Abokin Aikina Book 1 Page 18

 


LAMBA SHA TAKWAS.*


         Nufo ni ya yi gadan-gadan yana ƙoƙarin haɗa jikin shi da nawa, cikin zafin nama na tura shi ya yi baya. Sannan na nuna shi da hannu cikin ƙololuwar ɓacin ran da ya ziyarce ni. 

      "Kada ka yi gangancin zo mini da wani sabon sanabe, don sanin kanka ne babu wata alaƙa da ta yi saura tsakanina da kai yanzu. Sawunka a likkafa ka fice mini daga ɗaki tun muna shaida juna, idan kuma ka fi so ka tunzura ni na yi maka aika-aika to ka sake zuwa kusa da ni."

        Kallo na ya tsaya yi na ɗan lokaci, kafin ya sake nufo ni yana dariya kamar bai ji kashedin da na yi masa ba. Janyo ni ya yi da ƙarfi na zille, nan take muka fara kokawa ni da shi, cike da ƙarfin zuciya nake ta hana shi abin da yake ƙoƙarin aikata mini. 

     Ganin da gaske ba zai samu haɗin kaina ba, ya dawo magana cikin haki yana faɗin, "Wallahi duk abin da ya biyo baya kada ki ga laifina. Ba dai kin hana ni haƙƙina ba? To ke kuma ki jira me zai faru cikin kwanan..."

       "Kai har kana da bakin faɗar wani haƙƙinka da ke kaina yanzu? Kenan ka manta tsawon lokacin da ka ɗauka ba tare da ka neme ni ba? Ko an faɗa maka kai kaɗai ne mai haƙƙi ni ko oho? To ka je ka ɗauki matakin kada ka yi sanya, idan kuma ka fasa wallahi ban gode maka ba. Mitsssss! Aikin banza tura agwagwa cikin ruwa."

         Na ƙare maganar a fusace saboda furutan shi sun sa na ji ya kai ni bango Ya jingine. 

     "Za ki gani!"

    Zancen da ya yi kenan ya ja rigar shi ya fice fuu tare da bugo ƙofar ɗakin da ƙarfi. Ƙofar na bi da harara tamkar idona zai faɗo ƙasa, sannan na je na saka makulli na rufe na dawo na zauna ina haki. Mamaki na shiga yi a kan rashin adalci irin na Mukhtar, saboda rabon da ya nemi ni a matsayin matar shi ta sunnah sama da shekara uku. Kuma duk na yi haƙuri na jure amma sai yanzu zai zo mini da guntun rainin hankali. 

         Wanda na sani idan da zan kai shi kotun musulunci take yanke za a raba aurena da shi, saboda iya cutarwar duniya ya yi mini kuma ya tauye ni da baƙar igiyar da yake tinƙaho da ita.  

      Daren ranar ma sai da na gamsar da kaina sannan na samu damar yin bacci cikin nishaɗi, saboda ya tayar mini da tsohuwar jarabar da kullum nake ƙoƙarin kawar da kaina kanta, tare da addu'ar samun sauƙinta a wurin Allah. 

        

      Da safe ma tun da ya fita bai dawo gidan ba, sai dare bayan mun shige bacci sannan na ji yana rufe gida, ban wani damu ba don daman can bai ɗaɗa ni a ƙasa ba. Haka ma ranar Lahadi bai zauna ba, don ko yaran bai bi ta kansu ba a lokacin. Saboda ba wannan ne karon farko da fara yi musu hakan ba, domin ya sha shafa musu laifina a duk lokacin da na samu saɓani da shi, don a baya ma ko abu ya siyo ba zai bai wa kowa ba ko da yaran sun gani. Haka zai cinye abin shi muna kallo ba tare da ya ba mu ba, tun yaran suna jin haushin abin har suka daina zuwa kusa da shi idan sun gan shi da leda. Saboda a can baya ma idan ta yi masa daɗi, miƙa wa ɗiyan 'yan'uwan shi yake yi Ummu Salma tana kallo ya hana ta. A tunanin shi ni yake yi wa baƙinciki don na ji haushi.

       

       Ranar Litinin tun da sassafe na tashi, na haɗa wa yarana abin kari sannan muka shirya tare da su muka fice. Ganin ɗakin shi a rufe ya sa na gano ya yi wurin aiki don ban san fitar shi ba. 

       Bayan na ajiye su makarantarsu, na ba su kuɗin tara da waɗanda  za su hau abin hawa idan aka tashi. Sannan mai adaidaitan ya ajiye ni wurin aiki bayan na nemi alfarmarsa, a kan idan lokacin tashi ya yi daga makaranta ya koma ya ɗauko mini su Ummu Salm. 

