Abokin Aikina Book 1 Page 21

 


*ASHIRIN DA ƊAYA.*


        Mun tattauna sosai da Amina, tana sanar da ni matsalar Basiru mijin Sara. Da irin tataɓurzar da aka yi da su a lokacin da suke ganiyar rashin mutuncinsu. Bayan an tashi muka fito bakin ma'aikatar muka tsaya, da niyyar neman adaidaita amma muka buge da hira. 

      Amina ta kalli agogon da ke hannunta ta ce da ni, "Yau dai na yi missing ba a tsakura mini komai daga cikin labarin ba. Ga shi na matsu na ji yadda ta kaya a lokacin da kika shiga ɗakin, domin ina so na ji me ya ba ki tsoro wanda ya sa kika yi salatin da, har yanzu ban daina jin sautinsa cikin kunnuwana ba."

      Baki kawai na riƙe cike da mamakin sharotan da take ƙoƙarin yi, domin kawai ta yi mini daɗin bakin da zai sa na ɗora mata labarin, daga inda na tsaya ban shirya ba. Cike da zolaya na ce da ita,

     "To ko za mu tsaya ki ji sauran kanun labarin ne?" 

      Cikin sauri ta dawo daga bakin titin da ta nufa tana ƙoƙarin tare wani ɗan adaidaitan da zai wuce. "Wallahi in dai za ki ƙarasa mini labarin yanzu, to na yarda mu kai wata safiya a nan ba tare da na ƙosa ba."

       "Rufa mini asiri kada ki sa Mama ta zo har wurin nan ta ci ubanmu."


      Dariya muka fashe da ita dukanmu, kafin na shammace ta na shige adaidaitan. Da hanzari ta matso inda nake tana faɗin, "Ji nake kamar na biyo ki mu je tare wallahi. Domin har ga Allah matse nake da jin labarin nan, kamar na yi tsuntsuwa na dira tsakiyar ɗakin domin na ga komai ba sai na jira an sanar da ni ba."

      "Ai kuwa dole ki jira har lokacin da za a sanar da ke, don haka mu haɗu goben kawai Hajiya ko shi idan da rabon ki. Domin haka kawai ba za ki janyo mini fushin Mama ba. Tsautsayi ya sa a binciko mata inda nake ta ci kwakwata, ni kin ga tafiya ta mu kwana lafiya ki gaishe da my boy."

     Daga haka muka tafi muka bar ta a tsaye tana aika mini harara har da ƙwafa. Hakan ya sa ko da muka yi nisa ban rufe bakina daga dariyar da ta ba ni ba, sosai nake tsintar kaina cikin farincikin a duk lokacin da muna tare, domin tana ɗebe mini kewar 'yar uwa macen da na rasa kuma ƙawa makusanciya.

 

***

     Mamaki fal raina a lokacin da na shiga gidan na yi tozali da kayansu Ummu Salma tsibe , na bi kayan da kallo cike da tunanin me ya kawo jakunkunan su a ƙofar ɗakina. Duk da oyoyon da suke mini bai sa na ɗauke kallona daga kan kayan ba.

     Da sassarfa na isa bakin ƙofar ɗakinsu ina murɗa handle idona ƙur a kansu, tare neman ba'asin dalilin da ya janyo hakan, tambayar da tun kafin na furta ta fito da kanta cikin ƙwayar idona.

       "Mu ma ko da muka dawo mun taras da kayan a wurin. Kuma har yanzu Abbanmu bai dawo ba balle mu ji ko shi ne ya fito mana da su."

     Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi sannan na ce, "Ku ɗauko kayan mu je ɗakina, idan ya dawo mu ji me yake nufi."

       Da ƙyar na yi maganar saboda hadarin baƙincikin da ya taso ya rufe idona. Guguwar takaici ta sa ban iya ɗaukar komai daga cikin kayan ba. Domin har da katifunsu biyu tasu ita da Iman da ta Haidar.

     Sun shigar da kayan duka a lokacin da na kammala sallah, a kan kayan na ɗora idona saboda tunanin abin da yake nufi da abin da ya aikata. A take zuciyata ta hasko mini zallar manufar shi duk da bai faɗa mini ba, duba da kalaman barazanar da ya yi mini a ranar da ya tuna da haƙƙinsa da ke kaina.

     'Wallahi duk abin da ya biyo baya kada ki ga laifina. Ba dai kin hana ni haƙƙina ba? To ke kuma ki jira me zai faru cikin kwanan..'

      Maganar shi kenan da ta faɗo mini rai, kuma ta shiga kunnena tamkar a lokacin yake furta mini ita.

     "Waton aure zai yi?"

     Tambayar da na jefi kaina da ita kenan a fili, sannan wani murmushi mai sauti ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba, saboda tabbacin da zuciyata ta ba ni a kan hasashen da nake yi. Nan take wani sabon kuzari ya ziyarce ni, wanda ya kore rabin damuwar da ya haifar mini a lokacin. 

