsakiyar ɗakin na ji wani abu ya fito jikina, nan take jini ya ɓalle mini tamkar an buɗe famfo. Ya taso yana yi mini sannu na ce da shi ya riƙa ni na tashi, ya fara ɓata fuska cikin ƙyanƙyami ya riƙa ni a lalace kamar ba ya so. Haushi ya sa na ƙwace hannuna na dafa ƙasa na miƙe da ƙyar abin ya faɗo daga cikin zanina zuwa ƙasa._

       _Babu shiri ya ja baya tare da yin salati saboda ganin abin da ya faɗo tamkar ɗan ƙadangare. Na yi toilet jini yana biya ta duk inda na taka. Jikina na wanke sannan na cire zanin na fito a daddafe saboda jinin da bai daina bin ƙafafuwana ba._

      _Always na linka na saka a tunanina za ta iya tare jinin, sannan na samu kuzarin saka wata riga na kwanta. Mukhtar ya shigo ɗakin yana faɗin, na tashi na gyara ɗakin shi ya jefa abin masai. Har ga Allah ban ji daɗin masan da na ji ya ambata ba, domin sai da ƙwalla ta zubo mini saboda wani tsoron Allah da ya shige ni. Banza na yi masa kamar ban ji me ya faɗa ba, saboda takaicin rashin imanin da ya sa muka aikata wa albarkar da Allah ya azurta mu da ita."_

     _Miƙewa na yi ina layi na koma toilet na wanke inda jinin ya ɓata, sannan na dawo ɗakin na gyara shi tas na fesa turaruka saboda ƙarnin jinin. Na koma na kwanta ina tunanin ƙyamar da Mukhtar ya nuna mini, ban san lokacin da bacci ya kwashe ni ba sai da asubar farin ana kiran assalatu marata ta karta. Nan take jini ya banke always ɗin da ke jikina yana ta ɓulɓulo mini gundali-gundali._


No comments

Powered by Blogger.