        Saboda akwai sanayya tsakanina da shi kuma sosai yake girmama mutuncina a zahiri. Ina tafe zuciyata cike da tunanin  riƙon shi a matsayin wanda zai dinga kai su Ummu Salma makaranta, kuma ya ɗauko su a duk lokacin da aka tashi. Da zummar idan an yi mana albashi na dinga biyan shi kuɗin shi gabaɗaya.

       Zancen zucin da nake yi ya katse a daidai lokacin da mutanen wurin suke ta yi mini ya ƙarfin jikin ina amsawa. Turus na yi saboda babu makullin ofishin a hannuna, domin a ranar Alhamis da na bar wurin tashin hankali bai sa na tsaya rufe offishin ba. Ficewa kawai na yi saboda kwata-kwata na manta kowa da komai, face neman hanyar da zille wa auren Mukhtar a idona. 

      Ofishin MD na nufa raina yana suya, saboda ba na farinciki da ganin shi saboda haushin shi da nake ji. Na yi wa kaina katanga da shi kuma na kwance ƙaƙƙarfar alaƙar son da na fara ginawa a tsakanina da shi. Kaina a ƙasa ina shan ƙamshi na ƙwanƙwasa masa ƙofa, 

     "Yes! Come in"

      Ita ce maganar da na ji ya faɗa na tura ƙofar kaina a tsaye na isa gaban shi. Ban damu da gaishe shi ba cikin haɗe fuska na ce,

 "Key za a ba ni."

      Ya miƙo mini yana ta rubutun shi ba tare da ya kalle ni ba, cike da haushi na fice saboda ganin ko-in-kular da ya yi mini. 

       Zama na yi bayan na zauna, ina nazarin abubuwa da yawa a cikin kwanyata. Sannan na fara duba files ɗin da na gani a saman teburina, na shiga aiki tuƙuru ba tare da na nemi ba'asin komai kansu ba. Saboda ina da masaniyar komai nasu, bayan lissafin da na shiga bugawa da calculator, ina ta rubuta adadin da na samu a wuraren da ya dace a jikin files ɗin.

         Turo ƙofar ofishin da sallamar Amina bai sa na ɗago daga aikin da nake yi ba, na dai amsa mata sallamar saboda ba na so ta katse mini aikin har sai na gama. 

      Tsawon minti goma tana zaune har na kammala aikin na ture files ɗin gefena. Tagumi na yi da hannuna biyu muna kallon juna muna murmushi, sannan na cire farin gilashin da nake sanye da shi ina faɗin, 

        "Sannu cika-aiki. Wannan sammako haka ba kya bari a kira ki?"

          "Gara dai na zo don zuwa da kai ya fi aike." 


      Dariya muka saka a tare sannan na jingina bayana jikin kujera ina ɗan juyawa a hankali. Murmushi ɗauke a kan fuskata na ce da ita, "A ina muka tsaya da labarin? Don na san kin fi ni sanin inda za mu tashi."

       Zama ta gyara sannan ta ce, "Abu mai sauƙi cire wando ta kai, mun tsaya ne a daidai inda cikinki ya kai wata tara haihuwa yau ko gobe. A lokacin da Abban  su Ummu ya yi miki laifin da ya so katse igiyoyin aurenku."

       "Madallah da ke, don ni haddar kaina ta daɗe da gogewa." 

       Shiru na yi ina nazarin abubuwan da suka faru a lokacin, sannan na yi murmushin da iyakacin shi leɓe tare da sauke ajiyar zuciya na ɗora daga inda na tsaya.


      _EDD na yana cika na ce da shi ya bari na koma wurin Ummata, saboda koyaushe zan iya haihuwa amma ya nuna ba zan je ba har sai na haifu. Domin ita kanta Ummar ta so a mayar da ni wurinta na haifu gabanta, amma babu kunya ya nuna ya fi so sai na haifu gidansa. Ba ta ja da tsauri ba ta bar maganar saboda ya fito ƙarara ya nuna ba ya so._

       _Duk da girmama al'ada irin ta Sakkwatawa haka ta haƙura, domin abu ne wanda kowa ya sani haihuwar farko a gida yarinya take yi. Wani lokaci ma da wuri ake komawa a yi ta dakon zuwan haihuwar._

       