       Ummu Salma na ƙwala wa kira, ta shigo ido tsakar ka bayan ta amsa kiran, sallayata na shiga naɗewa ina cewa, "Zo mu saita kayan nan. Kafin lokacin makaranta ya yi."

     Da Mamaki ta bi ni da kallo wanda ya nuna tambayar da take son yi mini, ina mata 'yar dariya na ce, "A nan za ku dawo da zama dukanku. Don daman can ina ta so ku dawo nan mu dinga kwana tare. Kafin lokacin da Haidar zai ƙara girman da za a ware masa makwancinsa daban."

     Farinciki mayalwaci ya ziyarci fuskarta, ta fara murna tana ƙwala wa su Haidar kira bakinta har kunne, ko da suka shigo ta fesa musu labari suka hau ihu, domin alamunsu ya bayyana jin daɗinsu a kan sabon tsarin da nake ƙoƙarin zartarwa. 

      

      Tare da su duka muka gyara ɗakin tsaf komai muka tanadar masa a muhallinsa, duk da katifar Haidar ba ta samu wuri ba dole jingine ta muka yi. Saboda an laƙume ɗan filin ɗakin da katifar su Ummu Salma, sannan da jakunkunan kayansu. Don ma na cire wasu na saka a wardrobe domin a rage tarkacen kayan. 

      Saboda suna da sutura sosai domin ba na ɗaukar lokaci ban yi musu ba, musamman Haidar da ko kan hanya na zo wucewa na hango yadin da ya burge ni, sai na saka an yanka masa ko da iya kuɗin jakata kenan. Wani kuma idan ban da kuɗin, cewa nake yi a yanka a ajiye mini. Daga baya na dawo na karɓa tun a lokacin da yake cin yadi ɗaya, har yanzu da yake shekara bakwai ya fara laƙume yadi ɗaya da rabi.

      Su ma atamfa ɗaya nake saya a ɗinka musu su biyu, saboda Ummu Salma shekararta goma sha biyu, Iman ce mai shekara tara. Domin tsakaninta da Haidar babu tazara mai yawa, kuma yana da jikin girma, don ya kusa kamo tsawon Iman.


      Bayan sun tafi makaranta da murna, na shirya na nufi gidan maƙociyata Maman Taufiƙ. Saboda na yi sha'awar ganin ta kwana biyu ba mu haɗu ba, daman can makulli ke sa ina shiga gidan idan yara sun bar mata. Ita ma halin Mukhtar da zargin da yake yi mata, a kan tana zuga ni ya sa ta rage zuwa gidanmu.

     Da fara'a ta tarbe ni muka zauna murmushi a kan fuskata muka gaisa, ta kawo mini molt da ruwa a faranti, sannan da doghnut a gefe. Domin ɗabi'arta ce da wuya a shiga gidanta a fito ba ta karrama mutum da abin da take da shi ba. Su Ummu Salma har ɗokin suke yi na aiko su wurinta, domin ba za su fita hannu rabbana ba sai ta musu alheri ko da babu yawa. 

 Saboda kaf unguwar babu inda nake zuwa sai wurinta, haka su ma babu inda nake bari su je sai gidan. Ko shi iya aiken da ya kai su kawai suke yi su fito, saboda maigidanta kullum yana gidan. Sannan a gaban kowa ba ta shayin nuna masa ƙauna sai dai shi mutumin da ya zo ya ji kunya, saboda yaronta ɗaya Taufiƙ kuma ya yi shekara sha huɗu har yanzu ba ta sake haihuwa ba. 

     Rayuwarsu tana burge ni sosai, saboda ta yi dacen mijin ƙwarai kuma wanda ya san muhimmancin aure. Dalilin da ya sa ba ta gano matsalar Mukhtar a yadda nake sanar da ita, ta fi ɗora mini laifi a kan wasu abubuwa ko da ta gani da idonta. Ganin take yi rashin tattalin miji ne yake janyo mini abubuwan da ke faruwa. Kayan mata babu kalar da ba ta ba ni, amma sai dai na ajiye ko na kyautar don ni babu amfanin da za su yi mini. 


     "Kwana biyu kin ɓuya!"


  Maganar da ta yi mini kenan a lokacin da na gutsura doghnut ina taunawa. "Shirye-shiryen zuwan amarya muke yi. Shi ya sa kika ji ni shiru, ga kuma aiki da yake hana ni zama kullum ina zarya kan titi."

      Kallo mamaki take yi mini sannan ta ce, "Wace Amarya kuma?" 

      "Amaryar Mukhtar!"

Amsar da na ba ta kai tsaye kenan, murmushi a kan fuskata. Baki a sake take kallo na bayan  tagumin da ta rafka, dariya na shiga yi mata alamun ko a jikina illa tsabar farincikin da nake ciki. Wanda ya kasa ɓoyuwa har sai da ya bayyana kan fuskata.


     "Yanzu ke don Allah a kan auren Mukhtar kike wannan murnar?"

      "Sosai ma! To miye cikin ido ban da ruwa? Ai inda akuyar gaba ta sha ruwa, ko ta baya idan ta zo a nan za ta sha."