      _Ranar da zan haifu, tun cikin dare na fara naƙuda, amma ban da bacci babu abin da yake yi. Sai idan na ji azaba ta yi mini yawa na ƙwala masa kira ya tashi yana jera mini sannu. Da ƙyar na ga asuba, zuwa lokacin na galabaita sosai ta yadda ko magana ba na iya yi. Ko da 'yan gidansu suka zo ban san lokacin da suka kai ni asibiti ba, saboda jinin da ya fara zubar mini ya sa na cire rai da duniya balle ganin abin da zan haifa._

       _A gurguje aka karɓe ni cikin sauri aka yi labor room da ni, a saman gadon ɗaukar marasa lafiya jini yana ta bin jikina. Cikin ikon Allah har an fara zancen yi minti aiki sai ga yarinya ta kunno kai. Nan take na haifo 'yata ba tare da cikina ya sha askar likitoci ba._

        _Bayan na samu kaina na ga an kimtsa ni tare da abin da na haifa. Ummata na fara gani sannan Inna Kulu da sauran 'yan gidansu Mukhtar, har da ƙawata Hafsa waton ɗiyar maƙocin Kawu Sale da muke kai ɗaya a nan Bafarawa Estate. Murmushi na bi kowa da shi cike da jin daɗin ganin kyautar da Allah ya ba ni. Mamaki fal raina tare da bin Mukhtar da kallo saboda ganin wasar bakin da yake yi, wanda alamu ya nuna fili ya yi farincikin da samun Bbyn. A raina na ce 'Ashe dai ana so ake kai wa kasuwa.'_

      _Kwanana ɗaya Asibitin ana ƙara mini jini, saboda jinina ya yi zubar da dole sai an ƙara mini da wani. Da dare aka sallame ni muka yi tsinke sai gidan Kawu Sale, a nan ma mutane suka fara tururuwar zuwa gani na tsakanin 'yan'uwa da abokan arziƙi._

       _Kwana huɗu da haihuwa 'yan gidansu Mukhtar suka kawo mana kayan fitar suna, kayan da suka janyo mana ce-ce-ku-cen mutane. Domin kala uku ce da kayan jarirai biyar sai wasu tarkacen da rashin su ya fi kawo su rana. saboda ba a kawo sauran kayan da Sakkwatawa suka mayar tamkar ibada ba. Domin babu kayan yajin da suka daɗe da camfi kansu, a kan duk maijegon da ba a ba ta su ba, ko lahira sai an biya ta su a gaban Allah. Surutun mutane ya sa Umma ta je kasuwa da kanta ta siyo tare da wasu kayan da ya dace a ce Mukhtar ne ya kawo su._

      _Ana gobe suna mutanen Kebbi suka zo, farinciki fal raina saboda ganin babbar ƙawata Asma'u. Wadda muka yi karatu tare tun daga matakin primary har zuwa Sakandire, ko a Jami'a mun yi makaranta ɗaya sai dai kowa da ɓangaren da ya karanta. Akwai shaƙuwa sosai a tsakanina da ita, irin wadda kowa ya san ta zai san ni, haka ma wanda duk ya san ni ya san ta a baki ko a zahiri, saboda ƙarfin abotarmu._

        _Ranar suna aka raɗa wa yarinya Ummu Salma,  an sha hidima sosai komai a wadace ma Sha Allah, saboda ƙoƙarin Ummata da Baba Sale har ma da Baba Ali. Domin sun yi namijin ƙoƙari wurin fitar da ni kunyar 'yan biki, saboda ɓangaren abinci da abin sha Alhmdulillah har rara aka yi da dare. Domin girka abincin ake yi wani kan wani, sai da sawun mutane ya ɗauke aka dawo jinyar jiki._

       _Da safe aka fara rabon tsokar abin sunan kusufa-kusufa lungu da saƙo. Saboda babu laifi Mukhtar ya yi abin kai gida, domin dabba biyu ya yanka amma sai da Umma ta dawo siyen ƙaramar tunkiya saboda mutanen kunyar da ba su samu ba._

        _Yan Kebbi kuma suna gama sallar zuhur suka fara sallama da mutanen gida. Don daman can sun haɗa kayan tafiya tun da sake aka dakatar da su domin a ba su nasu kaso. Sai da suka soye namansu sannan suka yi haramar tafiya, har raina ban so tafiyar Asma'u ba. Na so a ce ta zauna amma ta nuna mini wannan tafiyar da da ƙyar aka bar ta, saboda Babansu mutum ne mai tsattsauran ra'ayi da masifar faɗa tamkar ya ci babu. Amma ni duk da faɗan shi Allah ya haɗa jinina da shi sosai yake mutunta abotarmu._


       _Sai da suka isa gida sannan hankalina ya kwanta, domin lokaci bayan lokaci ina kiran su na ji sun isa ko suna kan hanya._

       

        _Na ci gaba da zaman jego a gidan Kawu Sale har yi arba'in, sannan na tafi Kebbi cike da jin daɗin ganin Baba Ali da sauran 'yan'uwa da abokan arziƙin da aka yi zaman mutunci. Satina biyu a can na dawo saboda matsin lambar Umma da Kawu Sale suke yi mini, a kan na dawo haka nan na koma gidan mijina. Sai dai su abin ba su sani ba, koyaushe muna waya da shi, amma bai damu da sai na dawon ba. Bayan wata tambayar da ya yi mini wadda ta sa na kasa tantance ina zancen shi ya dosa. Domin a lokacin da muka gama waya da Umma a kan dawowar sai ga kiran shi, na dauka cike da tunanin shi ma zancen da zai yi mini kenan. Sai ga shi na ji sabanin abin da zuciyata ta zata._

        "Telar nan taki da firij. Kina so a sayar miki da su kafin ki dawo?"

       "Kada a sayar domin idan na dawo zan fara koyon ɗinki, kuma zan dinga yin zoɓo da ƙanƙarar zaƙi na san yaran unguwar za su saya."

       "To" _Kawai ya ce sannan ya katse kiran, bayan mintina kaɗan ya sake kira yana yi mini gargaɗi a fakaice._

     "Yawwa! Ki bar zancen nan a tsakaninmu ba sai kin faɗa wa kowa ba."

        _Murmushi kawai na yi masa sannan na ce,_ "Wannan maganar ai ba ta kai na yi yamaɗiɗi da ita ba." 

       _Daga haka muka yi sallama tare da sanar da shi gobe zan koma Sokoto, sai dai ban ji ya yi murna ba balle ya yi zumuɗin dawowar ta yadda zan gane._ 

   

      _Tun da safe na yi sallama da waɗanda ya zama dole, sannan Baba Ali ya sa aka kai ni tasha tare da kayan alherin da na samu niƙi-niƙi. Saboda mutanen Sokoto da Kebbi akwai ƙara kuma akwai girmama baƙunta._ 

        

       _Sai dai abin da su Umma ta tarbe ni da shi ya kaɗar mini da 'yan hanjina, duk da ban bari na fito da firgicin a fili suka gani ba. Amma na shiga rashin natsuwar da ta janyo mini kiran Mukhtar babu shiri, saboda Inna Kulu ta sanar da ni,_

      "Mun yi ta zuwa a gyara miki ɗakinki ba a iske Mukhtar gida. Kuma an sanar da Mahaifiyar shi ta karɓi makulli a hannun shi idan muka zo mu karɓa, nan ma duk muka je haka muke dawowa babu makullin. A ƙarshe ma cewa ta yi da mu ya yi tafiya, kuma bai bar musu makullin ba.  Amma ya ba da haƙuri a kan ki koma gidansa shi ma zai dawo garin a ranar da kika dawo."

       

       _Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce ta bari na kira shi na ji yaushe zai dawo. Ni ma hakurin ya ba ni a lokacin da na kira shin, tare da saka mini ranar da zan koma domin shi ma a ranar zai dawo._

        _Kasancewar rana ba ta ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, hakan ya sa na tattara kayana na koma gidansu Mukhtar. Tare da rakiyar su Inna Kulu da Hafsa, sai wata ƙawar Umma da wasu mata biyu daga cikin dangin su Ummata da ke Dunguza._

        _Sai dai har tara na dare ta wuce goma ta doso Mukhtar bai dawo ba, dole suka tafi ba tare da sun kai ni ɗakina ba. Ni ma a nan ɗakin Mahaifiyar shi bacci ya kwashe ni, kasancewar Ummu Salma tana hannun matar Baban shi._ 

        _Cikin bacci na ji muryar shi na yi firgigit na tashi, ya iso inda nake cike da mayalwacin farinciki a kan fuskar shi. Ni ma sosai na ji daɗin ganin shi har raina, ya saɓa Ummu Salma a kafaɗar shi muka yi ɓangarena. Makulli ya ba ni sannan ya miƙo mini ita ya ce; bari ya je ya kwaso mini kayana da muka baro ɗakin Mahaifiyar shi. Ban kawo komai a raina ba, kawai na buɗe na shiga da guntuwar sallamata, sai dai babu shiri na zaro ido tare da kwarma ihu iya ƙarfina ina faɗin,_

       "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!" 






Shin me ke faruwa ne😨 na yi nan ni ma🏃🏻‍♀️

No comments

Powered by Blogger.