      "Hmmmmm! Kina wasa da lamarin maza Maman Haidar. Ke a tunaninki abin da ya yi miki shi zai yi wa wata idan ta shigo?"

      "Sosai ma kuwa! Don ƙwaryar sama ce take dukan ta ƙasa. Kuma ni wannan auren ma da ina da dama har sadaki ni zan biya masa. Domin kawai ya gano na fi shi farinciki da ƙulluwar auren."

       "Lalle da sauranki har yanzu Maman Haidar. Ai wallahi ni da na ga ranar da Amini zai yi aure, gwara na ga ranar mutuwata."

       Dariya ta suɓuce mini babu shiri, da abun ya yi mini daɗi ma har da bajewa na yi a kan kujerarta riƙe da ciki. Saboda zancenta ba ƙaramar dariya ya ba ni ba, domin zurfin da ta yi a kan sha'anin maza, ya nuna har yanzu ba ta san zafin duniya ba.

      Natsuwar dole na gayyato, saboda yanayinta da na ga ya juya zuwa kalar tausayi.         

      "Ko ni na samu mijin ƙwarai wanda ya san zafina, wajibi ne kuma dole na yi kishin abuna. Amma kuma ba zan zafafa kishina irin haka ba, saboda ba gare ni aka fara ba kuma ba za a ƙare kaina ba. Sannan shi ɗa namiji, a duk lokacin da kika zafafa kishinki a kansa, matuƙar ba ki yi dace da mai dogon nazari da hangen nesa ba. To zai yi miki kallon wata shashasha wadda ba ta san abin da take yi ba, ƙarshe ma ya ce ba kya son zaman lafiya, ko kin cika fitina da janyo abin da zai kawo muku faɗa. Saboda a lokacin idonsa a rufe yake da son auren, duk abin da za ki yi masa ba zai burge shi ba, matuƙar ba goya masa baya za ki yi a kan auren ba."  

        "Ai kuwa wallahi sai dai kada ya gani, domin ba zan taɓa goya masa baya ya yi mini kishiya ba. Cabɗijam! Allah kada ya nuna mini wannan ranar, don na san tun kafin lokacin auren ya yi zan mutu saboda mugun kishin Amini da nake yi. Shi ma ya sani ba zai taɓa zo mini da irin wannan zancen ba."


      Shiru na yi ina kallon ta, domin idan akwai naƙasunta da na sani duniya bai wuce kishi ba. Kuma ina yi mata uzuri saboda shaƙuwar da ke tsakaninta da Aminin mijinta. Wanda saboda tsabar so da shaƙuwar da ke tsakaninsu yake kiran ta Aminiya ita ma ta kira shi Amini.

      "Ni dai kam! Ko a kwalar rigata Maman Taufiƙ. Idan zai yi huɗu a rana ɗaya wallahi babu abin da zai ɗaga ni sama balle ya buga ni a ƙasa. Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka. Kuma wanda duk ya ce zai iya haɗiye gatari ya dace a riƙe masa ɓota."


      "Wallahi Zaituna kina ba ni mamaki, shin wai ba auren soyayya kuka yi da Abban su Haidar ba?"

      "Soyayyar gaske ma, irin ta bugawa ga jarida a yi talla. Amma yanzu, ƙiren sonsa ba na ji a cikin zuciyata, kamar yadda ko wulagawar shi na hango daga nesa, sai na ji haushin sa ya yi mini rumfa."


       "Anya ba namijin dare ne yake aurenki ba?" Tambayar da ta jefo mini kenan na ba ta amsa.


     "Idan ma shi ne ya burge ni, domin ya nuna zallar kishin da yake yi mini wanda ba ya son kowa ya raɓe ni. Domin ina da tabbacin zai ba ni kulawar da za ta gamsar da ni, kuma zai hana ni kukan kaɗaaicin da nake yi yanzu."

        "Hu'ummm! Kin yi nisa Zaituna, amma ni kam har abada ba na fatar Amini ya yi mini kishiya ko da a mafarki. Ke akwai wata da ta so zautar da ni a kan nacin da ta yi masa ya aure ta, don bala'i macen da yaranta har sun je jami'a. Wai a haka ta nace masa dole sai ya aure ta tun da mijinta ya mutu ya bar mata gado. Ai na rantse da Allah ranar da na gano, daga ni har shi ba mu yi bacci ba, asubar farin na bar garin nan na yi Kano. Domin gabaɗaya idona rufewa suka yi ba na hangen komai a lokacin face mutuwata. Abin baƙinciki kuma babu wanda ya goya mini baya a gidanmu, sai laifina da aka dinga gani ana ƙoƙarin nuna ya fi ni gaskiya. Sun kasa gano zafin da nake ji idan na tuno girman matar da manyan 'ya'yanta. Don akwai wata 'yarta da ta ci ta ƙoshi, wadda ko yanzu aka ce ta haifi yara uku ba zan musa ba. Amma wai a hakan take son Amini ya aure ta don baƙar zalama irin ta wasu ƙattin mata."



No comments

Powered by Blogger.